﻿💫A MAFARKI NASANTA 💫
   In my dream I know her
                   By
    Pha'eezah almustapha
Daga alkalamin✍️✍️Fa'eeh Bungudu

BISIMILLAH RAHAMANI RAHIM
Wanan shine litafina nafarko Dana fara wallafawa Allah Ina rukonka daka bani damar kamalashi lafiya kamar yanda nafarashi lafiya👏

*PERFECT ESSENTIAL  WRITER'S ASSOCIATION
            💫P.E.W.A💫
Home of Perfect Writer's together we stand🤝

     ESSENTIAL WRITER'S 📚🖊️*
Pen 🖊️is mightier than the sword🗡️*

Dedicated to my lovely sis Laila Almustapha Murai💔

Yaa Allah ina rokon  ka kabani damar rubuta abunda Al umma zasu yi aiki dashi kuma su Amfana, kabani ikon rubuta shi cikin koshin lafiya na kammala shi lafiya👏👏👏            
Warning!!!Banyarda wani ko wata su juyamin labarina ba ta kowace siga batare batare da an nemi izini na ba wannan dokace kuma duk wanda yayi ban yafe ba  wannan labari kirkira ne bada gaske bane duk wanda yayi dai dai da labarinsa to yayi hakuri akasine.                    
  Daga cikin abunda littafi na ya kunsa             *tausayi*                                                              *zumunci*                                                         *zazzafar soyayya*                                             *sarauta*                                                               *cin amana*                                                       *ta,addanci*          

DASUNAN ALLAH MAI RAHMA MAIJINKAI

EPISODE 1️⃣
FREE PAGE1️⃣

Natsatssiyar  budurwa ce ke tafiya anatse bata kallon komai face inda take sanya kafafunta, tayi nisa acikin tafiyarta  kenan ta tsinkayi muryar wata budurwa na kwala kiran Halee! Halee! da jin wannan murya ta budurwar dake kwala kiran Sunan halee ko ba,a fada mata ba tasan khady ce tsayuwar ta da minti biyu sai ga khady ta iso inda take atsaye.
 Isowar khady keda wuya ta furta haba Halee kinsan bakya da issashiyar lafiya ya za,ayi kije Aiken baba ta  ta maimakon ki fada mata gaskiyar cewa baki da lafiya nasan zata k'yaleki ni sai intafi  kinga ko yanzu gudo wa nayi bayan bayan tashiga bandaki,nasan da kin sanar mata da ni sai intafi koh haka ke da dadi ga uwar rana gashi bakya da lafiya,har taga ma mitar ta  kyakkyawar budurwar nan da aka kira da halee bata tanka mata ba.. Daga ni dai yarinyar miskila ce😄  chan bayan kamar minti biyu haka ta cigaba da tafiyar ta kamar bataji abunda khady ke fada  ba duk da kuwa tana jinta rass kuma tasan tabbas ko ba,a fada ba khady gudowa tayi tabiyo ta.
Da khady taga alamar ba tsayawa zatayi tabata kudin  aikar ba  na baaba tsaibe,kuma taga alamar yan miskillancin sun motsa  dole haka tabita suka cigaba da tafiya  atare har suka iso kantin da zasu yi siyayyar ta kayan miya 
Sallama sukayi atare   amsa musu sallamar tsohon dake tsaye akan tebir na kayan miyan yayi cikin sakin fuska Dan dama baba tsohon yasan su musamman halee ya saba da ita sosai tunda kusan kullum sai an aike ta yin cefane da sauran aikace aikacen  akasuwa.  
 Washe baki  tsohon yayi yana furta a,ah Haleematu sadiya ce kayataccen murmushinta tasaki jin ya ambaci cikakken sunanta  Wanda mutun daya ne ke kiranta da wannan Sunan sai kuma mutun daya Wanda bata San ko wanene shi agareta ba Amma tabbas aka ambaci cikakken sunanta tana jin wani iri ajikinta
Muryar baba tsohon ce tadawo da hankalinta agaresa yana furta na nawa za,a bada cikin Dan murmushi ta furta baba tsohon ina wuni lafiya,ita ma halee haka amsa musu yayi duka yana dariyar halee aransa najin ga tambayar da yayi mata ga abunda ta furta masa shiyasa yarinyar tashiga ransa Dan akwai tarbiya gata kamila anatse kara mai maitawa yayi" na nawa za,a bada"cikin Dan yin kasa da kai ta furta acikin zazzakar muryar kamar ana busa sarewa ko algaitu gata da sanyi Wanda intana magana zakaji har tsikar jikin ka natashi na Dari uku da ta furta ne yasanya ni dawo wa daga sumar tsayen danayi tun lokacin da ta buda baki ta gaisar da tsohon.
Toh baba tsohon ya furta aleda ya saka musu baka ya mika musu sallama sukayi masa sukayi wucewar su, suna tafiya khady na zuba uban surutu alokacin da ita kuma Halee take ta zullumin komawar ta gida Dan tasan gamuwar  su da Babah Asabe bamai kyau bace dan tasan sai ta mata fadan dadewar ta duk da  dama ta saba,Amma yau da yakasance batajin dadin jikinta tana fama da  matsanancin ciwon kai sai take jin shakkun yadda zata iske gidan,tana cikin wannan tunani sai ga hawaye shar😢 a idanunta gwanin tausayi Khady data lura da yanayin da take ciki ne duk da ba bakonta ganinta hakan Dan danan hankalinta yatashi Dan tana mugun son halee kamar jinin jikinta,da tausayinta cikin tausayinta ta furta haba Halee meyafu kuma, dan Allah kitsaida hawayen nan suna Sosa mun rai kuma kinga kan hanya muke kiyi hakuri nasan damuwar da kike ciki bata wuce sanin ko ke wacece bah da damuwar baabah ta 'baaba Asabe' kiyi hakuri  in sha Allah komai zai zamo tarihi Halee nah hawayenta ta share mata wayenda ke tsiyaya a I danunta tana girgiza mata kai alamar ta tsayar dasu da kyar ta tsayar da hawayen ta ganin damuwa kwance akan fuskar Yar uwarta!tafiya suka cigaba da yi kowa da abun da yake sakawa aransa,babu Wanda yakara furta uffan har suka iso gidan,
Dan madaidaicin gidane suka tsaya kafin su shiga cikin dar dar musamman Halee gidane dai dai na talaka mai rufin asiri ginin bulo da filista zauren gidan suka tsaya suna shawarar Wanda zai fara shiga domin gudun abunda zasu tarar dakyar dai dukansu sukayi shahadar shiga da sallama abakunan su
Sallamar su ta  ta katse ganin  Baba Asabe na mitar rashin dawowar Halee akan lokaci da kuma fitar Khady bada saninta ba,
A hankali halee take ta durkusa gurin Yar matashiyar matar da bazata wuce shekara talatin da uku ba a duniya!Baba Asabe kenan wadda Sunan ta yake Lauratu amma mafi yawan mutane suna kiranta da Asabe saboda masifarta da ankira Baba Asabe za,a San itace Dan Sunan ta kaf ya bace.    
Cikin sanyin muryarta da yazame mata jiki tace baaba ga kayan miyar kinga na dad'e koh wallahi Baba tsohon ne mun tarar da layi  agurin sh...uwar hararar da baba Asabe ke sakar mata ce tasan ya ta yin shiru badan ta shiryawa hakan ba,dama kanta adone yake dan bata son kallon cikin idanun manyanta musamman ma na Baba Asabe ....taci karo da hararar da take sakar mata,bata ida ganin tsawon hararar ba ta kara done kanta kasa cikin tsoron abun da zai biyo baya..
Kiran Sunan Allah take yi a zuciyarta Dan tasan yau tata takare sai ta sha rankwashi akai da gori kala kala da zagin da bata so zuciyarta ce taji tsinke tausayin kanta da kanta yakamata.
Bata ida gama tunaninta ba ta tsinkayi muryar Baba Asabe nama khady fadan binta da takeyi abaya inta aiketa duk da kullum haka suke muddin Baba asabe ta aiki Halee to tabbas in Khady tadawo sai ta bita sundawo tare koda kuwa dawowar su daga makaranta ne aka tura Haleen sai ta yi sand'a ta bita...
Baba asabe ce take furta wallahi Hadiza ki shiga taitayinki Dan ubanki na fahimci bakya game zancen da nake maki ace ke kullin sai kinsaka ni yakar baki ehh~bakinta har kunfa yakeyi saboda masifar da ke cinta dama Baba Aabe masifaffiya ce ta bugawa ajarida.

Wai nikam nace dama haka masu suna Lauratu suke ne??😂 
Hankalin khady (Hadiza) yayi dubun tashi bata kanta takeyi ba Dan tasan karshen masifar kan halee zai kare.             Ahankali ta furta innata kiyi hakuri ke dallah rufe mun baki sha shar banza kawai ana miki gata kina botsarewa,inji cewar Baba Asabe , aikullun haka kike cewa ayi hakuri tau Dan ubanki ki kara kiga yadda yadda zanyi da suyar namanki agidan nan takai karshen maganar tana ban kamata harara  
Kiwuce ki cire uniform dinki kizo ki Debi ruwan zafi gasu chan nadora miki amadafa.
Toh Khady  ta furta cikin tutse bakinta mai makon ta wuce sai ta tsaya taga yadda za,a kwashe da Halee tana jin tsoron tashin ciwon Yar uwarta Wanda take ganin hard a damuwa kesanya tashin sa,tana mugun son ta da tausayinta, gashi yanzu haka tana fama da kan daya zame mata al ada dan duk yatashi tana wahala sosai wasu lokuttan har suma takeyi inyatashi saboda yadda take samun high temperature.
Bayan Baba Asabe tajuyo kan Halee wadda ke durkushe har yanzu bata daga duk da yadda rana ke gasata ga sumintin yadau zafi  hawaye take  zubarwa na tsoron masifar ta Baba Asabe Dan tasan kanta abun zai dawo ya kare ga ciwon kanta da ke ta kara hawa jikinta sai kara dumewa yake yi da zafi..hawayene  shar suka zubo a I don  ta suna sauka abisa kyakkyawar fuskarta.

Mu hadu a next page domin jinya zata kaya tsakanin Halee da Baba Asabe
Me kuke tunani akan Halee??
Kucigaba da bibiyata domin warware muku duk wani tunanin ku.✌✌ 
Yawan like dinku da comment shi zai tabbatar mun da kuna bibiyata,in har naga comments da like da yawa zan kara muku yawan pages.
Nasan zaku ga chanji na sunan Baba tsaibe da yakoma Asabe ga wadanda suka fara karantawa babu editing      

💫A MAFARKI  NASANTA💫 
     in my dream I know her 
               By 
      Pha'eezah Almustapha 
Daga alkalamin✍️✍️fa'eeh Bungudu

   *PERFECT ESSENTIAL 
    WRITER'S ASSOCIATION 
      
        💫P.E.W.A💫 

home of perfect writer's together we stand 🤝           
   
     ESSENTIAL WRITER'S 📚🖊️*
Pen🖊️is  mightier than the sword 🗡️*
              

  EPISODE1️⃣   
  FREE PAGE2️⃣&3️⃣

Typing📲📲📲
  
Gefen hijab dinta tasanya ta share hawayenta   muryar Baba Asabe ce tadawo da ita daga maganar zucin da takeyi 
Da masifa take furta munafuka algunguma wallahi bari kiji duk ranar da kika kara bari Hadiza tabiki  in na aike ki wallahi ko na lahira sai yafi ki jin dadi  sha sha marar asali kawai tsintacciya yar gaba da fatiha  wadannan kalmomi  da Baba Asabe take yawan furta mata suna daga mata hankali sosai fiye da zaton mai tunani   duk ranar da Baba Asabe ta furta su agareta sai tasha kukan ta ita kadai alokacin kuwa Khady ce kawai ke iya lallashinta.

Har tunani take yi anya kuwa ita badaga sama tafado ba,wasu  lokuttan kuma takanyi tunani kodai ita din yar gaba da fatiha  ce kamar yadda Baba Asabe ke yawan furta mata,tunani barkatai dai ke shiga akanta aduk lokacin da ta tunano da kalmomin masu muni agareta sai dai kawai takori shaidan da Addu,ar neman tsari  daga sharrin zuciya.

Dan tun Tashinta gidan wayennan kalmomin su suka bayyanar mata da ita din wacece agidan Baba Adee tun alokacin da ta fara mallakar hankalinta ta fahimci cewa ita din ba jinin Baba Adee bace da Baba Asabe  sai dai duk da cewa ta fahimci komai  akai bata taba gigin tambayar dayan su asalinta ba dan gudun maganar da zataji wadda zata iya saka ta rasa  rayuwar ta wadda ayanzu take maleji da ita,Barema   koda  zata tambayi Baba Asabe baza ta iya sanar mata da komai ba domin koda Baba Adee ya kawo Halee gidan bai sanar da ita komai akanta ba,yadai sanar mata ya tsinceta ne akan hanyar shi takomawa gida tsakin gusau da furfuri dake jihar zamfara wannan kenan.
 Cigaba....
Maganar da  Baba Asabe ce keyi tadawo da ita daga dogon tunanin da tashiga na munanan kalmomin da Baba Asabe ta furta agareta  Baba Asabe ce ke furta sakarya munafuka  ana magana kina sunne kai kamar takwarai  sha sha sha ballagaza kuma wallahi kinji narantse na kara aikarki kika dade sai kinci ubanki, mtssw taja uban tsaki tawuce warta fuuuu.

  Kamar ance tajuya tahango Khady tsaye itama tana tsiya yar da hawaye kamar yadda itama Halee take zubar da nata hawayen 
Yau nina naga ikon Allah inji cewar Baba Asabe  wai ke Hadiza Uban me kika hada da yarinyar nan ne ehhh  sha sha wuce kiban guri ko in tattakaki anan mtsww tana sanya hannu ta warci ledan kayan miyar ta shigewar ta madafa  tana mitar ita kadai,Ta dora sanwar rana dan dama duka aikin gidan Halee ce keyi toh yau ma anyi lattin dora girkin ne kuma tasan Baba Adee   yana  nan dawowa bada  jimawa ba shiyasanya ta kyaleta bata  tilas ta mata yin girkin ba. 

             Alkalamin✍️✍️
💫💫fa'eeh bungudu💫

💫A MAFARKI NASANTA💫

Bayan shigewar Baba Asabe a kitchen Khady tayi sauri ta matso inda Halee ke durkushe tayi zukunnin rakumi cikin uwar ranar da ta bude tana  ta faman zubda hawaye ga hannunta dafe da kanta dan tun lokacinda Baba Asabe ta zage ta  da kalmar dan ubanta kanta yakara sarawa bayan jin wadanchan kalmomin na farkon Baba Asabe take yawan furta mata na marar asali tsintacciya bayansu babu abunda ke kona mata rai kamar azagi mahaifinta da mahaifiyar wanda ko da za,a yankata bazata  iya  cewa ga yadda kamanninsu yake ba ko tana da iyayen oho?Amma duk aka zagesu tana jin bakin ciki marar misaltuwa wanda bazai fadu ba,tana sonsu duk da bata taba ganinsu ba ko jin labarinsu.
Dafa kafadanta da Khady tayi ne yadawo da ita daga dogon tunaninta dakuma kara gudun ruwan hawayenta wanda zuwa yanzu kukanta yafara karfi har da shessheka dago lulu eyes din ta tayi wayenda suke dauke da zara zaran eyelashes masu tsarin kyau masu dauke da kwarjini farare tass dasu kwayar idonta har wani walkiya take yi na farin cikin idanun nata,A yanzu kuwa sunkoma jajaye saboda damuwa da ciwon kan datakefama dashi  ga kuma kukan da tafara yi.
Zararan eye lashes nata sunkara curewa guri daya saboda ruwan hawen da suka jika su,Khady kuwa tunda suka hada idanu da Halee taji guiwoyin ta sun sage dan kuzarin datake dashi taji ya gushe,tausayi  Babbar kawar tata kuma  wadda tazame  mata yar uwa wadda takejinta kamar tsoka da jininta.
Ahankali ta furta Halee! kanta ta kara dagowa akaro na biyu  bayan mayar dashi kasa da tayi  tana tsiyayar hawaye da idanu Khady tama alamar ta tashi suje daki tunda tasan yanzu bata bukatar wani dogon zance saboda ciwon kanta gashi taji jikinta yakara  daukar zafi sannan in Baba Asabe ta iskosu wata masifar ce sabuwa wadda kuma take tunani ayanzu kwakwalwar Halee bazata iya dauka ba,Hannunta ta mikamata Halee bata ce komai ba takama  hannun Khady ga gamn ta rike.
Ahankalin suke takawa  kowa da tunanin da yake yi azuciyarsa harsuka isa dakin da yake chan gefe mallakinsu su biyu  
Baba Asabe da duk taga komai .....✍️✍️✍️

💫A MAFARKI NASANTA💫             
daga Alkalamin✍️✍️
    
💫fa'eeh bungudu💫
please like share & comment

💫 A MAFARKI  NASANTA💫
    in my dream i know her  
                 By              
Pha'eezah almustapha
    Daga Alkalamin ✍️✍️                
  💫fa'eeh bungudu💫

Dedicated to my lovely sis laila Almustapha murai💔

 *PERFECT ESSENTIAL   WRITER'S   ASSOCIATION
        💫P.E.W.A💫
Home of perfect Writer's together  we stand🤝

        
ESSENTIAL  WRITER'S📚 🖊️*
pen 🖊️ is migthier than the sword🗡️*

EPISODE 1️⃣
FREE PAGE4️⃣

   Typing📲📲📲

 Bata ce musu  kala ba har suka shige dakin tsaki taja mtssw tana furta yarinya  sai kace mayya  da shegen taurin ran tsiya ace duk wahalar da  nake  gana mata  bata sanya ta guduwa  daga gidan nan ba  mtssw takara jan wani tsakin tana furta mayya kawai tun randa tazo gidan nan Baban Hadiza samun shi ya ragu gashi komai  shi  shalelensa dan naman miyar ma da muke samu da yawa ya ragu ada daga ni sai hadizata yanzu kuwa  takai karshen maganar cikin jan dogon tsaki wanda Yafi nadazu tayi shigewar ta daki tana cigaba da masifarta ita kadai
  
Nikam nace Baba Asabe shi naman miyar halan dai bakisan sauyin ubangiji ba 😇

  💫fa'eeh bungudu💫
 
Halee da Khady shigar su daki keda wuya dukkaninsu suka samu  guri suka zauna kowa rai ba dadi musamman khady wadda take jin haushin abun da mahaifiyarta keyiwa Haleen.
    Matsowa  Khady tayi  inda Halee ke shingide gefen katifarsu  data sha gyara kamar gadon Amare🤩

Zama kusa da ita tayi tare da kamo  Hannunta daya ta furta cikin tausayin Haleen kiyi hakuri kibarwa Allah  komai   ninasan Babata bata taba kin kiba har cikin ranta kawai dai shaidan ne ke zugata da kuma  sharrin wani yanki na zuciyarta  dan yin shiru tayi kafin tacigaba da magana  Halee!  dago kyakkyawar fuskarta tayi ta kalli  Khady  ....banason Son ina ganin damuwa abisa kyakkaywar fuskar nan taki,Mai sanya samarin zamfara hadarin titi😉
      
  Tunda Khady tafara magana bata tanka mata ba amma maganar ta takarshe sai da tasaka ta yin wani kayataccen murmushi wanda har sai da two side  dimple dinta dana kasan gemun ta suka lob'a  gwanin burgewa.
 
Itama Khady Murmushinta  tasaki mai  kyau wanda har cikin ranta yake nuna tsantsar  farin cikinta naganin murmushin yar uwar tata Halee wanda yake ba kullum take yinsa ba duk da fuskarta irin ma,abociyar yalwar murmushi ce kamar ta junaid Abban sojoji😄Amma  damuwa ta hana ta bayyanar da  asalin annurin Fuskarta.

💫Fa'eeh Bungudu💫

Dama Khady tasan tabbas ta furta mata irin wannan kalmar sai ta yi murmushi,ita abunda ke sakata yin murmushin gani take bawani kyau ne da ita ba kamar yadda  Khady ke yawan fada mata da kuma classmate nasu,saboda ba kullum take samun damar duba fuskar ta ta ba  Amadubi  dan cewa take bashine agabanta ba,ita gani take kyawon da duk ake fada tana dashi nabanza ne saboda kyawu ba asali baida amafani acewarta,ita yanzu sanin asalinta ya fiye mata kyawun komai agareta a cikin  duniyar nan.


So dayawa  in Khady ta matsamata da cewar tana da  kyau na fitar hankali takan cemata "kyawu ba asali babu amfani" kuma  da ta  fadi wannan kalmar sai ta fashe da  kuka Khady tayi  ta aikin lallashinta   Yanzu ma khady bata matsa mata da  wata maganar ba dan gudun karamata damuwa.....

 Wash hannu nah wallahi typing wahala 🥹
 kuyi manage da wannan ba yawa

    Mu hadu a next page domin kara warware muku  matsayin Halee agidan Baba Adee
 
Kuyi hakuri  da sauyin  dakuka gani🙏

Masu comment da like ina godiya🙏🥰

khadseen🥰
Halimatu  B Auki🥰

💫fa'eeh bungudu💫
Pls like share & comment



💫A MAFARKI NASANTA💫
     in my dream i know her 
                  By 
 Pha'eezah almustapha 
     Daga Alkalamin✍️✍️
💫fa'eeh bungudu💫

Dedicated to my lovely sis laila Almustapha murai💔

   *PERFECT ESSENTIAL  WRITER'S  ASSOCIATION
                💫P.E.W.A💫
Home of perfect  Writer's together  we  stand 🤝
    
       ESSENTIAL WRITER'S 
📚🖊️*
Pen🖊️is mightier than the sword 🗡️*

    Proud of my  first  my novel👌
   
*JIN JINA TA💪💪 MUSAMMAN ZUWA GA BABBAR KUNGIYAR MU*
             💫P.E.W.A💫
Ina alfahari daku musamman uwayen gidana🏢

*MHIZ BAREEMAH*  (marubuciyar yan biyu macizai ne) the twins snake🐍🐍

*OUM AMJAD*  (marubuciyar yan biyu)the twins👭
  


EPISODE1️⃣
FREE PAGE5️⃣


TYPING📲📲📲 


Kawar da shirun nasu tayi ta hangar  ta hanyar furtawa Halee kitashi ki watsa ruwa  bari indebo muna ruwan zafi tana gama fadar haka ta cire hijabin uniform dinta tayi waje.

Bayan fitar ta daga dakin Halee ta tashi daga kishingid'en datake tacire hijabinta ta nad'esa Sa tasanya acikin  acikin sip dinsu wadda Khady bata ya mutsa ba,sannan ta  jawo zanen da take wanka dashi tayi  tadaura bayan ta cire kayan jikinta tasanya acikin basket na Tara  datti   Dan karamin hijabinta Wanda take wanka dashi tasanya ta cigaba da gyara kayan da duk suke ahargitse  acikin sip dintasu Wanda Khady ce ta ya mutsa su dazu da zataje  makaranta..

Tana cikin gyaran sip d'in ne sai ga khady tadawo da ruwan acikin small bucket  bayan ta amsa mata  sallama ne 
Ta Tsinkayi Muryar Khady Tana Furta  nidai Halee kibar gyara kayan nan kinga baki da lafiya duk da naga yau jikin naki da sauk'i nazata sai munje asibiti ~takai karshen maganar fuskarta da alamar damuwa 

Hararar wasa wasa Halee tasakar mata tana idasa lankafe  hijab daya daya rage saura ta gama,Ahankali ta juyo ta dauki ruwan zafin da Khady ta ajiye mata  tare  da furtawa  Khady  karki damu Sisi nah  nafara zama strong women tayi maganar ne cikin sanyin muryarta da yazame mata jiki takai karshen maganar tana sakar mata kayataccen murmushinta mai Sa maza👨 had'ari  atiti😎
----------------------------- 💫fa'eeh bungudu💫

Itama Khady murmushin ta mayar mata dashi  bata k'ara cewa komai ba ta kama hangar da zata sadata da  d'an madaidaicin toilet dinsu  dake cikin dakin  har ta kusa  isa ta tsinkayi muryar Khady na furta "Halee  kibari inzo  in had'a miki ruwan tunda naga baki da karfin jiki tafiyar taki  takara. Zama slowly"
Ko ayanzun ma murmushin Halee tasakar mata Wanda har kyawawan hakora ranta farare Tass suka bayyana gwanin burgewa,itama Khady Murmushin tayi tana furta ohh! Yau su Anty Halee yan sarautar sun motsa kenan girgiza kanta tayi tana kara sakin murmushi na mamakin halin Yar uwarta na rashin son yin magana.
 
   Itama cire uniform din nata tayi tadaura zanen da wankanta tayafa katon mayafi tana ficewa daga dakin
-------------

 Tun akofar dakin nasu tafara magana cikin farin ciki take furtawa Baba Adee sannu da zuwa  saboda tajiyo muryar shi lokacin suna magana  da Khady.

        A bangaren Halee kuwa tana shiga toilet din ta fara gudanar da wankanta cikin natsuwarta da tazame mata jiki duk da yadda ranta yake ba dadi....

"Dady sannu da zuwa" ya hanya?Muryar Khady ce ta ratsa tsakar gidan nasu har zuwa barandar da wannan dattijo yake azaune.
Murmushi  wannan dattijon yi har takara so inda yake dattijon kirki Wanda sunan shi yake Abdul rashid  Amma anfi saninsa da Baba Adee Wanda akalla zai kai shekara hamsin aduniya.
 (wannan suna Khady ce tafara sanya masa shi  alokacin tana karama  bata iya fadin Dady kamar yadda Halee ke fadi sai ta mayar dashi Adee Wanda ganin  haka yasa itama Halee ta mayar dashi Adee jin Yar uwar ta na kiransa haka)
Sai kuma sunan yabisa har na waje suka kara masa da Baba wannan kenan..

Har ta durkusa agabansa Murmushi ne kwance akan fuskar Sa ganin yadda ta turo baki gaba nak'in amsa mata sannu da zuwan da ta masa,Baba Asabe ce dake tahowa da amadaidaicin kofin silver domin kawo masa yasha ta furta kekam dai Hadiza meyake damunki ehhh!daga dawowar Sa sai fara turar masa baki kamar wadda aka daka tana  magana tana tsiyaya masa ruwa akaramin cup shima na silver mai kyau

Kurb'a ruwan da Baba Asabe ta mikamasa kurba guda yace rabu da ita kinji dije,aiko ida rufe bakinsa baiyi ba Khady takara turekke bakin nan gaba....

Dariya yayi wadda take fitar da suffar shi ta magidantan kirki yace ke koh:khadija Dan Ankiraki da dije ai bawani abu bane suna ne mai dadi koh! yakai karshen maganar yana Dan yin murmushi,ganin tayi shiru  batace komai ba,yace nasan  fushin da like yi nafarko ban karba miki sannu da zuwan ki ba na biyu na kiraki da sunan tsofaffi yakai karshen maganar yasa cikin yin Yar karamar dariya wadda har far in hakorinsa na Makkah ya bayyana sannan yacigaba da magana kin san Khadija nace kibar yimin sannu da zuwa tundaga nesa shiyasa na kyaleki  na biyu kuma ayi hakuri laifi nane shalelen Laure....yana murmushi
Baba Asabe dake gefe itama  murmushinta yi,Itama Khady murmushin ta saki jin ankira ta da shalelen Babarta cikin dariya ta furta hard a ta dadynta dukan su dariya suka sanya.
Maganar Baba Adee ce ta dakatar da da riyar su Wanda maganar bata yima Baba Asabe dadi har fuskanta ya nuna,inda yake furta "yake cewa ina Shalele ".................
   
Yawan likes dinku da comment shahizai Sa Ku samu page biyu arana 

*A mafarki nasanta *📒
     Daga Alkalamin 
  💫fa'eeh bungudu💫
 

 Mu hadu next page✌✌
  Dan jin cigaban maganar ta Baba Adee
Dakuma jin Amsar da Khady zata bashi,   nasan kun matsu kuji asalin Halee
------------------
Kucigaba da bibiyata ahankali zan warware muku duk wani sashe na  littafina....
   WASAN YANZU AKA FARA👏

Kuyi hakuri ba editing domin dazu sai da nagama wahalar typing gaba daya ya goge.
  
Pls like share and comment.

💫A MAFARKI
 NASANTA💫
In my dream I know her 
             By 
Pha'eezah Almustapha 
    Daga Alkalamin✍️✍
     💫Fa'eeh Bg 💫
   
Dedicated to my lovely sis Laila Almustapha
 Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION
           💫P.E.W.A💫
Home of perfect essential writer's together we stand🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️*
Pen 🖊️is mightier than the sword🗡️*


EPISODE1️⃣
FREE PAGE6️⃣
   

dama na fada muku page dinku na friday sai yau to ga alkawarinku nan na cika✌️✌️

TYPING📲📲📲
 
Khady cikin murmushi ta furta tana daki na barota ta shiga wanka kai yad'a ga mata alamar gamsuwa,firarsa ya cigaba da yi da yarsa cikin lumana yana tambayar ta ya   karatunsu  na islamiyya da na boko tana bashi amsa  da alhamdullillah, masha Allah sai akara dagewa kinji Ya furta cikin jin dadi,kai Khady ta d'aga masa tana furta in sha Allah  Anan take sanar masa da Halee bata je ba yau,Assha!Assha! meya hanata zuwa injin dai ba ciwon kanne nata yatashi ba...Yakai karshen maganar cikin nuna tausayinta kara furta wa Khady yayi tun yaushe yatashi ?tun dazu da asuba,tashi ki kira mun ita in ta fito tau tace sannan ta tashi ta wuce dakin nasu domin kiran Halee.
     
  💫Fa'eeh Bg💫

Kanshi ya juyo dashi gefen da Baba Asabe take Yana furta Laure shine baki gayamun ba tunda nashigo,Baba Asabe da tun da tun dazu take cike da jin haushin shi nakiran Halee da yayi da shalelensa duk da bayanzu ne tafara jin yana kiranta haka ba tun tana karama,Dan bata son  yana nuna wa Halee soyayya fiye da Khady duk da yana kamantawa Acewar ta yar tsintuwa ba "ya bace,dakyar ta bud'a bakinta tabashi amsa  saboda  haushi ga tsoron ta nuna mishi  taji zafin maganar da yayi mata dakuma Kiran Halee Shalelensa,Haba Baban Hadiza yanzu fa ka dawo,ruwa kadai kasha ni dama yanzu nake  niyyar sanar maka  takai karshen maganar cikin danne wani  kololon bakin ciki da yataso mata,niyya ya maimata abayyane yana gyad'a kansa  cikin alhini ya nagayamiki duk randa ciwon shalelena yatashi ki rika kirana awaya in ba nanan sai inturo nurse kamal ya duba ta Amma da yake ita ba Khadija bace sai kike yin biriss da lafiyarta,ace kullum sai na maimaita miki maganar  cewa ita din amana ce ta Allah agare mu,Amma na fahimci bakya ganewa kuma na fahimci  har yanzu na baki dauke ta amatsayin yarki ba dan ina da tabbacin da Khadija ce keda wannan lalura  haka da kin kasance mai kulawa nasan da gudu zaki sanar mini in ya tashi  amma dan rashin Amma ni kike shaida ma wai yanzu kike da niyyar sanar mini,nasan kuma da khadijan ce da tun da asuban nan kinkira kinsanar mini,nasan kin sani keda kanki kika karbi amanar yainyar nan ba wani ba dan haka kiji tsoron Allah ki kara riketa da Amana.
  Duk wannan maganar dayake kanta nakasa dan tasan yau ta dan ballo wani yanki na fad'ansa,ita inbanda tasan duk randa Halee bataje makaranta ba  ciwon ta yatashi da bazata san bata da lafiya ba,tunda kosu yaran sun sani ko sungayamata babu abunda take iya yi face ma tabi Haleen da zagi  ko gwacine,batun yau ba Halee na rashin lafiya Amma Baba Asabe bata kiransa tasanar masa in baya gida da yake ba,a garin yake aiki ba in yatafi yana kwana biyar ko sati kafin yadawo shiyasa wasu lokuttan har ta gama jinyarta bai sani ba.
 Maganar shi tadawo da ita daga maganar zucin da takeyi....Yana furta wallahi Laure ki guji b'acin raina izuwa wannan lokaci ransa yakara baci ya hasala jin saoboda shirun  da tamasa,Cikin danyin kasa da kai Baba Asabe ta furta Baban Hadiza Allah yabaka Hakuri,bai tanka mata ba sai ma cigaba da maganar sa da yayi yana  furta baki san girman  Amana ba Laure ba shiyasa Amma zanyi maganinkin dan bana son kikawo mini shirme cikin gidana dan haka kikiyayi b'acin raina karki kai ni baango ...........
Sallamar su  Halee ce ta dakarar shi daga sake yin magana,Assalamu alaikun dady nah 
Halee ce ke ke maganar da murmushi kwance  abisa kyakkyawar fuskarta kyau da annuri  wanda ke nuna farin cikinta na dawowarsa gidan,cikin shigarta ta wata doguwar riga yadi pink mai taushi da d'an madaidaicin hijab dinta fari wanda yakara haska farar fatar ta wanda har kashe ido take yi  kamar  zinari acikin azurfa,inka kalle ta kyakkyawar fuskarnan sai  sheki take yi kamar wankakken gold  gwanin burgewa kai bazaka ce tana da daamuwa....
                         
               💫Fa'eeh Bg💫

Wslm  Halimatu Sadiya mai tagwayen suna kuma shalelena  inji cewar Baba Adee cikin farincikin ganin ta yake furucin murmushi kwance afuskar shi shima.
"sannu da dawowa  ya  hanya" ? inji Halee tana kara sakin kayataccen murmushinta jin yakira cikakken sunanta wanda kamar ga bakinsa aka rada sa,kuma tana jin dadi  yakira ta da hakan,Alhmdllh  lafiya qlau hanya yakarfin jikin ki ance baki ji dad'i ba, cewar Baba Adee,ehhh naji sauki alhmdllh ai har nasha magani na yanzu kafin in fito,d'anyin shiru  tayi tuna yadda tasha maganin wanda sai da Khady tace zata hada ta da dady ne sannan tasha shi dakyar kamar tayi kuka dan ta tsani magani ko allura,Dan kallon khady tayi wadda itama ita take kallo jin yadda take bayani kamar ba sai da ta tilasta mata ba,kawar dakanta tayi daga kallon Khady tana maida hankalinta ga Baba Adee wanda ke furta masha Allah haka ake so ai har ina maganar akira likita ko muje asibiti 
Murmushi tayi tana yin kasa da kanta wanda har kyawawan hakoranta farare tass suka bayyana gwanin burgewa  tace Naji sauki dady kuma sosai,murmushi ya karayi yana furta to madalla Allah yakara Afuwa,Ameen Halee da Khady suka   amsa, yakaratun su da makaranta  ya tambayeta kaamar yadda yatambayi Khady,Alhmdllh ta furta,kara  furta mata yayi ya gidan kuma dan shiru tayi sai kuma cikin yanayin sanyinta ta furta   lafiya  lau kai yajinjina  kawai batare da yakara furta komai,Baba Asabe ce da tagama girkinta na jallof din taliya da taji alayyahu,Ahankali tasauke wanda ta zubowa Baba Adee agaban sa cikin wani filet na tangaram irin  na da mai kyau tana furta Baba Hadiza ga abincinka nan tayi maganar fuskar ta sai sa sai sa ba fushi ba murmushi dan bataso tana wani abu yakara  hawa,wadda  tun lokacin da ta samu su Khady sukazo gurin ta bar wurin tare da kayansa ta kai masa daki sannan ta wuce kitchen.
       Bayan ta aje abincin ne ta koma ta debo masa ruwa na randa masu sanyi acikin jug mai kyau na kofin silver sannann  tazauna,bai cemata komai ba yajawo  filet din da ta aje agabansa yadora gabansu Halee yana furta kuje ku wanko hannayenku kuyi bisimllah muci abinci koh cikin  farin ciki suka amsa masa da tau,Baba Asabe  ce tayi karaf tana da niyar da katar dasu tana  furta gana su chan akitchen na zuba musu suje su dauka,hannu kawai yadaga mata yana kara mata maimaita  musu da suje su wanke hannayensu,wanke hannayen su keda wuya suka fara cin abincin tare dashi bayan duk sunyi bisimillah abayyane yaji su suna ci da hannu shi da spoon,cikin natsuwa suke cin abincin su tare dashi gwanin burgewa wanda dagani sun saba ne,Baba Asabe bata kara furta komai ba harsuka gama cin abincin su suka sha ruwan randa masu sanyi wayenda takawo masa,bayan sun wanke hannayensu suka furta alhmdllh atare wanda dama dab'i ar da ya sabar musu da itace,zasu yi basmala atare hamdala atare komai suna yinsa atare ne sun tashi da soyayyar junansu tun suna kana na.
                   💫Fa'eeh Bg💫
Masha Allah ya furta to tunda duk kun koshi sai aje afara shirin zuwa  makarantar  islamiyya koh,ehh suka amsa suna mikewa suka wuce dakin su  cikin  natsuwa ..
Shima tashi yayi ya wucewarsa nasa dakin  domin watsa ruwa,Baba Asabe bata iya cemasa komai ba har ya yi shigewar sa dan tasan ta ba'llo ruwa,tasan bazai jirata ta hada masa  ruwan  wankan ba duk da shi ba mutum ne mai riko ba.
     Abunda yafaru kafin fitar Khady gidan shine bayan tadawo makaanta 
Cikin sallama ta shiga madai daicin  gidan dai dai rufin asiri gida ne mai dauke da daki uku biyu  suna kallon juna sai daya  achan  gefe wanda yake shine nasu halee biyun kuma nasu Baba Adee da Baba Asabe,sai toilet daya natsakar gida, da kichen shima chan gefe farkon shigowa gidan ga  tsakar gidan ma da wali gidan masha Allah ko ina ka duba kwal kwal yaji suminti,inda ta  iske Baba Asabe tsakar gidan tana fifita da yake lokacin zafi ne,Sallamar ta Baba Asabe ta amsa mata da murmushi ta na furta tagaban goshina kindawo itama khady cikin mayar mata da murmushin ta furta ehh Babata nasame ki lafiya,lfyalau Hadizata 
    Babata yau Dady zai dawo koh!inji Khady,ashe kina lissafi yar nan yaufa ne zai dawo murmushi mai hade da murna khady tayi tana furta yo ba dole ba Babata, Munyi missing nasa ne tana maganar tana dosar  dakinsu  da gudu tana kwalawa Halee kira,Halee! Halee!

Tana  yaye  labulen taga wayam  katifarsu  bakowa adakin, katifarsu kadai ce da tasha lailaya sai kayan sip dinsu wanda Khadyn ta ya mutsa kafin taje makaranta,wanda Halee ce take aikin bayan tadan ji dama damar jikinta,tana cikin aikin ne Baba Asabe ta kirata ta Aiketa kasuwa kutsa kanta tayi cikin tare da kara lelleka ko ina  dan tabbatar wa indagaske Haleen bata ciki ne har toilet dinsu ta leka bayan ta kwankwasa taji shiru tambayar kanta tayi toh ina Halee taje ita da bata lafiya kuma?ganin bata da mai bata amsa yasanyata fita daga dakin bayan ta sargafe jakkarta ama 'ajiyarsu,fitowar ta keda wuya ta yo tsinke gurin Baba Asabe tana mai furta Babata ina Halee taje ne,fuska adaure Baba Asabe ta furta na aiketa kasuwa,tun yaushe Khady ta kara furtawa cikin jin haushin Babar ta ta,shiru Baba Asabe tamata wanda dama tasan tunda taji tana kwala kiran sunan Halee tasan cewa sai tazo ta tsureta da  tambayoyi kamar yar jarida ,kuma ta san tana  iya bin bayanta  yanzu dan haka kuwa bazata bartata fita ba komai kafuwarta 
Khady ganin bata bata amsa ba yasa ta furta babata kinfa san bata da lafiya kika aike cikin wannan uwar ranar tana maganar kamar zatayi kuka shine kuma kika ta har kasuwa duk wayennan kantin basu isaba sai kasuwa.....
  Baba Asabe ce ta furta an aiketa din wani ta fadawa bata  lafiya ne eh dazaki zo ki tsare ni da surutun banza....


Nikam nace 💁Baba Asabe adaiji tsoron Allah.
ALLAH YASA MU DACE 🙏

muhadu daku anext page 

Zuwa monday in sha Allah lahadi babu update.

jiya kunjini shiru nayi typing sai da nagama na danna wani gun by mistake duka  ya goge ga dan  ciwon kai danake fama dashi,kusakani a  addu'o'in ku
🙏🙏🙏
    
💫A MAFARKI NASANTA💫 FANS 
INAYINKU OVER MUSAMMAN MASU BIBIYATA FACE BOOK  INA GANIN COMMENT DINKU INA GODIYA 🙏KUMA  NA WHATSAPP INA GODIYA SOSAI MASU COMMENT DA WAYENDA BASA YI🙏
           ku cigaba da bibiyar alkalamin
             💫Fa'eeh Bg💫
in sha Allah daga gobe zamu bar kasar nan domin dauko muku rahoto  sai kuma mundawo,in akwai masu zuwa su fito mutafi jirgi 🚄kyautane

 Wayenda  badasu za,a sai gyara zama tsaf dan jin rahotannin mu.....

  * Allah yasa mudace*🙏🙏
Pls like share and  comment 

💫A MAFARKI
 NASANTA💫
In my dream I know her 
             By 
Pha'eezah Almustapha 
    Daga Alkalamin✍️✍
     💫Fa'eeh Bg 💫
   
Dedicated to my lovely sis Laila Almustapha
 Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION
           💫P.E.W.A💫
Home of perfect essential writer's together we stand🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️*
Pen 🖊️is mightier than the sword🗡️*
 
Ban amince a had'a mini document ba ko achanza mini wani sashe na littafi na inkuma kikayi nabarki da rabba👌

EPISODE1️⃣
FREE PAGE7️⃣
 
                     
TYPING📲📲📲 
 
Wuce kibani guri  ko in tattaka ki gurin nan,jiki ba k'wari ta wuce d'akin su tana zagayen neman yadda zatabi bayan Halee kasuwa,tabar Baba Asabe na masifarta ita kad'ai,Chan kamar minti uku haka taji tsif dama tana tsaye ne bakin k'ofa,koda ta lek'a ta tabbatar da Baba Asabe tabar tsakar gidan aiko da sauri  da sand'a  ta fice gidan gudu  gudu sauri  sauri ta  fice daga gidan har ta cimmata Dan dama tasan hanyar da  Haleen ke bi har ta isketa.
       💫Fa'eeh Bg💫   
Itakuwa Baba Asabe data shiga toilet din tsakar gida Dan tayi fitsari,tana fitowa   tafara kwala Kiran sunan Khady,Hadiza!Hadiza! Domin tagaya mata ta d'ora mata ruwan zafi,Tsif taji ba,a amsa mata ba k'ara Kiran sunan tayi sai dai shiru aiko da sassarfa ta lek'a d'akin nasu Dan tabbatar da zargin ta,aiko tana yaye labulan taga wayam babu Khady  babu ba alamarta Jakarta kadai ta hango sargafe, Nan ta rike k'ugu bayan tasaki labulen d'akin  tana  cigaba  mitar ta na rashin dawowar Halee da wuri da kuma fitar Khady gidan,ita kuwa Halee ta fiyarce tata gata ga kamar ta dama,dama bata da saurin tafiya ne,wannan kenan ....

💫Fa'eehBg💫
Mukoma cikin  labari .......

Jirgin✈️ mu yayi landing lafiya😊

* INDIA,MUMBAI*

  Babban Birnin India-mumbai garine Wanda yatara kowace irin al umma daga k'asashe daban daban,Wanda yakasance kowa da abunda yakawo shi garin inka cire yan asalin India din mazauna garin na  Mumbai,wasu karatu wasu kasuwanci,wasu kuwa neman lafiya,wasu yawon shakatawa,wasu kuma aiki ne yakawo su.
  
Nasan wasu zasu ce Babban Birnin India ai new  Delhi ne karku damu😊 wannan shine kawai abunda nayi ra,ayin sakawa🙏
    
-----------------------
  Gujarat 105 unguwa ce Babba ta masu idon nera shiyasa zakaji ko ina tsif kamar ba bil adama acikin manyan ginukan na alfarma, inda na kutsa kaina  acikin cikin wani katafaren gida Wanda yakasance upstair ne,  kuma ya amsa  sunansa house,Wanda yaji farin fenti da ash colour mai haske da daukar ido,gida ne Wanda yaji kawa ta ko ina tunda compond din gidan zaka shaidar  da hakan,k'aton parking space ne achan gefen dama dauke da manya manyan motoci wad'anda ake Kira car wayenda akalla zasu Kai goma,daganin motocin dai bugun America ne new design yan 2022 sai 2023 wayenda bakowa ke taka su anigeria ba sai Wanda yaji gishiri da sugar,sai wani k'aton  swimming fool dake Chan ta gefen hagu Wanda yakara kawata gidan,ruwan cikin sa har wani sky blue sukeyi gwanin burgewa, swimming pool din  yadan shiga lungu da alama akwai kofar sa achan ta baya, bayan ta gaban gidan,ko ina tsaf ga iska tana kad'awa shuke shuken gidan sai kad'awa suke yi suna bada wani k'amshi mai dad'i ko ina sai walkiya yake yi part biyu ne acikin gidan iri daya gidan ya hadu iya had'uwa rabinsa duk gilas ne tundaga bakin kofar shiga ciki zaka gane hakan.
Muryar wani guy naji 
Daga ciki yana kwala Kiran Ammar!cigaba da kiran sunan yayi kamar ransa abace,Ammar yakara furtawa! wai uban me kake jira haryanzu baka fitoba har na fita compound nadawo,shiru danaji ne yabani damar shiga cikin falon bayan wannan guy din yacire code din kofar,nikuma na antaya daga ciki🤗wani had'adden falo na fad'a Wanda yaji kayan more rayuwa ta ko ina gashi yasha had'addun cusions masu taushi farare kar dasu,ga katuwar Tv Nan manne abango,ga k'aton dinning table anan shima gwanin burgewa,Wanda yake kusa da wata kofa Wanda nafi tunanin kofar kitchen ne mai had'e da store, falo ne na kasa Wanda yake dauke da d'akuna uku agefe suna Dan nesa da juna  agefen hagu,sai wani ahannun  dama inda nake tunanin toilet, bayan nagama karema dakin kallo,kuma ina da tabbacin nan ne naji muryar wannan guy d'in,juyawar dazanyi kenan dan hawa kan upstair din da ya raba tsakanin hagu da dama,idanuna ne suka tsaya chak sanadiyyar kicibus da sukayi da wani had'adden guy a hoto yasaka kanana kaya ya daura labcoat akai irin dai shigar likitota wadda takara kawata shigar tasa,sai wani k'aton hoton Wanda yakara Jan hankali na yana sanye da kayan tiyata ajikinsa blue colour tare da abun awon Bp waton stethoscope ya rungume hannayensa akirji yana sakin wani had'adden murmushi chocolate colour skin dinsa sai sheki take yi,ga Zara zaran eyelashes dinsa cike wayenda suka Kara kawata manyan idanunsa wayenda ke kwance akarkashin cikakkiyar gashin gyarar sa,sumar kansa kuwa daganin ta kasan tana Shan gyara na musamman  tare da sajen sa,pink colour din labbansa  sai sheki sukeyi gwanin burgewa hancin Nan kuwa zungur kamar biro Masha Allah.
Sai wani hoton shima na wani farin guy shima dai kyakkyawane saye da irin shigar ta wancahna guy din na farko.
 Maganar da naji daga saman ce ana furta Ammar Amma dai Kai Dan iska ne ace har yanzu baka shirya ba tun d'azu nabarka kashiga wanka fa Amma Dan wulakanci har yanzu baka gama shafe shafenka ba,shiyasa nayi maza nafada ciikn d'ai daga  cikin dakunan wanda naji sautin maganar na fitowa,Muryar wannan guy dince tadawo Dani dai dai daganin zubin halittar Wanda ke zaune akan mirror da towel daure akugunsa daya kuma agefen kafadarsa, kwantaccen gashi ne  abisa kansa Wanda dagani ya hada da jinin larabawa ko fulani daga bayan sa zaka fahimci yana da faffadan kirji tare da kwantaccen gashi Wanda yake luff gwanin burgewa jikinsa ko ina lui lui dashi daganin sa kaga Dan hutu kafafuwansa da tafin hannun sa wayenda yake ta faman murtsuka mai dasu gwanin burgewa Wanda dagani zasu yi kamar na sabon jariri,chocolate colour fatarsa sai sheki takeyi.inda wannan guy din yake furta ai narantse bazan jiraka ba tafiyata zanyi yana maganar ne kamar ransa abace kasan yau muna da meeting ga tarin patients na jiranmu Amma shine kak'i saurin shiryawa,wadannan maganganun dayake yi su suka dawo Dani daga sumar tsayen Dana yi, inda nakai duba na ga saurayin dake maganar,shima dai hadadden ne kamar Wanda naji ankira Ammar, ashe ma shine wannan fari tass din guy Wanda nagani afalo, yasha 
Kyau cikin kananan kaya yadora labcoat akan kayan sa inda naga an rubuta Dr .Al Amin jabir Muhammad soja Wanda mafi yawan colleagues da abokansu  suna kiransa da Dr AJ...
Dacin Raine bayyane akan fuskar Dr AJ bayan yagama mganar   
Yana batun fita ne yaji anriko hannun sa,yana kucce kuccen ya kwace hannunsa kenan yaji an rungume shi dasauri ya turesa yana furta ji iskanci Kai fa Ammar Dan iska ne mtsww yaja dogon tsaki,jiyayi Ankara riko hannunsa wannan karon .....

Mu hadu next page🙏
Gobe in Allah yakaimu 

 Comment din ku kadai nake bukata...

💫Fa'eeh Bg💫

💫A MAFARKI NASANTA💫 FANS 
INAYINKU OVER💯 MUSAMMAN MASU BIBIYATA FACE BOOK  INA GANIN COMMENT DINKU INA GODIYA SOSAI🙏KUMA  NA WHATSAPP INA GODYA MASU COMMENT DA WAYEN DA BASAYI 

Pls like share and comment...

https://chat.whatsapp.com/HO4hVB1luhXGyRzaOdWy68

💫A MAFARKI
 NASANTA💫
In my dream I know her 
               By 
Pha'eezah Almustapha 
    Daga Alkalamin✍️✍
     💫Fa'eeh Bg 💫
   
Dedicated to my lovely sis Laila Almustapha
 Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION
           💫P.E.W.A💫
Home of perfect essential writer's together we stand🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️*
Pen 🖊️is mightier than the sword🗡️*

Dan Allah duk wanda yakaranta wannan page yayi mini Addu,A🙏
Allah yabiya mini da dukkanin bukatu na tare da dukkan kulluhin musulmi🙏

EPISODE1️⃣
FREE PAGE8️⃣
 
 TYPING📲📲📲                 
        
+++++++++++++++++++++++++++++++++++

wannan karon daya fisge hannunsa baiji an rungume sa ba sai dai yaji anja hannunsa,anzaunar gefen gado,baice kara cewa uffan ba har ya zauna.
Had'a idon da sukayi daDr. Ammar ne yana sakar masa wani shu'umin murmushi ne yasan ya sa galla masa wata katuwar harara yana mai jan tsaki,shiko Wanda naji ankira  Ammar A hankali cikin wata kasalalliyar murya ya furta just give me three minute ohk! yakai karshen maganar yana mai k'ara sakin yalwataccen murmushi a fuskarsa, wanda maganar da yayi iya kar labbansa ta tsaya,maganar da yayi ce bayan barowar sa kan madubin,tasanya ni kara cikin natsuwa ta daga sumar tsayen da na kara yi  ganin hadadden guy din da na gani ahoto falo Amma tabbas afili yafi kyau  daganinsa kaga ingarman namiji mai ji da kudi,mulki da izzah ga fatar nan tasa sai sheki take yi kamar an mata wankan madara sai narasa tantance shin chocolate colour ne skin nasa ko fari ne mai dan duhu,wanda fuskar sa takara nuna hutun da yake samu....


Zazzak'ar muryar sa kuwa kamar ana kad'a sarewa inyana magana kmar kayi bacci saboda dadin ta,saboda zakin ta da taushinta in yayi magana kamar ba,a bakinsa tafito ba,daga yanayin  Kallon da masa na fahimci akwai jan aji da izzah da yanga kamar mace kuma baida son magana,Ammar dai daga ni miskili ne na karshe...

Bayan ya gama maganar da iyakar labbansa ta fito inba ka kalli bakinsa ba ba zaka san dakai yakeyin maganar ba,juyawa yayi ahankali yataka kamar yana tsoron carpet din dake kwance male2  ad'akin ta huda masa k'afa,har ya isa inda doguwar sip dinsa take wadda ake bud'ewa da thumbprint inda yasanya dai daga cikin zara zaran yatsun sa na hannu  take hadadden sip din tashiga budewa da kanta har ta kai karshe wow! bansan lokacin da baki na ya furta hakan ba,Allah yasa ba wanda yajini...
Kayane birjik kamar botique wasu asama wasu ak'asa,sashen ko wanne daban su trouser,men panties,t shirt ,necktie suma gasu nan atsare ta ko ina sip din kayane atsare chan daga karshe suit ne jere kala kala sai walkiya sukeyi,sai sashen shaddodi,yadukka da huluna irinsu mu hadu banki ,su ku'be,  har da irin su tadara mai irin na gidan sarauta kamar yanayin na(raba gardama) labarina...sai dai na wannan likitan sunfi na  (raba gardama) kyau kuma design dinsu ba,a irin na nigeria bane  daga ganin su kaga bugu turai sun sha kari har sun gaji,sai daga chan sama wata hanger ce rataye da wasu fararen riguna masu kama da labcoat,dasu long sleeve,under wears,short nikers da vest,handkerchief, kowanne da gefensa akan hanger din.

................
Hannunsa ne yana jawo d'aya daya daga cikin fararen rigunan  labcaot,
Shi kam Dr.Alamin Aj  murmushin bakin ciki kad'ai yake yi yana jan tsaki yana mai duba hadadden agogon da ke hannunsa kamfanin apple,dogon yakara ganin har minti uku ya wuce har yakara biyar akai,Dr.Ammar kuwa duk da yaji jerin tsakin dayake ta faman saki kuma yana ganin hararar da yake ta sakar masa bai tanka saba
.....Komawa yayi yadauko wani had'dden wandon jeans bak'i,bayan ya aje labcoat din,ya juyo kenan Dan ya ajesa kan gado yaji Dr Aj yakara jan wani mugun tsaki wanda sai da Dr. Ammar ya rufe kunnuwansa yana mai yamutsar beautiful face dinsa D'an kallon Dr.Aj yayi  wanda yayi tik'in tik'in da fuska,Dauke kansa yayi,A hankali yajuya gurin sip din yana sakin kayataccen murmushi a fuskarsa wanda ya bayyanar da dimple dinsa na gefe daya yatsan sa yasanya cikin kwarewa kamar wani jarumin ya lalaci tsinin hancinsa,wannan dabi'ar sa ce ta lakarta tsinin hanci in yana cikin yanayi mai dadi dakuma yan maganar sa nakai.
Dama haka yake Idan yana jin shirmen sa haka yakeyi da d'ai dai yake zabo kayan da zai saka acewar sa suna masa nauyi ne ahannu,wani lokacin ma in Dr Aj ya ga zai tsayar dasu shike zab'o masa kayan kamar wani karamin yaro
Abun da yasa yajuya ya fahimci Dr Aj yakai kololuwar b'acin rai yanajin uwar hararar da yake sakar masa,ga tsukkin da yake ta faman ja suna neman jaza masa light headache,shiyasa kawai ya juya batare da ya aje trouser dinba yakoma  domin ya hado kayan baki d'aya,da isarshi bakin sip din yasanya kyakkyawan hannunsa yazaro farar vest da long sleeve fara kar  mai dogon hannu,da handkerchief  fari, yana gama zab'ar kayan yadanna wani madanni kamar na ura daga kasan inda ake thumprint,A hankali katuwar sip din tarufe ruff  kamar dai yadda take farko.

              💫Fa'eeh Bg💫

A hankali yataka zuwa bakin gadon ya aje su anan gefen  labcoat din a kusa da Dr.AJ din
Wanda kallo daya yayiwa Al amin Aj ya dauke kansa,  yana cigaba shirinsa cikin natsuwa wandon yafara jawowa zai sanya wanda yayi dai dai  da d'ago idon Dr Aj,ganin abunda Dr yake kokarin yi ne na sakin towel d'insa kasa yasanya sa dasauri yadauke kansa yana fadin marar kunya kawai yana jan karamin tsaki,bai san cewa Dr motsinsa Dr.Ammar na ankare dashi ba har dauke kan da yayi,shi atunaninsa babu short ajikin sa shiyasa yayi saurin dauke kan nasa duk da yasan ba halin shi bane sakin tsaraici tun suna yara shi ba ya yadda wani ya gane masa jiki in za,a musu wanka dakyar yake yadda wata rana sai dai akai shi gurin Aunty....


Murmushi kawai Dr Ammar yayi yana cigaba da sanya wandon sa acikin dan short din da ya chanza tun atoilet cikin wayen da ke a lakkame a hanger,vest dinsa yasanya da long sleeve dinsa masha Allah na iya furtawa takawaa yayi zuwa kan madubi yana kara gyara lallausan gashin sa da sajensa  tare da kara taje sa da murtsuka masa kalolin mayukka bayan wanda yashafa acikin toilet,sannan ya fefesa turare kusan kala biyar oud masu bala'in kamshi,man bakin sa ya shafa :lips balm: wanda yakara kawata kyakkayawar fuskar sa da aina hin kyawonsa da shekin  fatar sa,dama bakin sa bai rabo da maskin lips balm domin wannan dabi'ar yasaba da ita tasha man baki kamar mace,shidai Dr Aj kallon ikon Allah kadai yakeyi yabuga tagumi yana yi yakai duban sa ga agogo,ace katon saurayi yazauna ya dinga shafe shafe kamar mace, azuciyarsa yayi furucin.
Dan  yin murmushi DR .AMMAR  yayi jin maganar da Dr. AJ yafurta  wadda  yayi kasa kasa,tsinkayar muryarsa  Dr Aj yayi yana  furta  nagode ma Allah da ba maccen nake ba kamace kagani yakai karshen maganar cikin yin dan karamin murmushi Dr aj da yaji abunda ya furta duk da baiyi  tsammani yajisa ba  dan ciki ciki yayi maganar,sai bai yi mamaki ba dan yasan yadda dan uwan nasa yake da mugun ji kamar kunnen maciji..
sai bai bai basa amsa ba yashare sa .
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
©💫Fa'eeh Bg💫
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
cikin dan kan kanin lokaci dakin yakara gauraye da kamshin turarrukkansa 
A Hankali yajawo labcoat dinsa irinta ta Dr. Aj samfurin ta likitota   fara tass sai shekin sabon taka takeyi kamar ma sabuwa ce akan kayan sa yadaura irin da yadda kuka san likitota nayi masha  kawai zamu ce domin tsaya wa rubuta  kyawon da yayi page din bazai dauka ba,stethoscope  dinsa  dake akan hadadden  gadon sa  ya sargafa abisa wuyan rigar sa dan danan yakara fitowa likitan sa sak,ga sunan shi nan ya bayyana radam agefen rigar tasa cikin tsari mai kyau inda aka rubuta DR. ABDUL RASHID A ALIYU da manyan baki Amma colleques nasu nasu da childhood friends na kiransa da DR.AA
 wasun ma cikin colleques nasu suna kiransa Dr. Ammar a gida kuwa suna kiransa Ammar Saboda sunan kanen mahaifinshi da yaci shiyasa aka masa lakani da Ammar.

A hankali ya juyo inda Dr aj yake sannan ya kalli hadadden agogon zinarin  dake daure a tsintsiyar hannunsa kirar kamfanin rolex  wanda yadaura bayan tsayuwar sa kan madubin  wanda yakara kawata shigar tasa skin din sa sai sheki takeyi.

A hankali bayan yataka ya zabi dai daga cikin shoerock din dake  dauke da takalma iri iri masu kyau wanda sai da yafara saka sock baka aciki sannna yasanya takalman nasa masu kyau  bakake rufaffi sai walkiya sukai gwanin burgewa 
     A gogon nasa yakara dan kallo ganin lokacin da yadiba har ya wuce wani ya zo wani yakaru, sannan cikin izza ya  furta man katashi mutafi karmuyi late...
wani ...
Kallo da Dr aj yamasa ne yasa sakin wani killer smile wanda ya tsaya iya labban sa,dama da gayya yayi maganar dan yasan mutumen nasa acike yake kamar ya fashe wanda kuma yasan fushin nadan  lokaci ne zai sauko ......

Shiko Dr aj dayake kan pressing phone dinsa baice masa komaiba yadauki nashi stethoscope din ya sargafa,wanda dama sargafe yake awuyansa ne,gajiyar jiran Dr Ammar ce tasa ya cire ya ajiye shi gefe,duba kansa yafara yi agaban madubin dan tabbatar da komai normal sannan ya fice daga dakin shima uban gayyar dake tsaye yana  kallon sa A hankali ya matsa gefen gadon yadauki wayar sa dake chaji abisa bed side drower sannan ya fice daga cikin dakin cikin tafiyar takama da izzah yana ta faman zuba uban  kamshi kamar sabon ango........

Fitar su dakin ce tabani damar
Karewa da Katon  bedroom din kallo fari ne tass mai  kyau  wanda yake katone ne nagaske ashe ma Ciki da falo ne ban lura ba wurin uban sauri,bedroom din tana da fadi sosai gadon ya hadu iya haduwa,da sip din sa wadda take lafe abango  kamar babu ta sai gefen hagu ga katon mirror mai dauke da kayan gyaran  jiki  irinsu mayukka masu tsada  manyan manyan turarukka da man gyaran gashi da sauran kayan amfani,sai wata kofa dake gefe  wadda nafi tunanin toilet ne inda na lek'a sa ya hadu iya had'uwa dukkaninsa glass ne aciki ga katon bahon wanka nan irin na turawa mai kyau da katon madubi da yaji kayan  amfani irins sabulu shower gel da turarukkan wanka,toothpaste, brush komai akwai ga tsakiyar toilet din gudan fankacece  komai akwai aciki na  bukata ya tsaru iya tsaruwa,curtain din kuma milk ne masu kyau.

Falo na dawo bayan na fito daga toilet din  inda falon ya hadu shima ya hadu komai na cikin  sa yakasance lite blue and white har cusions da labulayye komai agyare gwanin burgewa kamar ba dakin men ba.

Sawun tafiyarda naji ne yasani waigawa dan ganin wanda ke tafowar 
Dr Ammar ne yana shigowa direct bedroom nasa ya yi tsinke 
Cikin sanda nima nabi bayansa 

Gurin aje takalmi yanufa shoe rock wadda ke cike da takalma na alfarma masu kyau,wadda ke akusa da sip dinsa takalmin dake kafarsa  yacire ahankali tare da ciro wasu masu masu kyau sai walkiya suke yi suma cover shoes ne kamar  na farkon sai dai kalace ta banbanta wadanchan baki ne a kala su kuma waddan nan fari,bayan  yachanza su ne ya dauki  yar  madaidaiciyar bag tasa kamar ta school mai kyau yasar gafa  agefen kafadarsa yana  ficewa.
Ahankali yake takonsa har ya fito falo sannan  ya isa inda wata dankararriyar mota take fake kirar benz a tsakiyar compound din gidan ,dama Dr aj yayi  ya kunnata har sun yi reverse, Ammar yace yayi mantuwa cikin jin haushi Aj ya tsayar da motar anan tsakar gidan.

A hankali yasanya zara zaran yatsunsa yabude front sit yazauna Dr .Aj bai cemasa uffanba duk da yaga chanjin takalmin da yayi cikin ranshi kuwa kuwa fadi yake mutun sai shegen kichifi kamar mace,kai kam Ammar matar ka tabani mtssw yana jan tsaki abayyane, Dr Ammar kuwa bayan ya gyara zaman sa har ya maida karamar jakarshi sit din baya yana jiran Dr aj yatada motar  shiru sai dai yaji tsakin da yayi,murmushin mai kyau kawai yayi yana furta man gulma ta kakeyi azuciya koh yakai karshen maganar yana kafesa da manya idanunsa ......Shiko Dr.Aj harar wasa yasakar masa yana furta abunda ma yafi gulmar ka za,ayi,yafigi motarsuka fice daga gidan bayan sun sanya belt mai gadi na wangale musu katon gate din.......


💫Fa'eeh Bg💫


next page tommorrow in sha Allah 

Comment dinku kadai nake bukata FANS 💔💋💋 domin shine kwarin gwiwata 🙏🙏

godiya agare ku ta musamman 
..........................
fiddausi dan galadima 
siddiqerh muhammad 
halima bashar bello
ukuteey 
anty zee
oum amjad
sha'awa hamis  
Oum sudais 
Umma 
Da ma wayenda ban ambata ba
wannan page naku ne 
💋💋💋💋💋💋
Allah yabar kauna💔💔
 ina ganiin comment dinku ina jin dadi sosai🙏🙏🙏


Allah yakai haske acikin kabarin ka 
Baba Bello ya yalwanta kabarin ka dana dukkan kulluhin musulmi,🙏🙏
Mukuma kasa mucika da imani ya Allah 🙏🙏pls say amin !

  * Allah yasa mudace*🙏🙏
Pls like share and  comment


 💫A MAFARKI NASANTA💫
 in my dream i know her 
            By
Pha'eezah Almstapha 
   Daga Alkalamin ✍️✍️
      💫Fa'eeh Bg💫

Dedicated to my  lovely sis laila Almustapha Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION
          💫P.E.W.A💫
Home of perfect essential writer's together we stand 🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️*
pen🖊️ is mightier than the sword🗡️*

Group na whatsapp ina mai kara baku hakuri akan abunda ya faru🙏

`´`´`´`´`´`´`´`´`´`´`´`´`´
EPISODE1️⃣
FREE PAGE9️⃣

TYPING 📲📲📲

Tafiya suke yi ahankali kan katon titin dayake da abun burgewa ta yadda aka tsara shi,ba,abun da ke tashi a cikin motar face sautin sanyayyiyar wakar rihana mai taken my umbrella 🌂 
Uban gayyar yayi shiru ya jingina da sit din sa yana sauraren wakar idanunsa alumshe fuskar nan sai sa,sai sa ba murmushi ba dariya,karar wayar sane da aka kirane dake ringing waka mai sanyi ta mahaifiya ne yasanya sa bude manyan idanunsa a hankali tare da daura su akan screen din wayar  wanda sunan nurul  hayat ya bayyana b'aro b'aro b'aro akan wayar da numban nigeria + 234......A hankali bayan ya gama karewa wayar kallo wanda har kira na biyu ya shigo yasanya kyakkyawan hannnunsa ya dauki wayar tasa dake gefensa aje kirar iphone latest one 15 pro max picking din call din yayi yana mai kara wayar akunnen sa  akunnensa tare da sakin kayataccen murmushi yana furta Assalamu alaiki nurul hayat,daga chan dayan bangaren,murmushi aka saki wanda yakara sanya masa natsuwa,wslm kyakkyawan likita na takai karshen maganar cikin nuna farincikinta,murmushi ya mayar mata dashi tare da furta fatan kina lafiya nurul hayat? daga chan bangaren ta amsa da lafiya lau ya aiki?Alhamdulillah,ya furta mata cikin kulawa kamar yadda tayi masa tambayar,A hankali yakara furta inasu maheer da nisa,maheer na school kasan suna shirye shiryen graduation ne oh hakane fa jiya ma munyi magana dashi yasanar mun,Nisa fa?ya kara tambayawa cikin kulawa da ladabi amsa tabashi da dama ai nida maher kadai ne agidan sai sarki,yuhanis tana gurin sister Husaina tatare gurin sumy,A hankali bayan gama saurarenta ya furta meyasa kika barta kinsan bata son karatu ga  sumayya ma duka daya suke,yakai karshen maganar kamar yana jin tsoron yin maganar yana kokarin danne wani abunda ke shirin taso masa na jin sunan sarki da ta ambata,murmushinta ne yaji tana furta nur yanzu fa ba yarda bace sun girma kowa censu tayi hankali 18+ suke fa kaga kuwa sunyi hankali da channe dai basa son zuwa makarantar kuma lokacin babu Wayo ne gashi ma yanzu suna gab da yin  ss.c e.graduation  Uhmm kawai yace,bawai dan ya yadda da karatun nasu ba shi atunanin sa mahaifiyar tasu  tana kokarin kare su ne kawai dan yasan yadda yake fama dasu in sunje nigeria dakyar da lallashi suke samu suje school...Kuma ehh dagaskiyar ta yanzu sun girma da daine yake tilasta musu zuwa makarantar itada  sumy amma ayanzu su da kansu suke zuwa dan sun mahimmancin karatun,wannan kenan......


       💫Fa'eeh Bg💫

Shirun da taji yamata ne yasanyata ta A hankali furta YARIMA,  gaban sa ne yayi muguwar fad'uwa jin furucin nata yanzun ma shiru yamata dama tasan abunda zai faru kenan, dama irin hakan tana yawan faruwa duk ta kirasa da sunan bakin sa yana masa nauyin amsa sunan, dalili kuwa shine takirasa da sunan ne ko zai nuna alamar cewa yasauko daga fushin da yake ne da mahaifinsa,da kuma jin in yanzu ko yana son sarautar  da yake  gudu wadda mahaifinsa yake  son lakaba masa shima yasamu ya huta  wanda kuma shine yasanya sabani atsakaninsu  domin kowa kafaffe ne like father like son ,da dai taga alamun bazai ce komai ba,ta furta cikin sanyin murya ABDUL RASHID   har yanzu kana nan kan bakan ka ?takai karshen maganar cikin yanayin da bazai iya juraba,wannna karon faduwar da gabansa yayi sai da yadafe kirjinsa wanda ko Dr aj dake tuk'i  a hankali sai da yajuyo ya kallesa dan ganin alamar razana atattare dashi ga kuma hannunsa dafe da kirjin sa,A hankali yaji shima  jikin nasa yayi sanyi ganin d'an uwan nasa cikin wannan yanayi,Dayan Hannunsa kawai ya riko  da hannun da baya driving dashi ya damk'e acikin nasa, yasan cewa tabbas ko ba,a fada ba maganar sarauta ce,  akayi masa,wanda ya rasa wace irin kiyayya ce tsakanin Ammar da sarauta  da har baison mulkin wanda kuma yake tunanin shine abunda yasanya sa  rashin son komawa kasarsu,idanu suka had'a dashi ya girgiza masa kai da alamar be strong man shikuwa  Dr.Ammar dauke kansa kawai yayi batare da ya nuna wani abu afuskarsa ba .
Achan bangaren mahaifiyarsa dataji shiru ne yasanyata duba wayar dan tabbatar wa inyana online,,,,,,,,,,,,,,,,,,kuma dama akan sarautar ne yakarbi aikin da kasar india tabasu bayan kammala karatunsu,wanda shikuma Dr Aj yana da burin dawowa k'asar  sa ta haihuwa domin yin aiki acikinta dan su taimaki kasarmu ta nijeriya,Amma saboda  Dr. Ammar yasadaukar  da nashi burin suka fara aikin tare anan kasarta india wanda izuwa wannan lokaci sunansu yayi shura a india dama fadin duniya baki daya,kowa yasan Dr.Abdul rashid Aliyu Ahmad da Dr.Al Amin Muhammad soja,inda kowace k'asa masu  dauke da manyan asibitoci  suke son su samu  damar gayyatar su sumusu aiki koda na dan lokaci ne amma basu samun wannan damar saboda shidai Dr.Ammar kaifi daya ne acewar sa kasar  india su suka fara daukarsu aiki har suka yi suna a ko ina to ayanzu bazai iya barin kasar ba dan yaje wata kasar da sunan aiki ba,haka shima Dr. aj duk da yana da burirrika,inda kawai zai iya yin aiki yabar india shine kasarsa ta nigeria ko shi dan saboda nan  ne cibiyarsa take,kuma yana son taci amfanin ilimin suwannan kenann......

mukoma inda muke ......
A   hankali ta furta  karka damu kaji tana mai sakin murmushi,Ina d'ana yake takara furtawa,cikin sauke wata nannauyiyar ajiyar zuciya wadda har sai da taji sautin ta,Wanda shi yakara tabbatar mata da Dr ammar har yanzu yana nan kan bakansa nak'in son sarautar, da wata murya mai sanyi ya furtama ta gashi nan,to basa wayar  ta furta masa,Dr aj dake driving yakarbi wayar bayan ya saki hannun na dr ammar a hankali yakara ta akunnen sa yana furta momy yakike cikin murmushi ?lafiya lau my son ta furta kuntashi lafiya,lafiya lau  yabata amsa kara furta masa tayi ya aiki Alhmdllh yakara bata amsa toh masha Allah!A hankali takara furta naji kamar a hanya kuke koh?ehh momy,sai ina halan ? dan naga kunfita da wuri yau,ehh momy muna da meeting ne kuma kinga yau monday akwai tarin patients, eh hakane fa toh Allah ya kaiku lafiya akula da titi,in sha Allah yafurta mata,sannan takara furta in kun gama abunda kukeyi anjima inkana freee ka kirani akwai maganar da nake so inyi dakai,cikin girmamawa yace in sha Allah momy i will contact you A hankali takara furta asauka lafiya,Allah yasa ya furta sannan sukayi sallama tare da yanke kiran..........

Kuyi manage da wannan ba yawa...Naso inbaku page biyu but abunda yafaru dazu yadan taba ni,kaina ke ciwo ko typing din nadan yishi sai ahankali.

Allah yasa mudace,Abunda ya tsanan ta agaremu Allah ya yayemuna 🙏

 pls like share and comment 🙏🙏🙏🙏

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/HO4hVB1luhXGyRzaOdWy68
💫A MAFARKI NASANTA💫
 in my dream i know her 
            By
Pha'eezah Almstapha 
   Daga Alkalamin ✍️✍️
      💫Fa'eeh Bg💫

Dedicated to my  lovely sis laila Almustapha Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION
          💫P.E.W.A💫
Home of perfect essential writer's together we stand 🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️*
pen🖊️ is mightier than the sword🗡️*


EPISODE1️⃣
FREE PAGE🔟

TYPING 📲📲📲

Dora wayar,yayi abisa laps din Dr Ammar a hankali Wanda ke jingine da sit dinsa ya lumshe da idanunsa yayi tsif kamar Wanda ruwa yaci ko kwakkwaran motsi,ba abunda yake tunani face maganar da mahaifiyarsa tamasa wadda kusan bayan dan lokaci takan yimasa maganar taji ta bakinsa ko yajanye nasa Ra,ayin bisa ga na mahaifinsa,fatan Sa kawai A wannan karon Allah yasa batayi fushi dashi ba,dan bazai iya jure fushinta ko na second ne abun yawa zai masa azuciya

      Wayar Sa da Dr Aj ya aje masa ce tadawo dashi daga tunanin zucin da yaje a hankali yasa hannu yadauki wayar ya tsura mata lumsasaun idanunta kamar mahaifiyar tasa ce agaban sa,Ajiyar zuciya yasauke mai nauyi,yana kara lumshe idanunsa tare da budesu
 
Maganar da Dr Aj yayi ce tasa yadago idonsa daga kallon da yake yi ma wayar tasa,inda yake furta masa kar ka sanya damuwa aranka nasan  awannnan karon  batayi fushi mai zaifi ba kai inaji bazata tayi fushi dakaiba saboda daga yanayin yadda muka yi magana da ita na tabbatar da hakan,Wata katuwar ajiyar zuciya Dr .ammar yakara saukewa,baice furtawa Dr. Aj komai ba,Dai dai sun kawo katafaren asibitin da take Babba afadin India wadda mutane da dama ke yowar tattaki India domin samun ingantacciyar lafiya,Asibiti ce da tayi shura a fadin duniya,Babbar asibiti ce da ta Tara many an likitota ta sassa da ban da ban kama daga likitan kwakwalwa,na zuciya,likitan mata kai ko wanne fanni akwai 

Su Dr Ammar da Aj suna dai daga cikin manyan likitotan dake taka rawa ta kowanne fanni acikin asibitin shiyasa sunan su yayi fice musamman Dr.Ammar.

      
💫  A mafarki nasanta 💫
         Daga Alkalamin
          💫Fa'eeh Bg💫

MAHARASTRA 24 HOURS HOSPITAL MUMBAI  INDIA

...... Asibiti ce Babba wadda ta tsaru iya tsaruwa taji kayan aiki a ko ina,da kayan more rayuwam,musamman ita wannan asibiti su suke jinyar  marar lafiyar da kansu,kudi kawai zaka zube kagama naka aikin....

Bayan wangale musu gate da mai gadi yayi tare da nuna farin cikinsa na zuwan su,duk da yadda yake cike da mamaki naganin wadannan manyan likitota sukadai batare da masu tsaron su...Kunsan indiawa akwai bada kariya ga wayenda suke musu hidima dan ko kare ne tsaf za,a sanya mashi bodyguard bare manyan likitota wayenda india take ji dasu dama kasa baki daya.

Haka dai ya rufe gate yana mai tambayar kansa lafiya ?suka zo sukadai ganin kamar suna risking rayuwarsu ne tafiya su kadai, abunka da turawa..nima dai ohon nace dan bangansu tun chan gidan ba,ashe dama suna sa body guard to amma lafiya?na tambayi kaina,bani da mai bani amsata haka nayi shiru abuna.

Wurin da yaksance na musamman dansu wato parking lot nasu wanda suke motocinbsu suda sauran colleques nasu,gashi nan kowa anyi tagging din sunansa akan  board din mai kya.

Inda naga an rubuta Dr.Al amin dr  aj yanufa dan nan ne nafarko kafin na Dr ammar Wanda shima sunan sa arubuce yake cikin tsarin burgewa,Bayan sun parker motar tasu kowa  yacire sit belt dinshi Dr.Ammar dayajawo karamar bag din shimai kama da school ba,wayarsa dake ajiye atsakanin lap dinsa yadauka,A hankali yadora kafarsa ta dama wadda take sanye hadaddun takalmansa yana mai kara gyara zaman stethoscope dinshi da labcoat dinshi yana ida fitowa da gangar jikinsa baki daya,futowar sa keda wuya yaci karo da wasu garadan maza kirar america atsaye agefenn motar tasu kowannensu fuskarsa ba Annuri,Shima Dr aj haka ce takasance dashi bayan  yafito yaci karo  da irin garadan mazan da Dr Ammar ya ci karo dasu ,Murmushj kawai Dr.Aj yayi,nasan arina ya furta domin dama ya hango motocinsu pake agefen titi kirar hilux da wasu daga cikin motocin da gwamnatin ta bada masu kyau,Amma baiyi tunanin zasu cikin hospital din ba,ashe dama suna ciki.

Abangaren Dr ammar kuwa bayan cin karo da yayi dasu take yakara murtuke kyakkkyawar fuskar sa kamar bai taba koda murmushi ba.

Daya daga cikinsu ne  ya furta sorry sir! duk sauran suka  hada baki suna maimaita abun da  ya furta,wannan umurnin  gwamnati ne mutumen yaci gaba da magana,mukare ku  tako wani hali yanzu idan yanzu idan akaji ka koremu zamu iya  rasa   hanyar   samun cin abinmu,wannan aikin shimuka dogara  dashi kayi hakuri bazamu kara ba,ko wacchan  ma matsala akasamu  we are  sorry sir haukat suka kara hada baki atare suna maimaitawa,yana maganar ne cikin harshen indianci 

Sassauta fuskar sa yayi tun bayan jin bayanin d'aya daga cikin su wanda  yake   shine tsoho acikinsu.

Dalili kuwa shine bazaiso ace ta sanadinshi baa sun rasa hanyar samun abincinsu,danshi yakasance mai tausayi ne ga nakasa garesa,ma'ana talakawa wayenda yafi su arziki,A hankali yak'are musu kallo  sannan yadauke kansa,su kam daganin yanayin fuskar ta boss dinsu sai suka yi calming na zukatan su   ,maganar da yayi ce tasaka su furta thank you sir ,duk sai suka juya gefen da Dr aj yake,bayan ya d'aga musu hannu kawai,alamar ya isa, Cikin hada baki suka furta ma Dr. aj Goodmrnng Sir! mrnng fn ya furta cikin sakin fuska ya cigaba da magana dama yaji maganar da Dr.Ammar yayi nacewa suje wurin sa inyace su dawo kan aiki shikenan,shine Dalilin godiyar da suka ma Dr. AA din Dan sun riga sunsan inta tashine bama zai koresu ba kan dan karamin laifi,Murmushi yasaki Bayan tunawa da duka  wannan case  din akanshi ne, A hankali ya furta dasu karku k'ara irin haka kunji,cikin yaren na indianci domin acikin su akwai wayenda basa jin turancin, Amsa masa sukayi da yes sir  atare  duk da yasan komai tsarinsa ne,tunanin da yafaru ne yadawo masa masa arai.......
Fitarsa ce keda wuya a cikin gari sai motar sa ta tsaya,inda tayar motar tayi faci gashi kuma babu spare tyre a cikin motar  wanda basu san da hakan ba sai da ta tsaya musu kuma adai dai inda ba Al umma,tafiya ce zaiyi domin wakiltar su taro shida Dr.Ammar,A wani taro da zasu  gudanar na likitota,dole haka samu gefen titi shida bodyguard dinsa suka parker motar,anbuda booth ko za,a samu spare  amma babu,domin motar tamusu bazata ne,sai an duba lafiyar mota ake fita da ita,yau saboda urgently meeting ne sai basu tsaya dubawa ba ashe tayar motar na bukatar iska.

Agogon hannun sa ya duba yaga lokacin su yana yana ta yin gaba kawai sai ya yanke shawarar kiran Dr.Ammar.......
Kwance yake a cikin k'aton swimming pool din ya nutse aciki kamar ba mutum aciki ko ina tsit sai kamshin flowers da kukan tsuntsaye ke tashi, ko ina yanata walkiya sama tayi sky blue ga ruwan dake cikin swimming full din gwanin burgewa....

               
    💫Fa'eeh Bg💫

 Tunani yake yi akan maganar da duk mahaifiyarshi ta kira sa,sai ta tunatar dash,kuma aduk lokacin da yanuna kamar bai fahimci maganar ta ba sai tayi fushi dashi,wanda  damuwar ce ta zame masa biyu gata mahaifinsa wanda duk akanta ne mahaifiyar tasa take yin fushi dashi,ga kuma mafarkin sa dayazame masa jiki,wanda duk wani shaki ki nasa yasan da wannan mafarkin nasa saboda tun yana  D'an shekara bakwai yafara yinsa,ko mafarkin mene ne ?oho!

K'arar kiran da yasanyawa Dr. Aj ne  a waya ke amsa kuwwa akunnensa cikin sauti mai dad'i,A hankali ya katse tunanin da yake Bayan  D'agowa daga Nutsen da yayi..
A hankali  ya fara takowa har yafito cikin  ruwan lemar ruwan ta kwanta ajikinsa cikin burgewa,kyakyawan gashin kirjinsa yakwanta luff,da sumar kansa,k'aramin short ne ajikinsa,wanda yadaura towel akai  da wani karamin towel ahannun sa yana goge kansa da shi,wanda wani d'ai daga cikin yaran sa suka miko masa,wayarsace bai bada damar tab'awa ba.

A hankali yasanya zarazaran ya tsunsa yadauki  hadaddiyar wayar tasa wanda zuwa wannnan lokacin har kiran yakatse,wani yasake shigowa a wayartasa  picking call din yayi.

A bangaren Dr .aj kuwa tsaki yake ta faman bugawa har sai da bodyguard nasa suka furta yallabai ko d'ayan mu yakoma yadauko wata motar tunda bakayi reaching nasa ba,Domin suma bodyguard nasa mota biyu suka je da fito da ita kuma duk irin budaddun nan masu kama da hilux,tasa ce kawai Audi,cigaba da magana bodyguard din yayi yana furta tunda naga ka kira sa har sau uku bai daga ba,ko baya kusane

Shiru Dr aj yayi yana sauraren maganar ta yaron nasa dan yasan halin kayan sa yanzu haka yana  chan yana laziness dinsa gurin daukar kiran yana dialing numban again.... picking din call din yaji anyi shi yasanya shi kara wayar akunnen sa kirar i phone 15 pro max irinta da Dr aj,yana mai jan dogon tsaki 

Abangaren Dr ammar kuwa A lokacin da yaji saukar tsukin acikin kunnensa sai da yajanye wayar akunnen nasa sannan yakara mayarwa tare da d'an kallon wayar tasa inda naga an rubuta blood line b'aro b'aro ajikin wayar tasa,tab'e dan karamin bakin sa yayi bayan ya ya dan kalli wayar sai kuma yasa ki kayataccen murmushinsa mai kara wa fuskar sa annuri,dan yafahimci mutumin nasa  har yanzu akai yake dama koda yafita fushi yakeyi dashi,Dan yace bazai je taron ba sai dai shi ya wakilcesu,tunawa da yadda yafita ne yakara saka shi sakin murmushinsa wanda ke kara bayyanar da kwarjininsa,
A hankali yafurta man lafiya ?kai da ke cikin meeting ya akayi kuma kake kokarin damu na da kira,haushine yakara turneke Dr aj Bayan gama sauraraen furucin nasa,cikin jin haushin sa ya furtama Dr aj ka turo mun dai daga cikin body dinka da wata motar,motar da nashigo tasamu matsala tayan yayi faci ne kuma babu spare yana gama maganar ya katse kiran ....

Page guda kuka  samu maitsawo..
mu hadu next page monday in sha Allah 
Ina  godiya  amafarki nasanta fans🙏

Allah yasa mudace 
Ya Allah ka kara kawo muna zaman lafiya acikin wannan kasatamu 🙏

Like share and comment pls .
💫A MAFARKI NASANTA💫
 in my dream i know her 
            By
Pha'eezah Almstapha 
   Daga Alkalamin ✍️✍️
      💫Fa'eeh Bg💫

Dedicated to my  lovely sis laila Almustapha Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION
          💫P.E.W.A💫
Home of perfect essential writer's together we stand 🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️*
pen🖊️ is mightier than the sword🗡️*


EPISODE1️⃣
FREE PAGE1️⃣1️⃣

TYPING 📲📲📲


MUYI SALATI  GOMA GA ANNABI....
Allahumma salli ala muhammad wa ala ali muhammad kama sallaita ala ibrahim wa ala ali ibrahim innnaka hamidun majid,Allahumma barik ala muhammad wa ala ali muhammad kama barakta ala ibrahim wa ala ali ibrahim fil alamina innaka hamidun majid🙏
ya Allah kasanya mu acikin wayenda zasuyi makwabtaka da Annabi Muhammad s a w💓 agidan Aljannah🙏



A b'angaren Dr.Ammar kuwa bayan Dr.Aj yakatse kiran sai yaji duk baiji dad'i ba,bai kyautama sa ba,kuma yasan haryanzu fushi yake yi dashi....



Ahankali yakira d'aya daga cikin yaran nasa ya basa izinin daukar daya daga cikin motocin dank'ara dank'ara din motocin nasu dake parkey a parking lot,sannan yayi Amfani da Gps  tracking yanemi inda su Dr.Aj suke,da numban aj din,sannan yakaimusu spare tyre yadawo da wacchan yakai karshen maganar cikin bada umurni...


Ohk sir!  sannan yabasa umurnin yaje yakarbi car keys din,gurin ma,ajinsu,bayan yakarbo d'ai daga cikinsu ya fice daga gidan cikin wata arniyar mota,
Bayan fitar sa shiko Dr.Ammar falo yadosa yana tafiya d'ai d'ai kamar mai tsoron taka k'asa,code din kofar yasanya wanda yasanya kofar ta glass bud'ewa ahankali,shigewar sa yayi abunsa bai zarce ko ina ba sai upstairs inda bedroom nasa yake da shigarsa direct toilet yafada.


Bayan kamar awa d'aya haka ya fito daga wanka yana kimtsa kansa....Yana tsaye agaban fankacecen mirrorn nasa yana taje lallausar suman kansa,wayar sa tayi karar shigowar message har yaso yashare saboda a tunaninsa Dr. Malini ce  wadda ta addabi rayuwar sa yayi blocking numbannta yafi akirga da sababbin layi amma abanza kullum cikin turo masa sako take yi....

DR.MALINI
dai wata had'addiyar budurwace jinin indiyawa jinin larabawa,domin ita din ruwa biyu ce mahaifiyarta balarabiya mahaifinta ba indiye,shiyasanya ta ko ina malini ta had'u iya had'uwa bata da makusa,gata yar gawu,son kowa kin wanda ya rasa.

Class mate dinsu ce alokacin suna medical schl, sunyi karatu tare,dan alokacin ma team dinsu daya da ita,kuma suna abota da ita duk da dai shi Dr ammar bai cika magana ba da ita ba saboda tun farko ya fahimci inda ta dosa sai dai bata bayyanar ba....


Sai bayan sungama karatu ne ta fito  mishi da abunda ke zuciyarta,kuma tun anan yagaya mata shi baida ra,ayinta Dama yasan abunda ke ranta,wanda shiyasanya har tayi yadda zatayi tashigo rayuwarsu........

Batayi mamaki ba tunda tasan shi mutunne mai sanya ido akan abunda yake ganin kamar  zaizamo cutarwa agaresa tasan cewa sai da yayi bincike kanta kafin ya yadda ta shigo rayuwar su...

wanda A yanzu ma a hospital daya suke aiki,anan ma tabiyo su,tanemi aiki anan saboda shi

duk da yafito fili  Yagayamata baida ra'ayinta hakan baisa ta saduda ba saima kara kutsa kanta da takeyi agareshi wannaan kenan....

Bayan kamar minti goma haka,bayan ya idasa kimtsawa cikin shigarsa ta gajeran wando milk da riga ligt purple,yatako ahankali inda wayar tasa take yashe akan gadon zara zaran yatsunsa ya sanya yadauki phone din,danna power yayi wanda take wayar takawo haske,inda yafara kallon notification,inda yaci karo da  message from blood line yadanyi mamaki kad'an na meyasa bai kirasa ba,har yaso yashare  mxg din kamar farko da yake tunani Dr.malini ce ....

A hankali ya bude mxg din inda naga anyi  rubutun  da yaren india kamar haka "Dude Naga car din nagode"abunda kawai sakon ya kunsa,yakaranta sa yafi akirga,he ask him self morethan three times  why Aj thanks him like that?daga karshe dai ya yanke shawarar kiran layin nasa....

Kiran wayar Ammar ne yashigo a wayan Dr aj inda naga an rubuta bloody yanaganin kiran yadakale,wani kiran ne yasake shigowa awayantasa,yayi kwafa yana picking call din cikin jin haushinsa,wayan yasanya akunnensa yayi shiru,A bangaren Dr ammar shima shirun ce tabiyo baya,A hankali ya furta kai ka turo mun sako dan yakara tabbawatarwa duk da yaga numban sa ce..

shiru dr.aj yayi masa yak'i kara cewa duk sa yaji yamaimata masa tambayar,shiru ne yabiyo baya Dr ammar yagama tambayar shi....

………Allah sarki Dr.AJ  Bawan Allah Kana hak'uri.

  Dr.Aj ne ya katse shirun nasu YAna watsar da tambayar da ammar yake masa,dacewa banga motar ba ni yanzu ma ina nan gefen titi inda motar ta tsaya nida bodyguard dina,shiru Dr.ammar yayi yana sauraren Aj yana k'ara tunano da sak'on da ya rubuto masa na godiya...

No wonder shiyasa ashe yayi masa godiya ashe  yaron da ya tura bai kaimasa motar ba,to meya faru?ya tambayi kansa,iee zuwa wannan lokacin da yake maganr zuci har ya fara hasala  zuciyar ta maza ta motsa,katse kiran yayi,yazari car key dasauri da wayar sa a hannu yafito bai zarce ko ina ba sai inda had'addun motocinsu suke parkey gwanin burgewa, kamar motocin DLD😂.....
Bodyguard dinsa naganinsa suka taso da sauri  dakatar da su yayi ta hanyar d'aga musu hannu,cikin katsa musu tsawa ya furta musu cikin harshen turanci "what d hell are you  fucking to do guys? Duk sukayi shiru suna zare ido cikin yanayin tsoro sudai asanin su basu masa komai ba kuma ba halinsa bane......
To meya hasala haka?d'ai daga cikin sune yafurta sorrry sir  may be he does'nt have charge and he don't want to tell you directly sir,dan yafahimci inda bacin ran na ogansu yasamo asali tunda yaga haryanzu enuuch bai dawo ba wanda ya bawa Car  key...

Dr.Ammar komai bai cemasa ba yadanna makullin haddadiyar motar dake hannunsa dan danan had'addiyar motar farar motar kirar lemozing ta bude kanta gwanin burgewa murfin yanayin sama,shigewa sa yayi ahankali yadannan wani abu acikin motar ta rufe da kanta kamar ba,a budeta ba,mai gadinsu wanda yake d'ai daga cikin yarannasu ne ya wangale katon gate din gidan ganin ogan nasu ya doso wurin gate tafiyar minti uku ta kawo sa bakin gate din gidan wanda yake wangale,yana isowa yataka wani burki yana zuge glass din motar,yana furta kabawa sauran yan uwanku sako kar wanda yabiyoni in nafita i want be alone,yakai karshen maganar cikin bada umurni,dan ya hango su sun shisshiga motocinsu ,cikin rusunar da kai ya furta yes sir dan shi bai san abinda ke faruwa ba saboda shi nashi aikin tsaron gate ne.........

💫Fa'eeh Bg💫
ba yawa kuyi manage dashi 
Banda lafiya ne,Ina barar  addu,arku🙏


To be  continue tomorrow in sha Allah 

Pls Dan Allah kurika comment domin shine kwarin gwaiwarmu 💯🙏🙏


like  share nd comment pls

💫A MAFARKI NASANTA💫
    in my dream i know her 
                 By
Pha'eezah Almstapha 
   Daga Alkalamin ✍️✍️
      💫Fa'eeh Bg💫

Dedicated to my  lovely sis laila Almustapha Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION
            💫P.E.W.A💫
Home of perfect essential writer's together we stand 🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️*
pen🖊️ is mightier than the sword🗡️*


EPISODE1️⃣
FREE PAGE1️⃣2️⃣

TYPING 📲📲📲


*Announcement*
Ina tunatar daku  A mafarki nasanta ba  free book  bane,yanzu muna kan free pages ne da mungama  free pages za,a fara payment......gamasu bukata👌


~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Yana gama maganar sa ya figi motar da karfi jikake tana wani k'uuw,suma yaran sa dake bayan sa ahankali suka tada nasu motocin bayan fitar sa gate suka duk da sun hango gate man yana kokarin rufe k'ofa.....


Suna isowa bakin d'in suka dakata,d'aya daga cikin su ne ya furta sir bude muna gate d'in ,saboda dukansu ya girme su,shiyasa aka bashi tsaron gate...


A hankali wannan tsohon  gate man din ya mayar musu da amsa cikin yaren india domin shi baya jin turanci,ya furta Dr.yace kar wanda yabisa,jin wannnan magana tasa ta tayar musu da Hankali,shi  bai ma  san yadda abun  yake ba sai da suka sanar dashi,an aiki enuch da mota yakaiwa Dr.Aj amma har yanzu bai je ba,kuma meeting  din na gaggawa zaije....

Dan danan hankalin sa yatashi,dan dukkansu sun san muhimmancin wannan meeting da uwayen gidansu zasuje,saboda meeting ne daya tara manyan likitoci na kasashe daban daban,gashi d'ayansu bai je ba tun da in d'aya yaje a wani lokacin ya isar sai d'aya yayi attending a system live  ta hanyar comference call da ake hadawa ga wayenda basu samu damar halarta ba..

Jimami suke atsakaninsu,d'aya daga cikin sune yayi k'arfin halin furta guys muna cikin matsala idan wani yasamu Dr.bazamuji dad'i ba domin munyi ma gwamnati rantsuwar karemata su,kuma munyi rantsuwa ga abun bauta shiva,dan haka dole mu daure hakan nan mubisa duk da yayi warning namu ......Ga ra nasa fushin da wanda lord shiva zai yi damu 

......Kunsan indiyawa da rikon Addini.....
Allah yakyauta,yakara tsare muna imanin mu🙏


Bayan sunyi na,am da maganar ta dan uwansu sai suka nemi gate man da ya bud'e musu gate din wanda shima yayi na,am da shawarar tasu duk da shi musulmi ne,duk da kuma ta wani gefen yana jin shakku,wanda suma sauran duk hakance azukatansu.....
......nima dai anan alkalamina yakara k'aimi wajen dauko muku rahoto.....Ku cigaba da bibiyata.......

      💫Fa'eeh Bg💫
Ficewa sukayi  atsare cikin gidan a cikin manyan2 motocinsu kirar hillux da wasu daga cikin normal car nasu bakake wulik,bayan wangale musu gate d'in da yayi..

************************* 
Suna fita ya rufe gate din yana jimamin Abinda zai biyo baya.

A bangaren Dr.Ammar kuwa bayan fitar sa bai zarce ko ina ba sai inda Dr aj sukayi parking na motocinsu,Domin gudu ne yayi ba d'an kad'an ba, ta hanyar amfani da Gps tracking ya isa inda suke, A  hankali   ya tunkari motar da Aj yake ciki duk da yaji gaisuwar da yaran suke masa amma ba wanda ya tankama,Dr aj dake cikin mota har sakon zuwan Dr.Ammar ya iso masa ta hanyar Babban yaronsa dake gefen motar atsaye....

A hankali yaron Dr aj dake atsaye kusada murfi motar  ya bu'de  masa murfin bayan  motar ,mai makon ya shiga sai yayi tsaye yana k'arewa cikin motar kallo,Bayan kamar minti biyu yasanya yasanya k'afarsa d'aya a hankali ya zauna yana mai k'ara tamke kyakkyawar fuskarsa,A hankali itama dayar leg dinshi ya janyeta zuwa cikin motar kamar wanda ankayiwa dole shiga,shiko Dr.Aj duk da yasan da zuwansa kuma yaga shigowarsa bai nuna masa ba yamai da hankalinsa kan meeting d'in da yake  kallo live a yar madaidaiciyar tvn dake makale akujerar driver,wanda ake gudanarwa ahadadden hall na garin mumbai mai suna......
( MUMBAI  EXPENSIVE HALL )
wanda shine Babban hall wanda gwamnatin  india ta zube mak'uddan kudade gurin ginshi,wanda yaji kayan more rayuwa ta ko ina....

Shima Dr.Ammar  baice masa uffan ba kawai yayi joining meeting din ta hanyar kunna tvn dake bayan kujerar dake gabansa tare da makala bluthood a kunnen sa kamar yadda aj din yayi,cigaba da kallon  yadda meeting d'in ke gudana sukayi,Bayan yayi joining duk wanda ke gurin yaga Dr ammar A hankali sukayi ta daga masa hannu alamar gaisuwa shima yana d'aga musu  .....Bayan sungama  gaisawa suka ci gaba da gudanar da meeting din su kamar yadda suka fara banbancin kawai dr.Ammar ayanzu yana musu yan gyare gyare ne,ko yayi solving wani issue  tunda duk suna ganinsa ..

Dr.Aj ba abunda yake face murmushi da alhinin halayen dan uwan nasa baiyi zaton zaiyi joining meeting ba haka,ganin rigimar da suka sha tashi bazai je ba sai dai shi yaje ya wakilcesu,haka dai suka gama gudanar da meeting din atsanake  har suka kai matsaya sukayi conclusion suka watse,sukuma suka kashe tvn....

Enucch ne yak'araso jiki asanyaye bayan ganin motar  ta uban gidan nasa,Parkeyn yayi agefe,ya gaiggaisa da "yan uwansa,tsaye yayi gefen da ogan nasa yake,Bayan  tsayuwar da minti biyar sai ga sauran bodyguard din sun iso gurin ta yin amfani da location,duk suka firfito daga  cikin motocin su a hargitse......

A bangaren su Dr aj kuwa bayan gama meeting din su,shiru ne yabiyo baya,Dr aj yakatse shirun nasu ta hanyar furtawa Dr ammar wanda ke jingine da sit dinsa idanunsa alumshe,cikin murmushi "meya ka woka nan"shiru yayi masa duk da yana jin sa,"fitar mun amota"
wannan furuci na Dr aj ne yasanya sa a hankali ware manyan idanunsa masu cike da kwarjini da haske ga kwayar idonsa maroon mai shining,Kafe aj yayi dasu wanda har sai da Dr aj yakara ja baya yana furta lafiya?

Shiko uban gayyar murmushi ne ya wanzu akan kyakkyawr fuskar sa,yana ficewa daga cikin motar koda yafito enucch ya fara cin karo bawan Allah yana ta kame kame am yallab'ai sir kayi hakuri wallahi namanta wayana a gida kuma ina tsoron komawa gida bayan nayi nisa karkaga kamar namaka rainin wayau ko yanzu ma su joshu ne nakira da karamin wayana suka min kwatancen gurin (dai daga cikin yaran aj).......


~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Duk wannnan maganar yanayinta da indiancine saboda shina bai jin turanci,kuma duk abunda yake fadi dr ammar najinsa sai dai bai ce masa komaiba har ya  isa inda ya parka motarsa yaren sa dake gurin duk suka taso da hannu ya dakatar dasu yana shigewar sa motarsa ......

Reverse yayi yabata wuta sai kan titi tare da shara raara gudunsa,shima dr aj umurnin ya bawa yaransa wanda cikin minti daya suka bar wurin har yaran dr ammar din....

~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
Alkalamin Fa'eeh Bg mai kaifi ne kamar wuk'a,kucigaba da bibiyata dan jin karshen wannan labari mai cike da abun tausayi,soyayya,cin amana,ta,addanci duk acikin littafin amafarki nasanta....Nasan wasu zasuce ai haryanzu ba,a fara nuna mafarkin ba😂to karku damu kudai sanya hakuri duk zamu kai chan .......

Dan Allah kurka comment domin shine kwarin gwiwarmu akoda yaushe🙏

💫A MAFARKI NASANTA💫
 in my dream i know her 
            By
Pha'eezah Almstapha 
   Daga Alkalamin ✍️✍️
      💫Fa'eeh Bg💫

Dedicated to my  lovely sis laila Almustapha Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION
          💫P.E.W.A💫
Home of perfect essential writer's together we stand 🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️*
pen🖊️ is mightier than the sword🗡️*


EPISODE1️⃣
FREE PAGE1️⃣3️⃣&1️⃣4️⃣


TYPING 📲📲📲

---------------------------------------------------------------
Lokacin da Dr.ammar yatashi motar Sa har ya hau kan titi duk akan idon Dr aj murmushi kad'ai yayi yana girgiza kansa....

A b'angaren Dr .ammar kuwa yana kawowa bakin gate d'in gidan ya dannan horn sai ga k'aton gate din yana wangalewa,Wanda dama gate man din yana kusa da controller din gate din ya bude masa.

Yasanya hancin motar cikin katafaren gidan nasu yana dosar parking space,bayan yayi parking dinta a inda yadace
Ya fito da had'addiyar kafar sa mai sanye da wasu rufaffun takalma boot  masu kyau milk colour sannan a ahankali yasanyo dayar waje tare da gangar jikinsa,mik'a yayi  sai kuma a hankali  yafara takawa bayan rufe motar tahanyar danna key din dake hannunsa,katon falon nasu ya nufa zama yayi daya daga cikin cusion dake d'akin yana sauke nannauyiyar ajiyar zuciya,sai kuma ahankali ya lumshe idanunsa....

Motocin su Dr.Aj  ne suka shararo harabar gidan bayan bude musu gate da akayi,A hankali suke diddirowa daga motocinsu,wanda shima dr aj yafito daga motar tasa bayan bude mishi kofar da bodyguard dinsa yayi.

Kofar shiga falon yadosa,sukuma sauran yaran suka gyara parking nasu...Sallamar da yayi ce tadawo dr ammar tunanin zucin daya kasance masa dole akullum inyayi mafarkin nan nasa to duk yinin ranar zai kasance acikin tunanin sa ne,badai natsuwar zuciya,
A hankali ya bud'e manyan idanunsa da suka dan fara sauyawa na damuwa,ya dora su akan,Dr al amin aj,dake gefen sa wanda har yazauna ma,A hankali  kuma yadauke idanunsa  kan aj din wanda shima kallonsa nasa  yake yi dan ya fahimci kamar akwai damuwa a fuskar dan uwan  nasa.......

A hankali dr.Aj yafurta masa meye matsalar dude,shirun daya masa shi yakara tabbatar masa da zarginsa na cewa tunanin dake kezo masa arai bazasu wuce mafarkinsa ba da kuma mahaifinsa, sai mahaifiyar wadda ke yawan yin fushi dashi akan sarautar da baida ra,ayi kanta...
Bayan ya k'ara k'are masa kallo sai kuma yadafashi ahankali yana furta calm down man anything will be fine ohk!yakai karshen maganar cikin tausayin dan uwan nasa....
-----------------------------------------------------------
A hankali kuwa Dr.Ammar yaware manyan idanunsa kan dr aj sannan yacire hannunsa da ke kan kafadarsa ya mik'e a hankali ya doshi upstair har yafara taka step na daya na biyu  sai ya  juyo   a hankali  yadan kalli aj dake zaune kan rugs yana kallonsa,A hankali kamar bai son yin maganar irin an masa dole cikin zazzakar muryar sa mai yanayin natsuwa  ya furta wa dr aj thanks,wanda koshi dan saboda hankalin sa nagaresa ne da bazai ji abunda ya furta ba da iya labbansa ....

Yana gama maganar ya cigaba da tafiyarsa,shiko dr aj murmushi kad'ai yayi yana girgiza kansa,dan hangosa da yayi ya lakaci tsinin hancin wanda alamace dake nuna yana cikin yanayi mai dad'i,Shigar sa haddadden falon nasa wanda yake ko ina  tsaf ank'ara gyarashi bayan fitarshi,takalmin sa ya fara cire da safarsa bayan yazauna akan rugs dake dakin masu taushi bayan kamar minti biyar ya bude idanunsa dake alumshe bayansa najingine da kujerar ya mike ahankali ya wuce yashige had'adden bedroom nasa,yana maida takalimin a inda suke,Kayan jikin sa ya fara cirewa a hankali komai yana yinsa atsare kamar wata mace yana gamawa yajawo d'ai daga cikin towel nashi dake cikin sip sabbin kal  yad'aura nan take hadaddiyar surar shi takara bayyanar da kanta ga lallausar cholcolate skin din sa sai kyalli takeyi....
Toilet yayi shigewar sa cikin takun kasaita,kansa yasakarwa shower ruwan masu dan dimi suna dukan sa atsaye idanunsa alumshe,bayan ruwan sun duke sa sosai sai yadannan wani abu take shower din yatsaya,kan hadadden katon  bahon wankansa na kwalba wanda kana iya hango na waje daga ciki amma shi bazai iya ganin ka ba,yashige bayan ya cire towel nasa yajefa shi a cikin haddaden washing machine na cikin toilet din..
ya dade acikin bahon wanka inda yayi nutse,sannna ya dauro wanka sa da turarrukansa da shower gel mai kamshi,a natse yafito yana takawa in da jerin towel din sa suke da bathrobe,wata farar batherobe yajawo fara kar gwanin burgewa domin shi Allah yamishi son farar kala shiyasa zaka mafi yawan komai nasa farine,bayan yasanya ta ne yajawo dai daga cikin kananan towel dake wurin ya daura akansa bayan yagoge kansa dashi,kansa yake karewa kallo amadubi dake cikin toilet din....
Ficewa yayi ahankali cikin toilet din bayan yagama tsayuwar sa abakin mirror din yana karema kansa kallo...

Stool din dake gaban kamfacecen madubinsa dake shake da kayan gyara jere gwanin burgewa...
Cigaba da goge gashin kansa yayi mai taushi da walkiya,bayan yazauna,bayan kamar minti uku  ya goge gashin kan nasa da sauran danshin ruwan dake jikinsa,yafara murza mansa na fata mai sanyayyen kamshi kamar turare lungu da sako haka yake murza man nasa  akan fatar sa,bayan yagama neyajawo hair cream nasa mai kyau mai kara ma gashin sa sheki ya murzasa tare da taje sa,dan  danan kyawon sa yakara bayyana sumar kansa sai sheki takeyi,lipsbalm din sa yashafa akan kyakkyawan labban sa pink colour masu laushi,turarukkansa ya fesa tunda kan body spray oud masu kamshi,kala kala wanada akalla zasu kai guda biyar,kan sipdinsa yakoma inda yadan thumprint take kuwa sipdin ya shiga bude kansa,sashen da yake na  under wears da short trouser yamatsa,jawo dai daga cikin short trousers din yayi sky blue color da short fari da kuma best fara sai yakoma sashen armless yazaro mai layin blue ajikin yana gamawa yadanna abun rufewa take ta rufe ruf,cikin natsuwa yafara shirinsa.

       💫Fa'eeh Bg💫
A b'angaren dr. aj shima bayan wucewar dr ammar ya wuce shi dake kusa da na Ammar din daga gefen damar shi dakin yaji komai na more rayuwa,banbancin dakin shine cusion shi nashi maroon color ne dan shi kalar na matukar burgesa da fari kamar dr ammar din.....
-----------------------------------------------------------------
  * Nikam ban ga laifin ku ba domin farar kala tayi,ko mala'ku kagani masu farin kaya tokai kawuce wurin,a kabarin mu ma sune suturar mu domin sune suturar mu takarshe a duniya,Annabi muhammad s a w farin kaya yake sakawa duk ranar idi,haka ma ranar juma,a wannan yana dai daga cikin sunnoninsa...Allah yasa mudace yasa muyi kyakkyawan karshe,Yasa da mu da mala'kun rahama🙏🙏*
------------------------------------------------------------------
shima dai yashityawr sa tsaf cikin irin kayan dr ammar.

A hankali yake taka step step  din da wayar sa a hannusa dayan hannun kuma acikin aljihun wandonsa yana tafiya dai dai cikin izza daga yanayin tafiyar kasan ta zaratan maza ce wadanda suka da mulki iko...
Kamshin turarensa ne yasanya dr aj dagowa daga kan wayar sa dayake kan preesing,wanda ke zaune akan dining table wanda shima bai dade da fitowa ba....
A hankali yatako izuwa kan dining har ya iso inda aj yake,cikin sanyin murya ta gwarazan maza ya furtawa aj  lafiya?yana mai jan kujerar dake facing dr aj,ganin ya tsare sa da idanu,zama yayi yana ajiye wayar tasa agefensa.
Murmushi kawai dr aj yayi yana furta dude dole dr malini ta zauce wannan madarar  kyau haka,ya k'une kyakkyawar fuskar sa yayi jin furucin dr aj din yana sakin karamar tsuka wadda aj kadai yajita shida yake kusa dashi " mts",murmushi kawai  aj yayi yana aje wayar tasa agefe...
 kukunsu ne sajid khan yakaraso  yana fadin afternoon sir yana mai kokarin yin serve na dr ammar,dakatar dashi yayi,da hannu,sai kuma ahankali yajawo dai daga cikin haddadun filet din dake kan dining din yafara saving kanshi,farar shimkafa da miyar da taji  na man sa yadiba sannan yajawo wani filet din ya debi hadadden farfesun kaji wanda yaji hadi sai tashin  kamshi yake yi.
A hankali cin abincinsa dan shi kam ingurin ci ne bai wasa da cikin...
Aj dayake ganin duk abunda ke faruwa murmusawa kadai yayi dan dama yasan abunda zai faru kenan,kusan kullum haka suke shida sajidkhan indai yazo  zai zuba masa abinci cewa yakeyi baiso duk da zaman kukun nasu musulmi,dan shi mutun ne mai bakar tsandar tsiya,ansha chanja musu masu dafa abinci saboda shi,sai akan wannan ne haryanzu baiyi complain ba,shi abun ma dariya yake basa da haushi mutun ya girka abinci amma kace baka son yayi serve naka saboda bak'ar rigima,kara girgiza kansa yayi yana cigaba da cin abincinsa da sajidkhan ya zuba masa....
Motsin chokulla kadai ke tashi a falon sai karar ac,dr aj ne yayi ma kukun alama da ya wuce kawai,a hankali ya dago kansa ya kallesu duk su biyun cikin second guda yamayar da kansa kasa yacigaba da cin abincinsa.....
Bayan wucewar sajidkhan  kitchen suka cigaba da cin abincinsu hankali kwance.

Karar shigowar sako ne a wayan dr ammar yasaka dr aj dago kansa yakallesa,a lokacin shima yadagi nasa,ido daya dr aj yakashe masa yana sakin kayataccen murmushi dan tabbas yasan sak'on wayene yashigo wayar ammar din,shikam dr ammar duk da yaga abunda Aj din yamasa bai nuna ba sai ma cigaba da cin abincinsa da yayi hankali kwance yana mai kara tamke fuskar sa.

Aj yana gama cin abincinsa ya mike tare da daukar wayar yana barin kan dining table din ...............................
A hankli dr ammar shima ya mike yabar kan dining a hankali fuskar nan a tamke,a falo shima yazauna kan 3 sitter wanda shikuma aj yana kan 2sitter yana pressing phonedinsa.
kyawawan kafafunsa ya mike yana mai daura hadadden throwpillow akan dan shafafen cikin sa,har yakwanta kuma meya tuna sai ya mike zaune yana jawo wayarsa dake gefen kafens,thumprint yadanna wanda take takawo haske har yayi niyyar ya wuce sakon da yaga anturo da private number ,sai kuma yaji yana kwad'ayin bud'esa,abunda yaci karo dashi ne ybasa mamaki dan shi baiji alamar shigowar sakon ba dan yaga sako biyu ne suka bayyana na biyunne  wanda yaji shigowar sa shine na dr malini nafarkon baiji shigowar sa ba,ya karanta sakon ya fi akirga har private number din yake karantawa,inda na leka kan wayar  dan ganin abunda aka basa mamaki dan shi baiji alamar shigowar sakon ba dan yaga sako biyu ne suka bayyana na biyun ne  wanda yaji shigowar sa shine na dr. malini na farkon baiji shigowar sa ba,ya karanta sakon ya fi akirga har private number din Da yabayyana yake karantawa,inda na lek'a kan wayar  dan ganin abunda sakon ya k'unsa nan naci karo da rubutu kamar  haka da manyan haruffa da yaren mu na hausa "¿KA NEMI YAR UWARKA TANA RAYE¿?"
..............Tambayar kansa yake yi waya turo sak'on ?…ba amsa ¿
Nima dai kaina yad'aure kowa cece wannan yar uwartasa oho?kuma a waya turo sak'on ????????nima dai ana n alkalamina ya fadi......,kucigaba da bibiyar akalamin✍️✍️💫 Fa'eeh Bg💫domin warware muku duk wani abun da yashige muku duhu acikin littafin a mafarki nasanta...........  Kuyi hakuri da
 rashin samun update jiya hakan yazo sanadiyyar rashin chaji da banida.......
Shiyasa ma na had'a muku page biyu..

Comment kadai nake bukata ko like 
Sannan plskutayani sharing🙏

inayin ku 💯 percent a mafarki nasanta fans💋💋💔 over Allah yabark kauna


💫A MAFARKI
 NASANTA💫
In my dream I know her 
               By 
Pha'eezah Almustapha 
    Daga Alkalamin✍️✍
     💫Fa'eeh Bg 💫
   
Dedicated to my lovely sis Laila Almustapha
 Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION
           💫P.E.W.A💫
Home of perfect essential writer's together we stand🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️*
Pen 🖊️is mightier than the sword

EPISODE1️⃣
FREE PAGE1️⃣5️⃣
 

 TYPING📲📲📲                   

**************
**********
*******
****
***
**
*     
Ina mai kara baku hakuri akan abunda yafaru in sha Allah hakan bazata sake faruwa ba domin mun dau kwakkwaran mataki na farko link dinmu na wannan sabon group  bazai  fita  ko ina ba,sai wanda muka ga dama muka saka..

----------------------------------------------------------------

....Rasa mai basa amsa ne,da kuma wanda zai warware masa sakon  ne yasanya shi goge sa gaba d'aya. 

Sai sak'o na biyu wanda atak'aice yabud'esa ya karanta inda sak'on yak'unshi kalaman soyayya masu zafi da tsayawa arai da  yanayin tausayi acikin kalmomin,ko k'ir baiji ba alokacin da yake karan ta wannan sak'on na Dr.Malini yana gama karanta wannan sak'o na dr.Malini  ya gogeshi yana jan k'aramaar tsuka...

Tare da  jawo tv control yana kara volume da  bayan chanza tasha izuwa ta labarai,cigaba da kallon labaran sa yayi hankali kwance duk da tunanin wannan sak'o da yad'an tsaya masa arai,shidai aj duk da yaga yadda dr ammar yake ta kallon screen d'in wayar sa da alamun mamaki da rud'u bai bai matsa wa kansa da son tambayar sa  ba,dan ya fahimci akwai abunda dr AA yake b'oye masa ayanzu k'ila sak'on sirrine duk da baisan ta ina sak'on zai fitoba,to wane kalan sirri ne wanda Dr.Ammar zai b'oye masa  oho?ba amsa yakice tunanin da yake aran sa yayi jin sallamar d'ai daga cikin yaran nasu yana  neman izinin shigowa.....


Gate man ne yashigo dama shi musulmi ne daga  cikinsu kuma yagirme musu...

Hannu dr.ammar yad'aga masa  yana  basa izinin shigowa bayan amsa sallamar sa dasuka yi, A bangaren dr aj tunani yake aransa meya tado da gate man yanzu...

Bai gama tunanin sa ba yaji gate man din wanda yake da kagansa kaga tsufa atattare dashi yana furta sir gani naga kiran dakamun,aj ya furta wa kansa ohh ashe ammar ne yakirasa ko saboda me,?rasa mai basa amsa yasanya shi zubamusu idanu su biyun....

A hankali Dr.Ammar yad'ago kansa suka had'a ido da dr.aj saurin d'auke kansa yayi tare da lumshe idanunsa,yana mai bud'e bakinsa  a hankali ya ce da wannnan tsohon  mai gadi "hv a seat father"murmushi kawai tsohon yayi mai suna sabirkhan cikakken ba indiye,yana  furta aa'ah sir nagode,aj  dai  kallon su kawai yake suka gaisa da tsohon baik'ara cemasa komai ba.......

A hankali dr Ammar yak'ara  maida kansa k'asa bayan jin amsar da tsohon ya basa ya yi rejecting request nasa,bayan ya bud'e idanunsa dake lumshe,sai yaji duk baiji dad'i ba danshi kam yana  darajja tsofaffi kuma yana tausayinsu,har yanajin hukuncin da yake son ya yanke kamar yafasa na korarsu gaba d'ayansu  da nufin akawo musu wasu sabbi tunda wad'annan basa aikin su yadda yadace danshi baisan kuskure ba,cewa yake gangancine,duk da baiso aka basu suba tun farko........
   
  Bayan gama zancen zucinsa ne ya bud'e dan k'aramin bakin dan karamin bakin sa mai dauke da pink lips da suka sha lipsbalm sai glowing suke,father   
Could I ask you to move a little?you and your colleques sannan ya cigaba da maganar sa da yaren india ga tsohon tunawa da yayi baijin english cikin kwarewa da yaren ,har yagama maganar sa sabirkhan bai ce komai ba face murmushin da yake ta saki,sai da yagama  ya furta masa sorry sir,ya juya yayi wucewarsa ......

Bayan fitar sa shikam aj da yacika da mamaki dan wannan ne  karo na farko da yaji aj ya yanke game dasu batare da shawararshi ba,cikin kafe ammar da idanu ya furta saboda me ?zaka nemi su matsa daga nan gidan kuma har da suspension na wata daya eh?
           yana mai cigaba da tuhumarsa da idanu,Cikin halin ko inkula kamar bazai amsa ba sai kuma ya furtamasa ra,ayi yana gama  fad'in maganar sa yatashi da wayar sa ahannu yayi wucewrsa upstair zuwa bedroom nasa,da ido kad'ai aj yabisa yana girgiza kansa,shima yana mik'ewa ya fice compound din su domin dakatar dasu,bayan yafito ne yatarar dasu cirko cirko atsakiyar compound d'in atsaye suna jimamin umurnin ogan nasu,bayan ya gama kallon gaba daya tare da karantar yanayinsu,yayi gyaran murya,duk suka hankalta dashi suka fara mik'a masa gaisuwa yana amsawa musu cikin sakin fuska....

a hankali ya furta musu kar wanda yaje ko ina nasan ko mene zuwa anjima zai bar maganar zan shawo kansa..

Duk sai sukayi na,am da maganarsa,yacigaba da magana nasan abunda kuke tsoro kar gwamnati taji abunda yafaru na suspension din da yabaku,namuku alkawaro bawanda zaiji,nasan cewa incident din da yafaru d'azu da safe ne yasanya sa baku wnnnan hukuncin duk da banga alamar fushi afuskarsa ba,dan shi mutun mutune wanda baicika bayyyanar da fushinsa ba...

Godiya duk suka masu nuna jin dad'i har ya juya sai sabirkhan ya tsaidashi ta hanyar fad'in sir,juyowa yayi dan ga tsoho sabirkhan yace da aj yallab'ai ban tari numafashinka ba,amma inaga da kabar hukuncin yadda yake saboda ina da tabbacin duk wannnan abun akan ka yayasa saboda fahimtaar da yayi ranka ya sosu alokacin da aya aika akaima maka mota,kuma ba,aje da wuri ba,shiyasa,dan nima na fahimci bada son ransa ya furta musu maganar suspension ba ,shiyasa tunda yafara maganar sa ban nuna alamun b'acin rai afuskata ba sai dai murmushi da ya wanzu akanta,inda ka lura ko d'ago kansa baison yi gudun had'a ido dani,kabarshi kawai dan inyaga katsaidamu zaiga kamar ka kwatse sane.....................

Murmushi kawai aj keyi har zuwa lokacin da tsohon nan yagama maganar sa,yak'ara da cewa kuma inada tabbacin ransa ya b'aci matuk'a dan naga alamar hakan alokacin da zai fita suka biyosa ya furta bai bukatar kowa ya bisa acikinsu....Kuma kasan  halinsa baison ya sanya doka atake,nasan wani laifin ne kuma binsa da sukayi,mukuma yallabai kasan munyi rantsuwa akan zamu kare ku ta ko wanne yanayi kuma nasan kasan mahimmancin rantsuwa.

Uhmm aj ya furta yana mai girgiza kansa tare da sakin murmushi a fuskarsa,toh shikenan father dan haka suke kiran tsoho sabirkhan,kuje amma nan da kwana uku ku dawo nasan zuwa lokacin ya sauka ya furta musu,touh suka amsa masa dashi.Suka fara watseqa suna shisshiga motocinsu domin zuwa quaters nasu dake chan gaba da gidan su aj,bayan sun mimmika car keys ga aj dakuma gate controller...
Dr.Ammmar dake chan tsaye kan windown din dakinsa ne ya furzar da iska mai zafi abakinsa yana mai jin ba dad'i aransa duk da yasan yayi ne  dan ya farantaran dan uwansa,A hankali yabar bakin window din yana komawa kan hadadden gadonsa ya kwanta flat yana kallon ceilling  daga shi sai towel dama fitowar sa  daga wanka kenan....

Aj nashiga  shima ya wuce nasa dakin wanda izuwa lokacin har ankara gyara falon sai tashin kamshi yakeyi ankwshe food flask din dasuka ci abinci angyara lungu da sako sai sanyin ac daya kara ma falon natsuwa ko ina masha Allah.

      💫💫Fa'eeh BG💫💫

Aj ne bayan  shigarsa nasa dakin  ya aje car keys din da gate controller din ya jawo wayar sa yana dialing numban sabirkhan gate man....
Bayan yad'aga kiran sun gaisa cikin mutunci,tambayar sa yayi daya turo mai dai daga cikin yaransu wanda zai kula da gate din kafin su dawo aiki to kawai yace sannan sukayi sallama...

A b'angaren dr.Ammar nan bacci yakwasheshi bai farka ba sai dayaji ana kiraye kirayen sallar la,asar,A hankali kiran sallar  ke shiga kunnuwansa mikewa yayi a hankali yana addu,ar tashi daga bacci tare da ambaton kalmatu shahada.....fuskarsa yake yamutsa wa bayan duba hadadden agogon dake kan bedsite drowernsa hud'u dai dai  ya gani ta buga shi yasanya sa tashi da hanzari dan yaga lokacin yayi kusa,ankusa tada sallah,shaf shaf yashiga wanka  bayan yayi brush yayi wankansa tare da dauro alwallah,bayan yafito tsane jikinsa dayayi turare kadai ya fesa  sannnan ya bude sip din sa yazaro dai daga cikin jallabiyoyinsa  da short,da vest baka dasauri yazura jallabiyar bayan sanya underwears din yasauka kasa yana ta sakin kamshi,koda yasauko kasa yatarar da aj tsaye yana jiransa,shima cikin shirin jallabiya irinta dr ammar sai dai banbancin colour shi aj tashi fara shikuma ammar dark maroon wadda ta karbi fatarsa,ba wanda yaceda dan uwansa kala  har suka  fita falon suka shigamota aj yajasu zuwa masallaci....Dama mai gadin ya iso yakarb'i gate controller din suna zuwa ya wanagale musu gate  din ta hanyar danna remote din,yau da mota suka fita ganin sun makara ,duk da masallacin basu da nisa dashi cikin unguwar tasu ta manyan masu naira maisuna gujarat 105 estate.......

Next page monday in sha Allah
Like  pls...Nd comment 



  * Allah yasa mudace*🙏🙏
Pls like share and  comment



💫 A MAFARKI NASANTA💫
      In my dream i know her
                      By  
   pha,eezah Almustapha
       Daga Alkalamin✍️✍️
        💫Fa'eeh BG💫


Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION📚🖊️

        💫  P.E.W.A💫

Home  of  perfect essential writer's together we stand🤝
  
      ESSENTIAL  WRITER'S 📚🖊️
Pen*🖊️is mightier than the sword🗡️*

EPISODE1️⃣
FREE PAGE1️⃣6️⃣

TYPING 📲📲📲

--------------------------------------------------------------*DRUG ABUSE  
 🚭❌❌❌
SHAYE SHAYE ILLANE GA RAYUWARMU,INA SAMARI, INA YAN MATA KU GUJI TA AMMALI DA MIYAGUN K'WAYOYI DOMIN  SUNE ABU MAFI SAURIN HALLAKAR DA RAYUWAR MU....MUNA📢📢📢 KIRA DA BABBAR MURYA,DAKUMA BADA SHAWARA A GUJEWA DUK WANI KAYAN MAYE DAN SAMUN INGANTACCIYAR RAYUWA MAI AMFANI*
-------------------------------------
HANYOYIN DA ZAKA KARE KANKA💁 DAGA AIKATA WANNAN DABI'A SUNE 
*KAUCEWA ABOKAN BANZA
*ZAMA DA MUTANE NA GARI 
*SANYA TSORON ALLAH AZUCIYAH
*BADA SHAWARA TA KWARAI GAMASU AIKATAWA
*CIRE KWOKWANTO GA AL AMURRANKA
*KAUCEWA MASU AIKATAWA 
*YADDA DA KADDARA KO WACE IRI CE ILLA MAI KYAU CE KO MARA KYAU CE.

🙋🙋MU KIYAYE DOMIN RAYUWAR MU ABA CE MAI AMFANI ATATTATARE DAMU,DOMIN AMANA CE UBANGIJI YA BAMU....ALLAH KAYIMUNA MUWAFAK'A🙏🙏
----------------------------------------------------------------
**********
*****
***
**
*Bayan sun dawo daga masallaci suka cigaba da kallonsu afalo a tashar da ake hasko wasan ball, har magriba ta gabato suka dunguma akafa sukaje a wannnan karon domin sauke farali...
 
"kowannen su dakin sa yawuce direct bayan bayan dawowar daga sallar dan fresh up,AA ne fara fitowa Dan bakar yunwar dayake ji shiyasa bai tsaya shiriritar sa ta shiryawa ba,dama yunwa ce kadai kesanta sa yayi gaggawar yin abu sa dasauri sai kuma in yasan suna da tarin patient da zasu gani ko kuma akwai emergency case a hospital din....

A hankali ya doshi kan dinning din nasu yana baza kamshi cikin shigar short trouser fari da kuma vest blue wadda takara haska fatar sa ...

''zaman shi keda wuya sai ga sajidkhan dan dama yaga fitowar ogannasa daga tagar kitchen ta chan mai kallon dining,

"barka da dare yamasa sannnan yajawo pilet yana mai bud'e manyan food flask dake kan dining din masu kyau,duk da yaji bai amsa masa maganar sa sai ya furta sir mai za,a zuba  maka,"Anything" ya furta atakaice
 Tuwon semo ya zuba masa da miyar egusi da taji busasshen kifi,ya dora masa agabansa tare sa sanya masa spoon a ciki da zuba masa ruwa a karamin cup na glass da lemu,A hankali ya fara cin abincinsa,Aj da tun d'azu ya iso wurin yaga abunda yafaru  yau Dr AA ne ya bari kuku ya zubamasa abunci...Yasan cewa bak'ar yinwa ce nanake da cikin sa shiyasa ya yadda amma da ba haka ba da kai tsaye zai dakatar dashi....

"Kansa kawai ya girgiza yana mamakin halin dan uwan nasa

"shima dai tuwon shinkafa da miyar wadda taji naman sa rago  ya  zaba,bismillah yayi cin abincinsa hankali kwance kamar ammar din,Muryar Dr ammar ce ta karad'e gurin yana mai furtawa sajidkhan "have me some water in a rubber"cikin calmly voice dinsa,ohk sir!ya furta, ruwan ya kawo masa aroba mai dan fadi

"hannunsa yacire dake kan spoon ya kada sa acikin robar ya ya wanke hannunsa sannna yasanya acikin filet din tuwonsa,Yunwar da yake ji bazata bar sa cin abin da spoon gani yake kamar yana bata masa time,domin shi mutunne da baya wasa da cikin sa,shiyasa ya cire spoon din yasanya tattausan  hannunsa,mai da robar sajidkhan yayi kitchen ya maida robar ma,ajinta bayan yayi discard din ruwan..
  
Abincinsu suke ci hankali kwance,musamman dr.Ammar wanda kaikayi zaton manyan lomomi zaiyi daya sanya hannu sai dai ahanklai yake saka abincin adan karamin bakinsa cikin natsuwa kamar ma bai tauna tuwon..Yana gama cin semo dinsa yayima sajidkhan alamar akara masa,Sai yanuna masa na shinkafa,a wani sabon filet din ya cigaba da cin abincinsa hankali kwance..

Shikam Aj tuni yabar kan dining din yana waya wanda daga ji macece ta hanyar yadda yake mayar mata martani......

Shima dr ammar nagama cin abincinsa ya mik'e ahankali ya wanke hannunsa a sink din dake gefen dining din,lura da akwai aikin da mai aikin nasu yake yi akitchen din....


Wayar sa yadauka  kawai yawuce warsa falo  cikin tafiyar kasaita wadda sarauta tagama ratsa jikinsa,da zuwan sa yazube akan 2 sitter yana lumshe idanunsa jinsa yafara dawowa nrml da yunwar da ta dibesa, bayan kamar minti biyu ya lura da wayar sa aj din keyi,wanda koba,a fad'a ba yasan sumayya ce yake waya da ita wadda ke bima aj din,Amma anfi kiranta da sumy .....................................................………………

       💫 Fa'eeh BG💫

Jin tambayar da yayima nacewa ina Auta husna ne yasanya sa kara tabbatarwa.

Ahankali ya kunna piano game yana bugawa cikin kwarewa da natsuwa,Maganar da aj yayi ce tasanyasa dakatar da game din,inda aj din ke furta wa sumy din kin raina ni ko sumayya tun yaushe nace kibar min wannna maganar amma bakya ji  koh,yakai karshen maganar da yanayin hasala,cigaba da maganar yayi yana furta ki sani matsayi daya na dauke ku da ita,nace kibar mun maganar NISA domin kuwa itama kanwa ce agurina bayan wannnan  babu komai,daga chan dayan bangaren naji ana furta sorry yaya aj,shiru yayi bai tankamata ba jin wata murya mai sanyi nakwala kiran sumy!sumy!wanda har sautin yake ratso kunnuwansa daga cikin wayar ..
  

Chanza firar da dayan bangaren akayi shi ya tabbatar yakara tabbatar  masa da muryar da yaji,Ajiyar zuciya yasauke ab'oye ya makarnata ya furtamata kamar basu yi wannan gaisuwar ba inda take furtamasa ya aiki,lfylau ya furta itama tana furta karatu alhmdllh,Bayan jin ta amsa ma wadda ke kiran sunan nata,ta hanyar furta na,am nisa lafiya wannnan kira haka da murmushi a fuskarta ta furta kizo anfara shirin" imlie " dan suna matukar son shirin wanda starlife suke haskawa  akullum mai dogon zango ,musamman nisa wadda sunan ta yake (yuhanisa)tana mugun son shirin dan ita takoyawa sumy sonsa,a cewar ta jarumin mijin imlie na farko yana kama da yaya aj dinta dan tana mugun son aj kamar ranta,sumy kadai tasan da maganar sai kuma wasu daga cikin kawayensu.......


Fahimtar da nisa tayi sumy waya take kuma da  yayansu ganin yadda ta natsu,yasanya A hankali ta karaso kan gadon tana mai fadin allah yasa baiji ni ba tana rufe dan karamain bakinta,Murmushi ne ya subucewa dr.aj jin radar da tayuwa sumy,sannnan ya furtawa sumy bata wayar,A hankali sumee take mikamata wayar itama tana murmushi da addu,ar Allah yabawa kawartata ya yannasu ta yi wucewar ta falo...

A bangaren dr AA najinsan kuma yaciga da buga game dinsa,dan tun dazu Aj yamayar da wayar handsfree sanadiyyar rashin network na kirki da babu baiji sosai..
..........Shiru ne ya biyo baya bayan ta amshi wayar,A hankali  tace yaya ina wuni murmushi yasaki yana furta kinmanta mu yanzu dare ne,laah ta furta tana rufe bakinta mai kama dana yayanta,tamboyi yamata game da kart tana amsa masa da alhmdllh cikin dan rashin sakewa dashi 

Shiru ne yabiyo baya sai kuma ta katse shirun nasu,ta hanyar furta masa ina yaya Ammar ?
yana jin sautin Muryar kanwartasa sai   dai yayi kamar baiji ba,duk da kallon da aj ke masa domin sarai yasan yanajinsu ...

Jin tana magiyar abatashi inyana  kusa yasanya a hanklai yabaro kan kujera din sa yake yadaw kan hannun kujerar da aj kezaune,dan jin raunanniyar muryar kanwartasa  tana rkon akan kawai taji muryarsa yasan  duk laifinsa ne da baya cewa abasu waya inyakira,tunda basu da waya har yanzu basu bada izinin abasu ba wayan saboda kallon kananan yara da suke musu,ganin haryanzu basu gama secondry ba,a yanzu suna ss 3ne  akarshen shekara zasu gama..


Hello!"yaya A ta furta tana sakin kayataccen murmushinta da hr aj dake kusa dashi yaji sautinsa dan yacire handsfree  din bayan amsar wayar daga hannun aj..

Shima murmushin yasaki yasaki har saida dimple dinsa suka loba gwanin burgewa  dama ayanzu duk kaga murmushinsa irin haka  mahaifiyar sa ce ko kanwarsa wadda takasance ita ce autar su,suna mugun son juna datausayin junansu musamman Babban yayannasu da ayanzu yake abun tausayi...
hw are u ?fn ta furtamasa,ya schl da krt  yakara tambayar ta ta furta masa Alhmdllh,Anbar doja  koh tace ce eh cikin murmushi toh acigaba da kokari duk da bai yadda  da maganar taba yasan su da rashin son zuwa makaranta tun suna kananan .

A hankali ya tsinkayi muryar ta tana tamabayar sa,yaya A yaushe zaku zo kugammu?murmushi yasaki yana fadin ashe kina  gidan maaminah yayi hakan ne dan kawar da tambayar tata,ehh ta furta yau sati na daya,ohk!ya furta tare da tambayar ta inasu husnat da sumayya,"duk suna falo ta furta to ki gaidasu,toh ta furta cikin sanyin jiki jin yakawar da tambayar da tamasa don dama ta harbo jiginsa....
Yanzu dai je ki bawa maaminah wayan dan haka yake kiran kanwar ta mahaifiyarsa,mahaifiyar Aj,Hajiya husaina,kai yaya batasan andauko wayanta ba nima na isko sumy da itane,kuma yanzu intaga mundauko fada zatayi,murmushi yayi dan yasan halin mamin da bata daukar wargi duk da zaman ta nason barkwanc,kuma  dama  yasan basu fada mata zasu dauka ba,tunda yasan basuda waya,murmushi yakara saki yana mai fadin "to kudaina daukar mata bada izininta ba,babu kyau hakan,kurika tambayarta indai kungayamata ta "ya 'yanku zaku kira zata baku kunji koh"tau  yaya in sha Allah ta furta.....

"in sha Allah inkuka samu result mai kyau a qualified exams naku zan siya muku waya mai kyau,murmushi tasaki mai hade da dariy tana fadin dagaske yayah ,kansa yadaga kamar yana gabanta yana furta eh,i love you so much yayah,proud of you the best brother in the world takai karshen maganar cikin farin ciki marar misltuwa domin dama sun matsu asiya musu wayoyi saboda mafi yawancin kawayen su na da ita,"me too ya furta cikin farincikin dayasamu kansa aciki Bye ki je ki aje waya yanzu kar taganku koh,toh yya tafurta tana masa godiya da sallama suna yanke kiran.........
Kowa ransa fess,cikin murmushin sa mai kara kawata fuskarsa ya juya ya dubi aj yana furta masa take your phone yana  kara furta bari inje in dauro alwallah naga isha'i tagabato,da ohk kawai Aj ya bisa,shima yana mikewa yarage voluke din tv yana chanza tasha izuwa inda ake kira,ar qur'ani,ya wuce upstair shima tare da wayansa shaf shaf dukkaninsu suka dauro alwallah suka wuce masallaci don gabatar da sallar isha'i acikin jam'i....

Bayan dawowarsu aj kashe wutar falon da tvn kowa ya wuce nasa bedroom din dan yin bacci bayan sunyi sallama wannan kenan.........

BACK TO THE PRESENT .....
Murmushi kawai Dr aj yakara saki bayan gama tunano abunda yafaru kwana biyar da suka wuce yana mamakin  hali irin na abokin nasa kuma dan uwansa.

Godiya bodyguard din nasu suka k'ara masa kafin suka koma gurin da dr .Ammar d'in yake tsaye shima suka kara masa godiya da basa hakuri,karbar jakar hannun sa daynsu yayi domin kaima sa office nasa.

Wanda shima bangaren dr aj hakance ta kasance agurinsa..
 A hankali suka doshi hadadden hall din da yake cikin wannan katafaariyar asibitin ta mumbai wadda take da dubbanin tarihi na cigaban da ake samu ta hanyar  kula da marassa lafiya shigarsu katafaren hall din daya tara dubbanin likitotah masu ji da kud'i da wanka,kowa yana zaune akan kujerar da take mallakinsa wadda ke dauke da sunansa.

A Hankali suka fara gudanar da taron cikin kwanciyar hankali,dama suna meeting din ne kan cases da ake yawan samu ne akan yawan mutuwar mata awajen haihuwa,suna son gano dalilin da silar faruwr hakan cikin alumma.......

..........................................
Kudai kucigaba da bibiyar 💞alkalamina…………A  sannu zan warware muku wannan labari maicike sa tausayi,nishadi ilman tawarwa,soyayya,sarauta,cin amana,ga xumuncibugu da kari kuma ta,addanci wanda yakasance abunda yake ciwa alummar mu tuwo akwarya ganin yadda shuwagabbani suka zuba ido aalamarin  da har yanxu ankasa samun mai yin katutu da al amarin,ganin kamar sunfi karfinsu wanda kuma ba haka bane,mu munsan addua bata bar komai insunfikarfinsu ai basu fi karfin ubangiji ba....sannnu bata hana zuwa sai dai adade ba,aje inji hausawa,dan haka karku sanya kucigaba bibiyar labarin....

NEXT PAGE TOMORROW IN SHA ALLAH 
KUTAYANI SHARING BOOK DIN NAN PLS DOMIN AKWAI DARASI MAI YAWA ACIKI ...................


💫 A MAFARKI NASANTA💫
   In my dream i know her
                   By
     Pha'eezah Almustapha
        Daga Alkalamin✍️✍️  
           💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION📚🖊️
    
             💫P.E.W.A💫
  
Home of perfect writer's together we stand🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️

pen 🖊️*Is mightier than the sword🗡️*
---------------------------------------------
TYPING📲📲📲


EPISODE1️⃣
FREE PAGE1️⃣7️⃣

     WANENE DR.AMMAR(AA)
cikakken sunansa Abdulrashid Aliyu Ahmad,haifaffen garin Gusau,jihar Zamfara,Dane  Ga sarki Aliyu  Murai,sunan mahaifiyarsa hassana hamza wadda suke kira da unni,mama kenan ayaren (korea) mahaifinsa da mahaifiyarsa Auren soyayya sukayi,kuma auren zumunta,Mahaifinsa sarki Aliyu murai rikakken Dan kasuwa ne,wanda yake da kaloli kuma manyan kamfanona akasashen daban daban a duniya,A yanzu haka shine yake rike da sarautar ta zamfara  A babbar masarautar murai ta Gusau'Ammar shine d'aa na farko ga iyayensa,sai mai bimasa hamza wanda yaci sunan kakansa na uwa,ana masa lakani da mahir,sai Auta yuhanisa inda taci sunan  yayar kakarta ta uwa,suna kiranta da nisa,Ammar yana da shekara ishirin da takwas aduniya,mahir kuma yanada  shekara goma sha biyar,sai nisa tana da shekara goma sha takwas aduniya,Mahaifiyar sa gimbiya hassana "yace ga wan mahaifin su sarki Ali Sarki,Hamza  murai kenan,takasance yan biyu ita da mahaifiyar aj,sai autar su laila,sunan mahaifiyar su fateema suna kiranta Ammie,Ammar yaci sunan k'anin mahaifinsa Abdul rashid wanda shine autan su  sarki Ali  su uku ne maza,suna da mace daya mai suna khadija,suna  kiranta mama dije wadda ke aure agarin kano tana auren wani custom,tana ya guda sunanta umaimah,wadda ita kadaice rabonta,tun rasuwar yan biyun ta na fari,sai kuma umar shine ke bima sarki Ali murai,Sai Abdul rashid ,sannan khadija,sunan mahaifiyar  su sadiya suna  kiranta hajiyar safkare,a takaice hajia,dukkanin su sunyi aure,..........Dr.Ammar yayi karatunsa tundaga  secondry har tertiary a kasar india inda kuma kuma yasamu aiki achan shida aj,Dr ammar mutun ne mai tsantseni ga tsandar tsiya duk da yana da laziness bai yadda yasaka ma kansa kanzanta ba,baida daukar raini,dan gayu ne na asali,baida daukar raini,kuma bai da wulakanta talaka hasalima shi mai tausayinsune,mutun daya ne yake iya wa da halinsa shine dr aj kuma shine babban abokin sa,domin sun kasan ce kamar yan biyu kamar yadda iyayensu suke,dr ammar dai kyakkyawa ne na karshe,har yanzu bai da budurwa duk da harin da yan mata suke kawo masa,natayin soyayyarsu,mutun daya ce tazame masa kamar cingum itace dr malini,domin Allah yasanya mata wani sonshi duk d yana kokarin nuna mata bata cikin tsarinsa hakan baisa tayi sanya ba wannnan kenan...
SAI DR.AJ
Cikakken sunansa dr Al amin jabir muhammad soja,dane ga leutenant jabir muhammad wanda yakasance army ne na nigeria,shine shugaban sojojin arewa,sunan mahaifiyarsa husaina inda suke kiranta ummi,Aj yanada kanne uku inda namijin dake bimasa yarasu tun yana karami mai sunan mahaifinsu jabir ,sai mai bima margayi jabir sunanta sumayya,sai Auta  Asma'u suna husnat,wadda taci sunan kakarta su ta wurin uba,Aj sa,a ne da dr. ammar kwana arba'in ne tsakaninsu,Sai sumee wadda take da shekaru sha tara sai auta husna nada shekara goma sha uku,aj da sun taso komai sunayinsa atare,Aj shima baida wata tsayayyar budurwa har yanzu Wannnan kenan...

*MUDAWO LABARI*
------------------------------------------------------------------
*~~NIGERIA ZAMFARA~~*
*~~ BUG~~*
*~~UNGUWAR SABON  GARI~~~*

...........Bayan fitowar Baba Adee daga wanka Ya shiryawar sa cikin shiga ta kamala dai dai rufin asiri cikin yadinsa mai kyau black,bayan fitowar sa wanka wanda da taimakon Bba Asabe  ya shirya wanda kuma shine dalilin saukarsa da wuri dama shi  ba mutun bane mai riko..
" A bangaren su Halee kuwa bayan kammala shirin su na zuwa islamiyyya  suka dauki jakun kunansu,sunfito rass dasu cikin uniform ash colour  hijab har kasa masu kyau sai sheki sukeyi,dukannin su  sun amshe su musamman ma Halee wadda farar fatar ta tak'ara haskawa, kyakkayawar fuskar ta ta fito rass doguwar fuskar ta kara yin wani shaf mai kyau cikin dogon  hijab dinta  gwanin burgewa,sunata zuba kamshi mai dadi,wanda sai ka matso su zakaji shi,ba mai cutarwa ba kamar dai yadda aka annabi ya siffanta turaren mata,
'Dan Baba Adee akwai son kamshi domin mafi yawancin  tsarabarsu ta turare ce,shiyasa koda yaushe zakaji su cikin kamshi....

Sallama sukayiwa Baba Adee da Baba Asabe Dake zaune a barandar gidan suna dan taba fira jefi jefi...

Miji da mata sai Allah..

ficewa Gidan sukayi  bayan amsa addu,o'in da yasaba yimusu inyana gida...

Bayan wucewar su Halee islamiyya,shima Baba Adee  yaficewar sa zuwa masallacin unguwartasu dan gabatar da la,asar kan lokaci.....

*~~GUSAU,ZAMAFARA~~*
Gusau ta sambo mai dimbin al umma noma shine abun alfaharinku,Gusau Babban birni ne na jahar   Zamfara wanda yatara dubbanin Al umma ta kowane sashenn yarukka da yan kasuwa,musamman manoma,da ma aikatan gwamnati da manyan yan siyasa,Babban Abunda yake abun burgewa agaresu shine  yadda sukayi riko da aladunsu,da addini da kuma sarautunsu,sai kuma abun da yake mai mahimmanci da suka rike shine Bin shari'ar musulunci,gari ne daza kasamu suna bin dokar musulunci wanda ko gidan karuwai zai yi wuyar samu a  jihar...

*MASARAUTAR MURAI*
Babbar masarauta ce dake cikin jihar zamfara gusau wadda gaba daya nigeria suna alfahari da ita domin kafaffiyar masarauta ce tun zamanin Sarki Ali murai wanda shine sarki nafarko wanda yafara yin sarauta ajihar tun zamaninsu shehu usman dan fodiyo Na sokoto,shiyasa takasance mai mai dimbin tarihi...

'kuma shine yayi ruwa yayi tsaki gurin kafa wannan masarauta mai tarin Al ummah ,wadda tazamo abar alfahari a idon al ummar nigeria jin irin kokarin da sarki  Ali murai yayi gurin kafa masarautar..

Mutane daban daban daga cikin ya yan Ali murai sun rike sarautar wannann masarauta har izuwa yanzu da ake k'ara samun cigaba...

Tattab'a kunnen Ali murai  a yanzu shiyake mulkar masarautar,inda take samun kulaawa dakuma Al.ummar dake karkashin ta,Ahannun d'an d'an sarki Ahmad..

WASH TYPING AKWAI WAHALA...KUYI MANAGE DA WANNAN....BANJIN DADIN JIKI NANE.....

GOBE IN SHA ALLAH ZAKU SAMUN KARIN PAGE

Kuyi sharing,
Sannan ku danna min like akasan page din....

Ina godiya sosai masoyan amafarki 
Halee tace agaishe ku...

💫FA'EEH BG💫

💫A MAFARKI NASANTA💫
In my dream i know her
                 By
Pha'eezah Almustapha
    Daga Alkalamin✍️✍️
    💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION📚🖊️

        💫P.E.W.A.💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

   ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️
 
Pen🖊️*is migthier than the sword🗡️*

------------------------------------------------------------
EPISODE 1️⃣
FREE PAGE1️⃣8️⃣↔

TYPING📲📲📲

*TUSHEN MASARAUTA*

"Ali murai shine Asalin wanda yarik'a masarautar yana da mata  kwaya d'aya tal,sunan ta  Hajiya lubah (iyami)  da "ya "ya maza biyar,d'an sa nafarko sunan sa bello,sai nabiyu sunan sa Haruna,na ukun Abdul aziz,sai na hud'unsu Isma'il,sai Autansu yahaya..

Bayan rasuwar sarki Ali murai sai aka nad'a d'ansa na farko Bello wanda shi yacigaba da kula da masarautar yana da mata d'aya da y'a y'a hud'u namiji biyu mace biyu,Bayan wasu shekaru shima Bello yakwanta dama,wanda mutuwartashi ta kowa ya jita A Masarautar saboda sak halinsa irin na mahaifinsa  sarki Ali murai,Mahaifiyarsa takoka da rashinsa da y"an uwansa da ma Alummar Masarautar.

Bayan gama zaman makoki Aka nad'a d'an uwansa Haruna,Haruna yak'arb'i mulki cikin salama ,Sai bayan shekaru sittin sannan Allah yakarbi ransa..
   
..Abdul Aziz Yakarb'a shi kwata kwata ma  bai ka shekara hamsin ba akan karagar mulkin saboda ciwon daya ci k'arfin sa na k'oda,sai aka nad'a Isma'il,Bayan Nad'in Ism'el,Sarki Abdul aziz  yakwanta dama....

Isma'el ya cigaba da mulkin masarautar Bayan shekara saba'in bisa karagar mulki yakwanta dama,wanda bayan rasuwar sa,Anyi rigima sosai da Yahaya danshi kwata kwata bayason sarautar,acewar sa kayan wahala ce  da takura,bai karb'a har sai da mahaifiyar su iyami ta  kwanta ciwo akan hakan,ciwon zuciyaar ta yatashi wanda yasameta tun bayan rasuwar mijinta sarki Ali murai,sanadin bak'in cikin 
Yahaya da yakafe bazai k'arb'i masarautar ba,masarautar da mijinta sarki Ali murai yasga gwagwarmaya wurin ginata,daga k'arshe dai yakarb'a ganin yadda ran mahaifiyar sa ya b'aci gashi harda kwantawa ciwo....

'Anyi bikin nad'in sarauta da ba'a tab'a yin irinsa ba alokacin kowa kaga fuskar sa da annashuwa da farinciki  kamar sauran lokutta domin sun san cewa ba su shiga mugun hannu ba dan duk cikin ya"yan sarki Ali murai babu wanda yamusu mugun riko,Yahaya yakarbi mulki cikin aminci tare da alkawalin kula da Alummar masarautar,yana da shekara talatin akaragar mulki matar shi tahaifi namiji wanda shikad'ai ne rabonta har tabar duniya,yaron yaci sunan margayi tsohon sarki Bello,bayan wasu yan shekaru,Kwatsam ranar aka wayi gari da mutuwar sarki  Yahaya murai,wanda mutuwar sa ta girgiza kowa musamman yaronsa sa Bello,Bayan rasuwar sa da kwanakki itama tsohuwa Iyami mai ran k'arfe ta kwanta dama,tana da shekaru D'ari da hud'u a Duniya.

Wanda kowa yaji mutuwar wayen nan bayin Allah Acikin Masarautar da ma wajen Masarautar..
Bayan rasuwar yahya Anyi rigima sosai A fada akan wayenda za,a dora akwai d'an wajen margayi bello da yace yanaso sai kuma d'an wajen magaji wanda yaya ne ga Sarki Ali murai,daga k'arshe dai Muhammadu bello D'an wajen sarki Yahaya shi aka bawa bisa ga chanchantarsa duk da akwai k'aranta atare dashi dan duk sun girme masa.

Anyi nad'in sarauta tareda Daurin Auren Sarki Bello Alokacin yana da shekara ishirin da hud'u A duniya,Bayan hawansa akaragar mulkin yana d'a yan uwansa manyan muk'a man masarauta,domin cigaban Alumma .

Ya Auri yar wajen sarkin zazzau na hud'u alokacin mai suna Gimbiya Ruk'ayya bayan shekara gimbiya Rukayya ta haihu ta samu yan Biyu maza,Alokacin ne kuma matar tsohon sarki margayi yahaya uwar muhammadu bello tabar duniya,Anyi taron suna cikin alhinin wannan rashi,tacigaba rainon yan biyu dinta,Bayan wasu  shekaru  tasamu wani cikin inda tahaifi Namiji yaci suna Aliyu,sunan tsohon sarki...
'A Daren sunan Aliyu ne wani Babban tashin hankali yafaru inda wuta ta kama ad'akin su hassan da husaini duk suka k'one k'urmus sanadiyyar wutar lantarki  suda mahaifiyar su gimbiya Ruk'ayya wadda taje dubasu daga nan ta musu Addu,ar kwanciya bacci duk da tasan cewa bazasu kwanta hakan nan domin takoyar dasu,alokacin suna  shekara shidda A duniya,Mutuwar data girgiza Sarki Bello da kuma masarautar wanda sai da sarki Bello yasuma alokacin da aka sanar dashi,Bayan jimamin rashin Sarki Bello yaci gaba da rainon D'an sa Ali....

**Bayan  shekara guda sarki Bello yayi  Aure ya Auri wadda take baiwa ce Amasarautar, ya Aureta ne  saboda ganin irin kulawar da take bawa Aliyu wanda kuma ita kad'ai yake yadda da ita,Sai ya " yenta ta kuma ya Aureta domin samun farin cikin D'an sa tilo daya.
Lafiya lau masarauta take tafiya tareda cigaba mai yawa,Bayan wasu shekaru Sarki Bello na Biyu yabar Duniya yana da shekaru hamsin akan karagar mulki,inda yabar Aliyu cikin maraici mai yawa duk da  wannan yentacciyar Baiwa mai suna Nana Asma'u tana sonshi tana bashi kulawa mai kyau saboda yadda take jinsa kamar d'anta na cikinta..
 

BAyan gama jimamin mutuwar sarki Bello na  || biyu aka nad'a  d'ansa Aliyu alokacin yanaa da shekaru ishirin da hud'u a duniya.

Bayan na d'insa da shekara guda yayi Aure ya Auri yar masarautar sokoto jikar yar sarkin musulmi na ||| na uku;mai suna  ummulkhairi ana kiranta gimbiya  (umma),Bikin yatar dubbanin Al umma takowace masarautun nigeria da manyan yan siyasa,masu kudi..Ankawo Amarya lafiya cikin fada acikin sashen ta mai kyau,suna cin Amarcin su lafiya lau tare da zaman Amana....
Komai yana tafiya dai dai ta b'angaren mulki yadda yakamata.

Bayan shekara d'aya gimbiya umma tahaifi santalelen d'anta namiji ranar suna yaro yaci sunan sa HAMZA ALIYU MURAI,Anyi taron biki lafiya,inda tacigaba da rainon yaronta,Bayan haihuwar Hamza da wata takwas tasake samun wani cikin alokacin gimbiya ummulkhairi  taso zubarda cikin ganin Hamza ko shekara bai had'a kar yasha ciki,sai dai mai martaba sarki Aliyu yahana zubar da cikin  sai dai  yasa aka cire Hamza daga nono...

Taraini cikinta lafiya lau batare da tasha wuya ba,watannin haihuwar cikin nayi nak'uda ta motsa amma yaro yaki fitowa ak'arshe dai CS akayi mata aka ciro santalelen d'anta mai kama da uban sa sak,yaron yaci suna Ahmad...
 .....Bayan wasu "yan shekaru sarki Aliyu D'an Bello jikan Yahaya D'an  Sarki Ali Murai yabar Duniya alokacin,yabar Duniya da shekaru arba'in  akaragar mulki,Mutuwar sa tagirgiza y"a yansa guda biyu a duniya da matar sa ummulkhairi,inda tacigaba da kula da yayanta cikin kulawa,Bayan Rasuwarsa da yan watanni Nana Asma'u matar margayi sarki Bello na || tabar duniya...

Sarautar dole aka bawa magajin gari rik'on kwarya kafin ya'yan sarki Ali su kai lokacin iya rike sarautar,domin dukkaninsu bazasu wuce shekara goma sha biyar Alokacin ba.

Bayan wasu shekaru  Ahmad yayi aure ya auri matarsa Bafullatanar Adamawa itama yar gidan sarautace sunanta Haleematu sadiya suna kiranta hajiyar safkare wanda sunan da kakarta ta lakamatane,ya Aureta yana da sheakara ishirin da shidda aduniya sunyi Auren soyayya da gimbiya halimatu,kuma aloakacin ne aka damk'a sarauta hannun Ahmad duk da sai da akayi rigima dashi dan yace bazai karb'a ba sai dai abawa y"a yanshi tunda shine Babba,Dakyar aka samu yakarba bayan ya yan nasa ya sanya da mahaifiyarsu gimbiya ummulkhairi  suka tasoshi gaba....
Anyi  bikin nad'in sarauta lafiya cikin annashuwa da salama,ta fannin zaman takewarsa da matar sa masha Allah za,ace gwanin burgewa.

****Bayan shekara daya gimbiya halimatu sadiya ta haifi santalelen d'anta mai kama da ubansa sak  jinin fulani,farin cikin wannan masarauta bazai boyu ba musamman sarki Ahmad da D'an uwansa hamza,wanda ke ji kamar shi akayiwa haihuwar...

*Ranar suna yaro yaci sunan kakan sa sarki Aliyu Bello jikan yahaya d'an  Ali murai*yaro yasamu gata ta kowanne fanni,Alokacin shima Hamza yayi Aure ya Auri Gimbiya Hauwa'u yar masarautar Fulanin Bungud'u ana mata lak'ani da fulani,fulani macece mai fadin rai da rashin son talaka,da mugun son kanta,ba kamar gimbiya halimatu ba mutuniyar kirki mai mutunci,BAyan Aurensu da Hamza sai tafara nuna mishi ai sarautar dashi ta dace domin shine Babba yace abashi sarautar,ai shine dana farko ga sarki Ali Bello,sai ya rik'a nuna mata baida buk'ata,kullum haka suke rigima da ita,har zuwa lokacin da tasamu cikin Mustapha A lokacin kuwa matar sarki Ahmad Halimatu  tasamu ciki na biyu ta haifi umar,sunan mahaifinta kenan,tana kiransa da emir,Bayan  kamar wata takwas sai ga wani cikin  na ukku inda ta tahaife sa lafiya,tasamu Abdul rashid,tacigaba da rainon ya yanta cikin kwanciyar hankali.

Daga  cikin abin bak'in cikin da yafaru Akwai rasuwar gimbiya ummulkhairi  matar tsohon sarki Ali,Mahaifiyar sarki Ahmad da Hamza,sunyi rashin mahaifiyarsu abar kaunar...sai dai muce Allah yajikanta da al ummar musulmi baki daya.........

*Yaa Allah Duk wata mahaifiya 💔💔dake kwance akarkashin k'asa,Allah kajik'anta da rahaama,da musulmi baki daya,Yaaa Allah wayenda suke raye kuma ka k'ara musu lafiya mai amfani tare da tsawon rai mai albarka*🙏

Rashin uwa rashine 😭Babba Arayuwa
Allah yabar mu dasu 🙏
--------------------------------------------------------------
 
Matar Hamza Fulani tak'ara samun wani cikin nabiyu ta haifi d'anta namiji mai suna Muhammad ana masa lak'ani da Malan,tana da ya"ya biyu kenan.
Itama sarauniya halimatu taka'ara samun wani cikin bayan shekara uku inda ta haifi yarta mace mai suna khadija  inda daga gareta haihuwar ta tsaya mata chak......
Sarauniya Halimatu yaranta sun taso cikin soyayyar junansu Da yan uwansu yan gurin magaji hamza,domin shi d'an uwansa ya nada magaji bayan rasuwar wanchan magajin.....
Duk da tsangwamar da Fulani take nuna musu amma hakan bai hanasu jan yan uwansu ajiki bah.

Ta b'angaren magaji Hamza kuwa yana shan matsin lamba gurin Hauwa'u (fulani )kan karbar mulki alokacin takara samun ciki tahaifi ya mace mai suna ummulkhairi suna kiranta               (khairiyya) dan taci sunan kakar ta ne  wanda daga gareta  haihuwar ta tsaya ma fulani chak..
 A lokacin  Duk fulani tana masa matsin lamba wanda har tafara cin galaba akan sa,dan bata tsaya haka nan ba,sai da talek'a gurin malammaan tsibbo (bokaye) Wal iyazubillah....

bokaye mana domin tahakan ne wasu suke amfani dashi sai suce ai malami ne shi bokan,ana amfani da sunan malamman ana shirka ana cutar Al umma..ALLAH YAYI MUNA TSARI DASU...Masu zuwa gurin bokaye Allah yashiye su🙏
 MU HADU GOBE IN ALLAH YAKAIMU 
YAU KAM KUNSAMU LONG PAGE,DAN KONI NAJI AJIKI NA,KUNGA NA GOGE LAIFINA NA JIYA,DUK DA BANI DA LAFIYA NE

NAGODE SOSAI  ALLAH YABAR KAUNA🙏
KUFARA SHIRI ANKUSA GAMA FREE PAGES,DAN BATUN SAMBAD'O KUD'INKU......

Kucigaba da bibiyar Alkalamina

Yau duk sai A hankali  typing din  domn page d in yatado mini da rashin da mukayi...Allah yajik'anku da rahama Baba Bello,kakana Baba Yahaya,Alhajin Auki,Mariya,gwaggo yar sarki, Allah yasa Aljannna takasance makomarku da dukkan musulmi baki daya..AMEEEN...

💫A MAFARKI NASANTA💫
In my dream i know her
                   By
Pha'eezah Almustapha
    Daga Alkalamin✍️✍️
      💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,Na episode two*!!!✌✌💥💥

*TALLAH!!! TALLAH!!! TALLAH*
*Ina yan kasuwa masu son tallata hajarsu,ga dama tasamu domin Muna tallata kowace irin hajace daga jihohi daban daban harda ma k'asashe,akan farashe mai sauk'i,zaku iya tuntubarmu ta lambobin waya kamar haka*......
  + 2348069059746
  + 2349078741775

-----------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION 📚🖊️

        💫P.E.W.A.💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

       ESSENTIAL WRITER'S📚🖊️  
 
Pen🖊️*is migthier than the sword🗡️*

------------------------------------------------------------
EPISODE 1️⃣
FREE PAGE1️⃣9️⃣


TYPING📲📲📲

________________________________________
" Rana ta farko daya isko sarki Ahmad da maganar yana son sarautar ta dawo hannunsa,Sarki Ahmad bai nuna komai ba akan fuskar sa,sai dai murmushi da ya wanzar akanta tare da furta masa zaiyi magana da manyan masarauta,duk da yasan lallai su amince ba,saboda tun farko da yardarsa aka d'orasa,kuma ba,a chanza sarki kai tsaye ba da kwakkwaran dalili ba a wanchan lokacin..

Koda sarki Ahmad yagana da manyan masarauta sun nuna k'in Amincewarsu kaitsaye.

'kiran d'an uwan nasa yasanar dashi domin badashi anakayi zaman ba,kamar ganawar sirri ce,daga su sai maimartaba sarki sarki Ahmad sukayi ta,yana yin yadda yaga D'an uwansa yana kuka kasharb'an hankalinsa yatashi sosai,dole yasanya taron gaggawa yace yayi murabus kan kujerar tare da katse duk wasu tambayoyin da aka so tsiyesa dasu inji manyan masarautar..

'Farin cikin da yagani kwance akan fuskar d'an uwan nasa Hamza shine Abunda yatsaya masa arai,Bayan komawar sa gida bai b'oyewa gimbiya Halimatu sadiya komai ba,Tayu mamaki sosai duk da tasan akwai wata a k'asa sun san halin matar sa sarauniya Hauwa'u zata iya yin komai sun yarda cewa bayin kansa bane..

:::::::Rayuwa tana tafiya yadda yakamata,sarauniya Hauwa,u (fulani) mulki ya shigo hannu sai taka talakawa take yi son ranta duka bayi alokacin sun san halinta tsoronta sukeyi sosai domin wulakanta su bakomai ne awajenta ba,musamman na sashenta,Yadda take da mugun hali haka tab'ata D'anta Muhammad,shi mustapha ba haka yake ba halin  babansu suka biyo shida macen da takara haifawa mai suna  ummulkhairi,wadda taci sunan kakarsu Ta wajen uba,suna kiranta khairiyyah..

A lokacin da akayi juyin mulkin duka ya yan sarki Ahmad maza basa nigeria suna wajen karatu,Aliyu yana china yana  karantar Business Administration,sai umar yana Kasar Uk yana karatu fannin bincike da tsaro,sai Autan maza Abdul rashid yana kasar sudan yana karantar MBBS karatun likitanci kenan,Duk da alokacin sunji mulkin yabar hannun mahaifinsu ba wanda yadamu dan dama basu wani  dauki mulkin wata tsiya bah.

Bayan kamar shekara bakwai lokacin umar yagama nasa karatun har masters ya had'o,yadawo gida  alokacin ne kuma  mahaifinsu sarki Ahmad yakwanta dama,😭mutuwar data girgiza kowa dole dukkaninsu suka dawo nigeria dan ganin gawar mahaifinsu,wanda kafin suzo ma an binne ta,ganin basu iso da wuri ba,khadija kadai tasamu damar isowa da wuri ita  dake Adamawa gurin kakaninta tana karatun  a wata private school ta Nursing wanda tashiga a wannan year din,koda suka iso rashin ganin gawar ta mahaifin nasu sai takara rikita su,in kagansu alaokacin sai ka sun baka tausayi,wannan mutuwa basu kad'ai ta girgiza ba harda Alummar zamfara baki d'aya domin sanin halayen sa na kirki da kyautatawa al umma da yake yi...

'Matuk'ar girgiza sarki Hamza ya girgiza ba kad'an ba Alokacin da aka sanar dashi yana tsaye,shine ma dalilin dawowarsa hayyacinsa,kuka yakeyi wiwi,yana furta kaichona,na k'untatawa D'an uwa nah,da k'yar fadawa da manyan masarauta suka lallashesa .....

"Gimbiya Halimatu sai da tayi kwana biyu bata farfad'o ba daga suman  datayi bah...

Bayan kwanakki da rasuwar sarki Ahmad, Sarki Hamza yatara taron gaggawa na manyan masarauta,take yasanar musu da kudurinsa na son yin murabus,maganar takawo cece kuce a fada lokaci da sarauniya Hauwa,u taji wannnan zance tayi farinciki sosai jin cewar sarauta zata dawo hannun ya yanta,ita a tunaninta Muhammad ko Mustapha za,a bawa tunda mahaifinsu ne yasauka,wanda dama shine burinta tun farko shiyasa ta yishigenta da fice har sarautar ta dawo hannun sa..

Sai kuma 'wani Babban   labari na tashin Hankali daya sanya Gimbiya Fulani suma.......

'Jin sarki Hamza yagabatar da 'matar sa ta biyu waddaya aura shekaru sha bakwai da suka wuce,tare da ya yanta  mata uku,duka kyawawa,na  farkon  sune yan biyu hassana da husaina sai ta karshen su Auta mai suna lailat,yagabatar dasu ne A masarautar dan yana so sudawo dazama ciki tare da sauran dangi...
Sunyi Aure da matar sa Fateema yar k'asar makkah,ana kiranta Ammie,Fateema dai balarabiya ce sak gaba da baya,sunyi Auren soyayya da sarki Hamza A lokacin da yaje k'asar ta makkah yin wani taro na sarakuna,Tanuna tana sonsa  Alokacin shima kuma yaji yana sonta Duk da lokacin akwai sihiri mai K'arfi ajikinsa wanda ba kowa ke iya ganewa bah...

Ya Aureta ne Achan k'asar jidda inda Asalin iyayenta suke,tana zama wurin ya yan tane sarkin makkah alokacin.

Mutane da dama sun shaida d'aurin Auren fateema hakim da kuma sarki Hamza Aliu murai ...
Bayan D'aurin Aure yad'aukota suka dawo nigeria wanda dik cikin masarautar sarki Ahmad kad'ai yasan da Auren sai kuma wasu daga cikin manyan masarauta,saboda ya nemi Alfarmar yazamo sirri bayaso maganar takai ga sarauniya hauwa,u domin  Alokacin harda d'an tsoronta aka saka masa azuciya..

Sarki Ahmad har ziyara yana kaiwa fateema (Ammie) a gidan da sarki yakaita a d'ai daga cikin manyan unguwanne da suka Amsa sunansu na masu naira ...
kuma tun lokacin da Ammie ta haifi  twins dinta sarki Ahmad mai mutuwa yabar wasiyyar ko bayan ranshi yana son cikin zaratan mazan ya yansa koda d'aya ne ya Auri cikin wayen nan twins d'in,Bayan twins tak'ara samun mace aka lailat......................

 SU FULANI ANGA TASHIN HANKALI WANNAN KAM SHI AKE KIRA TA LEK'O TA KOMA....Zafi bibbiyu...

         
💫FA'EEH BG💫

Wannan labari yazamo farinciki ga wasu wasu kuwa bak'in ciki,domin itakam gimbiya Halimatu sadiya tayi farin ciki dan dama mijinta yasanar mata da Ammie din wanda sak'o tana basa inzaije,yakaiwa hassana da husaina da lailat,kuma suna musayar gaisuwa wa junansu,har numban wayar juna suna da ita,Murmushi kad'ai tayi dajin wannann labari dama kuma tana dakon zuwansu,suma su umar (emir) da su Aliyu  sunyi matuk'ar farinciki musamman  Mustapha da khairiyyah sunyi murna sosai ganin sun kara samun yan uwa....

Bayan gabatar dasu ga fada aka damk'a su gurin gimbiya halimatu domin tama rakkiya sashen ta domin itaace Babba Amasarautar,dama tasanya ma,aikata sun gyara sashen da yake Mallakin Ammie ne ita da  " ya "yanta...

Bayan gama gaisawa da juna tagabatar da ga dukkanin bayi ma,aikata dake aiki asashen ta da kuma wayenda zasu yi aiki asashen Ammie din..

Sannna suka d'unguma zuwa katafaren sashenta wanda yaji kayan more rayuwa ta ko ina..
 "A fada kuwa suna tattaunawa kan maganar murabus na sarki Hamza,ya kuma sanar musu cewà shi ya nemi d'an uwansa sarki Ahmad yasauka yabasa mulki  kuma bay in kansa bane shidai yasan ko mene  umurni aka basa,Amma bai sanar musu wanda yayi mishi hakan ba domiin kariyar mutuncin ya yanshi..

Kuma yace yana son yamika'a sarautar ka yayen d'an uwansa sarki Ahmad da sarautar tunda dama dukkaninsu sunkai mizanin hankali,sunyi na,am da zancen sa kuma sunga dacewar hukuncin sarki Hamzan,zancen yama  wasu dadd'i wasu kuwa bai musu ba,A lokacin inkaga fuskar Muhamad
 ( Malan )zakaga tsantsar bak'inciki da b'acin rai tattare dashi daga farkon maganar yazata shi za,a bawa baiyi duba da shine k'arami ba ma...Fuskar nan tasa tayi jawur cikin abunka ga farar fata har kwanci jini tayi,ga bak'in cikin bayyanar wasu ahalin nasu inda ma yayi farinciki ba maza bane...

'Baiko bari akagama magana ba yabar fada rai b'ace yayi sashen mahaifiyarsa,wanda achan ma yatarar da wani tashin hankalin sarauniya hauwa,u kamar tayi hauka duk ta rud'a sashenta,ga Ammie da gimbiya Halimatu sunzo sashenta dan agana da juna amatsayinta na uwar gidan Ammie din,dakuma zaman ta na sarauniya matar sarki, su laila dasu hassana da husaina, sai kuka  sukeyi khadija nataya su,wadda takejin kaunar yan uwan nata, domin basu tab'a ganin tashin irin wannan tashin hankali ba.

Mustapha ne ke jan ta tana kucce kucce dan shima dama zuwansa sashen kenan ya isko wannan kayan haushi kayan kunya  gaban bayi take zage zage zuwa ga maimartaba  sarki Hamza da kuma Ammie harda ma gimbiya Halimatu,Bayan mustapha yasamu nasarar janyeta daga falon izuwa uwar d'akinta,shima Muhammad yabi bayanta da fuskarnan tashi kamar tayu aman wuta,itadai khairiyyah sai aikin lallashin yan uwan nata take yi dan itama tunda tagansu taji sun kwanta mata arai tanajin soyayyarsu har cikin zuciyarta...
 Gimbiya Haleematu da Ammie A hankali suka bar sashen  nata tareda su hassana harda khairiyyah ma zuwa sashen  na Ammie kowa zuciya ba dad'i.

A b'angaren sarauniya Hauwa,u fulani kuwa kuka take wiwi kamar wadda akayiwa mutuwa,sunyi lallashinta harsun gaji sai da mustapha yayi dubarar kiran mahaifinta sarkin Fulani sannan suka samu kanta.

"Mustapha gaba d'aya sai da yaje sashen su Ammie da gimbiya Halimatu yabasu hakuri kan abunda yafaru sannan yak'ara lallashin  yan biyu da su  khadija.......

A bangaren fada kuwa bayan fitar Muhammad  maimartaba sarki Hamza yanemi jin ta bakin ya yen sarki Ahmad,Bayan sanar musu da bukatar
 sa,Kamar yadda yasanarwa sauran mutanen acikin fadar,bayan gama jin zancensa duk sukayi shiru,dan dukkanin su babu wanda sarautar ke kod'awa ak'asa kanwarsu ce khadija ke d'anjan sarautar,ko yadda suke gudanar da rayuwarsu inka kalla zaka san akwai jinin sarauta ajikinsu mai karfi...
   
Maganar sarki Hamza ceta katse shirun inda yake cewa yana jiran Amsar su,suka ce abasu nan da,gobe in sunyi  shawara da mahaifiyarsu,da haka zaman nasu ya watse anbarshi akan gobe za'ayi hukuncin dasuka yanke......................................................................................
   
*Nima anan na dakatar da alkalamina*
*Bayan ya subuce daga hannu na😂*

*Sai monday in Allah yakaimu da rai da lafiya*
*Zaku samu cigaba*
Like pls share nd comment

Like pls nd comment kuma atayani sharing Dan Allah...


💫A MAFARKI NASANTA💫
 In my dream I know her
                  By 
Pha'eezah Almustapha 
  Daga Alkalamin✍️✍️
      💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,na episode two*!!!✌️✌️💥💥

*TALLA!!! TALLAH!!! TALLAH*
*ina yan kasuwa masu son tallata hajarsu,toh ga dama  tasamu domin muna tallata kowace irin hajace daga jihohi daban daban harma da k'asashe,akan farashe mai sauk'i,zaku iya tuntub'armu ta lambobin waya kamar haka*........
+2348069059746
+2349087741775

     💫A MAFARKI NASANTA💫
*💫In my dream i know her💫* 2023  novel *is the story of an* *innocent girl call Halee yarinyar da* *tataso cikin rashin iyaye sannan ta* *had'u da kalubalin rayuwa mai matukar* *girgizawa inda bayan haduwar ta da* *iyayenta,wayenda suke nesa da* *rayuwarta  tasamu loosing memory,sai* *kuma takara samun "psycho" tab'n* *hankali kenan shin ko meye silar* *faruwar hakan?SHIN WAD'ANNAN* *YAN BINDIGA DA NA HANGO KODAI SUNE SILAR RABA* *HALEE DA IYAYEN TA,?ME KUMA IYAYEN NATA SUKA MUSU INHAKA* *NE?KAI WANNNA ALAMARI AKWAI* *RIKITARWA,SOYAYYA KAM ZAKU* *SHATA,SANNAN YAR UWA ZUCIYARKI* *ZATA TABU*.....*SHIN KO WAD'ANNAN YAN TA'DDA* *ALKALAMINA ZAIYI AIKI KANSU?SU WANENE ABAYANSU ?SHINSUMA ZASU IYA KARBAR HUKUNCI ?DUK  DA KASANSEWARSU MANYAN KASA*
*DUK AMSOSHINKU ZAKUJI SU ACIKI WANNAN BOOK KUCIGABA DA BIBIYATA.*
 --------------------------------------------------------------------
------------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION📚🖊️
      
                💫P.E.W.A.💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

             ESSENTIAL WRITER📚🖊️

    pen🖊️*is mightier than the sword🗡️*
__________________________________________
EPISODE1️⃣
FREE PAGE2️⃣0️⃣

TYPING📲📲📲


Bayan  barin sarki Hamza fadar bai zame ko ina bah,sai sashen sarauniya hauwa'u dan yasan tabbas akwai matsala yasan bai kyau tamata ba duk da ya fahimci alokacin akwai sa hannunta cikin macin da yasamu na karb'ar sarauta,kuma a lokacin da yayi auren b'oyen duk laifintane shi baisan abunda yashiga kanshi ba na tsoronta ba alokacin,Auren ma nasu da Ammie Allah ne yak'addara shine..

Shigar sa sashen nata ma,aikata nata russunawa tare da fadawan dake abayan sa,kai kadai yake iya d'aga musu har yakai ga shiga Babbar uwar d'akanta wadda  take taji komai har kujeru akwai ciki da tv,duk haka d'akunan suke na masarautar kowanne sashen haka yake,gimbiyah halimatu ce kadai tasa aka cire mata ta ta tvn ta uwar dakanta,saboda ita macece mai natsuwa hayaniyar tvn na takura mata acewar ta,tafison taji ta shiru ita kad'ai tana jan charbi tana azkar dinta domin macece mai son ibada kullum bata rabo da charbi a hannunta ko tana karatun alqur'ani.....

Bayan sarki Hamza yayi sallama,acikin uwar d'akanta yashiga bayan yaji shiru,ba,a amsa masa sallama ba...

*Nikam nace dama ya,za,ayi a amsa maka sallmah yallabai kishiya ai ba wasa bace bare ta auren boye,abun akwai ciwo,sai dai dan Allah yan uwa mata mudaina kishin hauka,arika kai zuciya nesa....Akamanta kuma arik'a daukar k'addara Duk yadda tazo,Domin Allah yariga yarubuta cewa matar sace itama,sai dai abi da addu,ar zama lfy da haduwar hankali*..

Jingane take kan gado takura wa tv ido kamar akwai abunda take fahimta hankalin ta baima jikinta..Gimbiya fulani kenan,Fulani! sunan ta da yakira ne yasanyata d'an kallon inda yake tsaye hawaye ne suka cigaba da tsiyaya a idonta ganin  ga dukkan Alamu ya nuna maganin yasaki jikin sarki Hamza,.........
*nikam nace dama boka ko malan sun isa su juya mutun ne har karshen rayuwarsa ai abun hajiya nadan lokacine ,ke kuma mai kwasar kafafu kije dan neman agaji gurinsu saboda rashin hankali ,wai harda kayan dakin ki kika siyar dan ki samu wani abun ga wanda shima ubangijin ne ya samar dashi to bari kiji kyi hattara,domin kuwa bokaye kudin ki kadai suke ci babu mai yima bawa face Allah,dan haka kimayar da yar tabarmar ki dakike shirin siyarwa dan kaima kunkurmin kato,wanda zai mutu acikin azabar Allah,inva tuba yayi ba,domin Allah mai jinkan bawansane,Allah yatsare muna imanin mu🙏🙏,masu niyar zuwa Allah kaga nar dasu,domin ko sau daya kika taka gurin malaman tsibbo ko bokaye Allah zai yi fushi dake za,a jingine komai naki na ibada,Har sai kinyi kwana arba'in,kinga idan kika mutu awanna lokaci kin mutu kafira,anyi zuwan zomo duniya,Allah ykara ganar da mu,ya kuma k'ara muna karfin imani domin mai k'aramin imani shiyake kai kansa ga wadannan kafiran musulman*

*-------- *------------*-------------*---------*---------*-------------*
'Da  dadane jikinsa narawa zaizo yadurkusa mata yana tambayar ta meya faru,Amma yau gashi yanzu harda kiran sunanta babu alamar tsoronta a idonsa,zafi bibbiyu gana  zuwan Ammie da iyalanta gana murabus din zaiyi yamayar da mulkin hannun ya yan gimbiya Halimatu...

Hakuri yabata akan Auren da yayi batare da yanuna mata komai ba,ganin tadan saki yasanya sa fita yakoma sashen sarauniya Ammie baiwar Allah,domin ganawa dasu dakuma jin in sashen yamusu,su hassana sunyi farincikin ganin mahaifin nasu dan sun saba dashi sosai

Hakuri yabata da abunda yaji yafaru lokacin da suka je sashen na fulani domin mustapha yasanar dashi komai bayan barowarsa sashen na fulani.

BAiwar Allah tanuna masa bakomai dan dama Ammie akwai saukin kai,kamar yadda nafada muku chan baya lak'aninta ne har ya yanta ma haka suke kiranta dashi..

    A bangaren yaran gimbiya halimatu kuwa sun sanar da ita komai tanuna farincikinta afili dama burin margayi sarki Ahmad ne cikin ya yansa wani ya gaje sa,sun yanke hukuncin abawa umar tunda shi yagama karatunsa kuma har yasamu aiki ma,federal government sun masa appointment na minister of security and investigation crime (S.I.C),ganin yadda takardunsa sukayi kyau da kuma kwazonsa awurin bikin yaye dalibbai,umar yaso yayi ja inja da yan uwan nasa musamman yayansa Aliyu sai da mahaifiyar su tasanya baki aciki ya amince ya karb'a,

"Anan yakawo maganar Aure duk da yanajin nauyin,amma baijin zai  iya bari yayi sake ba,yasanar musu da kudurinsa na cewa shikam yayi mata domin yaga laila yana so yar wurin Ammie,tun lokacin yayi arba da ita yaji yakamu da tsananin  sonta,sunyi farinciki sosai dajin wannan labari musamman ma gimbiya halimatu,duk da laila tana da shekaru sha biyar ne lokacin dan secondry ma tagama alokacin,su hassana da husaina ne su sunwuce tertiary institution daya tana karantar fasion and designer daya kuma masscom a skyline university a branch dinsu dake gusau.....

Sunyi na,am da zancen sa kwarai dagaske Alokacin da zancen yaje kunnen sarki HAmza yayi farinciki sosai zai cika burin dan uwansa na had'a auratayyar ya yansu...
     Itama Ammie tayi farinciki sosai ta bangaren lailat tunda aka sanar mata da maganar sai ta tsinci kanta soyayyar emir,kowa yayi farinciki banda mutun daya itace sarauniya hauwa'u taso hana haduwar auren Allah yahana,tunda taji wanda za,a bawa sarautar shine laila zata Aura,sai taji ina ma khairiyyah yazab'a....kaaji soin kai 

*Niko nace tun ran gini tun ranzab'e fulani, matar mutun k'abarinsa*

''Anyi nadin sarauta tare da daurin Aurensu cikin lumana,inda aka k'ara gyarawa da k'awata manyan ginukkan na  zamani  na masarautar,inda aka ware musu ,bayan angyara dai daga cikin  bangarorin masarautar  wayenda suke atsare ginukkan gwanin burgewa irin ginin sarauta na asali,anyi taron biki lfya an watse tareda Addu,ain samun zaman lfya ga amarya da angon ta sabon sarki....

Bayan gama bukukuwan kowa yakoma kan harkokin gavansa,Aliyu da Abdulrashid kowa yakoma kasar karatunsa harda khadija dasu khairiyyah da mustapha,dake karatu a suma acikin gari a noun university dake kano ,muhammad(malan) kad'ai akabari domin yace yafison karatu agida shiyasa aka yake karatu a FUG,yana karantar politial science...


''''''''''''''''Bayan wasu shekaru shima Aliyu yazama cikakken dan kasuwa dan yasamu damar da kowace zai iya kafa kasuwancinsa batare da wata wahala ba,yayi Aure ya auri Hassana,inda har ta haifi santalelen yaron ta namiji kyakkyawa  jinin larabawa da fulani,inda yaro yaci suna Abdul rashid ana masa lak'ani da Ammar Anyi shagali sosai wanda ba,atab'a yiba,inda itama Husaina ta yi Aure ta Auri wani Babban Abokin  sarki umar mijin laila,Wanda yaganta A auren su laila din har ya nemi Aurenta,leutenant jabir muhammad soja Abokinsa ne nak'udda tare su sukayi karatu a  uk,bayan dawowarsu najeriya ne shima jabir yasamu matsayin leutenant....
Inda itama ta haifi d'anta sak kamar ta jikinne na babansa bayan tayi arba'in ne,itama Hassana ta haife nata cikin...

Yaron  husaina yaci suna Al- amin sunreni ya yansu cikin Aminci da kwanciyar hankali 

....A bangaren sarauniya lailat da umar tsif kake ji har yanzu tun abun bai damun laila har yafara damunta,A wasu lokuttan zata zauna tayi ta kuka ganin yan uwanta wayenda ma tariga aure sun haifu ita kuma shiru,sarki Umar shike lallashinta  da kuma gimbiya halimatu,kaji*surukar arziki**Allah ya had'a mu da irinsu*🙏

Da kuma Ammie ,daga cikin abun bakincikin da yafaru akwai rasuwar tsohon sarki Hamza,inda mutuwar ta gigita Ammie saboda bata wasu dangi sai shi akasar nigeria shine gatanta sai ya yanta,shine take samun sanyi agaresa saboda gimbiya Hauwa'u kullum cikin musguna mata takeyi aboye tun kafin su hassana suyi Aure take wahalar dasu tahanyar furta musu bak'ken maganganu ko sanya su aiki wanda basu saba da yinsa ba,Amma ammie bata taba fadawa mai martaba ba,zagi kala kala tana sha har cewa da ita takeyi wayasani ma ko sarki takari yakwaso ita ba balarabiyar kwarai bace,*nace su larabawan dama akwai na  k'arya*..Duk da taga dukkanin tsarin halitta ta larabawa atare da ammie din..

Sunyi kukan rashin mahaifinsu,khairiyyah 
harda suma itada lailat shiko malan ko ajikinshi dan yana ganin kamar mahaifin nasa yatare masa gaban hantsine gurin kwatar sarautar...


Hassana da Husaina laila sunji sosai mutuwar,bayan gama  zaman makoki suka cigaba da rainon y yansu.....
"""""'''''''''''''''''''''''""""""''"''"''''''''''''''"""""""""""""Bayan wasu shekaru .....Kyawawaan yara ne  wanda ak'alla zasu kai shekara Biyar tare da  wata kyakkyawar yarinya d'auke a hannun d'ayan wanda skin dinshi take chocolate colour,kuma kyakkyawa ajin karshe.wadda bazata wuce shekara d'aya ba...

Fuskar sa da alamun damuwa ganin yadda kyakkyawar  farar yarinyar dake hannnunsa take zille zille takoma a hannun d'ayan yaron wanda yakasamce  fari ne tass afata shima dai kyakkyawane..

Murmushi d'ayan yayi yana furta ni bazan d'auke ki ba,salon kimun fitsari  ya iyar da magaanar yana matsawa baya....

Aiko kamar jiratake yana matsawa baya tak'ara b'are  baki tana kuka,duk da karantar shekarunta,Amma irin yaran nan ne masu shegen wayo,kukan da ta tsala ne yasanya kyakkyawan yaron sakinta  a k'asa saboda yadda kukan yashiga kunnensa Yana yamutsar kyakkyawar fuskar sa Kamar yasaki kukan shima.....

Aiko da gudu d'ayan yaron ya koma cikin gida yana kwala kiran Aunty! Aunty ! wata farar kyakkyawar matashiyar matace wadda bazata shekara ishirin da hud'u ba ta b'ullo daga k'ofar kitchen  tasha kaya na alfarma,tana furta lafiya Yarona,cikin shesshekar gudun da yayi yake fad'in Aunty Ammar ne yasaki norah k'asa,bai rufe bakinsa ba sai ga nanny din dake kula da norah tare da yaron danaji ankira Ammar d'auke a hannunsa tana tsala kuka,harda shid'ewa shima kuma Ammar d'in hawaye ne ke tsiyayar masa a ido..


Muryar nanny d'ince  take fadin Allah yataimaki gimbiya sarauniya ya matsamun sai nabasa itane,gashi ba wani iya daukar ta yayi ba,shine nabasa nadan zagaya ne sai chan nji kukanta,ki gafarceni,yanzu haka ma nayi nayi dashi yabani ita inlallasheta  yak'i gashi shima kukan yake yi,murmushi kawai tayi bayan gama sauraren bayanin baiwar,

Jawo hannun wanda aka kira ammar tayi sannnan ta karb'i yarinyar da naji ankira norah a kafad'ar ta tadaura ta tashiga girgiza ta,shikuma Ammar tazaunar dashi akan kujera tana share masa hawayen sa  da suka kasa tsayuwa....Nora da zuwa wannnan lokaci tayi shiru jinta abisa kafad'ar mahaifiyarta sai shesshekarta kad'ai kake ji,tak'ara tsala kuka wanda yafi na farko tanayi tana shidewa fararen manyan  idanunta sunyi jawur dasu na azabar datake ji, wanda take jikin ta yagashe,cikin shesshekar kuka Ammar yake furta Aunty kibawa nora hak'uri tadaina kukah yana cigaba da kukan shima,d'ayan yaron ne ya matso kusa gareshi yana fadin Ammar kayi shiru kaji yakai karshen maganar cikin tausayin sa,daga yanayin yadda suke kasan cewa suna mugun son junansu,hawayen sa yashare masa yana k'ara furta norah tayi hakuri Ammar bakaji tay shiyu ba.....................


💫A MAFARKI NASANTA💫
 In my dream I know her
                  By 
Pha'eezah Almustapha 
  Daga Alkalamin✍️✍️
      💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,na episode two*!!!✌️✌️💥💥

*TALLA!!! TALLAH!!! TALLAH*
*ina yan kasuwa masu son tallata hajarsu,toh ga dama  tasamu domin muna tallata kowace irin hajace daga jihohi daban daban harma da k'asashe,akan farashe mai sauk'i,zaku iya tuntub'armu ta lambobin waya kamar haka*........
+2348069059746
+2348087504734
----------------------------------------------------------------
     💫*A MAFARKI NASANTA*💫
     *💫In my dream i know her💫*2023  novel *is the story of an* *innocent girl call Halee yarinyar da* *tataso cikin rashin iyaye sannan ta* *had'u da kalubalin rayuwa mai matukar* *girgizawa inda bayan haduwar ta da* *iyayenta,wayenda suke nesa da* *rayuwarta  tasamu loosing memory,sai* *kuma takara samun "psycho" tab'n* *hankali kenan shin ko meye silar* *faruwar hakan?SHIN WAD'ANNAN* *YAN BINDIGA DA NA HANGO KODAI SUNE SILAR RABA* *HALEE DA IYAYEN TA,?ME KUMA IYAYEN NATA SUKA MUSU INHAKA* *NE?KAI WANNNA ALAMARI AKWAI* *RIKITARWA,SOYAYYA KAM ZAKU* *SHATA,SANNAN YAR UWA ZUCIYARKI* *ZATA TABU*.....*SHIN KO WAD'ANNAN YAN TA'DDA* *ALKALAMINA ZAIYI AIKI KANSU?SU WANENE ABAYANSU ?SHINSUMA ZASU IYA KARBAR HUKUNCI ?DUK  DA KASANSEWARSU MANYAN KASA*
*DUK AMSOSHINKU ZAKUJI SU ACIKI WANNAN BOOK KUCIGABA DA BIBIYATA.*
 --------------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCITION📚🖊️
  
              💫P.E.W.A💫

Home of perfect  essential writer's together we stand🤝

          ESSENTIAL WRITER'S
 📚🖊️
pen🖊️*is mightier than the sword🗡️*

------------------------------------------------------------------
EPISODE 1️⃣
FREE PAGE 2️⃣1️⃣

 
  TYPING📲📲📲

...'Sallamar wani matashin mutun ne cikin shiga ta alfarma ta kayan sarauta alkyabba da rawani  masu kyau  tare da wani bafade guda amma shi yana bakin  bakin kofa ne,Muryar shi ce ta katse da yazo dashi yakin furta meyasamu mamanah labari ya isar  mun fada gata chan tana kuka,Murmushi matar da aka kita tana fad'n haba Babban sarki Norah ai ta dena kukan ma ka kwantar da hankalinka baka ji tayi shiru ba,cikin ya nayinsa da sanyin hali ya furta layla miko mun ita inganta,yana zama akan hadaddun rugs d'in dake falon na alfarma,tab'a jikinta yayi bayan tamika masa ita,ajiyar zuciya yasauke,jin jikin nata zau da zafi,lokacin baiwar Allah har ta fara baccin wahala,Murya asanyaye yace meyasameta ne.?..

A hankali gimbiya laila tafurta tafad'i ahannun mutumin tane,kaganshi chan gefe ma shima  yana nashi kukan,duban sa yakai inda Ammar suke,Bayan yagama k'are musu kallo tsaf su duka,sai kuma Ahankali ya k'yafato su ,alamar su zo,a hankli suka taso hannyensu rik'e dna juna,Ammar ne ya duk'a k'asa yayi kneeldown tare da kama kunnuwansa yana tsiyayar da hawaye yana kallon norah  dake baccin wahala beauty face dinta tak'ara fitowa fess, cikin wani yanayi   ya furta  kace norah tayi hakri  itace fa tasa na sake ta ba da ganganba,dodon kunne na naji zai fashe yakai karshen maganar kamar ya yayi ihu yake ji na jin zafin halin da norah din take ciki.....

Murmushi wanda aka kira da uncle yayi yana share ma Ammar hawayen sa dasuka kasa tsayawa,jawoshi yayi yazaunar agefensa inda D'an uwansa yazauna,A hankali yafurta mai sunan Autan maza yana jin wani abu na taso masa bayan kiran sunan Autan mazan,kayi shiru kadaina kukan nan  kaji  Halimatu sadiya tayi bacci ma kaga tadaina kukan  yakai karshen maganae yana shafa beauty face dinta,

Ajiyar zuciya ammar yasauke mai nauyi kamar wanda waci bakar wahala yasamu hutu,Jin cewa ta hakura, wanda har uncle din saida yaji fitar ta,har Aunty da yanzu tazauna bayan gama bawa ma'aikatan dake cikin kitchen umurnin  abunda zasu aiwatar yau domin bazata samu  damar shiga kitchen dinba norah ba lafiya... 

murmushi mai taushi gimbiya laylat ta sauke tana mai shafa lallausar sumar dake shimfid'e abisa kansa,domin kuwa tana mugun son Ammar musamman yadda yake nuna kulawar ga norah dinta,wadda tun ranar da fad'o duniya yake kokarin daukar dawainiyarta duk da karancin shekarunsa,wannna soyayya dayake ma nora har maamaki take bata ba ita kadai gaba daya a halin ma sun san yadda norah take agurin Ammar ,shiyasa take jin wani kud'uri yana shigarta ahankali ..........

Bayan kwana biyu tun faduwar da  norah tayi kullum cikin kuka take ga rashin bacci har saida aka kira family doctor nasu ya duba ta sannaan yatabbatar musu da ciwon kaine ke damunta mai tsanani,tun lokacin  tasamu sauki bayan an rubuta mata magungunna,daga baya sai abun yadawo wanda duk bayan kamar watanni sai tayi ciwon kai da zazzabi mai zafi,Ammmar shine mai jinyarta lokacin duk da yarintarsa dan Alokacin yana da shekara shidda itakuma shekara daya da rabi Aduniya,  kuma tun alokacin yadau alkawarin zama likita saboda norah ganin yadda take wahala,Domin yakula da ita ita kadai...Wannnan kenan............

*MUKOMA CIKIN LABARI*

Bayine  ta ko ina suna gabatar da dukkanin  ayyukan dasuka zame musu Al adah wato kai kawo domin  gudanar da aikin su,kowa da kalan uniform na sashen da yakewa hidima da masu kula da kofa fada, masu kula duk wani motsi na fadar,masu kula da dawakai,abun gwanin burgewa sai wanda yagani...

Tangamemiyar masarauta ce mai tsaunukkan gine gine masu kyau irin dai yadda kuka san ginin gidajen sarauta suke,tako wanne gefe haskene tar kamar rana na ban mamaki ko lif lif da shuke shuke,ga gurin aje dawakai da motoci na alfarma.

Wata faffadiyar koface wadda zata sadaka da fadar sarki nan  na kutsa kaina domin dauko muku rahoto duk da manyan dakarun dake tsaronnata ..

Had'addiyar fada ce mai abun burgewa tako ina fadawa ne atsaitasye ga wata kujera ta alfarma wadda tasha adon gold sai shining take yi ga fadawan dake gefen kujear baibaye da ita sai fifita sukeyi ma wanda ke kan kujerar ta alfarma Ahankali duk da AC din dake huro iska mai dadi wanda yahadu dawani kamshi...

A hankali fadawan suke furta gyara dai sarki Mai dubbanin alkhairai,Allah yakara lafiya,jin tarin dayake yi wanda ke nuna alamar  mura ke damun mai yin tarin,Hannunsa yad'aga cikin nuna mulki da Izzah,Alamar ya isa A hankali naji kyakkyawan dattijon da bai haura shekara sittin ba yayi magana da muryarsa mai nuna dattako da manyan taka,yana mai furata "har yanzu yarima baice komai ba ne galadima"?
Mutumin da naji ankira da galadima ne naga yaduk'ar dakansa yana furta Allah yataimaki sarki,ehh haryanzu bai nuna yaga sak'on mubah,yau wata takwas kenan,ni anawa ganin Allah yataimaka sarki kawai akyale sa sannan Ku gyara tsakaninku....

Wani murmushi mutumin yasaki Wanda yatsaya iyakar labbansa,zaka gane hakan inka kura mai ido duk da yana cikin rawani ,shiru baiba galadima amsa ba,saima mikewa da yayi,Dan danan fadawa suka fara karesa suna furta gyara dai sarki mai dubbanin  alkhairi,gyara dai sarki mai masarautar gado mai garin na sambo,,,

Mai garin na sambo zai fito,wata murya CE ke d'aga wannnaa sauti a waje,kirari suka cigaba da yimasa tare da kara gyara masa alkyabbar sa ta alfarma sai walkiya take na duwatsun gold,A hankali yake takawa harsuka fito daga babbar fadar tasa sai dai yau baibi ta kofar dazata sadashi da sashen UNNI ba 
Yafito ne ta kofar dazaka iya ganin komai dake gudana atsakiyar masarautar,tafiya yake yi Ahankali inda duk inda sukabi ma'aikata bayi sai sun masa irin gaisuwar nan da yan Korea suke yi a series dinsu na sarauta ga shuwagabannisu gamasu kallon su zaku gane yadda nake nufi Niko vow suke cemishi....
( Adan sunkuyar dakai kadan sai alankwasa hannu biyu ahade su guri daya kamar mai daidaton sallah,sai a saita shi akan tsakiyar goshi)Allah yasa kunhgane😜

Kansa kawai yake d'agawa alamar karba gaisuwar tasu acikin lemar da suka ware masa ta alfarma, har ya isa inda manyan motocin suke aparkey na alfarma,Isar sa wurin d'ai daga cikin fadawan da ke lullube dashi ya bude masa wata arniyyar parado new design bak'a wulik mai tinted glass  irin yan 57billion dake parkey agefe cikin wata had'addiyar rumfa inda dagani nan ne mazaunin aje wasu motocin na musamman😱 kai FA'EEH wannan karya...koda yake abunda nagani ne ai😇
 
Ahankali yashiga cikin motar dai dai Wanda ke rike da dai Wanda ke rik'e da had'addiyar umbrellan da suka kara masa tun lokacinda aka shimfida masa bugaggiyar carpet ta alfarma an rubuta MURAI'S PALACE  akanta cikin tsari mai kyau....


Bayan shigarsa motar tafiya kad'an sukayi da direban da yatuk'osa da sauran fadawan sa dasuka k'asa da algaitu da busa suna masa kirari,motar drivern yafaka A wani tangamemen gida dake d'ai daga cikin gidajen masarautar na alfarma,take fadawa suka zagaye motar suna masu kakkaresa bayan yafito a lokacin har an kara shimfida masa carpet  tare da bud'e masa umbrella ta alfarma abun gwanin burgewa sai Wanda yagani wollah in maku hausar mu ta sakkwato😀.


Tafiya kad'an yayi ya Iso kofar shiga mai rike da had'addiyar kofar ce wadda zata sadaka da falo, ya wangale masa bayan  ya rusuna masa alamar gaisuwa

Shigarsa had'adden falon na alfarma yabani damar debe keyar ido nah masha Allah nake furtawa tsayawa kwatantamuku tsaruwarsa bata lokacin ne,falon yaji komai na more rayuwa....

A hankli dukkanin bayin  dake kai kawo suna hidima asashen suke rusunawa suna gaidashi  hannu kadai yake iya d'aga musu har ya isa wata kofar inda naga wata  dattijiwa mai uniform  wasu colour masu kyau  tafito,Ashe Babbar Amintacciyar masarauta ce tun lokacinsu Ammi take hidima dasu,
 Inda yanzu ma ita keyiwa sarauniya hassaana da sarki duk da bawata hidimar bace kawai dan duba sauran ma,aikata ne sai yin iso ga sarauniya,
Iso tayi ma sarki ga sarauniya bayan tagama yimasa kirari nuna gasuwarta bayan ya karba tawucewar Alokacin duka ma,aikatan kowa yacigaba da aaikinsa....


Sallamar ce acikin uwar dakin  tasanya kyakkyawar matar dabazata wuce shekara Arba'in wadda daka ganta kaga zubin larabawa, in kallo daya zaka mata kagane wacece ita idan har kasan gwarzon d'anta,Amsa sallamr tayi atsanake cikin murya mai nuna farinciki,furtamasa tayi "marhaba biki shugaba adili ya zaujaty  ,Abul mahir Abul yuhanis,Abul Abdul rashid " takai karshen maganar ciki. Kara kawata fuskarta da murmushi,Murmushi yake ta saki Wanda yake kara  kawata fuskarsa dan yana mugun son wannan kirarin Nata murmushinsa ne yafara gushewa jin furucinta nakarshe Wanda dama tasan hakan zata faru shiyasa bakasafai take yimasa shiba,Wanda aduk lokacin da tamasa  kirarin ta ambaci sunan Abdul rashid,Abu uku ne ayanzu ke zomasa arai damuwar d'an yarima,dakuma k'anensa daya b'ata shekara talatin da suka wuce dakuma dakuma babban rashi dasuka yi na dan uwansa da iyalansa a shekarun baya,b'at murmushin dake kan fuskarsa yakyau zuwa hawaye bayan jin komaai yadawo masa sabo arai.......


Chakwakiya to ko meyasamu dan uwan nasa da iyalansa?wane kalar  rashine ne wannan 

Shin wanene kuna d'ayan d'an uwansa daya b'ata kuma ashekarun baya?

Ko suwaye wayen yan uwan NASA?
Gaskiya yabani TAUSAYI dattijon nan 😢nima kamar inzubda masa da hawaye 
Shin ko kungane wane yarima ake
 magana ?

Duka zaku samu cikon amsoshinku anan gaba kadan 
Kucigaba da bibiyata duk zan warwaremuku in sha Allah In Allah yamauna aron rai 

💫A MAFARKI NASANTA💫
     In my dream I know her
                        By 
     Pha'eezah Almustapha 
        Daga Alkalamin✍️✍️
           💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,na episode two*!!!✌️✌️💥💥

*TALLA!!! TALLAH!!! TALLAH*
*ina yan kasuwa masu son tallata hajarsu,toh ga dama  tasamu domin muna tallata kowace irin hajace daga jihohi daban daban harma da k'asashe,akan farashe mai sauk'i,zaku iya tuntub'armu ta lambobin waya kamar haka*........
*+2348069059746*
*+2348084504630*
----------------------------------------------------------------
     *💫A MAFARKI NASANTA💫*
*2023 novel is the story of an innocent girl call Halee yarinyar da* *tataso cikin rashin iyaye sannan ta* *had'u da kalubalin rayuwa mai matukar* *girgizawa inda bayan haduwar ta da* *iyayenta,wayenda suke nesa da* *rayuwarta  tasamu loosing memory,sai* *kuma takara samun "psycho" tab'n* *hankali kenan shin ko meye silar* *faruwar hakan?ya  ALAMARI AKWAI* *RIKITARWA,SOYAYYA KAM ZAKU* *SHATA,SANNAN YAR UWA ZUCIYARKI* *ZATA TABU*.....*SHIN KO WAD'ANNAN YAN TA'DDA* *ALKALAMINA ZAIYI AIKI KANSU?SU WANENE ABAYANSU ?SHINSUMA ZASU IYA KARBAR HUKUNCI ?DUK  DA KASANSEWARSU MANYAN KASA*KO MASU MUKAMIN *MENE DASU DA HAR ALKALAMINA YA KIRA SU MANYA  KASA*....
*DUK AMSOSHINKU ZAKUJI SU ACIKI WANNAN BOOK KUCIGABA DA BIBIYATA*
 --------------------------------------------------------------------
https://chat.whatsapp.com/GNSky8tcQT72iE1IVm7Vpt

💫A MAFARKI NASANTA💫
     In my dream I know her
                        By 
     Pha'eezah Almustapha 
        Daga Alkalamin✍️✍️
           💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,na episode two*!!!✌️✌️💥💥

*TALLA!!! TALLAH!!! TALLAH*
*ina yan kasuwa masu son tallata hajarsu,toh ga dama  tasamu domin muna tallata kowace irin hajace daga jihohi daban daban harma da k'asashe,akan farashe mai sauk'i,zaku iya tuntub'armu ta lambobin waya kamar haka*........
+2348069059746
+2348084504630
---------------------------------------------------------------   
    *💫A MAFARKI NASANTA💫*
    *💫In my dream i know her💫*

*2023 novel is the story of aninnocent girl call Halee yarinyar da* *tataso cikin rashin iyaye sannan ta* *had'u da kalubalin rayuwa mai matukar* *girgizawa inda bayan haduwar ta da* *iyayenta,wayenda suke nesa da* *rayuwarta  tasamu loosing memory,sai* *kuma takara samun "psycho" tab'n* *hankali kenan shin ko meye silar* *faruwar hakan?ya  ALAMARI AKWAI* *RIKITARWA,SOYAYYA KAM ZAKU* *SHATA,SANNAN YAR UWA ZUCIYARKI* *ZATA TABU*.....*SHIN KO WAD'ANNAN YAN TA'DDA* *ALKALAMINA ZAIYI AIKI KANSU?SU WANENE ABAYANSU ?SHINSUMA ZASU IYA KARBAR HUKUNCI ?DUK  DA KASANSEWARSU MANYAN KASA KO MASU MUKAMIN MENE DASU DA HAR ALKALAMINA YA KIRA SU MANYA  KASA*....
*DUK AMSOSHINKU ZAKUJI SU ACIKI WANNAN BOOK KUCIGABA DA BIBIYATA*
 --------------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCITION📚🖊️
   
               💫P.E.W.A💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

         ESSENTIAL WRITER'S📚🖊

Pen🖊️*is migthier than the sword *🗡️

EPISODE1️⃣
FREE PAGE2️⃣2️⃣


TYPING📲📲📲

A hankali tataso daga kishingid'en da take zuwa wurin mijinta cikin had'addiyar alkyabbarta

Hannunsa talakamo acikin nata sannan ta zaunar dashi akan hadaddun rugs din dake cikin bedroom din nata mai had'e da tafkekiyar tv da wankacecen gado na alfarma da tintimi irin na gidan sarauta mai taushi akan tattausar turkish  carpet  dake malale adakin

......Hawayen sa share masa tana mai kwance masa rawanin da yarufe rabi da kwatar fuskarsa,nan da nan fuskar Ammar ta bayyana agaresa hatta yanayin chocolate colour skin dinsu iri daya ne,duk da yafi kama da mahaifiyarsa ta idanunta da lips dinta ammar hatta girarsa irin ta mahaifinsa ce da tsawon,inbaku manta ba mahaifiyarsa da mahaifinsa tsatso daya ne  Diyan wa da k'ane ne shiyasa zaka ga kamar dukkansu kamar su d'aya iayayen nasu da.....

Bayan ta cire masa rawanin ta taimaka masa yacire alkyabbarsa tare da taimakon sa,A hankali ta bd'a fridge din dake chan gefen wata kofa da nafi tunanin store ne da karamin kichenn,dauko filet da glss cup mai kyau tayi na alfarma tadauro ruwan da juice masu sanyi 
Tsiyaya masa tayi tana mai kara masa abakinsa kurb'a guda yayi yajanye bakinsa yana mai sauke ajiyar zuciyah,A hankali ta bud'a bakinta ta ambaci sunansa "Ya Aliyu"haka take cemasa idan suna keb'ance ko zaujy , agaban al umma kuwa tana kiransa da maimartaba wannnan kenan.


jin Bai amsa mata ba, sai tayi Murmushi tana furtawa aranta yau kenan sarautar takaara motsawa,murmushi takara saki tunowa da duka rabin  halayen Ammar shiya kwaso komai nasu duka d'aya tafannin halayya...

Magana  ta cigaba da yi cikin natsuwa  "kayi hakuri yaa Aliyu  nasan dukkanin  damuwar ka,In sha Allah Hamma Abdul zai bayyanah"
' sai ga hawaye shar a idanunta gefen hannunta tasanya tashafe cikin jin wani zafi yana taso mata acikin ranta,

"Tabbas ina ji ajiki nah laila da hamma umar suna acikin ni'imar Allah,kabar sanyawa kanka damuwa kuma in sha Allah ko wanene sila asirinsa zai tonu duk da bamu da wata shaidar cewa ga yadda abun yafaru Amma inaji ajiki nah komai yafaru ne akarkashin sharrin wasu kuka ne ya kubce mata mai karfi,bai hana ta ba,sai da tayi mai isarta sannnan ta tsagaita dan shima kanshi hakuri kadai yake yi yana ji kamar ya fasa nasa kukan ne...

Jawota jikinsa yayi ya rungume ta yana cigaba da lallashinta,A hankali sarki Ai ya furtawa gimbiya hassana "bansan abunda yasanya zuciyatah takasa gasgata cewa emir da layla sun mutu ba 
Ako dayaushe inaji kamar zasu dawo garemu ne,inaji ajikina dukkaninsu har Autan maza zasu dawo garemu nan bada jimawa ba,Bayan  sauraren maganar mijin nata sai tayi murmushi wanda yafi kuka ciwo.....

 ta furta" yayah  Aliyu  sai dai mujira dawowar hamma Abdul...shida kawai mun wayi gari babu sa,kamanta Cewa Ansamu gawawwakinsu bbu kyan gani norah ce kadai ba,asamu koda kashinta ba,sai hawaye shar aidonta cigaba da maganar ta tayi kagakuwa Kuwa babu yadda za,ayi su dawo garemu.....Ta idar da  maganar cikin wani yanayi mai radadi da ciwo..

Murmushi yak'e yayi bayan jin zancenta,danshi sai yanzu ma yake kara tuna wasu abubuwan a lkacin da yarasa d'an uwan nasa da iyalansa,

Tambayar kansa yayi tabbas akwai zoben azurfa wanda mahaifinsu yasamusu duk su duka kuma alokacin da yasanya musu shi yasanar musu da cewa azurfar zinari  ce mai kyau wadda ko wuta baza ta iya k'onata ba,ko da ace wutar ta tab'a ta zaiyi wuya ta fita hannun mai ita inbashi yacire ba,

K'ara tuno lokacin da za,a wuce da gawawakin su kushewa bayan yimusu yar dubar domin ruwa bazai sanyu ajikinsu saboda yadda suka chanza kamanni,sai dai gwargwado abunda gawar zata iya dauka,riko hannun d'an uwan nasa yayi mai kama da kwarangwal yana hawaye yana tofa masa Addu,a,A lokacin baiga zoben a hannun sa ba,sai maganar mahaifinsu tafad'o mai arai.......Zoben baijin wuta...


Tou Amma ina zoben yashiga da suka k'one k'ila yafita tare da naman jikinsa,touh ina zoben yashiga  acikin gidan?sai maganar mahaifin su ta fado masa arai inda yace  "koda wuta ta tab'a zoben zai zauna hannun maishi ne,sai idan  ancire sa da dubara",Alokacin tunani barkatai ne sukayi ta zomasa arai,duk sai ya watsar dasu saboda tashin hankalin  da suke ciki alokacin.....


Abu daya ne yatsaya masa arai maganar rashin samun gawar norah ko wata alama ta nuna akwai ta awurin....

Maganar gimbiya hassanat ce tadawo dashi daga firar  zuci ko ince tunanin dayake "Cin abinci ko wanka zaka fara ?sannan insa Akawo ma nan?ganin yafada duniyar tunani....

Murmushi ya dajin jerun tambayoyin da ta jero masa,Cikin kara yin murmushi " har yanzu yarinya kike komawa,hassnat duk wayenn  nan tambayoyi yanzu amsa suke nema,murmushi tasaki tana mai d'aga masa kai tare da gyara daya,murmushin yakara saki mai hade da dariya ganin yau rigima take ji,itama karamar dariyar tayi,furta mata ya afara hada mun ruwan wanka,nabiyu abinci da adining zanci tareda "ya "yana...


Murmushi tayi tana furta kamanta yau akwai school mahir yatafi itakuma yuhanis  taana gurin husaina,murmushi yasaki yana shafa gemunsa wanda yafara tara yar furfura ooh hakane fa kinga na manta da auta na kusa yau da anga rigima cewa zatayi namanta ta ta baki daya tunda har namanta cewa tana gidan husaina...


Murmushi unni tayi tana furta aiko dai sarkin rigimar ka sai kai 

Murmushi yakaryi yana furta toh akawo mun nan gimbiyata,murmushi tasaki jin furicinsa,har tajuya ta tsinkayi muryar sa yana furta shin kunyi waya da mai sunan Autan maza?

Chak ta tsaya domin abazata taji domin anyi shekara bai mata magaanarsaba  saboda fushin da yake yi dashi,Akan kafewar sa,wanda har ita sai da abun yashafa sarki yashareta nawata daya kanta saka bakinta ya bar mganar tunda baiso wanda  kuma kullum cikin bincikar yaron nata take koza'a dace tunda shima kaifi daya ne kamar mahaifinsa....

Idan bazata manta ba yau shekara da wata takwas ko ma tara za,ace da sarki Ali baiyi maganar Ammar din agabanta ba duk da abaynta yana bibiyarsa,ta email wanda kosun tura sakon baya dubawa,yana boye mata ne gudun kar ta ga kamar ya karaya shiyasa bai bata damar yimasa maganar sa agabansa ba...

Murmushi ne yasubuce mata.....


Nima anan zan dakata sai gobe in Allah yakaimu 
Inkunyi comment da yawa zaku samu long  page gobe ,zanbiyaku bashi ne kawai na jiya alhamis da bakusamu ba 


Kunsan weekend bana typing ranar hutu ce 
Like pls comment share 
        
     DAGA ALKALAMIN ✍️
        💫FA'EEH BG💫

*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCITION📚🖊️
   
                💫P.E.W.A💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

         ESSENTIAL WRITER'S📚🖊

  Pen🖊️*is migthier than the sword *🗡️

EPISODE1️⃣
FREE PAGE2️⃣3



TYPING📲📲📲

Juyo wa tayi a hankali tataka inda yake zaune ta kafesa da idanunta,jin idanunta akansa yasanya sa kawar da kansa Yana mai lakace tsinin hancinsa,irin yadda Ammar yakeyi inyana cikin yanayi mai kyau 


Hannayensa ta rik'o tana furta Alhamdulillah aranta,A hankali ta bud'a bakinta tafurta  nayi magana dashi shekaranjiya,yana lafiya shida d'an uwansa,tambayar ta yak'ara yi har yanzu yana kanbakansa duk da yana da labarinsa,Amsa tabashi cikin d'ar d'ar "eh amma ina nan  ina kokarin janyo tunaninsa izuwa garemu da fushina...

" Dan duk lokacin da mukayi waya dashi ina nuna masa fushi na inbarsa cikin zullumi nasan cewa baison damuwar d'ai daga Cikin mu,ko sharekan da yayi nasan kai kafara  nuna masa taurin kai irinka naka,Allah kad'ai yasan yanayin dayake ciki ayanzu,zuciyarsa akar ye take,ni nasan waye Ammar cikin sa da bayansa,kuma nasan waye mahaifinsa...takai karshen maganar cikin jin tausayin yaron nata wasu hawaye ne suka zubo a idonta..

Murmushi sarki Ali yasaki jin kalamin ta na k'arshe..

"A hankali ya furta na janye maganar bashi sarautar,ayanzu inaso su dawo kusadamu gaba d'aya 

Ayanzu haka nakusa kammalla Gina masu babbar asibitinsa domin sudawo su rik'e ta shida d'an uwansa su kula da ita....

Farinciki ne mai yawa ya bayyana A fuskar gimbiya hassana,rungume sa tayi tana zubarda hawayen farin ciki da godiya ga Allah,daya nuna mata wannnan rana data dad'e tana mafarki

Shima rungume ta yayi cikin farin cikin dayasamu kansa a cikin cigaba da maganar sa yayi " nasan cewa Ammar yana da kud'in da zai Gina wannan Asibitin,Amma na zab'i inginata masa ita dakaina saboda inason yarike ta da mahimmanci idan yatuna wannann kyautar mahaifinsa ce a garesa,kuma A duk lokacin da akayi ceton rai acikin Asibitin nasan cewa ladar zata je garemu kobama Raye muda sauran iyayenmu...

In sha Allah wannnan Asibiti zata zamo Abin Alfahari acikin wannna kasar mu tana Nigeria  dama sauran kasashen...

'Murmushi da dariya ne yake fita akan fuskar gimbiya hassana a lokaci d'aya  k'ara rungume sa tayi  acikin jikinta,

 Murmushin ne shima yake yi na farincikin ganin yalwataccen farinciki a akan fuskar matar tasa,Wanda tada d'e batayi ba, Wanda tun bayan da yafara maganar murabus,juya mulki ga Ammar d'in,Wanda alokacin anti tak'addama sosai dan yakafe yace baiso mulkin shiyasa mai bai cika kawo musu ziyara tun da yaji anfara maganar,sai dai tawaya su gaisa shida mahaifiyarshi da "yan uwansa,Dan har wayar sarki yabar kira tun lokacin da akayi rigimar yakira mahaifin nasa yafi missed call ishirin bai d'aga ba,domin alokacin yana fushi dashi mai tsanani,saboda maganar da sukayi inda yake sanar masa kar yak'ara kiransa da mahaifinsa indai bazai karb'a ba,shiyasa daya kirasa bai d'aga ba domin yasan ba maganar da yakeson ji d'aga bakin sa bace zai furta masa...shiyasa shima sai yasharesa bai k'ara Neman saba tun lokacin duk da dukkansu suna azabtuwa,Amma zuciyar d'ayace,kowa kafiya da taurin rai..


Sarki Ali yatsinci kansa sosai cikin farinciki sanin da yayi Ammar d'nsa zaiyi farinciki fiye da nasa jin wannan labari....

Wayarta tadauko dasauri bayan mik'ewarta d'aga jikinsa,muryarsa ta tsinkaya yana furta karki sanar masa sai ankammala komai har janye  maganar  basa mulkin,b'ata fuska tayi,tana furta "saboda me adili"? "
 Murmushi yayi ganin yadda tayi kamar wata k'aramar yarinyar,yana furta inaso ne kawai yazame masa Abun kamar A MAFARKI ne murmushi tasaki,tana furta hakan yayi, Amma dai bari insanar wa  sister  wannan abun farincikin  sai  muyi farincikin tareπ


"Murmushi yayi yana furta to ki kwatse ta koh  kar ta kirasu ta sanar da Al Amin,Amsawa tayi cikin k'aramar dariya ai ko haka za,ayi......


Ruwan wanka ta had'a masa a cikin k'aton bahon  wankan na silver mai kyau,dake a cikin had'ad'den k'aton toilet din dak'in nata Wanda yaji kayan k'yalk'yali ta ko ina......
Bayan yashiga yayi wanka tafito masa ta da kayan da zai sanya,sannan ta fita domin Bada umurnin akawowa abinci a turakarta,A falon da na  biyu  kamin kashiga uwar dakin nata,Abincin suka jera cikin tsari mai kyau akan wata had'addiyar carpet din dake malale afalon,Alokacin duka ma'aikata sun gama ayyukansu na rana...

Kuyi hakuri da wannan ba nida isashen chaji ne 

Shinko kuna ganin Dr.Ammar zaiyi farinciki?
Kuma zai baro k'asar India?

Shin ko akwai sanadin da yakai sa k'asar India karatu,ko ko dai Ra,ayin kansa ne?.......

Jama'a ina labarin Halee nasan wasu harsun manta da ita ......


A gobe in sha Allah zamu lek'a rayuwar Halee baiwar Muji a wani hali take sannan wace irin rayuwa take fuskanta ne ayanzu shinko Baba Asabe ta shafa mata lafiya ganin idanun Baba Asabe ko kodai tacigaba da muzguna mata......

Wacece ita?

Mekuke tunani game da rayuwar Halee?
Mu had'u a comment section dan jin hasashen kowannenku.......✍️✍️

Shin tsintacciyar ce dagaske kamar yadda Baba Asabe ke yawan furtama taa?

Shin waya bada Amanar  Halee da har Baba Adee yakirata da Amana?
Sannan waya bada Amanar ?
Waih........🤭


Nima fa kaina ya kulle 🤔
Kudai kawai kucigaba da bibiyar Alkalamina✍️✍️domin Warware muku wannan labari mai cike da darussa...

Kuyi sharing kuyi comment    
   💫 FA'EEH BG💫


💫A MAFARKI NASANTA💫
     In my dream I know her
                        By 
     Pha'eezah Almustapha 
        Daga Alkalamin✍️✍️
           💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,na episode two*!!!✌️✌️💥💥

*TALLA!!! TALLAH!!! TALLAH*
*ina yan kasuwa masu son tallata hajarsu,toh ga dama  tasamu domin muna tallata kowace irin hajace daga jihohi daban daban harma da k'asashe,akan farashe mai sauk'i,zaku iya tuntub'armu ta lambobin waya kamar haka*........
*+2348069059746*
*+2348084504630*
----------------------------------------------------------------
     *💫A MAFARKI NASANTA*💫
*2023 novel is the story of an innocent girl call Halee yarinyar da* *tataso cikin rashin iyaye sannan ta* *had'u da kalubalin rayuwa mai matukar* *girgizawa inda bayan haduwar ta da* *iyayenta,wayenda suke nesa da* *rayuwarta  tasamu loosing memory,sai* *kuma takara samun "psycho" tab'n* *hankali kenan shin ko meye silar* *faruwar hakan?ya  ALAMARI AKWAI* *RIKITARWA,SOYAYYA KAM ZAKU* *SHATA,SANNAN YAR UWA ZUCIYARKI* *ZATA TABU*.....*SHIN KO WAD'ANNAN YAN TA'DDA* *ALKALAMINA ZAIYI AIKI KANSU?SU WANENE ABAYANSU ?SHINSUMA ZASU IYA KARBAR HUKUNCI ?DUK  DA KASANSEWARSU MANYAN KASA KO MASU MUKAMIN *MENE DASU DA HAR ALKALAMINA YA KIRA SU MANYA  KASA*....
*DUK AMSOSHINKU ZAKUJI SU ACIKI WANNAN BOOK KUCIGABA DA BIBIYATA*
 --------------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCITION📚🖊️
   
               💫P.E.W.A💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

         ESSENTIAL WRITER'S📚🖊

Pen🖊️*is migthier than the sword *🗡️

EPISODE1️⃣
FREE PAGE2️⃣4️⃣

TYPING📲📲📲

*INDIA*.....

wata kyakkyawar yarinya ce mai zubin asalin larabawa fara tass da ita ta isko sa zaune abakin ruwa,itama sai ta zauna akusa dashi,ba yanzu ne yafara ganinta ba bare ya damu Akullum tana zuwa wurinsa suyi fira wata rana ma fad'a,ta bud'a bakin ta kenan Tana furta D'an uwanah sai ga wasu mutane masu bak'ak'en kaya sunzo wurin da zuwansu suka yi kan wannan yarinya suka daddafeta tana kuka tana rok'on karsu cutar dashi,wanda shima wasu sun rirrik'esa kasancewar su majiya karfi sai yaakasa kwatar kansa agaresu bare itama yataimaketa,haka suka sanya bindiga suka harbeta yana kallo ga kukanta da yake ji har tsakiyar kansa zuciyarsa har wani b'al b'al take na tashin hankali,suna gamawa da ita duk sai suka gudu har wayenda suka rik'esa suna masu furta masa kaima zamu dawo kanka,baibi takansu ba sai yadda zai ceto ranta yakeyi, sai ma Rungume wannan  yarinya da yayi wadda har yanzu baian sunantaba Amma yasaba da ita sosai har sonta yashigesa baisani ba duk da yana kokarin b'oyewavzuciyarsa hakan 

Kuka yake kamar wani k'aramin yaro  yana jijjigata wanda take mayafin dake kanta yazame wanda yabbayanar da lallausar doguwar sumar ta har yarufe mata rabin fuskarta saboda yadda yabarbazu,ganin ta fara nisa ne Alamar mutuwa zatayi yayi ga jininta yana ta zuba,yasanya vail dinta yad'aure mata inda suka harbetan aciki ganin jinin yak'i tsayawa ne kuma yasanya sa cikin rud'u yak'ara sanya handkerchief d'insa yana k'ara danne wurin harbin,kuka yake cigaba da yi yana girgiza kansa alamar no cikin rud'u lallausan gashin  kansa duk ya  hargitse,sungumar ta yayi kamar  wata jaririya yana yi yana kallon kyakkwar fuskarta ganin yadda take fitar da numfashi na wahala,
Takawa yafara yi daniyar bata agajin gaggawa acikin gidan nasa sai yaga hannayenta sun saki yaraf Alamar ta mutu kenan,wata uwar k'ara yasaki yana girgizata a matuk'ar rud'e yana furta "nooo karki  tafi  kibarni",ganin bata motsaba yakara furtawa cikin fitar hayyaci  "karki tafi ki barni" Yana kuka kamar karamin yaro ..........................


Misalin karfe 3 :00 na dare 
Kwance yake akan had'adden gadonsa  juye  juye yakeyi akan gadon kamar wanda ke cikin wani yanayi na damuwa,ya had'a zufa duk da karfin a.c dake a bedroom din nasa da sanyin da gari yake dashi na watswar hadari Dr.Ammar kenan.......

Bayan kamar minti hud'u ya farka agigice cikin fitar hayyaci yana furta "karki ki tafi ki barni",A hankali yafara yadawo wa cikin natsuwarsa Addu'o'i yayi na neman tsari Akan mafarkin dayayi,take mafarkin da yagama yi yafara dawo masa akai kamar ayanzu abun ke faruwa duk da yasaba yin mafarkin sa da wannan yarinya,Ammana ya yau yabashi tsoro..

Tagumi Ya rafka bayan gama tunano da mafarkinsa wanda yasha banban da sauran mafarkan nasa da yarinyar,Dan shin ruwa da yaji akwar min idonsa ne yasanya shafo kyakkyawar fuskarsa da lallausan hannunsa guntun hawaye ne yaji sun gangaro  suka zubo acikin idanun nasa bisa beauty face dinsa big  sparkling eyes nasa sai suka kara haske da shining na ruwan hawayen da ke cikinsu curly eyelashes nasa suka k'ara cure wa waje d'aya...


Tambayar kansa yayi shin yanzu dagaske sun kashe masa ita?kuma suwane ne wad'an nan mutane da har suka yi masa barazana?,me  ta musu?meye had'inta dasu,?yana jin badadi aransa zuciyarsa tayi d'aci mafarkin nasa na yau abun yatab'a shi duk da yasan mafarki ba gaskiya bane,Amma yasaba da yarinyar tana tayashi fira abakin swimming fool nasu shiyasa akodayaushe yake yawan zuwa bakin ruwan ko zai ga koda fatalwartace ....


Tambayar kansa yak'ara yi wacece ita da har ta iya kiransa da D'an uwanta? duka wayen nan tambayoyi suna tayawo ne acikin kwakwalwarsa,rasa mai basa Amsoshin tambayar sa ne yasanya shi tashi yayo alwallah,ya zura jallabiya fara mai taushi,akan short d'insa,ya shimfid'a sallaya ya raya darensa sannan yayi karatun alqur'ani mai girma acikin zazzakar muryar sa domin kuwa Dr ammar akwai kira'a yana da hizif talatin akansa ne,
Addu'o'i yayi na Allah yasa mafarkinsa ba gaskiaya bane,sannan yanemawa kansa kariya da wannan baiwar Allah da haryanzu ko sunanta baisani ba,sannan yayi Addu'a ga k'anen mahaifinsa da nora da na Allah yajik'ansu da rahama,yakuma bayyanar da takwaransa lafiya,sannann kuma yana Addu,a da fatar  Allah mahaifinsa yasauko daga fushinsa,sannan yayiwa Al ummar musulmi addu,ar zama lfya, ire iren wayen nan Addu'o'in sune yayi sannnan yacigaba da kira'ar sa har yaji ankusa tada sallar asuba,fitowa nasa d'akin yayi yana k'wankwasa ma Aj kofa A lokacin shima Aj ya shirya suka d'unguma sai masallacin unguwar su....


*NIGERIA*
*BUNGUD'U ZAMFARA*

Halee ce ta mik'e zaune daga barcin da take yi tana furta innalillahi wa inna ilaihi raji'un,khady ce itama ta mik'e zaune tana tambayarta lfya?,

A hankali ta bud'a bakin ta cikin rashin kuzari da tsoro ta furtawa khady cewa "mafarki nayi",dafa ta khady tayi tana tana furta kamar wane kalar mafarki kenan..Shiru tayi mata tana jin zuciyar ta ba dadi,sai kuma ta fara bata labarin mafarkin nata 'wasu mutane ne suka zo kasheta sai ga wani mutun mai kayan sarauta ajikinsa yazo yataimake ni sai dai banga fuskar sa ba saboda rawanin dayarufe fuskartasa,ahaka yayi iya kokarin yakare ni sai dai Allah bai nufa ba sai suka kasheni,sannann kuma kafin in mutu naji suna furtamasa saura shi shima zasu dawo kansa,dukkaninsu jikinsu yayi sanyi musamman Halee dake bada labarin tanaji kamar abun zai faru dagaske ne,kasheta d'in da maganar da suka furtama wannan bawan Allah,Khady ce cikin kwantar ma Halee da hankali ta furta karki saka damuwa Halee mafarki ba gaskiya bane,ni wai ma kinyi Addu,ar kwanciya kuwa?ta tambayeta ne duk da tasan Halee bata wasa da Ibada,tasan awasu lokuttan ma ita ke shafeta da Addu, a in bacci yadauke ta batayi ba,ta tambaye ta ne kawai domin kawar mata da tunanin da ke shirun addabar ta,d'an kallonta Halee tayi cikin damuwa tana langab'e wuyanta kyakkaywar fuskarta takara kyau,kara furta mata khady tayi ganin bata bata amsa ba,aikin shed'an ne kawai may be kinyi kuskure awurin yin Addu,ar ne musakeyin Addu'ar  ta furtama Halee da ke ta Kallonta,murmushi tayi tana  furta mukawana lafiya bayan gama Addu,ar tasu suka gyara kwanciyar su,Amma ita kam Halee har Asuba tayi bata runtsa ba,tunani ne barkatai ke zomata...

A hankali ta mik'e daga kan katifarsu zuwa toilet nasu ta dauro alwallah,raka'atanil fajr ta gabatar sannan tayi Asuba tagabatar da Addu'o'in ga wannan bawan Allah,wanda ko da ace tagansa afili bazata iya ganesa saboda rawanin da yayi k'awanya wa fuskarsa,sannan tayi Addu'ar Allah ya had'a ta da iyayen a Aljanna idan har sun mutu..
Inkuma suna raye Allah yabayyanar mata dasu,Byan tayi karatun alqur'ani acikin zazzak'ar muryar,dogon hijab dinta na sallah ta cire ta lunke,sannan tasanya d'an k'araminta na tsakar gida komawa tayi kan katifar su d'an runtsawa kafin gari ya waye taje yin ayyukkanta  basai Baba Asabe tazo tashinta ba,saboda weekend ce babu makarantan boko  sai ta islamiyya,gashi Baba Adee ya koma  mafara gurin aikinsa tun satin da ya wuce.....

Bayan ta kwanta baccin yagagareta tunanin mafarkin da tayi take

Hawaye ne ke silala a idonta wanda bata san dalilin su ba,ko na tausayin wannan bawan Allah ne ko na tausayin rayuwarta ne,shesshekar kukanta ne yasanya khady bud'e idanunta tar akan Halee bayan jin shesshekar kukan nata,wadda tunda takoma barcin bata tashi ba saboda tana fashin sallah...

Leka kyakkyawar fuskar Halee tayi dan ta tabbatar indagaske ne kukan takeyi duk da tasan kuka bai wa Halee wahalar yi,sharkaf taga kyakkaywar fuskar Halee da hawaye batace mata komai ba tabarta tacigaba da shesshekar kukan ta sai da tayi mai isarta ko zuciyarta zata samu salama,domin yin kukan ma wata rahama ce ga d'an Adam...

Bayan ta tsagaita da yin kukan sai kuma bacci yakwasheta daga nan kishingiden da take......


Halee baiwar Allah


Koda ta farka har khady tayi wanka tahad'a mata musu abun da zasu karya dashi sannan ta gyara ko ina na gidan har jidan ruwa ma tagama A murtsatse.

Kallonta kawai Halee keyi wadda tafarka cikin zullumi tuna wa dayau batayi aikintaba,kafe khady tayi dake zaune akan d'an madaidaicin mirron d'akin nasu ta shiryawarta cikin doguwar riga ta atamfa, da manyan idanunta da tambayoyi barkatai aranta, khady lura da kallon datake mata ne yasanyata yin murmushi tana furta madam ki tashi kiyi wanka mu karya sai kiji komai,Murmushi itama Halee tayi har sai da fararen hak'oranta suka Bayyana tana mai mik'ewa tazuro fararen kafafun ta sannan takama hanyar toilet,tareda daukar  flask na ruwan zafi ahannunta,har takusa kai bakin kofar toilet din ta tsinkayi muryar khady na furta Aunty na had'a miki ruwan wankan ki maido da flask din murmushi Halee tayi,tana juyowa Ahankali tasakarma khady yar karamar harara tana furtawa cikin sanyin murya "nikam banace kibar cemun Aunty ba?,harda wani rik'e habarta irin ba wasan nan,khady kuwa mezatayi in ba dariya ba ganin yadda halee tayi,"watan ma dariya nabaki tak'ara furtawa cikin d'an murmushinta mai narkar da zuciyar yan maza,har sai da dimples dinta suka bayyana,take kuma tak'ara turneke fuska irin ba wasan nan,Khady ce cikin dariyarda ke cinta gani fuskar da Halee tasha,kama kunnuwanta tayi tana kokarin hadiye dariyarta tana furta sorry shalelen  dady,Itama Halee dariyar ce ta kubcemata,jinta ambaci shalelen da Baba Adee ke kiranta dashi wanda take mugun so arayuwarta tun bayan iyayenta wayendabata ko san suwaye ba.........

Wassh hannu na ai namuku kokari
Kuyi hakuri ban samu namuku editing ba.

next page tomorrow in sha Allah

Me kuke tunani game da wannan mafarki na Dr ammar?
Shin wace yarinya ce wannan?
Kucigaba da bibiyar alkalamina duk zan warware muku kowanne babi na book d'ina


Comment,like,share pls

https://chat.whatsapp.com/IjZCle5c6V3BGRlnZ0yKim

💫A MAFARKI NASANTA💫
     In my dream I know her
                        By 
     Pha'eezah Almustapha 
        Daga Alkalamin✍️✍️
           💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,na episode two*!!!✌️✌️💥💥

*MASU SON*
*TALLA!!!SHOULD* *CONTACT ME VIA*

*+2348069059746*
*+2348084504630*
------------------------------------------------------------------
 --------------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCITION📚🖊️
   
               💫P.E.W.A💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

         ESSENTIAL WRITER'S📚🖊

Pen🖊️*is migthier than the sword *🗡️

EPISODE1️⃣
FREE PAGE2️⃣5️⃣


TYPING📲📲📲


Dasauri ta juya zuwa toilet din tana furta mama dije ruwan wanka na zasu huce tana dariya,tare da turo kofar toilet d'in,Dan tasan khady batason sunann nan na mama dijen da take kira mata ita kuma batason auntyn datake kira mata duk cikin su babu wanda  yasan wanda yagirmewa  wani  acikinsu..

Khady da aka kira da mama dije har ta kumbura koda halee ta fito daga tolet daure da towel mai dan girma da hijab dinta d'an karami wanda tashiga dashi toilet din da zanen da tashiga dashi a hannunta,tunda ta fito take k'unshe dariyarta ganin yadda khady tayi kichin kichin da fuskaWadda har tabar kan madubin nasu..

 d'an madaidaicin madubin nasu da yaji kayan gyara gwarwado na talaka,musamman turarukka sunfi yawa saboda Bba Adee akwai son kamshi,har sun saba da sanya sa ako da yaushe sai dai yana gargadin su kar su rika sanya mai tashi sosai inzasu fita ,sai  dai su rika sanya wanda kamshinsa bai tashi kamar yadda annabi saw  yasiffanta turaren mata,da na maza..Mai kala shine na mata amma kamshinsa bai tashi kamshi na jan hankali  bare yazamacutarwa ga wani,wanda inkika shafa sai anmatso kusa dake za,aji kamshinsa,na maza kuwa marar kala ne sai dai mai karfi ne wanda duk inda suka giffta sai anji sa...

Bayan ta zauna akan kujerar madubin tafara yin  "yan shafe shafen mu na mata akan lallausar fatar ta wadda kullum kamar ana mata wankan madara duk da bata da wata natsuwar zuciyah da kwanciyar hankali,turaruka ta fesa sunyi biyar nan da nan d'akin nasu yarikice da kamshi dan itama Halee nmba Banza ba wurin son k'amshi kajol tashafa da man baki lip glow take kyawonta yakara bayyana irin zubin larabawan qatar  da fulanin eqypt..

A hankali  tajanye hijab d'in dake kanta take yalwataccen  gashinta mai laushi da santsi yabayyana  wanda yake adunkule  saboda kwana biyu  baisamu gyara ba,warwareshi tayi masha Allah na iya furtawa,  tajeshi  tayi yasauka har kan gadon bayanta tasanya man gyaran gashi har wajen kala uku  wanda take kannata yad'auki walkiya gwanin burgewa,Daure gashin take kokarin yi sai dai yana kuncewa sai danbe takeyi dashi gajiyar datayi ne yasanya ta fara alamar sakin kuka tana kallan  khady ta madubi wadda ke zaune akan gabar katifar su,Khady dake ta k'unshe dariyar ta ce ta fito fili har tasauko daga fushin nata na wasa,'tana furta Allah yak'ara bake bace kinsan yadda gashin nan naki yake da santsi haka kika yi ta labta masa mai nikam ba abunda zan iya miki ta iyar da maganar ta na k'ara kwashewa da dariya har da rik'e ciki ganin yadda kyakkaywar fuskar Haleen ke nuna Alamar takai k'arshe kiriss take jira ta fasa kuka,kukan tafara kuwa dagaske harda buga kafafu ak'asa,fararen kafafunn ta kawai kake hangowa tana tsitsillasu akan tiles d'in d'akin kanta akan desk na madubi tana furta "nikam aske gashin zanyi na huta kawai, khady kuwa na kwasar dariya...

Rezor blade ta zago daga chan sakud'an madubi,harta d'aura akan jelar dogon gashin  ta dake chan kan gadon bayanta tajawoshi gaba,zata yanke khady ta rik'e hannunta tana furta hurul aini meya yayi zafi haka yanzu dai bani rezor d'in mik'amata tayi tana cunno bakinta gaba,mik'ar da ita tayi tana daga kan madubin tana "furta mata Aunty yanzu idan kika aske gashinfa kuma kikayi Aure  mijin ki naso yaza'ayi ....takai kqrshen maganar tana boye dariyarta ....

A hankali  Halee ta furta sai insauka na kanti man irin na yan Nigerian film..

"Khady CE ta furta to inyace baya son sa fa ya zakiyi?,hararar khady tayi domin ta fara isarta da surutu Ga kanta yafara ciwo..

"A hankali ta furta Ke ni bazanyi Auren 
Ba ma tana mai takawa izuwa sip dinsu sashen da kayanta suke ajiyeta bud'a dan kowa Dana sa gefe domin dinsu daban daban ne saboda Khady tad'ara Halee jiki,wata doguwar Riga roba ta fiddo da hijab karami,bayan ta sanya hijab har k'asa dama d'abi'ar tace sanya kaya acikin hijabi saboda kunyarta...

Ko khady dasuka tashi tare bazata iya kawo yadda take da kyan sura ba tunda suka fara girma ko bacci in zatayi sai ta sanya hijab,khady tayi tayi tabari Amma ina yazame mata jiki....

Tana cikin sanya rigar ne Tatsinkayi muryar  khady na furta matar liman kiyi  sauri kar Abincinmu ya huce gashi na zuba toh,tace mata tana furta,"Aa ah ba matar liman ba matar Malan cikin sakarma khady harara,dukan su dariya suka sanya na furucinta,tsaf ta shiya acikin doguwar Rigar ta wadda ta bayyanar da duka dirinta acikin hijab din kasancewar sa na roba ne kuma bakin kunkurunta ya tsaya ga tsayayyun breast din ta nan cikin rigar sun bayyanar da girman su saboda bata saka bra,acewar tana takura ta,turare  ta fesa akan kayanta ta taka ahankali kan carpet din da Khady ta ke zaune wadda ta shimfid'a itama ta zauna,khady da ta fara cin abincinta CE ta furta zuba naki ga filet nan dan nikam naga alamar shirin naki bazai kare ba,filet ta dauka tazuba jalof din macaroni dan kad'an Khady CE tagaza yin hakurin maganar dake cinta ta furta " kin san wani abu?" Kai Halee ta girgiza mata, "wallahi Halee mijin ki zaiyi fama......

*GUSAU*
Abangaren su sarki Ali da unni  bayan ya fito  wanka ya  kimtsa da taimakon  ta...
 manya manyan food flask ne farare kar tafara kwasowa daga falon nata zuwa uwar d'akin nata dakanta domin haka take bata yadda wasu suyi wata hidima ga mijin ta indai wurin cimakarsa ce dakanta takeyin komai,Kuma bata bari bayi su shiga har uwar dakin NATA inba Aminttacciyar masarauta ba wadda takasance tun ta kakanni ita take masa komai koda asashen sa ne.

Bayan tagama jera kulolin atsakiyar katuwar carpet  din dake malale sai tayi masa I so  yazauna kafafunsa ya tankwashe bayan zamansa,favourite food dinsa tazuba masa tuwon shinkafa da miyar kuka da taji busashen kifi zai tashin kamshi takeyi spoon tasanya masa aciki,d'ayan filet d'in tasanya masa farfeson kayan ciki dayaji gyara sai tashin kamshi yakeyi...

Abincinsa yake ci ahankali shayi ta had'a ma kanta itama tana kurb'a a hankali....

Muryar dan matashin saurayine dabazai wuce shekara ishirin da biyar ba ko da hud'u take yin sallama A cikin falon dukkaninsu Amsa sallamr sukayi suna masu kallon kofar shigowa,wani  kyakkyawan saurayi ne Wanda daka gansa kaga gimbiyat hassana( unni)
Hatta farin fatar sa natane tsawonsa zai ne na mahaifinsa,kumbure fuska yayi ganin yadda duk  suka tsira masa idanu kowa da kallon tuhumar da yakeyi masa....
Takowa yakeyi cikin tafiyar takama irinta tafiyar sa sak irinta Ammar zama yayi Ahankali kusa ga mahaifiyarsa yajingina da jikinta,sarki Ali dake kallonsa ne yagirgiza kai yana sakin  murmushi yacigaba da cin abincinsa,kwantacciyar sumar kansa take shafawa da hannunta d'aya tana cigaba da kurbar shayinta....


 💫A MAFARKI NASANTA💫
     In my dream I know her
                        By 
     Pha'eezah Almustapha 
        Daga Alkalamin✍️✍️
           💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,na episode two*!!!✌️✌️💥💥

------------------------------------------------------------------
 --------------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCITION📚🖊️
   
               💫P.E.W.A💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

         ESSENTIAL WRITER'S📚🖊

Pen🖊️*is migthier than the sword *🗡️

EPISODE1️⃣
FREE PAGE2️️6


TYPING📲📲📲

     
Gyaran murya sarki Ali yayi Wanda yasanya mahir d'ago manyan idanunsa yakallesa,muryar sarki Ali ke furta wai kai Baba yaushe zaka girma ne eh kullum Kullum haka kake komawa d'an jiya Yanzu idan ka karya mun kad'ar mata fa ya ida maganar Yana sakin  murmushi,Dukkaninsu ma murmushin sukayi, cigaba da magana yayi wai ko kamanta akwai yuhanis A bayanka ne Yana rike hab'arsa irin mamaki...

Dariya mahir yasanya ganin yadda mahaifinsa yayi,A hankali ya furta Ayyah Abbanmu ni Dama nine Autan ba wacchan sakaryar ba,...

"Ai inson jiki ne da shagwab'a sai naga kamar ka fita ma inji" cewar sarki Ali
Murmushi kawai gimbiya hassana take ta saki jin rigimar tasu,bata cika sanya baki ba saboda Karrama sunan sunan mahaifinsu dake gareshi,shiyasa take d'an basarwa saboda Alkunyar jinin larabawa da Fulani dake yawo ajikinta..

A hankali ta furta Baba na meya dawo dakai gida irin wannan lokaci kai da kace kuna da lectures har har uku ko ma hudu ne,Agogon hannunsa ya duba karfe biyu 2:00 pm na rana ya mutsa fuskar sa yayi yana furta" unni kinga sai karfe hudu bayan la'asar zamu koma hall kuma kinga lecturen da zai muna lecturen karfe hud'un akayiwa mutuwa mahaifiyarsa ta rasu  sanadiyyar gobara sanadiyyar wutar lantarki datakama gidan tsohuwar shine dukan mu duka yan hall din mu har lecturen da yake lecture awannan lokaci duk muka tafi gidan mutuwar muyi gaisuwa,shine daga chan nacewa su Abdallah na wuce saboda kaina dake ciwo",Addu,a suka yi ga mamaciyar cikin jimamin domin kowa yasan kunar wuta yadda take da azaba bare ma Ace duka jikinka ta cinye,ALLAH YAKARE MU DA SHIGA WUTAR JAHANNAMA🙏

Wanda Alokacin dukkansu sai da suka ji wani kololon aransu,ganin yanayin da  mahaifannasa suka shiga yasanyasa jin ba dadi  yanaji dama bai sanar dasu batun mutuwar ba domin yasan dama dole zasu badadi,tun da irin haka ta yataba faruwa ga uncle dinsu lokacin bashida wani wayo kuma Ammie tana yawan yin maganar agaban su cewa sun tab'a rasa family d'aya acikin zuri'ar su,ta sanadiyyar gobara,domin tana cewa dasu su rika sanya su a Addu'a,duk dashi yasan su harda yar tasu Sai dai bazai iya tuna yadda fuskokinsu suke ba duk da ance suna kama sosai ne da su,Ayanzu  yana son yaji yadda labarin abun yafaru duk da yasan wani abu daga ciki...

Muryar mahaifinsa ce tadawo dashi daga tunanin zucinda yashiga"maheer kaci abinci sai kasha magani ko kaje ka d'an huta"?murshin yake yasaki jin maganar  da mahaifinsa ya furta,gashi shikuma yana da tambaya agaresu,Amsawa yayi da touh! sai kuma ya bud'a bakinsa da murya mai rauni yace "Abba da Unni please ku k'ara sanar dani labarin su uncle dasuka k'one achan baya  Domin Ammie tana yawan furta mu musu Addu'a  inason insan silar wutar tasu...

Murmushin karfin hali irin na mahir sukayi sai kuma  Ahankali sarki yafurta kanason kasan yadda labarin yake duk da nasan kasan su alokacin baya wanda bawani wayo ne dakai ba...

kai mahir yad'aga.


*LABARI*..........................
A wata safiyar laraba da bazamu tab'a mantawa da ita ba A cikin masarauta muka wayi gari cikin tashin hankali bayan samun labarin gidan D'an uwa na Sarki Umar Yakama da wuta.......

A lokacin da labarin ya riski sarki Ali dasauran mutane masarautar sun kid'eme sosai fiyeda tunanin mai karatu,koda aka kira fire service domin kawo taimakon gaggawa duka dukan gidan yacinye da wuta ba'asamu komai agidan ba face gawawwakinsu dasuka koma babu kyan gani,A lokacin Ammi da su hassana da husaina kamar su fad'a cikin wutar dakyar akasamu suka natsu bayan anrirrike su, musamman Ammar  Inka ganshi yakoma kamar zararre duk da karancinsa,kowa kagani alokacin tashin hankalinsa Abayayne yake musamman na rashin ganin komai da yashafi yarsu kwaya d'aya tilo a duniya yar shekara biyu da ba'ayi ba sai tokar,mutun d'aya  zuwa biyu wayen da suka nuna ko inkula akan kaddarar da ta farma su Sarki umar ,shine muhammad (Malan) Da mahaifiyarsa fulani duk da yadda suka nuna ko ajikinsa Amma babu wanda ya zarge su  akan wani abu,duk da anyi bincike ba, angano  sanadiyyar tashin wutar tahanyar jin kamshin fetur acikin sashen nasu wanda aka tabbatar zubasa akayi kuma shine sanadiyyar tashin wutar, kowa yayi mamakin kasancewar fetur din acikin gidan hankalinsu ne yakara tashi fahimtar kamar akwai wani abu akasa...

Anyi zaman makoki an watse lafiya wanda har lokacin Ammar bai koma dai dai ba tun bayan da yaji yaga yadda wuta ke cin gidan uncle dinsa,kuma yaji ance gabaki d'aya sun mutu har Auntynsa da norah, duk da yadda akayi kokarin boyemusu shida mahir da Al amin,yayi suma yayi biyar ana ukun ne yayi doguwar suma wadda bai farfado ba har saida akayi ukun su sannan,Tun alokacin yafara mugun mafarki naban tsoro agigice yake farkawa sai kuma yafara yadawo yafara yin na k'aramar yarinya na kuka tana neman taimakon sa wuta na cin jikinta sai yaje taimakon ta sai ta zille ta karasa fadawa cikin wutar bata bari yarik'o ta haka yake mafarkin kullum har mahaifiyarsa da mahaifinsa suka gane abunda yake faruwa agaresa bai dawo dai dai ba sai da akayi wata biyu,wanda Alokacin Al Alamin ne mai lallashin sa ko mahaifiyarsa inda zuwa lokacin mafarkin nasa yazamo yabar ganin karamar  yarinyar acikin wuta..


A baya A kullum yakan yawaita furta uncle dinsa ba mutuba da auntynsa da norah d'insa sunyi tafiya ne,inda sai da ka tayarmasa tsaye aka dage da Addu'a yadawo normal ganin abun yafara tabasa yakusa zame masa hauka,Bayan samuwar kansa sai aka tura su k'aasar india ganin cewa idan yanisanta da gida zaifi dawo wa dai dai yasake kamar kowa,Achan suka cigaba da karatunsu tundaga primary three din da suke a nigeria,sai dai kamar yadda kayi tsammani bayan  zuwansu kasar india  nadan lokaci,suka ga yara ire irensu ga wuraren wasanni nan kuma karatun su suke ba wasa sai Ammar yafara mantawa yafara  sakin jikinsa ga sauran makarantar tasu domin boarding ce,wanda kuwa afarkon zuwansu Al amin kadai yake mu,amala dashi,A lokacin ne  mafarkin daya keyi achan baya yadawo masa,A wanchan lokacin yana ganinta cikin kuka ayanzu kuwa cikin tafiyarta irinta ta yara masu wayo yake ganin tana wasarta tana dariyar ta gwanin bugewa,bata ma kulasa duk da yana ganinta tana ganinsa.

Tun mutuwar nora dinsa yace bayason yin karatun likitanci bayan tabbatar da cewa dai tatafi domin dama danta zaiyi,shi burinsa dayatashi dashi shine karatun pilot waton matukin jirgi,wanda shikuma Al Amin nasa burin keman yayi karatun likitanci,wanda   sai  da mahaifinsa yabashi  baki yace yayi yataimaki Al ummah saboda Alllah itama dasu  uncle dinsa zasu samu lada wannan kenan.

Kaji dalilin zaman yayanku doctor akasar india, da kuma dalilin dayasa yayan ku yake zama india shida Al Amin  har yazamana sun zamo manyan likitota akasar da batasu ba...
                  **********
                   *******
                    ****
------------------------------------------------------------------
"Sarki Ali ne yaci gaba da maganarsa D'an uwana sarki umar a wanchan lokacin shine ya mulkar masarautar nan,yana "yaa norah wadda taci sunan kakarku hajiya sai kuma matarsa lailat ina fa'd'a make kawai duk da nasan kasani yadda zakaji komai yadda yake alabarin ne..yakai karshen maganar cikin wani yanayi yana jin komai yadawo masa sabo...


Hawayene Suka zubo a idanun mahir dasu yuhanis,da sumee da zuwansu kenan aka fara bada labarin sai da babu wanda ya lura dasu,sunyi sallama sai dai ba'a amsa musu ba shine dalilin dayasa suka shiga falon kaitsaye,Haka itama unni hawaye take zubarwa mai zafi maimartaba sarki Ali shine mai lallashin su,shine yafara lura dasu Nisa A tsayen dasuke ido jage jage da hawaye kyafato su yyi tahanyar yimusu Alama..

A hankali suka taka inda suka zauna akusa dashi suka sanya sa tsakiya,suna masu cigaba da zubar da hawayen su,domin su ana goyonsu ne lokacin basu san komai akan labarin ba sai yau duk Ammi na yawan furta musu sumusu Addu'a..

Share musu hawayen yayu yana furta musu kudaina kuka kunji "ya "yan Unni,kai suka d'aga masa da alamar toh,suna masu sake share  hawayensu,"kara furtamusu yayi kumusu Addu'A kunji ita suke buk'ata agareku..
 
Yau ansamu long page😎 

https://chat.whatsapp.com/IjZCle5c6V3BGRlnZ0yKim
💫A MAFARKI NASANTA💫
     In my dream I know her
                        By 
     Pha'eezah Almustapha 
        Daga Alkalamin✍️✍️
           💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,na episode two*!!!✌️✌️💥💥

*MASU SON A TALLA TA MASU HAJARSU*
 *SHOULD CONTACT ME VIA*
*+2348069059746*

------------------------------------------------------------------
 --------------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCITION📚🖊️
   
               💫P.E.W.A💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

         ESSENTIAL WRITER'S📚🖊

Pen🖊️*is migthier than the sword *🗡️

EPISODE1️⃣
FREE PAGE2️⃣7️⃣

TYPING📲📲📲

Bayan dukkaninsu sun samu natsuwa sai Sarki Ali yatambaye su daga ina suke gida ko schl 

YAr bak'ar wadda take kama da Dr.Ammar sosai ce ta furta" Abba muntaso daga school ne shine muka ce driver yakawo mu nan muganku.

Murmushi sarki Ali yayi yana furta" su sumayya uwayen yawo",sumayya datake d'an satar kallon mahir tad'an kawar da kanta gefe cikin jin kunya tana furta

"Allah Abba bana da yawo,Nisa ce tace sai munzo nan kuma gashi bamu ma gaya wa Ummi ba".

mugun duka Nisa takai  mata Abaya Bayan jin kazafin da tayi mata, cikin  shagwab'a Nisa ta furta Allah ni Abba ba ruwana itace tace muzo zata karbi sako gurin yaya mahir.

Abbah da jin wannan magana ta Nisa sai yayi murmushi irin nasu na manya dan dama dazu yaga yadda Sumy ke satar kallon Mahir Din sai dai bai kawo komai ba aransa,Murmushi yakarayi irin na jin dadi,sannan  A hankali ya furta"Sumayya wani irin sako ne halan?sumayya dake cikin zullumi dama tana tsoron hakan tafaru dan tasa halin nisa wani lokacin bakinta baida sayi,shiyasa tun amota sai data kwatse ta,Dan ta girme ma nisa da shekara daya kuma tafita wayau ita nisa surutu ne dai bai wani sha mata kai ba kamar sumy d'in. 

Gabanta ne yafad'i da jin tambayar da sarki Ali yayi mata in ina tafara Alamar rashin gaskiya sai kuma ta donar da kanta kasa,tayi danasanin cewa nisa gurin yaya mahir zata karbi sako dama cemata tayi suje sugaida Unni da duk haka bata faru ba,Kwadayin ganin mahir din take shiyasa tace sako zata  karba  awajensa,saboda yakwana biyu baije gurin Ummi ba saboda schl data rikesa.

Shiko mahir duk da yana kusa kuma yana jin komai dake wakana bai nuna ko a fuskarsa ba Alamar dasunan shi azancen..

'''''''ganin taki basa amsa,sai ya juya akalar tambayar sa ga mahir shiru mahir yayi duk da yaji tambayar da mahaifinsa yamasa "wane sako ne halan zaka bata"itace tambayar da yamasa,da gayya sarki Ali ya furta masa tambayar,kara furta masa yayi  cikin raha kodai sakon sirri ne yana d'an kallon sumy dake gefensa,Ai dasauri ta mik'e cikin jin kunya tayi hanyar Babban falo,Dariya sarki Ali yayi irin tasu ta manya yana girgiza kansa.

Shiko mahir tunjin furucin mahaifinsa na karshe ya sunkuyar da kansa yana mai turar labb'ansa yana furta " nifa Abba bawani sakon sirri bane kawai dama yaya Aj ne yace zaiyi magana da ita ne"

"Touh itakuma wayar Umminku fa,ko bata da amfani ne " inji sarki Ali,bakinsa yakara turowa jin k'aryar tasa bata hauva,Amma akarfin hali irin nasa sai ya furta Abbah inaga ta lalace ne,Murmushi Unni tayi kawai ita da sarki Ali suna girgiza kansu ganin soyayyar ta yaran zamani.

Ahankali Unni ta furta tashi kaje Babana kasha magani  ka kwanta tunda kaki cin abinci,Hararar Nisa Yayi dake jinhgine da kafad'ar mahaifinsu tana dariya kasa kasa na muguntar da tayiwa Sumy.

Ahankali mahir ya furta " Unni kinganta koh,wallahi yarinyar chan bata jin magana duk Abba da yaya Dr A suka sakanta ta "murmushi Unni tayi tana mai fad'in kyaleta kaji ai kaima unni ta sakantaka koh,Murmushi sarki Ali yayi ganin ydda zuri'ar tashi suke  cikin farinciki yana  jin ina ma Akwai Ammar dinsa akusa.MganarUnni ce data  furta wa mahir ai kai Autan Unni Ne,ta tsayar masa da maganar zucinsa..

Autan Unni din da Unni ta furta ne yasanya yuhanis ta taso da sauri tana ita wallahi bata yadda itace autar Unni har Da Ummi ma tana maganar tana matso hawayen shwagwaba,tana mai zaunawa a d'ayan gefen Unni Sarki Ali murmushi yakarayi yana furta kyaleshi maji dadi na kinji ai ni ke kadaice AUtanah bada yaya dr ba bada yaya   mahir ba,kivar Unni chan danata tarkacen kidawo nankinji yakai karshen maganr cikin wani yanayi dalilin saka sunan Dr Ammar,sbd haka suke kiransa yaya dr,Ita kanta Unni wani yanayi tashiga mai dadi jin karo nabiyu yakara sanya nur d'inta cikin zancen sa.

Nisa kuwa da sauri takoma inda Abban tana dariya tare furta yawwa Abbana ni kadai bada yaya rigammenme ba,ganin mahir na kokarin yimata  rankwashi akai jin takirasa rigamamme.

Kyafci mahir yayi yana mai mikewa tsaye sallama yayi musu,sannan yayi ma Nisa Alamar zamu had'u,yayi fucewarsa yana murmushi.

A b'angaren sumy kuwa bayan ficewarta  daga dakin sai tayi zamanta afalon jin zaman  y isheta kuma tana jin nauyin  komawa ciki  ganin tabada kanta,dan  taji kunya sosaiii,sai tayi ficewarta daga sashen fitar ta kenan ta hango motarsu Abdallah da yusuf tashigo Jikokin fulani,Abdallah d'an gurun yaya mustapha shikuma yusuf d'an wurin malan,Yayyen su Unni.

A hankali suke firarsu ta yan uwa shida sumy bayan gama parkng motar A chan achan Babban parking space dake a fadar yusuf ya  wuce nasu sashen bayan gaisawa da sumy,shiko Abdallah yatsaya domin su gaisa kwana biyu basu had'u ba...


A bangaren Mahir kuwa bayan fitowarsa daga dakin yaduba falo baiga sumy sai yafito gaba d'aya cikin sashen ckin mamakin ina ta tafi kuma,a compound din sashen nasu yahango su ita Abdallah Akan wasu chairs suanat firarsu gwanin burgewa kamar wasu masoya,wani kololon bakin cikin ciki ne ya ziyarci mahir daganin Babban Abokin nasa da sumy zaune sunata raharsu,takawa yayi zuwa inda suke yayi,ya yyi tsaye,Abdallah ne yafara lura da tsayuwarsa Abayan sumy dake ta maganarta hankali kwance,lura da yanayin fusakarsa ne yasanya Abdallah tambayar bros lafiya dai koh?sai alokacin sumy ta gansa dasauri ta mike ta fara kame kamen rashin gaskiya... cikin "sanyin muryarsa ya furta lafiya qlau".Unni ce tace inkira mata wannan yarinyar,ohk Abdallah yafurta yana fadin" big girl sai anjima ko dan nasan dakyar mukara had'uwa kila.. inkoma gida kigayar mun da Ummi  da husnat"toh tace tana mai rab'a mahir tawuce cikin gidan..

Abdallah ne yakara furta ma mahir yakannaka bros?kasha magani?eh kawai mahir ya furta wucewarsa cikin jin haushin Abdallah,bai tab'a jin haushin big girl din da Abdallah ke kiran sumy dashi ba sai yau,sauri sauru yacimmata Sumy da har tashiga falon..

Ke yadakatar da ita daga kokarin bude kofar second falon datake kokarin yi  A hankali ta juyo suka had'a ido dashi yana mai kafeta da dara daran idanunsa masu yanayi dana da Dr ammar,Saurin duk'arcda kanta ta tayi kasa ganin irin kallon dayake jifarta dashi,wanda bazata iya jurewa bah,muryarshi ce tadaki dodon kunnenta,yana furta "wane sako ne zaki karba hannu na"? rass gabanta yafadi nan tafara kame kame duk da bata furta komai ba,ganin yanayin da tashiga yasanyashi dauke kansa,yana kawar da wanchna zancen ta hanyar tambayar ta maganar me sukeyi da Abdallah?

niko nace mahir kamanta da yan uwata kai ne 😄


Kanta tayi saurin dagowa danjin tambayar da yayi mata ido suka kara had'awa dashi tayi saurin janye nata ganin uwar hararar da ya sakar mata,murmushi ne ya subuce mata wanda ganin irin hararar da yayi mata sai taga yakara yimata kyau,Amsa masa tayi A hankali "yaya mahir gaisawa ce mukayi sai kuma firar school din mu danake basa,"ke uwar bada labari koh"shiru tayi jin abunda abunda yafurta girgiza masa kanta kadai tayi tana kara sakin murmushi a fakaice,Bata san cewa yaganta ba,shima ana bangaren  murmushin gefen baki yasaki  yana mai furta "meye na murmushi"kai takara girgizawa tana kokarin bud'a bakin ta kenan taji tafi abayanta raff raff ....


Waye kuke tunani kenan ya musu kutse suna tsaka da shan love 😍?shin ko dai mahir ya fad'a ne?

Like,share and comment pls.

Idan kina bukatar daga farko zaki iya tuntuba ta....
 https://chat.whatsapp.com/IjZCle5c6V3BGRlnZ0yKim
💫A MAFARKI NASANTA💫
     In my dream I know her
                        By 
     Pha'eezah Almustapha 
        Daga Alkalamin✍️✍️
           💫Fa'eeh BG💫

Dedicated to my lovely sis lailat Almustapha Murai💔

*Mun kusa gama free pages in sha Allah,Da mungama book one📖,Episode one kenan za,a fara payment,na episode two*!!!✌️✌️💥💥
*masu son a tallata musu hajarsu  should contact me via* 
*call +2348069059746*
*chat +2348066995473*

------------------------------------------------------------------
 --------------------------------------------------------------------
*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCITION📚🖊️
   
               💫P.E.W.A💫

Home of perfect essential writer's together we stand🤝

         ESSENTIAL WRITER'S📚🖊

Pen🖊️*is migthier than the sword *🗡️

EPISODE1️⃣
FREE PAGE2️⃣8️⃣


TYPING📲📲📲

Duk da bata juyo ba tasan aikin waye,Nisa ce ke sakin karamar dariyarta tana tare da tafa hannayen ta  a hankali bayan isowarta kusa da sumy ta furta acikin kunnenta "me kika gayawa yaya mahir naga yana sakin murmushi"


Aiko da jin maganar ta Nisa sumy ta kai mata d'an karamin dundu abayanta,da sauri ta Nisa ta juya dagudu bayan jin dundun da takai mata tana furta sai nagayawa Unni da Abba soyayya kukeyi,ai kafin takai ga bude kofar Second falon na Unni har mahir ya chafko hannunta ido ya raina fata Nisa A hannun mahir dan tasan bawai wani raga mata yakeyi ba take ta raina kanta hawayen karya tafara matsowa tana bashi hakuri tun kan ya kai ga hukunta ta ta.


Kansa kawai ya girgiza yana mai furta "mai  kikace zaki fadawa su Unni ne "?
Shiru tayi sai dai faman girgiza kanta kawai takeyi tana cigaba da kakalo hawaye,warning ya buga mata akan kar ta yadda tasanarwa da kowa tagansa tsaye da sumy,Sannan yasake hannunta yana furta stubborn girl.

,,,,,,sai da ta bud'a kofar shiga falon sannna ta juyo ta murgud'a masa baki.

Itakam sumy dariyar ta kawai takeyi kasa kasa.

Bayan wucewar Nisa ya kalli sumy kallo irin na zamu had'u,ya juya ya yayi hanyar nashi dakin wanda yake chan jere shidasu dr Ammar  A wani lungu da yashiga ta falon unnin.

Bayan wucewarsa itama sumy ta taka afalon na unni da tunani barkatai aranta.

A bangaren Abdallah kuwa yanayin yadda mahir ya amsa masa ne bai masa ba,Amma sai bai kawo komai aransa ba,face tunanin kila ciwon kannasa ne ya sanya sa zama haka 

*BUG*
 Abangaren su halee kuwa wallahi mijin ki zaiyi faman da khady ta furta ne,yasanya Halee data debo yar madaidiciyar loma a spoon tagaza kai ta kan d'an karamin bakinta wanda yake d'auke da pink lips,dasuke shekin maik'o dan maganar ta Khady ita dariya tabata,sai da takai lomar abakinta tana tauna a hankaali sannan cikin sanyin muryar da zame maata jiki ta furta"meya sa kikace haka"?

Cikin zakuwa  khady tafara jero mata halayenta wayenda suka zame mata jiki ko ince wayenda aka halicceta da su ,"kinga na farko ni ban masan yadda zaiyi dake ba mutun kullum ciki hijab tafurta cikin  dariya ni na namatsu in ganki gidan mijinki inga yadda zaki yi"
A bangaren Halee murmushi kadai ke wanzuwa akan kyakkyawar fuskarta tana cigaba da cin abincnta hankali kwance,khady ce ta cigaba da maganar ta"mutun inkayi magana bai baka amsa ina lafiya" wannan karon Halee  sai da tadara harda rike ciki,wanda sai da fararen hakoranta suka bayyana, itama khady dariyar takeyi ganin yar uwarta na farin ciki.

A hankali ta furta  bayan gama dariyarta "to me kike so ince ne yar karamar harara khady ta watsa mata chan takara furtawa "bari kiji mama dije cikin d'an murmushi wanda ya fito da side dimple dinta da ya lob'a gwanin burgewa ta ce ni bari kiji koda nayi Aure babu wanda ya isa ya hana ni sanya hijab dina,sai maganar dake cinki ta biyu dan naga kina kalllon filet dina,kinfi kowa sanin ban cika son cin abinci mai nauyi ba saboda bana son inyi kiba inkoma mama dije tulluka gaki nan kina ta zama lukutarki takai karshen maganar cikin sakin karamar dariya,itama khady dariyar tayi tana furta  nice yar lukuta,zan rama ,ai gashi nan ke kuma kina ta zama iccen kara mutun kamar iska yakwashesa inbanda wannann abun da wannana abun da bakomai cikin ki tana nuna breast dinta da hips dariya dukkan su suka kwashe da ita musamman Halee da maganar ta bata dariya...

Bayan gama cin abincinsu ne, Khady tafara yiwa Halee  kalabar dogon gashinta mai santsi da dubara,ana take shaida mata....

Ai Baba Asabe ta fita tun karfe takwas tayi wurin zaman makoki mamaar Babar Aminiyarta larai,sai maraice tace mata zata dawo.

*Niko nace kaga su Baba Asabe an zake dayawa sai kace masu wata hidima ta biki tun safe sai maraice,ko da yake yanzu haka nan akeyi musamman ingidan mutuwar akwai maiko Allah yasa mudace muyi kyakkyawan karshe.*

Hamdala Halee tayi A zuciyarta na farinciki jin wannnan labari na Khady  ganin yau zata wala,Tambayar khady tayi cikin yanayin farin ciki "to amma meyasa baki tada ni ba nayi ayyukka na"
"yau ni tace in yi Ayyukkan bake ba" khady tace mata hakan ne kawai.

Halee dai tasan  sarai karya khady ta fad'a mata dan tasan wacece baba Asabe,Tunano yadda sukayi da Bba Asabe tayi ajiya kan kawai ta dade ba kawo ko sawu  daya na ruwa ba domin harda marinta tayi wanda ita kuma jira ta tarar a bohol din....

Hawaye ne shar suka silalo mata a ido tayi saurin gogewa gudun kar khady ta gani,sai dai khady ta riga taganta kai kawai ta iya girgizawa tare da share nata hawayen daya zubo mata na tausayin yar uwarta.


........Mganar Baba Asabe ce ta fad'o mata arai kafin fitar ta zuwa gidan gaisuwa Halimatu!Halimatu shine sunan da BAba Asabe take ta kwad'a kira,wanda sautin neya farkar da Khady jin Bba Asabe na doso d'akin nasu ta mike da sauri bayan bude idanun nata kazazam ta yi saurin lullub'awa Halee bed sheet   dake tsakanin filonta da na Haee Sannan ta isa bakin kofar da sauri alokacin itama Baba asabe takawo bakin kofar....

Gaidata ta Amsa mata cikin sakin fuska 
Sannnan ta furta" ina yar iskar yarinyar nan take bataji ina kiran sunan ta bane ko wani sabon iskan ci ne ta tsiro dashi ehh"?takai karshen maganar tana kokarin yaye labulen dakin sai dai Khady ta hanata ta hanyar kara kare bakin kofar tana ta faman susar kai na rashin gaskiya Baba asabe kuwa kafeta da idanu kawai tayi ganin wani sabon iskancin gun yarta furta wa  Baba Asabe tayi innata tashiga toilet ne,Uhm meye na kare mun kofa eh sannan uban mi takeyi acikin toilet din tabarni inata turar labb'a ga yar iska,Ganin tana neman tada HAlee da hayaniyar ta yasanya ta marairaicewa tana furta  innata kaina ke ciwo gashi kinata d'aga mun murya aka.

Sassauta murya Baba asabe tayi tana furta inta fito kigaya mata tadaura miki abun karin kumallo da ruwan zafi  sannan ta gyara mini d'akina na Alhaji nasan basai nace ba ashare agoge ko ina ,harda toilet,sannan intagama acika kwannan gidann nan kuma akaimani ruwa makewayi na,saura kuma ki sanya mata hannu tunda nasaka ki tana gama maganar ta fuuu ta fice daga gidan har ta kusa ficewa khady ta furta inna ta inazaki tunda safen nan,gidan larai zani mahaifiyarta tsohuwa ta cika dazu anfada amasallaci,Ayyah khady ta furta" Allah yajikanta da rahama" Amin Ta furta tasa kai ta fice gidan.

KAI BABA ASABE AJI TSORON ALLAH WANNAN SONKAI YAYI YAWA.

Bayan fitar ta ne khady tayi dukanin ayyukan da Baba asabe yar sonkai ta lissafawa Halee domin tasamu koda hutu yaune kafun dawowar Baba
 Adee.

 
Bayan  Gama wannan tunanin sai ta fara jan Halee da fira duk da ba duka take amsawa ba domin har yanzu akwai sauran tunanin mafarkin nan aranta dakuma zaginta da Baba asabe ke yi.

*GUSAU*
A Bangaren sarki Ali kuwa bayan ficewar Nisa A dakin ne ya furtawa Unni "ya "yanki fa kamar akwai wani al amari atattare dasu ni gashi tuni har nafarawa ba indiyen yaronki kame,sai kuma naci karo da wannan sabon al amari yakai karshen maganr yana murmushi,murmushi Unni tasaki itama tana furta to dad'a yaran yanzu ba,a gane cikin su ta yuyu akwai wani abun atsakanin su amma suna boye wa ne duk da nasan Baaba na baida nuk'u nuk'u  a irin wannan maganar kamar  Ammar wanda har yanzu ko budurwa baida ita gasu girma nata zuwar musu gaskiya insuka dawo ka nema musu mata ko cikin ya yan kawayenka ne na matsu inga jikokinmu takai karshen maganar cikin dan murmushi najinin larabawa da fulanida ke yawo ajikinta,shikansa sarki Ali murmushi yayi yana furta gaskiya kam dole in nemo musu mata tunda har gimbiya sarautar mata tafara maganar jikoki agabana yakai karshen maganar yana leken fuskar Unni data sunnar kasa na kunya.

Wallahi soyayyar tsofaffin nan na burgeni...😄

Sai da taga yajanye daga kallon ta dayake yi sannan tacigaba da magana,maganar  Ammaar mu kyaleta kawai Adili kabar ta bamusan Alkhairin da ke shirin shiga atsakaninsu ba wanda Allah ne kadai yabar wa kansa sani.

Hakane sarki Ali ya furta sannan yakara furtawa su mutanen india mubarsu sudawo muga inbasu fitar ba sai anema musu, shi yarima inbanda kaddara ai dayanzu da matar shi ahannu Allah ya jikanki norah keda mahaifanki,Ameeen suka amsa su duka cikin wani yanayi shikuma Al amin Auta ta zan bashi inyanaso..Yakai karshen maganar yana murmushi,itama Unni murmushin kadai tayi tana furta Allah yatabbatar da Alkhairi,Ameen sarki Ali ya Amsa.

yana mai Mikewa tsaye rawaninsa yanad'a wanda da taimakon Unni yadaurasa sannan ya sanya alkyabbarsa wata colour maroon mai stone da wata zaiba abun sai wanda yagani.

Shigowar Nisa da minti kusan Uku sai ga Sumy tashigo,A hankali sarki dake gyaran Alkyabbarsa yabfurta y"a yan ummi nizan koma fada,yaushe zaku wuce ne,cikin sauri Nisa ta Amsa da Abban Yanzu tana zunburarar baki dan duk gidan ya gundureta tunda mahir yayi mata rankwashi akai,


Murmushi kawai Unni tayi tana fadin har angaji damu kenan?kai ta girgizawa unni tana mai kara turo d'an karamin bakinta gaba.

Sarki Ali kuwa yar dariyah yayi yana furta waya tab'a mun Auta nah yana murmush,ai kamar jiran tambayar tasa takeyi sai ta fashe masa da kuka,jawota yayi yana lallashi yana kara tambayar ta meya faru?.


In sha Allah ayanzu har weekend zaku rika samun update domin namatsu mu gama book one.

DAGA ALKALAMIN✍️
💫FA'EEH BG💫

Pls like,share and
 comment
