⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ *BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIR* *GABATARWA:•* _Yabo da godiya da'iman wa abbadan na Allah ne. Salati da sallama su ne na fiyayyen halitta, shugaban annabawa kuma jagoran manzanni Annabi Muhammad, da iyalansa da sahabbansa baki daya._ *Shafin farko sadaukarwa ne ga kungiya mai albarka da marubutan cikinta, BRILLIANT WRITER'S ASSOCIATION Allah ya kara hadin kai.* *Bazan manta da ku ba aminan albarka ina alfahari daku saina tunaku ko ina a bakin kura* 🐆 *HALIMATU SADIYYA* _{{ My Leema }}_ *HABIBA IDRIS* _{{ Hubbie }}_ *HAUWA'U USMAN* _{{ Smasher }}_ *MAIMUNA O . G* _Gaba daya littafin nan sadaukar ne gareku,_ *ASMA'U ZAYYAN* _{{Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 1 ^^Shekaruna goma sha bakwai cas a duniya. Babana yana da mata hudu da "ya "ya hamsin da bakwai.^^ Mahaifina ya kasance dan auri saki ne, bakin abinda kunne na yaji mahaifina ya auri mata ashirin da takwas. Babana ya kasance talaka ne baya da wata sana'a wadda ta wuce "yan bige bige, ya gwanance wurin iya karya sannan kuma babu abinda kware dashi sai cin bashi......... Talaka ne amma baya saka sutura irin tasu, idan kika gansa zaki rantse da Allah yana iya kyautar naira miliyan biyar, yasan dadin kudi sosai amma a sutura baya tausawa naira. ^^°Baya da gidan zama haka kuma baya da fili ko taki daya, munyi zama a anguwanni da dama sosai wanda duk anguwar da muka sauka suna mana lakabi da gidan inna ratata, ko kuma suce gidan yawa... Baya da aiki sai shaye shaye sannan kuma duk gidajen cacar dake garin katsina babu inda ba'asan shi ba, ya saka kansa caca wanda ake kira da nigerful, caca ce wacce take cinye tattalin arziki kuma ba kananan talakawa keyinta ba sai masu kudin gaske saboda idan har za'a buga wasan cacar mahaukatan kudine ake zubawa. Baya bayar da abinci haka kuma babu abinda ya damesa da rashin lafiyar "ya "yansa ko matansa, idan dai caca tayi masa dadi zai siyo kwanon shinkafa daya da kuma rabin doya, Da safe idan zai fita zai bayar da kudin kalaci ko wane daki naira talatin babu wani abinda ya damesa da yawanku. {}{{{}}} Wata rana can wurin wasan caccarsa aka cisa, amma baya da kudin da zai biya daga cikin abinda aka saka masa, dan haka suka cire masa sutura, tun daga inda ya buga wasan har zuwa gidanmu daga shi sai gajeran wando haka ya ratso mutane saboda tsabar shi tantirine har ya iso gida. Babu ruwansa da tarbiyar dan sa ko yar sa, shi yasa muka mayar da gidanmu kamar gidan karuwai, domin dai kowa abinda takeso shi takeyi dan babanmu yace sana'a itace tafi cancanta ga duk diyar daya haifa, ya daina biyan kudin haya yace mu zamu rika biya tunda kowa ya kawo karfi, dan haka duk yayuna suka tashi dan neman na kansu kowa ya kama sana'a amma banda ni, Abinda yasa kuwa shine, lura da irin kyawun da Allah yayi min, karkuyi tunanin kyawu na wasa ko ku lakaba abin da shirme ni nake gaya muku haka, bawai a gidanmu ba gaba daya zuri'armu babu yarinya mai kyau da daukar hankali kamar nawa.... Ina da kyau fiye da tunanin mai tunani, ina da diri daidai irin wanda maza ke so, ina da babban kugu sannan kuma Allah ya bani baiwar iya murzasa. Haka kuma ina da cikar kirji ina da manya idanuwa sannan ina da fari irin na fulanin asali, gaba daya zuri'armu babu mai haske na, idan na shigo taro mata sun gama wali haka kuma babu macen da zata kara tasiri harsai na bar wurin. Ni "yar gayu ce, na iya wanka kuma na iya shafa turare gaba daya bani da tsara idan na ziyarci wuri kamshina zaiyi ta kasancewa a wurin, haka kuma idan na barsa turarena zai dade bai daina tasiri ba, sannan duk gidanmu babu mai ilimin addini na wanda na samesa ta dalilin mahaifiyata saboda nayi sauka kuma bakin gwargwado nasan hadissai amma gaba daya zuri'armu babu mai barna irin tawa, ga sani ga barna dan duk yanda nake dakai a danginmu idan har na kwallafawa raina saina bata ka tou fa lallai saina bata maka rayuwa. Ku kasance dani a cikin littafin *KWARATA* domin jin wannan wane irin ubane ita kuma wace irin diya ce ? Kuma a cikin ita da uban waye yafi tantiranci ? Domin dai ni sana'ar da na zabawa kaina itace *KARUWANCI* danni a gani na itace sana'ar da tafi saurin kawo kudi. Babana mahaifi shine mutum na farko daya fara budemin lasisin karuwanci, domin dai a wurin wasan cacarsa yayi kyauta da budurcina, wannan dalili yasa na zabi sana'ar karuwanci, shine ya fara ni kuma naci gaba da kasancewa da wasan domin dai masu iya magana sunce so da yawa kana koyawa mutum abu amma saiya fika kwarewa. Ni babban kamfani ce kamar yanda ake sakawa a jikin kayan masarufi ace ingrediants to nima ina da nawa ingrediants in, kamar yanda company yake sarrafa abubuwa to nima company ce mai zaman kaina. Wannan labari a kiyayi juyashi ta ko wace siga domin yin hakan babban kuskure ne , ba kagoshi nayi ba a haka ta fadamin shi domin ina so ya zama izina ga matan aure, {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} Baba da Allah ka bamu naira goma zamu cika mu siyo magi, Ba tare daya kalleta ba yace me zakuyi da magi ? Cikin in ina tace dama kanzo ne zamu kwada, Naira biyar ya fiddo daga cikin aljihunsa, ya mika mata tare da cewa anshi idan kin samu kudin magin ki cika ki siyomin sigari...... Mahaifiyar ta dake tsaye tana daka kulin da za dasuci kwadon tace haba mai gida idan tana da kudin zata tambaye ka ? Itama bai kalleta ba yace wannan matsalarku ce keda ita, keni yi sauri ki kawomin sigarita jiranki nake ya fada tare da shashantar da maganar matar sa. Fa'iza mahaifiyarta ta kirata tare da cewa ina zaki samo kudin ? Bai bari Fa'izar ta bada amsa ba yace samarinta zasu bata ? Ke kike ganin bata da kudi duk yaran nan da kike kallo sun fiki kudi , ke ki hadomin da lemu mai sanyi kafin mai samomin abincin da zanci ta shigo. Fa'iza na kokarin fita daga gidan sukaci karo da Farida a bakin kofa, da yake gidan baya da zaure wanda ke wucewa ta waje ma zai iya hango na cikin gida, gidan kuma babu kaure sai labulen buhu da aka saka a jikin kofar, Babu sahihiyar katanga sai fasashshin buloluwa da aka jera, wanda ko yaro karami ya wuce zai hango na zaune. Fa'iza ganin Farida yasa ta tsaya tare da cewa, Farida da Allah ko kina da kudi ki rantamin na siyowa Baba sigari da lemu, anjima idan nayi awara zan baki, babu sauran kudi a hannuna duk na kasosu kasuwa canjin daya rage kuma nakai zubin adashe kinga lokacin biyan kudin haya ya kusa. Dan murmusawa Farida tayi tare da cewa ai tunda kika ganshi can ya mimmike kamar gawar sababi yau bashi da ko sisi, dan haka ma wallahi bazan shiga gidan ba komawa zanyi. Tun kafin Farida ta rufe bakinta ya fara kwarara mata kira amma tayi kunnen uwar shaggu dashi ta fice abunta. Rungume na fito da magena sanye cikin kayan islamiyata, nasha nikaf dina kayana sun dauki guga sai zabgaga kamshina nake da turarena dana siya na naira hamsin wurin masu siyar da turaren dure. Da sauri Baba ya tashi zaune tare da cewa Mamana barka da fitowa ? Murmushi nayi tare da cewa yawwa Babana barka da hutawa, Yawwa Mamana za'a tafi neman ilimin ? Eh Baba na fada a takaice, mikewa yayi tare da cewa muje in rakaki, wannan shine dabi'ar mahaifina duk inda zan tafi indai yana gida tou fa lallai shine zaiyi rakiya, A kofar gida muka hadu da Fa'iza sigarin ya ansa tare da cewa ki ajiye min lemun in dawo, shigewa tayi gida tare da cewa tom. A tafiye muke yana zukar sigarinsa hankali kwance, Baba wai har yanzu baka samu kudin da zaka siyamin keken ba ? Na tambayeshi, magen hannuna ya ansa tare da cewa machine zan siya miki uwa ta gari. Murmushin farin ciki nayi sannan nace Allah ya bada sa'a Babana , da amin ya ansa tare damin fatan alkairi dan mun iso bakin islamiya, magena na ansa na shige shi kuma yayi gaba. Yau inacikin farin ciki, domin dai idan har Babana yacemin zaimin abu tou fa ko zai mutu sai yayimin, yana min san da duk duniya bayayi wa kowa irinshi, yana kaunata fiye da yanda yake san kanshi, yana so ya ganni a cikin farin ciki saboda ina da sunan mahaifiyarsa. Yau ban wani yi karatu ba, hankalina ya tafi makarantar boko, na kagara gari ya waye dan injewa kawaye na da labari mai dadi zanyi sabon machine, nidai makarantar bokon haka nan nake zuwa dan ba abinda nake ganewa kaina fanko ne , a islamiya kadai Allah ya dafamin nake ganewa, amma a boko bana gane komai. Haka nan nake zuwa na dawo, Koda na dawo gida na kasa boye farin cikina, amma babu damar na fada, uban da ya kasa biyan kudin haya taya zan fada zai siyamin machine ? Dan haka naja bakina nayi shiru, saboda nasan idan suka ganni da machine in zasuyi tunanin kanin Mamana ne ya siya domin shine yake dauke da hidimata. Ina cire kayan islamiya ta na matsawa Inna sai ta bani kudi na siyowa magena kifi, bazan bayar ba shine amsar data bani , tare da hadamin da cewa itama kanta gari taci , saboda haka bataci kifi ba babu wanda zata siyama kifi. Gaskiya Inna bazan iya ba "yar madara gari taci ba, nice sheda saboda kin hana kanki kin cida magen banza, inna ta bani amsa, Tana fadar haka ta shige daki, na dade zaune a wurin ban samu mafita ba dan duk wanda ke gidanmu haushina yakeji kamar ya sakani wuta wannan dalilin yasa bana shiga sabgar kowa, Saida na gaji da zama na tashi a wurin ganin ban samu mafita ba, daki naje na kwantar da "yar jinjirar mage na nabar gidan dan samo mata abinda zataci, gidane babu kayan dadi daga gari sai kanzo inama amfanin talauci, shi kuma Baba ko tsoron Allah bayayi yazo gaban kowa yaci kaza dan zalinci, Amma duk wannan masifar Maman Fa'iza hada wani ciki ina tausayin dan nan da za'a haifa domin dai zai shigo rayuwar bala'e dama ya sani yayi zamansa baizo ba. Haka nayi ta galbaro a cikin anguwa babu tsiyar dana samo, dole na hakura na dawo gida dan lokacin sallar magrib yayi, Har bayan sallar isha'e Baba bai dawo gida ba, tunda naga ya wuce lokacin dawowarsa na sanyawa zuciyata salama tare da ba "yar madara hakuri, tunda ko mun tsaya jiransa bige zai dawo nasan yana can ya shawu iya shawuwa, mata hudu a gida amma yana neman matan waje. Tirrr da wannan hali. Tunani barkatai a zuciyata, ciki kuwa harda tunanin yanda zamu wayi gari ba tare da bango ya fado mana ba, dan gaba daya gidan nan ya rube ga wani irin hadari sai bakin rai yake, lallai wannan ruwan yau idan ya kwace gaskiya akwai matsala. Allah ka tsaremu da rayuwar talauci, rufe idona nayi domin inyi bacci addu'a nayi a fili cewa ya Allah ka tsare bayinka daga mutuwar katanga, kasa in kasance rayayya, in wayi gari cikin farin ciki, Allah ka shirya Babana ya daina abunda yakeyi, Inna ta ansamin da amin, tare da cewa Allah ya tsare gaba daya gidan, ban mata magana ba dan haushinta nakeji ta hanani kudin da zan siyowa mage na kifi, wani busashshen garinta can ta ajiyemin kuma banci ba, nasan idan naje makaranta gobe Amisty zata kawo mana shayi da biredi daga gidansu, shi yasa kafin kekena ya lalace nake saka "yar madara cikin kwandon gaban keken mu tafi tare itama ta maida miyanta. Da tunanin shayin gidansu Amisty nayi bacci, kuma dashi na tashi, tunda na farka naji yanayin garin da sanyi nasan jiya an kwana kwarara ruwa, dan haka tun kafin na sauko daga saman katifa nace Inna halan kin tara ruwan sama ? Na tara, ai jiya banyi bacci ba saida na tabbatar na cika komai nawa da ruwa, cikin damuwa na kara jan yagaggen zanin da nake rufa dashi tare da cewa wallahi bana san wanka da ruwan sama sai jikinka yayi ta wani sulbi kamar ka kama maciji, Banza tayi dani bata sake cemin komai ba, tsoki nayi tare da tashi ina mai mita cewa saidai kawai inyi sallah amma wallahi banyi wanka da ruwan sama, tsakar gida na fito rike da buta, ina maijin kyankyamin shiga bayinmu, Danni tunin duniya nayi sallama dayin fitsari daga tsugune, ko zanyi bayan gida makota nake shiga, wanka kuma dama tsakar gida nake wanke jikina baya da cikina kawai nake wanke wa a cikin bayin, ina watsa ma jikina ruwa tsikar jikina tana tashi. Dan gajeran tsoki nayi tare da daga labilen bayin na shiga, fitsari nayi na fito, a tsakar gida na wanke cinyoyina, nayi alwallah na dawo daki. Tun ina sallah Babana yake kirana tare da cewa uwar masu gida kiyi sauri mun makara naga har 7:30am, bana so Baba yana bina makarantar boko saboda duk kawata daya gani sai ya bita gidansu ni wannan abun yanamin ciwo. Tsaye na ganshi a kofar dakin mu yana daura agogo sai zuba kamshi yake yasha farar shadda sai daukar ido yake, murmushi nayi a zuciyata nace Baba kenan ko ba'aba ciki ba aba kaya, Katsemin zance zuci yayi da cewa maida hankali Mama mu tafi, mikewa nayi ba tare da nayi magana ba naci gaba da shiri, a gaggauce na shirya, tare da shafa "yar madara nace zan rago miki, Babana ya rikemin jakar makaranta muka fito daga gida....... _Gaba daya kaine sile, dan iska domin ni kai zan kira da kwarto, kaine silar rushewar rayuwata_ Cikin farin ciki muka fito daga gida, ina fadawa Babana yabi sannu karya bata jikinsa kasancewar ruwan daya kwanta saman kasa, Cikin jin dadi muke tafe muna fira, har mun kusa fita bakin titi ya sheko da gudu tuki na rainin hankali, tuki na gadara, tuki na wulakanci da rashin arziki, tukun da basa kaucewa mutane saidai mutane su kwauce masa, duk lokacin da zai shigo anguwar nan haka yake shigowa idan ya taka mutum ya taka banza, ko dabbobi gareka saidai ka daure abunka amma badai maganar ka sakesu ba. Tunda na hango motar nake cewa Baba dawo ta nan, amma kafin Baba ya hayo inda nake tuni yabi takan ruwan ya wuce shaddar baba ta koma brown, iya wuya raina ya baci kuma nayi alkawari ko zai kasheni tunda har ya tabomin Babana sai naci uwarshi a safiyar nan. Da gudu nabi motar ina watse hannuwa na yanda ake zagi dakkuwa, ina zaginsa, shima Baba biyoni yayi da gudu cikin tashin hankali, yana Mamana dawo, wanda yayi nisa bayajin kira, a kofar gidanshi da yake kiwon dokunan shi anan Baba ya sameni ya rikeni, shi kuma ya fito daga motar da bulala dorina irin wacce ake dukan dokuna da ita. Zagin dana taho inayi shi ya jawo hankalin mutane yasa duk mutane suka fito daga gidajen su, wanda ke waje suka iso wurin da muke dan ganin kwam, Rikeni sosai Babana yayi tare da rufemin baki saboda yasan ban iya zuciya ba, shima abokansa da sauri suka rikeshi tare da cewa *Dikko* karka daketa dan Allah yi hakuri, Babana kuma cewa yakeyi ranka ya dade kayi hakuri don Allah bata san kaine ba, Raina baci yayi ganin kamar mahaifina yana bawa yaron da haifa hakuri, dan haka na bambare hannun Babana daga bakina nace, nasan kaine kuma na zageka, ban kara maganar ba Babana ya wanka min mari. Tunda nake a duniya magana mai daci ko muni Baba baya fadamin ita, yana tattalin rayuwata yana kaunata amma yau saboda wani sakarai ni Babana ya daka, Ina cikin wannan bakin cikin Baba ya bashi hakuri da taimakon abokansa ya hakura suka ja banza suka shiga gidan da yake kiwon dokuna, A raina na dauka alkawari yanda Baba ya dakeni saboda Dikko saina rama dukana a wurinshi...... Hannuna Baba yaja muka taho yana bani hakurin marin da yayi min, wai yayi haka ne saboda Dikko kar yayimin wani abu, saida ya sakani napep sannan ya koma gida, Cikin bacin rai na tafi sch amma tabbas Dikko sai yaci kaniyarshi......... {{{}}} {{{}}} 30/07/2019 Meelat Musa ce 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 2 Duk sanyi sanyin da akeyi saboda ruwan da aka kwana kwararawa a daren jiya hade da wani irin iska mai dadi amma Baba zufa yake kamar an tsare mai jegon da a saman gadon kara...... Cikin tashin hankali ya fara cire kayanshi yana dorawa a saman katanga, sai bakinshi dake motsawa babu wanda yakejin abinda yake fada saidai lokaci bayan lokaci yakan goge zufar data bulbulo daga jikinsa.. Ganinshi cikin wannan yanayi ya dagawa kowa hankali, gashi ya fita da farar shadda amma ya dawo da shadda kamar miyan goro, Idan yana cikin yanayin fushi baya so kowa yayi masa magana haka kuma bayasan ganin kowa kusa dashi, mata da "ya "ya suka gane haka shi yasa babu mai shiga sabgarshi, idan yana cikin yanayin damuwa Sultana kadai ke zuwa wurinshi ta bashi hakuri kuma ya sauka saboda soyayyar dake tsakaninshi da ita, Har na isa makaranta tunanin yi hakurin da Babana ya bawa jakin dana manta sunanshi nakeyi, sunanshi ya bacemin kwata kwata na manta sunan da aka kirashi dashi, nidai Allah yayi min jakar kwalwa, saboda ko "yan gidanmu ba dukansu nasan sunansu ba, amma na alakanta abun da yawan da muke dashi, yayin da wasu suke ganin rainin hankali ne...... Ko a aji naso na bawa Amisty labari amma na manta sunan wanda zan fada mata, Amisty itace kadai abokiyata duk a ajinmu, abinda kuwa yasa na zabeta tana da kokari sosai kuma idan ana jarabawa tana bani satar amsa, Amisty irin yaran nan ne da idonsu ya waye tun suna cikin zanin jarintaka, bata da labari sai labarin maza, bata da aiki sai kallon B F, duk hotunan da zaka gani a cikin wayar Amisty hotunan tsiraici ne, walau nata walau na wasu, babu mai tarayya da ita saini kadai domin an dade da canfata cewar tana lesbian, nikam babu abinda ya dameni idan dai zata bani shayi nasha a tashi jarabawa ta bani satar amsa idan anyi rubutu nima tayimin a littafina shikenan banda wata damuwa. Lokacin dana shiga aji har malami ya shiga ya fita, ga rubutu nan a saman allo, bana gane sunan subject haka nan kawai na kalli allon nadan basar tare da cewa ashe malam harya fita. Da Eh kusan rabin ajin suka amsamin dan ina da masoya sosai, wasu saboda kyauna suke sona yayin da wasu kuma gashin kaina yake daukar musu hankali, okey shine abinda na fada kamar wata shegiyar baturiya dan itama okey din na dade ina koyonta a bakin Amisty dakel dai na samu ta zauna ram a cikin kaina, idan na fadi okey zakayi tunanin nasha turanci na koshi, amma babu abinda nake ganewa duk duniya sai sallolina biyar da Allah yasa na iyasu saboda nacin zuwa islamiya. Ina zuwa mazauni Amisty tace yau ina kika baro mana Baban namu ? Wata irin faduwar gaba naji dan nasan Babana shima ba karamin tantirin dan iska bane, kodai itama Amisty Baba ya zagaya ne ? Kinyi shiru, Amisty ta katsemin tunani na, maganata daukewa takeyi duk lokacin da ake tambayata abu, ina da nawar magana akan magana karama sai inja lokaci sosai, inayin in ina kadan wannan dalilin yasa ban cika yawan magana ba. Dan gajeren murmushi tayi tare da matsawa, zauna tacemin tare da maida hankalinta akan allo taci gaba da kwafar note. Zama nayi tare da cewa wane malami ne ya shigo ? Malama dai , wace malama ce ? Malamar English ! Me take koyawa na tambayi Amisty, turanci ta fadamin a takaice, murmushi nayi tare da cewa yarinya ai na gane dama dan inji idan zakiyi min karya. Kedai kika sani, ni ciro littafinki na rubuta miki idan kin gama rainin hankalin naki, Amisty ta fada........ Bude jakata nayi sawon wani lokaci na kasa gano littafin da Amisty tacemin, tun ina dubawa a cikin jaka har na fito da duka littafan banga littafin turanci ba, dan gajeran tsoki nayi tare da cewa Amisty inajin nabar littafin a gida gaskiya. Daukar littafin tayi domin shine a sama, ajiyar zuciya nayi dan nima ta gane wata jar wuya ce , nace da yake jiya nayi karatu na dauka na barshi a gida ne, tou kawai tacemin bata sake magana ba, Haka malamai mata da maza sukaci gaba da shigowa har aka tashi daga makaranta, a bakin get din makaranta na tsaya ina jiran isowar Babana , tabbas nasan zaizo duk inda yake naji yana kusa dani yana zuwa bada jimawa ba. Banfi minti 2 ba Babana ya iso cikin wata irin kafirar mota yanzu ma yasha wanka ya murza wata irin dakekiyar shadda, sai kasaita yakeyi, murmushin jin dadi nayi domin dai Babana ya kankaro min mutunci na idan yayo wanka saboda dan gayu ne na koyi a idon duniya..... Cikin farin ciki na isa jikin motar na bude gidan gaba na wani kame abuna, zugar kawayena ne sukayo kanshi suna gaishe shi kamar yanda suka saba idan yazo daukata, Dan murmusawa kawai yakeyi tare da karkacewa cikin izza ya jawo wasu irin "yan dubu dubu wanda shi kanshi baisan ko nawa bane , Amisty ya mikamawa tare da cewa ku saka kati. Yana basu bai jira godiyar da suke mishi ba yaja mota muka tafi......, ba'a hana alkairi amma inajin bakin cikin abinda yakeyi, yabar gida da yunwa yazo waje yana alkairi, gida bai koshi ba yakai ma na waje banda gori da zagin iyayenmu babu abinda akeyi a cikin anguwa cewa Babanmu yana tsaye akanmu amma duk mu tsinannin Allah ne mu , haka zaisa ayi ta shiga da buhun na, na shinkafa gero masara katin katin na madara sugar da komai na sarrafawa idon duniya sun gani haka zai biyo dare ya kwashe abinshi yaje ya siyar wannan rayuwar zalinci ce, kuma bai sani ba kanshi kawai yake yaudara, Kasa hakuri nayi nace gaskiya Baba ni kadaina zuwa daukoni makaranta daga yau, ba tare daya kalli inda nake ba yace miyasa Mamana ? Kawai banajin dadin abinda kake ne , me nakeyi wanda bai miki dadi ba ? Wannan kudin da kake bayarwa dama gida kabawa su Inna sukaci abinci gidan kowa yunwa ta kamashi babu mai wani sahihin abinda zaici maganar daya ce kullum daga gari sai kanzo. Dariya yayi sosai tare da cewa Mamana kenan, aisu wannan mutane basa godiyar Allah, kima daina biye musu dan kona basu kudin cefane makalewa sukeyi, duk wanda kika gani a cikinsu daga mai tumaki goma sai mai shanaye babu adadi, idan na basu kudi boyewa sukeyi su hana ku abinci, suna can sun sayi dabbobi sunkai kauyika an boye musu, idan kuma kina magana akan abinda akayi ma wani kuma wannan halin shi ake kiran da hassada idan kikaga anyi ma mutum alkairi koya samu wani abu kikaji bakin ciki a zuciyarki shima hassada ne, kuma ita hassada tana cinye kyawawan ayyuka ne kamar yanda wuta takecin karmami, kuma yawan surutu yana sa mutum ya zama sakarai , ki daina hassada kuma bakinki shiru akan fadar wasu maganganu akaina idan kinki ji kuwa jahannama tsaye ko kina san ki shiga wuta ne uwar masu gida ? A , a Babana, amma zan fadawa su Inna gaskiya su daina irin abinda sukeyi zalinci ne, abun tausayi Baba kaji yaran nan suyi ta kukan yunwa wallahi ni har tausayinsu nakeji, kyalesu Mamana kina iya fada musu gaskiya suji haushinki barsu da halinsu................Maganarsa ta kare ne a daidai lokacin da muka tsaya wata majalissa. Fita muje, fitowa mukayi daga cikin motar muka tunkari taron dandazon mazan, kallo daya zakayi musu kasan cikakkin "yan tasha ne ko wannensu ya koshi da iskanci, Gaishe su nayi tare da matsawa daga gefe na zauna, kai bata abincin nan taci mu wuce, Babana yayi maganar a daidai lokacin da yake zama, Mikomin abinci akayi a cikin ci ka yada, { take away } gyara zamana nayi tare da juyawa inda babu mutane naci gaba da aiki, daga nan bansan abinda yaci gaba da faruwa ba, saidai naji hayani tayi yawa sosai anata bawa Babana hakuri ana rirrikeshi. Cikin tsananin bacin rai yake cewa da Allah ku sakeni wallahi saina kwakwale mashi idanuwa tunda nayi rantsuwa saina makantashi duk cikar garin katsina babu wanda ya isa ya hanani aikata abinda nayi niyya, da sauri na tashi nayi wurin Babana ina bashi hakuri, Abokin fadan Babana yake cewa, yo kai "ya "yan wasu nawa ka batawa rayuwa, saini kawai dan na kalli diyarka nace babban lambu zaka nunamin rashin kunya, cewa nayi zan shiga ciki ? Yabawa fa kawai nayi.... Sai kawai hankali ya tashi ? Sanin kanka ne duk kasuwar data burgeni saina ci ta hanyar shiga inyi siyayya a cikinta, duk gidan giyar daya burgeni idan na shiga saina sha kwalba biyar karanci kenan idan banda kudi, haka kuma idan naga gidan karuwai zan shiga ne inyi ta ciyayyar abinda ya sawwaka ba tare dana gajiya ba, Ka sani nima nasan haka, tunda saina gama nake ma gwanjon mata, banyi maka shamaki da matana ba haka diyana, kenan yanzu idan nace ka bani aron Sultana mu bata dare haka zakazo bakin kofa kayi tamin babatu ? Da sauri Babana ya rufe idanuwan shi tare da kauda kanshi gefe guda, tunda ni bansan abinda ya assasa fitinar ba, tou miye b'ata dare ? Kila shaye shayen su suke nufi, Jinjina kai Babana yayi tare da cewa kaci sa'a Mamana tana kusa amma zan maida ita gida na dawo na nuna maka karyar barikanci, yana fadar haka yaja hannuna mukayi gaba, har muka iso gida baiyi min magana ba, saida ya tabbatar na shiga gida sannan ya koma, Da sallama na daga buhun kofar gidanmu na shiga, gaba daya gidan suna tsakar gida uwaye da yara, yaran mazansu da matansu sun gurfana gaban wani dakekin mutum bakikkirin da cikinshi kamar ace Allah saukeshi lafiya, ni a tunani na assembly ake musu saida naga Inna na tuna ba makaranta bace. Saida nazo daidai inda suke nayi musu sallama kamar yanda na saba, ina kokarin wuce yace ke zonan, ban kalleshi ba kuma banzo ba haka kuma ban tsaya ba naci gaba da tafiyata na kusa shiga dakinmu naji yace waccan yarinyar ta raina mutane wallahi da nayi niyar yin hakuri amma na fasa sai kun tashi kunbarmin gidana. Hayani ta kwace bakajin maganar wani duk maganar ta koma iri daya yi hakuri , Allah ya taimake ka Allah ya kara arziki ka taimaka dan Allah karka tashemu, kaji hauka akan wannan rubabben gidan suke wani hadashi da Allah yayi hakuri, Allah ma yasa ya tashemu nayi addu'a ta a bayyane, Zainab ce ta tashi taje wurinshi tana wani irin karye karye, sai kace karyar gidan karuwa taga maza, magana tayi mishi babu wanda yaji abinda tace, saidai suka fita da mutumin, ganin tafiyarshi yasa kowa ya tashi yaci gaba da sabgar gabanshi, Babana da Zainab bansan yanda suka kare da mutanen su ba, haka Dikko bansan inda yake ba, dan an dauki wani lokaci banji labarin yazo anguwanmu ba, Kwanaki da dama sun shude, rayuwa tana tafiya babu abinda yayi gaba sai ci baya ake samu, amma ni na samu ci gaba na rayuwa domin dai Babana ya siyamin sabon machine kamar yanda yayi alkawari, a cikin matanshi kuwa maman fa'iza ta samu karuwa ta aihuwa, yanzu mun zama mu hamsin da takwas cas a gidanmu, Zaune nake a kofar dakinmu ina yanke farce na, "yar kyakkyawar magena tana shan madara, Baba ne ya siyomin madarar da yawa nake bata danni yanzu na daina tausayin "yan gidanmu tunda na gane duk munafikai ne, Kuma Babana ina gani duk safiya yana basu kudi amma bansan ko nawa bane, Kadangare ne ya fado daga saman bango fef, yana ganin mage ya ruga, ita kuma daina shan madarar tayi tabi kadangaren da gudu, nima binta nayi ina kiran "yar madara' dan bana so tana cin kwarika, kadangare ya rugawa mage, ni kuma nabi magen haka muka fita a guje mu dukanmu muna gudu a tsakar santa.... Shima a guje ya shigo kamar yanda ya saba, ganin yanda mutane ke rike yaransu, masu tumaki na kamawa hakan ya tabbatar min dashi dinne ya sake dawowa, Nima kokarin kama "yar madara nakeyi, amma kafin in isa wurinta tuni dan iskan yabi ta kanta da mota ya wuce, jininta yayi tsartuwa a saman fuskata, yana wucewa na ruga na durkusa wurin magen, saida tayi miyau.......... Sannan ta daina motsi, wata irin ashariya na babba tare da kurma wani irin ihu dan naji bakin cikin takata da mota da akayi. Cikin kuka na nufi inda yake, dama ina jiran zuwan shi saboda marin da Babana yayimin ta dalilinshi, shima din jirana yakeyi saboda zagin da nayi mashi waccan ranar, kowa yana jiran kowa, Bayan yayi parking ya fito ya zauna saman bayan mota, yauma bulalace a hannunshi yana wasa da ita, sai wani cin cingom yake sai kace karuwa... Abokan da yazo dasu waccan ranar yauma sune ya dawo dasu, mutum biyu tsaye a gefen damarshi biyu a haggunshi daya kuma tsaye ta gabanshi ya dade da bakin glashi, Lafiyayen kato ne mai kirar "yan dambe, singileti ce a jikinshi sai wani maski maski yakeyi kamar anyi mishi wanka da mai, dan nesa dasu na tsaya tare da cewa a cikinku waye yake tuka motar nan ? Na nuna motar da hannuna, Nine nan, mai kirar "yan dambe ya bani amsa, sannan yaci gaba da cewa ko wani abu ya faru ne ? Saida na kalleshi sama da kasa sannan nace da Allah mi yasa ka takamin mage ? Nayi maganar cikin sanyin murya, bashi ne ba nine na taka ta, kema idan kika tsaya a hanya gobe haka zanbi ta kanki in wuce kinji ko an mata, duk shi Dikko yayi maganar. Mai kirar "yan dambe ya anshi maganar cewa, ubangida na yanajin dadi yayi da yaga yana wulakanta talaka irinki, yana farin ciki idan ya zauna daga nan muka fara watso kayanku daga cikin kangon can, da nayi niyar murde miki wuya ki mutu , mutuwa irin ta beraye a ranar da kika wa mai gida rashin kunya, abu daya yasa ban kasheki ba kasancewar ke ba kowa bace, Murmushi yayi tare da cewa ta hanya mafi sauki za'ayi miki hukunci, juya kisha kallo, juyawa nayi a hankali dan inga abinda yake so na gani, babu gidanmu tuni wurin ya koma fili, lokacin da na juyo babu su Dikko babu alamarsu dan tuni sun jima da tafiya daga wurin. Salati nayi tare da tunkarar inda "yan gidanmu suke tsaye cirko cirko domin babu abinda aka bari suka fitar dashi komai an danneshi cikin kasa, sai motaci dake ta kwashe kasar wurin, Ina zuwa kusa da Inna da zumar tambayarta abinda ya faru ta rufeni da duka tare da cewa miya hadaki da Dikko kin dauko mana fitina kin jawo mana masifa Allah kadai yasan karshen wannan masifar. Cacai cacai kowa hayani yakemin a saman kai babu damar a dakeni Babana yaba mace rasid'i, ke kuma diyar gida kimin magana kijawa uwarki masifa, dan haka abinda kawai suke cewa miya hadani da *DIKKO ?* ................ {{{}}} {{{}}} {{{}}} 31/07/2019 Kubi sannu ku kasance da wannan labari, Taku a kullum Meelat Musa 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 3 Saida na gama kallesu daya bayan daya sannan nayi murmushin takaici da gefen bakina, kallon inda gawar "yar madara take na kalla wani makoko yazo ya tsamin a makoshi wanda ko yawun zan hadiye sai naji kamar lumfashi na zai dauke. Dikko......................! Saida na jinjina sunan a zuciyata da kuma bakina, sannan na kalli dandazon taron ahalin gidanmu, nu na su nayi da dan yatsa manuni, sannan na dafa daidai kirjina da hannun haggu na , zanyi magana sai kuma maganar ta kasa fitowa dan bana iya magana a cikin yanayin bacin rai.. Wuri na samu na zauna ina ta sauke ajiyar zuciya, tsinuwa da zagi da Allah ya isa bansan iyakar adadin dozinan da suka saukemin ba, zagin ne dai kawai amma nasan bazan daku ba, Har yanzu babu wanda nayi ma magana kuma babu wanda na sake kallo, zama nayi na sauke kaina kasa, yayin da wasu suka gaji da tsayuwa suka durkusa wasu kuma suka bazama neman gida, dan su zasu nemo shi dan ko sun tsaya jiran Baba ko yazo bazaiyi wani abu ba, Bayan sun zauna ne sukaci gaba da tattauna maganar abinda Dikko yayi, ashe tun waccan ranar zagin da nayi masa ranar da zamu tafi makaranta tare da Babana bayan an bashi hakuri ashe baiyi hakuri ba. Da zai jira har na dawo daga makaranta ya takeni da mota ya wuce abinshi, tou bayan ya fito daga gidan da yake kiwon dokuna yaga Babana ya fito daga gidanmu, Shi Dikko mugune na gaskiya da gaskiya, duk duniya babu abinda ya raina yake kyankyami irin talaka, Dikko baya dariya haka kuma baya murmushi kullum fuskar nan tashi a hade take kamar hadarin tsakar dare, Bakya ganin dariyar shi kwata kwata, idan kuwa har Dikko yayi murmushi tou tabbas yaga cuta, idan kuma yayi dariya tou tabbas ku idan kuka ga abun sai kunyi kuka saboda tsabar tausayi. Danshi sai yaga mugunta yake dariya..... Bayan Babana ya wuce, Dikko ya kalli gidan ya sake masa kallo babu abinda baya gani na gidan daga nan waje inda yake tsaye, Kallon rainin hankali yayi ma gidan tare da bata fuska ya juyar da kai ya kalli daya daga cikin wanda suka zo tare sannan ya kalli agogon hannushi yace waye shi.... Ya nuna Babana da gidanmu... Bai tsaya yin magana ba ya bazama cikin anguwa, a cikin kankanin lokaci yaje ya samowa Dikko duk wasu bayanai daya kamata akanmu da rayuwarmu, Jinjina kai Dikko yayi bayan yaji komai tare da cewa karta mutu, amma barsu na jikatasu zata gane Dikko ba sa'ar ubanta bane daga wannan rana tsoron Dikko zai shiga zuciyarta maza a nemo min mai gidan daya basu hayar gidan, dan gajeren tsoki yayi tare da cewa talaka banza a banza, za'a nuna mata su kudi jigo ne masu nuna ishashshen iko. Daga wannan rana zata gane mai kudi ba'ayi masa hawan kasa, Cikin anguwa ya sake komawa dan binciken mai gidan da muke haya, aka fada musu anguwar da yake zama, da kuma wurin da yake zama dan kasuwancin shi, Bayan sun gama daukar duk bayanin da suke bukata, sukayi tafiyarsu, ashe Dikko gidan da muke haya yaje ya siya, kuma mai gidan da muke haya yace wa Dikko Babana baya biyan kudin haya tuni yayi niyar tashinmu sai wata yayata take biyanshi kudin haya daga cikin kaddarar rayuwarta, Tun wannan ranar Dikko ya biya kudin gidanmu, bayan ya biya tafiya ta kamashi, saida yayi wata biyu baya nan, shine fa yana dawowa babu notice kawai yasa aka rushe gidan...... Ajiyar zuciya na sauke bayan na gama jin duk bayanan su, yanzu ita Zainab zuwa takeyi anayin iskanci da ita kenan ? Amma ta bata wayanta, Yawwa an samo gida ku taso mu tafi, gaba daya sowar farin ciki suka dauka tare da mikewa suna cewa a ina gidan yake ? Gidan Alhaji Sabo ne yace mu zauna dan yaji abinda ya faru damu kuma ya tausaya mana sosai, amma duk watan duniya yace zamu rika biyan dubu goma, Eh hakan yayi babu wani damuwa, ku tashi mu tafi, yeay yara da manya sukayi ta shewa muka tafi dukanmu yayin da wasu ke cewa dan uwar Dikko yazo ya anshi wannan idan ya isa. Haka muka koma gidan Alhaji Sabo dake makotan gidanmu da Dikko ya siya, bamu da komai haka muka shiga gidan, kowa daga ita sai kayan jikinta, Nidai har yanzu banyi magana ba, abun duniya duk ya dameni kuma babu wanda yabi ta kaina ko Inna bata sake shiga sabgata ba sunyi ayari wuri daya ana ta shawarar yanda za'ayi a samo kudin Alhaji a bashi dan ya basu daga yau zuwa jibi su kawo mishi kudin shi. Har safiya basu samu mafita ba, haka kuma Babana bai kwana gida ba, bansan yanda akayi ba suka shiga suka fita suka bawa Alhaji kudin hayarshi ba, Kwanan mu hudu a sabon gida Baba yazo gidan, bai tambayi yanda akayi muka dawo ba haka kuma baibi takan kowa ba zance ya akayi aka biya kudin haya ba, haka kuma baiyi ma kowa magana ba saini daya, Uwar masu gida lafiyar ki qalau kuwa ? Lafiya qalau Baba na amsa masa, yace kwana biyu bakije makaranta ba har kawarki ta tambayeni ko lafiya ? Nace mata lafiya qalau gaskiya, kinsan nima bana nan naje Abuja, Allah sarki na fada, tou miya hanaki zuwa makaranta ne ? Ya sake tambaya na, saida na tattara bakina sannan nace Baba ai an rusa gidan, komai namu kuma an tattarashi an kwashe anje an zubar, banda kayan makaranta da littafai, Wayyo Allah Mamana, taso muje waje muyi magana, mikewa nayi nabi bayanshi, yana gaba ina binshi har muka fita kofar gida, Wuri muka samu muka zauna, muna zama Babana yace in fada masa dame dame nake bukata ? Nace masa ko kayan sakawa dukanmu gidan bamu da, kowa kala daya yake dashi, amma makota sun dan tattara mana kaya, murmushi yayi tare da cewa wallahi Uwar masu gida bata saka kwancen kaya, na dawo garin nan jiya da kudi fiye da tunaninki Mamana, Tunda naji abinda ya faru tsakanin shadda da yadi da boyal saida na siya kusan kala arba'in, takalmi da agoguna da hulana duk babu abinda ban siya ba, kayan suna can na kai dinki, Tsare Babana nayi da ido, a zuciyata kuma ina ganin rashin adalci irin na Baba, amma Baba bakada imani iyalinka na nan suna neman abinda zasuci karma ayi maganar wurin zama amma kai har lokacin siyan kaya kake yi Baba......? Duk a zuciyata nake wannan tunanin. Mamana, ya kira suna na, kallonshi nayi ba tare dana ansa ba, tunanin me kikeyi ? Bayan gani a duniya ! Idan har ina nan a raye baki da matsala nayi miki alkawari zan kula dake zan kange miki duk wani bakin ciki da damuwa, idan dan maganar kayan makaranta ne da littafai zan siyo miki komai ma ki daina damuwa, zan miki duk abinda kike so dan kiyi farin ciki Mamana , wallahi da ina da iko ko kuda da sauro da ban barsu sunzo wurinki ba, haka nake alfahari da aihuwarki farar mace lantarkin ciki gida, da nasan zan haifeki wallahi da ban tara wannan yame yamen "ya "yan ba, A ranar da aka aifeki a ranar naci makudan kudade a wurin wasan caca , tun daga ranar na gane ke mai sa'a ce, wannan dalilin yasa nasa miki sunan mahaifiyata ya karasa maganar yana murmushi, sannan yaci gaba da cewa zuwanki yasa talauci ya guji rayuwata, shi yasa na tattara miki buri da yawa domin nasan kedin mai arziki ce. Yana fadar haka yace tashi muje, tashi nayi nabishi, yauma cikin wata zakanyar mota muka shiga, ta gaji da haduwa sai sanyin A C ke tashi ga kamshi mai dadin shaka, Babana fa dan gayu ne gashi da wayewa kuma yana da kalar burgewa amma babu halin kirki. A daren nan saida Babana ya tabbatar duk abinda zan bukata ya siyamin, sannan muka wuce wurin dinki, tela ya aunani Baba ya biya kudi muka dawo gida, Tunda muka dawo matarshi Mariya ta tada hankali ta fara zagina tare da aibatani, bata san Babana yana tare dani ba da batamin ba, yana shigowa cikin gida yace mata ta tafi ya saketa, maimakon Mariya tayi farin cikin sakin kawai sai ta kama kuka, dani Babana ke aure ya sakeni wallahi sai nayi farin ciki sosai na rabu da rayuwar wahala, Amma Mariya saita durkushe tana bashi hakuri, wallahi ko sauraren ta baiyi ba, anyi an gama domin Babana idan ya saki mace ya gama da ita har abadan duniya baya maimaita mace idan har ya riga ya rabu da ita, dan yace ko sitira sawa daya yake mata mace kadai yake ma maimaici a rayuwar shi, shi yasa idan har ya saki yake mantawa da babinta a rayuwarshi. Fita yayi yabar gidan, Mariya kuwa kuka takeyi kamar zata mutu, wallahi ta bani tausayi sosai dandai ba hurumi na bane dana bashi hakuri kuma tabbas nasan zai hakura amma ba ruwana tunda ba hurumi na bane, kuma nasan tsakanin gobe da jibi tabbas saiya karo aure....... Zaune muke lafiya a gidanmu, rayuwar dai tana nan kamar kullum kowa shi yake cida kanshi, gaba gaba dai yayuna sun fara harkar barikancin su har a cikin anguwa, saboda Baba baya tsawa tawa dan yaga dama ma ya kwana biyar ko sati baya gida, Bayan sakin Mariya da sati daya Baba ya auro wata "yar fiririyar yarinya wacce zata tsaya iyakar sa'ata, kankanuwar yarinya itama mai zubin karuwai, wankan tarwada ce kallo daya zakayi mata kasan ta gaji da fekewa da bari... Idan kayi mata magana saita wani yamutsa fuska sannan zata daga idonta dakel tayi maka magana, kai nidai sam tsarinta bai burgeni ba haka kuma bata wani shiga raina ba, dan bata da kunya ko ta misali, caccakakkar "yar iska ce , tasha iskanci ta koshi, amma anyaBaba auro yarinyar nan yayi kuwa ? Rayuwata nakeyi cikin farin ciki, bani da wata damuwa shi yasa bana gane abinda kowa yake ciki a gidanmu, idan na fito daga dakinmu sai dare nake komawa saboda Innata bata san gani na, dan kishiyoyi sun tisota a gaba da habaici saboda ni, Babana yana kula dani sosai baya barina shiga damuwa, ina zuwa makarantar boko da islamiya , amma boko gugar kaya kawai nake inje, islamiya kadai nake da fahimta. Tafiye nake a cikin nikaf ina, sauri kawai nake na isa gida saboda hadarin daya taso, sai wani irin iska akeyi mai hade da kasa, walkiya da cidar hadari duk sun karade sararin samani, tunda na biyo santar nan banci karo da kowa ba har na iso inda nake tunanin nan ne gidanmu, Kamar yanda nayi hasashe haka na yanki hanya domin shiga gida dan bana ganin gabana saboda kasar data shigar min ido, na daga kafata in taka sumintin kofar gidan naji wayam, kara mika kafata nayi dan a tunani na ban tako daidai ba, kamar yanda naji daga farko yanzu ma haka naji, Da sauri na bude idona dan inga lafiya ? Filin wurin kawai na gani kamar ba'a taba gini a wurin ba, salati nayi na sanar da ubangijina to ina "yan gidanmu suka tafi ? Makota na shiga na tambayi inda "yan gidanmu suke, aka cemin Alhaji Sabo ya canza mana gida kafin wata ya kare mu tashi, tambayar dalilin tashin da rusa gidan da akayi nayi amsar da aka bani itace, *Dikko* ne ya siyi gidan amma wannan karon anyi ma kowa uziri ya fita da kayanshi. Bance komai ba saidai na sake tambayarta ina gidan yake ? Kwatanci tamin gida na like da gidan da aka rushe nan muka koma, ban sake cewa uffan ba na nufi gidan. Daki daya ne tak a gidan saboda haka kowa yana zaune cikin barandar dake tsakar gidan, sallama nayi amma babu wanda ya ansa min sallamar har Innarmu, nima ban sake sallamar ba na samu wuri na zauna tare da jan bakina na kameshi, Dukanmu a tsakar gida muka kwana yayin da wasu suka kwana a zaure, babban gida ne sosai amma daki daya ne ya gina shima ajiye ajiye yake a cikinsa, gari na wayewa na shirya na tafi makarantar boko, Baba bayanan sun tafi gasar caca, dan bai fadawa kowa sunan garin daya tafi ba, ni kadai yayiwa bankwana. A makaranta Amisty ta lura ina cikin damuwa, dan haka ta tambayeni abinda ya dameni, ban fada mata ba, saidai nace mata da Allah waye Dikko a garin nan ? Hmm su Amisty idon duniya saida tayi masa wani irin kirari sannan tace miya hadaki dashi ne ? Nace mata kawai dai labarinsa nakeji shi yasa nake san sanin koshi din waye. Abinda Amisty tacemin shine, yanda kike takama Babanki yana masifar sanki da kaunarki dan dole wannan misalin da kanki zanyi shi idan ba haka nayi miki ba tou fa lallai nasan baza ki gane ba, Dikko d'a daya tak a wurin mahaifin shi, yana da yayu mata sosai saboda suna da yawa gidansu suma, amma basu kai gidanku yawa ba, abinda yasa kuwa aka tara yawa a gidansu saboda san haihuwar d'a namiji da basu samu ba, Akan Dikko ya samu namiji daga shi kuma har zuwa yau din nan ba'a sake haihuwar namiji ba, Dikko gaskiya yana da kirki kuma shi ba dan iska bane amma gaskiya baya san raini, Yana da alkairi sosai amma shi baya dariya haka kuma baya murmushi, ni bayan wannan bansan komai ba haka dai kawai naji ana fada a gari, Gyara zama nayi tare da tambayarta shi kuma waye ubanshi ? Murmushi Amisty tayi sannan tace da Allah karki dauki ne wake da shinkafa mana, Dikkon ne a katsina baki san waye ubanshi ba ? Wallahi ban sani ba, na bata amsa, tashi tayi ta barni a wurin dan ita a tunanin na sani jan zance ne. Har muka tashi makaranta Amisty bata fadamin ko waye uban Dikko ba, ni kuma ana tashi makaranta ban tsaya komai ba na nufi gida tunda nasan Babana baya nan, Tunda napep ta ijiyeni, na hango kofar gidanmu daddabe da mutane, Dikko yana zaune a saman gaban mota ya kwantar da bayanshi saman gilas din motar kafarshi daya saman daya, ya tallabo kanshi da hannayen shi, kamar kullum yauma cingom yake ci, kananan kayane jikinshi ya dode da gilashi mai saukin duhu. "Yan gidanmu sun daddabe shi suna bashi hakuri amma ko inda suke bai kalla ba bare su sa a ransu zaiyi magana, sai waso mana kaya akeyi daga cikin gida, yayin da "yan zaginshi ke cewa ai tunda har kuka tabo mai gida a garin nan sai kun rasa gidan zama, wannan dinma ya siyeshi idan kunyi zuciya ku gina naku talakawan banza kuna jayayya da masu katsinar gaba daya, Inda jakar islamiyata take naje na duka na dauka, na koma gefe nayi tsayuwata tunda ko nayi magana babu wanda zaimin magana kowa haushi nake bashi, Wani dattijo ne shima makoci ne , yace ni inje in bawa Dikko hakuri duk saboda abinda nayi masa yake ta wannan saye sayen gidanje, dan gajeren murmushi nayi tare da cewa Baba kenan aini wancan dan iska nafi karfinshi wallahi baikai matsayin da zan kalleshi ba bare har na bawa banza hakuri, idan kuma har ka tilasta naje to lallai ina zuwa zan jawo dan iska ya fado kasa, Lallashi na dattijon nan ya farayi akan lallai sai naje na bawa Dikko hakuri, a lokacin har an gama fito da komai namu an fara rushe gidan. 01/08/2019 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 4 Ya uzura min sosai akan naje na bawa Dikko hakuri dan haka na tunkari wurin kai tsaye zuciyana tana min tsake tsaken mugunta iri daban daban. Cike da bacin rai na isa wurin, kamar yanda na fadawa tsohon nan zanyi haka kuwa nayi, dan ina zuwa na kamo kafar Dikko da zumar na fadar dashi kasa ya karya kashin baya, Amma ina, dan ina riko kafar shi daya, ya tattakura yakai min halbi da dayan kafar da ban rike ba, hanci baya raina duka lokaci guda jini ya ballemin kamar an yanka kosashshiyar kaza, Yana halbina ya diro daga saman motar shima ashe yayo dagon muguntar shi yana neman inda zan sauketa ya huta, ganin jini yana bimin baki har yana digowa kasa yasa hankalina ya tashi, Sosai nayo kan Dikko, yaranshi suna kokarin rikeni yace su barni yanzu zai koyamin hankali yanda idan na ganshi da gudu zan canja hanya. Daga nesa mutane suka fara bashi hakuri dan babu wanda ya isa yazo kusa dashi, babu wanda ya kalla bare kayi tunanin ko zai saurare ka, kusa dani ya matso sosai, yasa hannuwan sa biyu ya riko min fuska, sai yanzu nakejin halbin da yayi min yake ratsa duk ilahirin cikin kokon kaina, gaba daya jikina ya saki ya koma kamar ba nawa ba, Sama sama nake ganin Dikko har yanzu bai daina cin cingom in da yakeci ba, saida yayi min kyakkyawan riko sannan ya cire gilashin dake fuskarshi ya kalleni ido cikin ido sannan yayi dan kyakkyawan murmushi, wanda ke nuni da mugunta ta tashi... Sai mun sake had'ewa an mata...yana fadin haka ya k'uma min kanshi da nawa wuri daya wanda haka yayi sanadiyyar daukewar gani na gaba, amma har zuwa wani lokaci goshina da nashi yana hade wuri daya, Bai sakeni ba saida ya tabbatar na tafi suma, dan tabe baki yayi tare da dage girarsa ta dama sannan ya sakeni ya zura hannuwansa cikin aljihu ya nufi motarsa dashi da tawagarsa suka bar anguwarmu. Ni kuma na fadi kasa somammiya, Allah sarki dan uwa mai dadi duk "yan gidanmu basu ji dadin abinda Dikko yayi min ba, sun tausayamin iyakar tausayi gashi babu mai kwandalar da za'a kaini asibiti, saidai aka samo kankara aka rika dandan na min a goshina tunda habo ne nayi, Abokin Babanmu shi yaji labarin abinda ya faru damu, yana da wani gida na Alhaji Sabo da aka saka a caca ya ciwo gidan, shine ya bada makullin gidan aka kawo mana yace mu bude mu shiga, Daukata sukayi suka shiga hadani tare da bani kulawa ta musamman, amma duk abinnan saida nayi sati daya kafin na dawk daidai, Babana har yanzu bai dawo ba kuma bamuji labarinsa ba ko ta waya, kuma har yanzu ban yadda na sake fita ba koda zaure saboda zuwa wannan lokacin bana san ganin Dikko ko inuwarsa, Gaba daya na jingine islamiya da wata bokon banza, daga tsakar gida sai daki, idan ina tsakar gida naji karar mota ma daki nake komawa, Satinmu ukku a gidan abokin Babanmu Baba baizo ba, kuma baiyo aike ba, shima kuma wannan gida da muke ciki Dikko ya siyeshi, ba'a gidan kadai ya tsaya ba duk gidan da yasan na hayane a anguwar saida Dikko ya sayeshi duk sun zama mallakinsa, tashin hankali da damuwa kowa ya shiga, Saida abokin Baba yazo yake fada mana cewa an kama Babanmu yana can an kulleshi saboda ya ranci miliyan biyar din wani abokinsu bai bashi kudin ba, shine ya kaishi wurin hukuma suka tsareshi, Kowa ya jinjina miliyan biyar saboda babu wanda yasan abinda Baba yayi da kudin nan, shiba gida ba, ba mota ba ba fili ba, haka kawai ya saka kanshi rikicin duniya. Inna na kalla data zabga tagumi tana d'igar da hawaye, cikin yanayin tausayi nace Inna wai da zaki auri Babana bakuyi binciken halinsa ba kafin auren ku? Banza Inna tayi dani bata bani amsa ba, tsoki nayi tare daci gaba da cewa muma mata muna da matsala yayin da muka hangi tilin dukiya da babbar mota hankalinmu, ganinmu da kuma tunanin mu sukan b'ace , idan aka samu kwadayayyar zuciya sai kuma takai mutum ta baroshi, kamar dai ku duk zuciyoyi ne da kwadayin duniya suka kawo ku nan suka barku, kiyi ta addu'a kema Allah sa ya sakeki ki huta. Kunga mutum da arziki bakusan taya yai ya samu abinsa ba, Inna dai bata tankamin ba, muka fito domin "yan gidanmu sunce muzo mu tafi wata primary school dake bayan gidanmu mu kwana tunda dare yayi kafin mu samu gidan zama, duk muna tsaye a tsakar gida dan Dikko yace wallahi idan muka kara cikakkun mintina biyar saiya kunna mana wuta, Cikin kyarmar jiki nacewa Maman Fa'iza "yan uwan Babanmu basu da kirki kowa ya zura masa ido dashi da iyalanshi sai wuta mukesha babu mai roka mana sassabci a rayuwarmu, ansa daya ta bani itace, ai babu ubanda yasa shi aure auren kuma basune suka sa duk yayi cikunnan ku aka haifo ku duniyar ba. Haka tayi ta surutai marasa dadi na bad'ala da rashin kamun kai har muka fita gidan muka tafi makarantar, koda muka fito motoci sunkai biyar masu zafi tsadaddu masu burgewa da daukar hankali, an haska fitilinsu duka, amma yau babu Dikko dan naji suna magana cewa mai gidansu yayi tafiya baya k'asa amma ya umurcesu da su tabbatar bamu kwana gidan nan ba, idan mun fita mun huta idan bamu fita ba a kunnawa gidan wuta, wannan shine sakon da Dikko ya aiko dashi, A makarantar mukaci gaba da zama cikin azuzuwa, { Classes } idan dalibai sunzo zamu fita waje idan sun gama suka tafi zamu koma mu zauna, ni na gaji na fadawa matan Babana waisu basu da gidan iyayensu ne ? Wannan wulakanci ai ya isa haka, kowa ta tafi gidan ubanta ta huta mana, ai fa yak'ai yak'ai kamar zamu cinyeni d'anyata saboda tsabar masifa, dole naja d'an bawan Allahna nayi shiru. Satinmu daya kullum sai an koremu kamar karnuka kuma kullum bama tafiya sai mun dawo, da safe kuma su tura yaransu su shiga bara cikin gari, rayuwa dai wulakantattar rayuwa mafi muni da k'ask'anci, Babana baya da adalci kuma baya da imani hakika zai tadda Allah, domin wannan zalincin yayi yawa. Ranar da muka cika kwana takwas aka koremu da karfin bala'e mukabar makarantar malaman suka kara da cewa gwamnati bamu ta ginawa makarantar nan ba muje can musan inda zamu zauna amma ba makaranta ba, suka kara jaddada mana idan suka sake ganin wata wallahi sai sun kaita an kulleta wurin "yan sanda, Nanfa Allah ya bamu sa'a cikin malaman wani ya ji kanmu ya bamu kyautar fili dan mun fada musu matsalar mu, shi kuma ya tausaya mana, saifa suka fara yahani akan fili yayin da kowa ke cewa saidai a siyar da filin a raba kudin aba kowa, Yayin da wasu ke cewa ayi hakuri a zauna, masu cewa ayi hakuri a zauna sun rinjayi wanda keso asiyar, dan haka dole suka hakura, muka dinguma zuwa fili, bayan munje akayi tamalmala ta malmala aka siyo buhunna dasu aka zagaye gidan , Wannan fili dai bazai ansu a wurin Dikko ba, nima ganin mun samu mazauni hankalina ya komawa tunanin Babana, {{{}}} {{{}}} Bayan wasu kwanaki, Rayuwata nakeyi cikin jin dadi, nidai Allah ya taimakeni bana bara saboda kanin inna yana kawo mana dauki da abinci, kunsan idan mace ta koshi tou fa lallai bata da aiki sai iskanci da rashin kunya, toni dana koshi nawa iskancin Dikko kadai yake nema ido rufe, kullum ina bisa hanyar zuwa tsohuwar anguwar mu, haka zan hau napep kamar duka kenan saina tabbatar mun kusa zuwa sai in dire abuna, wasu basajin fita ta wasu kuma suna gani idan suka bini basu kamoni ba saidai suyi min Allah ya isa, nima na fara dauko kadan daga cikin dabi'un Babana. Yauma direwa nayi, da gudu nasha lungu na shige wani gida, zaure na tsaya saida na huta sannan na tattaro natsuwa na shiga ciki da sallama, Cikin sakin fuska matar ta ansa min, wuri na samu kasa na zauna ina gaisheta, ta ansa lafiya lau, shiru nayi zuwa wani lokaci nace mata hajiya dan Allah kin iya rubutun wasika ? Murmushi tayi sannan tace niko na iya rubutun wasika, nace tou don Allah kitaima min mijin Yayata ne suka rabu shine yayi mata shegen duka ya raba mata kai da tab'arya tana can asibiti rai hannun Allah, kuma sai rubutun zagi yakeyi yana aikowa gidanmu, shine aka rubutomin ansa na maida mishi kuma takardar ta fadi, ni kuma idan na rubuta sabuwa zai gane rubutu na ne , amma ki taimakamin don Allah, ni na karanta wasikar kuma zan iya fada miki yanda take kiyimin rubutun nakai mishi don Allah........! Ba tare da tunanin komai ba tace tou, daki ta shiga ta dauko jakar makaranta, da gani ta yara ce , a ciki ta dauko biro da paper tace min bismillah, duk ba tare da tayi wani dogon binkice ba ko yin nazarin yin hakan me zai haifar daga baya. Ni ko dadi naji sosai a zuciyata , tunda ni bazan iya rubuta uwar komai ba, amma nayi farin ciki sosai domin dai yau zanci uwar Dikko kafin in fara kashe dawanki dan iska. Bayani na farayi ta fara rubutawa, _Ka fita daga rayuwarmu yayin da ni kuma yanzun nakejin farin cikin shiga taka rayuwar, salon ka yana da matukar burgewa dan marasa tarbiyya, taya zaka fara rashin tarbiyya kuma ka gaji da sauri haka ? Ko kudin sayen gidajen ya kare ne ? To tunda kudin sayen gidaje ya kare nasan zakayi kokari ka samo kudin sayen dokuna, ina mai farin cikin sanar dakai daga yanzu d'innan har zuwa ranar da zaka bar zaman anguwar nan farin ciki zai bar zuciyarka, kuma zaman anguwar nan zai haramta a gareka kamar yanda ka haramta mana zama a cikinta, zanyi ta kashe dokunan ka harsai ciwon zuciya ya kama ka idan ka fasa kai ba d'an Babanka bane............_ _Sultana ce, Allah ya bawa mai rabo sa'a, idan kaje Islamiya kace amin......_ Mikomin tayi bayan ta kammala rubutawa, godiya nayi mata sannan na fita, nayi tafiya mai dan nisa ina kokarin bi hanyar da zata sadani da tsohuwar anguwarmu na hango Dikko ya sauko daga saman doki......, Jar riga ce a jikinshi amma ba irin ja d'innan ba ja mai kyan kallo, sai jar hula akanshi irin wacce matasa ke gayu da ita, fesin cap, bakin wando ya saka wanda suke kira 3quater da rufaffin takalmi, sai bulalar da ake dukan doki a hannunshi, daga gani dai daga kilisa suka dawo, A fili nace shege mai kama da mata, cin cigom kamar tsohuwar karuwa, duk'awa yayi k'asa ya d'auki wani abu wanda ban iya ganewa ba, bayan ya d'auka ya koma saman dokin yayi mishi diddige tare da tsuke bakinshi irin yanda ake kora doki yayi gaba, Da gudu ya wuce ya wani d'an jirge saman dokin yayi kyau sosai bazan mishi haddasa ba gaskiya, ci gaba nayi da tafiya, kafin in ida isa wurin kuma naga ya wuce da gudu cikin mota kura tabi bayan motar sosai kamar guguwa ta taso. Hamdala nayi domin na samu damar farko da zan kashe doki d'aya daga cikin dawakan Dikko, saboda nasan wata mugunta d'aya da ake ma doki, ba'a ba doki ruwa idan aka dawo dashi daga yawo, idan aka bashi ruwa a wannan lokacin tou cikinshi k'ullewa yakeyi ya mutu. Nikaf ina na ciro na saka tare da gyara tafiyata na tun kari gidan kai tsaye, a kofar get in gidan nayi ma mai gadin gidan sallama, ya ansa cikin sakin fuska, nace mishi dama wani mutum ne da jajayen kaya a jikinshi yace in turo mishi kai yana can yana jiranka..... Na nuna mishi hanyar da Dikko ya wuce da hannuna , Cikin sauri ya wuceni ya tafi, yana wucewa na shiga cikin gidan, doki d'aya ne kad'ai wato shine dokin da Dikko ya dawo dashi, an d'aureshi a gefe kuma an cika bokiti da ruwa an ajiye shi kuma dokin yana ta bubbud'a hanci yana maida numfashi, Da sauri na kinkimi bokitin ruwan nakai gaban dokin na ajiye, aiko ina ajiyewa ya duk'ar da kanshi yaci gaba dashan ruwa, a daidai lokacin da mai gadi ya shigo dan yabi hanya baiga Dikko ba ya dawo, Kay kay kay ba'a bashi ruwa yana k'ok'arin isa dan d'auke ruwan na tareshi tare da cewa anshi yace ka ajiye mishi wannan takardar idan yazo da daddare zai karb'a, bai tsaya ansar takardar ba kuma baimin magana ba ya wuce, Murmushin nasara nayi daga cikin nik'af ina sannan naje na ijiye masa takardar a saman kujerar da yake zama na wuce abuna. Kafin ya isa tuni doki ya shanye ruwan dana ajiye mashi, sai dai abinda ba'a rasa ba, cikin tashin hankali ya ciro wayarshi daga cikin aljihu ya fara kiran wayar Dikko, Mai gida kazo akwai matsala dokin daka dawo dashi yanzu, gashi nan zai mutu, yana fad'in haka ya kashe wayarshi, Cikin k'ank'anin lokaci Dikko ya iso, a k'ofar gidan yayi parking ya fita da sauri ko murfin motar bai tsaya rufewa ba, lokacin daya shiga cikin gidan tuni dokin ya kwantar da kanshi k'asa yana ta zabura irin na fitar rai. Meya faru haka ne ? Dikko ya tambayi mai gadin shi ! Cikin daburcewa ya fad'awa Dikko duk yanda mukayi dashi , sannan ya d'ora da cewa ga takardar can daka bata ta kawo ta ajiye, ajiyar zuciya Dikko yayi tare da furta wace ce ita tayimin k'arya ? 'Daukomin takaddar kila tana da wata manufarta a ciki, d'aukowa yayi yakai mishi, ya warware ya duba, cimimiye takardar Dikko yayi bayan ya gama karantawa ya dink'uleta wuri d'aya sannan ya jinjina kanshi, ya fito da sauri daga cikin gidan, Wurin motarshi ya tsaya, tare da kaima gaban motar duka sannan yace wallahi cikin k'ank'anin lokaci duk inda "yar iskar yarinyar nan take cikin garin nan ku d'auko min ita, yana fadi haka ya shiga mota yaja fa fafa ya tafi kamar zai tashi sama....... Har yayi nisa ya dawo, har yanzu mai gadin bai koma cikin gidan ba yana nan tsaye a wurin, yanzu daya dawo bai fito ba ya sauke glashin motar shi sannan yace, ku kawota wurina zan nuna mata nid'in d'and'an Babana ne wallahi wallahi wallahi sai tayi nadamar zuwanta duniya. Yana fad'in haka ya juya a guje ya tafi, lallai da ganin yanayin shi gaskiya ranshi a b'ace yake, tabbas idan har aka kamoni aka kawai Dikko ni a cikin wannan yanayin lallai Dikko kasheni zaiyi, Lokaci d'aya jikina ya d'auki kyarma naji fitsari ya kamani sosai, "yan hanjina suka juya ai bansan lokacin dana bar wurin ba, cikin tashin hankali na hau napep na nufi filin gidanmu, tun kafin mu isa na dire nayi gida da gudu........ Da sallama na shiga, Babana na gani zaune dashi da abokanshi kuma sune suka amsa min sallama, cikin farin ciki ya kalleni tare da cewa daga ina kike Mamana ? Cikin inda inda na sosa kaina tare da cewa daga gidansu k'awata nake, murmushi Babana yayi tare da mik'ewa yace muje waje muyi magana, naso nayi masa gardama dan gani nakeyi kamar idan na fita zanga Dikko k'ofar gidanmu, Muna fita na fara tambayar shi ya akayi ya dawo ? Yace min su Bello sukayo belin inshi, akwai wani wasan caca da za'ayi an saka naira miliyan hamsin kin san na kware sosai a wasan caca babu wasan cacar da za'ayi a ci ni saidai ni in ciwo shi yasa ake min hassada. Gyara tsayuwar shi yayi tare da d'an jan dogon hancinsa, sannan yace Mamana kinsan ba'ayin wasan caca a bashi sai an saka k'addara, bani da k'addara sai kayan sakawata, na saka amma ance ba'asan sutura, tou Bello ya bani shawara wai in sakaki a matsayin k'addarata, Cikin rashin fahimta nace Baba kamar ya za'a sakani a matsayin k'addara bayn nima banda komai... Murmushi yayi tare da cewa Mamana kenan ai kuwa kece ma mai komai domin keda kanki kece babbar k'addara ta shi yasa na zab'eki a cikin duk "ya "yan hamsin da takwas dana aifa..... Kiyi hak'uri kawai ki yadda duk wanda yazo ya tambayeki kece k'addarata kawai kice Eh, danni na yadda da kaina babu ubanda ya isa ya ciwo uwata a wasan caca saidai ni inciwo uwarshi wallahi, Mamana ki yadda da Babanki nayi alk'awari baza a samu matsala ba, ki yadda dani kinji Uwar masu gida, ya k'arasa maganar yana mai rik'e duka hannaye na duka biyun yayi kalar tausayi. Tou Babana idan aka tambayeni zance Eh kawai ko ? Yawwa Eh zaki ce kawai ya wadatar, insha Allah gobe kamar yanzu muna cikin kud'i kuma ga Uwata a tare dani, ya k'arasa maganar cikin farin ciki, murmushi nayi mishi sannan muka koma cikin gida dan in fad'awa su Bello na yadda.......... Allah yasa muyi juma'a lafiya, ubangiji ya sadamu da alkairan dake cikin wannan juma'a mai albarka, mugun ji da mugun gani tsaka mai wuya ubangiji ya tsare daga garesu, Allah ya karemu da jin kunyar duniya da lahira. Am3n, Jamila Musa ce 🤙🏻 02/08/2019 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 5 Muna shiga ciki tun kafin mu k'arasa inda suke zaune Baba ya fara cewa tou gata nan ku tambayeta kuji, a daidai lokacin da muka iso gabansu. Ina k'ok'arin durk'usawa Bello yace a , a basai na zauna ba in tsaya a tsaye akwai abinda yake dubawa. 'Dan b'ata fuska Babana yayi tare da cewa kamar ya kana duba wani abu ? Ai a cikin sharud'd'an babu maganar wani dube dube, dan haka kabar yarinya ta zauna ka wani daina yi mata kallon k'urulla saboda rake ba sa'ar tsoho bane ba, dan koya bada kudin sa ya siya saiya ajiye tunda baida hak'oran cizawa, ya k'arasa maganar cikin sigar duniyanci. Murmushi Bello yayi tare da cewa, ai zamani tafiye yake da ci gaba ko ba'a tauna ba a tsotsa, d'an b'ata rai Babana yayi tare da cewa, kaga da Allah mubar wannan maganar muyi abinda ya had'amu, ya k'arasa maganar cikin nuna rashin jin dad'in zancen nasu. Gyara zama Bello yayi tare da cewa, haba Aliyu kasanni fa farin sani, kuma haka nima nasanka ciki da wajen ka, wane dare ne jemage bai gani ba ? Na hau tudu nabi ta gangare, kasan ko inacin kwarika wannan kwaron yayi min k'ank'anta shi yasa kaga bana cin shinge saboda na raina girmanshi duk da kuwa yana da mai sosai nafi gane kura ko da kuwa an soyata babu magi ba gishiri, kalmar dai d'ayace ake kira amma wurin hidimar da banbanci karka samu damuwa yaro ne sabon jini kuma bak'one a harka, yasan dad'in komai a duniya amma har yanzu baisan dad'in mace ba shi yasa kaga inata k'ara dubawa dan bana san a samu damuwa, Dariyar mugunta yayi tare da cewa , wash ashe na manta malamar Babanta jarumin gaske ne a harkar wasan caca, Shima Babana murmushi yayi amma da ganin murmushi kasan na b'acin rai ne, yace Bello kenan, shiga ramin kura ba abu ne mai sauk'i ba, idan har kaga na fad'i a wasan cacar nan tabbas duk wanda yayi k'ok'arin kusantar min Mama saina ga bayanshi, wannan shine sharadi na, Bello kuma cewa yayi kar muyi haka dakai Aliyu yaron nan d'an rigima ne, mu daina wannan maganar kawai dai muyi fatan Allah yaba mai rabo nasara, kallona yayi tare da cewa kin amince ? Jinjina kaina nayi tare da kallon Babana sannan nace na yadda............ Dariya Bello yayi tare da cewa magana ta k'are mata tacewa mijinta shege, Kafad'ar Babana ya daka tare da cewa Aliyu muje, juyowa yayi ya kaleni tare da cewa yarinya ki shirya, idan kinga Babanki tou fa lallai an ciki a wasan caca, idan kuma kika ga Bello tou Babanki ya cinye matashin nan, ganinmu shine zai tabbatar miki Babanki yaci caca mu kuma munzo miki murna ne, suna fad'in haka sukayi gaba abunsu, Bayan tafiyarsu ina zaune suku suku dani kamar asirin mayya ya tonu, ni ba Babana ne damuwata ba Dikko shine tashin hankalina, yace duk inda nake a gano ni, sai yanzu na gane na tafka babban kuskure dana rubuta suna na a jikin takarda, lallai na cika babban dak'ik'iya. A b'an garen Dikko kuwa nema na sukeyi kamar rai da mutuwa, babu wanda yasan inda muka koma, daga makaranta prymary babu wanda ya sake jin labarinmu, Rashin gani na yasa suka fara ba Dikko hak'uri, amma fur Dikko yace wallahi kafin sha biyun dare sai an nemoni idan har ba'a ganni ba zai iya sargafe kanshi ya mutu, Duk iyakar yanda suka so Dikko ya hak'ura ya k'iya, ba nemoni bane wahala a wurinsu suna tausayin irin a zaftuwar da zanyi a wurin Dikko, dan ya fad'a musu ba mutuwar dokin ya b'ata masa rai ba, d'an marasa tarbiya dana kirashi dashi, bama shine baida tarbiyar ba iyayenshi ne basu da tarbiya abinda nake nufi kenan,sai kuma idan ya fasa shi ba d'an Babanshi bane. Wannan sune munanan kalamai masu muni da suke ta zungurar zuciyar Dikko. Dikko yana da zuciya sosai, kuma fushin shi baya da kyan gani, idan ya nace akan abu sai yayi babu wanda ya isa ya hanashi, idan yace bayayi babu wanda ya isa ya tursasa masa yayi abinda baisa kanshi ba. Yau Dikko yana cikin matsanan cin b'acin rai, yayin da ni kuma nake cikin fargaba da tashin hankali, dan yanayin dana ga Dikko d'azu ya bani tsoro, Duk wanda yaji wannan abun yasan nice bani da gaskiya, domin ni naje har inda yake na jawoshi fad'a, ya Allah ka rabani da Dikko daga yau insha Allah bazan sake janshi fad'a ba, ka mantar mishi dani a rayuwarshi kuma ka bashi hak'uri a zuciyarshi, ya daina nemana, Misalin 10:45pm Babana ya dawo gida, dashi da abokinshi Bello a lokacin har nayi bacci Baba yasa a tadoni in samesu kofar gida...... A waje na samesu, gaishe su nayi tare dayi musu sannu da zuwa, Bello kad'ai ya ansa amma Babana ya kasa magana, Bello ne ya fara magana kamar haka. Maryam, wannan shine sunan da Babana ya sakamin, wato sunan mahaifiyar shi, darajar wannan suna ne yake kirana da Uwar masu gida ko yace Mamana, Bello yaci gaba da cewa an samu matsala mahassada suka cuci Babanki bandai san yanda abun ya faru ba gab da za'a fara wasa kwalwarshi ta juya, ba buk'atar dogon bayani kawai dai Aliyu ya fad'i wasa. Tou idan ya fad'i sai kayi ya ya kenan ? Na tambayi Bello, sai zamu tafi dake wurin wanda ya ranta masa kud'in, dan a can basu yadda da ansar mace ba, sai wani ya buk'ata dan haka ya bada kud'in yace a kawo mishi ke, Waye shi ? Na sake tambaya, a tak'aice ya bani amsa cewa idan kinje kin ganshi, zan k'ara magana Babana yace Mamana babu abinda zai faru kiyi hak'uri kuje dan bana tunanin akwai wanda ya isa yayi miki wani abu a cikinsu saboda sun san waye ni, na bud'e bakina zan sakeyin magana a karo na biyu, wanda Babana ya sake tare min numfashi na da cewa idan dai har kare zai iya farautar kura tou lallai wani abu zai iya shiga tsakaninku, idan kuwa kare bazai iya ba tabbas zasu dawo dake, dan duk rashin kunyar kare ta gida ce, bishi kuje.... Yana fad'in haka ya juya da zumar shiga gida, Da gudu nabi bayan Babana na rik'e hannunshi ina kuka nace haba Babana laifin me nayi maka zaka sayar dani ? Cikin kulawa ya kalleni tare da gogemin hawayen da suka zubo saman fuska ta sannan yace, baki sawuwa Mamana saboda nima bada kud'i nasiyo ki ba, haka kuma bakya satuwa tunda Allah shine ya azurtani dake, hak'ik'a kuma baza ki ciwo ba ta sanadiyar wasan caca ko kun tafi sai kun dawo, dan haka ki zama d'iya mai biyayya a gareni,.... Baba.....Mamana ya fad'a kafin nace komai, yaci gaba da cewa, so guda d'aya ne tal a zuciyar ko wane d'an adam, amma shi wannan san a duniya za'a kasa shi kaso mutane so adadin haka, uwa, uba, d'a da kuma mata, banda uwa banda uba, kuma ni Allah bai d'oranmin ciwon son "ya "ya ba, bare mace da ban d'auketa a bakin komai ba, wannan son nawa gaba d'aya kece na martaba ki dashi saboda ki zamo d'iya mai sharewa Babanta damuwa. Sakin hannu na yayi tare da cewa sai kun dawo, yana fad'in haka ya shigr gida. Inaji ina gani suka tasa k'eyata gaba suka sakani mota mukabar k'ofar gidanmu, tafiya mukayi mai nisa sosai, sannan Bello da abokinshi daya taho dashi suka fara magana, Bello yace, alhamdulillah na zurashi rami na gama, kasan Aliyu yana tak'ama da tasha ni kuma zan k'ure mishi tashi tashar shi dan abinda yayi min bazan manta dashi ba nima saina rama akan wannan d'iyar tashi daya d'auka san duniya ya d'ora mata, Bello yaci gaba da cewa nine na bada kud'in nan cas saida na ajiyesu sannan akayi caca, bana asara zan kaita inda za'a bani kud'ina har a d'ora mani riba, ina tsoron wai wai da bayan da Aliyu zaiyi wallahi da nine zanyi mata kaca kaca da rayuwa amma yanzu zan kaita wurin gwamnati idan zai iya yayi fad'a da hukuma in gani. Ai kaji shi wai Allah baisa mishi ciwon san "ya "ya ba, nima shi yasa ban zab'i ko d'aya daga cikinsu ba dan nasan duk wacce na d'auka abin bazai mishi ciwo ba, nima ina so in dasa masa irin tabon daya dab'a min a zuciyata wanda bansan ranar da zai gogo ba, Ajiyar zuciya Bello ya sauke tare da cewa da Allah sake kiransu ni fa ba abinda ya dameni da wani fushin banzar shi, dan ba fushi yakeyi ba ko mutuwa akayi mishi ni kawai tafiya zanyi idan munje can ayita ta k'are, abokinsa yace to idan masu gadi suka hanamu shiga fa ? Daina min ma wannan bak'ar fatar taka da Allah, duba min magungunan nan Allah yasa ban zubar dasu ba wurin wancan sakaran, wata "yar k'aramar leda ya d'auko ya mik'a ma Bello tare da cewa gasu nan, dariya Bello yayi sosai tare da cewa kasan bak'one dole saida "yan rakiya, A daidai lokacin daya fara magana a waya, nifa dama basai yana harkar mata ba, to dama banda abinka duk wanda kaga yana harkar mata ai koya yayi, nifa taimaka min zaiyi kuma na taimakeshi, saurara ka taimaka mana kazo ka shigar damu gidan idan muka shiga duk nasan yanda zanyi da Allah, tou babu damuwa gamu nan isowa ba jimawa, haka yayi wayarshi har ya gama, yakan d'auke maganar sa danjin abinda abokin wayar tasa zai fad'a, yana fad'in haka yaja motar muka tafi. Ni kuma tunanin abinda Babana yayi masa kawai nakeyi wanda har yasa zaiyi ma Baba ramuwar gayya, ina tunani naji yana dariya tare da cewa an fad'a maka ni sakarai ne ? Ai kaima kasan baiyi cacar ba dan ubanshi dasai yaci, mugu ya saki baki ya lashe kud'i mu kuma muka lashe "yar sa, dariya ya k'arayi sosai tare da kaiwa sitiyari duka yace kud'i na biya malamai suka sa banza wasi wasi....... Amma ai kasan Aliyu maye ne da yayi wasan caca da gaske dasai ya lashe kudin nan kamar yadda karuwa ke lashe sabon harka.......... Ya kuma sabon harka ? Su sai suyi ta magana juyayya wanda sai su "yan bariki kad'ai suka isa su fassara yaren, ina ne nan kuma ? Na tambayi kaina yayin da muka tsaya gaban wani k'aton get, ga jami'an tsaro masu yawan gaske kowa ya kame da bindiga takai tsawo na, za'a fara magana wani daga cikin mota yace barsu su shiga tare muke, K'arfe ne aka d'age mana muka shige saida mukayi tafiya mai d'an nisa sannan muka tsaya, daidai da daidai kowa yana zaune cikin mota wanda ya shigo damu yace, Bello bana so nayi maka gardama ne kaga kamar wani abu amma na rantse maka da girman Allah Dikko baya neman mata, Wani irin tashin hankali naji yayin da naji an kira sunan Dikko sai yanzu na tuna da Dikkon da zaici uwata, hankalina na mayar a wurin Bello dake cewa kai ai sakaran banza ne idan zai nemi mata shawara zai maka ? Ai ba'a shedar namiji akan mace, murmushi mutumin yayi tare da cewa Bello na rantse maka da girman Allah har al-qur'ani zan iya dafawa Dikko bai harka mata, Tsoki Bello yayi tare da cewa muje idan zaka raka mu dare nayi, jinjina kai yayi tare da cewa muje, yana gaba muna biye dashi saida muka wuce get ukku kafin mu isa, kuma duk inda mukaje jami'an tsaro ne har muka isa bakin wata k'ofa, dukkannin mu anan mukayi parking, kulle min ido da hannu Bello yayi bayan mun tsaya. Rufe motar yayi da makulli sannan suka shiga ciki, wurin zama aka basu tare da cewa su jirashi yana zuwa, sunyi zaman daya wuce mintuna talatin sannan Dikko ya fito cikin tsananin b'acin rai dan har yanzu maganganun Sultana caccakar masa zuciya sukeyi, kuma ma koba komai dama shi Dikko ba ma'aboci sakin fuska bane, Gaishe shi sukayi, da kanshi kawai ya ansa gaisuwar tare da tsare su da ido, mutumin daya kawomu shine ya d'urkusa gaban Dikko yayi masa magana k'asa k'asa wanda babu wanda yake iya jiyo abinda yake fad'a, Kallo su Bello Dikko yayi tare da cewa da Allah kuyi hak'uri ita rayuwa sannu ake binta, babu wanda yasan abinda anjima zatayi bare kuma gobe, kar kace zakayi ramuwa akan duk abinda akayi maka wannan ba d'abi'a bace mai kyau, halin mutunan kirki sukan manta da duk wani abu mara kyau da akayi musu, ka zama mai yafiya akan ko wane irin mutum idan yayi maka laifi, kaima sai Allah ya gafarta maka, miliyan nawa ne ka kud'in ? Dikko ya karasa maganar tare da tambaya, Cikin kwantar da murya Bello yace miliyan biyar ne na zuba, Dikko yace tou kai Sani kuje dashi ka bashi miliyan goma, a rik'a hak'uri kaji bawan Allah, gyara zama Bello yayi tare da cewa kayi hak'uri gaskiya ni ko miliyan d'ari zaka bani wallahi basu ne gabana ba a yanzu kawai so nakeyi ka ramamin abinda ubanta yayi min. 'Daure fuska Dikko yayi domin duk cikin k'arfin hili yake magana, shi duk duniya babu abinda ya tsana irin mutum yace ya wulakanta shi, danne zuciyarshi ya sakeyi tare da cewa kayi hakuri gaskiya Dikko baya neman mata, Kayi hak'uri ranka ya dad'e ka ganta ko so d'aya ne nasan zatayi maka, kai jeka taho da ita da sauri, duk Bello ya fad'a ba tare daya bari Dikko ya sake cewa komai ba danshi Dikkon ma harya gaji da magana yayi shiru. Kamar wata b'arauniya haka ya jawoni har yanzu idona a rufe yake, lallausar kafet in dana taka da wani sanyi mai shiga jiki sai wani irin daddad'an k'amshi mai dad'in shak'a naji, hakan ya tabbatar min an kawoni inda za'aci mutunci na, har yanzu banyi magana ba amma idona ya cika da hawaye dan da ba'a rufemin idona ba babu abinda zai hana na cika d'akin da kuka..... A gaban Dikko aka durk'usar dani, amma shi ya kauda kanshi gefe d'aya bamu yake kallo ba, hankalin shi yana kan T V danma baya so ya kalli ko wace ce aka kawo dan babu zuciyar wanda shed'an bazaiyi wasa da ita ba, Bud'e min fuska akayi da sauri na bud'e duk girman idanuwana na fara kalle kalle, innalillahi na fad'a a fili a lokacin da idonuwa na sukaci karo da *Dikko* tare da fara k'ok'arin mik'ewa, Har yanzu Dikko bai juyo ba, dan haka nayi shiru dan karyaji magana ta, hijabin jikina suka ciremin da hular da na saka saman kaina, sannan aka turani saitin inda Dikko ke kallo, gaba d'aya kunya ta kamani dan haka na duk'ar da kaina k'asa, Dikko bai kalleni ba, kuma baiyi magana ba, inaa tsaye a wurin kaina na kallon k'asa hannuwana kuma suna d'aure ta baya na, ina tsaye a wurin shima Dikko bai dainaa kallon T V ba dan har yanzu bai kalleni ba bare na tabbatar daya ganeni ko bai ganeni ba, Shiru kowa yayi babu wanda ya sake magana har kusan tsawon awa d'aya, Bello ya gaji yace ranka ya dad'e zamu koma, yanzu ma kai ya jinjina ma Bello , matsowa Bello yayi a kusa da Dikko ya ajiye ledar daya zo da ita sannan yayi magana banji abinda yace ba, amma wannan karon Dikko bai ko motsa kanshi ba, fita sukayi suka tafi, shima wanda yayo mana jagora bin bayan su Bello yayi Dikko yace idan ka fita kaja man k'ofar, Cikin girmamawa yace tou, yana fita yaja k'ofar gam wanda rufeta yasa naji wani irin tashin hankali na saki baki na fara kuka da dan Allah kayi hak'uri kar muyi haka dakai, mugu kenan yaji mugunta dan haka ya fara murmushi, ashe ma yafi kyau idan yana murmushi, 'Dan wasa yayi da idanuwan shi sannan yad'anyi motsi da kanshi kamar yaji kid'a, saida ya k'ara k'ayataccen murmushi sannan ya d'aure fuskarshi kamar baisan miye dariya ba, ya tsareni da idanuwanshi masu sa mutum yaji yanajin fitsari, da sauri na mayar da kaina k'asa gabana yana ci gaba da bugawa. Wayarshi ya d'auka yayi danne danne sannan ya k'ura mata ido, d'an tab'e bakinsa yayi a daidai lokacin daya kara wayar a kunnen shi yana cewa duk duniya me mace "yar matshi ya ta tsana ayi mata ? Kallona yayi sosai sannan yace 16 zuwa 17, mai maganar a waya ya dad'e yanawa Dikko bayani, murmushi Dikko yayi har saida kyawawan hak'oransa suka fito sannan yace yayi tare da ajiye wayar, Mik'ewa yayi bayan ya gama wayar ya kulle k'ofar da makulli ya tafi dashi ciki ya barni anan falo tsaye kamar wata gunkiya, Bayan kamar wani lokaci mai tsayi ya dawo, inda ya zauna da farko a wurin ya sake zama sannaan yace min zo nan, babu musu naje gabanshi na durkusa kamar yanda naga anayi mishi, Ya sunanki ? Suna na Sultana, da Allah me kike so nayi miki wanda zai tabbatar miki dani d'an Babana ne, shiru nayi bance komai ba, gyara zamanshi yayi tare da mik'e k'afarshi ya taka saman kafad'a ta, yace ina saurarenki. Kayi hak'uri don Allah sharrin zuciya ne, to kinga kin kasa ba zuciyarki hak'uri a lokacin dana b'ata miki , ni yanzu waye zai ba tawa zuciyar hak'uri ? Kayi hak'uri don Allah insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba, kayi hakuri don Allah, kwantar da kanshi yayi jikin kujera yana nazari har yanzu k'afarshi tana kan kafad'ata, ba tare daya taso ba yace gaskiya kamar zan hak'ura amma na fasa, Dan Allah kayi hak'uri, tasowa yayi tare da cewa wallahi bazanyi hak'uri ba yau zan nuna miki cewa ni d'an Babana ne, kuma da kanki zaki sheda ya iya haihu a daren nan zuwa safiya zaki anshi hukunci mafi munin hukunci, zan baki mamaki kuma zan nuna miki Dikko ba sa'an wasan yara bane, zan biga tambarina a zuciyarki za kiyi ta kuka daga yau har zuwa ranar mutuwar ki, yanayin farin ciki ko damuwa duk wanda kika shiga wallahi baza ki manta da Dikko ba a rayuwarki, dani dake kinga saiki fad'amin waye ciwon zuciya zai kama..... Ka rufamin asiri, ke yarinya ya fad'a tare da takamin bakina da k'afarshi, da sauri na janye fuskata gefe guda tare da goge bakina da kafad'ata, kam balasti kafatace kike gogewa baki ? Tou bari kiji in fad'a miki wannan k'afar tafi ubanki tsafta, tafi uwarki ni kuma nafiki banza kazamiya d'iyar d'an caca, saboda san duniyar da bata da tabbas ubanki ya anshi kud'i ya bada ke, mutunci da ko wace "yar mutunci da iyayen mutunci suke tattalawa amma ke ya siyar dan biyan buk'atarshi, Da sauri na kalli Dikko raina amatuk'ar b'ace nace gaka babban d'an iska da zakayi fasik'anci dani a cikin gidanku, ni ba fasik'i bane yarinya ki tambaya kiji ni babu mata a tsarin rayuwata shi yasa bana sabgarsu, amma kedai yau sai nayi miki kaca kaca wallahi yanda ko sunan Dikko kikaji sai kinyi fitsari, ya kara sa maganar tare da sake maida k'afarshi ya takamin baki, Sake janye k'afar nayi daga bakina na k'ara juya kaina gefe, dariya Dikko yayi tare da sauko kafarshi saitin k'irjina ya taka tare da tura babban d'an yatsan shi cikin riga ta sannan yaja da k'arfi, b'earr k'arar yagewar rigata, cika idona yayi da hawaye kuma ga hannu na d'aure ta baya, dan girman Allah kayi hakuri karka ciremin kayana, Sai k'ara tattakani yakeyi, gajiya nayi da iskancin shi nace sakaran banza kwance min hannuna na kaga yanda zanci k'aniyar ka a daren nan, 03/08/2019 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 6 Idan na kunce ki zaki iyamin wani abu kenan ko ? Eh na fad'a cikin kwarin guiwa, Murmushi yayi kad'an da gefen bakinshi sannan ya kuncemin hannu na, mik'ewa nayi da sauri na d'auka hijabina na saka, sannan nayi hanyar fita da gudu, Dukan k'ofar d'akin na farayi tare da kwarara ihu a kawomin d'auki, Dikko bai sake bi takaina ba ya tashi ya shige ciki, dan yasan inda nake ihuna banza ne kururuwata wofi... Alwallah yayi bayan ya shiga yai kwanciyar shi, duk abinda Dikko zaiyi bayayin shi kai tsaye zai dad'e yana tunani idan yayi abun bayan wani lokaci me zai haifar mishi ? Yana duba duk abinda zaije ya dawo kafin ya aikata..... Ni kuma gajiya nayi da doke doken k'ofa na zauna a wurin saboda har muryata ta shak'e tama daina fita sosai, a wurin na zauna har asuba banyi bacci ba ina zaune, Koda asuba a gabana Dikko ya fito da jallabiya brown a jikinshi da hula fara wacce ake cema tashi da kwakwa hannun shi d'aya a aljihu d'ayan kuma rik'e da makulli, bud'e k'ofar yayi da makullin ya fita, kuma yana fita yasa makulli ya rufe ta waje, Nima tashi nayi na shiga ta hanyar dana ga Dikko yake bi yana tafiya, hanyace doguwa sosai ta tafi d'od'arar tasha tayils sai kyalli yakeyi mai d'aukar ido, sai tukwanen shukoki da suka sakani tsakiya, wato wasu a gefen damata wasu a haggu na, Ina zuwa k'arshe naga hanya ta rabu biyu, daidai bangon da hanyoyin suka rabu kuma anyi rubutu wanda bansan abinda aka rubuta ba, saidai zuciyata ta gargad'eni da na tsaya karna fad'a inda zan kashe kaina. Dole naja na tsaya daga nan, zama nayi a wurin, ban wani dad'e da zama ba Dikko ya dawo, a daidai inda nake zaune yace taso muje ya fad'i maganar ba tare daya tsaya ba, Da sauri na tashi nabi bayanshi dan zuwa wannan lokacin zuciyata ta tabbatar min babu abinda Dikko zaimin, yanayin shi abinda na lura yanayin abu na mutuntaka, yana da ruwan mutanen kirki kila zai tausaya min. Allah ka azurtamu shine abinda na fad'a a zuciyata yayin da na shiga d'akin Dikko, banda cikakkiyar natsuwa a wannan lokaci shi yasa ban wani damu da abinda d'akin yake ciki ba, saman kujera ya zauna tare da cewa ga wurin wanka can ya nunamin da hannunshi, Ki fara wanka sannan kiyi alwalla, zaki ga ruwa yana nan na zuba miki dan karki je kiyiwa mutane kauyanci, a inda ruwan yake anan akeyin wanka kuma karki sake kimin fitsari a ciki, Banza nayi na kyale d'an iska na shige, saida nayi fitsari na a inda yace baya so sannan nayi wanka nayo alwallah na fito, wurin da zanyi sallah ya nunamin ina kabbara sallah ya shiga toilet in, Jinjina kanshi yayi sannan ya fito ranshi a matuk'ar b'ace , ko ya akayi ya gane nayi fitsarin oho ! Rashin sani ashe ya gwada ni ne yaga idan ya kyaleni bazan sake mishi rashin kunya ba, idan ya tabbatar banyi fitsarin ba zai fitar dani na tafi gida, A fili yace shawar dare zan d'auka kawai, ledar da Bello ya ajiye mishi jiya itace ya d'auka ya fita, ashe maganin maza ne a ciki, Bello yace masa duk wanda yayi masa a ciko tou shi zaisha guda d'aya, shi kuma a nashi tunanin ko wanne zaisha guda d'aya a ciki, Duka magungunan nan babu wanda Dikko baisha ba, bayan ya gama sha ya shigo, a lokacin na gama sallah ina zaune wurin da nayi sallah, gyara labuleye ya farayi lokaci guda duhu ya fara bayyana a d'akin, kashe hasken fitilar dakin yayi lokaci guda yanayin d'akin ya koma kamar dare, Bansan ya taho ba saidai naji an rik'oni cikin duhu, saida ya rik'eni sannan ya mik'ar dani tsaye amma baiyi magana ba, fitilar wayarsa ya kunna sannan ya sakata a aljihun gabar rigarshi, Kamo fuskata yayi a bakina ya cuccusa min wani abu sannan ya nad'e bakin da salitaf, hijabina da zanin jikina ya cire ya zubar awurin, ganin da gaske yake yasa naji wani irin k'arfi yazo min na kwace na fara kai duka ba tare da nasan inda yake ba saboda duhun da d'akin yayi, So d'aya na sameshi kawai ya rik'e hannuwana duka yace ni kika daka ? Waye yace miki ana dukana ? Murd'e min hannu yayi saida yayi k'ara sannan yace ko a gidanmu ba'a tab'a dukana ba kuma babu mai min kallon banza kowa so yake ya kyautata min dan insan dashi. Ke kuma kimma samu Dikko a arha har wani kai mishi duka kike ? Zanyi maganin rashin kunyarki yanzu nan. Hannun daya murd'e shine ya jani dashi har zuwa bakin gado, jefani yayi saman gadon zuwa wannan lokacin ko motsin kirki bana iyawa saboda murd'ewar da yayi ma hannu na, shima jallabiyar shi ya cire tare da hawowa saman gadon. Gaba d'aya Dikko ya zare hankalinshi da tunaninshi ya fita daga jikinshi, babu wani sauk'i bare tausayi ya nufi hanyar masar ba tare da tunanin komai ba, Wata irin gumza nayi a lokacin da Dikko ya shigeni, jikina yana kyarma saboda azaba nasa hannu na mai lafiya na kware abinda ya rufemin baki, nace kaji tsoron Allah karka b'atamin rayuwa ka rufamin asiri dan girman Allah, ko saurare na baiyi ba, da hannu na mai lafiya dashi na fara yagushin Dikko tare da cizo, nayi kuka na bashi hak'uri amma kamar an watsa ruwa a k'asa, dan gaba d'aya tunanin Dikko ya b'ace saboda duk abinda nake masa bayaji, cizo da yagin ma kamar ina yagin karfe kwata kwata bayaji. Tun ina iya Allah ya isa, cizo yagi har k'arfina ya k'are na gaji na daina bai barni ba, wata irin azabtuwa nake sha wadda tunda nake a duniya ban tab'a jin irinta ba, haka kuma bazan iya musulta girman azabar ba, wai yau nice akayi ma fyad'e, wannan bala'in ne Zainab ke zuwa ai mata a bata kud'i ?....... Wurin kamar kimanin 12:45pm dukan k'ofar d'akin Dikko akeyi babu sauk'i, kuma har zuwa wannan lokacin Dikko bai kyaleni ba, na suma na dawo bansan adadi ba, baida niyar bud'e k'ofar kwata kwata, magana mai dukan k'ofar ya farayi cewa wai har me kakeyi ne baza ka bud'e k'ofar ba. Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, yai ta maimaitawa, tare da sauka daga saman gadon, ta jikin tagar d'akinshi ya lek'a a bayyane yace Dady...... Gajeran wando ya saka sannan ya kunna fitila, jawoni yayi daga saman gadon ya sauko ni k'asa sannan ya bud'e loka na bedsite ya d'auko gishiri, saida ya cikamin bakina da gishiri sannan ya zubamin ruwa a baki na hakan ya bawa gishirin damar narkewa yaci gaba da gangarawa cikin mak'oshina. Dakel na bud'a idona na kalli Dikko, tsoki yayi tare da cewa munafikar Allah bari kallona dan uwarki..... A hankali na maida idona na rufe, k'asa yajani har muka fito daga d'akin kuma har yanzu ba'a daina dukan k'ofar d'akin ba, Wani d'aki daban ya kaini ya ajiyeni, sannan ya kulle da makulli, saida ya goge inda jini ya b'ata daya jawoni sannan ya koma d'akin daya b'atamin rayuwa, zanin gadon ya cire ya tafi toilet dashi, Bai wani dad'e ba yayo wanka ya fito, saka kayanshi sannan ya bud'e k'ofar, hannu Dady ya mik'a wa Dikko suka gaisa yace masa Babana baka tashi ba ? Na tashi..., tou lafiya baka shigo ciki ba ? Me yake damunka ne ? Ba komai Dady, sosai Dady ya sake kallon Dikko sannan yace mu shiga ciki, Duk yanayin fuskar Dady ya canja zuwa na damuwa, jan Dikko yayi suka zauna har yanzu yana rik'e dashi a jikinshi yace Babana fad'amin abinda yake damunka, Dady nace babu, to miya hanaka shiga ka gaisheni, ba komai, tab'a jikin Dikko yayi cikin damuwa yace tou mi yake maka ciwo ? Kanka ne ? Ko bacci kake ji ? Shiru Dikko yayi duk abun duniya ya dameshi, Dady kad'ai yaketa ma Dikko sannu, yana san Dikko fiye da yanda kowa yake san d'anshi, yana tattalin Dikko ko ina Dady baya san Dikko yana zuwa dan duk fitar da Dikko keyi Dady baisan yana fita waje ba, yana lallab'a Dikko sosai gani yakeyi kamar Dikko zai mutu ya barshi, kullum addu'ar shi Allah ya k'ara kare mishi Dikko ya shirya shi ya albarkaci rayuwarshi, saboda d'a d'aya tsotsai gareshi. Yana da "ya "ya sunkai sha biyar amma duk mata ne Dikko ne kadai na namiji a gidanshi. Taso muje, Dady ya fad'a tare da dafa kafad'ar Dikko suka fita, cikin gida suka shiga, tunda suka shiga k'annen shi suka fara cewa Yaya munce ma Dady lafiyar ka qalau yace saiya ganka zai fita, kallonsu kawai yayi amma baima kowa magana ba, suma basu damu ba tunda halinsa ne shariya, sai kayi ta mishi magana ya kyaleka kamar bayajin ka. Gishirin da Dikko ya zubamin a baki nake ta tofarwa amma rabi ya riga ya gama shigewa cikin cikina, kuka nakeyi mara sauti, duk ilahirin jikina ciwo yakemin, ga kaina kamar zai fashe saboda rashin bacci da kukan da nayi. Haka na yini zubur babu Dikko ba labarinshi, ga ciwo da nakeji a k'asana kamar zai fita saboda azaba, kuma d'akin da nake babu toilet a ciki duk sallolin da akayi na yinin ranar nan inajinsu amma tun sallah asuba ban k'ara wata sallah ba. Sai dare sosai Dikko ya bud'eni, shigowa yayi yana waya, wallahi dawowa ta kenan naje Abuja kwata kwata na manta da yarinyar nan saida nayi alwalla zanyi sallah magrib ta fad'omin a rai, ko Dady basai na dawo ba kuma ina ajiyeta zan koma , ....... A , a, 06:30am ne, ai bana so Dady yaji ban tafi ba kasan yanzu sai ya shiga damuwa, bada driver nake ba, tou kudai ku sakani addu'a , yana gama wayar yace ke da Allah tashi muje, munafika kinja min tafiyar dare, daka min tsawa yayi tare da cewa ki wuce mu tafi kina b'atamin lokaci dare yana karuwa, K'iri k'iri na kasa tashi, kaina sai juyawa yake ga wani irin amai dake kai kawo tsakanin zuciyata da cikin cikina, jiki na yana kyarma nace masa bana iya tashi..... Na k'arasa maganar hawaye na zubomin daga cikin ido na, Zan tafi idan kin tashi kin basu labarin abinda ya kawo gidan nan ni kinga tafiyata, ya juya zai tafi nace dan Allah zan tashi, juyowa yayi ya kalleni sannan yace tou taso ya fad'a cikin sigar lallashi, Dakel na iya tashi amma a duk'e nake na kasa mik'ewa tsaye, yanayin fuskar shi ya nuna tausayi, akwai zafi ? Ya tambayeni, banza nayi dashi bance masa komai ba, murmushi yayi tare da cewa ki sameni ta baya, kuma kiyi hankali karda a ganki, Dakel nake tafiya har nafito, a lokacin harya d'auko motar daga inda ya ajiyeta, ina k'ok'arin shiga yace in tsaya kar in b'ata motar, ciki ya koma ya sake gyaggyara inda na b'ata sannan ya d'auko wani k'aton zani ya taho dashi, inda zan zauna ya shimfid'a sannan yace shiga, Shiga nayi na zauna ya rufe k'ofar tare da zagayawa shima ya shiga, waya ya kira yace gani nan zan fito bud'e min get in, yana fad'a ya ajiye wayar ba tare daya kashe ba, Da gudu yaja motar kamar zamu tashi sama muka tun kari hanyar fita, a daidai get ya tsaya sukayi ta masa addu'a da fatan alkairi ya amsa da amin sannan muka fice, hanyar filin gidanmu ya nufa, babu mota ko d'aya a hanya bare machine haka ya tabbatar min da dare yayi sosai, Lokaci lokaci nakan goge hawaye, tare da Allah ya isa zuciyata, saida ya kusa zuwa gidanmu ya tsaya yace ke sauka haka nan, kama murfin motar nayi sannan na kalli Dikko nace Allah ya isa ban yafe maka ba mugu azzalimi d'an isa mai bakin mata, murmushi Dikko yayi sannan yace ngode, Kuma ko zaka mutu bazan tab'a yafe maka ba, Dikko yace tou, in Allah ya yadda saika had'u da tashin hankali a hanya, bazan had'u dashi ba in Allah ya yadda, tsoki nayi tare da bud'e motar na fita, tillomin zanin dana zauna akai yayi a daidai lokacin da nace kuma wallahi sainayi k'arar ka, babu damuwa ina jiranki, azzalimi , murmushi yayi tare da cewa naji ba komai duk abinda zaki ce ki fad'a nidai nasan na more miki har abadan duniya, gwallo yayi min tare da jan motarshi ya barbad'eni da k'ura..... Wani irin bak'in ciki ya kamani nayi wani irin ihu daga nan ban sake sanin inda kaina yake ba saidai na farka na ganni kwance a gadon asibiti, an d'aure hannuna wanda yaji min ciwo, anmin dinkuna a k'ark'ashi na, Zainab itace ta zauna tare dani a asibiti dan Inna tunda taji abinda ya faru tayi tafiyarta tace ta gama auren Baba har abadan duniya, Sati na d'aya a asibiti aka sallame mu muka dawo gida, Babana kuma kunya tace ta koreshi babu wanda yasan inda ya tafi, tunda na dawo na samu labarin Inna ta tafi ban wani ji sha'awar binta ba, na hak'ura na zauna cikin "yan uwana. Naje nayi k'arar Dikko wurin "yan sanda abinda ma na fahimta sumo so suke suyi irin abinda Dikko yayi dani, dan haka na hak'ura na dawo gida. Babu ranar da zata zo ta koma ga Allah ban fad'owa Dikko a rai ba, ya shiga damuwa da tashin hankalin abinda yayi min, yaji bak'in ciki tare da tambayar kansa mi yasa yayi zina ? Mi yasa nayi ? Mi yasa,.....???? Wani lokaci haka zai zauna yayi ta kuka yana mai jin bak'in ciki da nadamar aikata abunda yayi, ya tambayi kanshi so babu adadi wai miye amfanin abinda yayi ? Yin hakan meya haifar ? Dadin me yaji ? Wane rayuwa yarinyar mutane zata shiga? Mi yasa saishi ne Bello ya zab'a ya farkewa Sultana mutunci ? Tabbas ya yadda ya zama babban mahauci iliminshi baida wani amfani baida banbanci da jahili, Kullum addu'a Dikko yakeyi Allah ya yafe mishi akan abinda yayi min,zuwa wannan lokaci ya fara tunanin ko ya sanar da Dady abinda ya faru kila zai bashi shawara tunda babu abinda suke b'oyewa juna, Ko isashshen bacci Dikko baya samu, daya kwanta shashkar kukana yake tashin shi daga bacci, a fili yayi magana cewa baiwar Allah kiyi hak'uri ni wannan na d'auke shi matsayin k'addara tunda nake a rayuwata Allah ma ya kulle min idona da zuciyata akan mata, Wallahi ko labarin mata bana so anayi a gabana, ban tab'a zina ba kuma wallahi ban tab'a jin sha'awarta a zuciyata ba, Allah yayi min kyankyami da tsoron sab'a masa , amma ya akayi banji kyamar yarinyar nan ba, na sab'awa Allah mi yasa na kasa control in zuciyata mi yasa wai..........? Dan Allah ki fita daga rayuwata ki barni, kiyi rayuwarki inyi tawa, hawaye ne suka sake tsirarowa daga cikon idonshi, cikin kuka yace ya Allah na rok'eka dan arzik'in annabi Muhammad S. A. W ka mantar min da lamarin yarinyar nan daga zuciyata, ka hanata zuwa man cikin bacci ta daina min wobuwa idan ina cikin mutane wallahi ina iya haukacewa, A b'angare na kuwa, zuwa yanzu na shafe babin Dikko a rayuwata, akwai wani d'an uwanmu da yake so na, kuma yayi alk'awarin aurena dama tunda ya fara zuwa Baba yace mishi ya bashi ni amma babu maganar zance kawai dai idan na isa aure zai aura mishi ni. Shima yaji labarin abinda ya faru dani, kuma yazo wurina, ya tambaye ni da gaske ne ko wasa ? Da farko naso na b'oye masa, amma daga baya kawai na fad'a masa gaskiya, yacemin tou shi gaskiya bazai iya aurena ba inyi hak'uri, ban wani damu ba nace Allah yasa haka shi yafi min alkairi a rayuwata. A hankali magana ta fara zaga gari, anyi min fyad'e kuma wanda yayi min fyad'e d'in ba'asan ko waye ba, amma asibiti sunce ina da cutar H I V, duk abinda na tab'a a gidanmu babu mai k'ara amfani dashi, duk wacce na zauna kusa dashi sai ya tashi, idan na fito mutane da sun ganni sai su dare.... Ko a familyn mu kowa baya shiga sabgata, kyara da tsana ake nunamin kamar mayya, ga mahaifiyata tayi tafiyarta garinsu, Baba bansan inda ya tafi ba, na rasa abinda yake min dad'i a duniya, banda mai bani abincin da zanci duk wanda naje wurinshi saiya koreni, azaba ta isheni na fara sana'a babu mai siye, Koda naje na fad'awa Amisty abinda rayuwata take ciki da fyad'en da aka min amma ban fad'a mata Dikko bane ba, shawara d'aya ta bani, shawarar kuwa itace, sana'a d'aya zanyi inyi arzik'i ba H I V gareni ba ko kabari ce ni sai an shigeni, Wace sana'ace ? Murmushi Amisty tayi tare da cewa zan kaiyi wurin uwar d'akina in yankar miki form zata baki lectures, lokaci guda zaki goge idonki ya bud'e zaki ga yanda maza zasu rik'a layi akanki,..... Idan sunyi layin me zan basu ? Abinda kika bawa wanda yai miki fyad'e,............... Taku a kullum. *JAMILA MUSA* 03/08/2019 Ku kulle marecen ku da wannan.......... Ku biyoni sannu a hankali danji dalilin da yasa na kira wannan labari da *KWARATA* nazo kuma nayi masa in kiya da *KALU BALE GARE KU MATAN AURE.............* ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* *_Ina miki sannu da gajiya fatan kin koma gida lafiya ? Ngode sosai Allah ya bada ladar zuminci ya kuma hutar da gajiya RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE_* 🅿 ------ 7 Haba Amisty wannan ai ba mafita bace, Sultana kenan wannan kuwa itace babar mafita, domin mazan yanzu yawancin su yanda kika san kura da nama haka suke akan mata, d'aid'aikun su ne Allah yatsare su, sai kuma wanda suka had'u da jajirtaccin mataye. Ni nan da kika ganni Sultana nasan abinda nakeyi kuma haka nasan irin mazan da nake tarayya dasu, banajin kunya asan ni "yar iska ce haka kuma bana b'oyon iskancina dan ta haka ne kad'ai za'a san ni karuwar gidan ce har na samu costomers. Na samu dubban kud'ad'e ta hanyar karuwanci ban san adadi ba, dubu goma dubu ishirin ga kud'ina kuma inji dad'i abu na babu wanda yaji ba wanda ya gani, in rik'e babbar waya irin wacce nake so haka kuma in d'inka sutura da talakalmi da jaka, abu d'aya yasa ban sayi motar hawa ba saboda bana so Baba ya harbo jirgina da wuri amma badan babu ba, Gyara zama nayi tare da tattara hankali na wurin Amisty, nace to ke mi yasa kike sha'awar karuwanci ne ? Murmushi tayi sannan tace gaskiya daga kalle kallen B F tun inajin tsoron abun har ya fara bani sha'awa, Tsare ta nayi da ido sannan na tambayeta a ina take samu ? Tsoki tayi tare da cewa tambaya kamar "yar jarida, idan zakiyi na had'aki da wani mak'ocinmu sakaran banza baisan darajar kud'i ba, kije yai miki yaimin muci gaba da k'wak'wale banza tunda matar tasa sakaryar banza ce, kud'i gareshi na tashin hankali amma matar bata wani iya sauk'e hak'k'insa kinji yanda yake tona mata asiri ? Gata da kyau kamar ita tai kanta amma kyan ya zama hoto tunda mijinta ke neman mata. Tou ke Amisty ya akayi kuka had'u kuma ya akayi yasan kina neman maza ? Hmm yarinya kenan ! Amisty tace min sannan taci gaba da cewa....... Gidan nake zuwa ita kuma bata da wani sirri bud'e take shegen surutu kamar an sakawa radio sabon battery, Kullum naje sai ta bani labarin mijinta d'an jaraba ne, da a tunani na mafad'aci ne, sai nace mata niko sai naga yana da kirki sosai bashi da wata damuwa, sai tacemin ba fad'a na baki ba jaraba kullum zai nemeni daga dare zuwa asuba yakai sau biyar. Cikin rashin fahimta na tambayeta, ban gane ba..... Tamin bayani na gagara fahimta shine ta fahimtar dani ta hanyar nunamin vidio a wayarta, Tana kunna min ta tashi dan zuwa duba girki, ni kuma tuni dama na fara iskanci na amma a lokacin ban dad'e da farawa ba, dan haka tana tashi na sace number mijin a wayarta, tunda iskancin kawai nakeyi a lokacin amma bansan fa'idar abun ba...... Tana madafar abinci naje na bata wayarta nayi mata sai anjima, ina fita ba gida na tafi ba kawai na sharce wurin uwar d'akina, wadda nace miki zan had'aki da ita kema ta mayar dake gahurtacciya kuma abun kwatacce a harkar barikanci. To ita naje ta sake bani haske a harkar, dan haka ina dawowa gida na fara tura masa sak'on gaisuwa ta whatsApp. Shareni yayi bayan yaga sak'on baiyi reply ba, ni kuma na nace na kwakwafe banyi zuciya ba naci gaba da aika sak'on, kusan sati biyu babu wani bayani, dan haka na fara tura mishi da irin vidios in B F da nake kallo na tura mishi masu zafi da yamutsa tunani dan wani lokaci sai yakai 1:30am yana online. Wai wace ce ? Ya tambayeni bayan yaga vidio inyi, nima basar wa nayi ban bashi amsa ba na sauka online, ina sauka yana kirana a waya..... Murmushi nayi a bayyane nace ashe kuwa mayen ne ? Mu zuba dani dakai..... Kuma ban d'auki wayar ba, Text ya turomin ta inbox, kamar haka.... _Wai wace ce ke ? Ki hau Online muyi magana don Allah !_ _Ai nayi fushi nima....._ Shine amsar dana bashi, _Kiyi hakuri don Allah ki hau online muyi magana_ Shareshi nayi na kashe wata duka nayi kwanciyata...... Saida na kwana biyu wayata na kashe, ranar dana bud'e wayar kuwa sak'onsa ne yai ta shigo babu iyaka, wasu na duba wasu kuma na share. Ko online dana hau sak'unan sa birjik, dan haka naci gaba da tura vidion iskanci, kuma idan natashi sai tsakar dare nake turawa, jakar tana can tana bacci, A hankali ya saba dani, amma ban fad'a mishi kaina ba, yau da gobe bata bar komai ba, har na tambayeshi dalilin da yake kai tsakar dare yana chat, kawai cewa yayi yana da damuwa da iyalinshi, bata bashi hak'k'inshi wai tace yawan sex da mace yana sa tayi saurin tsufa.... Amsar dana bashi itace, ya barta can ta k'unshe abunta har yayi wari, indai yana da buk'ata tou ni zan rik'a bashi nawa duk lokacin daya buk'ata, kinji shine fa idan bata nan nake zuwa gidan muyi komai namu cikin sirri. 'Dan gajeren murmushi nayi sannan nace Amisty kenan...... Idan dai har bin maza zanyi tou pha tabbas babu macen data bini ilimin iskanci, kinji hausa suna cewa d'an gado saiya zarta, nawa ba kalar naku bane, saboda naku iskanci mai arha kukeyi, tunda har banji kunyar mahalicci ba na tsab'a masa babu abinda zaisa naji kunyar wani banza, Hannu na nakai saitin prvt prt ina sannan nace idan dai wannan ne abinda maza suke buk'ata ni kuma duk saina halaka da yawansu dashi, kallon Amisty nayi sannan nace, babu wanda ya koya min saishi d'aya, ban fara ba shine ya fara, ban iya ba yayi da k'arfin bala'e, ba'ayi da zafi yayi min saboda k'eta, ke Amisty karki manta a caca aka sakani duk saboda talauci idan har ban tara kud'i ba ta sanadiyar karuwanci nayi suna a duniya lallai ni ba d'iyar Aliyu Binnaa bace, Tunda har ya bada budurci na saboda san duniya ni kuma zanci gaba da basu su bani dan na tara mishi abunda ya buk'ata, Amfanin zunubi roma Amisty, tunda zanyi kawai zanyi amma babu fashi, saidai ki sani akan sab'awa Allah babu namijin daya isa yaga ko pant ina da naira dubu goma ko ishirin, kud'in shigar ciniki naira dubu d'ari ne shine harajin da na yankawa duk mai sha'awar yin iskanci dani, idan kuma zaka shiga gidan dubu d'ari biyar, idan har haka yayi tou na siyar idan haka baima mutum ba tou ya tattara buk'atarshi ya koma, Amma tabbas duk namijin da yace zaiyi, saiya bada dubu d'ari, idan na yadda yayi idan kuma ban amince da dashi ba zai koma, amma dubu d'arinshi tazo kenan kamar gawa tazo lahira. Ki sani bana iskancin wahala, kuma bana iskancin cini incin tuwo, zan zauna gida bazan bar k'asata ba amma zan zama tarihi a duniyar nan, ki fad'awa uwar d'akin taki cewa ina gayyatar ta shigowa k'ungiyata da nake fatan kafuwarta daga yanzu zuwa ranar da numfashina zai k'are, ki sanar da ita cewa ni banda ilimin boko amma akwai na tsoron Allah kuma sanin ilimin bazai hanani bujire masa ba, nasan hukuncin mazina daga wacce tayi aure har wacce bata tab'a ba, hukunci kisa ga masu aure, bulala ce ga irinmu "yan mata, to anan duniya zan sameta ko sai naje can ? Duk na sani, kuma nasan a ina ake amso su, mik'ewa tsaye nayi tare da dafa wa Amisty kafad'a sannan nace bana buk'atar shiriya, kuma bana so a tausaya min, daga yanzu zuwa lokacin da zan gama kammalawa........, *BARIKI ASSALAMU ALAIKUM* Murmushi nayi sannan nace wa Amisty suna na , MARYAM ALIYU BINNA, na bud'e k'ungiyata daga yanzu, idan kina sha'awar shiga bisimillah, na barki lafiya......... Ina fad'in haka ban sake magana ba na juya na fita daga gidansu...... Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, shine abunda Dikko ya fad'a adaidai wannan lokacin, tare da cewa Allah na tuba.......... 🙏🏻 Ina fita na tare napep nace malam ka kaini kambarawa, can ne anguwar da muke zama. Abinda zan bashi ya fad'amin bayan ni ban tambayeshi ba, Shiga nayi yaja muka tafi, duk inda yaga fasinja ya tsaya zai d'auka cewa nakeyi muje bana so ka d'auki kowa, har muka iso filin gidanmu da yasha ado da darnin kara...... Ina fita na wuce abuna, malama kud'in fa ? Juyowa nayi tare da ce masa nawa ne ma ? 250, murmushi nayi tare da kallonsa k'asa da sama sannan nace naci na Allah bud'a, da kuma tsarinka yamin dana baka wani abu ka kalla sai kayomin ciko, Fitowa yayi daga cikin napep d'in yana fad'in ke zanci uwarki ko ki bani kud'ina, murmushi nayi tare da cewa tayi maka tsufa...... Ina fad'in haka nayi gaba abuna, haya haya ya fara hayani tare da ci gaba da d'uramin zagi irin na "yan tasha. Ja nayi na tsaya ba tare dana juyo ba. Saida ya gama zage zagensa sannan naci tou ka zagi kud'inka, kuma naci na cinyesu duk garin nan inga mai amsar su wurina, kaina yayo da zumar kaimin duka, nace ka dakeni ka dako ma kanka bala'e da kabi ta hankali daka tsira amma tunda iskanci ne abun dani dakai dan iska ka fasa,... Wani mak'ocinmu ne yazo wucewa, na fashe da kuka tare da cewa malam lawal kaga wannan shine yayi min fyad'e, dama nace muku ina ganeshi, yana jin zance fyad'e ya ruga zai nufi napep malam lawal ya fara a kawo d'auki, a tak'aice dai kafin ya bar anguwar bayan yaci shegen duka saida aka fasa mishi gilashin mota na gaba sannan suka k'wak'ule masa cini kin da yayi yabar anguwar a wahalce...... Yana tafiya na shiga gidanmu natashi masifa cewa sai an siyar da filin nan an bani hak'k'ina, yanda na birkice lokaci guda ya bawa al'ummar anguwarmu mamaki, an nuna min cewa ayi kud'i wa filin sai a fitar min da kud'ina su kuma su zauni fili, nace bansan wannan zance ba duka nake so a siyar uban kowa ya kama gabanshi, Tambayata akayi me zanyi da kud'in ?Babu kunya bare shakku nace, karuwanci zan fara shi yasa nake so a siyar a bani kud'i na naje na siyo kayan da zan zama karuwar...... Gaba d'aya wurin salati aka d'auka ! Yayin da wasu dattawa suka fara sulalewa suna barin wurin, ni kuma na shiga cikin gidan naci gaba da yanyara ruwan iskanci na san raina, Bayan kwana biyu mak'ocinmu ya kawo kud'in filin gidanmu domin shine ya siya, aka raba aka bani nawa, sallama nayi musu tare da cewa kuyi k'ok'ori kuna ziyarta na domin inaji a jikina nan da kwanaki kad'an zanyi muku wahalar gani....... Babu wanda ya bani amsa, murmushi nayi tare da tafiyata dan dai nasan nasha dasu.... Nima bak'in ciki yasa nace duka filin za'a siyar dan kar na shiga gararin rayuwa ni d'aya kowa ya lalace dan zuwa yanzu gaba d'aya na koma kamar wata kafira dan babu sauran tausayi a zuciyata...... Bakin titi na fito na samu mai abin hawa, inda zanje ya tambayeni........... Shiru nayi na wani lokaci sannan nace masa gidan karuwai zaka kaini, Kallona yayi sosai sannan yace ina ? Nasan yaji sarai iskanci ne yasa ya sake tambayata, dan haka nace gidan da "yan iska ke zama wanda suka gagari iyayensu, Jinjina kai yayi amma baiyi magana ba, ko har yanzu baka gane ba ? Na tambaye shi ? Shiru yayi baicemin komai ba, ni kuma nace tou ina nufin inda maza da mata ake had'uwa ayi bad'ala, kallona yayi cikin yanayin tausayi sannan yace ke yarinya ki rufawa kanki asiri rayuwar bariki tafi k'arfin ki, aure shine yafi dacewa da rayuwarki, Kai malam zaka kaini ko kuwa dai ? Tashin napep inshi yayi tare da cewa Allah ya shiryaki, amma nikam bana kaiki gidan karuwai, tsoki nayi tare da cewa jeka d'an munafika shege marar rabo... Gaki nan katuwar marar rabo duniya da lahira, indai mazan bariki ne sai sun kasheki murus kin kasa morawa rayuwarki, dan mace bata kashe namiji saidai ya kashe ta, baki san dafin namiji ba da baki hayewa mazan zamani ba kin koma gida, basu da imani haka kuma basa tausayi tunda sun san kud'insu suka biya, tou fa basa sassafta wa kamar mai gidan haya ne da "yan haya, tunda sun san ke ba tasu bace hawa d'aya zuwa biyu zasu tashe ki aiki kina kallon maza suna kallonki amma dan uwarki bazasu ciwu gareki............ Yana kaiwa nan yaja napep inshi yayi gaba. A bayyane nace komi zakace kaje kace saina zama cikakkiyar karuwa, kuma ni karuwanci nawa mai aji zanyi ba irin wanda kowa yake tunani ba. Bai dad'e da tafiya ba na samu abin hawa, kuma na fad'a masa gidan karuwai zai kaini, yace min na ina gidan karuwai d'in ? Nace inda fek'ak'k'un suke can zaka kaini, shigo muje, shiga nayi yaja muka tafi......... 05/08/2019 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* *_Ku nemi naku fitowa ta farko daga shahararriyar kungiya mai san farin cikin makaranta wato BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION, sabon salo ne daga shahararrin marubuta biyu, MAI JIDDA daga alkalamin MARYAM MUHAMMAD HASSAN, MAFARKIN NANAH, sabon sauyi na SA'ADATU LAWAL maman ilu, kar ku sake ku bari a baku labari......_* *_ZAINAB ATTAHIRU B ' K sakonki yazo gareni ngode sosai ina miki fatan alkairi, ki kasance cikin farin ciki da kwanciyar hankali har a busa kaho............_* 🅿 ------ 8 Tafiya mukeyi daga ni harshi babu wanda yayi ma wani magana, saini da a zuciyata nake ta addu'a, Allah na rok'eka ka bani farin jini ka zubamin kwar jini kasa na rik'a bud'ewa mutane ido duk wanda yayi ido dani, Allah kasa wannan kyawun nawa ya zamar min babban jari, kasa nayi suna sosai a harkar karuwanci. Tafiya mai nisa mukayi har muka iso k'ofar gidan, sai yanzu yayi magana cewa ranki ya dad'e anzo, ba tare dana fito ba nace masa, malam ya sunan anguwar nan ne ...... ? Sanin da nayi ma anguwar a da yanzu karuwai sun canja mata suna, gidan na sani ba sunan wurin ba, ki sauka ki bani kud'ina sauri nakeyi. Ina k'ok'arin fitowa nace kasan kana sauri ka bari aka haife ka ? Ka iya tafiya domin dai ni d'abi'ata idan nahau abin hawa gaskiya bana iya biyan kud'i, amma Allah ya taimaka sauka lafiya ! Fitowa yayi daga cikin napep in ya fara ke bansan rashin kunya bani kud'i na ko in wulak'anta ki a wurin nan, d'an gajeran murmushi nayi tare da cewa banda haukar ka wanda ya fito bariki ai baya tsoron wulak'anta, ai ta wulakanta ta kare tunda har na fito daga gidanmu na taho yawon karuwanci........! Shiru yayi ya rasa abin cewa, dan haka nace ko kana da sauran magana ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa jeki kya gani...... Dariya nayi sosai irin ta cikakkin "yan duniya na kashe dariyar da rangad'a gud'a, sannan nace shege kaji uwar bari ko ? Tou babu uwar da zan gani dan duk wani gagararren d'an iska dake fad'in garin katsina nice uwarshi nice ubanshi, duk wani kangararren dan iska da "yar iska da iyayensu sukace jeku kun gani, to wallahi idan suka taho ni zasu gani..... Sauk'i ya nemar min sannan ya koma cikin napep inshi, yana k'ok'arin tashin ta nace malam dakata, tsayawa yayi yana kallona, kana da waya ne ? Rik'e waya ai sai ke da kika fito neman haramun, to naji ba komai, kadai ganni sosai ko ? Kuma zaka iya ganeni gobe idan mun had'u, tsoki yayi sannan yace taya zan manta da fuskarki azzaluma kawai, yawwa ina so dama ka gane ni gobe idan ka ganni, ni suna na Sultana idan kayi gaba ka bada labarina dan ina san cikin d'an k'ank'anin lokaci suna na ya zagaya kaf fad'in garinnan, sauka lafiya.......... ! Ina fad'in haka na shige gidan karuwai, Tun a zauren gidan na farajin kuruwar wata karuwa, karuwinta ne yake dukanta da belt kamar uba yana hukunta d'iyar sa, babu ji babu gani yana dukanta yana cewa dan ubanki sai kin bar gidan nan, wallahi na gama zama dake, d'an murmushi nayi a bayyane nace Allah sarki duniya yayin da wasu ke shigowa yayin wasu ke fita, A hankali nabi gidan da kallo ga mutane nan iri iri, yayin da wasu ke caca, wasu na lido, wasu na shan sigari yayin da wasu ke kwance saman jikin maza babu kunyar Allah bare tsoranshi, wato abinda dai na lura duk abinda kake so shi kakeyi babu mai ce maka dan mine ne ......? K'arewa gidan kallo nayi sosai, d'akuna ne k'asa da sama, bene ya zageye k'asan gidan yayi masa rumfa sai yanayin gidan ya tabbata kamar irin hadari ya taso. Wani irin ihu na zabgaga tare da kashe ihun da gud'a, wanda haka yayi sanadiyyar jawo hankalin duk wanda ke cikin gidan na waje da wanda ke d'aki babu wanda aka bari kowa saida ya fito....... Kirari na fara kwararwa bari ba tare dana kalli dandazon mutanen dake kallona ba. Bariki ba'ayi miki tilas babu wanda ya rako wani kowa da k'afarshi yazo kuma in yaji wuya shi zai koma, baki duba mai kyau ko mummuna, haka kuma babu ruwanki da maye ko mayya mai lafiya da mai cuta duk wanda yazo kina da masaukinshi, baki san inda kowa yake ba amma kowa yasan inda kike, gani nazo ki sakamin albarka, baki da tabbas bariki haka nima bani da tabbas, matsalar ubace ta kawoni amma ina tare da had'ari guda d'aya, bana san shiga sabgar kowa karki sake ki bari wani ya shigo rayuwata, ilimi nazo d'auka a cikinki amma ni nafiki rashin tabbas, ina da masaukin kowa amma banda na mata.....duk namijin da uwarshi ko ubanshi yace jeka ka gani tabbas idan yazo ina da masaukin shi nima, Kija da'irarki ki bani tawa, bana shan sigari bana cin goro, abu d'aya ya kawoni shi zanyi na koma, bansan bincike haka kuma bana san bin kwakwaf, kar ku sake naji bakin wani nan, idan ba amsa zai bani ba, kuma magana d'aya nake so ta fito bakinku akwai ko babu, itace amsar da nake so a bani, tambayata itace kawai d'akin zama ko nayi gaba.........? Wani daga can saman bene yace ke "yar cakulkula dake har kin san dad'in namiji ? 'Daga kaina nayi sama na kalleshi sannan nace daga ganinka gidan haya aka haife ka, kaine matsala da kanka bakaji abinda nace ba ? Akwai ko babu kawai nake so naji. Daga bayana wani yace ki bashi amsar tambayar shi mana sai mubaki taki, murmushi nayi sannan na d'aga kaina sama na kalleshi tare da cewa, duk tayar abun hawa sunanta taya, amma kaga tayar daf tafi ta jirgi girma amma abinda jirgi zai d'auka daf bata iya d'auka, jirgi ya d'auke ka kuma ya d'au kayan ka, kamar dai kai kaga ga jibgegiyar mace a gefenka, amma a zahirance gwaram ce tunda har ka samu damar fitowa, saboda haka k'aranta ba matsala bace, abinda wata motar ta kasa sai kaga machine yayi. Tabbas muna da masaukin ki, d'aki d'aya 5k ne a wata haka kowa yake biya sai kuma zaki bayar da kyautar dare d'aya ga mai gidan wannan shine tsarin wannan gida me kika ce ? Wannan ba damuwa bace amma nima ina da nawa tsarin na basu amsa, muna saurarenki suka bani amsa, gyara tsayuwa nayi sannan naci gaba da cewa ina da ranakun aiki ina da na hutu, yau da gobe da jibi daga nan har zuwa k'arshen satin nan babu maganar kwanciya da ko wane na miji amma zai yadda daga nan zuwa sati na gaba.........? Nayi musu haka ne dan ni kwana ukku kad'ai zanyi na k'ara gaba abu d'aya zuwa biyu nazo koya kad'ai a gidan karuwai kuma a raina bazan biya kud'in hayar ba haka na yanke.. Na saman benan yace min mi yasa kike da wannan tsarin haka ne An mata.......? Wata irin fad'uwar gaba naji tare da kallonshi da sauri domin ya kirani da irin sunan da Dikko yake kirana dashi, janye zance Dikko nayi a raina sannan nace idan har ruwa ya kare a cikin tanki ko ka tara abun ibar ruwa baka samun komai haka nan zaka gaji da jira ka d'auke, amma idan aka bari ya taru kana tarawa zai cika ma duk abinda kake buk'ata, to nima haka take daga gareni karfina ya k'are dan na kwana ina aiki saboda haka a barni na huta na kwanakin dana iba, Murmushi yayi tare da cewa gaskiya ku bata d'aki tabbas muna da masaukin ki a gidan nan, sakaran banza na fad'a a cikin raina nace otiho dakai baka tsan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, duk shelar da nayi na ce bariki tafini tabbas ka gagara ganewa da gaanin wannan sha ka tafi ne, fuska ta d'auke da mugunta nace mashi idan an bani d'akin kai ka biya kud'in sannan kuma ka bani rance dubu d'ari, tukuicin d'aki zaka kwana biyu kana morewa dani nima daga cikin irin baiwar da Allah ya bani, dubu d'arin ka kuma da kud'in d'aki duk zan baka su idan na fara kasuwa...... Ba damuwa a bata d'akin sama lamba 59 ya fad'a cikin zaguwa, ga *kwartuwar* shi gefe ya manta da labarinta, hawa sama nayi aka nunamin d'akin, makulli aka bani na bud'e na shiga ina shiga na kulle d'akin ta ciki. Dudduba d'akin nayi bayan na shiga, falo ne sai d'akin bacci madafar abinci da bayi, d'akin bacci katifa ce irin ta "yan bodyn sch, falo tayils ne babu kujeru sai kafet, k'arewa d'akin kallo nayi sannan na koma jikin tagar d'akin na fara kallon yanda *karuwai* suke rayuwarsu. Ina tsaye na fara tunanin fuskar da tacemin An mata, ina k'ok'arin tunoshi kwalwata ta fara jakkancin data saba, a bayyane nace ki saurara kar kimin haka don Allah rayuwa mai had'ari na kawo kaina ki tausamin ki sanar dani ko waye waccan, kwana biyu kad'ai zanyi nabar gidan nan amma ina so ki sanar dani ko waye shi d'in...... Bugawa zuciyata tayi tare da cewa abokin Dikko ne wallahi, shine ya raka abokin Babanki aka kaiki wurin Dikko....... Kamar kasuwa haka zuciyata da kwalwata suka fara gardama hayani ke tashi daga cikin kwalwata da zuciyata, yayin da kwalwata ke cewa bashi ne ba zuciyata tana cewa tabbas wallahi shine, kyarma jikina ya farayi gaba d'aya d'akin naji yana juyamin, kamar ana jijjiga ni naji anayi dan haka da sauri na dafa bango na zauna k'asa tare da fara karanto duk addu'ar data zo bakina...... Bayan na samu natsuwa ne, na dafa daidai saitin zuciyata da kwalwata sannan nace idan nayi muku wani laifi da Allah ku gafarceni amma ku daina dakushe wa ku barni nayi komai cikin hikima kamar yanda na tsara zanyi. Kuyi hakuri ku daure ku bani gudamwa. Kwana na biyu a gidan karuwai ina koyon abinda yakaini, safe rana dare wannan d'an iskan yake kawomin abinci, a yanda nayi niya yaune zan tafi amma na fasa tafiya sai naga mai gidan bene....... Wato mai wannan gidan na karuwai. Da daddare misalin 9:30pm na sauko k'asa na samu wuri daga gefe na zauna banma kowa magana ba haka kuma babu wanda na kalla amma hankalina gaba d'aya yana wurinsu, Murmushi nayi a lokacin da naji wasu *kwarata* na ciniki, kallarni sama da k'asa kaga zubina ai kasan nafi k'arfin ka kwanta dani kace 1k zaka bani, yo wace kala gareki ni keda bakin masai baku da banbanci a wurina tunda kowa ma zuwa yakeyi ya hau ya kama gabanshi, ina ma laifina da zan baki 1k idan haka yayi miki in bayar idan baki yadda ba naje wurin Umma. Mai makon naga taji haushi sai kawai tayi dariya tare da cewa shege kenan, to kawo dubu d'in, d'an sosa kansa yayi sannan yace kai nama manta dubun zan siya ma iyalina biredi wallahi kuma machine ina baida mai amma bari dai in bada dari biyar, batayi zuciya ba tace to kawo dari biyar in, bata yayi suka shiga cikin d'akin..... Tsoki nayi tare da ganin wallan matan aure, kuna gida kwance mazajenku suna nan wurin sakarkarin matan da basu kaiku komai ba, kuna can kuna girman kai da kunyar banza da sakarci aje a yayo cuta a cusa muku babu gari babu dalili. Me Allah ya rageku dashi ? Me karuwa take dashi wanda Allah bai baki ba ? Naki ma yafi nasu daraja tunda ke ta hanyar bautar Allah zaki mik'ashi kuma Allah ya baki lada, amma matar malam bahaushe tanajin kanta yai mata girma ji takeyi idan ta nunawa mijinta tana buk'atarshi kamar zai rainata, wata ma macen idan bashi ya nemeta ba saidai ayi ta zama a haka, to ya nemiki jiya shekaran jiya kullum har "yar basirar dake gareshi ta kare, ko kuma sai yazo kwanciya dake ki tashi hankalinshi ki tado fitar da kila anyi sati ko wata da yin abu saboda ke kawai za'a kwanta dake, kin b'ata mishi rai yaji gaba d'aya abun ya fita a kanshi ko kuma yayi shi ba cikin natsuwa ba, da kanki kike jefa kanki halakar da babu mai iya fitar dake sai Allah , daga haka sai shedan ya fara doka masa gangar sa ya barki yaje ya nemi na banza, dan babu zuciyat wanda shed'an baya wasa da ita. Idan kika had'u da muguwar mace sai ta rabaki da mijin fafur ki kasa gane kanshi, daga nan sai ki fara tattara kaya ke a dole kinyi yaji. Idan an tambayeki abinda ya had'aku ki fara cewa baya dawowa gida da wuri, idan kin kawo abinci baya ci, idan kinyi kwalliya baya yabawa, bayan duk kece babban da kika jawo ma kanki wannan damuwar........... Mudai je zuwa zamu gano masu laifin tsakanin matan da mazan su waye masu matsala...... Ina zaune a wurin har 12:30am bai fito ba, tou me akeyi haka har yanzu wanda ba'a gama shi ba ? Duk gorin da yayi mata na had'a mata k'addarar ta da bakin masai batayi zuciya ba. Lallai bariki bariki ce, mutanen cikinta suma sun barikantu kodai taji haushin abun bata wani nuna mishi damuwa ba, ina nan zaune a wurin har mutumin da nake tunanin mutumin da nake tunanin yana tare da Dikko ya shigo, Da fito ya shigo babu sallama sai gyara wando yakeyi kamar wani sabon shigar *kwartanci* kallona yayi tare da cewa har yanzu baki bacci ba ? Nima irin yanda naga *karuwai* sunayi idan zasuyi magana nayi, d'an kashe idanuwa nayi cikin sigar bariki sannan nace banyi ba, to me kike jirane ? Kud'in da zaka bani ina so na shiga kasuwa gobe zanyo siyayya kasan jibi nake komawa bakin aiki na...... Murmushi yayi saboda yasan shine farkon layi idan na fara iskanci, kina da account ne ? Ya tambayeni ?Banda shi, to da safen zan baki idan naje wurin mai gida na, Allah ya kaimu nace tare da mik'ewa na fara tafiya cikin *kwartanci* sakaran banza ya bini da kallo, zakaci ubanka idan na gano ku, jibi kamar yanzu kana nan zakayi baccin bak'in ciki dan zan b'ace muku b'at kamar jirgi a cikin gizagizan sararin samani............ 07/08/2019 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* *_Ku nemi naku fitowa ta farko daga shahararriyar kungiya mai san farin cikin makaranta wato BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION, sabon salo ne daga shahararrin marubuta biyu, MAI JIDDA daga alkalamin MARYAM MUHAMMAD HASSAN, MAFARKIN NANAH, sabon sauyi na SA'ADATU LAWAL maman ilu, kar ku sake ku bari a baku labari......_* *_ZAINAB ATTAHIRU B ' K sakonki yazo gareni ngode sosai ina miki fatan alkairi, ki kasance cikin farin ciki da kwanciyar hankali har a busa kaho............_* 🅿 ------ 8 Tafiya mukeyi daga ni harshi babu wanda yayi ma wani magana, saini da a zuciyata nake ta addu'a, Allah na rok'eka ka bani farin jini ka zubamin kwar jini kasa na rik'a bud'ewa mutane ido duk wanda yayi ido dani, Allah kasa wannan kyawun nawa ya zamar min babban jari, kasa nayi suna sosai a harkar karuwanci. Tafiya mai nisa mukayi har muka iso k'ofar gidan, sai yanzu yayi magana cewa ranki ya dad'e anzo, ba tare dana fito ba nace masa, malam ya sunan anguwar nan ne ...... ? Sanin da nayi ma anguwar a da yanzu karuwai sun canja mata suna, gidan na sani ba sunan wurin ba, ki sauka ki bani kud'ina sauri nakeyi. Ina k'ok'arin fitowa nace kasan kana sauri ka bari aka haife ka ? Ka iya tafiya domin dai ni d'abi'ata idan nahau abin hawa gaskiya bana iya biyan kud'i, amma Allah ya taimaka sauka lafiya ! Fitowa yayi daga cikin napep in ya fara ke bansan rashin kunya bani kud'i na ko in wulak'anta ki a wurin nan, d'an gajeran murmushi nayi tare da cewa banda haukar ka wanda ya fito bariki ai baya tsoron wulak'anta, ai ta wulakanta ta kare tunda har na fito daga gidanmu na taho yawon karuwanci........! Shiru yayi ya rasa abin cewa, dan haka nace ko kana da sauran magana ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa jeki kya gani...... Dariya nayi sosai irin ta cikakkin "yan duniya na kashe dariyar da rangad'a gud'a, sannan nace shege kaji uwar bari ko ? Tou babu uwar da zan gani dan duk wani gagararren d'an iska dake fad'in garin katsina nice uwarshi nice ubanshi, duk wani kangararren dan iska da "yar iska da iyayensu sukace jeku kun gani, to wallahi idan suka taho ni zasu gani..... Sauk'i ya nemar min sannan ya koma cikin napep inshi, yana k'ok'arin tashin ta nace malam dakata, tsayawa yayi yana kallona, kana da waya ne ? Rik'e waya ai sai ke da kika fito neman haramun, to naji ba komai, kadai ganni sosai ko ? Kuma zaka iya ganeni gobe idan mun had'u, tsoki yayi sannan yace taya zan manta da fuskarki azzaluma kawai, yawwa ina so dama ka gane ni gobe idan ka ganni, ni suna na Sultana idan kayi gaba ka bada labarina dan ina san cikin d'an k'ank'anin lokaci suna na ya zagaya kaf fad'in garinnan, sauka lafiya.......... ! Ina fad'in haka na shige gidan karuwai, Tun a zauren gidan na farajin kuruwar wata karuwa, karuwinta ne yake dukanta da belt kamar uba yana hukunta d'iyar sa, babu ji babu gani yana dukanta yana cewa dan ubanki sai kin bar gidan nan, wallahi na gama zama dake, d'an murmushi nayi a bayyane nace Allah sarki duniya yayin da wasu ke shigowa yayin wasu ke fita, A hankali nabi gidan da kallo ga mutane nan iri iri, yayin da wasu ke caca, wasu na lido, wasu na shan sigari yayin da wasu ke kwance saman jikin maza babu kunyar Allah bare tsoranshi, wato abinda dai na lura duk abinda kake so shi kakeyi babu mai ce maka dan mine ne ......? K'arewa gidan kallo nayi sosai, d'akuna ne k'asa da sama, bene ya zageye k'asan gidan yayi masa rumfa sai yanayin gidan ya tabbata kamar irin hadari ya taso. Wani irin ihu na zabgaga tare da kashe ihun da gud'a, wanda haka yayi sanadiyyar jawo hankalin duk wanda ke cikin gidan na waje da wanda ke d'aki babu wanda aka bari kowa saida ya fito....... Kirari na fara kwararwa bari ba tare dana kalli dandazon mutanen dake kallona ba. Bariki ba'ayi miki tilas babu wanda ya rako wani kowa da k'afarshi yazo kuma in yaji wuya shi zai koma, baki duba mai kyau ko mummuna, haka kuma babu ruwanki da maye ko mayya mai lafiya da mai cuta duk wanda yazo kina da masaukinshi, baki san inda kowa yake ba amma kowa yasan inda kike, gani nazo ki sakamin albarka, baki da tabbas bariki haka nima bani da tabbas, matsalar ubace ta kawoni amma ina tare da had'ari guda d'aya, bana san shiga sabgar kowa karki sake ki bari wani ya shigo rayuwata, ilimi nazo d'auka a cikinki amma ni nafiki rashin tabbas, ina da masaukin kowa amma banda na mata.....duk namijin da uwarshi ko ubanshi yace jeka ka gani tabbas idan yazo ina da masaukin shi nima, Kija da'irarki ki bani tawa, bana shan sigari bana cin goro, abu d'aya ya kawoni shi zanyi na koma, bansan bincike haka kuma bana san bin kwakwaf, kar ku sake naji bakin wani nan, idan ba amsa zai bani ba, kuma magana d'aya nake so ta fito bakinku akwai ko babu, itace amsar da nake so a bani, tambayata itace kawai d'akin zama ko nayi gaba.........? Wani daga can saman bene yace ke "yar cakulkula dake har kin san dad'in namiji ? 'Daga kaina nayi sama na kalleshi sannan nace daga ganinka gidan haya aka haife ka, kaine matsala da kanka bakaji abinda nace ba ? Akwai ko babu kawai nake so naji. Daga bayana wani yace ki bashi amsar tambayar shi mana sai mubaki taki, murmushi nayi sannan na d'aga kaina sama na kalleshi tare da cewa, duk tayar abun hawa sunanta taya, amma kaga tayar daf tafi ta jirgi girma amma abinda jirgi zai d'auka daf bata iya d'auka, jirgi ya d'auke ka kuma ya d'au kayan ka, kamar dai kai kaga ga jibgegiyar mace a gefenka, amma a zahirance gwaram ce tunda har ka samu damar fitowa, saboda haka k'aranta ba matsala bace, abinda wata motar ta kasa sai kaga machine yayi. Tabbas muna da masaukin ki, d'aki d'aya 5k ne a wata haka kowa yake biya sai kuma zaki bayar da kyautar dare d'aya ga mai gidan wannan shine tsarin wannan gida me kika ce ? Wannan ba damuwa bace amma nima ina da nawa tsarin na basu amsa, muna saurarenki suka bani amsa, gyara tsayuwa nayi sannan naci gaba da cewa ina da ranakun aiki ina da na hutu, yau da gobe da jibi daga nan har zuwa k'arshen satin nan babu maganar kwanciya da ko wane na miji amma zai yadda daga nan zuwa sati na gaba.........? Nayi musu haka ne dan ni kwana ukku kad'ai zanyi na k'ara gaba abu d'aya zuwa biyu nazo koya kad'ai a gidan karuwai kuma a raina bazan biya kud'in hayar ba haka na yanke.. Na saman benan yace min mi yasa kike da wannan tsarin haka ne An mata.......? Wata irin fad'uwar gaba naji tare da kallonshi da sauri domin ya kirani da irin sunan da Dikko yake kirana dashi, janye zance Dikko nayi a raina sannan nace idan har ruwa ya kare a cikin tanki ko ka tara abun ibar ruwa baka samun komai haka nan zaka gaji da jira ka d'auke, amma idan aka bari ya taru kana tarawa zai cika ma duk abinda kake buk'ata, to nima haka take daga gareni karfina ya k'are dan na kwana ina aiki saboda haka a barni na huta na kwanakin dana iba, Murmushi yayi tare da cewa gaskiya ku bata d'aki tabbas muna da masaukin ki a gidan nan, sakaran banza na fad'a a cikin raina nace otiho dakai baka tsan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, duk shelar da nayi na ce bariki tafini tabbas ka gagara ganewa da gaanin wannan sha ka tafi ne, fuska ta d'auke da mugunta nace mashi idan an bani d'akin kai ka biya kud'in sannan kuma ka bani rance dubu d'ari, tukuicin d'aki zaka kwana biyu kana morewa dani nima daga cikin irin baiwar da Allah ya bani, dubu d'arin ka kuma da kud'in d'aki duk zan baka su idan na fara kasuwa...... Ba damuwa a bata d'akin sama lamba 59 ya fad'a cikin zaguwa, ga *kwartuwar* shi gefe ya manta da labarinta, hawa sama nayi aka nunamin d'akin, makulli aka bani na bud'e na shiga ina shiga na kulle d'akin ta ciki. Dudduba d'akin nayi bayan na shiga, falo ne sai d'akin bacci madafar abinci da bayi, d'akin bacci katifa ce irin ta "yan bodyn sch, falo tayils ne babu kujeru sai kafet, k'arewa d'akin kallo nayi sannan na koma jikin tagar d'akin na fara kallon yanda *karuwai* suke rayuwarsu. Ina tsaye na fara tunanin fuskar da tacemin An mata, ina k'ok'arin tunoshi kwalwata ta fara jakkancin data saba, a bayyane nace ki saurara kar kimin haka don Allah rayuwa mai had'ari na kawo kaina ki tausamin ki sanar dani ko waye waccan, kwana biyu kad'ai zanyi nabar gidan nan amma ina so ki sanar dani ko waye shi d'in...... Bugawa zuciyata tayi tare da cewa abokin Dikko ne wallahi, shine ya raka abokin Babanki aka kaiki wurin Dikko....... Kamar kasuwa haka zuciyata da kwalwata suka fara gardama hayani ke tashi daga cikin kwalwata da zuciyata, yayin da kwalwata ke cewa bashi ne ba zuciyata tana cewa tabbas wallahi shine, kyarma jikina ya farayi gaba d'aya d'akin naji yana juyamin, kamar ana jijjiga ni naji anayi dan haka da sauri na dafa bango na zauna k'asa tare da fara karanto duk addu'ar data zo bakina...... Bayan na samu natsuwa ne, na dafa daidai saitin zuciyata da kwalwata sannan nace idan nayi muku wani laifi da Allah ku gafarceni amma ku daina dakushe wa ku barni nayi komai cikin hikima kamar yanda na tsara zanyi. Kuyi hakuri ku daure ku bani gudamwa. Kwana na biyu a gidan karuwai ina koyon abinda yakaini, safe rana dare wannan d'an iskan yake kawomin abinci, a yanda nayi niya yaune zan tafi amma na fasa tafiya sai naga mai gidan bene....... Wato mai wannan gidan na karuwai. Da daddare misalin 9:30pm na sauko k'asa na samu wuri daga gefe na zauna banma kowa magana ba haka kuma babu wanda na kalla amma hankalina gaba d'aya yana wurinsu, Murmushi nayi a lokacin da naji wasu *kwarata* na ciniki, kallarni sama da k'asa kaga zubina ai kasan nafi k'arfin ka kwanta dani kace 1k zaka bani, yo wace kala gareki ni keda bakin masai baku da banbanci a wurina tunda kowa ma zuwa yakeyi ya hau ya kama gabanshi, ina ma laifina da zan baki 1k idan haka yayi miki in bayar idan baki yadda ba naje wurin Umma. Mai makon naga taji haushi sai kawai tayi dariya tare da cewa shege kenan, to kawo dubu d'in, d'an sosa kansa yayi sannan yace kai nama manta dubun zan siya ma iyalina biredi wallahi kuma machine ina baida mai amma bari dai in bada dari biyar, batayi zuciya ba tace to kawo dari biyar in, bata yayi suka shiga cikin d'akin..... Tsoki nayi tare da ganin wallan matan aure, kuna gida kwance mazajenku suna nan wurin sakarkarin matan da basu kaiku komai ba, kuna can kuna girman kai da kunyar banza da sakarci aje a yayo cuta a cusa muku babu gari babu dalili. Me Allah ya rageku dashi ? Me karuwa take dashi wanda Allah bai baki ba ? Naki ma yafi nasu daraja tunda ke ta hanyar bautar Allah zaki mik'ashi kuma Allah ya baki lada, amma matar malam bahaushe tanajin kanta yai mata girma ji takeyi idan ta nunawa mijinta tana buk'atarshi kamar zai rainata, wata ma macen idan bashi ya nemeta ba saidai ayi ta zama a haka, to ya nemiki jiya shekaran jiya kullum har "yar basirar dake gareshi ta kare, ko kuma sai yazo kwanciya dake ki tashi hankalinshi ki tado fitar da kila anyi sati ko wata da yin abu saboda ke kawai za'a kwanta dake, kin b'ata mishi rai yaji gaba d'aya abun ya fita a kanshi ko kuma yayi shi ba cikin natsuwa ba, da kanki kike jefa kanki halakar da babu mai iya fitar dake sai Allah , daga haka sai shedan ya fara doka masa gangar sa ya barki yaje ya nemi na banza, dan babu zuciyat wanda shed'an baya wasa da ita. Idan kika had'u da muguwar mace sai ta rabaki da mijin fafur ki kasa gane kanshi, daga nan sai ki fara tattara kaya ke a dole kinyi yaji. Idan an tambayeki abinda ya had'aku ki fara cewa baya dawowa gida da wuri, idan kin kawo abinci baya ci, idan kinyi kwalliya baya yabawa, bayan duk kece babban da kika jawo ma kanki wannan damuwar........... Mudai je zuwa zamu gano masu laifin tsakanin matan da mazan su waye masu matsala...... Ina zaune a wurin har 12:30am bai fito ba, tou me akeyi haka har yanzu wanda ba'a gama shi ba ? Duk gorin da yayi mata na had'a mata k'addarar ta da bakin masai batayi zuciya ba. Lallai bariki bariki ce, mutanen cikinta suma sun barikantu kodai taji haushin abun bata wani nuna mishi damuwa ba, ina nan zaune a wurin har mutumin da nake tunanin mutumin da nake tunanin yana tare da Dikko ya shigo, Da fito ya shigo babu sallama sai gyara wando yakeyi kamar wani sabon shigar *kwartanci* kallona yayi tare da cewa har yanzu baki bacci ba ? Nima irin yanda naga *karuwai* sunayi idan zasuyi magana nayi, d'an kashe idanuwa nayi cikin sigar bariki sannan nace banyi ba, to me kike jirane ? Kud'in da zaka bani ina so na shiga kasuwa gobe zanyo siyayya kasan jibi nake komawa bakin aiki na...... Murmushi yayi saboda yasan shine farkon layi idan na fara iskanci, kina da account ne ? Ya tambayeni ?Banda shi, to da safen zan baki idan naje wurin mai gida na, Allah ya kaimu nace tare da mik'ewa na fara tafiya cikin *kwartanci* sakaran banza ya bini da kallo, zakaci ubanka idan na gano ku, jibi kamar yanzu kana nan zakayi baccin bak'in ciki dan zan b'ace muku b'at kamar jirgi a cikin gizagizan sararin samani............ 07/08/2019 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 9 Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, itace kad'ai abinda Dikko yake ta maimaitawa a cikin wannan tsalelen dare, Juyi yakeyi sosai a saman gado sai kace macen da ciwon ciki ya taso ta gaba, kifa kanshi yayi a saman lallausan bargon dake kusa da kanshi ya goge hawayen dake bi masa idanuwa. Allah na tuba..., ya fad'a a bayyane tare da gyara kwanciyar shi, girgiza kanshi yayi , yayin da zuciyarshi da kwakwalwar shi suka hasko mishi abinda yayi ma Sultana, a hankali ya lumshe idanuwanshi na tsawon lokaci sannan ya fad'a a bayyane baiwar Allah baki dace mahaifi ba, Sai kuma Allah ya jefoki a rayuwar Dikko yayin da nake nemanki, kika zo a daidai lokacin da na d'auki hud'ubar shaidan , Allah ya baki hak'uri kinji, ya k'arasa maganar tare da bud'e idanuwanshi duka da sukayi jajir saboda kuka........ Ko ina kike ? Me kike yi yanzu ? Wane irin bak'in ciki kikeji idan kika tuna dani ? Ki zama mai yafiya a rayuwarki, manta da Dikko ki fuskanci rayuwa, ina nan ke kuma ina ki ke .....? Ina gidan karuwai,.... Ina shiga d'akina na mayar da k'ofa na rufe, ya zama lallai na gano waye mamallakin wannan gidan, sannan idan har na karb'i dubu d'ari a hannun wancan garan me ya kamata nayi da ita ne ? Ansar kud'in sune wahala Sultana anso su tuk'una idan suka zo hannu ba'a rasa abinda za'ayi ba, wannan shine shawarar da zuciyata ta fad'amin. Ajiyar zuciya na sauke tare da hayewa saman "yar k'aramar katifata na kwanta bacci. Da safe ina tashi sallah asuba nayi, na dad'e ina zaune a saman abin sallah ina addu'o'i na neman tsari d'aukaka farin jini da kuma k'war jini a harkar bariki. Sai 7:00am na tashi daga saman abin sallah, toilet na shiga nayi wanka, ina fitowa na shirya a gaggauce domin akwai inda nake so naje. Ina gama shirina na fito sanye cikin hijabina, sai nik'af dana dabkakawa fuskata, ina rufe d'akina mai kirana da irin sunan da Dikko yake kirana yazo. A k'ofar d'aki muka gaisa daga gaisuwa ban sake masa magana ba naci gaba da rufe d'akina. An mata ina zakije haka da safe ? Ban kalleshi ba nace zanje wurinka ne dama, murmushi yayi tare da cewa kuma gashi nima nazo wurinki yake nan .? Babu wani damuwa zamu iya maganarmu anan, mudai shiga daga ciki zaifi ko ? Ya fad'a yana kallo na, gyara tsayuwata nayi tare da cewa kayi hak'uri gaskiya na fito bazan koma ba, yana k'ok'arin bud'e bakinshi yayi magana nace kayi hak'uri da Allah bana san magana tayi tsayo na wuce, ina k'ok'arin tafiya yace d'an tsaya kiji mana. Tsayuwa nayi ba tare dana juyo ba, am dama cewa zanyi idan kina da hali anjima zamuje wurin Alhaji yace yana san ganin ki, ba tare dana juyo ba nace wane Alhaji ne ? Mai gidan nan, na bashi labarinki shi kuma ya matsa saiya ganki. Saida nayi shiru na wani lokaci sannan nace wurin k'arfe nawa zamu je kenan ? Yanzu ma dan zaki fita da munje saboda ba'a gida ya kwana ba yana nan bayan gidan nan yana tare da bak'i da sukazo wurinshi manyan alhazawa ne masu kud'i da suka ansa sunansu a kud'i, d'an mugun murmushi nayi a cikin nik'af ina sannan nace tou kai ya maganar kud'in da zaka bani ne ? Suna cikon mota muje, murmushin zalinci nayi irin wanda naga mugu Dikko yanayi sannan nayi gaba abuna ya biyo bayana. Cikin motarshi ya d'aukeni, muna shiga cikin motar na yaye nik'af ina tare da kallonshi sannan nace niko na tambaye ka mana ? Tambayarni mana ya fad'a a daidai lokacin daya fara tafiya da mota. Shiru nayi ban sake magana ba, shine ya gaji da shirun yace kinyi shiru kuma ! Ey zan tambaye ka amma ba yanzu ba dan na d'auka ne baka san tambaya da surutu ne kamar yanda nima bana so, amma tunda ka bani izini zan rik'a tambayarka a duk lokacin da tambayar yazo min, amma dai ya sunan ka ...? Murmushi yayi sannan yace suna na Umar, gyara zama na nayi tare da cewa me yasa Babanku yasa maka suna Umar ne ? Dariya yayi sosai tare da cewa sunan ubangidan shi ne, Zaici gaba da rattafo min bayani na dakatar dashi ta hanyar cewa barmin bayanin haka nan zan tambayeka wani lokaci, babu gardama ya kame bakinshi ta hanyar yin shiru.... Har muka isa bakin get in gidan babu wanda ya sake magana daga ni harshi, horn yayi mai gadi ya bud'e mana muka shiga, gida ne had'ad'd'en gida na "yan gayu yasha ado da shuke shuke na filawowi, daga gefe kuma wasu irin lafiyayun dawakai ne tsabtatacci kuma k'osashshi aka d'aure sai tattabaru masu kyau wanda suke sauka k'asa lokaci lokaci su kuma tashi sama firrr lokaci lokaci.... Gaskiya dokunan sun burgeni sun kuma bani sha'awa, amma dana tuna da Dikko yana san doki yana k'aunar doki a rayuwarshi sai kawai naji dawakan nan sun fita a raina, saima zuciyata ta fara tunanin taya zanyi in kashe su, domin na tuna cewa Dikko ya fad'a cewa yana san doki ko ba nashi bane, lallai ni kuma na tsani dawakai.. Muje Umar ya fad'a da yaga banda alamar fita daga cikin motar. Fitowa nayi tare da cewa Umar waye yake kiwon dokuna ? Wallahi na uban gidan Alhaji ne, ya bani amsa ne a lokacin da muka fara tafiya, tou shi Alhajin duk kud'inshi kenan yana da ubangida shima ? Na tambayi Umar, Umar yace Eh mana ai ubangidan nashi shine duk wata k'aryarshi, shine ya d'aure masa k'ugu shi ya tsaya masa saida ya tabbatar Alhaji ya zauna saman k'afafuwanshi , gaskiya mutumin kirki ne sosai, da yana harkar mata na tabbata idan na had'aki dashi yarinya kin warke, bake ba talauci, ke bake ba kaf zuri'arku da talauci ya k'are. Maganar Umar ta k'are ne a daidai lokacin da muka shiga palon gidan, k'aton palo ne mai girman gaske, sai wata irin dakekiyar tv tunda nake a rayuwata ban tab'a ganin tv mai girmanta ba, ko da yake ma ina naje ina na sani a wannan lokaci ? Saifa gidansu Dikko shima naga tashi tv n babba ce amma banda natsuwar gane wacce tafi girma, Bin palon nayi da kallo, d'an rumtse idona nayi na bud'e tare da k'ara d'ora idanuwana a saman hotunan dake palon, tabbas idan ban manta fuskar Dikko ba wannan shine Dikko, mutumin dana tsana nake san ganin bayanshi komin daren dad'ewa, dan ina sayen gida wa Babana Dikko shine mutum na farko da zan fara sabautawa rayuwa a duniya...... Muje suna ciki, Umar ya fad'a tare da katse mun tunani na, sauke nik'af ina nayi na rufe fuskata sannan nace mu koma gida, zai tambayeni dalili nace kawai mu koma zamuyi magana dakai daga baya. Haba Sultana har mun shigo wuri zaki ce mu koma.... Kallon Umar nayi sannan nace tunda nazo da kaina ai kasan zan sake dawowa ko ? Ina fad'in haka nayi gaba abuna...... Ina fitowa idanuwana suka cika da hawaye, tun ranar da Dikko ya ajiyeni a k'ofar gidanmu ban sake tunaninshi ba sai ranar da Umar ya kirani da An mata, ban sanka Dikko na tsani duk sunan daya fara daga kalmar D insha Allah ni zan zama ajalinka..... Kuma ta hanyar da kabi ka azabtar dani to nima ta hanyar zanbi in rama abinda kamin, yanda ka somar dani ni kuma saina kasheka.... Babana yaci darajar mahaifi na ne shi, zan tara masa dukiya ta hanyar karuwanci zaici yaci bulus amma wallahi kai Dikko bakaci banza ba..... Fitowar Umar yasa na saita kaina, na bud'e mota na shiga domin ya bud'emin ita tun lokacin daya fito, zakuji dalilin da yasa na fasa shiga ciki, Umar kad'ai yasan fuskata kuma yau ya zamar min wajibi nabar gidan karuwai domin wannan kwanakin sune kwanakin dana iba zanyi a gidan karuwai, na ga abinda nake so na gani, naji na kuma gani nima zanyi gaba dan nima in dogara da kaina. Muna fitowa yayi hanyar gida nace dakata ajiyeni nan, ina zakije ne ? Ya tambayeni , ban bashi amsar tambayarshi ba nace masa ga makullin d'akina kasa a gyara man, bani kud'in nan zanje in had'o makaman yak'i..... Miye makaman yak'i kuma ? Ba tare dana kalleshi ba nace ai kasan ba'a shiga gida dole saida sallama, gida ba shara ai baya dad'in zama, na ciki bai san akwai na waje ba idan baya kwankwasa ba, to haka bazai yuwu ba wani yaci abinci yace kai yaci mawa, kaidai bani kud'i kaji idan na dawo zan baka bayani, Kud'in ya d'auko ya bani, bayan na ansa nace samu wuri ka rubuta min number ka idan zan dawo zan kiraka kazo ka taho dani, yo ina wayarki ne ? Banda waya amma ka rubuta min zan samu aro na kiraka, rubuta min yayi a jikin takarda ya mik'omin, ansa nayi na fita daga motar tare da cewa sai munyi waya... Saida na daina hango Umar sannan nima na ibi tawa hanyar na shiga duniya......, Tafiya nayi mai tsayi ba tare da sanin inda zanje ba sannan na tsaya wani shago na samu aron waya, lambar Umar na basu nace da Allah su saka a waya su kirashi, ansa mai shagon yayi yasa lambar ya kira, babu wani b'ata lokaci aka sadani da Umar... Sultana ce, na fad'a a lokacin da Umar yace hello, Oh kin gama ne ? Ya tambayeni, maimakon na bashi ansa saina kece da dariya kamar hauka sabon kamu..... Meya faru ne ? Inji Umar, saida na gaji da dariya dan kaina sannan nace darasi. Yau na tabbatar ni bariki ta fini tabbas na tafi na barka, wannan makullin d'akin daka bani ne shine na dawo muku da kayanku, amma zan baka sak'o a wurin Dikko tunda kasanshi , ka fad'a mishi cewa Sultana tace zasu gauraya........ Ina fad'in haka na yanke wayar na mayar da ita ga mamallakinta nayi gaba abuna.... Wata irin zufa ta ketowa Umar mai makon salati sai ashariya, ya fara luk'ak'a zagi tare dayo waje da gudu, yana cewa amma lallai yarinyar nan ni zata danfara, wato wani bazaici abinci yace kai yaci ma ba, wato nine abinci itace bakin ni zakici ki gudu ? Kuma har kike wani cewa mai gida Dikko zaki gauraya dashi ? Kai wallahi idan na yadda shege ne ni, kuma yanzu zan kira Dikkon zaki ci kutumar ubanki, kici dubu d'ari zanci miliyan daga jikinki. Jikinshi na kyarma ya fara kiran wayar Dikko har ta tsinke bai d'auka ba, k'ara kiranshi yayi bai d'auka ba, ci gaba yayi da kiran wayar babu k'ak'k'autawa, saida ya kira Dikko yakai sau goma sannan miskilin ya d'auka wayar..... Ya akayi ne ? Shine tambayar da Dikko yayi ma Umar, cikin tausasa lafuzzan shi yace ranka ya dad'e kasan wata yarinya Sultana..... ? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Dikko ya fad'a a ranshi lokacin da aka ambaci sunan Sultana, Me ya faru ne ? Dikko ya tambaya ? Umar yaci gaba da cewa ranka ya dad'e yarinyar nan "yar damfara ce, tazo nan gidan "yanci ne , gidan karuwai suke cewa gidan "yanci, dan idan aka kira karuwai d'in haka abun babu dad'in ji. Shi yasa su gogaggin "yan bariki suke kiran gidan da gidan "yanci. Wata irin zufa ta tsatstsafowa Dikko amma yayi shiru yana sauraren Umar, ranka ya dad'e kwananta hud'u a gidan "yanci shine yau ashe ta shirya guduwa ta raina min hankali ta ansar min kud'i dubu d'ari akan zata bani tukuici, { zasuyi iskanci } shine ta gudu, wai kuma saboda ta d'aukeni sakarai wai tayomin waya in fad'a maka wai zata gauraya dakai. Saida Dikko ya goge zufa sannan yace yanzu kayi hak'uri zan biyaka kud'inka, ai ranka ya dad'e ni ba kud'in bane yafi damuna mummunar maganar data fad'a a kanka ne, bayan zata gauraya dani tace maka wani abu ? A , a batace komai ba, amma ina ruwanta dakai ? Tana da dalilinta na fad'in zata gauraya dani, ka fita harkar yarinyar nan zan tura maka kud'inka karka ma sake kace zaka sake tashin wata magana kuma karka sake ka nemeta , Umar yace mai gida zafa ta gaura dakai ? Ka kuwa san abinda gauraya take nufi ? Dikko yace ta gaurayo dani d'in ina ruwanka ? Kaine tace zata gaura ko ni ? Shiru Umar yayi, tsoki Dikko yayi da niyar kashe waya, Umar yace ranka ya dad'e nidai idan kaine zaka biya kud'in nan na yafe maka su, Dikko yace ita zaka yafewa bani ba tunda ni banci maka ba, taci albarkacinka na yafe mata, na gode shine abinda Dikko ya fad'a tare da kashe wayarshi. Miye tsakanin Dikko da Yarinyar nan ? Shine tambayar da Umar yakewa kanshi wanda ya rasa mai bashi amsar tambayar, tou yaushe mai gida ya fara harkar mata ne ? Dariya yayi tare da cewa shegiya duniya mata bala'e ne wato duk musulinci mutum da kawaicinshi babu uztaz babu mahaukaci kowa dai yasan darajar ku, ai dole nake yafe dubu d'ari nasan wasu miliyoyi ne zan ansa, inama zanga yarinyar nan da na tambayeta miye tsakaninta da Dikko. Mi yasa zakiyi haka ? Me zaki tsinta a harkar karuwanci banda wahala ? Me kike so ne ? Me kika rasa ? Kud'i ba damuwa na bane da zan ganki da na wadaki da dukiya har sai kin rik'ajin kyankyan kud'i, k'amshisu ma idan kikaji saiya rik'a tayar miki da zuciya, ke kuma duniyar kike so ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa Allah yasa miki natsuwa ki dawo daga rakiyar shaidan. Allah ya had'ani dake Sultana in baki hak'uri in kuma nemi yafiyarki, Mutane sunamin bahaguwar fahimta, yanda kike kallona ba haka nake ba, kuna min wani tunani na daban bayan ba haka Dikko yake ba, Duk abinda ya faru tsakani na dake wallahi ina ganinshi ne kamar wasa, banso haka ba, bansan ya akayi nima na koma kamar wani sakarai ba wallahi, Allah ya tsareki fad'awa halaka, idan har kika fad'a harkar karuwanci na cuci rayuwata da zuri'ata da banma fara tunanin auren ba. Farin ciki kamar in tashi sama yau gani ga naira dubu d'ari, kud'i suna da dad'i gaskiya da farko dai saina ci kaza, sannan na gano wani abu d'aya da maza suke so a tattare da mata, suna san k'osashshiyar mace, suna san tsaftatacciyar mace, suna san mace mai aji suna san mace ma'abociya k'amshi macen data iya soyayya da tattali, ina zan nufa yanzu ? .......... 16/08/2019 Da Allah kuyi hakuri rasuwa akayi min ne kukaji shiru da dad'ewa haka, Ina ma kowa barka da sallah, Allah ya maimaita mana yasa muna da rabon ganin na bad'in bad'ad'a, amin. Barka da sallah. ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 10 Lallai idan nayi shiru da maganar nan ban fad'awa mahaifin Dikko ba nan gaba ya gano wani abu lallai zan fuskanci baraza na dagani har mahaifina, kila ma ya kora mu, ya zama wajibi naje na fad'a masa halin da Dikko yake ciki, in yaso zaiyi bincike abinda ya had'ashi da ita yarinyar, Umar yake magana duk abin yazo ya dameshi yana mamakin abinda ya had'a Dikko da mace har take fad'ar zata gauraya dashi..... Dikko mai zafi akan mata, ya akayi ya koma mai sanyi ? Wuta ne mai tsananin k'unar gaske ga duk macen data matse masa, babu abinda ya tsana duniya irin mata, amma wai shine yake godiya akan mace... Wace ce ita ? Miye tsakanin su ne.... ? Kayi shaye sheyenka ne Umar shi yasa ka manta wace ce Sultana..... Tsohuwar anguwarmu ta farko na koma, inda Dikko yayi ta siye siyen gidanjen da muke kamawa haya, gida mai sauk'in kud'i na samu na kama d'aki d'aya, bayan na biya kud'in d'aki na tafi kasuwa dan siyo d'an abinda ba'a rasa ba na amfanin yau da kullum. Na dad'e sosai a kasuwa, saboda duk abinda nasan zan nema saida na tabbatar na siya saboda ni rayuwata ta duniya babu abinda na tsana irin aro, bana san na takura shi yasa zanyi k'ok'ori na bada k'addarata dan na samu kud'i....... Umar durk'ushe a gaban mahaifin Dikko, hada wani hawayen munafirci kanshi a k'asa kamar sabuwar amarya a daren farko, Dady kuwa gaba d'aya yanayin fuskashi ya sauya zuwa damuwa bayan ya gama jin duk maganar da Umar yazo da ita, shi baya hana Dikko yayi magana da mata bane ko wani abu a , a shi baya so dai ya shiga damuwa har wani abu yazo ya sameshi, kuma idan yayi ma Dikko maganar aure sai yace shi yaro ne a bari saiya k'ara girma, ga Umar kuma yazo ya fad'i k'arya da gaskiya dandai kawai a bashi wani abu, wannan fada ce ko kuwa maulace ? Kallon Umar Dady yayi sosai sannan yace kirawo min shi.... Umar ya kira Dikko yafi so a irga amma bai d'auki wayarshi ba, ganin haka yasa Dady ya fara kiran Dikkon da kanshi, shima bai d'auka ba, jinjina kai Dady yayi tare da turawa Dikko sak'o kamar haka.... _Babana idan ka gama abinda kakeyi ka kirani._ Umar kuwa yana tashi daga wurin Dady ciki ya wuce inda iyayenshi suke, a gidan su Dikko Umar da iyayenshi suke zama, suna a k'ark'arshin su Dikko ne, kuma Umar shine mutumin da yayowa Bello jagoranci aka kawoni wurin Dikko, ni da dare na ganshi amma Allah yasa na ganeshi duk da jakanci na, amma shi ya kasa ganeni kwata kwata.... Umar bai dad'e da tashi ba kiran Dikko ya shigo cikin wayar Dady..... Da farin ciki Dady ya d'auki wayar tare da cewa ina ka shige ne ? Ko kana tunanin surukata ne ? Ya fad'i maganar cikin sigar zaulaya, d'an gyaran murya Dikko yayi tare da cewa barka da yini, ya gaishe da Dady dan kauda waccan maganar..... Ansawa Dady yayi suka gaisa cikin farin ciki da soyayya irin na d`a da mahaifi. Bayan gaisuwa Dady ya tambayi Dikko labarin yarinya da Umar yazo mishi da ita, miye tsakaninsu kuma miye gaskiya labarin ...? Dady ya k'ara da cewa banso soyayya tayi min wasa da rayuwata, domin duk abinda ya tab'a hanci ido ruwa yake, tou duk abinda ya tab'oka ni ya shafa. Me ya had'aku har take zaginka ? Gyara zama Dikko yayi sannan yace ba komai, kuma ma ai bata zageni ba Dady, duba Babana yaushe ka fara b'oyemin abinda ya shafeka ? Ni zaka juyawa baya ? Me zaka b'oyemi bayan kasan ni bana b'oye maka komai ? Fad'amin abinda ya dameka muyi damuwar tare..... Shiru Dikko yayi na wasu mintoci yak'i yayi magana, Dady yace kai nake saurare Babana kaji tsoron Allah ka fad'amin abinda yake damunka idan har kana so nayi bacci a daren yau..... Har yanzu Dikko baiyi magana ba kuma bai kashe wayar ba, Dady ya k'ara cewa ka daiji tsoron Allah ka fad'amin gaskiya k'arya ba halinka bane kuma masu sunan manya basa fad'ar abinda ba gaskiya ne ba, gaskiyar mahaifina da amana irin tashi yasa na saka maka sunanshi saboda kwad'ayin kaima ka zama mai gaskiya da amana kamarshi, kuma ina fatan ka zama mai adalci ko bayan bana duniyar nan..... Ina so ka zama jigo ga "yan uwanka ka tausaya musu ka karb'i damuwarsu ka sakasu farin ciki karka barsu suyi kukan rashin mahaifi, inaji a jikina bazan dad'e duniya ba, nayi kuka kuma na shiga damuwa rashin samun d`a namiji, sai kuma nayi farin ciki a lokacin da Allah ya azurtani dakai... Idan kaga na damu da nasan abinda yake damunka saboda in d'oraka hanya idan naga zaka sauka daga saman layin gaskiya, ina fad'a maka tawa damuwar ne dan ka gane abinda duniya take ciki. Me ya had'aka da yarinyar mutane take zaginka ne Babana ? Cikin kame kame yace Dady nifa ba zagina tayi ba, kuma ma yake maganar cewa tana min rashin kunya a ina akayi haka ? Ni ba ruwana da ita sab'ani ne kawai muka samu kuma ma ai abun ya wuce.... Saidai inayin mafarkinta idan ina bacci, inajin damuwa ne idan na tuno da ita, sai kuma inji kamar tana kiran suna na wani lokaci, kuma sai inji kamar tana tare dani, inajin kamar numfashinta a jikina sai kuma shashshekar kukanta tana dai zuwa min sosai a ranaku da dama, shi yasa ma nake d'an tunani, amma bayan haka banda wani damuwa da ita. Tou soyayya kakeyi da ita ne ? Dady ya tambayeshi, no ba soyayya kawai dai rashin kunya tamin sai nayi maganin bakin tsiwa, kamar ya dady ya sake tambayar Dikko, shiru Dikko ya sakeyi ya kuma rasa abin cewa. Kai nake saurare, Dady ya fad'a, kwashe komai Dikko yayi ya fad'awa dady amma bai fad'a masa labarin wani abu ya shiga tsakaninshi da Sultana ba, kawai dai yace ya sissiye gidajen da suke haya ne, a haka aka tsaya ba maganar yayi wani abu da ita. Nasiha Dady yayi ma Dikko kamar yanda ya saba, yace yayi ta addu'a, kuma zasu tayashi har Allah yasa ya manta da labarin Sultana a rayuwarshi, godiya Dikko yayi ma Dady sukayi sallama. Haka kuwa akayi domin dai Dady ya mik'e tsaye yasa ayiwa Dikko rok'on Allah dan shi a tunaninshi Sultana aljana ce, ko kuma mayu ce ko tanawa d`ansa asiri ne, dan haka Dady ya tsaya akan k'afafuwanshi saida ya tabbatar Dikko ya manta da labarin Sultana a rayuwarshi sannan hankalinshi ya kwanta........... Wannan kenan........... *** _{ kalu bale gareku matan aure.......... }_ Gidan da na kama haya gaba d'aya gidan matan aure ne babu zawara ko d'aya haka babu budurwa idan bani ba........ Kowa da mijinta daban babu wacce ta had'a miji da wata, abinda na fuskanta da rayuwar mazauna gidan kowa yanayi ma d'an uwansa kallon hadarin kaji ne, babu wanda yake san kowa sai zazzafar bak'in ciki da jin zafi da gasa da kowa yake nunawa abokin zamanshi ido biyu kunne tsaye babu kunya bare kawaici. Gidan babu katsari kuma bashi da saiti kowa yaga dama shigowa yakeyi, sai a tara dandazon taron mata ayita maganganun sakarci da rashin kamun kai, shi yasa zawarun anguwar da "yan mata wanda suka bushe fitilarsu suka maida gidan dandalin sauke lalatarsu. Suna da wata d'abi'a d'aya dana lura da ita ta wasan banza, kuma basajin kunyar nuna tsiraici wa junansu, ma'ana kamar irin cire riga da bra a lokacin fira, irin wancan tace amma wance gaskiya kinfi wacce nono, basajin kunya sakin maganganu na sakarci da fallasa sirin mazajensu. Duk da ni yarinya ce mai k'aranci shekaru a cikinsu na raina musu wayau gaskiya, kuma na d'aukesu wawaye idan naga dama zan basu shawara kuma idan suka d'auka zata musu amfani, amma gaskiya banga dama ba, haggu zanyi amfani da ita dan ni yanzu ba shiriya nake so ba lalacewa itace na zab'a kuma duk wanda naga zai lalace saina kama mishi ya lalace, dan nayi alk'awari saina kafa tarihi a garin katsina, ina so in zama cikakkiyar karuwar da sai suna na ya shiga cikin sahun "yan iska a duniya, dan bazan yadda nayi karuwanci wahala ba. Kujerata na d'auka na nufi k'ark'ashin bishiyar da ake zaman majalisar, ina k'ok'arin kafa kujerata zan zauna wata zawara tace ke Sultana tashi nan ba wurin zaman yara bane ba kinji..... Gaba d'aya suka shek'e da dariya tare dayin gud'a, { ayyuri yuri yuriiiiik.... } aka kashe, murmushi nayi tare da ajiye kujerata na zauna, ba tare dana kalleta ba nace dan anyi ciwo an warke ai ba'a ba mutuwa haushi ba, abinda kike takamar an baki nima naci irinshi, tou me za'a b'oyewa ruwa bayan babu inda bai shiga, ansha kuma anyi wanka dashi aikuwa kinga farin wata ba bak'on dare bane ba. Duk macen dake wurin saida ta kalleni, murmushi nayi irin na "yan duniya tare da d'aga girare na duka nace muci gaba da zance ai abokin cin mushe ba'a b'oye mishi wuk'a. Sama sama dai akayi firar wannan rana babu wani labarin ci gaba da guda guda kowa ya sab'e duk wanda ba gidan yake ba yayi tafiyarshi aka barmu iyakarmu "yan gidan..... Bayan sun fashe ne kowa ta tashi ta fara aikin gabanta tunda masu labarin iskancin sun tafi, dan haka sukeyi idan dai ana wannan firar jarabar babu macen dake motsawa, idan kuwa d'anta zaiyi kukan mutuwa bata kulashi. Maganar sallah kuwa saidai a mik'ata a jimlace, wai sai an gama zance duniya za'aje ayi alwalla lokacin za'ayi azahar la'asar magrib isha'i, wata ma idan ta makara bata tashi sallah asubahi ba, har gari ya waye tou duk wacce ta fito ta samu an fara fira tou wannan sallah sai anjima za'ayi ta, nan mace zata jibge kamar asara ayita kiraye kirayen "ya "yan dan ubanki baza ki kawomin kaza ba, Saida kowa ya tashi sannan nima na d'auki kujerata nayi d'akina, buta na d'auko nazo nayi alwallah magrib na shige tare da rufe k'ofata ba kuma zan sake fita ba sai Allah ya kaimu gobe lafiya..... Dan babu abinda banda shi a cikin d'akina na masarufi, ina da indomie ina da kayan tea kuma ko wane lokaci flarks ina cike yake da ruwan zafi, saida nayi sallah isha'i tare da addu'o'in samun d'aukaka kamar yanda na saba a duk lokacin da nayi sallah. Bana buk'atar komai domin banajin yunwa, a inda na gama sallata a wurin nayi kwanciyata, ban dad'e da kwanciya ba bacci yayi gaba dani..... Can cikin bacci naji hayani wanda tak'i k'arewa muryar Nana sama sai zabgaga ashariya takeyi tare da cewa auren ka ko auren wahala, auren cida kai niba ga gidan gayu ba na bige ga zaman haya, har kunya nakeji k'awayena su san inda nake dan darajata da nasabata ta wuce in aureka haka nan Allah ya had'ani da wannan auren k'addarar da k'aranci shekaruna duk kabi ka bigar dani na koma wata abun tausayi, tou wallahi idan kaga yau na kwana dakai saika biyani duk bashin daka san inabinka.... Ajiyar zuciya na sauke tare da kallon "yar agogon dana mak'ala a jikin bangon d'akina 11:45pm, maida kallona nayi wurin da Nana da mijinta dake rik'e da wandonshi yana mata magana amma bana iya jiyosu.... Zazzaga Nana tayi tare da cewa wallahi ka mutun ba abinda ya dameni idan ma ka mutu ko ka sakeni ai dubunka suna can suna jirana, magana ya sakeyi still banji abinda yace ba, Nana kuwa ta sake d'aga murya cewa bazan koma d'akin ba, kamata yayi da kokowa yana k'ok'arin turata cikin d'aki, d'an gajeran tsoki nayi tare da tirr da Allah wadai da wannan hali.... Bansan yanda suka k'are ba na koma nayi kwanciyata naci gaba da bacci na. Tunda na kwanta ban sake farkawa ba saida aka fara kiraye kirayen sallah asuba...... 17/08/2019 *JAMILA MUSA*🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 11 Tashi nayi na fito nayi alwallah, bamma kowa magana ba na koma d'akina... Kuma koda na gama sallah kwanciya na k'arayi dan inajin gajiya sosai ga kuma bacci. Amma k'iri k'iri baccin ga yak'i zuwa, hankalina da tunani na gaba d'aya ya tafi ina tunanin irin yanda Nana ta tozarta mijinta daren jiya a cikin bainannasi, miji da yake da daraja yake da matsayi yake da mutunci abin tattalawa idan Allah ya baka, ubangiji ya rataya ma Nana rigar arzik'i amma tana k'ok'arin yagata ta ratayawa kanta rigar wahala, idan har Nana ta fito daga gidan mutunci ko a gaban d'iyanta batayi wannan iskanci ba amma shine har ta fito tsakar gida kuma gidan ma na haya dan ta nunawa mutanen gidan cewa ita ta hana mijinta hak'k'inshi. Gaskiya abinda wasu matan sukeyi bai kamata ba, duk yanda akayi a zaman jiya aka rud'awa Nana tunani, ashe kuwa idan har zaki biye ma labarin "yan iskan mata babu ranar da hankalinki zai kwanta a gidan aure, su basuyi auren ba kuma su hana masu zaman auren suyi aurensu, sai su rud'aki da zance babu labarin k'arya a samu a kakkab'oki sai kin fito daga gidan mijin kizo kiga labari yasha banban..... Maganar Karima najiyo tana cewa jama'an gida ku fito majalissa d'inki duniya ta fara tattaruwa, ga A' i nan ta taho da labari, Nana tace ai bama labari kad'ai tazo dashi ba naga ta shigo da leda duk "yanda akayi daren jiya anci kaza mu ta ragowa sauran, kaji jakka sai kace rainon mayu dan ubanta. Hayaniyar matan gidan naji da alama kowa tayo waje, agogo na kalla naga duka 6:22am, gaskiya dai hakan bai kamata ba da zasu yadda dana basu shawara amma bara nima na fita wajen mu gani.... Nana na gani tana wanke fuskarta tare da cewa ai ilimi yafi sallah ita sallar bara a jingineta idan na gama d'aukar darasin nayi ta daga baya..... Kallonta nayi k'asa da sama amma banyi mata magana ba, duk yanda akayi Nana uwayenta jahilai ne, wata zuciyar tacemin karki zargi iyayenta Sultana wallahi kina iya ganin babu laifinsu d'a nawa kake ba tarbiya idan yaga ba idonka ya barbad'ar da ita yayi wanda yake so. Ina isa inda kowa yake na kalli A ` i, nace gaskiya ki daina yo mana sabko duk fa masu gidan basu fita ba kawai sai ki baro gidanku kizo ki hana mazajen wasu baccin safe ? Irin haka da kukeyi gaskiya bai kamata ba, kallon Nana nayi tare da ci gaba da cewa gaskiya kuma matan gidan nan kuna da naku laifi da kuna zamanku a wurin mazajenku baku fito ba babu wacce zata rik'a dako muku sammako ta hanaku samun ladar kwanciya a jikin mazajenku..... Nana zatayi magana A ' i tace barta in bata sani ba a fad'a mata, kallona tayi tare da cewa ke Sultana kinsan makaho idan yana kashi baisan ana kallonshi ba sai an tsokalo d'uwawunshi, munsan tal munsan sal abu d'aya yasa bazan gaya miki ko waye ubanki ba da rayuwar gidanku amma yau dana bud'e miki zani cikin kasuwa. Ke harma kina da bakin da zaki zo ki wani ce an hana mazan wasu bacci , ina kika san wannan keda uban naki ma ko gidan bai kwana..... Murmushi nayi ba tare dana nuna naji zafi akan tabo Babana da tayi ba nace..... Ai duk ubanda ya ganni yasan ubana zauna gida ne, ko bai kwana ba kinsan yayi k'ok'ari kuma ya fita hak'k'in mata tunda har ga sakamakon mu ya fito, duk namijin daya zauna gida ai soko ne tunda babu k'ashin zuciyar da zaisa ya fita neman abinda zai ba iyali, niko zuciyar ubana tsaye take wurin nema ya nemo aci asha kuma ko bai kwana gidan ba da safen idan ya dawo suma matan gidan zai basu hak'k'insu kinga kuwa dan bai kwana ba ai ba aibu bane ba tunda dai abinda suka aure shi danshi d'in ai yana basu bai hanasu ba. Saboda mata da yawa wannan abun dake kika raina su sunsan darajarshi, wasu matan kuwa zasu iya hak'uri da talaucin namiji amma wannan abin d'aya da kike magana akanshi basu yadda su rasashi ba, wata macen kuma mijinta ya daketa ya hanata abinci amma idan dai zai kwanta da ita ta samu gamsuwa zatayi hak'uri taci gaba da zama dashi a haka tasan arzik'i na Allah, amma wata ita ba shi take mawa ba rayuwarta da tunaninta ya tafi wurin tunanin neman duniya, kamar dai ni dake kinga ba abun ya fiddo mu ba kasuwanci muka d'auke shi, tou haka matan gidan nan suke su ma, da mazajensu masu kud'i ne ko sunyi wani abun wani sa d'aga k'afa dan duk yanda ka raina d'an tsintsu bakacin shi da gashi, namiji ya sakarwa mace ragamar gida ai dole ta koma mijin shi ya zama matar, amma duk da haka dai ki sani Allah ba ruwanshi da kin nemo kinba miji tunda hak'k'in cida da sha sutura da wurin zama lafiya da ilimantar wa duk saida ya d'auki alk'awarin zaiyi a gaban waliyyanki , To tunda anyi auren kin gane bazai iya ba ai sai a raba auren ki huta amma bawai ki zauna kiyi ta yayar ma kanki zunibi ba, zaiyi wuya kiji mace taje gidansu takai k'arar mijinta yana basu abinci so d'aya a rana. Amma mafi yawancin mata namiji ya hanasu hak'k'insu ko baya gamsar dasu sai kinji sunyi tsegumi, aba k'awaye labari aba mak'ota labari aminiya da duk wanda kike hud'd'a dashi sirrin mijinki fallashshe ne, tou wa kikayi mawa ? Nidai shawara ce idan ta muku zafi sai kuyi hak'uri, amma ya kamata ku rik'a sirrinta sirrin mazajenku domin dai wannan sirri ba abin yayad'awa bane shi yasa yake rufaffen sirri ko an shiga d'aki sai an rufe k'ofa.... Tsoki Nana tayi tare da cewa mu idan zaki zauna kiji ki zauna idan bakiji ki k'ara gaba, Karima tace da Allah kyaleta tafi ma mill tsayuwa bamu fasa zancenmu, ke A ' i albishirinki ....! Saida A ` i ta harareni sannan tace goro, Jiya fa Audu yaci ubanshi da gudu ya biyo Nana har tsakar gida, kallon Nana tayi tare da cewa kai jiya fa Nana tayi bala'i gidan nan , can naji gurnanin munafiki kamar an kwacewa mahaukaciya diyarta..... Ke Nana bada dai labari da kanki kinsan masu iya magana nacewa wak'a bakin mai ita tafi dad'i, mu na waje muka gani bamu kalli na d'aki ba. Tab'o ledar hannun A ` i tayi tare da cewa da Allah idan dai namu ne ki bamu mu cinye sai miyau na yake tsikewa, mik'a musu tayi "yan iska masu kama da maguna suka rarraba suka cinye, Nana na cewa dan Allah A ` i ki kawo min ice cream rabona da insha shi tun ina budurwa, Karima ta katse ta da cewa haba da Allah bamu labarin Audu ki daina wani zancen ice cream, lashe hannunta tayi sannan ta fara cewa, in fad'a muku tunda na ganshi ya shigo da leda nasan dole yana buk'ata... Ajiye ledar yayi a gefe na tare da cewa karfa kiyi bacci, inajin yace kar nayi bacci nasan tafiye yake da damuwarshi, saida na bari ya gama abinda yakeyi tsaf yazo ya hawo ta bayana yana wani shashshafoni na fara mutsirniya, cikin raunanniyar murya magana mai fitar da numfashin wahala yace kar muyi haka dake Nana yau kusan sati biyu kenan kina hanani hak'k'ina bakyajin tsoron fushin Allah ya sauka kanki ......? Aiko na b'ata rai nace gaka k'atoton wanda fushin Allah zai saukar mawa , ai idan dai har kaga ka kwanta dani tou wallahi sai ka biyani duk bashin da nake binka..... cikin rawar jiki ya fara k'ok'arin juyoni yana cewa kiyi hak'uri Nanata wallahi ba'ayimin biyan bashin ba, kuma banyi ciniki sosai ba yau abinda na samu gashi nan na biya na dafo miki indomie, tsoki nayi tare da cewa ai sai ka cinyeta ka kwanta kayi bacci. Haba Nana idan dai har kika ga anci ko ansha saida natsuwar ci, ina tare da babbar yunwar da abinci bazai gusar min da ita ba kin sa na zama wani susutacce na zama kamar wani tab'ab'b'e banda natsuwa bare kwanciyar hankali kiyi hak'uri don Allah yauma karki ce zaki hanani.... Ai ban gama jin zancenshi ba na duro daga saman gado nayo waje..... Ni kuma naji tana wannan haukan shi kuma ya jata suka koma d'aki. Murmushi nayi tare da cewa kin burge Nana.... Tou me ya faru bayan kun koma d'akin ne ? Tunda na lura basa san gaskiya shi yasa nima zan biye musu mu zama riftattun gaba d'ayanmu, Nana tace ai koda ya maidar dani d'aki da k'arfin tsiya babu abinda na yadda ya shiga tsakani na dashi, yayi magiyar yayi nacin kuma ya jaraba ansa ta k'arfin tsiya amma ya gagare shi, dole ya hak'ura ya fita baima kwana gidan ba...... Dariya nayi tare da cewa tou ina kike tunanin ya tafi Nana ? Yo can shi ta matse mawa koma gidan uban waye ya tafi bai dameni ba wallahi saiya biyani bashi na ko zaici gaba da kwanciya dani. A ` i kuwa cewa tayi kwarai Nana karki sake ki yadda ko gidan haya kake zaune kud'in wata ya k'are idan baka biya ba no uziri tashinka akeyi, ya baki idan babu kullum yaita kwanan hak'uri, gaba d'aya suka bushe da dariya...... Banda ni da nabi Nana da kallon tausayi !!! Mijin Karima ne ya fito cikin kunya yana san ya shiga bayi amma kunya ta hanashi fitowa dan yanzu mun k'ara yawa, daya d'aga labule ya hangomu sai ya koma, k'arshe dai hak'ura yayi da wanka yasa rigarshi yabar gidan..... Fira akaci gaba dayi tunda muka zauna har zuwa yanzu babu macen data tashi koda wasa, ganin rashin aikin yin nasu bashi k'arewa yasa na tashi dan ina da wurin zuwa anyi firar dare dani idan banyi baccin wuri ba, Saida na share d'akina na gogeshi tass na kunna tsintsiyar k'amshi sannan na zuba ruwa naje nayi wanka, ina fitowa na shirya saida na gama shiri na sannan nasha ruwan tea ko biredi babu ina gamawa nayi ma mutanen gida sallama tare da rufe d'akina nayi gaba abuna..... A zaure na sauk'e nik'af ina na fice daga gidan tare da addu'ar yo babban kamu idan na fita, A ` i na gani tsaye da wani amma bansan ko waye ba, ni mamaki ma ya kamani dan bansan lokacin da A ` i ta fito daga gidan ba... Har zan wuce naji tace ina zuwa haka Hajiyata ? Yaye nik'af ina nayi tare da rage girman idona na dama nace farauta zanje kinsan sai ka gane girman gida kake sanin ta inda zaka fara shara.... Murmushi A ` i tayi tare da matsowa kusa dani ta d'an rik'o k'uguna da hannu d'aya, sannan tayi min wani irin kallo wanda ni bansan abinda yake nufi ba...... Saida ta wani yi k'asa da murya sannan tace da ganinki zakiyi tunon asiri amma ina gargad'inki da ki rik'awa bakin linzami ta k'arasa maganar tare dayin murmushi, bud'e idanuwa nayi dukansu wanda idan har na d'an ragesu na bud'esu lokaci d'aya nasan ina k'ara kyau kuma mutane sunsha fad'amin haka. Kallonta nayi da duka idanuwana sannan nace dama tunda kike kin tab'a ganin mazinacin da yayi sirri ? Miya had'a karuwa da sirri dama ? Ai da amana da kunya da sirri da gaskiya duk karuwa bata dasu, kunya tana tasowa ne daga b'oye tsiraici tou ban b'oyeshi ba zan bud'ashi wa duk wani mai kud'i ya gani, kinga nan rashin kunya ta fito, daga inda babu kunya kinga babu imani duk mutumin da baida imani kuma bashi tare da rahmar Allah, ina bud'ewa ga maza, namiji kad'ai ya isa ya gani yasha kuma ya tab'a dan haka sakarmin k'ugu daga yau karki kuskura ki sake tab'amin jiki, idan har na baki sha'awa tou ki zama namiji kizo da dubu dari shidda sai in baki duk abinda kike gani a jikina ya burgeki, na k'arasa maganar tare da sauke hannunta a jikina.... Kallona A ` i tayi tare da cewa ai duk saurin anguwar zoma ta bari a haihu ? Duk saurinki kin bari kiji uzirin da nazo dashi..... Bud'e k'ofofin hancina nayi sannan nace ai tunda har aka tanaji aikin ungozance ansa haihu tana zuwa kinga kuwa duk daren dad'ewa amfaninta zaizo. Tou ni bana jira idan na gani saina tanka na dakatar dake ne tun kafin cikin ya samu bare kisa ran ansar haihuwar.... Na sanki cikinki da waje, duk macen dake gidan nan nasanta kuma tun ranar da na kwana na gama karatun halin kowa, kwalwa ta gane inda mutum ya dosa Allah ya bani amma bai bani kwalwar gane rubutu da karatu ba, ina iya gaya miki duk macen dake lesbian a cikin gidan nan , kuma ina gane duk macen da namiji ya kwanta da ita ba tare da na sani ba, ki kiyayeni ina da had'ari ne mai girma domin nima kaina tsoron kaina nake, ki fita idona tun kafin inyi miki terere....... Shiru A ` i , tayi ta kasa magana..... Murmushi nayi tare da dafa kafad'arta nace yawwa kisan wani abu gaskiya ni bana gaba da mutum ina so abun nan ya tsaya iya mu biyu, zan wuce ki gaishe min da mijin Nana kuma bazan bata labari ba , ina fad'in haka nayi gaba abuna..... Cin amana da rana k'iri k'iri wannan fa shine an raka zomo rami an dawo.... A ` i takai Nana ta barota gashi kuma tana tare da mijinta, kila ma jiya da yayi zuciya da Nana wurin A ` i ya tafi ya kwana, tabbas ma can yaje tana nan tana haukan banza mijinta yaje ya siyo ma k'atuwar banza kaza taci ta rago musu.... Zuciya ta ce tace Sultana kiji tsoron Allah zato zunibi, tsoki nayi tare da cewa wannan ai ba zato bane abinda yake filin Allah kowa yana gani dandai kawai gaskiya bata fad'uwa, sudai suka sani amma idan tayi tsami kowa yaji. Napep na tare na fad'a mishi inda zanje, ciniki mukayi na shiga yaja muka tafi. Yau babu inda zan sauke zango sai wurin Alhaji mai gidan "yanci, wato inda Umar yakai ni da farko ban shiga ba na dawo, dalilina na haka kuwa yanzu zakuji....... 18/08/2019 *JAMILA MUSA Ce* 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 12 Abinda yasa banbi Umar mukaje gaban Alhaji saboda na shirya lafiyayyar yaudara da zanyi masa, sana'ar karuwanci tayi min kad'an gaskiya dan haka dole sai na had'a da sata, shekaru biyu kacal zanyi a cikin wannan mummunar d'abi'ar, ina so na shigewa Alhaji sosai a rayuwa idan ya saba dani zan kunce dawakan Dikko duk in siyar dasu, nasan duk doki d'aya za'a siya da kud'i masu yawan gaske. A wancan lokacin da munje tare da Umar Alhaji yaga fuskata tou kud'in Umar da nayi wayau na kwace masa tou Umar zai koma ya fad'awa Alhaji cewa wannan yarinyar b'arauniya ce ayi hankali da ita... Bani da tabbas kuma bani da alkibla nima kaina tsoron kaina nake bansan abinda yake damuna ba umarni kawai zuciyata ke bani ni kuma ina biye da ita..... A k'ofar gidan Alhaji napep ya sauke ni, kud'inshi na bashi ya wuce nima na shige ciki, kaina tsaye na tunkari gidan babu wani tsoro fargaba bare kuma jin kunyar kowa amma har yanzun ban cire nik'af ina ba..... Ko mai gadi baiyi yunk'urin dakatar dani ba domin dai yasan mata abokan hud'd'ar ubangidan nasa ne... Hanyar da Umar yabi dani hanyar nabi naci gaba da tafiya har na shiga cikin palon gida.... Saida na shiga cikin palon na cire nik'af ina, d'an kallon palon nayi sannan na kallo inda hotunan mak'iyi Dikko yake raina ya b'aci sosai tsinan ne duk shine silar rushewar gidanmu kowa ya bazama ya shiga duniya, duk da bai sissiye ba da muna zamanmu cikin farin ciki, idan dai kud'i yasa kayi mana haka nice zan mayar dakai talakan k'arfin da yaji, uhum da kinsan waye Dikko da baki ce haka ba ..... Sallama na kwarara daidai yanda nasan za'a iya jiyoni, daga ciki naji ance shigo mana ! Inda naji sautin maganar ya fito nabi na shiga, kwance mutumin yake saman gado ya wani baje sai kace anyi b'arin asara... Kallo d'aya nayi masa tare dayin murmushi na zauna a gefen gado, kuma nayi karatunshi tun shigowa ta bakin gwargwado kuma na fahimci wasu d'abi'u nashi, da gani zaiyi sauri fushi kuma yana da saurin sauka, yanayin shi ya nuna abun duniya bai rufe mishi ido ba, amma wannan da ganin idonshi mayen mata ne lallai wannan idan ya dafi mace aradu mai ansarta sai Allah...... !!! Alhaji barka da yini, cikin sakin fuska ya amsa min da cewa barka dai malama ya kike ? 'Dan gyara zama na nayi tare da cewa lafiya qalau ya aiki ? Kallo na yayi tare da cewa ki ganni kwance kuma kice min ya aiki ? Murmushi nayi tare da cewa ai na kwance kuwa shi yasha aiki Alhaji inba ba'ayi tuk'in zaune ba ai anyi na kwance.... Kallo na yayi tare dayin dariya irin tasu ta gogaggin "yan bariki sannan yace wace ce ke ? Kama kaina nayi tare da tattaro natsuwa ta dan ni nawa ba kalar nasu bane, saida na tattaro class ina sannan na d'an rage yawan fara'a , suna na Maryam Aliyu Binna........ Amma anfi sani na da Sultana. Talla na kawo maka da fatan zaka siya ? Na k'arasa maganar tare da kashe mishi ido d'aya.... Dariya Alhaji yayi tare da gyara zaman belt inshi sannan yace yarinya me kike siyarwa ne ? K'addara......... !!! Kasan kowa da irin tasa k'addarar haka kuma kowa da irin k'addarar da yake siyarwa, idan talauci ya ishi mai rai yakan siyar da duk wasu abubuwa nashi daya siya ya adana, manoma sukan b'oye hatsi yayin da sai yayi tsada suke siyarwa, dillalai kuwa sukan adana k'addara ta k'asa sai tayi kud'i su siyar, macen da kud'i suka kama idan tayi ajiyar d'an kunnen zinari zobe ko awarwaro wannan talaucin zaisa ya ziyarci kasuwa, yayin da duk macen da tasan ciwon kanta take k'ok'arin adana tata k'addarar da Allah ya bata kyauta sai taje gidan mijinta, Ni kuma talauci ya dameni ba gidan zama bare motar hawa, kuma ban ajiye hatsi ba ban aje gold ba, shi yasa na d'auko nawa mutunci zan siyar amma sai na lura babu wanda zai siya da daraja idan ba kai ba, dare d'aya tak zaka more amma farashin farko kuma ba tayi miliyan d'aya ne, Ka ganni dai a fuska gwanin burgewa, masana sirrin mata sunce duk macen data cika muni zaiyi wuya tayi wani armashi, sai kuma sukace kyakkyawar mace kuma wannan riba biyu ce harda gyara ma, karfa kaga kamar ina yaba kaina ne fuskar gida ba itace take nuna tsarin sa da haduwar sa ba, sai an bud'e an duba ake ganewa.... Duk mota sunanta mota amma wata motar bata kai mota ba, tou haka take ga mata duk mace sunan ta mace amma wata macen muna mata ce..... Na k'arasa maganar tare da kallon Alhaji nayi masa kyakkyawan murmushi mai tattare da jan hankali. Saida na kauda kaina sannan nace amma ina da sharadi d'aya , idan anyi ba'a sake maimaici wannan shine sharad'in kasuwata idan zaka zuba hannun jari bisimillah, na mik'a masa hannu na da niyar mu k'ulla alk'awari.... Gyara kwanciya Alhaji yayi da niyar magana amma na lura da yanayin fuskarshi kamar bai yadda dani ba, dan haka na tare maganarshi da cewa karka cuci kanka wannan harka duk taimakekeniya ce , ka bani gishiri in baka mand'a , kaga masanya ce za'ayi fa ni wannan ba matsalata bace kud'in ne kawai damuwa ta, ka yadda na rana d'aya tak 👌🏻........ Kallo na Alhaji yayi tare da cewa tou ai ked'in ce kin tsananta miliyan d'aya fa..... Kin kuwa san girman miliyan Sultana ? Idan na baki ita ina zaki zuba ta ? Waye zai d'aukar miki ita ? Me zakiyi da ita kuma ? Ajiyar zuciya na sauke tare da cewa, wurin zubata da d'aukarta da abinda zanyi da ita duk ba huruminka bane ba, kayi kawai ka bani idan kuma baya yuwuwa in hak'ura inyi gaba kila na dace....... Tashi yayi zaune tare da tattaro duka hankalinshi gareni sannan yace karki k'i fad'amin, kika sani ko zan iya miki maganin damuwarki ne ? Kuma kike maganar miliyan d'ayan d'aya kika sani ko in baki abinda yafi miliyan d'in ? Ni kud'i ba matsalata bane amma ina san sirri dan duk wannan harkar da kikaga inayi gaskiya banayinta da d'anyar kwalwa saboda gudun b'acin rana..... Alhaji kenan idan na fahimta kallon yarinya kake min ko ? Tabbas a zahirance ni yarinya ce amma a bad'ini ni mai tunani ce, babu wanda ya koyamin yanda ake bariki ni na koya da kaina, ban yadda da zama k'ark'ashin kowa ba nima saboda gudun b'acin rana, "yanci na, mutunci da kowa yake tak'ama dashi ya siyar akan kud'i k'alilin k'arshen wulak'anci da tozarci mak'iyina da bana k'auna shine ya taka ruwan ciki na, a cikin gidansu ya keta min hijabin da nake ta boyewa shine yayi mata kaca kaca.... Shiru nayi saboda idan dai har naci gaba da magana zan iya kamo sunan Dikko in d'ura wa uwarshi zagi. Hak'uri Alhaji ya bani tare da jawoni jikinshi yace kiyi hak'uri ku matan ne baku da amana sai a had'a kai daku a cuci mutum, murmushi nayi tare da cewa ai ko zanyi cuta bana tsaya inda aka sanni ba, kana dai da kud'i kusa dakai dan bana amfani da banki danma karka wani ce zaka turamin..... Cikin raunanniyar murya yace karki damu Sultana d'akin nan cike yake da kud'i, zan sake magana ya had'e bakina da nashi wuri d'aya labari ya fara canja salo..... Murmushin mugunta nayi tare da bawa Alhaji duk abinda nasan zaisa ya samu natsuwa.... Ya dad'e yana gurje kud'inshi kuma ban waniji wata damuwa ba, har saida ya gaji dan kanshi ya kyaleni. Sauka yayi daga saman gado ya nufi toilet ni kuma ina nan kwance, yana shiga na zaro wayata dana soke a jikin gado wanda duk abinda mukayi da Alhaji saida na d'auka, dariya nayi bayan na gama kallo sannan na mayar da wayata cikin jaka... Kafin Alhaji ya fito har na gama saka kayana na maida nik'af ina na zauna bakin gado.... Ina jiran fitowarshi ! Bai wani dad'e ba ya fito da sauri ya nufi wurin wayarshi saboda tun dazu ake kiranshi banyi gigin dubawa ba saboda ko na duba bana gane suna.... Kayi hak'uri mai gida shine dai abinda yake ta maimaitawa, bansan abinda abokin wayar yace mishi ba naji yace Eh an basu ranka ya dad'e , tou insha Allah, Allah ya tsare ubangijj ya k'ara taimakawa. Sallama sukayi dashi Alhaji ya ajiye waya sannan ya kalloni tare da cewa ke yanzu ya zamuyi ne ? K'afa d'aya a saman d'aya na d'ora sannan na ajiye hannuwa na ta baya nace bani zakayi in wuce marece yanayi, tou baza kiyi wanka ba ? 'Dan girgiza k'afata nayi sannan nace bana sauke najasa a wurin da bai kamata ba ka bani kawai na wuce..... Tou waike taya zaki d'auki miliyan d'aya ne ? 'Daga nik'af ina nayi tare da cewa karfa ka raina min hankali ka bani in wuce kana b'atamin lokaci kaji.... Murmushi yayi tare da cewa ya zaki d'auki zafi da wuri haka ? Tou ya zakiji idan na hanaki kud'in nan, murmushi nayi tare da cewa kai kuma ya zakaji idan ka samu hotunan vidio abinda mukayi a yanar giza gizo ..... Na k'arasa maganar ina masa kallon rainin hankali. 'Daure fuska yayi tare da cewa sai in kashe ki, murmushi nayi da gefen bakina tare da cewa tou da suka shiga duniya kuma ya zakayi da duk wanda ya gani ? Ta ina zaka bi ko gogesu a cikin wayar kowa ? Akwai "ya "ya akwai surukai ga kuma matanka abinda kake b'oyo tou gashi a cikin wayar "yarka ko d'anka tou ya zakayi dasu......... Zufa ta keto mishi sosai, dariya nayi tare da cewa tou goge ai haka ma bazata tab'a yuwuwa ba, kawai nima nayi maka barazana ne kamar yanda kake neman hanani kud'ina, kaga abinda bazai yuwu bane bani na wuce, Ya kama kanshi sosai dan haka yace zan baki dubu dari biyar yanzu anjima ki dawo ki amsa sauran, gaskiya idan na tafi bana dawowa ka bani kawai sai mu rabo lafiya, tou wai babu zan baki ? Nace itama babun idan tana kamuwa ka bani ansa zanyi ba cemin kayi d'akin ka cike yake da kud'i ba ? Mutum cikakke mai arzik'i kamar ka ai bai kamata ya rik'a d'aga murya ba akan miliyan d'aya kacal ba, miliyoyin da suka tafi babu dalili baka san iyakarsu ba bare wannan idan ka bada ita ai kasan ta inda tabi ta wuce... Dubu d'ari biyar ya bani yace muje in baki sauran suna cikin mota, cikin jakata na zuba dubu dari3 muka fita dubu dari biyu na hannu na, muna zuwa ya bud'e mota ya bani sauran kud'in, bud'e gaban mota nayi na shiga tare da cire kallabin kaina na d'auresu a ciki nace ka ajiyeni bakin titi.... Baimin magana ba ya tada mota muka tafi, saida muka tsaya inda zai saukeni nace da Allah rubutamin number wayarka, har yanzu baiyi magana ba ya ciro biro a gaban aljihunshi ya rubutamin a jikin takarda ya bani, Nima ban sake magana ba na bud'e mota na fita, napep na tare dan zuwa gida, a k'ofar gida ya saukeni na shige, da sallama na shiga gidan sannan na wuce d'akina ina shiga na ajiye kud'in na zuba ruwa na tafi dan tsarkake jikina banyi ko azahar ba kuma ga la'asar ta kusa.. Saida na gama sallolina sannan na dafa indomie naci, bayan na gama na zazzage buhun kayana na zuba kud'in a k'asa sannan na d'auki kayan na maida daga sama, fitowa nayi tsakar gida na nufi majalissar matan aure.... Barkan ku da hutawa mata masu duniya, Karima tace wai ke duk yau ina kika shige ne ? Ban bata amsa ba na canja tambayar da cewa yau kuma zawarawan anguwar nan dame suka zo mana ne ? Karima tace ai gasu nan sai ki zauna ayi dake, zama nayi saman takalmana sannan na kalli inda Nana take kwance a saman cinyar A ` i wai tana kakkab'e mata dandirof, Karima kuma sai cewa takeyi Allah dai ya tsinewa talauci albarka, kullum a rasa abinda za'ayi ta baka sai tuwo maganar d'aya dai tuwo tuwo babu wani ci gaba kullum zance kenan, shi yasa gani nan kullum sai bushewa nakeyi ina k'armashewa kamar mai cutar kanjamau. Niko da bani da zuciya nace aiko Karima ki godewa Allah, domin dai Allah yayi miki rufin asiri ke kin raina tuwo ko ? Na tambayeta, bata bani amsa ba naci gaba da cewa yo aike cin tuwo yanzu basai wanda Allah yaso yake ci ba ? Da safe kina dama d'an kokonki da rana idan Allah ya hore zakiyi d'an wanke ko teba wata rana ma har taliya kuke dafawa, da daddare kuyi tuwo kuci ku k'oshi keda "ya "yanki kuma duk daren duniya naga sai mijinki ya shigo miki da fura, tou ina laifi ? Aike tsakaninki da Allah saida kice Alhamdulillah bawai ki zauna kiyi ta tsinewa talauci ba ai ina ganin haka kamar rashin godiyar Allah ne..... Saudatu tace, { itama ba'a gidan take ba shigowa takeyi } ai rayuwa tana san canji kullum abinci d'aya an kama dindindigau kamar kukan mutuwar uwa, ai ya kama a samu sauyi mana Sultana. Nace haba Saude ai duk namijin da kikaga ba'aci mai dad'i a gidanshi ba tou baya dashi babu namijin da yake so a tsarewa iyalinshi, Saudatu tace ai wallahi k'arya ne mijin Karima yana da kud'in da ko naman rago saiya ciyar da ita dashi, dandai kawai had'in fad'a baida dad'i amma wallahi dasai na fad'a mata abinda yakeyi da kuma inda yake kai kud'in nashi , ita ya rainawa wayau ya barta nan tana ta sassak'ar tuwo sai kace matar ladar noma. Daga wannan maganar har Karima ta kawo wuya, ta fara zazzaga luk'a luk'an zagi tana cewa ai da ganin biri yayi kama da mutum tsakanina da Nuhu sai Allah ya isa ban yafe mishi ba, kuma zai dawo gidan ya sameni saina ci uwarshi.... Kallon Karima nayi tare da cewa idan dai kuna biye ma zawarawan anguwar nan wallahi duk sai sun kashe muku aure, baku san maganar d'auka ba baku san abinda kuke fad'a musu ba ku biye musu su kaiku su baroku, su basuyi aure ba kullum suna biye daku suna halakar daku, Karima tace ai wallahi Sultana na yadda da maganar Saude saboda rabon da muyi kwanciyar aure dani da Nuhu yau anfi k'arfin wata d'aya, dama idan ba neman mata yakeyi ba ai kema kinsan abunda bazai yuwu bane ba.... Tsoki nayi tare da cewa ai wallahi saina fad'a miki ko zatai miki zafi, ba Nuhu ba wallahi koni dakel nake iya zama kusa dake, mace da aka santa da gayu da kwalisa da k'amshi da tsafa da tsaftacewa tou ku matan gidan nan ba haka kuke ba, kullum safiya kunzo kun jibge a k'ark'ashin inuwa ba wanka ba wanke ido babu sallah bare salati, baki cuwai cuwai ba abinda kuka sani saidai inuwa ta k'are ku ja tabarma ku k'ara gaba, Kun fito tun kafin mazajen ku su fita daga d'akin ku kun rigasu fitowa, yara sun kwana zabga fitsarin kwance baku tsaya kun gyara kun wanke ba, yanda namiji yabar d'aki haka zai dawo ya taddashi, baku iya magana da mazajenku ba kuna ma mazanku magana muryarku ta kere tasu mace da aka sani da sanyi, kina ma miji magana tsawa tsawa kamar yaron gidanki, duk daren duniya idan Nuhu ya dawo sai yayi wanka ya tsaftace jikinshi a haka zai rungumeki ki b'ata mishi wanka ? Kalli kanki Karima ji k'afafuwanki waike matar aure ! A haka har kike tunanin namiji zai samu kwanciyar hankalin da zai baki natsuwa ? Aini wallahi ko toilet na shiga mara tsafta banda natsuwar da zanyi komai a cikinshi wuta wuta zan fito dan kar in d'aukowa kaina cuta, gashin hamatarki ma kad'ai wallahi abin zubar da yawu n....... Mik'ewa Karima tayi tare da kaimin duka dan uwarki ni kike cewa kazama ce ? Rik'e mata hannuwa nayi duka tare da cewa saurara kiji ni bance miki k'azama ba kawai dai ina fad'a miki matsalarki ne, amma kiyi hak'uri ni ba'a fad'a dani gaskiya ce baki so kuma daga yau na daina insha Allah, amma duk da haka zan baku shawara d'aya dake da Nana wala Allah tayi muku dad'i wala Allah tayi muku zafi Nana tace ki rik'e banzar shawararki kila ta miki amfani can gaba..... Murmushi nayi tare da cewa tou ba damuwa na gode amma kuma ku sani bazan daina zaman majalissar nan ba, yanzu ma sallah magrib zanyi na dawo... Babu wanda ya bani amsa dan haka naje na d'auk'i buta ta naje nayi alwallah, saida nayi sallah isha'e sannan na fito majalissar su...... 19/08/2019 *NICE DAI...* *JAMILA MUSA...* 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 13 Sallama nayi musu amma babu wacce ta amsamin, na maimaita sallamar har sau ukku amma dukansu babu wacce ko kallona tayi bare nayi tunanin zasu amsa min, murmushi nayi tare da cewa aikin banza kare da gudun layya. Wuri na samu na zauna, ina zama gaba d'ayansu suka tashi suka bar wurin aka barni zaune ni d'aya kamar mayya, banji wani damuwa ba haka banji bak'in ciki ba domin dai nasan gaba d'ayansu nafi su ta ko ina da ko ina, tunda kuwa nafi su ai babu dalilin ni na biye musu muyi gaba, bawai dan ban iya ba na iya kuma idan na fara nawa bashi da kyau.... Ban tashi a wurin ba na haska wayata na fara kwafar lambar Alhaji daga saman takarda zuwa cikin wayata da nayo mishi vidio, nafi minti biyar ina rubutawa karantawa ne dai bana iyawa amma ina kwafar abu, idan kuwa zan kwafa da guda guda nake d'aukarshi, kuma zansa a bud'emin whatsApp amma ya zamar min na "yan gaisuwa saidai duk wanda zanyi magana dashi inyi masa voice note, na ajiye number shi a wayata, abinda na saka mishi shine lamba 1 Mik'ewa tsaye nayi tare da cewa bak'in ciki da fushi ba naki bane Sultana tunda kina da aikinyi, d'aga muryata nayi tare da cewa waye yake san k'amshi mu bashi turare ? Tou tabbas maik'o saidai a barwa balangu ansha gaban mai tsiri...... Kujerata na d'auko na zauna k'ofar d'akina tunda na lura suna neman su haramta min zaman tsakar gidan ne kuma aradu basu isa ba, watsa kunnuwa na nayi ina jiyo firarsu k'asa k'asa bana iya cewa naji abinda akace duka ba amma da yake Saude bata iya maganar sirri ba, bama itama ba duk matan gidan ga haka suke, ji nayi tana cewa ai wallahi ki had'ani dashi in nemi taimako.... Daga inda nake zaune nace hattara dai matar aure, idan dai an ciza a busa, ki kiyayi duniya da rayuwar mutanen cikinta, ita duniya da kika ganta juyi d'an magwaro takeyi yayin daya fad'i k'asa zai kwaso k'asa da tsakuwa, idan kika wanke zak'in zai fita idan kuma kika sha baki wanke ba zaki ci da k'asa duniya tafi karfin kowa, wanda yafiki iskanci yazo yayi ya koma ki kama kanki kuma kiyi k'ok'ari ki koma gaban Allah kina mai kamanta gaskiya, amma na horeki da ki kiyaye darajar aurenki tun kafin duniya ta juya miki baya.... Cikin hayagaga Nana tace ai ba tsoronki akeyi ba a gabanki ma za'ayi maganar dan kutumar ubanki idan kin isa ki hana wani abu in gani, tirr na fad'a tare da cewa kutumar ubana tafi k'arfin kaff zuri'arku wallahi, saboda ko da yake raba kutumar wa mata badai irinku masu tsamin daud'a ba... Kaina Nana tayo da gudun bala'i kafin ta iso na d'auki kujerata na rik'e nace wallahi kika kuskura kika iso nan saina raba miki kai gida biyu, tsoro ya hanata ta iso taja tayi tsaye, tsoki nayi tare da cewa k'aryar rashin kunya sakarkarin banza daku, insha Allah ko gani nayi zaku shiga wuta saina watsa muku fetir, ina fadin haka na shige d'akina na kyale jahilai, dan gaskiya na lura wallahi jahilci ne kawai yake cizar musu kwalwa, inma banda b'atar basira matar aure za'a kai wurin wani namiji ta nemi taimako..... *** *** *** Sati na d'aya kenan bana shiga safgar kowa a gidan da nake haya, ni dama fil'azal magana bai dameni ba, shigowa na ma gidan nan ne naga har na iya surutu idan dai har magana da sune zaisa su raina ni har kowa yake k'ok'orin magana kad'an ya dakeni tou na fita sabgarsu danni ina da wata irin zuciya da idan har na gama da abu tou fa tabbas na shafe labarinsa a babin rayuwata, niko nace hada Dikko Sultana ? Cikin kud'in da Alhaji ya bani na shiga kasuwa na kwankwaso tsadajjiyar sutura, na siyi kaya na kece raina, gyale takalmi jaka turaruka mayuka na shafawa irin ya wayayyun mata, agogo sark"a da "yan kunne "yan hannu zobuna saida na tabbatar nima na zama gogaggiyar mace ta sahun farko a fanni sutura. Sannan naje nakai dinki wurin telan da nasan shima yasan hannunshi, kuma da naje kai d'inkin na fad'a mishi cewa irin d'inki karuwai nake so yayi min, nace yamin d'inkin dako tuk'i namiji yakeyi idan na wuce saiya dakaya saiya manta da kan sitiyari yake ya tsaya ya kalleni, mukayi tsada dashi na biyashi kud'inshi tare da sharadin idan fa ya lalatamin kayana wallahi saiya biyani, yace kuma yaji ya yadda. Na gyara d'akina sosai nasa kayan kallo na sake katifa mai kyau na saka ledar tsakar d'aki na saka fanka amma ta k'asa, na kuma k'ara biyan kud'in haya daga lokacin da suka k'are daga lokacin zan siyi gida haka shine tsarina na gaba... Saina sayi gidan zama sannan zan sayi mota kuma duk zakuji ta inda kud'in zasu rik'a fitowa babu b'ata lokaci.... Hankalina kwance banda wata damuwa, banda rashin ci haka kuma babu rashin sha, cikin "yan kwanaki k'alilan na fara sauyawa, k'oshi babu abinda ya bari dan duk daren duniya sai naci nama abinda nake so ci nake ci kuma duk abinda naga dama shi nakeyi babu mai kwab'a kuma babu mai kyahra, jikina kuwa yasha mayuka gani bana jin wahalar wanka dan ko agwagwa bata kaini san ruwa ba, ya jama'a ku tayani hasko kyau ya had'u da gayu, ku tayani ganin gayu ya had'u da wanka, ku tuno wanka ya had'u da k'amshi...... Wuta Sultana lokacina ya fara...... Kalu bale gareku k"azaman mata..... Kwance nake saman katuwar katifata da tasha shinfid'a da tsaftataccen zani, { bedsheet } iskan fanka sai kad'ani yake ta ko ina, ga wani ni'imtaccen k'amshi dake tashi daga d'akin har jikina, yanzu tunani na bai wuce in addabi Bello ba abokin Babana..... Dan yanda ya haramta wa Babana wali a cikin garin shi, inda aka haifeshi ya girma a ciki yayi iyali, amma ya gudu ya bar "yan uwa da "ya "ya da matanshi tou shima katsina zata haramta yayi wali a cikinta, idan kuma yayi iskanci saiya d'aure kayanshi yabar birinin katsinar gaba d'aya.... Hannu na, na saka k'ark'ashin katifa na jawo wata "yar k'aramar kwalba dana anso hannu wani d'an daba, ya fad'amin sunan abun amma wallahi kafin inzo gida har na manta, abun fesawa gareshi kamar na turare, kud'i na bashi ya siyomin nace mishi abinda idan na fesawa mutum kawai zai kama bacci babu b'ata lokaci shine ya kawomin shi.... Tashi nayi na rufo d'akina dan ina so in gwada inga ko abun yanayi, saman katifa na kwanta sannan na fesa shi a fuskata..... Luuu wani bak'i na gani ya gittamin daga nan ban sake sanin inda kaina yake ba saida 11:30am tayi..... Salati nayi tare da godewa Allah dana farka na ganni a duniya, d'auko kwalbar nayi tare da sunbatar ta, tabbas kece abokiyar tafiyata, amfani biyu zakimin daga Bello sai Dikko daga nan aikinki ya k'are zan yadaki shikenan..... Wanka naje nayo tare da d'auro alwalla nazo nayi sallah asuba da ban samu nayi ba, ina gamawa na hau shiri domin yau ba abinda zai dawo dani gida sai nayi ido ido da Bello kuma saina tabbatar da k'udurina akanshi..... Mai da powder na shafa sai kwalli dana shafawa idona, ban shafa jan baki ba saboda bakina baya buk'atar shafe shafe sai kuma lura da nayi da irin manyan mata mawuyaci kuga sun daddab'awa fuskarsu irin abinda muka shafawa, irinsu jagira aishadow duk basa shafawa shi yasa idan suka shiga wuri suke fita daban, bana buk'atar bilicin koda na kasance ni b'aka ce shima ku lura da kyau bilicin na maciyata ne, d'iyan masu kud'i basa shafe shafe mayuka gaskiya.... Doguwar rigar shadda getzner na saka bak'a, kuma tayi matuk'ar martabani domin dai ta zauna min a jikina ciff na d'aura d'an kwalina coge, na kawo gyale na ida kafe wankan dashi komai dai dana san zai martabo min mutunci na saida na saka a jikina, sannan na yayyafa ruwan turare nayi gaba... Tun kafin in fito k'amshin turarena yakai tsakar gida, a lokacin dana fito ina rufe k'ofar d'akina kuma gaba d'aya hankalin duk wanda ke gidan saida ya dawo kaina, ina rufe d'aki na saka makulli na a jaka na wuce abuna banma kowa magana ba... Da kallo suka bini domin dai sun gane kura ba sa'ar kare bace ba..... Tunda na fito gida har nakai bakin titi na zama abin kallo ga jama'a , ban damu dasu ba domin dai duniyar yanzu gaba na bata ba baya ba..... Napep na tare na fad'a mishi inda zai kaini na shiga muka tafi, cikin "yan mintoci kad'an muka isa, na sauka na bashi hak'k'inshi, majalissar ciki take kamar zata fashe saboda yawan dandazon mazan dake cikinta, ina fitowa napep duk wanda ke wurin idonshi ya dawo kaina... Banji fargaba ba haka kuma ban daburce ba, banji bazan iya tafiya ba dan ana kallona duk wani bargaba da kunya ko tsoro duk basa tare dani a wannan lokaci, tafiya na farayi zuwa wurinsu na k'addara ma kawai ba maza bane mata ne.... Tsofaffin banza tun daga yanayin kallon da sukemin zaku gane duk sun fad'o rami, kallon tarko suka faramin kamar mage ta ritsa bera. Sallama nayi musu yayin dana isa wurin, kusan gaba d'ayansu saida suka amsa kamar ana biyawa dalibai karatu.... Nima kujera naja na zauna sannan na gaishe su, duka suka amsa cikin sakin fuska, inda Bello yake zaune na kalla tare da cewa Baba wurinka nazo , tou yace amma ban ganiki ba, sadda kaina k'asa nayi sannan na d'an murmusa cikin sigar bariki nace d'iyarka ce ta wurin Aliyu Binna...... Na k'arasa maganar tare da d'ago kaina na kalleshi da kyawawan idanuwa na da suka sha da ado da kwalli nakai karshen maganar tare da d'an sassauta kallo na, sannan na bud'e idanuwan dukansu, Yashe baki yayi yana dariya kamar yaga wawan zama, sannan yace ahaf tou tou Uwar masu gida ce ? Murmushi nayi tare da cewa Eh, kinyi aure ne ? Ya tambaye ni ? Da kaina na bashi amsa cewa A , a, tou kina ina ne haka ? Ba tare dajin kunyar kowa ba nace ina bariki ne ? Dariya yayi sosai tare da cewa "yar gari kenan yarinya ta gane makoma..... Nima dariyar duniyanci nayi harsai da kyawawan hak'orana suka bayyana idan dai nayi irin wannan dariya ni kaina nasan tana k'ara min kyau sosai sannan na kalleshi nayi murmushi sai kuma na kama kaina, kallon maita ya bini dashi kamar ya cinyeni a bakin titi sannan yace ina kike zama haka ne ? Ina nan tsohuwar anguwarmu daka sani dai.... Tou taso mana ya fad'a tare da mik'ewa, a raina nace wato tunda na zama karuwa bari a bini a lalace ! Zakaci ubanka domin nima kaina tsoron kaina nakeyi, duk a zuciya ta nayi magana.... 'Daukar kujerata nayi muka matsa gaba, zama nayi na d'ora k'afa d'aya saman d'aya sannan nace ya ake ciki Baba ? Am tou aike zan tambaya kinga tunda ga gida ai ba'a kai k'aruwa waje ba.... 'Dan gajeren murmushi nayi sannan nace gaskiya kam, amma yanzu kana da mota kuwa ? Eh akwai mota hannuna mana, wace iri ce ? Na tambayeshi yana k'ok'arin fad'amin nace dakata ma barshi kawai kasan ko ka fad'a bazan rik'e ba zan manta ne , Duk'owa yayi kusa dani waini zai tambaya yanda muka k'are da Dikko kwanaki, dariya nayi sannan nace ai Dikko ba abinda yayi min kuna tafiya yasa aka dawo dani gida, tsoki Bello yayi tare da cewa kaji sakaran banza wannan tunjumemiyar mace ya bari baisha ruwa ba ? Murmushin mugunta nayi tare da d'aga girarena nace kila bayajin k'ishirwar ne, tou waike kawai sai kika fara bariki abunki ? Nace sosai ma, tou ya akayi kika zab'i wannan harkar bayan baki san yanda abubuwan suke ba ? Duk zan baka bayani idan kana da wurin saukeni mu tafi kaji komai.... Tou ina zuwa, ya fad'a tare da tafiya wurin abokansu, sallama yayi musu tare da cewa zai dawo da daddare duk zasuji bayani, wani ne daga can yace kayi min register idan ka gama ina layi nima.... D'iyar abokinku maimakon kuyi k'ok'arin d'orani hanya A , a, saidai kuyi k'ok'arin k'ara dilmiyar dani.... A mota ya d'aukeni muka tafi, ko a hanya sai wani kyarma yake yana k'ok'arin kai hannunsa cikin rigata, kallonshi nayi tare da cewa saurin me kakeyi haka ne wai ? Ban bari ya bani amsa ba naci gaba da cewa ko da kayi tunanin yau zaka sameni ? Yace a , a nace tou kasa ma ranka natsuwa har muje inda zamu baje kolin iskancin namu muci karenmu babu babbaka babu wanda yaji kuma babu wanda ya gani... Kyah kyah kyah ya kyalkyale da dariya tare da cewa gaskiya ne Uwar masu gida, kunji ihu kura ta samu nama, wannan dariya itace yayi shi ya samu Sultanar banza zaije ya gurji banza a tunaninshi, baisan ni nafi shi iya iskanci ba domin dai ni naci uwarshi nasha ruwan kanwa maganin kwarnahin ciki.... Har muka iso ban sake magana ba, horn yayi mai gadi ya yaye mana get muka shige ciki, parking yayi sannan yace muje, kai jama'a kuji rashin kunya don Allah dan kwatawalci d'iyar abokinka, uhum cije lebona na k'asa nayi sannan nace masa rubutamin number wayarka don Allah a takarda, yo baki da waya ne ? Ya tambayeni cikin gatsali, murmushi nayi sannan nace aini ko a cikin kwarin k'arama ce har yanzu da sauranmu kafin mu gama nuna Baba.... Hahaha a haka ma baki nuna ba ? Nace yo dana nuna ka ganni a napep baki da dama yace tare da fara rubutamin number wayarshi, mik'omin yayi bayan ya gama, yana k'ok'arin fita nace ka sallameni kafin mu shiga mana..... Dubu biyar ya mik'omin , ansa nayi tare da jujjuya kud'in nace ashe gara da bamu shiga ba, yo Baba banda abunka wannan ai ko kud'in fira baka biya ba, zaro ido yayi tare da cewa dubu biyar ? Ke kin raina dubu biyar ? Murmushi nayi tare da cewa tou turaren dana shafa idan akace maka kayi tukwuici ai kasan nafi k'arfin ka bani 5k , koni ai nayi kyautar dubu biyar wallahi, ka bani kud'i masu yawa idan kana bani kaji malam.... Daga gaban motarshi ya jawo wani wuri kud'i na gani kamar in zabgaga ihu saboda yawansu , saida na gani sannan ya maida ya rufe kin gansu nan kud'in da zamuyi caca ne na had'a gobe na k'ara miki ki anshi 5k in mana... Babu gardama na ansa muka fita daga motar dukanmu muka shiga ciki, saida ya rurrufe ko ina mu kuma mukayi ma junanmu masauki saman gado.. K'ik'iy k'ik'iy ya cire riga ya cire wando, jakata na bud'e na d'auko kwalbata sannan nayo wurinshi cikin karairaya, yana k'ok'arin rungumata nayi ma shege feshin maganin sauro, babu b'ata lokaci ya tafi bacci rik'eshi nayi har yakai k'asa sannan na cire mishi gajeren wandonshi na dauki d'an iska hoto, nayi mishi kuma vidio ko ina saida na d'auka, bayan na gama na janye shi daga saman hanya, saida na lalube aljihunan shi kaf sannan na zauna gefen gado na shigar da numbershi cikin wayata, bayan na gama na ajiyeshi da lamba 2. Makulin motar na d'auka da jakata na bud'e d'akin na fita, cikin mota na koma saida na kwashe kud'in nan kaff sannan na rufe na maida makullin kusa dashi na ajiye, fitowa nayi na tunkari hanyar fita daga gidan, dubu biyar d'in daya bani itace naba mai gadin gidan kyauta, yana ta godiya na wuce abuna ban tsaya saurarenshi ba na fice daga gidan abuna.......... 20/08/2019 *JAMILA MUSA...* ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 14 Saida ma na fita daga gidan nakejin wani irin bak'in ciki ya tokaremin zuciyata, wallahi dana iya mota saina taho da motar Bello, zanje gida na jira zuwan shi domin dai nasan nabar baya da k'ura babu yanda za'ayi ya barni na ci kud'in nan , murmushi nayi sannan nayi magana a bayyane cewa Allah ya kawo ka lafiya Baban kwali Baban tusa..... Ban tsaya wasa ba haka kuma banyi gigin biyawa gidan kowa ba na yanki santa na fara neman gidan da nake kwana.... Tafiya mai zurfi nayi kafin na fito bakin titi, Allah kuma ya taimakeni ina fitowa na samu abin hawa ban wani b'ata lokaci ba, ko ciniki ban tsaya yi ba na afka nace muje. Inda zamuje ya tambayeni, ni kuma na fad'a masa yaja muka tafi, raina fes zuciyata dunk'ule da farin ciki na isa gida, ko mai napep 1k na bashi yayi ta zabgaga min godiya tare da jawo addu'o'in samun nasara a rayuwata... Godiya nayi masa sannan na shiga gida da sallama kamar yanda na saba bawai dan zasu amsa min ba, a , a, inayi ne dan fita hak'k'in musulinci, kai tsaye k'ofar d'akina na tsaya na ciro mukulli na bud'e na shige abuna.... Saida na fara adana kud'ina a ma'adana mai sirri sannan na fara neman abinda zanba baba uban ba'u, { ciki } saida na d'ora girkin abinda zanci sannan na fita nayo alwallah dan ganawa da mahalicci na... Bayan na fito daga bayi ne naji su Saude suna fira kuma ga dukkan alamu zance Dikko ne sukeyi, da wutsiyar ido na kalli wurin, wata bak'ar cikakkiyar buduwarce na gani tsaye, amma ban tab'a ganinta ba sai yau, kallo d'aya zakayi mata ka tabbatar tanaji da hutu domin ta huta d'in, duk inda ta fito yarinyar can d'iyar wani attajiri ne... Fasa alwallar nayi na tashi na koma d'aki na kashe d'an gass d'ina na d'auko asawaki dan inaso inji inda labarin nasu zai tsaya, dawowa nayi na zauna ban kalli inda kowa yake ba kuma banyi ma kowa magana ba na tusa buta a gaba naci gaba da gogo asuwaki a bakina.... A ` i ce ke cewa kai amma gaskiya Hafsat baki da hankali ai da ki nemi d'an mai kud'i da asiri gara ki tafi tsirara kawai ki huta, kina ganin ubanshi banza ne ? Wannan Dikkon da kike gani tun yana ciki an gama dafashi da asiri yanda Babanshi yasha wahala kafin ya samu namiji kina ganin daya sameshi da wahala zai barshi ne yai ta yawo figifigi a duniya ba tare da an bashi dafa'i ba ? Kai wallahi kimayi hak'uri , Cikin muryar sakataccin "ya "ya tace no ai da ina kiranshi wani lokaci yana d'aukar wayata amma yanzu ya daina d'auka kwata kwata, da sauri na d'aga kaina na kallesu sai kuma na basar kamar ina kallon wani wuri, wato ita tana ma da number Dikko, tunani na farayi yanda wayarta zata zo hannuna na, ba ansar wayarta zaimin wahala ba yanda zan gano sunan Dikko shine wahala a wurina.... Kawai gaba d'aya tunanina ma har ya tashi daga d'aukar number, kawai harma na hango gani nan na d'auko tsiraicin Dikko na balbad'a a social media, tabbas Dikko saina had'a shagalin partyn wulak'anta mishi rayuwa.... Tunani na ya dawo ne a lokacin da naji Saudatu na cewa aiko ki dage yarinya dan nan da shekara d'aya Dikko baya rik'uwa, tunda shi dama bai dogara da kud'in gidansu ba gaskiya Dikko yana da sa'ar rayuwa idan kika auri shi kin more rayuwa domin dai cikakken namiji ne... Banyi musu magana ba dai naci gaba da goge hak'ora na, wayau sukayi ma Hafsat suka amshi kud'i masu yawa a hannunta da sunan za'ayiwa Dikko asiri, ci gaba da tattaunawa sukayi amma hankalina baya wurin firarsu ya tafi wurin karatun halayyar Hafsat, tab'e bakina nayi a bayyane nace itama dai "yar mad'igon ce { Lesbian } Kallona tayi nima na watsa mata mayatattun idanuwana masu sa mutum ya rikice na k'ura mata su sosai domin ina so ta yabani idan har ta shigo hannu na nice zan koya mata barikin da zata kawo min Dikko k'asan k'afaafuwana nima in rama wulak'anci da yayi min dan nayi alk'awari nima sai Dikko ya lashi k'afata kamar yanda yasa na lashi tashi... Shegiya ta kuwa daskare ta kasa barin kallona, kyakkyawan murmushi nayi mata tare da cewa sannu ko ? Na k'arasa maganar tare da d'an wasa da idanuwana... Murmushi tamin tare da cewa ya kike ? Ban bata amsa ba naci gaba da alwallata... Ina gamawa ban sake bi ta kansu ba nayi d'aki inajin tana ta magana amma na basar da ita, nadai juya ta ganni maza ma sun gani sun rikice ina ga mata mayun mata kuma ? Ina shiga na kunna gas ina na kabbara sallah. Bansan yanda suka k'are ba, amma nasan tabbas saita dawo saboda taga ina da irin k'addarar da suke nema... Bayan na gama sallah na zuba abinda zan dafa a tukunya sannan na zuba ruwa na tafi wanka, lokacin da nayi wanka na dawo har ya dahu, dan haka kashe gas ina nayi sannan na shafa mai da powder, d'aurin gaba nayi sannan na zuba abinci na naci gaba daci.... Bayan na gama duk abinda nake na kunna kallo, sannan na saka kayan bacci na koma saman katifa na kame kamar d'iyar wani shege... Kai gaskiya inajin dad'in wannan rayuwa tawa, saida na kwanta sannan na bud'e data ta, lamba d'aya na gano bayan na ganoshi na tura mishi vidion dana d'auko , tare dayin voice note na tura mishi. Ina turawa na sauka online na kashe wayata gaba d'aya, na kashe kallo na rufe d'akina nayi kwanciyata....... Tashin hankali shine kalmar da Alhaji ya fad'a a lokacin da yaga vidion dana tura mishi, wata irin gagarumar zufa ta yayyafo mishi a lokacin da ya saurari voice note ina, tashi yayi tsaye cikin tsananin tashin hankali ya rasa gane a wace rayuwar yake rayuwar mutuwa ce ko ta duniya ? A gefe kuma wayarshi ce take ta kwarara ihu, lambar mai gida Dikko ce keta tsalle babu k'ak'k'autawa amma Alhaji yau kam bata Dikko yake ba, saida kiran ya tsinke sannan Alhaji ya sake kunna maganar Sultana yana sauraro, ga abinda take cewa.... _Ina mai farin cikin sanar dakai wannan mummunan labari, d'abi'a na ne yin albishir da farin ciki yayin fad'ar abu mai munin gaske, kuma nakanyi farin ciki yayin fad'ar abun farin ciki, wannan vidion dai dani dakai ne a ciki kuma kaga irin bad'alancin da muke aikatawa a ciki, nidai banajin komai idan wani ya gani domin ni iyayena tuni sun sallama ma duniya ni, saboda haka ni duniya itace uwata kuma itace ubana, idan na yad'a wannan vidio banajin komai tunda biye nake da mutanen cikinta ina basu, nayi tunanin maidashi faifayin filet na sidi dan in siyar na samu kud'i , sannan kuma in watsashi a yanar giza gizo dan inyi suna, kai kuma kana da dama d'aya tak data rage maka, idan har ka bani naira miliyan d'aya nayi maka alk'awari zan goge shi sai in hak'ura basai nayi suna a duniya ba...... Idan kuma baka dasu in turawa "ya "yanka ko suna da kud'in fansar ka ! Sultana, Sultana ce yarinyar mai dogon zamani, idan kuma kace zakayi gigin sako hukuma a ciki na riga dana turama k'awata nace da taji an kamani firr zakaji su sun watsu a duniya kamar saukar tsuntsaye. Ka huta lafiya habibinah muah_ 💋 Goge zufa Alhaji yayi tare da cewa Allah ka tsinewa yarinyar nan albarka, shegiya tsinanniya ubanta da uwarta basuyi addu'ar kwanciyar aure ba yayin da zasu kwanta Allah ya basu cikin d'ebabbar albarkar yarinyar nan, a daidai wannan lokacin kiran Dikko ya sake shigowa. Jiki a sanyaye Alhaji ya kalli wayar tare da cewa mai gida kayi hak'uri wannan abun kunya ina za'a dashi na watsu cikin duniya ina zina, abun bak'in ciki da d'iyar da nayi d'iya da ita, garin ciye ciye na har naje na ciwo ma kaina bala'e, kila sai ta k'arar da arzik'ina, kuma tace idan na fad'awa hukuma taba k'awarta vidion zata yad'ashi wannan shine ciwo ya riga ajali zuwa... Kuka Alhaji yayi tayi tare mitar ya shiga 3 ya bani ya lalace, wannan labarin abun kunyar waye ma zai fad'a mawa bare kuma yasa ran zai samu wata sahihiyar shawara, kai ya bani ya bani ya bani........😰🙆🏻‍♂😭, a daren nan Alhaji baiyi bacci ba kuma baibi kiran Dikko ba, wayar Sultana kuma ya kirata yafi so adadin yawan dutsinan da ake jifar shedan dasu amma maganar dai d'aya ce cewa a kashe....... Da safe , tunda nayi sallar asuba na koma bacci, can cikin bacci naji ana dukan k'ofar d'akina, addu'ar tashi daga bacci d'auke a bakina bayan na gama nace waye ? Na tambaya cikin muryar bacci tare dakai idona saman agogon dake lik'e a saman bangon d'akina k'arfe 10:36am, cikin muryar murna Nana tace "yan sanda aka d'auko miki Sultana.... Murmushi nayi tare da jawo wayata na kunna sannan nace ma Nana da Allah kije kice waye ya d'aukomin "yan sanda ? Cikin farin ciki ta koma zaure sannan ta tambayi d'an sanda waye yake k'arata ? Fad'a mata yayi tayo cikin gida da har yanzu tanajin dad'in k'arata da akayi, a bakin k'ofar d'aki ta tsaya sannan tace wai abokin Babanki Bello, jinjina kaina nayi tare da cewa tou ina fitowa.... Data na bud'e na nemo lamba 2, hotunan dana d'auke shi jiya na tura mishi tare da yin voice note na antaya ma banza, ina gamawa na kashe wayata, saida nayi wanka naci gayuna na watsa turare na d'auku iyakar yanda hankali baya tunani duk wanda ya ganni saina burgeshi, fitowa nayi banma kowa magana ba na tunkari zaure, dan zuwa wurin hukuma a yanayin talauci yana jawo ma mutum raini.... A k'ofar gida na samu d'an sandan nan ya gama shak'e b'acin rai daga gani yana jira muje can yaci uwata, a yangance na fito cikin aji na kalleshi tare da cewa "yar labai barka da aiki...... 'Dan sakin fuska yayi tare da cewa yawwa, gaishe shi nayi tare da ce masa nice Sultana, kallona yayi sama da k'asa sannan yace tou hajiya muna gayyatarki zuwa ofishinmu ai anyi miki bayanin mai k'ararki ko ? murmushi nayi tare da cewa babu damuwa muje amma Allah yasa ba'a cikin motar "yan sanda zaka d'aukeni ba, murmushi yayi tare da cewa ai hajiya napep zamu shiga, ajiyar zuciya nayi cikin sigar jan hankali sannan nace tou ai har naji natsuwa. Napep muka hau muka nufi c p s , kuma nice na biya kud'in 1k ne na bayar kuma daya anso canji nace ya rik'e yasha ruwa, tunda muka fita a napep gaba d'aya wurin saida hankalin kowa ya dawo kaina, na farko dai ga wanka ga gayu ga k'amshi uwa uba kyau Allah yayi min kyawun da mutum baya gajiya da kallona, ga gashina na tik'ashi nayi mishi wani irin parking irin na wayayyin mata, baka isa ka rainani ba ko waye kai domin sitirar dana saka ita kad'ai ta isa ka gane ni ba sa'ar wasan yaro bace ba..... Ofishin d c o muka nufa, a ciki na samu Bello zaune tare dashi da wasu abokan Babana, sallama nayi sannan na gaishesu dukansu cikin kyakkyawan yanayi, bayan mun gaisa nima na samu wuri na kame kamar yanda naga kowa yayi..... Kallona d c o yayi bayan ya gama karanta wata takarda dake gabanshi sannan yace Maryam miya had'aki da Bello ne ? Murmushi nayi tare da gyara zamana nace ranka ya dad'e ai Baba Bello abokin kasuwanci ne, halak'a ta mutunci ne a tsakani na dashi bayan wannan babu komai.... D C O yace tou jiya ina kika had'u da Bello ne ? Ranka ya dad'e majalissar su naje gaishe su, bayan mun gaisa kuma ya tambayeni nayi aure nace masa A , a, yace yanzu ina nake zama ? Nace masa ina zama a tsohuwar anguwarmu daya sani, ya tambayeni ko ina kasuwanci ne ? Nace masa Eh yace me nake siyarwa ranka ya dade nace masa karuwanci nakeyi, tsakanin mai saye da mai siyarwa ai babu fushi anan muka daidai suka d'aukeni muka tafi wani gida, nuna yawan duka abokan Babana nayi sannan naci gaba da cewa ranka ya dad'e dukansu nan babu wanda baiyi ba kuma duk saida suka k'ara zagayawa "yar labai, kuma gasu nan ka tambayesu idan nayi musu k'arya. Kuma cikon kud'in ma har yanzu basu bani ba.. Kowansu zaro ido yayi tare da dafa k'irji cikin yanayin mamaki yace ke mune mukayi iskanci dake ? 'Daure fuskata nayi kamar gaske nace aini banajin kunya tunda dai banji tsoron Allah ba nayi zina wallahi banajin kunya gaban kowa in fad'a nayi, kunyi mana ko k'arya zan muku ne ? Lokacin da bakuyi ba nace kunyi ? Gaba d'aya wurin hayaniya ta tashi har bakajin bakin wani, d c o ya dakatar dasu tare da cewa suyi mishi shiru, bayan kowa yayi shiru ya kalleni sannan yace ke Sultana Bello yana tuhumarki kud'in shi da kika d'auka. Cikin natsuwa nace wasu iri kud'i kuma ranka ya dad'e ? Bayani d c o yaimin kamar yanda na sani, jinjina kai nayi tare da cewa idan sun gama k'arata nima zanyi k'ararsu saboda b'atamin suna da sukayi, ranka ya dad'e a gaban idon waye na d'auka kud'in ne ? Nifa bana sata amma ina neman maza gaskiya, duk abinda nakeyi bana jin kunyar asan inayi domin dai duk sana'a sunanta sana'a, idan ma na d'auka aka tambayeni idan nasan na sata kawai zan dawo musu da kayansu in basu hak'uri tunda karuwanci da nakeyi ai ban b'oye ba na fad'a tunda ba abun kunya bane.... Tambayar Bello D C O yayi ko yana da wata sheda ne ? Baida ita tunda an tambayi mai gadi yace shidai bai ganni cikin mota ba, duk iyakar binciken da akayi dan asamu wata sheda babu ita, dan haka aka rubuta takarda cewa an janye k'ara, bayan an gama rubutu aka bani na saka hannu da larabci nayi sigining ina, an mik'e za'a tafi nace ma d c o naga fa sunamin wani kallon hadarin kaji sufa fita ido na, d c o yace ai duk an rubuta, nace to ranka ya dad'e cikon kud'ina kuma sai yaushe zasu bani ? Hak'uri d c o ya bani tare da nunamin tunda anyi masa sata inyi hak'uri inma barshi da ramuwar biyan kud'in mutane, babu kunya ba komai nace kenan ni yanzu ranka ya dad'e sunci banza ? Duk wanda ke cikin office in saida ya kalloni, nace ranka ya dad'e kafa duba lamarin nan gaskiya ni ba'amin adalci ba, shiru wurin yayi wutar kowa ta d'auke, murmushi nayi tunda basu da amsa nace nawa ake yankar sammaci ? Sammaci ma ake cewa abin ko miye ? A kotu ake yankar sammaci d c o ya bani amsa tare da fad'amin abinda ake kiran nasu da turanci, oho dai da yake kan baya ganewa kasa maimaitawa nayi saidai kawai nace nawa ne ? Kud'in aka fad'amin na bud'e jakata na bada sannan nacewa d c o ga wanda nake k'ara nan Bello ina tuhumarshi akan b'atar mahaifina daya tafi babu wanda yasan ina yaje.......... 21/08/2019 *JAMILA MUSA...* ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 15 *_Had'inkai group ina tare daku aminan albarka, Allah yabar so da kauna ubangiji ya k'ara yadda da aminci, HALIMATU SADIYYA {{ Leema }} HABIBA IDRIS {{ Hubbie }} HAUWA'U USMAN {{ Smasher }} MAIMUNA O . G {{ Aunty Munari.... }} muna tare_* *_Mrs Abdul-aziz ina godiya sosai da dogon sharhi kuma ngode sosai page 14 na baki shi kyauta...._* Lahaula walakuwata illah billah, kiji tsoron Allah ke uwar masu gida a ina na b'atar da mahaifinki ? Sharri zaki min ? Kiji tsoron Allah in babu nan akwai ranar hisabi duk wanda yaci zalin wani daidai da kwayar zarra ubangiji bazai barshi ba, ki daina ganin kin samu dama ta tak'in lokaci yasa ki manta da rayuwar gaba, karki biyewa zuciya ki kafa abinda zaisa kiyi nadama wata rana..... Gaba d'aya jikina yayi sanyi tsoron Allah ya kamani nasan k'azafi da sharri ba abu ne mai kyau ba, kuma addini na bai koyar dani haka ba, amma d'an kamewa na sakeyi sannan nace ni rayuwar dad'i baza ta tab'a zama takaitacciya a wurina ba, jin dad'i na d'aura insha Allah daga nan har zuwa ranar da numfashi na zai k'are, ina Babana yake wai ina ka kaishi ne............? Cikin nadama Bello yace na rantse da ubangiji daya bani aron lumfashi ya bani aron lafiya nake ganinki nake kuma saurarenki ya bani hankali da tunani idan nasan inda mahaifinki yake Allah ya tsinemin albarka. Wallahi Uwar masu gida bansan inda ya tafi ba na rantse miki da girman Allah. Tausayi ya bani yana rantsuwar yana wani kwantar dakai kamar an ritse macen da tayi cikin shege ta haihu kuma ta kashe d'an.... Kallon D C O nayi tare da cewa "yar labai shikenan tunda yayi rantsuwa baiyi ba kawai na janye, zan iya tafiya ? Na tambayi D C O, cewa yayi na zauna zamuyi magana, zama nayi su kuma su Bello aka sallamesu suka tafi ni kuma naci kud'in banza Ehe.... Ta wutsiyar idona na kalli d c o bayan fitarsu Bello domin ina son na gano tashi manufar a kaina, murmushi nayi bayan na gama fahimtar shi, a bayyane nace lamba 3 tazo kenan, ajiyar zuciya ya sauke tare da tattaro duka hankalin shi wurina yace ranki ya dad'e ya hak'uri da jama' a ? Kallonshi nayi ba tare da nayi magana ba domin wallahi tsarin bakinshi kwata kwata bai burgeni ba. Amma ba komai zan hak'ura nayi maleji dashi haka nan saboda idan na taro watan aug zai gina min gada nabi na wuce ba tare dana sha k'ashin ruwa ba.... Wayan cewa nayi tare da gyara zama na nace Allah dai yasa aiki zaka d'aukeni mai girma d c o, murmushi yayi tare da komawa ya kwanta saman kujerarshi irin masu juyawa d'in nan, sannan yace wai gida zan saukeki idan ba matsala, d'an yamutsa baki nayi tare da cewa na gode amma ni ba gida zanje ba... Ina zakije haka da rana ? 'Daure fuska nayi dan ya fara cika min ciki nace wurin aiki zanje, wane irin aiki ? Tsoki nayi tare da cewa kai komai sai anyi maka b'aro b'aro kake ganewa ko ? Tou abokin lalata zanje nema..... Murmushi yayi tare da cewa ke bakya gajiya ? Cikin wuta wuta nace ka tab'a ganin inda mutum yake rayuwa babu abinci ? Yace a , a, nace tou ni da kud'i da karuwanci sune abokan rayuwata, domin sai nayi nake samu sannan naci nasha na kuma d'aura har in fito na burge abokan harka , idan kuma kaima d'an hannu ne karka wani cuci kanka kawai kayi magana idan kajira sai an maka tayaki tou fa lallai zaka kwana da yunwa, amma kayi hak'uri da tambayar da zan maka tsakanin ka da Allah nawa ne albashin ka...... ? Kallona yayi tare da cewa hajiya maryam kenan , miya shafi albashi da harkar bariki ne ? Bai shafa ba amma ni ina duba nasabar namiji da cancantar shi kafin wata sahihiyar mu'amula ta shiga tsakani na dashi, dan duk wanda ya jawo maganar aure a rayuwarshi tabbas ya tara abun hidima, bata yuwuwa na biye maka ka k'ok'ar dani ba tare da ka sake bani kud'in da zan sabon fenti ba, dan kai kanka da ban d'aukar maka ido ba duk yanda nake barikin baza ka taya ba, Kallon agogon dake d'aure a tsintsinyar hannu na nayi tare da cewa zama wuri d'aya tsautsayi inji kifi, malam d c o zan wuce ka rubutamin number ka a jikin takarda idan ayyuka sukamin sauk'i akwai dawowa...... Babu musu kuma ba tunanin komai ya d'auki biro da takarda ya gwagwad'amin number wayarshi, ansa nayi tare da mik'ewa tsaye sannan nace sai ka jini, baki bari mu tafi in ajiye ki ? Ya tambayeni, juyawa nayi na fara tafiya tare da cewa ban hawa mota sai napep a daidai lokacin dana fice daga ofishin.... Ina fitowa wuri na samu na tsaya, wayata na fiddo nayi saving in no d c o da lamba 3 , sannan na kira wayar Alhaji, babu b'ata lokaci ya d'auka tare da cewa ranki ya dad'e tun jiya inata kiran ki wayarki a kashe ko yau da safe ma na kira a rufe.... Ban bashi amsa ba nace kawomin kud'in yanzu nan ina nan c p s ina jiranka kuma karka b'atamin lokaci, ina fad'a na kashe wayata...... Lambar Bello na kira amma bai d'auka ba, daga kira d'aya nima ban sake kira ba, domin dai nasan idan yaga abunda na tura mishi shi da kanshi zai nemeni, k'ok'arin maida wayata nake cikin jikka naji ana cewa shegiya k'awata kece kika koma wata hajiya haka ? Da sauri na d'ago kaina domin jin muryar Amisty da nayi... Cikin farin ciki muka rungume juna, bayan gaisuwa sai kuma muka shiga firar duniya, yayin da nake tambayarta wane ci baya ta samu na bariki naga har yanzu bata fara hawa mota ba, ajiyar zuciya Amisty ta sauke tare da cewa kinsan mazan babu kud'i hannunsu kullum tsuwwa da kukan babu...... 'Daure fuska nayi tare da cewa waye ya fad'a miki ana hawan jirgin sama bashi ne ? Ai filin jirgi ma baka shigarshi dole sai kana da tikitin tafiya, haka nan kike basu suna hayewa basu baki kud'in mai, tou ina uwar d'akin taki ne ko bata nan bata fad'a miki illar maza ba ? Haba Amisty idan baki ridowa da yawa wallahi bariki kasheki zatayi, niko kin ganni nan ni zanyi gwanjo bariki kafin ta wurgar dani gefen titi, kinsan bariki bata da tabbas d'auka da ajiyewa gareta, ni zan kashe bariki bazan yadda ta kashe ni ba, zanyi amfani da talata ta kafin laraba ta, ta riskeni, wannan uwar d'aki taki k'atuwar jahila ce batayi karatun komai ba haka nan ta tara yawan dalibai, har yanzu kuna da dama ki nemi canji makaranta ki dawo makaranta ta zan baki ilimi akan namiji, kud'i kike so ko suna ......? Horn Alhaji yayi da mota wanda tun d'azu yakeyi amma magana ta hana na saurareshi, juyawa nayi tare da nuna mishi da hannu ina zuwa, ni kuma naci gaba da magana da Amisty, wata matace ta fito daga ciki tayo wurinmu kuma ga dukkan alama tare suke da Amisty, gaisawa muka yi yayin da Amisty ta fara tambayarta ya aka k'are, basu bani labari ba suna ta maganar ne cikin munafinci, ni na fahimta suna magana ne kamar tayi ciki.. Datsar maganar nayi da cewa keko ya akayi kikayi cikin shege ? Gaki a fuska kamar wayayya taya akayi haka ta faru ? Ita kuma a tunaninta Amisty ta fad'amin dan haka tace kin gane ni bawai cikin bane matsala a, a mijina yau watanshi bakwai baya nan kuma ga ciki wata hud'u, kuma nayi a zubar da cikin shi wanda yayi cikin yace wallahi bazai yadda ba saboda bai tab'a haihu ba, idan wannan abu ya fito ai kinsan akwai matsala..... Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un na fad'a tare da cewa ke matar aure kike zina ? Hasbinallahu wa ni'imal wakim, amma kinyi k'atuwar asara, kallon Amisty nayi tare da cewa zance zaune ba na tsaye bane idan kuna neman taimako ku sameni gida, ina nan tsohuwar anguwarmu idan kika shigo ki tambayi gidan da nake haya za'a kawoki, ina fad'in haka nayi wurin motar alhaji ina zuwa na kama na bud'e na shige nace muje... Har muka isa gida banyi ma Alhaji magana ba domin ni yau naga macen da tafini kafirci kina k'ark'ashin bautar aure amma kina aikata sab'o, wannan wai wane irin zamani ne muke ciki lallai ya kamata nasan ita kuma wane rud'un duniyar ne yaja mata neman mazan waje ga nata mijin da yake hak'k'inta amma ta tsallake shi ta tafi wurin na wasu , gaba d'aya jikina yayi sanyi kuma na dawo daga rakiyar duniya.... Ansar jakar da Alhaji ya zubomin kud'i nayi tare da direwa daga motar, zaiyi min magana nace mishi muyi waya kawai nayi gaba abu na, lokacin dana shiga gida bana ko ganin gabana saboda bak'in ciki da kishin aure, d'akina na bud'e na shiga, saida na adana kud'ina sannan naje nayo alwalla nayi sallah azahar, yinin ranar haka na yini sukuku kamar wata mara lafiya, koda nayi sallah isha'i kwanciyata nayi , duk yau banda ruwan shayi babu abinda ke cikin cikina, haka na kwanta da tunani iri iri, ko bacci nayi na farka abun yakan fad'omin a rai har gari ya waye da tunanin matar nan a zuciyata.. Da safe bayan nayi kalaci na gyara d'akina naje nayi wanka na shirya cikin doguwar riga ta atamfa da tasha d'inki buba, hula mai raga { net } na saka kaina na fice tsakar gidan.... Kujera na sa a k'ofar d'akina na zauna tunda fitowa wajen ya zamar min dole, kallon inda Karima take nayi sannan na maida kallo na wurin Saude dake zaune saman turmi, babu ko breziya jikinta kuma babu kaya sai siket ondie da taja saman kirjinta, amma komai na halittar ta babu abinda ya b'oye duk a bayyane yake..... 'Dauke idona nayi gefe na kallo inda Nana take kwance A ` i tana durk'ushe ta duk'a samanta sosai suna k'ushin k'ushin, jinjina kaina nayi sannan na sake kai idona wurin Saude nace ke Saude wai da Allah in tambaye ki ? Murmushi tayi tare da cewa tambayarni kanki tsaye, b'ata rai nayi sosai sannan nace nan gidan ubanki ne wai da zaki zo ki rik'a zama mana tsirara dan baki da kunya ? Gaba d'ayansu dariya sukayi ,sannan Saude tace tou ke mai tambayar gidan ubanki ne ? Ni nan ba gidan ubana bane amma ya zama na ubana tunda na biya kud'in haya, d'aki d'aya na kama amma ina da hurumin da zan sauke ubana a ciki, ke ko fa ? Nana ta anshi maganar da cewa yanda kike tak'amar kin kama haya muma kamawa mukayi kuma muma muna da hurumin da zamu kawo mutanen da muke so su zauna tare damu, kedai kawai kice kina so ayi dake. 'Dan gajeran murmushi nayi tare da cewa duk wanda yaci naman arne tabbas zai iya cin mushen alade , banda abinki miya had'a makaho da ganin wawan zama ? Ni bana iya cin naman jaki amma idan na samu doki zanci duk da an yanka shi nasan wata rana zanyi hazaka, ko banyi gudu ba tabbas nasan zanyi tafiya, magana ce na fad'a miki a jimlace idan kina da ilimi sai ki warwareta banzanye da ku masu wahalallen bariki..... Gaba d'aya wutar kowa d'aukewa tayi sukayi shiru babu wanda tace komai, murmushi nayi tare da cewa ba'a bariki dole saida ado kuje ku ibi ruwa kuyi wanka kusa toka ku wanke baki ko ya rage k'annin koko, daga haka ban sake ma kowa magana ba kuma suma babu wanda ya sake cewa komai, Bayan Alhaji ya bani kud'i ya dad'e k'ofar gidanmu ya kasa tafiya, hankalinshi a tashe saboda yaso yayi magana dani na goge vidion nan kuma yaji ina na dosa ? Amma samsam ban saurare shi ba, kuma yasan lallai saina sake tambayarshi wasu kud'in tunda akwai vidio a hannuna ban goge ba, Rasa yanda zaiyi yayi zuciyarsa ta yanke mishi kawai ya fad'a wa Dikko komai yasan babu mai iya magani na saishi amma fa a nashi haukar , d'aga waya yayi ya kira Dikko kuma har zuwa wannan lokacin yana k'ofar gidanmu bai tafi ba. Bayan Dikko ya d'auki waya Alhaji ya gaishe shi cikin girmamawa kamar yanda ya saba, Dikko ya amsa shima cikin mutuntawa, dan a haife Alhaji ya haifi Dikko amma igiyar naira tasa yana k'ark'ashin Dikko kuma k'asan k'asa ma, dan ubangidan Alhaji na ainahi shima yaron Dikko ne na biyu, tou abinda yasa Alhaji yake kiran Dikko kai tsaye saboda yanajin dad'in yadda yake kularmishi da dokunan shi, shi yasa shi Dikko da kanshi ma ya anshi number Alhaji ko wata matsala ta taso ga dokunan shi, dan dama ubangidan nashi na farko kafin yasan Dikko wurin kula da dokuna ajiye shi Alhajin.... Alhaji yace mai gida kayi hak'uri don girman Allah wallahi jiya daka kirani ina cikin yanayin da bazan iya magana ba, cikin jimami Dikko yace meya faru haka ? Wato ranka ya dad'e ina cikin tashin hankalin dana zab'i mutuwa ma da rayuwa, salati Dikko yayi tare dayin murmushi domin shi yaji mugunta, sannan yace Alhaji duk dad'in duniyar wato tai maka d'aci ko ? Alhaji yace Eh wallahi ranka ya dad'e, Dikko yace tou Allah ya kyauta... Da sauri Alhaji ya fara bayani wa Dikko dan yasan daga Allah ya kyauta kawai zai kashe wayarshi ne yasan baya doguwar waya, ranka ya dad'e wato wallahi wata yarinya ce muka d'an keb'e da ita, tou wallahi bansan yarinyar nan ta shirya sharri ba, ashe duk abinda mukayi ranka ya dad'e tana d'auka cikin waya ban sani ba, tou ta rik'e vidion sai wahalar dani takeyi tana ansar kud'ad'ena, yauma na bata kud'i kuma a police station nakai mata kud'in inaji wani ne ya d'aure mata gindi take iskanci a garin nan.... Murmushin mugunta Dikko yayi tare dayin kamar bai gane ba, yace wane irin vidio ne ? Gyara zama Alhaji yayi tare da goge zufa yace wato ranka ya dad'e harka daice irin wadda muka saba, Dikko yace wadda ka saba dai , wato ka samo daidai dakai ko ? Tou turomin vidion in gani ya fad'i maganar cikin sigar zaulaya, Alhaji yace ranka ya dad'e vidion fa irin na kafirawan nan ne masu d'aukar tsiraicinsu suna yayad'awa a duniya....... Dikko yace tou banda abunka kace taje ta yad'a ba hada ita a vidion ba ? Alhaji yace ranka ya dad'e ina za'ayi wannan abun kunya tsiraicina a yanar giza gizo cewa tayi fa har "ya "yana zata tura su gani, Dikko ya gaggab'e da dariyar mugunta tare da kashe wayarshi, irin wannan abun Dikko kadai yake ma dariya a duniya, duk abin burgewa ko na nishad'i Dikko baya mishi dariya kuma baya murmushi idan kaga murmushin shi ko dariya yaji ko yaga k'eta, amma kai kana iya ganin abinda zai baka tausayi kayi kuka wallahi Dikko sai yayi mishi dariya saboda tsabagen shi cikakken mugune.... Cikin sanyin jiki Alhaji yaja motarshi ya tafi, Dikko kuwa saida yasha dariyarshi ya gaji sannan ya sake kiran Alhaji, bayan ya d'auka yace tou waikai kawai sai tayi maka vidio ? Alhaji yace Eh ranka ya dad'e Dikko ya sake shek'ewa da dariya sannan yace kai amma wallahi yarinyar nan tantiriya ce ta fad'a a duniya, Dikko yace tou yanzu me kake so nayi maka ne ? Alhaji yace ranka ya dad'e so nake kayi min maganinta, dariya Dikko yayi sannan yace nima so kake ta d'aukeni ? Cikin biyayya Alhaji yace haba ranka ya dad'e kada Allah ya had'aka shegiyar yarinyar nan..... Dikko yace aini ko ta had'u dani bata da yadda zatayi dani, nidai bana neman mata kuma bana sabgarsu bana shiga huruminsu gudun raini, kayi hak'uri insha Allah zanzo katsina jibi idan Allah ya kaimu zata goge vidion dan wahala, ranka ya dad'e ai tace ta turawa k'awarta ne, Dikko yace k'arya take kadai jira zuwana ..... Godiya Alhaji yayi sannan sukayi sallama da Dikko, Murmushi nayi a daidai wannan lokacin sannan nace duk mai niyar yin magani na nice zanyi maganin d'an banza, zomon bana shike maganin karen bana, maganin d'an iska kuma karen maguzawa, dani dakai dashi mu zuba duk wanda ya fasa yaci k'aniyarshi....... Sallamar Hafsa ce da wasu zugar tantiran mata, a ciki kuwa harda Amisty, kila sunzo ne suci min uwa tunda nace uwar d'akinsu k'atuwar jahila ce, oho koma dai miye su shigo ina jiran isowarsu wurina inji su kuma da wace suka zo................??? 22/08/2019 Taku a kullum mai san farin cikinku wato . *MEELAT MUSA* ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 16 *_Bandai ji komai ba , 71 , 29 babu damuwa zamu rama muma..._* _____```^^=°°--- Basarwa nayi tare da d'auke fuska ta daga dubansu, mutum dai bai isa yazo har gidana ya dakeni ba, kallon banza ko maganar banza mutum yamin wadda batamin ba wallahi ina da Lamba3 d c o zaici k'aniyar mata.... A daidai lokacin da suka iso gabana maganar zuci ya k'are, Amisty ce tace wurinki fa muka zo kina yi kamar baki ganmu ba, saida na gama kallesu tsaf sannan nace sannunku da zuwa tare da mik'ewa zan shiga d'aki dan d'auko musu tabarma... Gaba d'ayansu rufa min baya sukayi suma suna k'ok'arin shigamin d'aki, ja nayi na tsaya tare da tambayarsu ina zasu je ? Amisty tace ciki zamu shiga ? Murmushi nayi tare da cewa kuyi hak'uri ku jirani ni bana kai mata cikin d'akina... Hafsa zatayi magana Amisty ta dakatar da ita, kallonsu nayi tare da cewa barta ta fad'i cikinta, Amisty tace barta kawai d'auko mana kedai, munafikin murmushi nayi tare da juyawa na shige cikin ɗaki, domin ita Amisty tasan wace ce ni, tabarma na d'auko nazo na shimfiɗawa banza nace su zauna... Dukansu zama sukayi lokaci ɗaya, su A ` i da Saude Nana da Karima duk suka taso suka dawo ƙofar ɗakina, nima zama nayi tare da cewa meke tafe daku ne ? Na ƙarasa maganar tare da kauda kaina gefe ɗaya.... Amisty tace Sultana ke kikace mu sameki gida ! Kallonta nayi tare da cewa sai akayi ya ya ? Amisty tace ai shine muka zo ! Kallon tantiran mata nayi sannan na maida hankalina wurin Amisty nace da Allah daga yau idan zaki zo wurina kidai min kwashe kwashe , da sauri Amisty ta kalleni sannan tace haba Sultana mi yasa haka kuma ? Kai tsaye nace kinsan bana san munafirci kuma ban tare da munafikai, waccan bak'ar yarinyar da kika gani na nuna Hafsa budurwar Dikko sannan naci gaba da cewa gaskiya aminci take da mak'iya na saidai ta zab'a ni take so ko su A ` i , murmushi Hafsa tayi tare da kallona sosai ni kuma na d'an gyara zama yanda zan d'aukar mata hankali sosai, saboda ina so na rabata tarayya dasu A ` i idan ina tare da Hafsa suma suna tare da ita riƙa zugamin ita zasuyi har su hanani na cimma buruni tunda na lura ita Hafsa doluwa ce kuɗinne kawai ba wayau sai tsabar neman matan bala'e. Kwazzaba tasa har bata iya tantance kifi bata gane kwad'o, Cikin ruɗewa Hafsa ta fara magana irin ta "ya "yan masu kuɗi, kin gane Sultana nifa ba abokaina bane kawai gaisawa mukeyi sai kuma wata huɗɗa tamu data haɗamu amma ba komai tsakaninmu gaskiya, Ɗaure rai nayi tare da cewa nifa ba abinda ya haɗaku nake so na sani ba cewa nayi kawai ki faɗa ni zakiyi abokiya dani kibar su A ` i ko kuwa su A ` i kika zaɓa, Hafsa tace haba aike tawa ce kuma ina tare dake, murmushi nayi tare da cewa magana ta ƙare mata tacewa mijinta shege... A ` i zatayi magana nace dakata malama ta bakin gulbi, ki taka sannu da lafiya kafin insa a ɓatarmin dake cikin garin nan, nuna yawan su Amisty nayi tare da cewa nan da kika gansu duk dalibai na ne, zan fara basu karatu daga jibi idan Allah ya kaimu, na kafa ƙungiya ta mai take *kwarata* duk wacce kika gani anan mabuƙaciya ce, zan haɗa ne zanba mace namiji idan an sallami mace zata fiddani, zan haɗa mata da mata amma a tafiyata ban tafiya da taron banza, sabbin ɗalibai ku na ɗaukeku kyauta basai kunyi register ba, amma daga ba yanzu ba duk wacce zata shigo cikinmu saita ajiye dubu talatin kuɗin register haƙƙina neman maza da mata masu abun hannunsu.... Miƙa hannuna nayi tare da cewa duk wanda yake tare dani ya ɗora hannunsa a saman nawa, kowa ɗora hannunshi yayi harsu Nana matan aure ba'a barsu a baya ba, ku ɗauki alƙawari babu cin amana , gaba ɗaya suka amsa munyi alƙawari bazamu ci amana ba, nace kuyi alƙawari zaku zama ɗalibai masu biyayya, munyi alƙawari zamu zama ɗalibai masu biyya nace idan kun samu ina nan ko bana nan zaku ajiyemin nawa kason, shima suka maimaita, sannan nayi addu'a tare da neman Allah yasa albarka a cikin wannan ƙungiya tamu mai albarka wanda nayi ma laƙabi da *KWARATA* saboda dukanmu lalatacci ne , Bayan an gama nace tou kowa ya tashi ya tafi nima zan fita inda fuskar jama'a take na samu gida na siya idan kuɗina yakai, idan basu kai ba kuma zamu kama shago, wannan shago zai zama nan ne kowa zataci gayu da safe taje ta zauna, yayin da zamu kafa ƙaton allonmu ya kalli al'umma, za'a rubuta a gaban shagon ko gidan tambarin *KWARATA* idan ma baka iya ba kazo za'a koya maka. Zamu rubuta a jikin takarda mukai kuma a buga mana su da yawa, ni zanbi manya ofisoshi da kasuwa da kuma kamfaninika da inda "yan siyasa ke zama saina zabo mana manyan alhazawa sai mu raba musu, duk wanda ya gani ya karanta dama ga number wayata nan a jiki, ku kuma kuna shago kunsha wanka kunayi kuna ƙara powder da jagira ina binku ina muku wanka da turare, da mutum yace zaizo zance ya iso akawai kaya a ƙasa, yana shigowa ya ganku wayyo shikenan labari zai canja salo, ni kuma ina da wata dabara ɗaya amma bazan faɗa muku ba saboda karuwa bata da amana, Nana tace tou mu da muke da aure fa ? Kallon ta nayi ƙasa da sama sannan nace duk iskanci da kukeyi keda A ` i sai yanzu kika tuna Allah ? Tsoki nayi tare da cewa tunda na lura kema kinasan duniyar sai in ɗaukeki aiki ki riƙa sharewa kina gogewa, ke kuma Karima idan mijinki ya barki zan zuba miki kayan mata da maza na gyaran harka duk wata zan baki dubu biyar ko anyi ciniki ko ba'ayi ba, amma idan mijinki ya barki fa. Tun kafin in rufe bakina Karima tace koma bai barni sai naje wallahi, dubu biyar fa ? Ina nan kullum zaune gida naira hamsin ma wahala take min , kuma Sultana ki rubuta a jikin takarda duk wanda zaizo ya taho da kaza kinga idan anci an rage ai muma zamu maida miyanmu..... Kallon Karima nayi sannan nace kazar Lbura'uba, an faɗa miki *kwartancin* wahala zamuyi ? Kudai kuyi ta addu'a a samu bakin titi, addu'a sukayi tayi Allah ya taimaka ya bada sa'a, daga ƙarshe dai kowa ya kama gabanshi, nima na kulle ɗakina na fantsa ma cikin gari... Ina bakin titi tsaye naji wayata tana ta kururuwa dan haka dole na dakata, fiddota nayi na duba dan ganin mai kirana, Lamba 2 wato Bello kenan, ɗauka nayi tare dayin sallama, bayan ya ansa na gaishe shi, bai ansa gaisuwar ba yace ke Uwar masu gida hotuna na gani ? Amma ai ka gane ko waye a jikin hotunan ko ? Eh nine , tou kuɗi zaka bani naira budu ɗari biyar nan da gobe idan Allah ya kaimu idan kuma kace babu sai ina watsa su duniya kowa ya kalla kyauta.... Ɗanka da matarka da abokanka duk suna kwance a saman gado zasusha kallo abunsu... Sirikinka da surukarka zasusha kallon siriki tsirara... Tou nabarka lafiya, ina faɗin haka na katse kiranshi, ina duba yanayin samun mutum kafin na yanka mishi haraji, Bello baida ko sisi kuma baida wata sana'a data wuce caca, kuma caca ba kullum akeyinta ba, gashi kuma na sace kuɗaɗanshi kaff da na gani a mota ba damuwa na bane nidai kuɗi kawai, ina gama waya da Bello na kira lamba3 wato d c o, mai girma ɗan sanda yarinyar jiya ce, Maryam Sultana Aliyu Binna, ya garin ? Haka nayi masa bayani bayan ya ɗauki wayata.... Hajiya ya kike ? Lafiya qalau kana ta ina haka ne ? Yace naje ganin gida ne baby, cikin salon cuta na kwantar da murya ƙasa ƙasa nace kuma "yar laɓai maimakon ka kirani inyi rakiya ? Murmushi yayi sannan yace wallahi nima tafiyar bazata ce wife ina ce bata lafiya, tou lallai wannan kuwa da sa'a take wace ce ita, dan bansan abinda wife in take nufi ba, dana dangantata da mace saboda naji yayi magana da sunan jinsin mace ne, yace wife itace ba lafiya, D c o yace matata nace, danshi yanda yake kallon wayewa ta ya ɗauka wata shegiyar baturiya ce, danaji yace mata nace ai shine nace wannan tana da sa'a, da kaji kuma nace wace ce ita ina tambayarka amarya ne ko uwar gida ? D c o yace ai mata ta ɗaya ce, nace tou yayi kyau yaushe zaka dawo ne ? Zan dawo amma sai ta samu sauƙi, to Allah ya sawaƙe ya bata lafiya, d c o ya amsa da amin mukayi sallama..... Lallai duk yanda akayi wannan matar tashi tasan damarta ne, idan ta riƙe d c o sosai taya zamu samu wani abu a wurinshi ne to ? Wato ita munafika nufinta ita ɗaya zataci ? Taci gidansu bari dai d c o in ya dawo bata ƙara ganinshi dan ubanta ba rashin lafiya ba ko mutuwa tayi sai anyi jana'izarta baije ba.... Napep na hau na nufi gidan Alhaji marenin wayau na, tsoho ya tsufa amma zuciyar bata mutu ba, buɗe na samu gidan dan haka na banka kaina tsaye na shiga, babu dawakuna ko guda ɗaya duk an fitar dasu an share gidan ƙwal gwanin burgewa, sai cire yana akeyi ana wani kakkaɓe kakkaɓe get in gida sai wanke shi akeyi ana goge duk inda yayi ƙura.... Cikin masu sharar na tamabaya lafiya ko Alhaji ya tashi ne ? Yace lafiya qalau bai tashi ba ubangidan shi ne zai dawo gobe, tsoki nayi tare da cewa shine ake ta wani share share ? Yace Eh , Dikko ko ? Na tambayi yaron yace Eh ai ance ma ya iso yana Abuja ko zasuyi me ne ne ? Amma dai naji ance jirgin safe zaibi yaje kano akwai abinda zasuyi sannan zai shigo katsina.... Jinjina kai nayi sannan nace tou shi ina Alhajin ne ? Ai sun tafi kano taroshi, daga nan har kano suka tafi su taho dashi saboda tsabar basu da aikinyi ? Yaron yace ai ba rashin aikinyi bane ba hajiya duk abinda kika ga sunayi dan sun san zasu samu, Alhaji fa baya saida fari baya saida baƙi kiwon dokuna yake amma kiji irin dukiyar dake gareshi, sun san suna samu da D ---K ɗin ne shi yasa suke laƙafe dashi, da yana nan da baya nan kuɗi suke samu kamar tashin hankali... Tou zan tafi kawai mayi waya dashi, jakata na buɗe nayi ma yaron alheri godiya yayi tayi tare da cewa Allah ya kareki ya ƙara arziƙi hajiya ubangiji yasa kifi haka Allah ya ƙara lilka darajarki ngode sosai. Ban saurareshi ba nayi waje abu na, Gida na koma saida nayi sallah isha'e sannan na fara nazari akan Alhaji abinda zance masa kawai ya bani mota da gida sai in fita daga harkarshi, dan ni duk inda zanji ƙamshi ko labarin sunan D ---K na tsani wurin tsakani da Allah bana san Dikko na tsani rayuwarshi wallahi, amma idan har Allah yayi min cikakken arziƙi saina wulaƙanta ma Dikko rayuwa, Wani irin baƙin ciki naji yana tasomin hawaye ya cikamin ido na abinda ya faru tsaƙanina da Dikko ya dawomin sabo fil a zuciyata, zuciya ta tace min ƙaryane baza a fita daga harkar Dikko ba sai na halakashi, kamar mai aljannu lokaci guda na burkuce nayi nayi na saita kaina amma na kasa wuƙa na ɗauko tare da kwarara wani irin ihu nace wallahi saina kashe ka........ Na ƙarasa maganar cikin kururuwa. Duk wanda ke gidan nan babu wanda baiji ihuna ba, da gudu Nana da Karima sukayo ɗakina amma banda su A ` i saboda yau da wuri suka tafi gida. Lokacin da su Nana suka shigo duk na yanyanki wasu wurare na jikina da wuƙa, abin ya tada musu hankali dakel suka riƙeni suna tambayata waye Sultana kallon Nana nayi cikin kuka nace wallahi saina kashe shi gobe zai shigo katsina bana ko ƙaunar jin irin sunanshi a rayuwata.... Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, shine abinda Dikko ya faɗa a daidai wannan lokacin tare da janye ruwan dake gabanshi, hankalin kowa yayo kanshi tare da tambayar lafiya ranka ya daɗe ? Dafa ƙirjishi yayi tare da cewa gabana ke faɗuwa babu gaira babu dalili. Duk kusa dashi suka matsa suna mishi sannu, kallon babban yaronshi yayi sannan yace maza kiramin gida, ɗaukar waya yayi ya kiro dadyn dikko, babu ɓata lokaci dady ya ɗauka D --- K babu ko gaisuwa yace Dady lafiyanka qalau kuwa ? Murmushi Dady yayi tare da cewa mi kuwa zai sameni ? Bayan ina nan zaune cikin iyalina muna farin ciki saboda zuwanka ! Dikko yace Dady karka ɓoyemin dan Allah miye ? Dady yace tsaya ma kaji, saida ya haɗa Dikko da kowa yayi magana sannan yace kaji ko ? Ajiyar zuciya Dikko yayi kamar wanda yasha kuka ya ƙoshi sannan yace kawai haka nan naji gabana yana faɗuwa, Dady yace saboda zaka ga ganni ne, kayi ta addu'a Allaah ya tsare kuma kayi bacci da wuri, jinjina kai Dikko yayi tare dayi ma Dady sallama suka ajiye waya.... Dakel su Nana suka lallasheni nayi shiru, Karima tace inyi ta addu'a don Allah sharrin shaiɗan ne, nace tou amma har yanzu ban daina baƙin ciki ba, saida suka tabbar hankalina ya kwanta sannan suka tafi bayan sunsha fama na faɗa musu ko waye naƙi faɗa musu... Suna fita na rufe ɗakina nayi addu'a na kwanta bacci, Da safe kuwa misalin 12:45pm na fara gwagwaɗawa Alhaji kira, bawan Allah banda zufa babu abinda yake haɗawa, idanuwanshi sunyi jajir saboda tsabar tashin hankali duk wanda ke wurin saida Alhaji ya bashi tausayi duk da babu wanda yasan abinda yake damunshi, amma banda Dikko dakeyin kyakkyawan murmushin dake fito masa da tsananin kyawunshi, da yasan yanda yakeyin kyau idan yanayin murmushi daya dawwama yanayin fara'a, duk da ko baiyi murmushi ba yana da kyau sosai gaskiya, taunar rainin hankali yake ma cingom in bakinshi sannan yace wai har yanzu ta hanaka ka huta ne ? Kamar Alhaji yana jira yace Eh ranka yadaɗe, Dikko yace bani ita, Alhaji yace ai kiran ya tsinki, ɗaure fuska Dikko yayi sannan yace kirawo min ita............... 23/08/2019 *JAMILA MUSA* 🤙🏻 Ina mana barka da juma'a, ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 17 _Don Allah kuyi haƙuri mu dukanmu mubi labarin nan a hankali, wannan labari na faɗa muku yanda yake, an rage wasu abubuwa ne wasu kuma an gyara su, labarin yana da yawa sosai ba'ayi komai ba yanzun muka fara wasan , kuyi haƙuri muje a hankali, ni jamila musa nake cewa asha karatu lafiya...._ Gajiya nayi da kira ba'a ɗauka ba dan haka na haƙura banyi yunƙurin sake kira ba, ina ƙoƙarin ajiye wayata kira ya shigo a cikin wayata mamaki ya kamani sosai ganin kiran Alhaji, taya zai kirani bayan ni na kirashi da kaina bai ɗauka ba ? Haka nan naji tsikar jikina ta tashi zuciyata namin wasi wasi lallai akwai wata ƙullallah da ake son ɗaura min, duk yanda akayi wani baƙon lamari zai faru tou amma bansan ko miye ba, kashedi zuciyata tamin tare da hanani ɗaukar wayar, sau biyu aka kira ban ɗauka ba dan haka suka haƙura basu sake kira ba... Kallon Alhaji Dikko yayi sannan yace yarinyar nan zata kai shekaru nawa ? Saida Alhaji ya kwantar da kai cikin biyayya sannan yace baza ta wuce sha shidda zuwa sha bakwai ba, D --- K yace tou wallahi wannan yarinya tasan abinda takeyi kila shekarunta ya wuce yanda kake tunaninta tana abunta da lissafi, amma baka taɓa kiranta a waya ba ko ... ? Alhaji yace Eh gaskiya chat kaɗai mukeyi da ita, sai ranar da ta turomin vidion nan shine na kirata, amma daga ranar ban sake kiranta ba saidai ta kirani, Dikko yace tou jikinta ya bata ba kaine kake kiranta ba shi yasa bata ɗauka waya ba, amma nasan zata kiraka zuwa anjima zatayi tunanin wayar ta koma hannunka, ajiye wayar yayi a gefenshi suka ci gaba da abinda sukeyi.. Ina ajiye wayar kiran Bello yana shigowa, ɗauka nayi bayan mun gaisa yace min Uwar masu gida nifa har yanzu ban samu kuɗin da kike magana ba, jinjina kaina nayi tare da murmushi nace kanajin wasa bazan iya tura hotunan ka ba a yanar giza gizo ko ? Tou wai babu zan baki ne ? Cikin faɗa yace tou banda su ko satowa zanyi in baki saboda inajin tsoronki to ki turawa uwar yanar giza gizo dan kutumar ubanki ko an faɗa miki tsoronki nakeji ko inajin tsoron a ganni tsirara, idan baki sani ba har gasar fitowa tsirara nayi daga ƙofar gida na har bakin masallacin juma'a naje ranar juma'a babu kaya a jikina na dawo, ni zaki ɗauka hoto kimin hauka ? Tou bake ba ubanki ma nafi ƙarfinshi ki riƙe kiyi ta kallo mtsw ya kashe wayatshi.... Murmushi nayi tare dabin wayar da kallo, har zan haƙura wata zuciyar tace wallahi ƙarya yakeyi bai wani fita tsirara ba idan kika fahimci maganar shi ta farko a sadudance yayi miki magana, karki sauƙaƙa mishi number wayar matarshi zaki fita ki samo ki tura mata zata bashi labari, idan kin tura mata ni na sani sai ya kiraki, idan ya kiraki sai kice kin turawa ɗanshi ma, shi kuma ɗan ba hoton za'a tura mishi ba voice note za'ayi mishi da wasu maganganu masu zafi zuciya zata tunzurashi yayi ma baban magana, tashi dai ki fita duk ki samo numbobinsu ki dawo sannan musan abunyi... Bello kuma shida abokinshi suka kashe sannan yace na faɗa mata, abokin yace tou yanzu zata shafa maka lafiya kaga kun rabu lafiya zata gaji da ajiyar hotunan ta gogesu, Bello yace ni tsoro na ɗaya tace ta turawa wata ƙawarta hotunan fa, karka damu sun gaji su goge dan ubansu, dariya sukayi tare da ƙara kashe wa cikin duniyanci.... Ina fitowa daga wanka nace ba'asan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, zakayi dana sanin hanani kuɗin nan, kila kuma rabona ne yake da yawa kuɗin zasu sake yawa. Har na gama shiri da abinda nake saƙawa nake warwarewa, Nana na kwaɗawa kira ta kwararo da gudunta tazo, kallonta nayi sannan nace Nana aiki yamin yawa zan fita neman wurin zama sannan kuma zanje wurin wani Alhaji dake tamin rainin hankali, ai kinsan majalissar babana ko ? Nana tace Eh na sani, nace ai kinma san Bello abokinshi ko ? Nana tace sosai ma, tou lambar wayar matarshi da babban ɗanshi zaki kawo number wayoyinsu zan baki dubu ɗaya... Yashe baki Nana tayi sannan tace godiya nake Sultana, wani sauran biredi da naman da naci jiya na rage na miƙa mata ansa tayi taita kwarara godiya harta fita, tana fita nima na tattara nawa ya nawa na fita nabar gidan... A ƙofar gidan Alhaji napep ya sauke ni, wasu irin zuƙa zuƙa motoci tun daga ƙofar gida har cikin get in gidan, kuma yauma get ɗin a buɗe yake daga inda nake tsaye ina hango komai na gidan ! Matashin jiya daya faɗa min cewa Alhaji yayi tafiya shine yazo wurina da sauri ya gaisheni cikin girmamawa ansawa nayi cikin sakin fuska sannan nace gidan naku lafiya naga taron motoci ? Lafiya qalau ubangidan nasu ne ya dawo ko gida ma baije ba ya fara da ganin dokuna, jiya da aka fidda dawakunan doki ɗaya ya kare a ƙafa shine ya fara da ganinshi kafin ya wuce. D --- K ne ya fito daga cikin palon yana magana daga ganin yanayin maganar shi faɗa yakeyi, saida ya fito tsakar gidan sannan ya riƙe ƙugunshi da duka hannuwan shi biyu yaci gaba da magana amma bana iya jiyo abinda suke cewa saboda tazarar dake tsakaninmu. Zubinsu da yawansu ya bani tsoro gasu ƙosasshi, inda Dikko yake tsaye na kalla, gaskiya Dikko ɗan gayu ne wankakken namiji yasha wanka ya ƙoshi tsaftatacce dashi ya cika ya fito cikakken namiji har wani gemun rainin hankali ya ajiye kamu ɗaya gaskiya duk da bana ƙaunar shi jarumin namiji ne duk inda mace take san namiji Dikko yakai tsakani da Allah zan faɗi gaskiya, domin Allah Dikko yana da kyau mai burgewa da ɗaukar hankali , sauke hannunshi ɗaya yayi daga riƙon da yayi mishi ya saka a aljihu ya ciro ibadar tashi, ya ciro cingom in daga cikin takardar shi ya jefa a bakinshi sannan suka fara taho wurin motocinsu... Murmushi nayi kaɗan yayin da wani sashe na zuciyata yake cewa kira sunanshi idan ya juyo ki caccakawa uwarshi zagi komai zai faru ya faru idan ma ta tafasa ta ƙone, yayin da wani sashe na kwalwata yake bani shawara cewa duk abinda zakiyi kisa nazari da lissafi kiyi ma takonki linzami mai kyau duk daren daɗewa Dikko sai kinci ubanshi. Zuciyata tace kiyi masa magana dan ya tunaki kuma yasan kina nan kuma ki faɗa masa cewa zaki ci ubanshi idan babu yau akwai wata rana.... Sallama nayi da matashin daya faɗa min Dikko ne yazo sannan na wuce ciki, a lokacin dana isa wurinsu tuni D --- K ya zauna cikin mota ana ƙoƙarin rufe masa mota na riƙe murfin motar , Kowa kallo wurin hannun daya riƙe murfin mota yayi dan ganewa idonsa ɗan rainin hankali daya isa yayi wannan iskancin, kwantar da kaina nayi saman murfin motar cikin tausasashshiyar murya nace Dikko, kallo na yayi tare da cewa na'am ya tsareni da idanuwa, shiru na wani lokaci ya ratsa wurin bai daina kallona ba kuma nima ban daina kallonshi ba haka kuma babu wanda yayi mana magana... Nice na fara cire idona daga kanshi dan idan har ina kallonshi tou lallai babu abinda zai hana in burma mishi wuƙa, kaina yana kallon ƙasa nace ka kuwa gane ni ? Na ƙarasa maganar tare da ɗago fuskata amma ban sake kallon idonshi ba... Cikin ɓacin rai yace Al ' Ameen mtsww muje ya faɗi maganar tare da jan murmufin motar da ƙarfi ya rufe, zuciya bata da ƙashi ganin Dikko zai maidani sakara yasa na dunkule hannuna na kaiwa gilashin motar duka saida ya tarwatse , jini kuwa yace gashi nan zuwa... Duk da haka Dikko baiyi niyar tsayawa ba saida nace kai ƙaramin ɗan iska yau itace rana ta ƙarshe a gareka kamar yanda na dasa lissafin kwanaki mutuwarka , idan har kayi nasarar guduwa ina nan tafe gareka sai ka ɗanɗani azaba kwatankwacin irin wacce ka ganamin baka da aiki sai cin cingom kamar wata karuwa sakaran banza daƙiƙi ɗan gidan matsiy...... Wanda aka kira da Al " Ameen shine ya ɗaga hannunshi da niyar kwarara min mari Dikko ya riƙe hannunshi tare dayin murmushin mugunta yace waye yace maka irinsu ake duka ? Tsaya daga gefe kaga maganin ta, Allah ɗaya nake tsoro amma yau dasai nayi mata allurar natsuwa, amma ka barta nayau zan mata kaɗai idan na sake ganinta tou nasan abinda take buƙata, Al ' Ameen yace mai gida ka sakeni in koya mata hankali, murmushin mugunta Dikko yayi tare da cewa bari in bata abinda ta roƙa... Sakin hannun Al ' Ameen yayi sannan ya matso kusa dani, ɗan kauda kanshi yayi gefe kamar yana nazari fuska a ɗaure ya juyo ya kalleni ni juyowar da yayi gaba ɗaya wurin kowa ya juya baya, hannuwana ya haɗa duka biyun ya maidasu ta baya ya riƙe, hannu ɗayan kuma ya riƙe fuskata, ƙasa ƙasa yayi magana cewa. Naga dai kina san cingom in nan kinsan kwanaki da muka haɗu ban "yan maki shi ba, kuma sai kiyi ta abu babu kawaici a gaban jama'a sai kiyi ta wani zalamar Dikko kuma ko an baki ni nayi miki yawa ba inda zaki je dani dan ruwa ba sa'ar kwando bane, kina da daraja ɗaya a wurina kuma albarkacinta kike ci amma wallahi dasai na nuna miki ni tantirin ɗan iska ne, darajar tasa kawai bazan wulaƙanta ki ba, amma idan kina neman rainin hankali da tsantsagwaron rashin mutunci daga kaina an rufe littafi. Tattaunawa yayi cingom in cikin salon jan hankali saida ya busa cingom in yanda ake cewa kwai, sannan ya kalleni da wani iri salo sai kuma yayi murmushi da gefen bakinshi, hannun daya riƙe min fuska ya ciro cingom in sannan ya tura minshi cikin bakina, tuf tuff na fara tofar da cingom in , murmushi yayi tare da rufemin baki yace ai ƙarya kikeyi sai kinci.... Iya ƙoƙari nayi na tofar yaƙi fita ga kuma ya riƙe min hannuwa duka, daidai saitin maƙoshi na yayi min wani duka wanda yasa dole saida na haɗi cingom in, dariya yayi sannan ya sakeni tare da turani baya yace sai mun sake haɗewa an mata.... Tangal tangal na tafi kamar zan faɗi su kuma suka shige motocinsu suka tafi aka barni a filin tsakar wurin daga ni sai Alhaji, dakel na iya haɗiye yawun bakina saboda azaba da raɗaɗin da maƙoshina yakemin saboda nushin da yayi min. Kallon hannu na nayi da jini yake ta ɗiga sannan na kalli Alhaji nace kaini asibiti, cikin damuwa yace muje, dani dashi muka nufi wurin motarshi muka shiga gaba ɗayanmu muka nufi asibiti, Muna zuwa babu wani daɗewa akamin diresin , bayan an bincike hannun kaf ko akwai wani gilashin a ciki, magunguna aka bani sai kuma allurai da akayi min duk Alhaji ne ya biya kuɗin bayan an gama komai ya ɗaukeni muka tafi gida ! A ƙofar gida yayi parking duk muna cikin mota daga ni harshi, shiru mukayi na wani lokaci sannan Alhaji yace hajiya dan girman Allah ki goge wannan vidio dan darajar manzan Allah S. A. W, ki taimaki rayuwata ki goge don Allah, badan halina ba, Ajiyar zuciya nayi sannan nace tou nima ka taimakeni dan darajar manzan Allah S. A. W dani dakai duk mu taimaki juna daga yau nayi maka alƙawari zan goge vidio sannan kuma zan fita rayuwarka babu dawowa... Tattaro hankalinshi yayi wurina sannan yace faɗamin me kike so idan har ina da hali zan miki ! Ba tare dana kalleshi ba nace mota kawai zaka bani daga ita na rantse maka da Allah na fita sha'anin ka vidiwo kuma zan goge... Goge zufa Alhaji yayi sannan yace wace iri kike so ne ? Ni bansan mota ba amma dai mai kyau nake so, kallon motarshi yayi sannan yace kina san wannan ? Ba tare da ɓata lokaci ba nace Eh tamin kuma ina santa, Alhaji yace tou na baki ita, kina da wurin ajiyarta ne ? Yanzu ma zan ajiye miki ita insa azo a tafi dani amma ki goge hotunan nan dan Allah, karka damu zan goge wallahi, a , a nidai ki goge a gabana don Allah, tunda nace zan goge ai zan goge, Alhaji yace tou bayan wannan sai me ? Abu na gaba ina so ka faɗamin waye Dikko ? Miye asalinshi waye babanshi a garin nan ? Wane irin matsayi gareshi kuma wane dalili ne yasa yake ɗagawa ta rayuwa ina san ka faɗamin asalin Dikko da kuma tarihin rayuwarshi..... Gyara zama Alhaji yayi sannan yace fara bani mazaunin motarki na ajiye ki goge vidio sannan sai muyi magana kinga lokacin ina cikin natsuwa, ba damuwa na faɗa tare da buɗe mota na fita na shiga cikin gida !:', Kuyi haƙuri don Allah yau ina can gidan uwar ɗakina nima inacin shagali da miyar mutunci, wurin uwar ɗakina wato *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* ina alfahari dake uwar ɗaki ɗaya tamkar da dubu banda kamarki kuma kina da matsayi na musamma a zuciyar *MEELAT MUSA*..... 24/08/2019 *JAMILA MUSA CE...* ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 18 *_KOMAI DADIN DUNIYA KIYAMA TA FISHI , daga alƙalamin Ummerherny Nerserllerh idan kika bari aka barki baya bazan baki labarin wannan ƙayataccen labari ba wanda ya fito daga alƙalamin haziƙar marubuciyar zamani, Allah ya taimaka surukuta yasa a kammala lafiya amin..._* Ina shiga gidan ko sallama banyi ba yaro ya shigo da saurinshi wai ance Sultana tazo Alhaji yana kiranta , Nana ta fara miya sameki naga hannunki a ɗaure ... ? Duk hankalin su A ` i ya tashi sunga uwar ɗakin kwarata hannu da ɗamara, murmushi nayi tare da cewa yawwa A ` i da Allah inda zan ajiye mota nake so nayi maganar dan kauda tambayar abinda yaji min ciwo, Hafsa tace ina motar take ne ? Ba tare dana kalleta ba nace tana waje, dan haushin Dikko ya fara shafar Hafsa saboda soyayyar da take mishi bana san Dikko haka kuma bana soyayya wa duk wanda yake ƙaunar Dikko, Hafsa tace sai in ajiye miki a gidanmu, ban bata amsa ba nabi yaron muka koma waje... Motoci biyu na gani a ƙofar gida , wurin motar Alhaji na tsaya daidai saitinshi sannan nace gani, wani wuri ya buɗe ya tattaro wasu takaddu ya bani ansa nayi naɗan basar ina kallo a zahirance karatunsu nakeyi amma wallahi a baɗinance bansan ko na miye ba... Fitowa yayi daga cikin motar ya bani makullin tare da cewa ga motar nan zanje mai gida yake kirana dana gama zan dawo insha Allah amma ki rufamin asiri Sultana ki goge vidion nan don Allah, wallahi karkaji komai Alhaji zan goge amma kaɗan bani na kati plz, yace ina zuwa bara in gama tattara tarkacena a motar nan... Komai nashi ya kwashe a mota ya zuba cikin motar dana gani, bayan ya gama ya ciro wayarshi yace kalli ki gani, kallon wayar nayi yace kinga na goge nawa ko ? Nace Eh nima zan goge insha Allah, godiya yayi sannan ya bani kuɗi amma basu da yawa yace idan ya dawo anjima insha Allah zai bani tukuicin goge vidio, godiya nayi masa sannan mukayi sallama ya shiga mota tare da cewa karfa kiyi wasa da takardun motar nan ki adana su kinji ko ? Sai yanzu na gane abinda takardun suke nufi godiya nayi masa suka wuce ni kuma na koma gida... Ina shiga gida Hafsa na ba makullin nace kije ki ajiyemin zan ɗauko ta ƙarshen satin nan insha Allah, ansar mukulin tayi taci gaba da maganar ta, kallonta nayi sannan nace saurara kiji, kije ki ajiyemin mota ki dawo, tashi tayi ita dasu Saude suka tafi ni kuma na shiga ɗakina, ban daɗe da shiga ba Nana ta shigo tare da bani number matar Bello amma bata samo na ɗanshi ba , ansa nayi da nayi niyar bata 500 sai wata zuciyar tace kawai in bata 1k in ka nema ma ka samu ai arziƙi ne... Jakata na buɗe na bata 1k nayi godiya, itama godiya tamin ta fice a ɗakin, tana fita na kulle ƙofa na kwanta saman katifa na fashe da kuka mara sauti , duk duniya babu wanda ya taɓa wulaƙanta ni kamar Dikko nice zai bawa cingom in bakinshi da yawun bakinshi na haɗe a cikin cikina , duk duniya babu abinda yakai miyau saurin sadar da shaƙuwa, shi yasa masu wayau ko bariki suke basa yadda suna haɗa bakunansu da na wasu, waccan ranar bai haɗa bakinmu ba amma shine yau ya ciro abu daga cikin bakinshi ya bani, yana da wata manufa ta daban shine dalilin da yasa yace ma Al ' Ameen bara suga magani na, wato wannan dalilin ne yasa kowa ya juya mana baya ko ? Saida na goge hawaye na sannan nace ƙarya kakeyi yawun bakin ka bazai taɓa zama hukunci a gareni ba... Nayi kuka har na gode Allah daga baya kuma bacci ya kwasheni wanda bansa lokacin daya zo ba kuma baiyi shawara dani ba, Washe gari koda na tashi nayi sallah bacci na koma bayan na gama kwashewa Dikko karama , misalin 09:30am Alhaji yasa aka kirani a waya, bayan na ɗauka nayi sallama dakel Alhaji ya amsamin sallamar cikin nishi yace Sultana ina federal medical center { F M C } saida ya sake yin nishi cikin yanayin wahaltuwa sannan yace ina nan Accident & Emargency kizo yanzu don Allah inasan zanyi magana dake.... Har a zuciyata banji daɗi ba cikin muryar tausayi nace kayi haɗari ne ? Hawaye ya gangaro masa daga cikin idonshi yace kizo dai dan bana tunanin zan ƙara awa ɗaya a cikin duniyar nan.... Subahanalla da Allah ka daina wannan maganar gani nan zuwa insha Allah, cikin rawar jiki na kashe wayata, da sauri na sauko daga saman katifa na zuba ruwa, a gaggauce naje nayo wanka tare da wanko bakina, mai fauda da kwalli kaɗai na shafa, baƙar riga ta jallabiya na saka na yana gyalen a saman kaina na zagoyo dashi har gashin kaina saida ya fito ta ƙasan gyalen jallabiyata, gilashi mai saukin duhu na saka sannan na wanke jikina da turaruka masu sanyi ƙamshi, masha Allah na faɗa a lokacin da naga kaina a cikin madubi, nayi kyau sosai na fito kamar baƙuwar balarabiya a nigeria, Wayata na ɗauka da jakata, na fito ina tsaye ina kulle ɗaki Hafsa ta shigo, ita ɗaya ce babu abokan nata su Saude, su Nana ma duk basa tsakar gida, ɗan gangarowa tayi da wani irin salon tafiya, ta wutsiyar idona na kalleta sannan na ɗaure fuskata na kallota dukanta a daidai lokacin dana gama rufe ɗakina... Wow uwar ɗakin karuwai kinyi kyau fa kamar dai ba'a mutu ba, share maganar nayi tare da cewa da mota kika zo ne ? Eh ta faɗa tare da bina da kallon cin wanka , gaba nayi tare da cewa muje ki saukeni f m c biyoni tayi muka fito a tare, a ƙofar gida muka haɗu dasu A ` i hada Amisty da Saudatu.... Amisty tace wurinki zamuje munji shiru har yanzu, kuma mun rubuto takarda an tsara jaddawalin yanda zai ƙawatar ya kuma tafi da hankalin maza gaki kuma zafi fita, buɗe gaban mota nayi na kame sannan nace ku shigo muje kuma, baya suka shiga, Hafsa kuma ta zauna mazaunin tuƙi taja muka tafi.... Saida muka fara tafiya sannan nace karanto min ina saurarenki, Amisty fa tasan komai tasan bana ganewa bana rubutawa kuma bana iya karantawa amma sai tace kidai duba ki gani Sultana, basar da ita nayi tare da miƙa hannuna ta baya na anso takarda ko buɗewa banyi ba na ajiye shegiya ban sake bi ta kanta ba kuma ban sake magana ba har muka isa asibitin... Wani irin tuƙin ganganci Hafsa tayi tare da sakin sitiyarin saboda taga D --- K , a tare muka iso dasu sai leƙawa take tana kiranshi, wato abinda na fahimta idanma ka nunawa mutum ka damu dashi sai yayi ta ɗagawa, kallon Hafsa nayi tare da cewa ke kuwa baki da aji a haka kike tunanin zan riƙa haɗaki da zafafan mata babu class, raina ya ɓaci sannan nace uban waye Dikko da kike ta hauka kina kiranshi mutane suna kallonki kamar wata zararriya.... A daidai lokacin da muka fito mu dukanmu daga mota shima Dikko ya fito kuma yaji zagin da nayi masa , bai kallemu ba yayi gaba ana take masa baya nima gaba na shiga su Hafsa suka rufomin baya, murmushi Dikko yayi a daidai lokacin da muka tsaya bakin ƙofar ɗakin kowa da muƙarrabenshi a bayanshi, kallona Dikko yayi tare dayin murmushi sannan yace zaki ci ne an mata yayi tambayar tare da ɗaga gira ? Ya ƙarasa maganar tare dayimin wani irin kallo mai tattare da mugunta, yaci gaba da cin cingom inshi cikin salon jan hankali gemunshi yana motsawa a hankali cikin salon ɗaukar hankali , murmushi nayi saboda gaskiya yanayin da yayi ya burgeni, ƙarshen harshenshi ya kawo cingom in yayi wasa dashi a daidai lokacin da aka buɗe mana ƙofa duk muka shiga, daga waje bai sake kallona ba kuma bai sake murmushi ba babu magana har muka isa gaban gadon Alhaji... Duk matan da muke tare ihu muka farayi saboda tsoron yanayi da Alhaji yake ciki yayin da wasu suka nufi hanyar fita, dani da A ` i aka bari yayin da A ` i ta duƙushe tana kuka ni kuma na cire gilashi na wurgar a gefe na rufe idanuwa na naci gaba da dire dire ina kuka saboda na kasa gaba na kasa baya.... Shi kuma Alhaji burinshi inje wurinshi in taimaki rayuwarshi na goge vidio sai kirana yake cikin dasasshiyar murya da yayi magana sai jini ya kwararo , Dikko yace ya daina magana amma yaƙi saurarenshi Sultana kawai yake kira, Kusa dashi Dikko ya ɗuka sannan ya tambayashi me zan mishi ne ? Hawaye na zuba a idon Alhaji yace ma Dikko ya rufa mishi asiri ya kawoni wurinshi magana zamuyi ta sirri, Dikko yace faɗamin na faɗa mata kaga ta firgita wani abu zai samunta, cikin wahaltacciyarar murya Alhaji yace kayi min wannan arziƙin na sauran mintunan da suka ragemin a duniya lokacina yana tafiya zan iya mutuwa ko wane lokaci, yanda yayi maganar ne yasa Dikko ya kallo inda nake tsaye ina ta direre kamar anyi ma lafiyayyan diko allurar hauka. Ɗauke idonshi yayi daga kaina sannan ya kalli zugar daya zo da ita, Al ` Ameen ya faɗa cikin wani irin yanayi kamar bashi ne yayi maganar ba, gaba ɗaya waje suka fita harda A ` i aka fita, inda gilashina yake Dikko yaje ya ɗauko sannan yazo kusa dani, ta gaban rigata ya jawo ya sagala gilashin sannan yace buɗe idonki, jikina yana kyarma na buɗe na kalli Dikko, dakel ya haɗe yawun bakinshi sannan ya tofar da cingom in bakinshi gaba ɗaya yanayin Dikko ya canza ɗaure fuska yayi sosai sannan yace miye tsakaninki da mara lafiyar nan ? Miye dalilinki na zuwa ganinshi ? Me kikaje yi gidanshi ? Kema "yar iska kike so ki zama ko ? Cikin gatsali nace Ey "yar iska zan zama ina ruwanka da iskanci na ne ? Jinjina kai yayi tare da cewa Allah ya sawaƙe wuce muje yana kiranki, tirjewa nayi tare da juya zan fita da gudu ya riƙoni yace ai ƙarya kike sai kinje, har gaban Alhaji ya jani ya kaini sannan ya zaunar dani saman kujera ya tsaya ta bayana yace gata nan me tayi maka ne ? Ko kaima taci kuɗinka kamar yanda taci na Umar ? Ɗaga kaina nayi na kallo Dikko ɓacin rai kwance a cikin idonshi zare min idanuwa yayi tare da cewa bari kallona kar fashe miki kwayar ido wallahi, jiki a sanyaye na sauko kaina daga kallon da nake ma Dikko naci gaba da kallon Alhaji ina kuka, dafo kujerar yayi ya duƙo kusa dani sosai saitin kunne na yace na rantse da girman Allah idan na gano akwai wani abu tsakaninki dashi saina kashe ki, ya faɗi maganar tare da shaƙemin wuya sosai na fara ƙoƙarin ƙwalƙwale hannunshi na kasa, tun ina iyawa har nasa wani abu na fara halbe halbe har na faɗo daga saman kujera Dikko bai saki wuyana ba naci gaba da halbe halbe, yanda nake halhalbe ya jawo hankalin mutane suka yo kanmu amma an kasa cire hannun Dikko daga wuyana, Hayani tayi yawa sosai wanda yasa su Al ` Ameen suka shigo ciki da gudu amma wallahi duk yawan mazan nan suka kasa ɓanɓareni daga hannun Dikko harsai dana suma, riƙe Al ` Ameen yake da hannun Dikko yana cewa don girman Allah mai gida ka ƙyale yarinyar nan karta mutu, zaro jajayen idanuwan shi yayi kamar yaci mutuwa yace fita idona Al ` Amenn ya faɗi maganar yana fitar da wani irin lumfashi kamar ranshi zai fita, Al ` Ameen kuwa ƙin sakin hannun Dikko yayi saboda tunda yaga Dikko a wannan yanayin yasan komai zai iya faruwa.... Yace mai gida karta mutu, Dikko yace ta mutu idan ta mutu kaine ka kashe ta ko kaine zakayi azumi ? Ya ƙarasa maganar tare da kwalalo idanuwanshi waje , sannan yace duk abinda ya faru da ita nine ya ƙarasa maganar tare da nuna kanshi, haƙuri akayi taba dikko dakel aka samu ya sakeni , Bakin gadon Alhaji ya koma ya ɗauki wayarshi iyakar bincike Dikko yayi bai samu komai ba, kuma number na dama Alhaji baiyi saving ba, jerin kira ya dawo yaci gaba da binke, saida ya gama sannan ya ajiye wayar , kallo gadon da nake kwance yayi har an sakamin ƙarin ruwa da taimakon Al ' Ameen dayayi tsaye yace a bani taimakon gaggawa, Kusa da Al ' Ameen yaje tare da cewa bani makullin mota, cikin girmamawa ya ɗauko ya bashi baiyi mishi musu ba saboda yasan Dikko baya san gardama idan yace ayi kawai ayi mishi idan yace a bari barin kawai za'ayi sai a zauna lafiya, Cingom ya ciro daga aljihu ya ɓanɓare ya saka bakinshi yaci gaba daci, Al ' Ameen kuwa bin Dikko yayi da kallo harya fita daga ɗakin yana mamakin hali irin na Dikko zuciyarshi tayi yawa idan ya burkuce wani lokaci kamar bashi ne yakeyi wasu abubuwan ba... Ta jikin window ya leƙa Dikko, har ya shiga motar yaja ya tafi cikin tuƙinshi na ganganci wanda baya kaucewa kuma baya ɗagawa kowa ƙafa idan ya tafi sai yakai inda zaije hankalinshi yake kwanciya, Allah ya tsare hanya Al ' Ameen ya faɗa tare da dawowa wurin gado na ya tsaya, su Hafsa da Saude da A ` i da Amisty sunyi jigum kowa yana jiran farfaɗowa ta yaji abinda ya haɗani da D --- K...... Dikko kuwa tuƙi yake amma yana tunanin maganar Alhaji ranka ya daɗe wato wallahi wata yarinya ce muka ɗan keɓe da ita , tou wallahi bansan yarinyar nan ta shirya sharri ba, ashe duk abinda mukayi ranka ya daɗe tana ɗauka cikin waya ban sani ba.... Dukan sitiyari Dikko yayi tare da cewa tabbas yacemin yarinyar nan shekarunta bazai wuce 16 zuwa 17 ba daidai saitin zuciyarshi ya daka tare da cewa kece .... ? Akan titi duk ƙurewar wuri Dikko ya juya kan sitiyarin mota ya koma baya ba abinda ya dameshi da halin da wani zai shiga kanshi kawai yakeji amma baya sauraren talakawansu, da gudu ya ibi shararra ya komo asibiti, a lokacin su Al ' Ameen sun fito zasu tafi ganin Dikko ya dawo yasa Al ' Ameen ya dawo cikin ɗakin da gudu yasa aka ɓoyeni, danshi Alhaji tuni Allah ya anshi rayuwarshi har an tafi da gawarshi, duk zunubin da Alhaji ya cacumar ma kanshi an samu wani marar rabo a lahira ya dira gidanshi yayi mishi caccakar wulaƙanci aka kawoshi asibiti dan ceton rayuwarshi Allah yasa ikar ibar da yayo kenan, Allah ya jiƙanshi yasa mu cika da imani ubangiji ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo... Ana ɓoyeni su Al ` Ameen suka fito, a waje suka haɗu da Dikko yana ƙoƙarin shiga suka faɗa mishi mutuwar Alhaji ni kuma an canja min asibiti, Allahu Akbar Dikko ya faɗa tare da cewa ubangiji ya ƙarɓi baƙuncinka Muntari Allah ya kyautata tamu bayan taku, da Amin kowa ya ansa sannan suka tafi a tattare baki ɗayansu... 25/08/2019 Taku a kullum *MEELAT MUSA...* ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 19 Har yanzu kalar idon Dikko bai koma fari ba, idon nan jajir kamar yaci bala'e, amma a hankali yake washewa zuwa kalarshi ta ainahi, fuskar nan a murtuke ya jingina bayan shi da kujerar mota kana kallonshi kasan yana tattare da tsantsar damuwa. Ɗan gajeren tsoki yayi tare da gyara zamanshi, hannunshi yakai ya shafe gefen fuskar shi, tunanin safiyar haɗuwarshi da Sultana ya fara dawo mishi sabo fitikil kamar yanzu ne abun yake faruwa, da sauri ya rumtse idanuwan shi tare da haɗe leɓunan sa wuri ɗaya ya danne su da haƙoranshi ta ciki, buɗe ƙofafin hancin shi yayi saboda lumfashin da yake shaƙa yayi mishi kaɗan ya buɗe ƙoƙofin hancin ne dan iskan ya yalwace shi. Har suka isa gidan rasuwa Dikko bai sake ma kowa magana ba, tunda dama shi ba ma'abokin surutu bane, mota nayi parking ya fita cikin damuwa danshi dama kullum haka yanayin shi yake , farin ciki da ɓakin ciki duk yanayin iri ɗaya ne a wurin shi, babu wanda ya isa yasan lokacin farin cikinshi kuma babu wanda ya isa yasan lokacin da yake damuwa. Tunda ya fito aka fara gyara mishi wurin da zai zauna dan zamanin ga mutane basa abu domin Allah basa darata girma shekaru da mutumci amma suna ba naira matsayi na musamma, Dikko yana da rashin mutunci amma alherinshi yasa mutane basa ganin rashin mutuncin nashi dan Allah yayi masa kyauta idan dai kukayi ido ido dashi tou tabbas zai baki kuma baya da kwauro idan zai bayar mai yawa yake baka, tou kyautar itace ta danne rashin mutuncin shi ga idanuwan al'ummar gari... Sabuwar tabarma aka amso daga cikin gidan aka shimfida mishi, takalman shi ya cire ya taka tabarmar da safa, saida ya zauna sannan kowa ya zauna kuɗi suka fara nuna ikonsu domin masu neman asan dasu sukayi ta zubewa suna bada gaisuwa, saida ya jinjina kai dan shi kaɗai yasan tsutsar baƙin cikin dake lasar masa zuciya... Wanda suka bawa duniya gaba ne suka fara bawa Dikko labarin yadda abun ya faru amma a zahirance yana jinsu amma a baɗinance hankali shi yana wurin Sultana so yake kawai a dawo jana'iza yaje ya ganota wallahi sai ta faɗa mishi miye tsakaninta da Muntari, inma banda take daƙiƙiya dan ta tona mishi asiri shine zai haɗa kirji da ita taje ita kuma ta haɗa da yaronshi... Wayarshi ya ciro yayi "yan rubuce rubuce bayan ya gama ya tura, wayar shi ya maida aljihun gaban riga a zuciyarshi kuwa yana tunani Sultana ta gama barbaɗashi a duniya kowa kallon ɗan iska yake mishi, Mikewa tsaye sukayi gaba ɗaya dan an fito da mankara, sai yanzu wasu keyin alwalla shidai yana da ita takalmin shi ya saka suka fita sarari dan sallatar gawar Alhaji Muntari , Allahu Akbar ubangiji kayi mana kyakkyawan ƙarshe hanyar dai ɗaya ce duk wanda yazo sai ya koma Allah kasa mu cika da imani idan ajalinmu yazo ameen.... A asibiti kuwa ina kwance cikin tsaka mai wuya, ina tafiya ne tsakanin rayuwa da mutuwa, duk wanda ya ganni saiya tausayamin ga hannu na naɗe da bandej wanda na fasa shi a jikin gilashin motar Dikko, su A ` i kuwa suna bani kulawa ta musamman tare da tattalina kamar mun fita ciki ɗaya ! Tsaye suke zagaye jikin gado na hankalin kowa tashe, jami'an tsaro ne suka shigo gaba ɗaya suka fatattaki su A ` i , kujerar da ake tura marasa lafiya aka ɗauko aka ɗorani a samanta suka tun kari hanyar fita dani daga cikin ɗakin, wani irin ihu Saude tayi tare da cewa ina zakuje da ita ne ? Basu saurari kowa ba suka fito dani, cikin mota aka sakani mazaunin baya sannan aka rataye ƙarin ruwan a jikin kujera yaci gaba da shiga cikin jikina, A wurin suka bar kujerar duk suka shiga mota sukaja muka bar asibitin, kuka su Hafsa sukayi tayi tare da tambayar kansu wane irin laifi nayi wanda har hukuma bata ragamin ba ina kwance a gadon asibiti, sunsha kuka har sun godewa Allah daga ƙarshe suka haƙura suka tafi gida... Daga maƙabarta Dikko basu dawo gidan rasuwa ba gida suka wuce kai tsaye, tun a get na biyu ya sauka tare da cewa zai shiga yayi bacci , Al ' Ameen yace ranka ya daɗe bara muje get in ƙarshe sannan mu sauke ka amma daga nan ai zakasha tafiya, ba tare daya kalli Al ' Ameen ba yace nan zan sauka ya ƙarasa maganar tare da kallon Al ' Ameen , tuba nake ranka ya daɗe Al ' Ameen ya faɗa tare da jan motar yayi gaba... Saida ya daina hango ɓurɓushin motar sannan ya fiddo wayarshi yayi "yan lashe lashenshi sannan ya kara a kunnenshi , bayan wani lokaci yace kuna ina ne ? Magana na cikin wayar yayi sannan Dikko yace ku shigo ta get in baya, yana faɗin haka ya kashe wayarshi tare da kiran wata wayar kuma. Ta baya ya dawo ya bi wata hanya daban , tafiya mai nisan gaske yayi wurin tsitt bakajin ƙarar komai sai motsin tafiyarshi tunda tsakuwowi ne baje a wurin irin wannan fararen wanda idan ana rana har kashe ido suke, idan ya taka sai kaji tsus tsuss ƙarar tafiyar shi , Wata hanya ya bullo sai gashi jikin wani makeken get, masu gadi yayi ma magana suka buɗe motarmu ta shigo cikin gidan, gaba yayi motarmu tanabin bayanshi saida mukayo nisa da get in sannan ya tsaya, shima matuƙin motar tsayawa yayi tare da fitowa Dikko bai mishi magana ba ya shiga mazaunin dirver yaja motar yayi gaba. A bakin ƙofar falonshi yayi parking sannan ya fito yaje ya buɗe ɗakin, dawowa yayi ya buɗe baya inda nake kwance rai hannun Allah, ciro robor ƙarin ruwan yayi ya fara riƙewa sannan ya ɗaukeni ya shiga ciki, a falo ya kwantar dani saman kujera 3sieter saida ya gyara ruwan suka ci gaba da shiga sannan ya fita tare da rufe ɗakin ta waje... Motar ya ɗauke daga bakin ƙofar falon sannan ya ajiyeta a inda suke ajiye motoci, motar ta gidansu ce kuma jami'an suma na gidansu ne yayi amfani dasu... Dawowa yayi tare da rufe ɗakin sannan ya wuce ciki, wanka yayi ya cire manyan kaya zuwa ƙanana, falo ya dawo ya zauna yana jiran lokacin da zan buɗe idona ya haɗa partyn shagalin wulaƙantani, Zama yayi saman kujera wacce take kallona, ba abinda yake tashin shi a wurin saidai yaje yayi sallah ya dawo, idan yazo ya zauna kuwa lokaci zuwa lokaci yakan kalli agogon hannushi sannan ya kalli inda nake kwance, waya kuwa idan an kishi saida ya duba kawai ya latse, Ruwa ma daya ƙare shine ya cire min, bai daɗe da zama ba aka fara dukan ƙofar ɗakin, ɗan latse baki yayi tare da cewa waye ? Dikko buɗe nice, muryar yayarshi yaji miƙewa yayi yaje ya buɗe ƙofar suka shigo cikin falon tare, Salati nayi a daidai wannan lokacin jin muryar Dikko da sunanshi da aka kira, wani irin abu naji ya daki zuciyata, na ƙara lafewa bamma yi gigin tashi ba haka kuma ban kuskura na buɗe idona ba, amma jikina ya mutu murus , zama yayi a saman kujerar da yake itama kusa dashi ta zauna saman hannun kujera sannan tace ina ka samo larabawan daji ? Ta faɗi maganar tare dayin dariya... Banza yayi baice mata komai ba, dariya ta sakeyi tare da jan gemunshi sannan tace dan ubanka bakaji ina maka magana, tayi maganar cikin sigar zaulaya, tsoki yayi tare da cewa ni bana san irin abinda kikemin yayi maganar cikin haɗe rai kamar dai yanda ya saba, kaiji ɗan iska ni zaka ɗaure ma fuska ko mutuwa zakayi na faɗa maka bazan daina janka ba, duk wannan haɗe haɗen fuskar gabana aka haife saida ma nayi aure dan ubanka kazo duniya wane girma zakayi gabana, ko inda take bai kalla ba, kuma baiyi murmushi ba bare tasa ran zaiyi dariya, sansar wauta dai tayi ta nunawa da sakarci amma Dikko tunda yace mata baya san abinda take mishi bai sake magana ba saida ta ƙari rashin wayanta sannan ta taho inda nake kwance... Ko kallonta baiyi ba dan hankalinshi ma yana kan wayarshi amma yana kallonmu da zuciyarshi, tsaye tayi gabana idona da jikina suka ɗauki kyarma da sauri na buɗe ido na kalleta a tsorace sai kuma na kallo inda Dikko yake zaune amma yanzu bayacim cingom maido kallona nayi wurinta kawai sai na fashe da kuka.... Sai yanzu ya ɗago kanshi cikin tsawa yace ki rufemin baki, da sauri na haɗe kukan tare da rufe idona dan wallahi a halin yanzu tsoron Dikko nakeji dan na fara tunanin kila mahaukaci ne amma har yanzu jikina bai daina kyarma ba. Juyawa yayar tashi tayi tai mishi magana da yaren arna { turanci } bansan abinda sukace ba, ɗan ɓata fuska yayi sannan ya ajiye wayarshi shima yayi mata magana cikin irin harshen da tayi masa, Allah ya bata lafiya ta faɗa tare da cewa zan koma wurin momy da Allah kayi ƙoƙari ka shigo, da kanshi ya amsa mata, saida ta ƙara kallona sannan ta kalli Dikko ta sakeyin magana da yaren ɗazu, kyakkyawan murmushi yayi sannan yace ngode ya faɗi maganar tare da ɗauko cingom ya fara ci, abinda na fahimta cin cingom in kila yana da ƙa'ida domin yafi amfani dashi a wasu lokutta wanda shi kaɗai yasan su... Fita tayi daga ɗakin tare dajan ƙofar garam, har yanzu idanuwa na a rufe suke jikina kuma bai daina kyarma ba, tashi yayi yaje ya kulle ɗakin sannan ya dawo ya zauna, cikin kujera ya tura hannunshi ya zauro wata irin zureriyar wuƙa sai kyalli takeyi saboda sabinta, Ke zo nan , kamar ina jira na tashi dan nasan babu wata ke a ɗakin sai ni, da sauri na isa gabanshi na durƙusa cikin tsoro na sauke kaina ƙasa, cikin natsatstsiyar murya yace kalli , ɗago kaina nayi na kalleshi amma ba ido cikin ido ba, cikin murya maisa natsuwa yace mi yasa bakijin magana ? Shiru nayi naci gaba da lissafin "yan yatsu na, bana san ina magana ina maimaitawa, raina yana sauri ɓacin ne , banda haƙuri zuciyata a kusa take ina tambayarki kawai ki bani amsa... Mi ya haɗaki da Muntari kikayi mishi vidio ? Wata irin mummunar faɗuwar gaba naji kardai Alhaji ya nunawa Dikko vidion nan, Dikko kuwa ɗoro tsinin wuƙarshi yayi daidai saitin maƙoshina, wanda ya shaƙeni a gaban mutane lallai zai iya kasheni tunda babu mai ganinmu sai Allah, ina san ganin idonshi domin ta nan ne kaɗai zan iya gano idan Alhaji ya bashi labarin vidio, Ɗan kartar min wuya yayi da wuƙar tare da cewa ke nake sauraro, cak na ɗauke numfashina tare da kallon kwayar idonshi sannan nace waye Muntari ? Na tambayeshi ne dan san gano ko gaskiya ne ? Da ƙafarshi ya takamin baki sannan ya halbi daidai saitin hancina har saida jini ya fita. Ƙasa ƙasa yayo da wuƙar daidai saitin ƙirjina inda daya burma min ita tawa ta ƙare, cikin kuka na riƙe wuƙar tare da cewa to yanzu kuma laifin me nayi maka ? Na ƙarasa maganar hawaye na kwarara daga cikin idona, shima hawaye ne kwance a cikin kwayar idonshi cikin damuwa yace saki wuƙar kinji, sakin wuƙar nayi sannan yace zaki iya kasheni ? Cikin rashin fahimta nace kamar ya zan iya kisa bayan nasan ba abune mai kyau ba ? Dikko yace tou mi yasa kika zaɓi zunubi mafi muni a rayuwarki ? Kin kuwa san illolin dake tattare da zina ? Kinsan bala'en ta kinsan matsalolin da take haifarwa ? Kina ƙaramar yarinyarki ki tunkari mazan bariki, kinsan bala'e kuwa irin na mazan bariki ? Kinsan haɗarinsu ? Mazan bariki basa taɓa jin tausayin macen bariki kuma basa tattalata basu san darajarta ba haka kuma bazasu taɓa raga mata daidai da ɗigon kwayar zarraba bariki ta fito kuma shi za'ayi da ita tunda sunsan idan sun lalataki gobe ma wata zasu nema, kinga kuwa da wannan bala'e da kika bashi gaba kawai gara ki sokawa Dikko wuƙa ki huta ya ƙarasa maganar tare da miƙomin wuƙar.... Kallonshi nayi amma banyi magana ba, murmushi yayi tare da ciro cingom in bakin shi yace na ƙoshi ko zaki ci ne ? Banza nayi kamar banji ba , ɗaga kafaɗun shi yayi tare da cewa kin huta 🤷🏻‍♂, ya faɗi maganar tare da maida cingom inshi cikin bakinshi yabi ni da kallon rainin hankali, Shiru na wasu mintoci sannan yace kinsan abinda yasa nazo dake gidan nan ? Keda ke gidanki idan kinyi magana tou na tankawa Dikko, ci gaba yayi da cewa anan kaɗai zanyi magana dake cikin natsuwa, ki daina hayemin kuma ki rage rashin kunya sannan ki taka a hankali duniya taƙaitacciya ce ga kowa amma babu kamar mace, Ki taka sannu An mata ki faɗamin duk abinda kike so a duniyar nan ko miye zan miki kuma zan baki idan dai zaisa ki kwantar da hankali ki natsu, kuma ba yau kaɗai ba zan ci gaba da kyautata miki daga nan har ranar da numfashina zai bar gangar jikina zanci gaba da kyautata miki dan kiyi farin ciki , ke yarinya ce baki san komai na rayuwa ba, amma zan sake faɗa Allah ya baki sa'ar rayuwa da har kika shigo rayuwata sheɗan kuma ya samu galaba a kaina, tunda ni zina ba aikina bane ban taɓa ba tunda nake wallahi sai a kanki. Kinsha dani kuma kin gama dani har badan duniya, kina da matsayi na musamman da bazai taɓa goguwa a zuciyata ba kuma kin shiga cikin babban tarihin da bazai taɓa gogewa ba a rayuwata har abadan duniya , duk wacce ta shigo kece farko, ni haɗuwata dake na barshi matsayin ƙaddara kuma bansan abinda ubangiji yake nufi da ita ba. Daga ni harke babu wanda yasan abinda anjima zatayi bare gobe, amma ina riƙonki da Allah kiyi haƙuri kuma ki yafemin akan duk wani abu daya faru tsakanina dake, taɓe bakina nayi tare dayi magana ƙasa ƙasa amma baiji abinda nace ba, Eye ? Ya tambayani tare da yatsina fuska yace banji me kike faɗa ba , Kai tsaye na kalleshi tare da cewa bazan yafe maka ba har abadan duniya, jinjina kai yayi tare da cewa to ba komai Allah yasa rashin yafiyar shine alkairi a rayuwata, kina buƙatar wani abu ne daga gareni ? Ni bana san komai saboda baka da abinda zaka bani ni bakayi kuɗin da zaka taimakeni dashi ba har yanzu, bai sake magana ba, ya ɗauki wayarshi ya kira mutumin daya kawoni yace yazo ya mai dani gida... Ci gaba nayi da zage zagena ƙasa ƙasa yanda bazai iya juyoni ba, anan nayi ganganci ɗaya kunsan masu iya magana sunce idan mutum matsiyaci ne ko an sakashi a tandun man shanu aka tsamo shi haka nan zai fito jikinshi ƙamas. Babu wani ɓata lokaci mutumin ya iso, Dikko yana jin tsayuwar mota yaje ya buɗe ɗakin ki ya dawo ya zauna, da sallama mutumin ya shigo tare da kallona yace muje, tashi nayi tare da ƙara kallon Dikko har yanzu bakinshi yana motsawa cikin salo mai burgewa da ɗaukar hankali yana cin cingom inshi cikin kwanciyar hankali , gaskiya nidai yanamin kyau idan yana cin cingom, amma fa bana ƙaunarshi, bai kallemu ba kuma baiyi mana magana ba hankalin shi yana saman wayarshi, Nayi tunanin DK zaiyi ta haɗani da Allah ko kuma idan yaga zan tafi zai kirani amma ko ɗaya ba abinda ya faru, haka nan naji babu daɗi haƙura kawai nayi na shiga mota muka tafi, 11:30pm a cikin ɗakina tayi min, daga Nana sai Karima kawai a gidan sunata jajantamin. Kuma sune suka faɗamin mutuwar Alhaji, nayi kuka sosai musamman ma a lokacin dana ga vidion dana ɗauka muna ai kata saɓon Allah wani irin imani da tsoron Allah ya tsargamin zuciya tare da ganin kamar mutuwa zanyi yanzu yanzu, Na daɗe ina kukan mutuwar Alhaji a cikin kwanaki ukku daga nan kuma na ɓarar da lamarin zance mutuwarshi muka fuskanci rayuwar bariki..... Bani canzawa, kuma yanzu aka fara.... Muje zuwa.... 26/08/2019 *JAMILA MUSA...* 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 20 *_Shafin ga gaba ɗayanshi kyauta ne ga group mai albarka da mutanen cikinshi masu mutunci MEELAT MUSA FANS kuna fa sakani nishaɗi idan kuna sharfi nakanyi dariya sosai domin kuma ilimi ne na musamma ngode sosai Allah ya ƙara haƙuri da juriya, wata ma dai wai cewa tayi Oga Dikko ! Star Dikko ubangidan KWARATA , nafa gode Allah ya baku wayoyi masu riƙon caji da caja mai saurin cika hand set amin... Ni Meelat ko ince JAMILA MUSA nake cewa asha karatu lafiya...._* *_Ina miƙa saƙon ta'aziyya ga "yar uwa kuma abokiyar aiki haziƙar marubuciya Fadeela Lamiɗo ina tayaki jimamin rashin ɗan uwanki Allah ya jiƙanshi ubangiji ya amfani zuri'ar daya bari , Allah ya baku haƙurin rashin sa annabi yasan da zuwanshi, mu kuma Allah ya kyautata namu zuwan bayan nasu ubangiji yasa mu cika da imani idan ajalinmu yazo..... Am3n ya Allah..._* Duniya sabuwa inji masu iya magana yayin da wani yake kuka a lokacin wani yake farin ciki, kukan mutuwa da jimimmamin rayuwa yana gidan Alhaji Muntari yayin da a gidan da muke haya yau muke shagalewa muna raƙashewa muna cin duniyar mu da tsinke... Zaune muke a saman tabarma yayin da ni nasha riga da zani na atamfa nayi ɗaurin ɗan kwali na irin na sabbin karuwai, na nemi bakin kwalli na daddaɓawa bakina, ga kitso na matan bariki da aka yanyaramin ɗinki rigata ya kameni sosai duk rabin halittun jikina sunyo waje, kallo ɗaya zakamin kasan ni tantiriyar karuwa ce wacce ta anshi lasisin iskanci bada jimawa ba, yanayi na ya fita a cikinsu kana gani na zaka gane nice uwar gidan *kwarata...* Miƙe ƙafafuwa na nayi a saman tabarma nayi zama irin na matan da basu da kamun kai, a gefen damata Amisty ce zaune da jaddawalin sabuwar bariki mai fara aiki a cikin satin nan.. Nana , Karima , Hafsa , Amisty , A ` i da Saude duk suna wurin daga gabana suna ta bani wani irin matsayi na musamman sai kace nayi musu asiri zakayi mamakin yanda suke darajani, yaran nawa dai su shidda ne duk dani mun zama bakwai mune sabbin *kwarata* a cikin wannan zamani kuma nice shugaba kuma zanzo da salon da tarihina bazai gogu ba a cikin tarihin birnin garin katsina... Juyawa nayi gefen hagguna zuga ce ta "yan daba dana ɗauko su haya zan riƙa basu albashi duk ƙarshen wata, dalilina kuwa na ɗaukarsu duk yana cikin labarin, sunsha kitso irin na ɗiyan kafirawa kallo ɗaya dai zakayi musu ka tabbatar sunsha iskanci sun ƙoshi... Saida na gama kallesu tsaff sannan na fara nazari da tunani , na farko dai zamanin ga ya canja rayuwa bata tafiya dole saida ilimi, waye zan samu mai amana da zai riƙa karantawa rubutuwa da fassarawa idan anmin turaci, babu shi zuciyata ta bani amsa tare da cewa karki sake ki yadda da matan bariki dan basu da amana... Kallon Amisty nayi tare da cewa karanto min ina saurarenki, miƙomin takardar tayi , murmushi nayi bance komai ba na ansa, biro na ɗauka na juya bayan takardar nayi rubutu da labarci kamar yanda nayi a police station miƙa mata nayi bayan na gama rubutawa sannan nace haɗa dukansu ki karanto ina saurarenki... Zazzare ido ta farayi ta ƙurawa jaddawalin ido, alifun kanshi idan zaki kasheta bata iya karantawa ba, ganin ta kasa nace tou ki kiyayi kanki da duniya duk baiwar ki wani yafi ki, kece kika rubuta kuma kece zaki yaɗa ba kowa ba, karki damu basai naji abinda ke ciki ba, kije kawai.... Ku tashi muje na faɗi maganar tare da miƙewa tsaye, ɗaki na koma na ɗauko gyale na sannan na fito, gaba nayi zugar daba ta da tasha suka biyoni baya harsu Nana ba'a bari ba, ina gaba suna bayana "yan daba kuma suna gaba cikin siga mai kalar bada tsoro, Gidan da zan siya a cikin anguwarmu mukaje dubawa, ƙaton gida ne sosai akwai ɗakuna birjik ɗaki yakai goma sha ukku, sai bayi guda biyu sai baranda inda ake dafa abinci, amma gidan gidan ƙasa ne irin tsufin ginin da can can, akwai yalwataccen filin tsakar gida... Nidai gidan yamin sauƙi gaskiya ko dan ina matse na siya ? Miliyan biyu aka masa kuɗi babu gudu babu ja baya gaskiya yayi arha dan da a bakin titi yake bazan iya siya ba , daren jiya na bada miliyan ɗaya da rabi, nace zan cika sauran yau idan Allah ya kaimu.... Shine muka zo gani da kowa , gaskiya sun nunamin farin ciki sosai kuma basu nunamin hassada ba, bayan mun gama dubawa muka fito, tunda muka fito yanayin yadda naga anguwar tayi shiru ya taabbatar min Dikko ya shigo... Shine kuwa ɗan iskan , ya fito daga gidan dokunan shi na anguwarmu da yake daga get in gidan zaka iya hango komai na cikin anguwar idan aka shigo santar kuma gidan dokunan Dikko yake kallonka, A tsiyace ya fito kamar yadda ya saba, duk tawagata suka koma da gudu baya suka kauce daga saman hanya yayin da ni kuma na shigo hanya hankali kwance Amisty ta taho da gudu zata jawoni wani mutum ya riƙeta dan a ganinshi biyu babu za'ayi tunda dai ni na tafi sunamin addu'a Allah ya jiƙana, ihu Amisty ta farayi tare da cewa Sultana don Allah karki biye wa zuciya ki dawo ko ki gudu bana so ki mutu yanzu wayyo Allahna, kowa duƙar da kanshi yayi yayin dana tsaya cas kuma Dikko ya sheƙo da gudun tashin hankali, wallahi da bani bace ko wacece sai Dikko yabi ta kanta ya wuce babu abinda ya dameshi... Gab dani ya taka wani irin wawan birki ya fito cikin tsananin ɓacin rai ko mota bai tsaya rufewa ba , hannushi ya ɗaga da niyar marina kuma ko meye ya hanashi ya mareni Oho, ganin ya juya zai koma mota nace Allah ya auna maka arziƙi yau dasai nasa anyi maka fiɗa irin wacce akewa raguna, daka takani ko ka bigeni dasai naga ko waye ubanka a garin nan... Uhum yace tare dayin gajeran murmushi da gefen bakinshi sannan yace ake yarinya ce a tunaninki kama nayi miki da ɗan wa a garin nan ? Dake da babanki da kowa naki da kike taƙama dashi talakawan mahaifina ne , ni kuma abinda na ɗauki talaka takalmi na ne zan takashi yayin da nake sha'awa in kuma cire na jefar a duk lokacin dana gaji da ganinshi, ke abinda na ɗaukeki baki da banbanci da dabbar layya a wurina ina kiwonki ne kafin ranar da zan yanka ki , abinda yasa kuma banbi takanki na wuce ba idan na kamaki zaki basu labari... Murmushi nayi tare da cewa duk takalmi takalmi sunanshi amma ko a cikin takalmin wani baka sakashi yayi maka daidai, talakawa suna taku amma kai da mahaifinka bata tasu kuke ba, duk wadda yace kayi takanshi ne baka zo ba, ba'a saka ka kayi ba'a saka ka daina zakin roba dana sanin mafarauta mugu ɗan gidan mugaye kana mugunta amma kana daɗa suna azzalim baƙin cikin talakawa, kafin ka gama ciwo na ni na gama naka ka saurareni ina dawowa ƙarshen shekaru biyu masu zuwa nan gaba nice maganin tsagerancinka.... Ina faɗin haka ban saurari abinda zaice ba nayi gaba na shige cikin gidanmu da muke haya , tafiya nayi irinta in ka isa wannan ma ka sayeshi.... Murmushin mugunta yayi mai nuni da na gama dake yarinya zaki nemi Dikko ruwa a jallo, juyawa yayi ya koma mota ya fita daga cikin anguwar... Ban daɗe da shigowa gida ba su Nana suka shigo harda ƙawar Amisty wacce muka haɗu da ita police station tayi cikin shege da aurenta, ɗaki suka sameni ina waya da Bello dan tunin duniya na turawa matarshi hotuna anyi tashin hankali na idon duniya kuma shima hankalinshi ya tashi ya yadda zan iya turawa media hotunan, ya yadda zai bayar da kuɗin anjima bayan sallah isha'i. Sannu nayi ma kowa bayan na gama waya nace ku zauna mana, wuri kowa ya samu ya zauna, kallon ƙawar Amisty nayi mai cikin shege sannan nace sannu hajiya, murmushi tayi tare da kallon ƙasa cikin yanayin jin kunya, Ɗan kauda kaina nayi gefe tare da cewa ya akayi da cikin ne ? Ba tare data kalleni ba tace... Wallahi har yanzu bai yadda ba, murmushi nayi tare da cewa bariki da ciki ko goyo wahalalliyar bariki kenan , bariki da tsarin iyali magani ko allura halaka ne saboda baki gwada mahaifarki ba kika tabbatar kina aihuwa ko bakyayi , kallon su Amisty nayi sannan nace tashin farko dai kowa ta nemi gishirinta ta saka a jaka yayin da buƙatar namiji ta gama kammaluwa akanki ki zuba gishiri a bakinki sai ki kora da ruwa, Nana ta tambayeni maganin me ? Kallonta nayi ido cikin ido sannan nace maganin hana ɗaukar ciki, waye ya faɗa miki haka ne ? Murmushi nayi tare da cewa wani feƙaƙƙen dan bariki mai bariki cikin gidan iyayenshi , tunda kuwa har yasan gishiri yana hana ƙaramin ciki zama a cikin mahaifa ai kinsan ya gogu a harkar bariki. Dariya kowa yayi tare da cewa wannan dai ai mugunta ce gishiri ai saida yasa maka cuta , ba tare dana kallesu ba nace shigar wata cutar itace take kore wata, Allah dai yasa mu fita bariki lafiya , kowa ya amsa da amin... Fira dai mukaci gaba dayi daga baya A ` i tace bara suje ita da Saude su anso mukullen shagon da muka kama haya tasan zuwa yanzu sun kammala fenti , sai sun dawo nayi musu suka fita daga ɗakin yayin da Nana da Karima suka fita suma, aka barni dani da Amisty sai Hafsa da ƙawar Amisty matar aure... Kallona Hafsa tayi tare da cewa uwar ɗakinmu idan babu damuwa nikam ina so na tambayeki. Hankalina yana kan wayata ina ganin rubutun da d c o ya turomin nace ina saurarenki yayin dana kanga wayana daidai saitin bakina nace ni aiki nakeyi ko ka kirani a waya, ko kuma kayomin voice note idan na kunna saina saurara , ina faɗa na tura , yayin da Hafsa tace wai miye tsakaninki da DK ? Ajiye waya nayi a gefe na sannan na tattara duk hankalina da natsuwa ta wurin Hafsa nace idan na faɗa miki abinda DK yayi min ke kanki sai kinci ubanshi da yake taƙama dashi yana ma mutane iskanci saboda shi , yau ya taɓo ubana yace talakan babanshi ne , nima kuma na taɓo babanshi a cikin magana na, nuna Amisty nayi tare da cewa duk wanda nace ya faɗamin waye uban Dikko a garin nan ba'a bani amsa idan zaki faɗamin Dikko ko waye ubanshi zan faɗa miki abinda ke tsakani na da Dikko.... Hafsa tace Gwamnan garin nan shine uban Dikko, shiru nayi banyi magana ba Hafsa taci gaba da cewa dole sai kunyi haƙuri sannan kuma kunyi ma Dikko uzuri soyayyar da ake nuna masa a gidansu da yadda ake tsoron mishi faɗa yasa yake ganin duk abinda yayi daidai ne a rayuwarshi , wallahi ba'a dakawa Dikko tsawa ba'a masa kallon banza domin mahaifinshi gani yakeyi kamar duk idan akayi masa zai mutu ne , ya ɗauki soyayyar duniya ya ɗora akan Dikko yana mishi soyayyar da duk duniya babu wanda yake ma irinta a rayuwarshi , fitar da Dikko yake yi da duk wannan iskanci da wulaƙancin da yakeyi ubanshi baisan yana fitowa ba , yasan dai ya baro ɗanshi gida... Cikin jin haushi na kalli Hafsa tare da cewa nikam bazanyi haƙuri ba kuma bazanyi masa uziri ba , can gidansu ya zama dole suyi masa duk abinda kika lissafo amma badai ni ba , wallahi ko Dikko zai mutu saina tozarta shi , saina wulaƙanta mishi rayuwa a garin nan , ki jira zaki ga yanda zanci uban da ya haifi Dikko saina maida shi abun tausayi da kwatance uban nashi kuma duk daren daɗewa saiya gama gwamna ya sauka tunda gidan gwamnati ba gidan ubanshi bane ba... Shiru Hafsa tayi bata sake magana ba , bayan wani lokaci tacewa Amisty ku tashi mu tafi , gaba ɗayansu suka fita tare da cemin sai Allah ya kaimu , ban basu amsa ba na ɗauki wayata naci gaba da abinda ya dameni. Hafsa kuwa kamar ubanta na zaga , tana shiga mota ta fashe da kuka tare da kiran wayar Dikko har ta gaji ta haƙura bai ɗauka wayar ba , daga baya ta yanke shawarar tura masa text duk zagin da nayiwa Dikko komai dana faɗa saida Hafsat ta rubuta ta ƙara da nata dan sharrin ya tafi daidai , bayan ta gama ta tura mishi. Sannan taja motar ta suka bar ƙofar gidanmu... Su Hafsa basu daɗe da tafiya ba su A ` i suka dawo kuma sun tabbatar min cewa shago yayi yanda ake so an tsara shi gwanin burgewa , naji daɗi sosai suma sunyi farin ciki idan Allah ya kaimu gobe lafiya zamu fara fita aiki , saida akayi sallah magrib sannan suka tafi gidajensu. Bayan sallah isha'i kamar yanda Bello yayi alƙawari ya kawo min kuɗi , a gurguje ya bani ya tafi dan yacemin suna da wasa jiranshi akeyi , a daren nakai cikon kuɗi kamar yanda nayi alƙawari zan bayar a gaban shedu aka rubuta takarda aka bani .... Umar ne durƙushe a gaban Dikko cewa mai gida kaga dan Allah tunda kazo gashi har zaka koma gobe don Allah kafin ka tafi ka taimaka ka siya gidan wallahi matar tana buƙatar taimako, Umar yana magana amma hankalin Dikko yana kan saƙon Hafsa , a fili yayi dariya tare da cewa rigima kenan Allah ya baki sa'a akan duk wani kudirin ki akaina An mata , murmushi yayi sannan yace Umar ni babu abinda zanyi da gida , amma nawa ne kuɗin sai in bashi ayi mata aikin... Ba'a mugun sarki sai mugun bafade , kuma wani abu za'a bashi a cikin kuɗin gidan idan an siyar dashi, dan haka ya gyara zama tare da cewa mai gida dan Allah tunda dai yafi so ka siya ka siya ɗin kawai , kila gidan ne ya gaji dashi tunda da taimakon yake so da zaice ka taimaka mishi. Dikko yace tou tunda yanzu yayi maganar siyar da gida ai kowa yasan taimako yake nema insha Allah kafin in tafi zan baka ka bashi , Umar yace mai gida abinda yasa nace ka siya gidan kusa da gidajen daka siya ne kaga idan ka siya sai shima a rushe maka a haɗe wuri ɗaya, Baiyi magana ba sai ƙara kallon text in Hafsa yake yi yana mamakin ɗabi'u irin na An mata da ba gobe zai tafi ba dasai ya ƙara zuwa ya jawota faɗa kuma yanzu dare yayi dasai ya firgito mata hankali , lallai zai haƙura ya riƙa waya da Hafsa dole kodan dan ya riƙa jin halin da Sultana take ciki. Umar yace mai gida kayi shiru baka ce komai ba , kallonshi Dikko yayi tare da ajiye wayar shi gefenshi yace wato so kake in ƙara baƙin jini ko ? Cikin rashin fahimta Umar yace wurin wa zakayi baƙin jinin ne ? Ajiyar zuciya Dikko yayi tare da kwantar da bayanshi jikin kujera lumshe idanuwanshi yayi cikin shauƙi sannan yace wai An mata ne tace zataji min mutunci bayan shekaru biyu masu zuwa, Ya ƙarasa maganar yana murmushi , Umar yace haba ranka ya daɗe ina ma zata ganka ? Kafin shekaru biyun masu zuwa kayi mata tazarrar da baza ta sake ganinka ba har abadan duniya , kai babbar ƙaddara ce da kayi nisa da tazara ga duk wani ɗan ƙaramin sakarai , ka siya gidan kawai ka manta da sha'aninta me zata iya maka ne ? Buɗe idonshi yayi tare da cewa baza ta iya min komai ba kuma badan inajin tsoron tayimin ba kawai dai tana bani tausayi ne... Umar yace bata da kunya ta raina hankalin mutane ka daina tausayinta shegiyar kanta ce , Dikko yace ba itace shegiya ba nine shegen barni dai da Dikko take wasan , zan bada kuɗin gidan na siya , wani irin farin ciki Umar yayi tare dayi ma Dikko godiya saida ya koɗashi sosai sannan ya fita, Fitar Umar Dikko ya ɗauki waya ya turawa Hafsa saƙo cewa shifa baima gane yarinyar da take magana ba , tayi masa bayani na yadda ya sani ta tuno masa asibiti da dai duk wani abu daya shiga tsakanina dashi Dikko yace sam bai ganoni ba amma idan tana da hotona ta tura mishi , Hafsa tace bata da hotona amma zamu haɗu da safe insha Allah zata ɗauko masa ni ya kwantar da hankalinshi , Dikko yace ai dama hankalinshi a kwance yake amma ya zama lallai zai koyamin hankali , Tunda gari ya waye muka sha gayunmu kamar yanda muka tsara , motoci biyu aka ajiye a ƙofar gidanmu ɗaya ta Hafsa ɗayar kuma tawa ce sai kenap ɗaya wacce "yan dabana zasu riƙa amfani da ita kuma ni na siyi , Dukanmu a ƙofar gida muka fito , muna ƙoƙarin shiga mota mai gidanmu da muke haya yazo bayan mun gaisa yace ya siyar da gidan nan saboda haka duk abinda muke so zuwa jibi mu kwashe kayanmu, Cikin ɓacin rai nace wai miya sa kuke abu babu adalci a rayuwarku ? Kai kuma nawa ya baka ya siyi gidan dan nasan za'ayi haka tunda har yaga gidan dana shiga nasan wallahi saiya siya , sakaran banza matsiyaci dashi tou idan ka ganshi ka faɗa mishi nayi gidan zama idan yanajin shi wani mai kuɗine yazo ya sayi anguwar nan duka... Ina faɗin haka nace ku shige muje , gaba ɗayanmu kowa ya shiga mota , Hafsa ta tuƙa nata , tawa kuma driver na samu saboda har yanzu ban iya mota ba , zugar daba ina kuwa suka shiga napep muka tafi, ashe duk abinda na faɗa Hafsa vidio tamin ta turawa Dikko dan ya gani da idonshi ya kuma ji ina faɗa da bakina , ni kuma bansan anyi ba tasan idan ya gani da idonshi dai zaici mutunci na yadda ya kamata bansan abinda ke cekin zuciyar Hafsa akaina ba... 28/08/2019 *JAMILA MUSA* 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 21 Cikin farin ciki muka isa bakin shagonmu wanda yasha fenti kuma aka gwagwaɗa masa tambarin *kwarata* , tsayuwarmu da fitowarmu shine ya jawo hankalin al'umma masu wuce da wanda suke zaune saboda munzo da sabuwar shiga mai matuƙar bada al'ajabi a karon farko da ta zama abin kallo ga jama'an gari... Takardun da aka gurzo wanda yake ɗauke da tallar karuwancin mu nasa "yan daba suka raba titi biyu duk motar da zata wuce aka ci gaba da basu babu sauƙi babu sauƙaƙawa ! Bakin shago mu mata muka koma muka jera layi amma babu wacce ta zauna tsaye muke , Nana da Karima suna daga gefe suna kallon ikon Allah , Waya Hafsat ta fiddo ta fara latse latse daga baya kuma sai naga ta koma gefe guda tana waya , ta ɗauki tsawon lokaci bata gama wayar ba haka nan kawai naji na tsargu da wayar , bayan ta gama sai ta goge number data kira... Ƙurawa Hafsa ido nayi harsai data kama kanta , tabbas akwai cuta a tare da rayuwar Hafsa akwai abinda take shiryawa ko kuma take so ta aikata idan kuwa na ganota da wani laifi na cin amana babu abinda zai hana na tona mata asiri, Yana gama waya da Hafsa ya buɗe saƙon da tace ta turo mishi , ɗan soɓaro baki yayi irin na sakatattun "ya "ya sannan ya cire vidio ya ɓoyeshi a gellery vault bayan ya gama gani... Saman kujera ya zauna ya saka takalmi har yanzu bakinshi a soɓare yake , saida ya gama sannan ya kalli Al ' Ameen yace mu fara zuwa ta wurin An manta sannan mu wuce don Allah , Al ' Ameen yace mai gida da Allah ka fita hanyar yarinyar nan , murmushin Dikko yayi sannan yace wallahi sai anje idan baza kuje ba sai ku jirani ina dawowa , yana faɗin haka yayi gaba , Al ' Ameen biyo bayanshi yayi ƙaramin yaron daya girma kawai zai riƙa juya su dandai suna ƙasansu... Da sauri ya wuce Dikko ya buɗe mota , ɗan ɓata rai Dikko yayi sannan ya shiga ya zauna tare da kwantar da bayanshi saman lallausan kujeran motar , wayarshi ya ciro yayi mata kyakkyawan riƙo da duka hannayen shi biyu , sannan ya ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya yake faɗawa Hafsat yana zuwa yanzu babu daɗe wa zaizo mata bankwana ! Wata irin kururuwa Hafsa tayi ta farin ciki sannan ta koma motarta da gudu , ƙara barbaɗa powder tayi tare da ƙara shafa turare sosai , sannan ta gyara ɗaurin kallabinta ta fito... Kallon mamaki nake ta bin Hafsa dashi anya yarinyar nan bazan zameta daga harkata ba ? Tafiyar nan kuwa zata tafi kodai in fita inyi harkata ni ɗaya ? Ina wannan tunanin zuƙa zuƙan motocin Dikko sukayi parking a ƙofar shagon mu... Cikin rawar kai Hafsa ta tashi tayi wurin motar Dikko , ƙafarshi ya ɗora saman murfin motar , kafin Hafsa ta isa wurin ya zura hannunshi aljihu ya ciro cingom , a daidai lokacin da Hafsat ta isa wurin motar , ko inda take bai kalla ba ya cire cingom inshi a cikin takaddar shi , Tahowa ya farayi zuwa wurina tare da ɗora cingom in saman "yan yatsunshi na hannun haggu ya daki tafin hannunshi na haggu da hannun shi na dama , buɗe bakishi yayi cingom in yayi tsalle ya shige , Ɗan tsuke bakinshi yayi kamar zaiyi kiss sannan ya lumshe idanuwanshi tare da nuna yanayin kamar abin harin sumbatar nashi yana kusa dashi , muah ya saki kiss a daidai lokacin daya tsaya gabana yaja kujerar rober ya zauna , sai yanzu ya fara tauna cingom ɗin cikin izza da nuna shi wani isashshe ne , ɗago ƙafarshi yayi ya biyo da ita ta saitin fuskata kamar zai takamin fuska naɗan ja baya , murmushi yayi tare da ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya :• Robar ruwa Al ' Ameen ya miƙowa Dikko bayan ya zauna , ɓalle murfin robar ruwan yayi yakai bakinshi yana kallona , shan ruwan yayi sannan ya cika bakinshi dashi ya miƙawa Al ' Ameen robar ruwan , murmushi yayi da gefen bakinshi sannan ya fara bultso ruwan daga bakinshi suna watsowa saman fuskata... Ƙoƙarin tashi na farayi dan banda lokacin Dikko a yanzu sai bayan shekarun dana iba , ina ƙoƙarin tashi ya maidar dani ya zaunar da ƙafarshi nayi na tashi na kasa saida ya gama watsa min ruwan sannan na buɗe idona daya cika da hawaye na kalleshi , Murmushi yayi sannan yayi magana cikin sigar lallashi haba ke ko an mata komai saurin kuka ke baki san wasa ba ? Karfa ki ɗauki abin da zafi albarka na saka miki , kin zageni tass amma zagin yamin daɗi bayan shekaru biyu idan muka fara farautar juna a ranar zaki gane Dikko ba zakin roba bane , zakin gaske ne farin ciki mafarauta , maganar dana faɗa mishi jiya, cewa zakin roba dana sanin mafarauta, ci gaba yayi dacewa dani dake duk wanda ya fasa , ya jinjina kainshi tare da nunani da hannu , Tura kujerar da nake zaune yayi da ƙarfi da bango bai tareni ba babu abinda zai hanani faɗuwa , Al ' Ameen ya kira da sauri yazo tare da miƙo mishi wata "yar ƙaramar jaka tashi yayi ya duƙo kusa dani sosai lumfashin shi yana sauka saman jikina , saman jikina ya ɗora tare da cewa ga cingom nan zai isheki amfani daga nan har zuwa lokacin da zamu fara wasa , ɗan taɓe baki yayi tare da kallon wani wuri daban sannan ya juyo ya kalleni da magana zaiyi kawai sai fasa... Miƙewa yayi ya juya ba tare daya sake cewa komai ba , bayanshi Hafsa tabi saida ya shiga mota ya zauna sannan yasa Al ' Ameen yayi rabon kuɗi wa duk wanda muke tare dashi har "yan dabana saida Dikko yasa aka basu kuɗi amma nidai bai bani ba kuma ban damu ba saboda dama ni basu nake jira ba ! Al ' Ameen yana gama rabon kuɗi ya koma mota , har yanzu Dikko ni yake kallo gilashin saitin shi Al ' Ameen ya ɗage zuwa sama sakamakon da yake ƙasa , bai daina kallona ba har Al ' Ameen yaja motar suka tafi , Goge fuska ta nayi da hannu na , sannan na buɗe jakar da Dikko ya ajiye a gabana , irin cimgom in da yake amfani dashi ne sai farar takarda da akayi rubutu a samanta , suke nan a cikin "yar jakar , ban buƙatar dubawa sabona nasan gani kawai zanyi bazan iya karantawa ba, kuma babu wanda zan ba ya karanta min saƙon Dikko daga nan har lokacin da zan iya karantawa da rubutawa.... Tunda Dikko yayi min wannan wulaƙancin ban sake magana ba har aka gama raba takardunmu muka koma gida ban sake magana da kowa ba , kuma tunda nayi wanka na shiga ɗaki ban sake fitowa ba saida gari ya waye ' Bayan na gama duk abinda nakeyi na fito tsakar gida na zauna saboda ba yau zamu fara fita ba sai an fara kira a waya lokacin zamu tabbatar da cewa tallarmu ta samu karɓuwa a wurin jama'an gari, Nana na gani riƙe da kwalar rigar mijinta tana zazzaga jikinta irin abin nan da yara keyi idan suna faɗa , zama nayi ba tare dana kalli inda suke ba amma hankali na da kunnuwa na suna wurin su , wallahi sai ka sakeni kalmar da naji ta fito daga bakin Nana kenan kuma har yanzu bata saki rigar mijin ba. Audu yace ba ƙin sakinki zanyi ba amma sai kin faɗamin abinda nayi miki wanda yasa kike so na sakeki ! Nana tace lallai bama ka da kunya da har kake tambayar abinda kayi , tou na gaji da zaman cida kaina zaman wahala zaman kunci kullin muna can barbaɗe kayanmu a saman kai bama ƙerau bama sabuwar anguwa zama gidan haya , tou wannan aure dai a sahalewa juna uban kowa ya huta... Daga inda nake zaune nace Audu wai duk meya haɗaku ne wai ? Ku kullum faɗa ke Nana kamar kece kaɗai matar aure a gidan nan ? Duk wadda kika gani da mijinta haƙuri takeyi ko suna wani saɓani basa fitowa tsakar gida ke kullum dake da mijinki kamar abokan faɗa ? Gaskiya ki daina wannan rayuwar kece ƙasan Audu dole sai kin kiyaye idan har kina san ganin daidai a rayuwarki. Sakar mishi riga kizo kiji wata magana, babu musu ta sake rigar mijinta ta taho wurina, shi kuma Audu fita yayi ba tare daya sake cewa komai ba, A ƙofar gida kuwa A ` i ce ta tare Audu bayan gaisuwa tace mishi naji shiru ya kamata kayi wani abu don Allah , zama Audu yayi a saman dakali sannan yace ki ƙara haƙuri , murmushi A ` i tayi tare da cewa ba komai Allah ya tsare ya dafa maka akan duk lamuranka , da amin ya amsa sannan ya wuce ita kuma ta shigo cikin gidanmu... A ƙofar ɗakina A ` i ta samemu ina bawa Nana shawara , amma tana zuwa gaba ɗaya ta jagula komai ta ida firgita Nana har na kasa gano gabanta bare bayanta, Ajiyar zuciya nayi tare da bin A ` i da kallo ban sake magana ba ina dai jinta tana ta ɗora Nana a hanyar banza ita kuma tana ta karɓewa dan a ganinta shawarar A ` i itace mafita a gareta , Ƙawar Amisty da tayi ciki suka shigo da sallama ita da wata mata , inda nake zaune suka nufo gaisawa sukayi dasu Nana sannan sukace wurinki muka zo , miƙewa nayi tare da cewa ku shigo na faɗi maganar tare dayin gaba suka biyo bayana ! Wurin zama na basu sannan nima na zauna muka gaisa , bayan gaisuwa ƙawar Amisty tace Sultana kin ganeni kuwa ? Murmushi nayi ban bata amsa ba , taci gaba da cewa idan da hali nima zan shiga ƙungiyarki , ga ƙawata itama zata shiga, kallo nabi su dashi bayan wani lokaci nace ita ƙawar taki tana da aure ne ? Dukanmu matan aure ne , Ni suna na Fadeela inji ƙawar Amisty mai cikin shege , sai kuma ta nuna ƙawar da suka zo tare tace ita kuma sunan ta Zalifa , saida na ƙara kallesu tsaf sannan nace miye dalilinku na shiga wannan ƙungiya ... ? Wacce aka kira da Zalifa tace wato ina da wata damuwa ce ta musamman wacce bazan iya biyanta ba ko cika burina ba dole saina shiga wannan ƙungiya mai albarka , ina so na samu goyon baya da taimakon tantiran dake cikin wannan ƙungiya , Murmushi nayi sannan nace wannan wace irin damuwa ce ? Gyara zama Zalifa tayi tare da cewa wato ina da wata maƙociya wacce na ɗauki amana da yadda na bata , bana ɓoye mata sirrina ko kaɗan . Wata rana ta shigo gidana sai taji muna hayaniya da mijina , bayan mun gama mijina ya fita sai take tambayana abinda ya haɗamu , ban ɓoye mata ba kamar yadda na saba na kwashe komai na faɗa mata , Na ƙara da cewa bansan abinda nayi masa ba duk abinda bai taka kara ya ƙarya ba sai yayi ta faɗa akanshi wani lokaci ma hada duka , sai tacemin yadda Allah ya halittani da kyakkyawar siga mai burgewa na kashe aurena zan samu wanda yafi mijina , Nuna mata nayi cewa bana iya kashe aure na amma zan haƙura gaskiya na zauna dashi a haka tunda ina sansa wata rana zai gaji ya daina , sai tacemin ai sai anbar zomo yake zama guza , mazan yanzu da asiri ake ladaftar dasu in bada kuɗi taje ta nemo min asiri inyi maganin mijina. Banji wani komai ba na bata kuɗi masu yawa dan tacemin itama mijinta da yake mata biyayya malamin yayi mata maganinshi , kuma naga yadda mijinta yake mata biyayya sosai kuma yanajin shakkunta dan haka na bata kuɗin nima a samomin asirin in riƙa dawwara mijina... Haka kuwa akayi tayi ta kawo magani ina barbaɗawa mijina a abinci ina zuba mishi a ruwan wanka da abin sha laya ƙarƙashin filo wasu layun a ƙarƙashin gadonshi , tunda safe kafin ya fita na kunna hayaƙi , shirka dai iri iri da ƙazanta nayi ta barbaɗawa mijina yana lashe wa , Haka tayi tamin wayau tana karɓemin kuɗaɗe , murmushi tayi tare da cewa kinsan me ya faru ? Nace mata A , a, tace kwasam sai ta tayar da fitina wa mijinta da yake aurenta , kuma yanayi mata wani irin azababben so yana ƙaunarta fiye da duk yanda zan faɗa muku , amma saida ta kunno masifa ya saketa , har wannan lokaci bata daina kawomin asiri ba , A daren ranar data kawomin magani na zubawa mijina a abinci yana gama ci babu laifin zaune babu na tsaye ya gwagwaɗamin saki 3 ita kuma ta aure min miji gani nan na fito bani ga tsintsu bani ga tarko kinji hukuncin da tayi min.... Murmushi nayi kaɗan sannan nace kin aihu da mijin ne ? Tacemin a , a , nace ita ubanta yana raye ne ? Tace min Eh nace ya yanayin samunshi yake ? Tace babu laifi gaskiya yana da rufin asiri , da kyau nace tare da cewa mijinki kina san ki koma gidanshi ko kuwa ya kike so ? Zalifa tace gaskiya bazan koma ba so nake kawai ku riƙe mishi wuya ku jawo shi a cikin ƙungiyarku ku ƙare duk wani tattalin arziƙinshi babu asiri Sultana ki fitar min ita daga gidan... Jinjina kai nayi tare da cewa ni bana asiri amma sharrina da kaidina yafi asiri bala'e a rayuwar ɗan adam , waya na bata tare da cewa sakamin lambar mijinki ki ajiye min ita da lamba 4 , ansa tayi ta sakamin tayi saving kamar yanda nace , bayan ta dawomin da wayana nace babanta a wane anguwa yake ne ? Zalifa tacemin gaskiya bai cika zama ba , nace to karki damu zai zauna dan dole ki samo numbershi ni kuma nayi miki alƙawari su dukansu zamuyi musu aiki ... Zalifa tacemin ina da motar hawa idan zakuyi amfani da ita , nace tou yayi kyau mun gode , jakarta ta buɗe ta fiddo kuɗi har naira dubu ɗari ukku tace gashi taba ƙungiya tata gudumawar , godiya nayi tare da ƙwalawa A ` i kira nace ta kawo musu form su cika , Zalifa tace karki damu zan cika anjima idan muka dawo akwai inda zanje yanzu , nace tou babu damuwa sai kun dawo... Miƙewa sukayi zasu tafi nabi bayansu dan rakiya amma ban wuce ƙofar ɗakina ba , anan na tsaya nayi musu addu'ar sauka lafiya , bayan sun fita na koma ɗaki naci gaba da "yan hididdumu na , na tattara kaya saboda zamu tashi daga gidan yau zuwa sabon gidan da na siya , kuma duk nace matan gidan subini mu koma gidana da na siya , sauran ɗakunan da suka rage zan nemo "yan gidanmu na tattara su wuri ɗaya hadashi gogon wato Babana dan nafi so nayi karuwanci a gaban idonshi ya gane cewa ba'ayiwa iskanci haye.... 29/08/2019 *JAMILA MUSA ...* 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 22 Saida na tattara duk wani abu da nasan ina buƙata na adana shi a ma'adar da nasan bazai wulaƙantu ba , ko wace macen da zamu koma da ita gidan nice nasa aka kwashe kayan kowa aka kai gidan da zamu koma da zama... Kafin azahar har mun gama saboda babu mai gado a cikinsu duk dai katifa ne kuma babu macen dake da ledar tsakar ɗaki saini ! Saida na tabbatar an ajiye komai a mazaunin daya kamata , sannan na shiga wanka , kafin in fito an share gidan ƙwal gwanin burgewa , Hafsa tazo sai kashe sulfie sukeyi ita da sauran jama'ar tamu , Ina fitowa daga wanka tace uwar room maza ki shirya kizo ayi dake kar a baki labari , Amisty ce tace babu wani uwar room uwarmu ce gaskiya a wani cire room kawai mu kirata da mother , shewa sukayi dukansu lokaci ɗaya suna cewa uwa... "Yar gajeriyar dariya nayi cikin sigar barikanci na wuce ɗakina banyi musu magana ba , hotuna sukaci gaba dayi har na gama shiryawa nima na fito ! Ina fitowa suka ɗauki sowa domin sun san mother tasu ba daga baya ba wurin iya ɗaukar wanka , banje koya ba kuma babu wanda ya ɗorani nice na koya dakai na kuma ni na ɗaura kaina , banda uwar ɗaki nice uwar ɗakin kaina kuma nice uwar ɗakin wasu , Amisty ce ta bani kujerar roba na zauna, da "yan daba da duk wata kwartuwa mun hallara wurin, bayani na farayi musu kamar yadda muka saba a duk lokacin da muka zauna... Hafsa kuwa ciro wayarta tayi ta faramin vidio kamar yadda naga ta koya kwanakin nan, saboda haka sai nayi shiru yayin da su Amisty suka ci gaba da goga bayani tare da ƙara ƙwarara wa kowa guiwar shi a cikin harkar bariki ! Komai ɓaro ɓaro sukeyi suna sakin maganganu yadda harshen kowa yake iya furtawa, Hafsa kuwa abinda yasa banyi mata magana ba na lura da halayyarta tana da saurin hasala sannan kuma tana da ɗauka da ajiyewa , na ukku kuma abinda na lura da ɗabi'ar ta zatayi tonan asiri haka kuma zatayi cin amana zata tona asirin wanda suke tare idan suka rabu ... Ni kuma banda haƙuri idan abu ya ɓatamin rai saina bigi mutum nake samun natsuwa , tou zan ƙyale Hafsa amma nasan irin zaman da zanyi da ita , sannan nikam dai sirri na ƙarya takeyi taji shi kuma anƙi a rabun da ita dan idan har na rabu da Hafsa zata yankamin ƙunya biyu dani da "yan team inta zamu zama abokan hamayya , kuma babu abinda zai hana asirce asirice saboda su sun ta allaƙa da malam tsibbu amma maganinta ɗaya shine zan sace wayarta ta ɓace kwata kwata babu layi babu wayar bare kuma tabi tsohon tarihin jerin kira ta samu wasu lambobi, idan taƙamarta sabko tabbas ni a wurin na kwana , Har aka gama zaman ban sake cewa umm umm ba, bayan an gama duk suka zagayeni akayi ta hotuna , duk wanda yaga hotunanmu yasan ni iskanci na ya fita daban a cikin nasu, yadda suka bani shugabar iskanci tabbas iskanci ya fito a tattare dani... Bayan an gama hotuna muka fito ƙofar gida , saman motar Hafsa nayi tsalle na haye , Hafsa tace bari in ƙara ɗaukarki hoto murmushi nayi tare da cewa ngode , ɗaukana tayi nanma kowa ya ƙara yayyaɓeni sai an mana maza da mata duka Hafsa taci gaba da bamu filasha ! Saida ta gaji da ɗauka sannan mukayi sallama da ita , ta wuce gidansu mu kuma muka koma namu gida , dukanmu a ɗakina muka sauka , har dare suna nan domin Amisty zata kwana wurina ne kuma ma dai ta dawo wurina da zama kwata kwata... Bansan abinda yasa ba kuma ban tambayeta dalili ba , sai dare sosai su A ` i suka tafi gida , Nana da Karima kowa ya shige ɗakinshi muka rage daga ni sai Amisty, addu'a nayi na kwanta bacci , A ɓangaren Hafsa kuwa dan ta wulaƙanta ni ta tozarni a idon Dikko idan ina da sauran mutunci ko ƙima ta kakkaɓe a wurin shi , duk hotunan data ɗauka gaba ɗaya ta tura mishi su , da vidio maganar dana fara da kalaman batsar dasu Amisty sukayi , da kirana da uwar gidan kwarata da akeyi duk saida ta bawa Dikko labari bayan ta gama tura hotunan da vidio ', Idan ran Dikko yayi dubu saida ya ɓaci amma bai nunawa Hafsa ba ranshi yayi mishi babu daɗi ba dan baiyi tunanin irin wannan hotunan zata riƙa kawo mishi ba , kawai dai ya ɗauka hotunan Sultana zata turo sai kuma idan tana zaginshi sune kaɗai zata faɗa , amma wannan vidio ya girmi ganin idanuwanshi maganganun sun girmi jin kunnuwanshi , Tabbas zai takawa Hafsa burki da irin wannan vidio kuma zai tsawatar da ita zai gwalashe abun idan ba haka ba irin wannan vidion na An mata zasuyi ta yawo a social media shi kuma idan har haka ya faru baiji daɗi ba, Tunani dai barkatai a zuciyarshi , amma ranshi da zuciyarshi yafi bashi cewa kayi mata magana gaskiya shekaru biyu idan suka tafi a haka kaga zakayi takon saƙa da karuwa mutuncinka martabarka da ƙimarka zai zube a wurin al'umma ga siyasa bata raina abun magana, sai ka tsaya takara zaka gane abun ya zama shirme, shawarar da zuciyarshi ta yanke shine ya fita daga harkar taron yara don asali nasaba da mutunci gidansu ba iri ɗaya ne dana gidansu Sultana ba. Burun duniya akan shi ɗaya tal mahaifinshi ya dogara yayi tsayuwar arfa wurin ganin ya zama mutumin kirki ya fito cikakkan mutum ya kashe kuɗaɗe da yawa wurin ganin ya tsaida ni a saman ƙafafuwana , mutane suna cewa duk "ya "yan da aka ɗauki soyayyar duniya aka ɗora musu gurɓatacci ne , mafiya yawansu basu da tarbiyya , ni kam ba lalatacce bane domin idan nayi duba da yadda nazo... Tsoki yayi tare da kiran Hafsa yayi mata tatas yace daga ita harma Sultana duk zaici mutunci su bayasan maganar Sultana haka kuma itama bayasan ta sake shiga sabgarshi ko kiranshi ta sakeyi ko text wallahi sai yasa an kulle mishi ita , yafa ci uban Hafsa sosai ya ƙara da cewa itama Sultanar ta sake ambatar sunanshi wallahi zaici ubanta ne, saida ya tata iskanci mai isarshi ya kashe wayarshi, Al ' Ameen yace mai gida lafiyarka kake ta faɗa , idanuwa jajir Dikko yace Al ' Ameen idan aka ce maka na taɓa zina tsakaninka da Allah zaka yadda ? Al ' Ameen yace mema yasa kake faɗar wannan maganar don Allah ka daina abinda ma bazai taɓa yuwuwa bane ba... Idon Dikko cike da hawaye yace kasan yarinyar dana shaƙe a asibiti ? Al' Ameen yace Eh nasanta mai gida , Dikko yace kaga ai yarinya ce sosai ko ? Al ' Ameen yace Eh , Dikko yace wallahi da nayi auren wuri ina iya haifar yarinyar nan , amma tsautsayi da ƙaddara yasa na saki wani irin ƙatoton layin da inaji kamar in cakawa kaina wuƙa in mutu kawai in huta, Murmushi Al ' Ameen yayi tare da cewa haba mai gida ina kai ina haifo mai shekarun yarinyar nan , da kayi aure kam da wuri baka tsaya karatu ba kuma gashi har yanzu duniyar nemanta akeyi duk wanda kuɗi yayi ma yawa so kawai yake a kirashi ranka ya daɗe , duk dai haka gaskiya baka haifi yarinyar nan ba , tsoki Dikko yayi tare da ɗaukar wayoyinshi ya shige ciki , gefen gado ya zauna tare da zagba tagumi ya fara tuno wa kanshi ko shiɗin waye..... *_WAYE DIKKO...?_* Dikko Umar Kurabau shine cikaken suna na... Mu cikakkin asalin "yan cikin garin katsina ne , bamuyi rayuwa a ƙauyen kurabau ba haka mahaifina da kakana basu rayuwa a wannan ƙauye ba , amma kakan dadyna shine yayi rayuwa a cikin wannan ƙauye dake ƙarƙashin kauyen rimi local government... Mutane ne masu cikakken arziƙi da wayewa kuma sarautar kauyen a gidansu kakana take wacce suka gada suma tun iyaye da kakanni , ko a wancan lokacin mutanen kurabawa tuni su wayayyu ne kuma tuni suka waye da ilimin zamani ! Kakan dady na duk da yake bakauye baya da kidadanci haka kuma bashi da jahilci , wayyen tsoho ne da yasan rayuwa , kuma tsohone mai cikakken ilimin addini, Abinda ya kawo kakana cikin birni shine neman ilimin zamani , kuma shima mahaifinshi shine mutumin daya fiddoshi dan neman ilimi bayan ya tabbatar daya haddace al'kur ani mai girma a saman kanshi kuma yasan littafai na musulinci . Karatun boko bai wani bashi wahala ba saboda yana da ilimin addini sosai , saida kakana ya gama karatun sikandire sukul { Secondry school } ya koma kauyen kurabau, Mahaifinshi yace tunda ya ɗagawa ƙauyen na wasu shekaru ya haƙura kawai ya koma cikin garin da zama , dan a samu ci gaban rayuwa ! Mahaifinshi da kanshi yazo ya nema mishi wurin zama sannan ya bashi kuɗaɗe ya kama kasuwanci ya nemi abinda zai dogara da kanshi, dan a wancan lokacin idan mutum yayi secondry sch anan yake tsaya dan duk wanda yazo wannan matakin gani ake an ƙure. Allah kuwa ya saka ma nemanshi albarka dan kano yake zuwa sarin atamfofi da shaddoji da yadika ,kafin shekar ya zagayo abubuwa sun fara canzawa domin Allah yasa ma neman albarka kuma Allahn ya yaddar mishi ! Dan ubangiji dayace maka zama zaka zama.... Haka rayuwa taci gaba da tafiya cikin ƙanƙanin lokaci sunan Dikko Muhammad wato kakana ya fara zagawa a cikim garin katsina dan zuwa wannan lokaci ya baza yara suna neman mishi kuɗi dan kasuwar tafi ƙarfin mutum yanzu, kuma mutum ne shi mai kauta , Shi kuwa Muhammad baban Dikko wato kakan babana ganin dukiya ta fara yawa hankalinshi ya fara tashi gashi har yanzu Dikko baiyi auren farko ba , kuma zuwa wannan lokaci ya rage zuwa gida dan sai yayi wata shidda ko fiye da haka baije gida ba , idan yaje malam yayi mishi magana yana daɗewa baizo ganin gida ba sai yace abubuwa sunyi yawa yanzu ma dakel ya samu yazo, Ganin haka yasa malam ya yanke shawara aura wa Dikko mata kuma "yar nan cikin ƙauyensu dan malam yace idan "yar gida ce yake aure dole za'a riƙa ganinshi ko baizo dansu ba zaizo dan matarshi, Haka kuwa akayi malam ya aurowa Dikko mata bada saninsa ba yasa aka kawo mishi amarya har katsina, saida aka kawo amarya akayi masa bayani malam ya auro masa ita , bai wani ji komai ba yace Allah ya basu zaman lafiya, Zaman lafiya sukeyi da matarshi Binta saboda matace mai haƙuri da kuma kauda kai da duk wani abu na rayuwa , saboda itama sai tayi wata nawa bata ga Dikko ba dan shi ba auren yake saurare ba duniyar kawai yake nema ita kuma Binta bata wani damu ba tunda ci da sha har sutura bata rasa ba , idan Dikko yazo mata as miji zasuyi rayuwar aure idan baizo ba babu abinda ya dameta... Haka dai rayuwarsu taci gaba da tafiya , kuɗin Dikko kuma har an fara zarginsu a cikin gari cewa tsafi yake yi , dan shima kanshi zuwa yanzu baisan iyakar abinda ya mallaka ba , koda Binta ta samu ciki gida Dikko ya maida ita ta aihu , tunda ya kaita bai sake komawa ba har ta aihu ta gama wanka baije ba, abinda ta aifa ma bai gani ba babanshi yayi duk abinda akeyi ma duk macen data aihu komai anma Binta da ɗanta da yaci suna Ummar wato mahaifina... Har Umar ya iya tafiya Dikko bai dawo ba kuma bai aiko ba yana can yana neman duniyarshi danshi matan ma basu ne gabanshi ba kuɗi kawai, baisan komai ba kuma baya gane komai sai naira , abun ƙauye aka fara tira iyayen Binta su kashe auren su mayar da Baban Dikko ɗansu tunda dai ɗanshi ya zama ɗan iska, Binta kuwa ta kifa kanta ƙasa tace ita duk duniya babu wanda ya isa ya kashe mata aure, Ganin za'a kashe mata aure dole yasa ta saɓe abunta ta dawo wurin mijinta , koda Dikko ya dawo gida ya sameta yaji daɗin dawowanta yace tayi haƙuri abubuwa ne sunka sha mishi kai da yawa da yawa shi yasa baizo ba , tace ba komai da yake itama bata da matsala. Can ƙauye kuwa da aka tabbatar da Binta ta koma wurin Dikko iyayenta sunsha zagi da tirr da Allah wadai da halin ɗiyarsu, basu da yadda zasuyi tunda suma basu san Binta zata koma wurin Dikko ba dan batayi shawara dasu ba ta tafi. Tun lokacin da Binta ta dawo wani abu bai shiga tsakaninta da Dikko ba , ita kanta wahalar gani yake mata dan yanzu kasuwancin nashi ya fara ketarawa , kuma babu damar taje ta faɗa gida dan tun abun baya damunta yanzu harya fara damunta. Yau kam ta hana idonta bacci ko Dikko zai kai safiya bai dawo ba zata jirashi kuma yau za'ayita ta ƙare , koda Dikko ya dawo gida daɗin bakin yayi ma Binta kuma ta haƙura amma kam a daren nan sunɗan caskaɗe dan tunda ta dawo wannan shine haɗuwarsu na farko, Tou haka kwanciyar auren ta koma duk lokacin da Dikko ya kwanta da binta wani rantsetstsen rabo zai fita , adadin yawan "ya "yansu adadin yanda Dikko ya kwanta da ita , yanzu tayi yara bakwai , Kuma rabonshi da gida tunda ya maida Binta aihuwar Babana bai sake zuwa ba har Binta tayi "ya "ya bakwai , saida itace kaɗai take zuwa, mahaifin Dikko kuwa yayi danasanin kai Dikko birni , Haka rayuwar taci gaba da tafiya saida malam ya rasu Dikko yaje ƙaunye ta'aziyya, mahaifiyarshi kuma tayi kuka da tir da rayuwar birni, da yake shegen wayau ne dashi lallashinta yayi saida ya kwantar mata da hankalinta sannan yace tunda bata da komai a ƙauye zai tafi da ita birni ! Haka kuwa akayi bayan addu'an bakwai suka tattaro suka dawo tare da kakar babana, zaman kakarsu dady ta gano Dikko bata mace yake ba , ta jinjina wa Binta da wannan haƙuri, ita dai batace komai ba tana dai kallon ikon Allah.. Ummar wato Dadyna, yana gama secondry sch Dikko ya korashi ƙasar waje karatu dan bayasan ganin yara kusa dashi, tafiyar Ummar babu daɗewa kaka Dikko ya tsirawa kanshi aure rana guda aka kawo mishi mata biyu shi mai kuɗi, idan an haɗa da binta sun zama 3 kenan. Nan fa haihuwar gasa ta tashi mata sunga kuɗi duk shekara sai an direwa Dikko "ya "ya amma banda Binta dan ita tana mamakin ma yaushe Dikko yake kwanciya dasu sakamakon ita ? Ko kuwa dandai su shine ya auro su da kanshi Oho, Tunda Dady ya tafi karatu Kaka Dikko ya hanashi dawowa , da yaga mai zai matsa mishi saiya dawo ya tusheshi da kasuwa can yace ya nemi kuɗi ya manta da rayuwar nigeria shima haka babanshi yayi mishi. Duk da Ummar yana ɗan farko saida Binta tayi magana a maido mata ɗanta karya halaka cikin duniya , Dikko yace bazai maido ba, shi ya akayi bai ɓace ba da babanshi ya kawoshi birni, dole Binta ta haƙura ta dainawa Dikko maganar Ummar , itama kakar Dady tayi harta gaji Dikko bai dawo da Ummar ba, Kwanci tashi asarar mai rai , abubuwa da dama sun faru a ciki kuwa hada rasuwar Kakar Dady , Dady kuma yayi shekaru kusan 15 yana ƙasashen yahudawa, tun yana marmarin gida shima harya goge ya janye zance gida a rayuwarshi. Shi kuwa Dikko yanzu hankalinshi ya tashi saboda mata sun tara tulin ɗiya sai meeting ɗin kasheshi sukeyi su kwashi dukiya , wannan dalili yasa ya cire Binta a gidan ya sake mata mazauni ita kaɗai daga ita sai "ya "yanta dan ya lura itace kaɗai take masa san tsakani da Allah. Tou wannan dalili ne yasashi ya ɓanɓako dady daga ƙasar waje shi kuma zuwa wannan lokaci baya san dawowa nigeria dan shima ya riga ya kafa kanshi a can yayi kuɗi wanda saida suka tadawa Dikko hankali duk neman duniyarshi, yace Ummar da nasan zakayi kuɗi duniya da na zauna na mori rayuwata ban ba kaina wahala wurin tara abun duniya ba, Dikko dai bai ɓoyewa Ummar komai ba ya sanar dashi cewa mata zaku kasheshi su gaji duk dukiyar daya sha wahala wurin tarawa , dan haka abinda Dikko yayi shine , duk abinda ya mallaka tsakanin gidaje filaye motoci filazozoji Dikko ya kasasu 10 ya bawa Ummar kashi 9 sannan yayi rabon gado da kashi ɗayan daya rage, Duk wacce ta samu kuɗin nan ruɗewa tayi dan wannan kuɗi da Dikko ya bada gado wa duk "ya "yanshi iyakar almubazzarancin mace rayuwar duniya dai ba ƙiyama ba ya isheka, ganin kuɗaɗe a hannunsu kuma sun tabbata babu saura yasa kowa ta tsige aurenta ta kama gabanta... Aure Dikko ya nemowa Dady ɗiyar wani aminishi suma attajirai ne na gaske , babu wani ɓata lokaci suka anshi tayin Dikko bikin bai wani ibi lokuta ba aka daura mishi aure da matarshi Maryam , mai irin sunan Sultana... Dady bai daɗe da aure ba , Kaka Dikko da Kaka Binta sukayi gobara gaba ɗaya gidan babu wanda ya fita , duk wanda suke uwa ɗaya da dadynmu wuta ta cinyesu sun mutu har lahira, Dady yayi kuka na tashin hankali duk mai imani saida ya tausawa Dady, Rayuwar dai haka taci gaba da tafiya , kakana na wurin uwa shine ya cusawa dady ra'ayin siyasa kuma Allah yasa ya shiga siyasar da sa'a domin ya riƙe manya manyan muƙamai dan siyasa tayi dashi kuma tana cikin yi dashi daga baya kuma ya tsaya takarar gwamna kuma Allah ya bashi yaci , Matan dadyna 2 a yanzu suka rage masa dan shima ya ɗan ɗana aure aure dan samun namiji amma Allah bai bashi ba , harya haƙura ya fidda rai Allah yasa ya sameni daga tsakiya dan mata sune samana kuma suke ƙasa na a cikinsu na rayu dasu nake gogayya banda aboki sai mata shi yasa ni ban ɗauki mace komai ba dan duk wani feleƙe da iyayi na mata babu abinda za'a layancemin , zancen cin cingom da duk wasu ɗabi'u na mata duk a wurin "yan uwana na koya, amma bana ɗabi'u irin na "yan daudu kuma bana magana irin na mata... Ina da ilimin addini domin nima sittin ce cikin kaina nasan hadissai sosai duk ƙaunar da ake nunamin da sangarta baisa na zama sakarai ba nasan abinda nake , tunda nake dadyna da mom ina basu taɓa dukana ba babu mai dakamin tsawa kuma babu wanda yakemin kallon banza tunda nake ban taɓajin kalmar zagi akaina ba saida Allah yasa an mata ta shigo rayuwata, itace mutum ta farko data fara zagina a rayuwa. Nima haka tunda nake ban taɓa neman mata ba kuma bana sabgar su akan ta ne na nuna mazantaka na, ni ba sakaran namiji bane ƙaddara ce kawai kuma bansan abinda hakan yake nufi ba , Gashi ta shigomin rayuwa banda isashshen lokacin da zanyi maganinta dan nima babana ya ƙusani cikin siyasa, ya fiddo ne akan wata kujera ta abokinshi daya rasu kuma inaji a jikina nine dan ban taɓa nema na rasa ba tun ina ƙarami duk abinda naso a rayuwata bai taɓa wuceni ba , dan bana san siyasa a rayuwata amma dole sai nayi ta. Mu fitaccin mutane ne muna da cikken asali bama da wani tambari na ɓatanci haka kuma bamu da sata bamu da maita , mu ba ɓoyayyin mutane bane sananni ne kuma fittaci tun zamanin iyaye da kakanni, haka nima sananne ne kowa ya sanni kasancewar ɗa ɗaya tal namiji a wurin mahaifina , shi yasa ban ɓoyu ba domin dady ya ɗaukeni kamar abokinshi baya ɓoyemin komai duk wani samunshi a tafin hannuna yake , ragamar komai a hannuna yake , dan zaka tara matashi kamarni wanda akeji dasu ko sukeji da kuɗi wallahi ka tara matashi talatin maiji da kuɗi da motoci basu Dikko ɗaya duk yawansu wallahi. Daga yau wallahi nayi rantsuwa idan har Sultana ta sake shigowa rayuwata saina keta mata mutunci wanda yafi wanda nayi mata a baya..... Taff wannan shine ƙudirin Dikko , ita kuma bara muji nata . Hafsa kuwa tunda Dikko ya zageta fess take kuka, Ni kuma bacci ɗaya nayi na farka ina tunanin yadda zan hudowa lamarin Hafsa....... 30/08/2019 *MEELAT MUSA* 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 23 Har gari ya waye ban sake komawa bacci ba , da safe bayan na gama duk abinda nakeyi na fara kiran lamba 4 , lamba 3 wato d c o kuma na haɗashi da Amisty bana iya wata mu'amula dashi saboda gaskiya baida tsabtataccen baki danni Allah yayi min ƙyanƙyami idan na raina maka tsaftar baki tou na raina maka kuma bazan yadda inyi wata mu'amula dakai ba gaskiya. Lamba 2 wato Bello shi yana nan kuma muna tare har yanzu babu wani abu daya shiga tsakani na dashi saidai ina fereshi yadda ya kamata ina kwalkwalar kuɗinshi babu dare babu rana, daya bani haƙuri ma cewa nayi saiya nemo min Babana sannan zan ƙyaleshi ! Lamba 1 Alhaji ne kuma ya rigamu gidan gaskiya , na goge komai nashi a wayana daga number har vidio babu abinda na bari, Lamba 4 shine mijin Zalifa kuma yanzu shine abun hari na, ɗan wasa na, domin shine zan jijjiga zanyi wasan kura dashi kuma saina lashe kaf tattalin arziƙishi saina cinye komai zan maidashi matsiyacin ƙarfi da yaji, idan kuma yana da rabo akaina tou in sameshi mai tsafta idan dai ɗan gayu ne kamar Dikko zan riƙe mishi wuya ya zama abokin tafiyana... Kiranshi nayi amma har ya tsinke bai ɗauka ba , haka tsarina yake kira ɗaya nakeyi idan ba'a ɗauka ba bana sake kira , idan kuma ya biyo kiran ina maraba dashi , Daga tsakar gida naji Amisty ta luƙaƙa wata irin ashariya irin na shararrin "yan tasha , saida gabana ya faɗi , ban gama saita kaina ba naji taci gaba da cewa na rantse da girman Allah wannan karon bazan bar Sultana tayi haƙuri ba , saita wulaƙanta shi ko waye ubanshi ... Da sauri na miƙe na fito tsakar gida jikina sai kyarma yakeyi saboda ni hayani da zage zage ɗimautani sukeyi , ina fitowa na kalli Amisty nace wai mene ne ? Kusa dani Amisty ta matso tace ke wai mu Hafsa zata tonawa asiri , kallon inda Hafsa take tsaye nayi sannan nace wai miye ? Wayar Hafsa, Amisty ta miƙo min tare da cewa shiga kiga cht insu da Dikko , bayan ta tura mishi saƙo ta whatsapp ya kirata tsakanin minti 10 bayan tura saƙo, kiji zagin da yayi miki Mother ƙarshen hukuncin da yayi yasa an rushe shagonmu kuma yace idan dai yana lumfashi kika fito karuwanci yace sai yayi miki wulaƙancin da ko ance ki faɗi kalmar iskancinci da bakinki sai kince kin tuba , Yace zai baki azaba mai azaba ɗaya daga cikin irin azabobin daya tanadar miki shekaru biyu masu zuwa , kuma idan kinyi taurin kai yace zai tafi dake ya ɓatar dake inda babu wanda zai sake jin labarinki daƙiƙiyar banza dake.... Zuciyata ta kawo maƙoshi amma ban nuna ɓacin rai ba nace ma Amisty wai duk inji shi Dikkon yace haka ? Amisty tace imana kinsan dai bana miki ƙarya idan baki yadda dani ba ki samo wani ya karanta miki duk duniya Sultana babu wanda nake ma soyayya irin wacce nake miki , nabar uwa da uba na zaɓe ke , rayuwata da komai nawa sadaukarwa ne a gareki idan ba duk abinda na faɗa miki Dikko ya rubuto ya turo ba Allah ya tsine min albarka ! Murmushi nayi sannan na kalli Hafsa nace to ke Hafsa mi ya kawo har kukayi magana na da Dikko ? Latse banzan bakinta tayi sannan tace niba magana nayi mishi ba shine yayi min maganarki , Amisty tace ke jira kiji zan ubanki ƙarya zan miki ko me kike nufi ne ? Kallona Amisty tayi sannan tace vidionmu ta tura mishi da hotuna kuma itace ta faɗawa Dikko muna da shago inba haka ba ya akayi yasan wurin harya zo ? Hafsa tace tou naje na faɗa Amisty kiyi magani na , ai tun kafin ta gama rufe bakinta Amisty ta rufe ta da duka tana cewa amanar ƙungiya zaki ci dan ubanki , an yadda dake zaki ci mana amana , ko an faɗa miki muma bamu iya karatun da rubutawa ba ? Tana magana tana dukan Hafsa , kokowa har ƙofar gida saboda cikin gida mata sun kasa ansar Hafsa dama su "yan gayu basu iya faɗa ba sai sakata suka iya... A ƙofar gida dakel masu aikin rusa tsohon gidanmu suka raba faɗa , kuma sukayi sasanci cewa da Allah mu daina faɗa ayi haƙuri , candai ake basu haƙuri niko wuri na samu na zauna wai nice daƙiƙiya , kamar ni abokin hamayya zai faɗa cewa ni daƙiƙiya ce , wallahi wannan kalmar tafi komai muni a rayuwata , itace kalmar da aka taɓa faɗamin ta ɓatamin rai kuma tamin ciwo ta kartar min zuciya har sai da naji masassara ta saukomin , wai ni Dikko yace ma daƙiƙiya , gumi naji yana bimin kumatu ina kai hannuna na shafo kunci na naji lema , ganin ruwa a hannuna ya tabbatarmin da kuka nakeyi.... Bayan an raba su Amisty shine suka zo kusa dani suka zauna hada Hafsa dan kunsan su "yan duniya basu fushi duk yadda aka cakusa dole sai an koma an jone , kowa tambayata yakeyi abinda yasa nake kuka amma banyi magana da kowa ba , Hafsa ce ta fara bani haƙuri akan abinda tamin murmushi nayi amma ban mata magana ba , Muna na zaune ƙofar gida a saman dandamali har su Nana mun jera layi babu mai mayafi a cikinmu mundai fito karuwan na zahiri da zahiri, saboda wancan hannu duk Dikko ya cinyesu babu gida ko ɗaya filin wurin ne kawai saboda duka wurin ya sayeshi harya tsallako gefen gidanmu yaci gaba da siyewa. Muna nan zaune muna jiran tsammani Umar yazo , yaron Dikko wanda ya yakaini gidan Alhaji , yana fitowa daga mota ni ya fara gani , shegiyaaaaa , ashe da kina nan ina kuɗi na da kika cinye "yar damfara ? Murmushi nayi da gefen bakina sannan nace zaki ya shiga gaban ɓauna , idan dai wanda ya mutu zai dawo tou ka kwantar da hankalin ka kuɗinka zai dawo aljihunka babu ɓata lokaci , Aiko kuɗina baza su ciwo wurinki ba sai kin bani abuna , dariya nayi tare da cewa wallahi basu ansuwa wurinka bakai ba kayan banza ko Dikko naci gabanshi naci uwarshi naci ubanshi a iskanci ai shine dai kake taƙama dashi ko ? Kusa dani Umar yazo yana ƙoƙari wanka min mari na riƙe hannunshi tare dayin wani irin lafiyayen fito , babu ɓata lokaci "yan dabana suka bayyana , kallonsu nayi tare da cewa ku shiga dashi ciki ku bashi ruwa yasha , ɗaukarshi sukayi sama sukai cikin gida dashi , saida suka bashi kashin bala'e sukai mishi lullusar fitar hayyaci , saida suka tabbatar jikinshi yayi tsami sannan suka tillo banza ƙofar gida... A lokacin ni kuma ina saman mota ta nayi kwanciyata , yayin da Amisty ke gefe na tana shan sigari A ` i da Saude kuma suna zaune kan dakali suna lido, Nana da Karima kuma nace su koma cikin gida saboda su matan aure ne , Dakel Umar ya miƙe ya shiga motarshi yaja ko masu aikin da yazo dubawa bai duba ba ya tafi , bai zame ko ina ba sai wurin "yan sanda , muna ƙofar gida zaune muka ga motar "yan sanda , wai anzo kamani , Bayan mun gama magana dasu nace su jirani ina zuwa , cikin gida na koma na shirya cikin shiga ta alfarma, wata riga na ɗauka na saka a leda bayan nasa anyi mata kitar wulaƙanci ga kuma jikina da yasha sahun akaifun Hafsa nasa ta yayyakushe ni dan na shirya ƙullawa Umar sharri na gaske. Dani da Hafsa da Amisty da A ` i da Saude muka tafi domin ni sune sheduna , mu biyu a gaba ukku a baya , cikin mota ta muka tafi saboda itace motar kece raini Hafsa ta tuƙa har muka isa police station, Umar na zaune a waje jini sai bin jikinshi yakeyi tuni ya kira Dikko ya faɗa mishi, Dikko yace da an kamoni a rufeni duk abinda yake zai shigo katsina gobe idan Allah ya kaimu , dan hankalinshi ya tashi da yaga dukan da nasa akayi wa Umar. Office ɗin d c o aka kai case inmu , ga gaske ni kuma gani nazo da kwarata masu biyawa mutum buƙatarshi , dan suma sunyo shiga mai ɗaukar hankali duk namiji mai lafiya ya gansu sai yaji hankalinshi ya tashi , Kujera Amisty ta jawo min na zauna sannan suka koma bayana suka tsaya , shigo da Umar akayi a daidai lokacin da ni kuma na fara gaishe da mai girma d c o , kafin ya ansa gaisuwar tawa Umar ya miƙa mishi waya Dikko ya sake kira domin ya faɗawa Dikko munzo station in , Faɗa Dikko yakeyi tare da cewa bai ce a jira aji abinda ya haɗamu ba kawai rufeni yace ayi , D C O yace ranka ya daɗe ai sai anyi binceke Dikko yace ba abinda za'a bincika umarni yaba d c o a rufeni kawai , d c o zai sake magana Dikko ya daka masa tsawa dole d c o ya dauke wuta , jikina fa yayi sanyi amma ta maza nayi tare da miƙewa na anshi wayar daga hannun d c o nace Dikko faɗa a cikin waya bashine ke nuna jarumta ba , kuma rufeni na kwana a ofishin "yan sanda bashi ne zai nunamin kai cikakken jarumi bane ba , Kaine kaɗai maganin fitsarata idan ka isa kazo kayi magani na basai kasa an kulleni ba , kuma kake cewa kar ayi bincike kasan abinda shi yaron naka yayi min ne ? Cikin ɗaga murya nace tou mutunci na fa zai buɗe kaga yadda ya yayyage min jiki ? Kuma da aka mishi magana cewa yayi kai ka tsaya mishi ya hau duk macen da yaji tayi mishi, kuma D C O ya faɗa maka idan bai yayyageni ba , da sauri Dikko ya rufe idanuwanshi tare da matse gwangwanin maltinar da aka kawo mishi baisha ba , azabar matsa yasa gwangwanin ya fashe maltinar ta watse... Har a zuciyarshi ya yadda da abinda na faɗa mishi dan yasan Umar manemin mata ne na ƙarshe yayin da Umar ke cewa wallahi mai gida ƙarya takeyi kawai naje duba masu aiki tasa "yan daba sukai ta dukana ! Cikin wata irin hayagaga Dikko yace rufemin baki ɗan iska mutumin banza idan na sake jin maganar ka saina ci mutunci ka wallahi , Tausasa murya yayi tare da cewa ba d c o wayar , miƙa mishi nayi Dikko yace da gaske ya yayyakushe ta ? D C O yace Eh ranka ya daɗe , to dole zaice Eh tunda ga sahun akaifa a jikina ya fito sosai, nidai bansan yadda suka ƙare ba D C O yace muje kawai , Muna shiga mota na sauke ajiyar zuciya , kai Dikko ɗan bala'e ne na ƙarshe baida mutunci gaskiya Allah ya rufamin asiri yau da sauro da zarnin fitsari ya hanani bacci , kallon Amisty nayi sannan nace kinji ɗan bala'e da saboda ni zaizo lallai dana yabawa aya zaƙinta , dariya nayi tare da cewa aidai mun daki banza.... Bayan wata ɗaya... A halin yanzu suna na ya fara zagawa a cikin gari, domin dai harkar iskanci ta buɗe mana sosai muna ganin maza daga shiyyoyi da dama , a cikin gidana nan maza ke zuwa su zaɓi macen da suke so a tafi hotel acan ake raƙashewa, yanzu bamu da shago domin Dikko ya saye wurin kuma yasa an rushe shi , tou ina gidana anan nake baje kolin iskanci na dani da yarana... Cikin wannan wata bakin gwargwado kowa ya samu ci gaba na rayuwa Nana namiji yake zuwa wurinta ta kora mishi sharfi akan kayan mata da maza , itama a hankali idonta ya fara buɗewa ta iya gogayya da maza , dan daga ita har Karima yanzu bata mazansu suke ba, A fanni na kuwa ni har yanzu ban samu tsaftataccen namiji kamar Dikko ba , amma idan aka zo tafiya da mace ni nakeyin ciniki namiji ya bani kuɗi kuma itama macen idan ta dawo zata bani kasafi na , tunda kafin a tafi nasan ko nawa za'a baki , na zama kawaliya kenan.. Idan namiji yazo ya duba a cikin matanmu bai samu wacce tayi masa ba ya faɗamin irin mace da yake so ni zan nemo mishi ita walau budurwa walau zawara har matar aure ma , Mijin Zalifa munyi waya dashi amma har yanzu bamu samu haɗuwa ba , yadai bada an kawo min kuɗi masu yawan gaske ta dalilin waya da mukeyi ta ɓatsa dashi , na siyar da motar da Alhaji ya bani nayi ciko na siyi mota ta gani ta faɗa , kuma ni nake tuƙa abuna domin yanzu na iya mota , jikina yaɗan ƙara ginuwa ya kuma goge hutu ya zauna dan dole dan idan baka san gidan da nake rayuwa ba zakace daga G. R. A na fito, na ƙara waye kuma idanuwana sunyi fashewar da duk mutum yayi mamakinshi, Shirye muke cikin shiga mai nuni da mutanen gari ga naku , ma'ana maza ga matan bariki, biki akeyi a gidan ƙanin Babana yana aurar da ɗiyarshi, dan haka nace kowa ya shirya muje , mota ukku mukayi hada Zalifa, mota ta , ta Hafsa sai ta Zalifa sai napep ɗaya ta "yan daba... Tunda mukayi parking idanuwan jama'a ya dawo kanmu, fitowa nayi tare dayin magana ƙasa ƙasa nace gafa "yar gado nayi gado amma kuma har na zarce... Ina gaba tawagar karuwai suna bin bayana , duk wanda ya ganni sai ya kauda kai tare yin gulma ta , a cikin gidan biki kuwa hankalin jama'a ya tashi ganin iskanci dana taro bamai riƙuwa bane , ƙanin Babana yana tsakar gida shima da mutane ana ta mishi Allah sa alkairi dan ba'a daɗe da ɗaura auren ba , mazauni su Amisty suka nemomin na zauna na ɗauki ƙafa ɗaya saman ɗaya na ɗora... Kallona yayi tare da cewa Sultana haka kika zama karuwa ? Saboda shi irin mutanen nan ne masu sakin magana babu tsafta , murmushi nayi tare da gyara zaman ɗaurin kallabi na sannan nace Eh wallahi ai shine nazo na nuna muku tunda nasan duk wani ɗan uwa da abokin arziƙi yazo shine nazo wanda basu gani ba suma su gani.... Dariya Amisty tayi tare da buɗe jakarta ta jawo shigarinta ta banka mata wuta , saida taja ta bada hayaƙi sannan tace wannan gaskiya ne Mother , ƙanin Babana yace nan zaki zo ki kawo mana iskanci ? Tou ki tashi ki koma inda kika fito tunda ke kin lalace karki zo nan ki gurɓata mana tarbiyyar "ya "ya kije can ki ƙari iskancin ke ɗaya.... Kallon Baba nayi tare da cewa gaskiya ne dan naga idan guguwa ta taso wuri ɗaya takeyin borinta amma tsawar hadari tana gaurayi kaf faɗin sararin samani , ruwan sama ko na sarari yake jeƙewa bai taɓa baa na cikin ɗaki kashi duk wanda kaga yasha kashin ruwa cikin ɗaki tabbas kwanon ɗakinsa ya huje , idan yayi dibara saiya doɗe wannan haryar da zai bawa ruwa damar shigo mishi ɗaki. Gyara zamana nayi tare da ci gaba da cewa duk na kirki baya san na banza amma ni mutanen kirki sune abokan rayuwa..... Miƙewa nayi tare da cewa ka bada tarbiyya a gida zamanin Sultana yana warware tuggun kowa , duk wanda ya kalleni a taron nan yace tir da halina ya saurari zuwan zamani na akan "ya "yanshi, har na fara tafiya na tsaya tare da juyowa nace yawwa idan kaga ɗan uwan naka Babana , ka faɗa masa cewa ina matuƙar kewarsa a kusa dani... Sallama nayi da duk wanda ya kamata tare da buɗe bakin jakata nayi alkairi , banga "yan gidanmu ba ko ɗaya amma nace idan sunzo ace musu ina nan tsohuwar anguwarmu , gidan karuwai kawai zasu tambaya za'a kawosu har ɗakin magaji Sultana , na ƙarasa maganar tare dayin murmushi sannan nayi gaba masu sauran imani suka bini da addu'ar shiriya yayin da wasu ke cewa ubana yajamin... Muna fitowa daga gidan kowa ya shiga mota muka ibi sararin hanya..... 31/08/2019 *JAMILA MUSA...* 🤙🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 24 Muna fita gidan biki Baba ƙarami ya ɗauki wayarshi ya fara kiran Babana abin alfahari na , mai nunamin soyayya ta zahiri da gaskiya , wayayyan mahaifi mai tafiya da rayuwarshi daidai da zamani... Bayan Babana ya ɗauka suka gaisa , bayan gaisuwa Babana yayi masa ya taro tare da addu'ar Allah ya bada zaman lafiya wa ma'auranta , Baba ƙarami yace ameen , Bayan Babana ya gama addu'a Baba ƙarami yayi gyaran murya tare da cewa wato Aliyu ɗiyarka dai ta zama cikakkiyar karuwa , ka shige ka ɓoye kabarma dangi baƙin ciki su gani... Rabbi annee massaniyadh dhurru wa anta arhamur rahmeena , Abdullahi Uwar masu gida baza ta taɓa zama karuwa ba ban haifi karuwa ba akanta amma karuwai suna zuwa kuma zasu tabbata akan duk wanda yake dangana min ɗiya da siffar karuwanci , ban gudu ba kuma ban ɓuya ba tunda har kuna nema na ku sameni ku bugo kuma in ɗauka muyi magana , na ƙauracewa zaman ne saboda duk duniya babu hawaye mafi ɓakin ciki inga suna gudana tsakanin idanuwa zuwa saman kumatu irin na Uwar masu gida, Duk kuwa ranar da naga kukanta tou tabbas shekarar mutuwa tane ya tsaya , ɗiya ɗaya tak a cikin taron yuyuyun "yan uwa , saita tallafeni sai ta tallafe ka sai ta taimakeni sai ta taimake ka sai ta taimakesu sai tayi ma kowa taimako kuma ko bana raye wallahi ka riƙe wannan maganar karka sake ka manta ta uwar masu gida cikakkiyar mai arziƙi ce , Idan ina da rabo inci idan banda rabo dangi su amfana ko ƙasa ta rufemin ido nasan nabar baya mai amfani , burin duk uba yabar baya jaruma ba lusara ba , idan kalmar karuwan ta sake fitowa bakinka akan Uwar masu gida na rantse da girman Allah gaba ɗaya zuri'ar ka sai sun zama karuwai..... Zufa ta ketowa Baba ƙarami tare da cewa Allah ya baka haƙuri Aliyu ban faɗi wannan maganar dan in ɓata maka zuciya ba , jarumin uba kenan murmushin "yan duniya yayi Babana tare da cewa nima ban faɗa maka dan zuciyarka ta ɓaci ba ina tunatar da kai dai ko waye Aliyu Binna dan naga tafiyana yasa ka manta me binna ɗin take nufi, haƙuri dai Baba ƙarami yaci gaba da bawa Babana saida ya tabbatar daya sauka sannan sukayi sallama... Wata irin ƙuna mai kartar zuciya Babana yaji wacce tasashi zaman dole , saida yasha kuka harya godewa Allah sannan yace ki yafemin Uwar masu gida ƙaddara tayi makauniyar waiwaya , an cuceni anci amanata banso ƙaddarar rayuwarki tazo miki a haka ba , amma na rantse da Allah daga Dikko har yaronshi Alhaji sun shiga uwatar bala'e duk wadda yaci yaciwo ma kanshi masifa , Abinda Bello ya guda kenan shi yasa shi baiba , amma yakaiki inda akayi nayiwa Dikko uzuri kuma na yafe mishi saboda nayi imani da yasan waye ubanki ko a santa ya ganki tsirara baya kallonki bare har yayi sha'awarki , duk abinda kike ciki na sani kuma ina da labarinshi , daga Dikko da Alhaji babu namijin da zai sake keta miki mutunci har abadan duniya , idan tsafin ne ba'a fini iyawa ba , cikakken ɗan caca manemin matan aure za'a nunawa iya sihiri ? Gaki nan zakiyi yawonki tare da rayuwarki cikin "yan ci kamar yadda ko wace ɗiya mai gata zata yi amma wallahi babu namijin da zai sake kwanciya dake sai mijinki na sunna in Allah yadda... Murmushi kasan dai Dikko yafi ƙarfinka duk wani ɗan ƙaramin tsafinka baya tasiri akanshi, kaine kaɗai halakakke ɓatacce wadda baka dogara da Allah ba ka dogara da tsafe tsafe, duk wanda ya riƙe Allah kuma ya dogara dashi Allah zai isar mishi duniya da lahira.... Dariya nayi adaidai wannan lokaci na daki sitiyarin mota ta domin fira mukeyi tunda muka taho , kallon Amisty nayi tare da cewa yaufa nasan na daki zuciyar maƙiya , mutumin dana burge a wurin bansan iyaka ba , tou dole ince mana , Kinga Sultana ga mota Sultana ga wayewa ga iskanci uwa uba karuwancin nan yamin kyau domin yasa na zama wata babbar hajiya da mutane ke ganin girmana , kuma nayi musu hauka da kuɗi zaki ga ikon Allah makwaɗaita sai sun biyoni saboda wannan zamani mai badawa shi ake mannemawa, Haka dai rayuwarmu taci gaba da tafiya ! Kullum iskanci na da lalacewa na gaba yakeyi amma har zuwa wannan lokaci ban samu wani cikakken namiji kwatankwacin Dikko ba , mijin Zalifa kuma har yanzu baizo ba da nayi masa magana bai zo ba saidai ya toshe ni da kuɗi tun abun baya damuna har ya fara tsaremin rai... Tsaye da kyau zaune da kyau babu inda Allah ya rageni amma mazan bariki idan sunzo basu tayani saidai idan nayi kawalci in samu kuɗi abunfa ya fara damuna na rasa inda zan saka raina dan ba irin wannan sana'ar na zaɓa ba gaskiya nafi so a nemeni ayi kuma a bani kuɗi , Amisty ta lura da halin da nake ciki ta tambaye ni abinda ke damuna , ban wani ɓoye mata ba na sanar da ita , dariya Amisty tayi tare da cewa wallahi hannu aka saka miki , Cikin rashin fahimta nace ina aka saka min hannun ? Na tambayeta ina kallon jiki na ! Dariya Amisty tayi sosai sannan tace haba uwar ɗakina bafa a jiki ake saka hannu ba , abinda ake nufi da sa hannu magauta zasu je wurin malaman tsubbu su biya kuɗi suce a toshe musu samunki a rufe duk wani ci gaba naki.... Tsoki nayi tare da cewa aisai suje suyi ta fama can su Allah ya azamawa , Amisty tace tou ai sai anyi maganin matsalar sannan zamu barsu suyi ta fama , kallon Amisty nayi tare da cewa wallahi kun cika canfe² babu wani jarabta na rayuwa sai asiri , an saka miki hannu , tou idan sun gaji da sa hannun zasu goge da kansu , Daga ƙofar ɗaki Nana tayi magana cewa Mother zamu ɗan shiga maƙota , daga inda nake zaune nace me akeyi maƙotan ne ? Nana tace Mother baƙi ne suka bayyana a cikin daren jiya anguwar nan , kinga matar wayayya ? Daga tsakar gida Saude tace matar kodai mijin ? Zamu shiga muga halinsu idan munga da lasa zamu yankawa mijin kati zai dawo gidan nan uwar ɗakinmu... Murmushi nayi irin namu na "yan duniya sannan nace tou ku dawo lafiya , saboda ni dama Allah baimin shige² ba ina nan inda Allah ya ajiyeni duk wadda nake tare dashi shine yake zuwa ya sameni dan gaskiya bana san raini shi yasa na tsare mutunci na a gidana... Gyaran murya Nana tayi tare da cewa ko zakije ne ? Cike da izza nace ku dawo lafiya , Amisty tace nima kam zanje , murmushi nayi amma ban sake magana ba , gaba ɗaya suka ɗinguma suka tafi gidan amma ni banbisu ba.... Gaba ɗayansu a palon matar suka sauka , kowa ta kama kujera ta haye kamar baƙon namiji a harkar mata , bayan gaisuwa kowa ta faɗawa matar sunanta tare da cewa sune maƙotan gidanta , itama sunanta ta faɗa musu Asma'u sannan ta kora da cewa bata taɓa aihuwa ba , Gyara zama Amisty tayi tare da cewa shekararku nawa da aure ne ? Asma'u tace gaskiya munkai shekara 8 , tou kina da abiyar zama ne ? Amisty ta tambayeta , Asma'u tace Eh mu biyu ne ? A ` i ta anshe da cewa tou kun taɓa neman maganin aihuwa ko itama abiyar zaman taki bata taɓa aihuwa bane ba ? Asma'u tace kai tana haihu sosai ma , Amisty tace tou matsalar daga wurinki take idan mun fahimta , Asma'u tace gaskiya , daga haka dai suka tsaya domin sun shiryo barikinsu wa Asma'u zance yau iyakarshi haka.... Miƙewa sukayi gaba ɗayansu cewa zasu tafi , Asma'u tace haba tun yanzu ? Murmushin "yan duniya A ` i tayi tare da lumshe idanuwa ita mayyar mata tace ai zamu sake shigowa , rakiya tayo musu har bakin get tayi godiya sosai , Tunda suka fito faɗa ya kaure tsakaninsu , yayin da A ` i ke cewa ta kama matar Saude kuma ta kama mijin , Amisty tace A ` i dani zaki haɗa hanya ? Bayan ni na fara isar da saƙo na zakice kin kamata ? Nana tace kai matar fa tana da mazauna sosai gaskiya , rikici dai sukeyi sosai , dan haka Amisty ta taka musu birki da cewa duk abinda zasuyi suyi shi a waje kar su bari naji wannan labarin domin sun san babu abinda na tsana irin harkar mace da mace.... Tun a waje sukayi ma Hafsa waya suka sanar da ita sun samu lafiyayyar mace kuma daga gani zatayi shan mai domin yarinyar da zafinta , Hafsa tace gani nan zuwa , Amisty tace karki zo yanzu kina zuwa uwar ɗakinmu zata gano wani abu kinsanta da saurin fahimta , duk satin nan karki zo ki bari sai cikin sati na gaba , Hafsa tace wallahi bazan iya ba sai nazo na ganta , Amisty tace saurara kiji yarinya , ba'a garaje ya kike abu kamar baƙuwar harka don Allah ? Ki natsu ki kwantar da hankali wallahi babu mai yarinyar nan sai mu , ki dai bari mu ɗorata hanya ita da kanta zata riƙa kawo kanta , dakal Amisty ta lallashi Hafsa ta haƙura, Tsakar gida suka sameni kowa tayi dabur ² murmushi nayi tare dabin Amisty da kallo sannan na kalli idon A ` i na kalli na Nana saboda sune "yan lesbian a cikinsu , da kinga sunayin kame² mace suka gani , sai kuma Hafsa itama manemiyar mata ce , jinjina kaina nayi sannan na tsare Amisty da kallo idanuwanta sunyi wani irin ja kamar taci tsidagu, Ƙafafuwan Amisty na kalla sannan na ɗago idona zuwa daidai saitin cibiyarta sannan na dauke kaina , ɗaki ta wuce Nana ma ɗakinta ta shiga yayin da A ` i ta samu wuri ta zauna , kallon inda A ` i take zaune nayi sannan nace sannun ku *kwarata* daga zuwa maƙota har hankalinmu ya tashi ko ? Duk yadda akayi matar gidan ta burgeku , Allah ya tsallaketa daga kaidinku.... Ɗaki na shiga Amisty na samu kwance saman katifa tayi ruf da ciki , tsoki nayi tare da halbinta da ƙafa nace tashi ki fitarmin daga ɗaki ni gaskiya bana san irin wannan ɗabi'ar , Allah ya baki haƙuri uwar ɗakina , tana faɗin haka ta miƙe tabar ɗakin ta nufi ɗakin Nana , da yake itama Nana naga yanzu taɗan waye tana wanka tana shafa turare , har akayi sallah magrib Nana da Amisty da A ` i suna ɗakin bansan abinda sukeyi ba gaskiya.... Kuma ban damu da sanin halin da suke ciki ba danni Allah baimin sa ido da bin diddiƙin abinda wane yakeyi ba , sai bayan isha'i Amisty ta shigo da ɗaurin gaba da alama wanka tayo , Ko inda take ban kalla ba , itama bata kalleni ba kuma batamin magana ba taci gaba da shiri saida ta gama abinda takeyi tsaf sannan tace min dame² za'a siyo ne ? Can zaki kwana ne ? Na tambayeta , tace ba'a can zan kwana ba wurin 1:00 zan dawo , indomie da madara kawai zaki ƙaro mana , kallona tayi sannan tace ke babu abinda kike so ne ? Ba abinda nake so na bata amsa tare da cewa Allah ya bada sa'a a dawo lafiya , da amin ta amsa sannan ta fice daga ɗakin... Kwanciya nayi bayan Amisty ta fita dan banda inda zanje , Nana ta shigo ɗakin da sallama ta ɗauki magunguna ta fita saboda mu yanzu garin "yan gidanmu ya waye , Ganin Nana ta ɗauki magunguna na tashi na feshe jikina da turaruka masu ƙamshi na ɗaukar hankali , doguwar riga ta shadda na saka nayi ɗaurin ɗan kwali irin namu na karuwai dan banda daurin ɗan kwalin daya wuce ture kaga tsiya... Tunda na fito daga ɗaki su Karima suka rufamin baya dan ko gyale tuni na daina sakawa , cikin isa da nuna ni wata shegiya , cike da izza nayi gaba sai baƙin rai nake na tun kari ƙofar gida su Nana duk suna biye dani , tsayuwa nayi a ƙofar gida nabi motocin dake ajiye a ƙofar gidan da kallo kamar anayin wani taro. Murmushi nayi yayin da aka ajiyemin kujerar roba na zauna , ƙafa ɗaya saman ɗaya na ɗora sannan mazan bariki suka fara kawo gaisuwa kamar yadda suka saba a duk lokacin da wani zai ɗauki wata domin nice uwar ɗakinsu , suna bani girmana basu rainani ba shi yasa duk wani *kwarto* yake ganin girma na... Duk namijin da yake zuwa wurin matan waje babu samari manyan mutane ne masuji da kansu wani ma wallahi yayi ɗiya da wacce zai kwanta da ita , ko me yasa suke baro matansu na gida suzo na bariki ? Gaskiya ina san insan wannan dalili ... Bayan na gama samun kuɗina na miƙe na koma ciki ,ɗakina na shige nabar musu filin tsakar gidan dansu ji daɗin harkokinsu , mace ɗaya tana iya kwanciya da namiji biyar saboda tsabar haɗama , *** *** Safiyar yau gidan Asma'u su Amisty suka sauka , acan suke baje kolinsu ranar da suka fara zuwa banje ba kuma yauma da zasu koma banbi su ba , gaba ɗayansu suka tafi ni kuma na fita ƙofar gida nayi zamana a saman dakali... Wayata na ciro na fara kiran mijin Zalifa , bayan ya ɗauka yace ina gida idan na fito zan kiraki , jinjina kai nayi tare da cewa ka fito lafiya ranka ya daɗe ina faɗin haka na kashe wayata.... A gidan Asma'u kuwa ga yadda lamarinsu ya kasance a yau , 02/08/2019 *JAMILA MUSA...* 🧚🏻‍♀ ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 25 Tunda suka shiga sukayi ta kwarara sallama shiru babu wadda ya amsa , Hafsa itace ta basu ƙwarin guiwa cewa kawai su shiga palo , gaba ɗayansu sunkayi na'am da wannan shawara dan haka suka ɗinguma suka shiga cikin palon tare dayin sallama... Daga cikin bedroom Asma'u ta amsa sallamar tare da cewa ku zauna ina zuwa , murmushi Amisty tayi tare da cewa ko munzo da wuri ne mai gidan bai fita ba ? Daga cikin ɗaki Asma'u tace ya fita amma yana dawowa babu jimawa wanka dai na fito ina ƙoƙarin saka kayana ! Wani irin ajiyar zuciya Hafsa ta sauke tare da cewa zanyi fitsari ta faɗi maganar cikin sigar kwartanci ma'ana tayi maganar a sakantace tare da kasalanci yanayin maganar dai sune kaɗai suka san fassarata , Akwai toilet a nan waje inji Asma'u tare da ƙoƙarin fitowa daga bedroom in dan nunawa Hafsa inda toilet in yake , towel ne ɗaure a jikinta ko guiwa bai kawo ba saboda tana da wani irin kugu ne shi yasa towel in ya haye saman ɗuwawunta shi ya hana towel in saukowa sosai ' Idanuwa Amisty ta zaro sosai kamar zasu faɗo ƙasa tare da jan wani irin gauron numfashi sannan tace babu toilet a bedroom inki ne ? Ta faɗi maganar kamar numfashinta zai ɗauke , murmushi Asma'u tayi tare da cewa akwai bara dai ta shiga na wajen ! A ƙofar palo sukaci karo da mijin Asma'u , tunda ya ganta ya haɗe girar sama da ƙasa tare da cewa wannan wane irin sakarci ne ? Ke wawiyar inace zaki fito haka ..... ? Cikin biyayya Asma'u tace ai ba kowa gidan ne duk mata ne , matan banza matan wofi da Allah wuce kije ki saka hijabi malama , yayi maganar cikin kausassar murya tare da ƙara ɓata rai kamar zai daki Asma'u , Simi simi Asma'u ta wuce ta koma ciki , saida ta shige sannan yabi bayanta , a palo ya samu su Amisty zaune riɗi² , duk gaishe shi sukayi amma babu wacce ya kalla bare su saka ran zai ansa gaisuwar wata daga cikinsu ya wuce ciki abunshi.... A bedroom kuwa faɗa ya rufe Asma'u dashi tare da cewa ina kika samo wa'anan karuwan ? Kai ƙasa ² tace maƙontanmu ne , zama yayi a gefen gado tare da ci gaba da cewa gaskiya ni bana so suna zuwa gidan nan kima taka musu burki kar na sake ganin kowa na faɗa miki , Cikin yanayin damuwa Asma'u tace haba Baban Abdul babu daɗi na ce su daina zuwa , cikin ɗaga murya yace tou wallahi idan baki musu magana ba ni da kaina zan musu magana zance kar na sake ganin ƙafar ko wace a gidan nan , daga shiga bayi kilbibi zai fara yaɗuwa , miƙewa yayi tare da cewa tunda tsoronsu kikeji ni bara inje in faɗa musu... Da sauri su Amisty suka miƙe kafin mijin Asma'u ya fito tuni sun fice daga gidan , koda ya fito palo bai samesu ba , dan haka ya koma yana cewa sun rufawa kansu asiri da suka gudu , ita kuwa Asma'u bataji daɗi ba saisu Amisty su gani kamar itace tasa mijinta ya tozarta su kuma tabbas nasan sunji kana faɗa irin haka babu daɗi... Cikin ƙara faɗaɗa faɗanshi yace ai dama bana so suji daɗin kuma idan na sake ganinsu gidan nan saina ci mutuncinsu , Asma'u tace tou shikenan ka haɗa hadani kaci mutunci gaba ɗaya , tou zanci hada naki ki barsu suci gaba da zuwa gidan nan kiga yadda zamu ƙare dani dake... A ƙofar gida su Amisty suka tsaya tare da saka takalminsu ko wanne yana maida nunfashi saboda gudun da sukayi daga cikin gida zuwa ƙofar gida , ajiyar zuciya A ` i ta sauke sannan tace kai wannan ɗan masifa ne zamu sha fama dashi domin zai ɓata mana lokaci gaskiya , Nana tace babu wani ɓata mana lokacinmu da zaiyi kawai mu haɗashi da Mother kunsan Allah ya bata ilimin saka namiji lungu , Hafsa tace idan muka haɗasu me kuke tunanin zai faru ? Kunfa san halin Sultana tana iya faɗa masa cewa ya hanamu shiga gidanshi mu maneman mata ne tunda ita bata wannan harka kuma sanin kanku ne baza ta rufawa mai irin halin asiri ba "" , Amisty tace tabbas zata aika wallahi , A ` i tace kuzo kuji mafita , haɗuwa sukayi wuri ɗaya sukayi magana ƙasa² dariya sukayi bayan sun gama tare da tafawa sannan suka nufo gida. ! A ƙofar gida suka sameni zaune ko inda suke ban kalla ba , zama sukayi yayin da Amisty ta ciro sigarinta daga cikin jaka ta kunna mata wuta saida taja ta sannan tace uwar ɗakina barka da hutawa , Bance yawwa ba kawai nace mata faɗi damuwarki , gyara zama tayi tare da cewa wallahi wani alhajin wuta ne muka samu , ga ƙira ga sarho { kwarjini } uwa uba hatimin nasara mota saidai ya shiga wannan ya fita a waccan , ga gida daya gina mai tafiya daidai da zamanin ƙarshe , jiya mata biyu yaba mota kuma nice sheda saboda na gani kuma na hau dan taya murna , matashi ne wayyan namiji ga aji kamar abokin gabarki { Dikko } Dariya nayi tare da kallon Amisty sannan nace kiyi magana kawai ki daina shiga buhu , kashe tabar hannunta tayi sannan tace nidai shawara zaki bani ina so ko ta halin ya nima in ɓata dare ko yini dashi , a gidanshi yake kai matan bariki idan matarshi bata nan , ki taimakamin ki faɗamin taya zan nemeshi... ? Kallon Amisty nayi sannan nace ke kin tabbata manemin mata ne ? Amisty tace ko ban tabbata ba dai inaso yayi akaina , karfa ki manta kece kikace mu nema ga mai nema kuma idan ya nema mu bashi , kuma kece kika ce idan mun gani munji muna da buƙata kar mu cuci kanmu muyi ƙoƙari mu bashi tun muna bashi yana tofarwa har mu samu ya fara haɗiyewa , nidai gaskiya ina so ya kwanta dani koda so ɗaya ne . Kallon Amisty nayi sannan nace a gidanshi kike so kuyi alaƙa dashi ? Amisty tacemin Eh , murmushi nayi tare da cewa kawo kunnenki a baki , matsowa tayi tare da miƙomin kunne na fara mata raɗa , har ga Allah ban kawo komai a raina ba kuma ban taɓajin sha'awar kowa ba a cikinsu , inawa Amisty raɗa ta kwanto a jikina sosai tare da lumshe idanuwanta , ashe ita daɗin maganar takeji , Ta bayana ta tura hannuwanta duka biyun cikin rigata ta fara shafawa a hankali tana wani ƙara mannewa a jikina tana nunfashi a hankali ² , ban gama maganar ba nayi tsoki tare da tureta daga jikina nace wannan wane irin ɗanyen iskanci ne kuma ? Dariya Hafsa tayi yayin data lushe idanuwanta sannan tace haba mother daga an riƙeki sai ki tayar da hankali ? Ba komai bane ba natsu kawai kici gaba da faɗa mata tunda kin fara kuma mu bakya so muji ! Ban kalli Hafsa ba nace bazan faɗa ba "yan iska masu guntuwar sha'awa ku ko kunyar Allah bakwaiji da kunga mace duk sai ku wani fitittike karuwai marasa aji , idan kunajin bala'e da tsabar maganin iskanci ku nemi maza sai kusan kunyi iskanci da hujja , mace me zata miki ? Inda kike buƙatar kije kafin ki sauka wurin kinsha wahala , Murmushi Amisty tayi tare da kishingiɗawa ta bini da kallon mai tatttare da tsabagen sha'awa sannan ta sauke ajiyar zuciya , miƙewa nayi Amisty ta jawoni ta zaunar dani , ta sake tsareni da wani irin mayataccen kallo , tsikar jikina naji ta tashi , lahira tazo min kusa kusa da sauri nace A'uzubillahi minashshaɗainir rajim , Gaba ɗayansu suka sheƙe da dariya , ɗaure fuska nayi tare da sake miƙewa , ƙara riƙo hannuna Amisty tayi juyowa nayi tare da cewa karki sakemin irin wannan abun daga yau bana so , makirin murmushi tayi sannan ta sakemin hannuna na tafi cikin gida , Suna ganin na shige A ` i tace Allah ya ɗoramu akan ni'imarki yarinya zamuyi wasan kura dake kowa saiya yagal galaki san ranshi wai ita a dole mai tsoron Allah , tuni na daɗe da haɗiyewa akan yarinyar can amma ta balɓaɗa min rashin mutunci tun kafin in furta , duk daren daɗewa saina afkawa yarinyar nan saidai duk abinda zai faru ya faru , Zama Hafsa tayi tare da cewa nifa na ɗauka "yar hannu ce ! Ganin farko da nayi mata itace ta fara nunamin wallahi a tunani na ta tafiya ce , ashe ba haka bene nima duk ranar data shigo hannuna saina horata , hawan farko zanyi da ita saita koma gidanmu da zama.... Ido ɗaya Amisty ta kashewa Hafsa tare da cewa ashe kuwa za'a haɗa rigima dan dai kinsan my Sultana tawa ce ni ɗaya , kinsan haɗarin dana fuskanta akanta kuwa ? Nabar uwa nabar uba na dawo zama da ita ? Lumshe idanuwa Amisty tayi tare da rungume duka hannayenta a ƙirji tace wallahi idan har na samu Sultana na more duniya , zan rabata da kowa da komai na ɗauketa na tafi da ita , A ` i tace ki ɗauketa ki kaita gidan uwar wa ? Ai yadda kikayi kowa sai ya more Allah dai yaba mai rabo nasara, sun daɗe suna ƙullawa da warwarewa yadda zasu samu nasara akaina daga karshe dai suka yanke shawara zasu kaini gidansu Hafsa acan zasu baje kulinsu dani... Tun daga wannan ranar na canjawa su Amisty fuska na daina cin abinci tare da ita , na daina kwanciya wuri ɗaya da ita , idan ta kwanta a katifa saina sauka ƙasa , gaba ɗayansu na rage musu fuska ko dariya na daina musu tunda dai na lura dukansu iskancinsu ya girmi nawa , Amisty kuwa muguwar tare tayiwa su Nana A ` i da Hafsa , ita kaɗai take zuwa gidan Asma'u basu sani ba ta shige mata sosai , har ta gane kwanakin da mijinta yakeyi a gidanta da ranar da baya gidanta ... Yau mijin Asma'u ba'a gida zai kwana ba tunda Amisty ta shigo gidan taƙi ta fita , har dare yayi sosai , gajiya Asma'u tayi dan taso Amisty ta tafi ta rufe gida , kasa haƙuri tayi tace wai nace ko yanzu zaki tafi dan kwanta ne bacci nakeji, Murmushi Amisty tayi tare da cewa ai yau nine zan tayaki kwana , Asma'u tace haba ai babu wani damuwa ni ɗaya ma nake kwana nan babu komai , ajiyar zuciya Amisty tayi tare da cewa ai nasan bakyajin tsoro tunda duk girman kwanakin da kikayi kina kwana bani nake tayaki kwana ba., Asma'u tace Eh kawai karki damu kya iya tafiya... Lemun dake gaban Amisty ta ɗauka tasha a bakinta sannan ta miƙe tsaye ta tunkari inda Asma'u take tsaye , Asma'u ganin Amisty a wani irin yanayi yasa taɗan ja baya , yaudararren murmushi Amisty tayi kamar yadda ta saba idan hankalinta ya tashi akan mace, Asma'u tana ƙoƙarin ƙara ja baya Amisty ta fizgo ta , Asma'u tace haba Amina miye haka ? Tayi tambayar tare da fizge hannunta ta ƙara yin baya , binta Amisty tayi har takai maƙurar bango maida hannayenta tayi duka ta baya ta dafa bango dasu ta tsaya tana kallon Amisty , Da duka hannayenta ta riƙe ƙugun Asma'u sannan tace wai miye duk kika wani firgice ? Kwanan da nine bakya so ko miye ? Asma'u tace ba haka nake nufi ba , ƙara fizgo ta tayi jikinta sosai sannan tayi magana mai tattare da ɗaukar hankali tace tou miye ? A wurin Asma'u ta sandare ta kasa cewa komai , sakin ƙugunta tayi ta jawo hannenta ta ɗora su a saman ƙirjinta sannan tace mu kwana tare ko ? Tayi maganar cikin rarrashi , kai kawai Asma'u ta iya ɗagawa Amisty , murmushi Amisty tayi sannan taja Asma'u ta zaunar da ita saman kujera , kamar ɗakin uwarta itace taje ta rufe ɗakin dan dama gidan rufewa sukeyi sai an ƙwanƙwasa take buɗewa, a inda tabar Asma'u a wurin ta dawo ta sameta , kusa da ita Amisty ta zauna sannan ta jawota jikinta tace miye ? Ko kinajin babu daɗi ne ? Cike da kasala Asma'u tace tsoro nakeji , ƙara jawota Amisty tayi sosai a jikinta sannan tace wane irin tsoro bayan gani ina tare dake ! Riƙo fuskar Asma'u tayi ta kalleta ido cikin ido sannan tace kin taɓa ? Asma'u tace a , a Amisty tace a kaina zaki fara kenan ? Jinjina kai Asma'u tayi alamar Eh , Amisty tace tou muje ciki , 04/09/2019 *JAMILA MUSA...* 🧚🏻‍♀ ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 26 Ƙiri² Asma'u ta kasa tashi , kusa da bakinta Amisty ta matsa da nata bakin sannan tace sweetheart miye ? Kallonta Asma'u tayi sannan tace na gaji , murmushi Amisty tayi da gefen bakinta sannan tace kin gaji tun yanzu ? Idan na fara suma zakiyi kenan saboda daɗi ko ? Shiru Asma'u tayi batayi magana ba , Uhum Amisty tayi tare da laso bakin Asma'u taɗan taɓo ƙirjinta ta waje , ƙara lasar saman luɓunanta tayi saita ɗago sannan ta ƙara tare da haɗa bakinsu wuri ɗaya tana mata wani irin sumbata wadda Asma'u ta danganashi da ko mijinta bai iya irinshi ba ! Tun a palo suka fara lalacewar su hankalin Asma'u yakai ƙololuwar tashi cikin sarƙayƙiyar murya tace muje ɗaki don Allah...... Amisty ta taimaka mata ta tayar da ita suka nufi bedroom , jikin Asma'u yana kyarma ta cire kayanta kaf sannan ta haye saman gado Amisty ta rufa mata baya suka ci gaba da halakewarsu ! Har ƙarfe 10:30pm babu Amisty babu labarinta , na kira wayarta yafi a irga bata ɗauka ba dan bata saba fita bata faɗamin taje wani wuri ba , duk wadda na tambaya ina Amisty sai yacemin baisan ina taje ba saboda suma kansu bata faɗa musu zata fita ba , Gajiya nayi da kiranta na haƙura nayi kwanciyata dan na huta , ina kwanciya Amisty tazo ta tsayamin a rai , tun lokacin da tamin abun nan a ƙofar gida duk lokacin dana raɓe ni ɗaya sai abun yazo ya tsayamin a rai , Tsoki nayi tare da gyara kwanciyata na rufe idona danyin bacci , murmushin Amisty nake gani sai kuma kallon da tamin , innalillahi wa'inna ilaihir raji'un nayi tare da miƙewa na ɗauki buta nayi waje .... Hafsa na gani ita da A ` i rumgume da juna , a'uziyya naja tare da cewa wai ku wane irin "yan iska ne da Allah ? Na rantse da girman Allah idan baku daina min wannan muguwar ɗabi'ar ba duk sai na tashe ku a gidan nan , Dariya A ` i tayi tare da sakin Hafsa tace Allah ya baki haƙuri uwar ɗakinmu , ban sake magana ba nayi gaba , bayi na shiga ban wani daɗe ba na fito ina fitowa nayi alwallah na shige ɗaki na , wannan rana kusan kwana nayi ina sallah dan banajin daɗin ganin Amisty a zuciyata ko kwalwata ! A ɓangaren su Amisty kuwa kwana sukayi suna baɗalancinsu Asma'u taji dadin wannan harka domin Amisty bata da ƙyanƙyamin taba Asma'u gamsuwar da ko a wurin mijinta bata taɓa samu irinta ba , ga Amisty ta iya soyayya domin ta daɗe a harkar lesbian gwanace kisan farko , koda safe itace ta wanke Asma'u a toilet kuma itace ta shafa mata mai da powder ta taimaka mata ta saka kaya sannan tace zata tafi gida. Asma'u tace da Allah karki tafi ? Murmushi Amisty tayi tare da jawota jikinta ta lumshe idanuwanta sannan tace karki damu ina dawowa anjima bana so mijinki yazo ya sameni a safiyar nan za'a samu matsala kinji ko ? Jinjina kai Asma'u tayi saida Amisty ta sumbace duk wasu muhimman wurare a jikin Asma'u tare da cewa ki kula , Asma'u tace to, sakinta tayi ta fito da sauri daga ɗakin dan har 9:00am tayi bata so mijin Asma'u ya ritsesu dan shima zata mishi horon da Sultana ta bata zata haɗasu dukansu taji dasu zata huta da Asma'u mijin kuma zatayi harka dashi dan ta samu kuɗi , dan da tana da wata sana'a ko hanyar samun kuɗi da baza ta bi maza ba , amma dole sai ta nemi maza sun bata sannan itama zata samu nayiwa karuwan matanta hidima... Tunda Amisty ta fito Asma'u ta koma gefen gado ta zauna , tunanin Amisty takeyi gaskiya ta yaba da jarumtar ta kuma Allah yasa yau ta dawo su kwana tare , Ina tsaye ina saka caji Amisty ta shigo ɗakin kamar an jefota , rumgumeni tayi tare da cewa oyoyo my Sultinah na dawo jiya inata kewarki sweetynah fatan dai kinyi bacci mai daɗi ? Kwantar da kanta tayi a saman ƙirjina , murmushi nayi tare da cewa tou sakarni mana , ƙara ƙanƙameni tayi tare da cewa uumm umm cikin sagwaɓa , har a raina abin yamin daɗi dan haka ban sake cewa Amisty tashi ba , jin nayi shiru yasa Amisty taɗan jijjigani sannan ta ɗago ta kalleni da kallo mai ɗaukar hankali tace me kika dafa mana ? Saida na zauna sannan nace ni ban wani dafa komai ba , idanuwa Amisty ta zaro tare da cewa tou me zanci kenan yunwa nakeji wallahi , sai kici haƙuri na faɗa , Amisty tace saida mai bada haƙurin kinsan ina ƙoshi da komai amma bana ƙoshi da mata... Tsoki nayi tare da kallon Amisty nace aike "yar iska ce wallahi , dariya tayi tare da ɗagamin gira ta kwanta sannan tace ai iskanci abun so ne wallahi danma baki san daɗin da akeji ba idan anayinshi.... Shiru nayi ban sake mata magana naci gaba da sabgar gabana , ita kuma wayarta ta fiddo bayan tayi latse latsenta ta kara a kunne , bayan an ɗauka tace ranka ya daɗe kana gari kuwa ? Banji abinda yace ba tace yawwa da Allah yunwa nakeyi aɗan kawomin abin ci yanzu ina jira , magana na cikin wayar yayi , wata irin dariya Amisty tayi tare da cewa tou babu damuwa idanma akwai wani mai ɗan ƙwari a tahomin dashi , tou babu komai ina jiranka , tana faɗin haka ta kashe waya... Kallona tayi sannan tace mother da Allah a fitar da lido waje yau banajin daɗin zama ɗakin nan , miya sa ? Na tambayeta ! Ba tare data kalleni ba tace idan ina ganinki a hakan nan komai zai iya faruwa ji nake kamar in haɗiyeki , ban kalleta ba nace Amisty ramin gafiya ba irin na maciji bane , wuta bata kamuwa haka kuma iska bata riƙuwa, domin fito da maciji daga rami dole saida hayaƙi , kamun maciji badai yaro ba saboda silɓinshi ,ki sani kama Sultana ba abune mai sauƙi ba dan kamun kifi dole saida fatsa.... Murmushi Amisty tayi tare da cewa aike sai kiyi ta magana da yaren da bana ganewa , nima murmushin nayi tare da cewa kamar yadda bakya gane yaren haka baza ki taɓa gane gaban Sultana ko bayanta ba domin shan ruwa da haɗiya lokaci ɗaya ba dai bakin mage ba , a fitar da lido ina nan fitowa idan nayi wanka... Fita nayi tare da ɗaukar ruwana na wanka na nufi bayi , Amisty kuma murmushi tayi tare da cewa zan kamaki yarinya zaki basu labarin fito da maciji dole saida hayaƙi ban taɓa neman mace ban samu ba zanyi waya da malam zulyadain na gaji da ganin abinci yunwa na damuna , lido ta ɗauka tayi ƙofar gida ita da sauran "yan tashar , Lokacin dana fito daga wanka babu kowa a tsakar gidan sai mijin Nana yana wanki , ban kalli inda yake ba nayi ɗaki abuna , ina shiga na fara shiryawa riga da sikat na saka na atamfa bayan na gama shafa , kayan kuwa sunyi matuƙar karɓar jikina ƙuguna ya fito sosai sai kace na wata uwar mata , turaruka na fesa tare da ɗaura kallabi wayana na ɗauka nima nayo waje bayan na gama , A ƙofar gida na samesu zaune saman dakali kuma da alama magana na sukeyi saboda naga sunyi shiru a lokacin da nake tahowa wurinsu , banma kowa magana ba na samu wuri na zauna naci gaba da latsa wayata , Amisty tace ga abinci nan idan zaki ci ! Ban kalleta ba kuma banyi magana ba , Amisty tace mother ina magana kinyi shiru , tsoki nayi tare da cewa na ƙoshi , cikin yanayin damuwa Amisty tace haba ya kuma kin ƙoshi ? Ban sake magana ba naci gaba da sha'anin gabana... Lido insu sukaci gaba dayi amma kaf hankalin Amisty da tunaninta yana wurina , ni kuma ina tunanin yadda zan fara kore mazan dake zuwa gidanmu dan na gaji da zama dasu Amisty idan babu mazan bariki tou kowa zai fita ya kama gabanshi... Ina wannan tunanin naji Amisty tace tou idan bazaki ci abinci ba kisha ko lemin mana , banyi magana ba na miƙe na matsa can wurin filin gidajen da aka rosa na zauna , Halbar da robar lemun Amisty tayi tare da cewa wallahi malam zulyadain bazai min ƙarya ba duk bala'en yarinyar can saina maida ita abun tausayi ta bana haɗiye miyau akan mace bansha ba wallahi , duk wacce tamin taurin kai asiri zaiyi tasiri akanta , tabbas itama Sultana zata yaba aya zaƙinta , Ban san gaibu ba amma tunda na lura da yanayinta bazan sake yadda da ita ba , ko yunwa zai kasheni na daina cin duk wani abu daya fito daga hannun Amisty kuma zan huro ma mazan bariki masifa duk wani kwarto saiya daina zuwa gidan nan , dama nina buɗe ƙungiyar kuma zan rufeta da kowarar kowa , Saida aka kira azahar na koma gida danyin sallah , har yanzu mijin Nana bai gama wanki ba tana can balbaɗɗiyar saman dakali sunayin lido , bayan na shiga gida ne Amisty take ba su Nana labari cewa malaminta yace duk daren daɗewa sai ta mallaki Sultana a hannunta kuma zata juyani san ranta ta kwantar da hankalinta lokaci ya kusa , amma a labarin malamin yace akwai wani yana nan shi zaizo ya tafi dani mutane dasu daɗe basuji labari na ba kuma yana nan ya kusa zuwa shima bada jimawa ba , Shine tace idan ta sameni zata maidani kaduna kafin wannan mutumin da yake magana yazo , dan malam yace babu makawa mutumin zai tafi dani kuma idan har yazo komai na rayuwata zai canza dan ko iyayena bazan sake gani ba gida ne zai kaini ya ɓoye ina ne ? Shine Allah bai nuna ba , idan ta kaini kaduna zatayi ta badani haya wa manyan hajijoyi tasan idan har tayi kasuwa dani ba kuɗi ba kuɗiɗina sai tayi... Hafsa tace tou waye wannan mutumin ne ? Amisty tace malam yace matashi ne kuma duniya ta tsaya akanshi , yace mai mulki ne kuma cikakken attajiri ne , shin mai mulki ne ko basarake wannan shine ban sani ba , jinjina kai Hafsa tayi sannan tace karki zubar da abincin nan kiyi mata wayau sai taci shi , murmushi Amisty tayi sannan tace kwantar da hankalinki wata ma jiya a ice cream na zuba mata da zan tafi saida tayi kuka , dariya sukayi dukansu tare da tabawa sukace Allah ya nuna mana Sultana tana kuka akanmu zamusha shagali domin yarinyar gaskiya Allah ya hore kayan marmari a tattare da ita , haka dai sukaci gaba da labartawa akaina da kuma yadda zasu mayar dani inyi ta binsu kamar wata karya... Suna ƙofar gida har bayan magrib suna hauka , da daddare bayan ƙofar gidanmu ya ɗauki harami kamar yadda ya saba a ko wane dare , bayan na fito nakejin labari cewa Dikko ya samu kujerar da yake nema yayin da mutane ke cewa yaron yana da sa'ar rayuwa gashi kamilin namiji , Magana ta karaɗe gari Allah ya bawa ɗan gwamna kujerar abokin babanshi daya mutu , duk inda ka nufa a gari maganar Dikko akeyi yayin da wasu keji idan sune a irin wannan damar ba ƙaramin farin ciki zasuyi ba , gashi Dikko ko auren farko baiyi ba amma ya shiga sahun manyan mutane da duniya zatayi alfahari dasu , wasu kuma cewa sukeyi tauraruwar ɗaukakarshi ne ya tsaya shi yasa na saman kujarar ya mutu dan Dikko ya hau , Har ga Allah naji baƙin ciki , yayin da naji dama baici ba shege munafikin Allah ɗayan mazinaci ya ɓoye ya saɓawa Allah amma a idon al'ummar gari suna masa kallon mutumin arziƙi bayan ni nasan mazinacin ne kuma shima yasan yayi zinar , hawaye ya cika min ido nace Allah ka kwace kujerar mulki a hannun Dikko babu mulki ma a hannunshi ya wulaƙanta al'umma inaga ya samu, Wani naji yana cewa yo ai wallahi yaron nan tsaron da zai samu ko gwamna baya samun irinshi kai kana wasa da kujerar kaza , mutumin ya faɗi sunan kujerar da Dikko ya samu nidai bansan ko miye yace ba kuma wallahi bana iya maimaitawa , Wani daban naji yace ai naji ance har gwamnan jigawa ya bashi ɗiyarshi , Eh ai mutane basu abu dan Allah Dikkon ne wallahi dole sai ka bashi ɗiyarka ga ilimi gashi ya fito tsatson mutanen kirki ga kyau ga ilimin addini ga ilimin boko Dikko ga kuɗi ga mulki Allah dai yasa muna da rabo duniya da lahira , wani yace kai saidai mu tara lahirar amma a duniya su Dikko duk sun tare komai... Tsoki nayi tare da juyawa na koma cikin gida ina tsinewa Dikko albarka wallahi idan dai ina da rayuwa ba tsaro ba ko tsoro yake tsare Dikko saina ci mutuncishi kamar yadda na ɗau alƙawari , Tunda na shigo ɗaki damuwa ta dameni na rasa inda zan saka raina naji sanyi wuri na samu na zauna a ƙasa na jingina da bango tunanin ta inda zan hudowa lamarin Dikko na farayi nasan ba lallai bane ya sake shigowa anguwarmu ba saidai ya bada umarni a duba dokuna kila ma yanzu babu wani ruwanshi da labarin doki Sultana kuma yasha banza kenan... Murmushi Dikko yayi a dai² wannaan lokaci sannan ya kalli Al ' Ameen yace bansha ba , ruwa ne aka ajiye shine Al ' Ameen yayi tunanin ya gama zai ɗauke Dikko yace baisha ba , fita Al ' Ameen in yayi Dikko ya kalli hoton Sultana a wayarshi sannan yace ki daina tunani kona manta dake daren daɗewa Dikko baza taɓa mantawa dake ba , kina da matsayi na daban a rayuwata dalilin abu ɗaya yasa nake ɗaga miki kuma bazan daina ganin mutunci ba har abadan duniya zanzo bada daɗewa ba ki ƙara haƙuri kuma ki zama mai yafiya banda yadda zanyi dake haka kema baki da yadda zakiyi da Dikko , ina cikin farin ciki a yau dan haka kema kiyi farin ciki a daren nan An mata.... Wallahi bazanyi ba , ni kuma Amisty ke tambayana abinda ke damuna nace mata babu dan ba wadda yasan abinda ke tsakani na da Dikko ban taɓa bawa kowa labari ba zuciyata da rayuwata kaɗai suka san wannan sirri , Amisty tace tou kiyi shiru kallon Amisty nayi tare da cewa yanzu na fara kuka kuma bansan ranar da zan daina ba , inaji a jikina baƙin ciki da ƙunci na rayuwa banma saka hannu ba zan haɗu da wani gagarumin tashin hankali da bansan ranar zuwanshi ba , zan rasa wani abu mai mahimmaci a rayuwata zan zama abin tausayi da kwantacci wata rana na ƙarasa maganar ina murmushi.... Simi ² Amisty ta miƙe dan a tunaninta na samu warwarewar tunani , a wurin na kwanta naci gaba da kuka har bacci ya ɗaukeni , Yauma Amisty saida ta shirya sihirinta ta tunkari gidan Asma'u , cikin farin ciki Asma'u ta tari Amisty tana maijin daɗin zuwanta , yauma ice cream aka bata ta lashe kamar wata mayya , idan babu kwaɗayi ba wahala, Babana zaune a gaban malamin shi , yace a zana masa ƙasa a duba masa halin da uwar masu gida take ciki ? Waya ɓata min waya faranta min ? Ina cikin farin ciki ko ina cikin damuwa ? Akwai wani dake harina kuwa ? ...... 05/09/2019 *MEELAT MUSA CE...* 🧚🏻‍♀ ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 27 Gyatsa malam yayi sannan ya ɗauko wuri ya feshe da turare irin nasu na matsubbata , a saman farin ƙyalle ya watsa wuri in suka watse ko wanne bai haɗu da ɗan uwansa ba sai guda biyu suka haɗe a wuri ɗaya... Kallon Babana malam yayi sannan yace waye wannan yake tare da ita ? Baba yace Allah ya gyara aikin malam aikai zaka warware mana komai wannan ɗin shine yake tare da ita uwar masu gida kenan ko ? Girgiza kai malam yayi tare da cewa bana tunanin wani namiji zai sake shiga rayuwar Maryam saidai mu bincika muga waye wannan ! Cikin damuwa Babana yace aiko idan bai fita harkar uwar masu gida ta salama ba zai fita da ƙarfin bala'e ko waye , Iyakar bincike malam yayi amma ya kasa gano ko waye yake tare da Sultana , an buga ƙasar an zana an goge an sake rubutawa amma abinda binciken ya nuna wai a kulle yake , wai prvt istihara jama'a kun taɓa ji ? Hankalin Babana ya tashi yace malam babu abinda ya gagareka ,{ kai jama'a saboda an taɓo ɗiyarshi harya manta da Allah yana iƙirari wai babu abinda ya gagari malam } duba min miye kuɗirinshi akanta malam ! Bincike malam yayi sannan ya ɗago ya kalli Babana yace kaga ka fita harkar rabata da ko waye wannan domin duk wanda akazo istihara aka kasa kamashi shirin duniyarshi ba ƙarami bane gaskiya , wannan yayi zarra kuma yasha gaban duk wani mai tada mishi ƙura abinda yasa nace haka idan har kace zakayi wani sihiri akanshi wallahi zaka lalace... Babana yace lalacewa kuma na nawa ? Aiko asiri zaka ma mutum idan kaga yana caca kawai ka barshi , tou Binna ba'a caca kaɗai ya tsaya ba ga caca ga neman mata idan akwai lalacewa wacce tafi wannan akan uwar masu gida na yadda zanyi wallahi ! Ƙara duƙufa malam yayi zuwa wani lokaci ya fara magana ba tare daya ɗago ba yace Aliyu wannan mutumin da muke magana yana gaf da Maryam kuma yana zuwa wurinta babu jimawa zaizo da farin ciki amma zai koma da ita yana mai baƙin ciki , abinda zai kawoshi da abinda zaisa ya tafi da ita duk ban gani ba amma tabbas zai tafi da ita kuma zata ɗauki tsawon shekaru babu wanda zaiji labarinta , Cikin tashin hankali Babana yace ina zai kaimin ɗiyata ? Malam yace ina zai kaita nima ban sani ba amma tafiya babu makawa , waye shi ? Malam yace sanin ko waye shi da ƙudirinshi duk sai mu jira zuwanshi , cikin ɗimaucewa Babana yace kafin yazo ina tare da "ya ta ina nan ina jiran zuwanka a gabana ka taɓa uwar masu gida saina gana maka azaba mafi girman azaba a duniya , ka fara lissafi daga yanzu kwanakin mutuwarka na tunkaro ka muddin ka tunkaro rayuwar ɗiyata kazo ina jiranka....... Ya ƙarasa maganar jikinshi yana wata irin kyarma idanuwanshi jajir kamar an watsa mishi yaji sai zufa yakeyi kamar wadda maciji ya sara.... Malam ya tausayawa Babana dan haka yaci gaba da bincike amma Allah ya ɓoye mutumin da zai shigo rayuwata , cikin tausayawa yace Aliyu kayi haƙuri tunda nake dakai baka taɓa nema baka samu ba sai wannan , kai kanka kasan iskancin da Maryam ta taro ba ƙarami bane banda muka dage akanta da yanzu bata taruwa a garin nan sanin kanka ne , Da sauri Babana ya rufe idonshi dan duk duniya ya tsani a danganani da kalmar iskanci , laya malam ya miƙowa Babana yace gata nan kaje ka samu jaririyar mage sabuwar haihuwa wacce dai bata buɗe ido ba , tou a yage bakinta a saka wannan layar sannan a kashe magen a jefar da ita a tsohuwar rijiya , bazan maka bayanin komai ba zaka zo ka bani labari yadda Maryam zata watsar da kowa da komai ta dawo gareka... Hahaha Babana yayi dariya irin ta basawa tare da cewa godiya nake malam uwar masu gida zata dawo gareni , zata manta da duk wani abun daya faru a baya ta dawo nutsatsitsiyar ta kamar baya , godiya Babana yayi sannan ya tashi ya tafi.... Baccin dai babu daɗi dan ko da nayi bacci ɗaya farkawa nayi daga nan na shiga tunanin rayuwa da tunanin mutuwana wacce zata iya riska na kai tsaye ba tare dana shirya ba , ina ƙoƙarin koyawa zuciya tsoron Allah na canja halayya amma sam sai zuciyata ta karɓi huɗubar sheɗan cewa yarinya dake ? Duka shekarunki nawa a duniya ? 17 zuwa 18 ne ai mutuwa ma baza ta wani zo wurinki ba ki dage kawai ki more talatarki kafin larabarki ta riske ki.... Karki kuskura ki bar bariki ba tare da kin kafa tarihi ba , ki zuge rayuwarki kaf wata rana zata tofo domin rayuwa ita da zogala basu da wani banbanci kinga dai zogala kullum cikin zugeshi akeyi amma kafin wani lokaci ya sake fitowa , mafita ɗaya ce su Amisty kawai zaki kora sai ki shiga cikin ahalin Baba ki sake haɗo wata daba , yess 🤷🏻‍♀ dama Baba ƙarami yacemin karuwa zan koyawa "yar sa karuwancin idan an tashi kwatance a cikin ahalimu za'ace karuwai biyu idan har na bari na zama karuwa ni ɗaya gori bai ƙare ba har ɗiyan ɗiyana amma idan na taɓo wasu a ciki shiru zakuji ustaz ya samu mace... Da safe bayan na gama duk abinda nakeyi wanka nayi na shirya cikin riga da zani na atamfa nayi ƙofar gida , dukansu a saman dakali na samesu zaune hada Amisty sallama nayi musu sannan na samu wuri na zauna , a cikinsu babu wadda yaimin magana kuma babu wadda ya ansa min sallama , sukaci gaba da labarinsu , Ban damu ba domin dama su ba ma'abota ansa sallama bane ba , cikin girmamawa Amisty ta taso tazo gabana ta durƙusa da wainar filawa an daka mata tashshi mai shegen daɗin ga tumatur da albasa tasha kallo ɗaya nayi ma wainar yawu na ya tsinke , Amisty tace ga abinda kike so nayo miki mother , Cikin farin ciki na ansa tare da fara kwararawa Amisty godiya sannan nabi kowa nace yaci , murmushi Amisty tayi tare da cewa ai kowa yaci taki ce ke ɗaya uwar gidan kwarata , jinjina kai nayi tare da miƙawa Amisty nace tou kici kema , no nikam bana ci kinsan waina bai wani dameni haka ba , miƙewa nayi tare da cewa ai wannan shagalin sai an rufe ƙofa , Dariya sukayi gaba ɗayansu tare da cewa sai kace dai kin samu mijin zalifa ? Nima dariyar nayi ba tare da shigewa ciki , umm waini za'a cuta da gwangwanin fulawa ɗaya tashshi naira talatin da manjan naira hamsin , Amisty kenan idan har bakisan halina ba har yanzu lallai babu ranar da zaki gane wace ce Sultana... Ina shiga cikin gida ɗakina na shiga na kwashe wainar na zuba a leda bayan na gama na fito na zubar a bola , ɗaki na koma naci gaba da danƙarar tashshina saida na haɗa zufa na tabbatar bakina ya kama tashshi sosai sannan na fito ƙofar gida da tissue ina goge majina , A gaban Amisty na ajiye flet in tare da ƙara fyace majina idona yayi jajir sannan na zauna kusa da Amisty , murmushin mugunta tayi tare da lasar bakinta kamar mayyar da ta daɗe batayi kamu ba , nima murmushin nayi tare da kallon Amisty nace ɗan matsa daga gefe kar ayi abun kunya bisa titi ! Kallon su Hafsa tayi tare da ɗaga musu gira alamar tayi nasara, ɗan cije leɓona na ƙasa nayi tare da ƙanƙance idona na dama , kallona Amisty tayi sannan tace wane irin abun kunya za'ayi ne ? Murmushi nayi tare da cewa ji nake kamar in lashe ki , na nuna lashewar da harshena sannan na haɗe haƙorana na gaba sukayi ƙara ƙass. Uhum kwarata kenan gaba ɗayansu sukayo kaina kamar an watso mutane a doka daji , yadda namun daji ke kawo hari kowa ya ɗauka karya rasa , murmushi nayi tare da ajiye hannuwana ta baya na jigina dasu ina kallonsu , Hafsa tace uwar room ya kikeji ne ? Rufe idanuwana nayi tare da girgiza kaina sannan nace ai bama zan iya musultawa ba , Nana ta riƙo ƙuguna tana kallona bayan wani lokaci tace ɗan daure ki misilta mana yadda kikeji ! Har yanzu idanuwana a rufe yake nace misali kece aka rufe a ɗaki kwana biyu babu ci babu sha idan aka fito dake kika ga abinci wane irin ci zaki masa ? Amisty tace ai ƙalu bale ga duk abincin dana damƙa , buɗe idona nayi sannan nace tou idan aka ajiye miki farfesun kaji sai aka kawo miki kwaɗon ganzo ko garin kwaki a ciki wane zaki ci ? Hafsa tace ai kowama kazar zaici , dariya nayi tare da cewa me yasa zaki ci kaza kibar ƙanzo ? Amisty tace saboda itace tafi daɗi da amfani a rayuwata , Gyara zama na nayi nace to idan kika samu namiji kika samu mace a ciki wannen zaki ɗauka wane zaki bari ne ? Amisty tace ai mace ba'a haɗata da kowa domin ita tafi kaza daɗi ke wane zaki ɗauka wane zaki bari ? Ta ƙarasa maganar da tambayana.... Gyara bakina nayi tare da cewa gaskiya dani namiji amma yanzu mace nake so nima , age agegege..... Kunji wani sabon taken iskanci wai agege , gaba ɗayansu suka faɗi age agege , Saida na gama kallesu tsaf sannan nace amma ina da sharaɗi fa ! Amisty tace faɗi sharaɗinki mother , yawwa idan dai zan faɗa harkar lesbian gaskiya sai kun bani haɗin kai na tsaya saman ƙafafuwana mun kora duk wani namijin bariki ta hanyar tambayarshi abinda yake bashi sha'awa a bariki , ta haka zamu gano inda matsalar take zamuyi gyara domin ceto matan auren da suka rasa mazajensu , domin gaskiya bana iya haɗa bariki da harkar mata , Shiru sukayi suna kallon junansu , nima ban sake magana ba ina saurarensu abinda zasu ce , Hafsa tace meya shafi harkarki da rashin kula namiji kuma ? Salon nawa ne a haka gaskiya dan idan baku manta ba yanzu maza nake bana mata , amma tunda zan ajiye maza na ɗauki mata dole saina fitar da maza a rayuwata .... Da ido sukayi magana sannan sukace har zuwa yaushe zamuyi aikin ne ? Na sati ɗaya ne , na basu amsa , tou munji mun yadda suka amsa gaba ɗayansu , jinjina kai nayi alamar na gamsu , Hafsa tayo ta kusa da fuskata da wani banza bakinta zata sunbaceni , murmushi nayi tare da tare bakin ta da ɗan yatsa na nace yi haƙuri hajiyata lokacin naku bai fara ba , A hankali taja baya , murmushi nayi a zuciyata tare da cewa Mother ta ibi ruwa ta jefa guga duk wanda yai wannan yazo da zamba , ko akan wannan zasu ɗau misalai , domin Sultana tayi naɗi da lauje , "yar birni tayi nitso da ƙoƙo gani naci banza zan zare adda , kowa yayi ƙuri sai yayi muzu a ƙarshe mu zuba dani daku... A ƙofar gida muka yini dukanmu amma ni ina tashi naje nayi sallah idan lokaci yayi kuma dana gama nake dawowa domin duk iskanci su Amisty a saman tafin hannuna yake , duk wani barbaɗe² ankare nake dasu domin suna sakin layi cikin magarnarsu , ni banci ɗiyar kowa ba uwata batayi ba babu wanda ya isa yayi akaina kallon biri sukemin ina musu kallon ayaba zasusha mamaki ranar da film in ya ƙare.... Da daddare , kamar yadda ƙofar gidan ya saba a ko wane dare haka ya fara ɗaukar harami motoci suka fara layi ƙamin yadda suka saba , kamar yadda muka saba muma a ko wane dare haka muka fito ina gaba su Amisty suna biye dani a baya , dan yau a gida zata kwana tunda mijin Asma'u gidanta yake yau... Wani zafaffen Alaji ne yace Allah ya taimaki uwar gidanmu , harna wuce nayo baya dan haka aka ajiye min kujera na zauna suka koma bayana dukansu suka tsaya kamar yadda suka saba , gaisawa mukayi na tambayeshi iyali ? Lafiya qalau yace tare da ɗan maida idonshi ga waya , murmushi nayi tare da cewa Alhaji wai matanka nawa ne ? Shiru yayi baiyi magana ba yaci gaba da kallon wayarshi , Alaji na sake kiran sunanshi , miƙomin wayar yayi tare da cewa ko kema zaki kalla ne ? A face buk sai maganarshi akeyi Allah dai yasa kar bakin duniya ya kashe shi mutane suke tayin posting hotunanshi suna tayashi murna... Ya faɗi maganar tare da miƙomin wayar , ƙin ansa nayi Hafsa itace ta ansa bayan wani lokaci tace Alhaji ya naga ana haɗashi da wata mai siffar maguna , dariya sukayi gaba ɗayansu Amisty tace ke kuma mai siffar kisau , duk kallo sukayi dukansu A ` i tace aiko wannan mai kyau ce gaskiya kedai kawai kice kinajin kishi , Alhaji yace ai itace zai aure ɗiyan gwamnan jigawa ce , sai yanzu na gane ko hoton waye ake kallo , Amisty tace yaushe za'ayi bikin ne ? Alhaji yace ƙarshen watan nan shi gwamnan keta sauri dan yaga Dikkon so yake ya zuƙe dandai suna da zuminci amma da bana tunanin za'ayi auren nan gaskiya... Miƙomin wayar Amisty tayi tare da cewa kalli mutuminki zaiyi aure , tsoki nayi tare da cewa ta ina ya zama mutumi na kuma ? Hafsa tace wanda kukayi faɗa asibiti wai mother mema ya haɗaku dan a lokacin naga kuna abu cikin gayya² dadai gani akwai azazza a tsakaniku. Murmushin ƙarfin hali nayi tare da ansar wayar amma banba Hafsa amsa ba , kallon hoton nayi yayin da wani hadarin baƙin ciki ya taso min , tsoki nayi tare da cewa Hafsa siffar me gareta kika ce ? Hafsa da baƙin ciki ke gurgurawar zuciya tace shegiya tsinanniya mai siffar karnuka ai in Allah ya yadda wannan auren babu ubanda zaiyi shi , Kawai dai haka nan nakejin babu daɗi a raina , zuciyata kuma tana kwaɗayin ƙara kallon hoton Dikko , amma na hanata tare da cewa kwantar da hankali keda zakici mutuncishi saurin me kike bayan lokaci ya kusa.... Maida hankali na nayi wurin Alhaji tare da cewa Alhaji matarka nawa ne wai ? Mata ta ɗaya mene ne wai ? Ba komai na bashi amsa tare da cewa tou me yaja ra'ayinka na faɗowa matan bariki haka rana kwatsam ? Kallona yayi cikin ɓacin rai yace me yasa kikemin irin wannan maganar da Allah ? Nima kallonshi nayi ido cikin ido sannan nace haka tsarinmu ya koma dole duk wani namijin dake cikin barikin nan saiya faɗa mana abinda ya kawoshi bariki , idan ya faɗa mu kuma sai mu bashi tsula²n mata ya more daga garesu saboda munyi oder manyan mata daga jahohi da dama , haka tantancewa mukeyi mu gano namijin da ya kamata muje dashi a cikin wannan tafiya tamu mai taken bariki ta giga..... 07/09/2019 Taku a kullum ... 👇🏻 *JAMEELA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 28 Kallo Alhaji ya bini dashi mai nuni da yama rasa abinda zaicemin , murmushi nayi tare da cewa da Allah kar kaga kamar cin fuska ne ko wani abu ko zaka taimakamin naga hoton matar ka ? Me yasa kike son ganin hoton matana ko zakije ki haɗamu da ita ne ? Ya ƙarasa maganar cikin sigar barkwanci , murmusawa nayi tare da cewa haba Alaji yadda da arne shi yake sa aci yankashi , kuma daɗin aure kesa mata tace miji Baba... Ganin hoton iyalinka bashi ne yake nuni zan faɗa ba , nasan gidanka komai da komai naka na sani hoto kawai zan gani sai nayi gaba abuna... Amma kafin na tafi don Allah me yaja ra'ayinka ka afkowa matan bariki bayan ka baro naka matar gida ? Ɗaure fuska yayi tare da cewa me yasa kike so kimin haka wai ? Dani dake da ku dukanku taimakekeniyar juna mukeyi manta da lamarin matana da kuma abinda yasa na faɗo barikinku mu fuskanci abinda ke gabanmu ! Miƙomin wayar yayi da hoton zuƙeƙiyar matarshi wacce ta gaji da haɗuwa duk inda ake neman mace takai kuma duk inda ya nuna matanshi abun kallawa ce , gaba ɗaya tafi su Amisty komai na morewa amma bata kai diddigen Sultana ba , danni a tara mace dubu baza'a iya samo ɗaya kamarni ba , Caf na faɗa tare da kallon Alhaji sannan nace wannan kyakkyawa ya akayi ka baro kyau siga da nagarta ka faɗowa kwarin mata ? Me matan bariki suka fi matar ka ? Me yasa ka kashe sunna kake ƙoƙorin ɗabbaƙa zunubi ? Me yasa kabaro inuwa ka dawo rana ? Ya akayi kabar rahama ka dawo azaba ? Me matan bariki sukafi matar ka don Allah ? Me ya ɗaukar maka hankali da macen bariki har ka baro taka kazo wurinmu....... ? Kallo Alhaji ya bini dashi na kece abun tausayi mai ƙaramar shekaru dake kina ɗaukar kayan daya fi ƙarfinki , kamar nasan abinda ke zuciyarshi nace manta dani ka fuskanci taka rayuwar , nasan matsayin zina , illolinta matsalolinta wahalhalunta tashin hankalin dake cikinta da kuma bala'en dake tare da ita , san zuciya da ɗaukar huɗubar shaiɗan ya mantar dani , domin yawan kusantar saɓo yana hana ganin girman zunubi , kasan surar da Allah ya sauke akanmu mu mazinata , ina matsalar take tsakanin kai da matar ka ne ? Gyara zama Alhaji yayi sannan yace :• me yasa matan bariki suka fi iya jan hankalin namiji ? Ba tare dana kalleshi ba nace shaiɗan ne yake ƙawata maka su domin yasan zina hanyace da take kai mutum ga halaka , zina tana zubar da mutinci tana rage ma mutum daraja a wurin ubangiji sannan mutuncin shi zai ragu a wurin al'umma kuma zina tana rage ƙwarjini fuska , Har yanzu baka bani amsar tambaya na ba , miya ja ra'ayinka shiga harkar bariki wai ? Alaji yace matan bariki kullum a shirye suke basa taɓa gajiyawa da ansar buƙatarka duk lokacin daka zo musu zasu anshe ka cikin farin ciki ba tare da gajiyawa ba , zaka kwanta da mace babu wari a jikinta babu ƙarni ko zarni bare kuma hayaniyar "ya "ya , yayin da zaka kwanta da matarka lokacin zata fara cewa batayi ma yara shimfiɗa ba , kana mata magana tana wani fiffizge kai tun kana sha'awar abun har yazo ya fita akanka , Kallon Alaji nayi sosai sannan nace , filawar bisa hanya tasha banban data cikin gida , mace kamar filawa take idan ta samu wuri mai kyau kuma akayi mata ban ruwa yanda ya kamata idan dai tasha ruwa ta ƙoshi duk wanda ya gani sai ta bashi sha'awa , lokacin da filawa ta rasa ruwa zata bushe ta soye duk wadda ya kalleta baya sha'awar ƙara kallonta , to haka mace take , matan bariki wayau suke muku kuna basu kuɗi suna gyara jikinsu a cikin kuɗin da kuka basu a ciki suke siyan abunda zasu ja muku hankali dashi , matarku ta sunna tana can viseline in da zata shafa wahala yake mata , taya zata gyara bare har ta baka sha'awa ? Idan baza ka damu ba zanyi magana da matarka idan Allah ya kaimu idan har tabi shawarata tabbas zaku samu rabauta , kai kuma zan koya maka yadda akewa mace ban ruwa .... Shiru Alaji yayi zuwa wani lokaci yace babu damuwa kije na yaddar miki , godiya nayi masa sannan na miƙe ɗauko kujerar sukayi suka biyoni da ita yayin dana tsaya wurin wata motar... Ajiye min kujera akayi na zauna , motar a buɗe take dan haka na ɗora ƙafata ta haggu a saitin mazauni driver tare da cewa malam barka da dare ! Allah ya taimaki uwar ɗakinmu ya haƙuri damu ? Alhamdulillah na faɗa tare da cewa ya iyali ? Kamar jira yake yace tana can shegiyar saida nayi mata jakin duka na fito , kallon agogon hannuna nayi ba tare dana kalleshi ba nace me tayi maka ne ? Ta rainani idan na shigo da leda takemin sannu da zuwa idan banzo da itaba ko daga ɗaki bata fitowa , yau na yanka rago dake duk sati nake yankawa , mahaifiyata tazo nace a ibar mata shine tayi mata rashin kunya ni banji daɗin abunba shi yasa nayi mata duka na baro gida , Kallonshi nayi sannan nace to me kazo kayi nan ? Dariya yayi irin ta sakarkari sannan yace nazo a ban natsuwa , jinjina kai nayi sannan nace tou yau babu maganar bariki kaje gida ka lallashi matarka muna zuwa gidan idan Allah ya kaimu , ina faɗin haka na miƙe nayi gaba , ɗauko kujerar sukayi suka biyoni domin cikin gida na nufa... Hayani mazan suka farayi tare da cewa ya zanyi musu haka ne ? Ai haka ma babu adalci , a zuciyata nace wannan matsalarku ne ba nawa ba , Ina shiga gida na shige ɗakina , Amisty ta rufomin baya , itace ta kulle ɗakin domin dare yayi kowa a gajiye yake babu abinda yake buƙata sai bacci , kayan jikina na cire na ɗaura zanin bacci , Amisty kuwa da kayanta tayi kwanciyarta , Tunda na kwanta fuskar Dikko kezomin a idanuwana , ya ƙara kyau abu ga farar fata ga hutu ga gayu gemunshi yasha gyara sai kyalli yakeyi , an gyara ƙasimbar ta kwanta sosai dake farine sai abun ya bada wani irin sirrintaccen burgewa , shi ba wani tsoho ba amma dole sai ya zama tsoho me yasa yakeyin haka ne ? Dan yaga gemun yana mishi kyau gaskiya fa yayi mishi kyau shi yasa yake ɗaukar hankalin mata , gemu da ƙasimba make up in maza kenan... Ajiyar zuciya na sauke tare da gyara kwanciyata , damuwa nakeji sosai ina ta ƙoƙarin molaƙe rayuwata ashe shi Dikko yana can yana ƙoƙarin gyara tashi , zaiyi aure ya barni ina cikin karuwanci , ina ganin zan masa rata ashe shine zaimin rata , ya zama shugaban al'umma ta wani gefen ni kuma na zama shugabar rusa rayuwar farin cikin wasu da tawa rayuwar ? Hawaye ya cikamin ido bayan sun gangaro na maida numfashi dakel sannan naci gaba da zancen zuci ! Me yasa na zaɓi na zama karuwa ? Me yasa banyi ƙoƙarin zama ta gari ba ? Mai makon na zama waraka ga al'umma sai na zama cuta a garesu... Kukan zuci naci gaba dayi irin mai kartar zuciyar nan wanda kesa mutum yaji kamar zai mutu shi naci gaba da yi numfashi na naji yana ƙoƙarin fita daga jikina dolena na tashi zaune da sauri naci gaba da fita dan ceto tawa rayuwar.... Zaune yake ya hakince irin zaman nan da yakeyi na ya raina mutane , ɗage yake kallon kowa yayin da bakinshi ke motsawa a hankali cikin kwarewa da goguwar iya cin cingom , Al ' Ameen ya kalla sannan ya kalli agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunshi yace wai mema zance mata idan tazo ? Murmushi Al ' Ameen yayi tare da shafa kanshi yace tuba nake ranka ya daɗe , dan tunda akayiwa Dikko kyautar Sadiyya bai taɓa zuwa ba sai yau , baya ko waya da ita yauma Dadynshi ne ya matsa mishi shi yasa yazo ! Dan ko hotunansu dake yawo a social media haɗawa akayi bashine da ita suka jera suka ɗauka ba , Dikko baiyi magana wa Al ' Ameen ba Sadiyya ta shigo cikin palon , gaisheta Al ' Ameen yayi sannan ya fita... Cikin karairaya da kwarewa da bariki tayo inda Dikko yake zaune , ɗan taɓe baki yayi a zuciyarshi yace bari inga rashin kunyarki , bai gama tunani ba ta zauna tare da ɗora kanta a saman kafaɗarshi tana mai sauki ajiyar zuciya cikin yanayin mai nuni da tana cikin shauƙi, daga waje har ciki Dikko baiji wani shock ba , dan haka yace sauke kanki mace bata hawana , na miki uziri nayau idan kika sake zaki samu matsala.... A shagwaɓe tace haba diye { dear } ... Yanayinka sch ne amma ya kake abu kamar class ? Banza Dikko yayi baice komai ba , jinyayi shiru yasa tace ya hanya da mutane ne ko ? Nan ma bai bata ansa ba , zagba surutu taci gaba dayi tare da cewa idan sukayi aure zata mishi soyayya , ba komai kake ta wani jan allo dana fara rubutuna zaka sauke , hauka dai tayi ta zuba mishi tare da son ƙara kwanciya jikin Dikko amma abun ya mata girma , Bayan ta gaji da surutun tayi shiru , can kuma taci gaba , kasha drinks mana , ta ci gaba da lissafo duk abinda aka kawoma mashi , har ta gaji ta sake ɗaukewa , ganin Dikko bazaiyi magana ba yasa ta fashe da kuka cikin kuka take cewa haba Yaya wai me yasa baka so na ne ? Ina ta magana amma kamin shiru ka mayar dani kamar wata mahaukaciya ! Nifa "yar uwarkace ka soni dan Allah kodan zumunchin dake tsakaninmu.... Kallonta yayi sannan yace ya isa , kije ki kwanta a gajiye nake muyi magana anjima , goge hawayenta tayi tare da cewa ai ko na kiraka ma baka ɗauka , karki damu zan ɗauka insha Allah , murmushi tayi tare da miƙewa cikin farin ciki , shima murmushin yayi zuciyarshi tace dama An matane a wannan yanayi , wata "yar jakace a gefenshi ya nuna mata yace ɗauka... Ɗauka tayi babu ko godiya ta fice a palon , wayarshi ya ɗauka ya nuno hoton Sultana , ya ɗauki tsawon lokaci yana kallonshi bayan wani lokaci yayi magana a bayyane cewa kuka kikayi , ina gane yanayin farin ciki da damuwa idan na kalli hotonki , duk yanayin da naji na shiga tou kin shiga yanayin meke damunki ne ....? Banda ajiyar zuciya babu abinda nake saukewa har yanzu zaune nake ban kwanta , ɗan ɓata rai Dikko yayi a daidai wannan lokacin ya kalli hoton Sultana sannan yace ki daina damuwa ki zama mai farin ciki a ko wane lokaci , taɓa screen in wayarshi yayi tare da cewa kiyi bacci cikin aminci da salama .... Ajiyar zuciya na sauke tare da komawa na kwanta , ban daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗaukeni , ..... Koda Dikko ya koma masauki wanka ya farayi duk saida ya gama abinda yakeyi sannan ya cire wayarshi daga airplane mode , kamar wani munafiki wai ba'a kunna waya sai dare sosai zai duba saƙon da aka turo masa , a lokacin zai shiga yanar gizo , a lokacin zai ansa waya idan aka korashi itama sai wacce yakeji zai iya ɗauka , da zaran kuma ya gama abinda yake zai sake rufewa sai kuma wani daren , wayarshi ɗaya kuma da ake samunshi ba kowa yake da number ba , daga gidansu saida wanda shine yaga dama ya bashi , dan dayaji an kirashi da wayar to yasan kirane mai mahimfaci , Wani vidio ya buɗe da abokinshi ya turo mishi , kafin vidion ya buɗe ya fara karanta rubutun ƙasan vidio da akayi , _Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , Allah yayiwa Fatima rasuwa sakamakon fyaɗe da akayi mata , abun babu kyan gani kuma ko su waye da gayya sukayi mata sun wulaƙanta yarinya bataji bata gani ba , sannan suka ɗauki vidio a waya suka bada wayar a cikin envilop aka kaiwa Babana har Office dan lokacin kwananta ɗaya da yini ba'a ganta ba , gawar kuma suka zo suka jefar a ƙofar gida..._ La'ilaha illa anta sub'hanaka inne kuntu minaz zalimeen Dikko ya furta a lokacin daya gama karanta saƙon ya fara kallon vidion , ƙattin maza ne sunkai su biyar amma duk sun rufe fuskarsu da maX , ihu Fatin keyi amma babu abinda ya damesu kowa burinshi ya biya tashi buƙatar , wani irin motsi Dikko yaji kwalwarshi tayi kanshi ya yamitsa da sauri ya ajiye wayar tare da dafe kanshi da dukan hannuwanshi biyu abinda yakeji da game da Sultana ya dawo mishi sabo.... Lahaula wala kquwwata illa billahil ' aliyyil azeem , Dikko yake ta maimaitawa ya ƙurawa kafet ido kamar Sultana ce a wurin , saida natsuwa tazo mishi yaci gaba da zancen zuci lallai ya cuci rayuwar Sultana shima bashi da banbanci da mutane biyar ɗin nan domin magungunan daya sha sun bashi wani irin ƙarfi wanda ko allura hauka akayi ma doki iyakar abinda zaiyi kenan dan nuna shi mai ƙarfi ne , hawaye ya cikawa Dikko ido tausayin Sultana ya ƙara kamashi lallai ya cuci yarinyar nan ! Yau wane irin baƙin ciki iyayen Fatima suka shiga ? Wane irin ɗaci sukeji idan sukaga wannan hoto ? Ya Abbakar zaiji yayin daya ga wannan hoton akan ƙanwarshi ? Da nine ya zanji idan haka ta kasance akan ahalina ? Kwantar da kanshi yayi a saman hannun kujara ya rufe idanuwanshi duk yanda akayi akwai abinda Baban Abbakar yayi suka ɗauka fansa dan yanayinsu ya nuna a lokacin da suke aikatawa kamar biyan bashi ne sukeyi , Allah na tuba ka gafartamin ka sakawa An mata soyayya ta mai girma a zuciyarta , sona ya hanata bacci da tunanin kowa a duniya saini , ta daina jin maganar kowa sai tawa , ka saka mata san kasancewa dani inuwa ɗaya kasa mata firgici idan ta yini ko ta kwana bata ganni ba , ka ɓadda mata tunanin kowa da komai na duniya saini , ka saka mata san jin muryata ka goge mata kuɗirin fansa akaina , nayi alƙawari zan zamar mata natsuwa zan zama uwa da uba data rasa masu kishinta bazan barta tayi kuka ba haka kuma zanyi ƙoƙarin sakata farin ciki , duk wanda ya ɓata mata ko yasa taji damuwa nine zan tsaya harsai naga tayi farin ciki , Allah ka gafar tamin ka goge damuwata a zuciyar an mata ta zama soyayya mai ban al'ajabi ga kowa , Buɗe idanuwanshi yayi tare da goge hawayenshi , sannan ya ɗauki wayar ya goge vidio ba tare daya gama gani ba , wayar Abbakar ya fara kira dan jajanta mishi kafin yaje mishi ta'aziyya , Sadiyya koda ta kira Dikko text ya tura mata idan ya gama zai kira , koda ya gama abinda yake ba wulaƙanci ba da gaske ya manta da labarin kiran Sadiyya , da tunanin An mata yayi bacci.... Da safe wanka nayi na shirya cikin riga da zani na atamfa , hijabi na saka sannan nacewa Amisty zanje in dawo ! Ina zakije tunda safe haka ? Ta tambayeni ! Takalmi na saka tare da ce mata zanga wani a bakin hanya , addu'ar a dawo lafiya tamin ni kuma na fice daga ɗakin... A ƙofar gida na anshi makullin mota na dana sa aka ɗaukomin , ɗan daba ɗaya na dawo dan ya rakani gidan Alaji koda an samu ɓacin rana , abinda yasa ban tafi dasu Amisty ba saboda kar ya zama naje gyara kuma gyaran ya zama ɓarna..... Tafiya mai nisa mukayi zuwa gidan Alaji , a ƙofar gida nayi parking sannan na fara kiran wayarshi dan dama banzo ba saida izininshi......... 09/09/2019 *JAMILA MUSA.....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 29 Bai ɗauka wayar ba ya fito daga cikin gidan , ina cikin mota zaune nima ban fito ba , shine yazo har wurin mota ya buɗe gidan baya ya zauna amma bai rufe ƙofar ba , juyawa nayi ina kallonshi tare da cewa dana kira naji baka ɗauka ba nayi tunani ko baku tashi bacci ba ! Gyara maɓallin rigarshi yayi tare da cewa ai ina ganin kiranki nasan kina ƙofar gida shi yasa nace kawai bara na fito basai na wani tsaya ɗaukan waya ba , murmushi nayi na juyowa ina kallon gabana wato na juya daga kallon Alaji nace muje ciki to... Tou muje amma bata nan ta shiga maƙota , ɗan zaro ido nayi amma banyi magana ba , a zuciyata nace maƙota tun wannan safiyar ? Lallai akwai ƙatuwar matsala , sauka nayi daga cikin motar tare da cewa muje *Wane Yaro* ɗan daban da nazo dashi , Rufe mota ta nayi muka nufi cikin gidan dukanmu , a ƙaton palon matarshi ya saukemu gafa kujeru har kujeru amma datti yasa sun tashi aiki , bakajin wani ƙamshi ko na tsitsiyar ƙamshi bare kayi tunanin zaka samu turaren wuta banda zarnin fitsari palon kaca ² a firgice babu abinda ke tashi sai wani ƙanni² a palon.... Saman hannun kujera Alaji ya zauna ni kuma kallabin kaina na ciro na shimfiɗa a matakalar da zata gangaro dakai cikin palon dan wannan kujerun idan har na hau su yau babu abinda zai hana ƙurajen ƙyama su fito jikina.... Fira muka farayi da Alaji ya ɗan fara karanto min matsalolin da yake fuskata , yace ga ƙazanta ga rashin ragowa ga fita babu gaira babu dalili , ga rashin godiya ko zai kashe kanshi ya bata bata taɓa masa godiya ba , wallahi idan har zai kwanta da ita sai ankai ruwa rana sannan kuma babu wanka bare yayi tunanin zai ji wani ƙamshi da zaisa mishi yaji wani shauƙi yayin da yake kwanciya da ita... Uhum har ga Allah ba sasanci ya kawoni gidan Alaji ba a wannan lokaci , ina da wani ƙudiri nawa na daban , ina so inga yanayin yadda yake hidima da gidanshi , surutar da matarshi take amfani da ita kuma har store insu yau sai naje dan inga idan naci gaba da tarayya da Alaji zai iya ɗaukemin duk wasu buƙatu na ? Dan nima in samu wanda zai tayani kula da tawa rayuwar , zan kuma bigi cikin matarshi ta faɗamin komai nasu da wasu sirrika na Alaji daga nan ni kuma zan ɗaukeshi sai tayi da gaske ma zata sake ganinshi... Babu ko sallama ta faɗo cikin ɗakin daga ita sai ɗaurin gaba hijabinta riƙe a hannunta , Abbu Afsar ka tashi kenan ? Bai kalleta ba yace na tashi daga ina kike ne ? Kallona tayi sannan tace wallahi gidan Naja naje tace zata shigo bata samu damar shigowa ba kusan kwana biyu mijinta ya hanata fita shine nace ta bari ni nazo , kallonta Alaji yayi tare da cewa ita da bata raina mijinta ba ! Ya hanata ta hanu ke kuma da kika raina naki sai kika fita babu izini na. Tsoki tayi tare da zama saman kujera tana cewa baka gajiya da tsegumi haba da Allah dan naje tou miye ? Murmushi nayi ina mai kallonta , gaskiya kyakkyawa ce sosai , ga kyawu har kyawu amma an kashe kyawun da ƙazanta , yarinyar mace kamar wannan tana zama da ɗaurin gaba , gashin hamatar ta kanshi idan kika kamashi zaki iya kitsashi saboda yawanshi , tana da haƙora masu kyau amma ta kashesu da rashin wankewa , kanta kuwa ƙaramar ƙarya kila yayi shekara rabonshi da a kwance , kitsone saman kan amma baka isa ka gane ta ina aka ɗauko tsagar kitson ba , Tou bamu dai gama maganarmu ba da Abbu Afsar Ummu Afsar ta shigo gidan , tsokin da tayi masa yasashi tashi ya fita daga ɗakin , ina kwana na gaisheta , ansawa tayi tare da fyace majina da gefen zaninta , sannan tace ban gane ki ba , Uhum ai baki sanni ba na faɗa ina sadda kai ƙasa cikin nuna mata ni ta gaskiya ce tunda nasha hijabi daga sama har ƙasa , kallona tayi sannan tace Allah sarki sannu da zuwa , ki dawo saman kujera mana ! Nan ma yayi na bata amsa , bara na kawo miki ruwa , tou na faɗa yayin data miƙe tabar palon , babu wani ɓata lokaci ta dawo da wasu irin haɗaɗɗin kulololi masu matuƙar kyau da tsada , ta wuce taje ta ajiyesu a saman tebirin cin abinci , Saida ta ajiye sannan tace bisimillah mana , ta faɗi maganar cikin sakin fuska , banyi magana ba na tashi na nufi tebirin cin abinci yayin da Wane Yaro ya zauna a wurin dana tashi , Kujera taja itama ta zauna kusa dani sannan muka sake gaisawa, ɗora hannuna nayi saman kular da take ƙoƙarin buɗewa nace suna na *Sultana* ɗiya ga Aliyu Muhammad Binna , Babana sananne ne kuma ya shahara a harkar caca , dani da Babana da kowa nawa muna zama a gidanmu cikin kwanciyar hankali , nazo wurinke dan gyara miki wani kuskure Allah dai yasa banyi shishshigi da yawa ba..... "Yar gajeriyar dariya tayi sannan tace ke kuma me yace miki nayi masa ne ? Kallonta nayi sosai dan na fahimci yanayin rayuwar tata , bata da babbar ciwon dake damunta wanda ya wuce rashin ɗaukar shawara , tana da taurin kai sannan kuma abinda taga dama shi takeyi babu wanda ya isa ya sa tayi ko ta bari sai ciwon rashin wayau dake ɗawainiya da rayuwarta... Kauda kaina nayi daga kallonta sannan nace ni bai faɗamin komai ba , gyara zama tayi tare da cewa baya da aiki sai kai ƙarata bana san wanka bana shara bana goge ɗaki ban iya girki ba , ban iya kwanciyar aure ba , cikin hayani tace yaje ya nemo wacce ta iya duk wannan abun dana lissafo ban iyaba ta ƙarasa maganar da dukan tebirin data ajiye kulolin da ƙarfi... Cikin tsoro nace saurara kiyi haƙuri ba hayani ta kawoni ba , shin ko kina fama da matsalar rashin abinci ne ? Ko rashin sutura sabun wanka ko na wanki ? Rashin turare ko man wanke baki ? Cikin ɓacin rai tace babu abinda na nema na rasa dalili dai bazai yuwu ba kullum namiji yayi ta sussukata ni ba gero ba , Dariyar mugunta nayi mata tare dayi mata kallon wawiya , data riƙe mijinta ram a hannu da bai kallo matan waje ba , wannan ba matsalar Alaji bace itace ta kai mijinta ga halaka , na rasa abinda yake damun matan ƙarshen zamani , babu biyayyar aure ba ladabi mace ta mayar da mijinta kamar almajirin gidanta baida wani mutunci ko daraja a idonta.... Yake "yar uwata ki sani aure yana da babbar matsayi haka kuma namiji yake da babbar daraja , mijinki shine sirrinki suturarki aljannarki sai kin gyara rayuwar aurenki sannan zaki samu rayuwa mai daɗi a gidan duniya da ƙiyama dan miji ba abin wasa bane , mijinki ba abin wulaƙantawa ba ne sannan kuma mijinki ba abokin gabarki bane , abin ƙauna ne abun tausayawa ne a gareki , ki kwantar masa da hankalinsa sai Allah ya kwantar miki da naki , ki bashi natsuwa sai Allah yasa kema ki samu natsuwa , kisa mishi farin ciki sai Allah yasa kiyi farin ciki a gidan duniya da lahira.... Matan bariki suna da illa kuma suna tattare da masifun dasu ma kansu basu san suna dasu ba , bariki wuta ce mai azabar raɗaɗi da wahala , zina halakace kuma babbar cutace , me matan barike suke dashi wanda baku dashi ne ? Komai iri ɗaya ne abu ɗaya suke dashi wanda matan aure suka rasa , kuma suma matan auren suna da abu ɗaya wanda matan bariki basu da irinshi ! Wannan abu ba komai bane sai sakaci , shine abinda matan aure garesu , matan bariki kuma basu dashi , matan bariki basu da sakaci abinda matan aure suka rasa kenan... Ummu Afsar ta saki baki ga wacce bata sani ba taci gaba da buɗemin sirrin mijinta wanda haka ba daidai bane ga duk macen data san abinda takeyi , ɗakinta da tsore inta babu inda bata kaini ba dan in gani da idona tana da komai na rayuwa tsaftarce da haƙƙin Alaji bazata bayar ba , tunzura ta nayi tare da cewa Eyy ki barshi gaskiya gaki ma yadda kike kyakkyawarki ko kun rabu sai kin samu wanda yafi shi , murmushin jin daɗi tayi tare da cewa ai cewa ma akeyi nafi ƙarfin shi , kallonta nayi tare da cewa gaskiya keɗin duniya ce da matsayin gidan sarauta... Sallama mukayi da ita tayomin rakiya har ƙofar gida inda nayi parking in motana , saida na fara tafiya sannan nasa Wane Yaro ya kiramin wayar Alaji , bayan ya ɗauka nace masa ina san ganinshi amma ya faɗamin sirrintaccen wurin da zamu haɗu , bayani yamin sannan nace masa na gode tare da kashe wayata... Kai tsaye gida muka nufa a bakin hanya na ajiye Wane Yaro ni kuma na wuce gida , a ƙofar gida nayi parking in mota ta na shige ciki , sallama nayi kamar yadda na saba na wuce ɗakina , ruwa na zubo a boket naje na watsa sannan na dawo ɗaki nayi kwanciyata dan hutama rayuwata.... Bayan sati biyu , abubuwa da dama sun faru , ga lamarin iskanci na kuma yanzu na zuƙa hannu na , Babana kuma ya samu mage kamar yadda malam yace kuma ya aiwatar da aikin kamar yadda akace yayi , Na samu Alaji munyi magana dashi kuma ya faɗamin cewa yana san wayayyar mace "yar gayu wacce zata biya masa buƙatarshi a duk lokacin daya so , ba laifi yana da wanka kuma yana gayu kuɗinshi a sake yake ga mata , dan haka na ɗaura dashi cewa ya saurareni ina san na haɗa gidanmu sannan naci gaba da harkar bariki na, Da alkairi na nake shiga cikin ahalinmu , nakan basu kwance kaya , in siya musu kayan kwalliya idan na samu kuɗi , ina aika musu da kayan abinci kuma ina zuwa lokaci ² ina basu sha'awa kuma cikin hikima na fara musu tallar bariki , Duk wata hidimata yanzu Alaji shike ɗauke da ita , babu abinda na nema na rasa fanni abinci kuɗin kashewa da kuma suturu ya kwacemin duk wani abinda zaizo ya dameni , yauma ƙaton rago ya kawomin dan haka na sakashi a napep na tura Wane Yaro yakai gidan Baba ƙarani da 100k nace ya sayi icce... Babana kenan , ɗan duniya abin alfahirin uwar ɗakin kwarata , cikakken namiji mai dogon zamani , namijin duniya gatan mata , ka gansu ka ƙyasa ko ba sisinka su bika , baka gada ba haye kayi Sultana tai gado ɗan gado kuma saiya zarta..... Uhum Baba kenan , Amisty ce kwance a saman Baban Sultana suna ɓalgacewa bayan sun gama ɓalɓalewa yake tambayarta ya Uwar masu gida ? Tace tana nan cikin ƙoshin lafiya , Amisty itace take kaiwa Baban Sultana labarin halin da Sultana take ciki , kuma shine ya tirsasawa Amisty ta kwashe kayanta ta dawo zamani dan kawai ya riƙa jin halin da nake ciki , abin kunya Baba ka rasa macen da zaka huta da ita sai abokiyar "yar ka , dakai da Amisty duk ranar da Sultana ta gano ku zaku fuskanci babbar matsala.... Lokacin da Baba ƙarami yaga rago abun ba ƙaramin burgeshi yayi ba dan babu biki ba suna kuma ba sallah kawai an bashi kyautar rago , yaji daɗi sosai a lokacin da Wane Yaro yaje kai rago ya samu Zainab da Farida a gidan dan haka daya tashi zai dawo suka biyoshi zuwa wurina... Nayi farin ciki da ganin "yan uwana , muka rungume juna cikin soyayya irin ta "yan uwan da suka daɗe basu haɗu ba , sannan muka shiga jajantawa juna yaushe rabo ? Bayan an gama suka tambayeni ko na fara kasuwanci ne ? Dariya nayi tare da ce musu sosai ma , me kike siyarwa ne ? Suka tambayeni kai tsaye nace *Karuwanci* shine sana'ar da nakeyi... Zasu fara wani mamaki nace karku wani damu kuma kar kuyi mamaki nayi amfani da huɗubar da Baba yake baku ku tashi ku nemi kuɗi domin ku kare mutunci kanku , huɗubar ce na ɗauka kuma da ita zanyi amfani kuma ma babu laifi an samu nasara tunda na siya gida ga mota kuma ina da "yan canjina , ku kun samu gida da mota ne ? Na tambayesu , shiru sukayi , murmushi nayi tare da cewa karku damu ƙanwarku ta kasa kuma ta samu masu siya nayi ciniki sosai dan haka kawai ku dawo nan muci gaba da zama dan tunda na siyi gidan na fitar da ɗakunan matan Baba shima Baban zan dawo dashi dan kasuwa bata yuwuwa babu shugaban ƙungiya.... Gaba ɗaya wutarsu ta ɗauke musu basu da zaɓin daya wuce su dawo zama tare dani tunda inda suke a raɓe suke , koda suka tashi tafiya na basu kuɗi na basu kayan sakawa , sunyi godiya sosai tare dacemin insha Allah zuwa jibi zasu dawo , rakiya nayi musu suka tafi... Baba ƙarami da jama'ar dake da sauran mutunci a idon Babana sune suka sameshi suka bashi magana cewa ƙauracemin bashi ne zaisa nayi halayen kirki ba , ya dawo kusa dani wani abun ma a gaban idonshi bazanyi ba , Baba yace shi ba wani abu yakeji ba kawai kunyata yakeji ya zama sokon uban daya kasa ceton "yarshi daga shiga wata baƙuwar rayuwa ! Magana suka ba Baba harya amince zai dawo gidana , kuma yaje wurin Maman Fa'iza suka ce zasu dawo suma jibi idan Allah ya kaimu dan haka gida zai dawo kamar yanda yake da , su Nana Karima da suke zaune a gidan kuma bazan tada su ba saidai idan sune suka tashi da kansu... Da marece ina kwance Amisty ta shigo ɗaki babu sallama , jakarta ta ajiye ta ɗauki buta ta nufi bayan gida , tana fita na tashi da sauri naje na ɗauko jakarta na buɗe , kuɗine masu yawan gaske a ciki dan haka na tattarasu gaba ɗaya na kwashe su na ɓoye sannan na koma saman katifa nayi kwanciyata kamar yanda nake daga farko... Ban daɗe da kwanciya ba ta shigo tare da cewa tashi gidansu Hafsa zamuje bata da lafiya , subahanallah na faɗa tare da tashi zaune nace meya sameta haka ? Ƙonewa tayi ta faɗi maganar tare da ɗaukar jakarta , nima tashi nayi banko ɗauki gyale ba makullin mota kawai na ɗauka tare da cewa muje , tunda nake ban taɓa zuwa gidansu Hafsa ba sai yau zan fara , a tsakar gida nayiwa su Nana saina dawo sannan mukayi waje dani da Amisty... Daga ni sai Amisty muka tafi ni naja motar har muka isa gidansu Hafsa , har zanyi parking a waje Amisty tace inyi horn za'a buɗe , banyi musu ba na dannan horn mai gadi ya kwashe mana get muka shige , kusa da motar Hafsa anan nayi parking in mota ta sannan muka shige ciki... Har muka isa ɗakin Hafsa bamu haɗu da kowa ba , palon ɗakinta ma ba kowa dan haka bedroom muka shiga kai tsaye , Hafsa tana kwance a saman gado an naɗe ƙafarta da farin bandeji , idonta a rufe kila tanayin bacci ne , zanyi mata magana Amisty tace karki tasheta bacci takeyi , banyi magana ba na samu gefen gado na zauna , palo Amisty ta koma babu jimawa ta dawo ɗauke da wata ƙatuwar roba bansan ko miye a ciki ba , wurin ƙoƙarin ta hawo saman gado ta ɓareminshi kaf a jikina , tsakiyar idonta kaɗai na kalla na gane wannan abun shiri ne , Kallon kokon data makomin a jiki nayi sannan na sake kallonta , kiyi haƙuri Amisty ta faɗa , ba koma nace cikin sanyi jiki dan Amisty tsoro take bani , cikin sigar lallashi tace ki shiga toilet saiki wanke , banyi magana ba na miƙe na nufi inda Amisty ta nunamin da ɗan yatsanta , kokon gaskiya baya wankuwa gefe² dole sai na cire kayan nayi wanka gaba ɗaya dan babu inda bai kai ba , Cire kayana nayi nai wanka , bayan na gama na wanke kayana na ɗauro towel na fito da kayan a hannuna da niyar ince a ina zan shanya ? Ina fitowa naga Hafsa tana rufe ƙofa da makulli bayan ta gama ta tillashi can saman waldrop , bayan ta tilla ta warware bandejin sannan tace hausawa sunce mai haƙuri mawadaci nasha haƙuri kuma na daɗe ina dakon yunwa da ƙishirwa , yau zanci insha zan kore duk wata tsohuwar yunwar dake cikin hanjina... Dariya sukayi tare da tafawa ita da Amisty.... Amisty ta ansa da cewa lallai zamuga wasan kura ga uwar kwarata gata lesbian , Hafsa tace tabbas yau zan koya mata irin namu salon tunda muma ta koya mana irin nata , a'uziyya naja tare da ƙara riƙe towel in jikina gam , murmushi Hafsa tayi tare da cire rigar jikinta tace kinga sheɗan baya tafiya gashi ma ya fara cire rigar jikina , kin gani ta faɗa yayin da ta ɓalle bireziyarta , ja baya na farayi da niyar komawa toilet ina ihu a kawo min ɗauki *kwarata* sun rufeni a ɗaki , Dariya Hafsa tayi tare da shan gabana tace ina zakije ne ? Kuma babu mai cetonki dan gidan ma babu kowa , shi yasa nace Amisty ta kawomin ke kwana biyu zakiyi kawai kafin nan nasan kema kin zama "yar hannu... A saman bedsite naga kwalbar mai mai gurguwa dan haka da sauri na yada kayana na ɗauka na kwaɗawa Hafsa a kai harsai da jini ya fita , ajiyar zuciya ta sauke tare da fizgoni tace nagode ta ƙarasa maganar tana ƙoƙarin haɗa bakina da nata , da ƙarfi na tureta naci gaba daba da ihu ina kai mata duka , kwata ² bataji dan haka ta janye towel in jikina , ita da Amisty suka kamani mukaci gaba da kokowa da ƙarfin bala'e suka ɗorani saman gado..... 11/09/2019 💅🏻 *MEELAT MUSA NE....* ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 30 *_Ina miƙa saƙon ta'aziyya ga "yar uwar aikinmu Halima Yahya 20 Allah ya bada haƙurin rashi ubangiji yasa ta huta Allah ya kyautata namu ƙarshen idan ajaliyyarmu tazo...._* Amisty ta danneni da ƙarfin tsiya Hafsa ta sauka dan ɗauko igiyar da zasu ɗaureni da ita , murmushi nayi tare da kallon Amisty sannan na nunata da yatsa na juya na kalli Hafsa itama na nunata da yatsa sannan na gaggaɓe da wata irin dariyar dani kaina bansan na iyata ba , Lokaci guda kuma na ɗaure fuska kamar bani nayi dariyar ba , da sauri Amisty ta kalli Hafsa suka kalloni a lokaci ɗaya , hawo saman gadon Hafsa tayi tana ƙoƙarin riƙe hannuna ta ɗaure , kallonta nayi kamar wata sakara sannan nace dake da Amina ku tabbata idan har kuka min wani abu kasheni shine kawai mafita a rayuwarku , amma na rantse da girman Allah wanda ya halicceni ya halicceku dani daku dukanmu shi muke bautama , mutuwa ta ko taku zata iya zuwa ko wane lokaci yanzu ko anjima , ko kuyi ko ku bari yanda kuka buɗemin sirri saina buɗe sirrin uban kowa a cikinki , Bayan buɗewa saina tona musu asirin da ku kanku sai kunsha fiya² kun mutu saboda baƙin ciki , kar wacce ta ɗauremin hannu ko ƙafa kuyi duk iyakar iskanci da kuka iya , bashi ne kuma bazaiyi kyau ba a lokacin da zan biyashi akan iyayenku , Muni , baƙin ciki , firgici , tashin hankali gaba ɗayanku zaku fuskance su yayin dana shigo rayuwarku , ina da illa kuma ina da bala'en haɗari haka nake dasa baƙin cikin da baya mantuwa a zuciyar duk wanda ya nemi ya dasa baƙin ciki a rayuwata , ciwo gareni haka nake da ɗaci kuka akemin kamar mutuwa yayin da na shigo gida dan ruguza farin ciki zuri'a ɗaya , ku lasa ku maida miyanku tunda kun buɗa ni kuma nayi alƙawari daga yanzu rayuwar farin ciki ta ƙare gareku , Kallan kallo suka tsaya yi kowa da abinda take saƙawa a zuciyarta , tsoki nayi tare da cewa kuna ɓatamin lokaci domin ni ruwan ƙorama ce zuwa nake da ƙarfi na tafi idan kuma na tashi tafiya nakan tafi da abu mafi soyuwa ga al'ummar gari za'ayi ta tunani na har shekara ta zagayo ba'a gama wani kukan ba zan sake caɓar wani abun inyi gaba dashi haka mutane zasuyi ta kuka dani har ranar da mutuwarsu zata riskesu , dake da dake duk wanda na bari a cikinku ya huta ban yafewa kaina ba... Dukan ƙofa akayi da ƙarfi tare da cewa Hafsa me kukeyi kuma ? A shagwaɓa tace Mom ya akayi kuka dawo ne ? Ƙara dukan ƙofar tayi tare da cewa ni banje ba tunda na shigo nakeji ana ihu *kwarata* wai me ke faruwa ne ...? Dukansu shiru sukayi , ci gaba tayi da dukan ƙofar tana cewa wallahi idan kika bari na buɗe ƙofar nan da kaina zaki ci ubanki.... Cikin yanayin ɗacin rai Hafsa ta kalleni sannan ta sauka ta fara ƙoƙarin saka rigarta a lokacin har Mom inta ta zuro makulli ta waje ta fara buɗe ƙofa... Murmushi nayi da gefen bakina nima na sauka daga saman gadon na ɗauka towel in na ɗaura , ban gama ɗaurawa ba ta shigo ɗakin , kayana na ɗauka da makullin motar na raɓa ta gefenta zan fita , riƙoni tayi tare da cewa ke daga gidan ubanwa kika zo nan ke kuma....? Ko kallonta banyi ba da nace mata daga gidan ubanta nake , bakiji ina miki magana ? Kema nan dako haihuwarki ba'a gama ba har kin iya iskanci haka ? Kallonta nayi sannan na faɗa mata kaf abinda ya faru na ɗaura da cewa kuma na rantse da girman Allah saina rama , Haƙuri ta fara bani , niko nace dama kin adana kalmomin haƙurinki kila zasuyi tasiri a lokacin da "yarki ta fara halbe²n mutuwa , ina faɗin haka nayi gaba , a palo naga wata ƙatuwar hijabi dan haka na ɗauketa nayi gaba , a ƙofar palo na saka sannan na wuce inda na ajiye mota ta , ina zuwa na shiga naja cikin gudun tashin hankali nabar gidan kamar babu rai a cikin motar... Tuƙi nake bansan inda nake bi ba , domin idona cike yake da hawaye yayin da hankalina da zuciyata suka tafi tunanin hanyar da zan samo iyayensu Amisty dan babu hanya mafi muni da zan saka musu inba inyi iskanci da iyayensu ba kuma in ɗauka vidio in tura musu... Wani irin wawan burki na taka dan ban lura ba traffic ta riƙeni , tsayawa nayi tare da sauke gilashin mota ta ina kallon wata mace data bugawa wata mota itama dai masiffiyace itace take da laifi amma sai rashin kunya takeyi , Kyawawan motoci ne masu tsada kuma ta kashe musu fitilar baya kuma sai zagi takeyi tana cewa idan sunajin su wasu shegune itace maganin "yan iska sai an biyata motar ta data goge , tunda sune sukayo baya , duk wanda ya bata haƙuri sai tace batayin haƙuri uban waye ma ake tuƙawa a motar ? Daga ciki aka sauke gilashin motar ya sauka a hankali , Dikko na faɗa tare da ƙarasa sauƙe gilashin mota ta dukanshi , matsawa matar tayi taci gaba da zazzagawa Dikko rashin mutunci , kuma ya hana kowa yayi mata magana , murmushi nayi tare da ɗaga kaina na kalli danja har yanzu ba'a sakemu ba , amma waccan wawiya ce da tasan Dikko da bata shiga rayuwarshi ba Allah dai yasa ba a gidan haya suke zama ba suma... Ina tunani naga ta juyo tana kuka kome Dikko yace mata Oho su kuma an sakesu sun wuce , ɗaga gilashin motar nayi nima ana sakinmu nabi bayan motar matar da gudu dan ina so inji abinda Dikko yace mata take kuka , Itama gudu takeyi sosai nima na take tawa sosai , muna samun sarari na shiga gabanta , dole ta tsaya har yanzu tana cikin ɓacin rai , fitowa nayi daga cikin mota ta ko takalmi ban tsaya sakawa ba , na nufo motar matar har yanzu kuka takeyi , gidan gaba na buɗe na zauna , kallona tayi tare da cewa lafiya ? Cikin yanayin damuwa nace abinda aka miki ne baimin daɗi ba shi yasa na biyoki in baki haƙuri me ya haɗaki dashi ne ? Cikin ɓacin rai tace ɗan iskan yaro ne gashi da siffar mutanen kirki amma baida mutunci , kuma baida kunya ko kaɗan , driver inshi ne yayo baya ya gogi motana ni kuma na kasa haƙuri na fita nayi musu magana shine duk sukamin shiru , ni kuma nace uban waye ma ake tuƙawa a motar ashe yana ji yana sauke gilashi ni kuma naje wurinshi da niyar ce masa bai kyauta ba shine yace min... Wai kar inmi mishi rashin kunya bayan yasan komai , cukwui da nonon raƙumi nasha aka bani kyautar motar na taho kan titi ina ma mutane ganganci ko an faɗa min titi ɗakin mijina ne ? Ban tsaya naji sauran bayanin shi ba na taho saboda yaci min mutunci da yawa... Lallai Dikko cikakken ɗan iska ne , haƙuri na bata tare da fita daga cikin motarta na nufi mota ta , wato ya yazo gari kuma hali na nan bai canja ba , mota na koma na shiga naja nayi gida , Tun kafin inyi parking naga Nana zaune a saman dakali sai kuka takeyi , ko inda take ban kalla ba na wuce cikin gida , dan har Nana haushinta nakeji saboda abinda su Amisty sukamin.... Wanka nayi tare da sake wanke kayana na bazasu a saman igiya , ɗaki na koma na shirya bayan na gama abinda nake na ɗauko kuɗin Amisty dana sace na fara irgawa , ban gama irgawa ba naji A ` i tana kwalamin kiran cewa kizo ana kiranki a ƙofar gida , Abinda raina ya bani Babana ne dan haka na ajiye kuɗin na fito , a tsakar gida Karima ke ƙyanƙyasa min cewa an saki Nana , idanuwa na zaro tare da cewa innalillahi garin ya ? Nayi maganar a sirrance tare da natsawa kusa da Karima ! Karima tace ai labarin sai kin dawo kije kiji kiran da ake miki , har ga Allah banji daɗin mutuwar auren Nana ba kuma na lashi takobin gyara aurenta da gaskiya , A ` i ta ƙara cewa jiranki akeyi , cema Karima nayi ki jirani ina dawowa , bayan na fito ƙofar gida nacewa A ` i waye yake nema na ? Filin da aka rushe gidaje ta nunamin kallon motar da akayi parking nayi sannan na kalli A ` i nace waye ? A ` i tace wani dattijo ne , wane kala ne ? Fari ne ! Ya yanayinshi yake ? A ` i tace wallahi ban lura dashi sosai ba yaro dai ya turo yace Sultana taje... Kai tsaye na nufi wurin , tunda mu "yan kasuwa ne ina zuwa na buɗe mota na shige naja na rufe garam , shi kuma ya sanyawa motar lock , ko faɗuwa gabana baiyi ba domin dama raina ya bani za'ayi haka , Waye kai ? Na tambayashi domin duhu ya shiga , ni ne , ya bani amsa , kaine wa ? Na sake tambayarshi , *Shekara biyu...* ne ya bani amsa , dama ana ganin shekaru ? Umm idan bakya ganinsu zaki wuce su ? Ɗan gajeran tsoki yayi tare da cewa yanzu ba wannan ba me yasa kike san yawan yin kuka ? Ni banda isashiyar lafiya sai kiyi ta kuka kina taramin damuwa ! Me akayi miki ɗazu ne ? Tou sai yanzu na gane ko waye , murya nabi na ganoshi , me kuma ya sake dawo dakai cikin rayuwata ? Na tambayeshi , bai bani amsa ba ya fara gangarawa da motar yana saukowa , riƙe sitiyarin nayi nace ina zaka kaini ne kuma ? Janye hannuna yayi daga saman sitiyarin baiyi magana ba a daidai lokacin daya sauko ya juya kan mota ta kalli titi... Haba wai ina zakaje dani ne haka ? Ba tare daya kalleni ba yace yi haƙuri An mata yanzu zan dawo dake bazan daɗe ba , shiru nayi , kinyi haƙurin ko ? Ya tambayeni cikin sigar lallashi murya mai kwantar da hankali dasa natsuwa , shiru nayi ban sake magana ba , a hankali yayi tuƙi har muka fita bakin hanya , yana hawa titi kuma ya fara falfala gudu kamar yanda ya saba. Tafiya mai nisa mukayi , sannan Dikko ya sauka daga saman titi yaci gaba da gurzar burji , ganin ɓoyayyar hanya yasa na fara kuka , kallona yayi tare da cewa wai miye ne ? Kina tunanin zanyi miki wani abu ? Ɗan soɓaro baki yayi sannan yace wannan hanyar tafi sauri ne bara mu koma titi tunda kinajin tsoro.. Nidai bana so ka mayar dani gida, kwaikwayo na yayi tare da cewa idan naƙi mayar dake kuma fa ? Sai in barka da Allah.... , murmushi yace An mata kenan waike bakijin kunyar min rashin kunya ? Banaji kai har abunda za'aji ma kunya ne , murmushi yayi bai sake magana ba , Wayarshi ya fiddo yayi latse² sannan ya kara a kunne , bayan an ɗauka yace fito na iso , kashe wayar yayi ya faka motarshi gefen wani gida , Duk dani dashi babu wanda ya sake magana har mutumin ya fito daga gidanshi , saitin Dikko ya tsaya ya gaisheshi cikin girmamawa nima ya gaisheni cikin mutuntawa , ko kallonshi banyi ba ban kuma ansa ba , gyara zama Dikko yayi sannan ya kalleni fuska a ɗaure yace bakiji ana gaisheki , gabana ya faɗi yanayin kallon da yayi min nace ai nace lafiya lau bakaji ba , kauda kanshi yayi sannan yace ya kukayi dashi ne ? Yake tambayar mutumin , Eh babu damuwa amma sai an koma hutu , Dikko yace har yaushe ne hutun zai ƙare ? Mutumin yace saura sati biyar , tsoki Dikko yayi yace ko na barta yanzu ? Cikin girmamawa yace ai matan gidan dukansu basa nan idan dai sun dawo zan kiraka insha Allah , Ba komai sai ka kira ɗin , inji Dikko godiya mutumin yayi sosai cewa yaga saƙo yafa gode sannan ya matsa , Dikko yaja mota muka dawo gida , A ƙofar gida yayi parking sannan yace ki kiyayi dawowa ta iskanci da rashin kunya cike da kai amma babu ilimi ni bana san zama wuri ɗaya da jahili kina ɗawainiya da fankon kai a haka kike tunanin zaki hareni shakaru biyu masu zuwa ? Dan dai zan fita katsina a daren nan amma wallahi dana zaune dake har tsawon sati biyar saina koya miki hankali bakauya dake kina fitowa ko hijabi babu ke ba ɗiyar kafirawa ba , zama saman dakali yawon banza fira da maza rashin kunya da tara "yan daba duk ranar dana waiwayoki jikinki zai baki labari fice ki ban wuri kafin in fara miki rashin mutunci , ya ƙarasa maganar tare da buɗemin motar na fice... Fita nayi daga cikin motar jiki a sanyaye dan duk duniya babu abinda na tsana irin inji an danganta ni da kalmar jahila , kuma ba ƙarya bane jahilarce ni , fita katsina kuma da zaiyi yanzu zaije jigawa saboda an fara shagalin bikinshi ne naji ana ta faɗa , Banda tsoki babu abinda Dikko keyi da ana canja hali daya canjawa Sultana hali , duk duniya babu abinda baya so irin mutumin da baya ganewa , wallahi idan har Allah yasa ya dawo lafiya sai an nemi An mata an rasa idan zata shekara dubu saita ta wadata da ilimi , baida inda zai ajiyeta daya tafi da ita , kuma yana so kusanci mai girma da shaƙuwa ta shiga tsakaninshi da ita , Rayuwarshi da ita ya fara kuma yana so ya kulle da ita , farin ciki da duk wani jin daɗin shi yana hannun Sultana bai taɓa tunani zaiji soyayyarta ko kaɗan ba a zuciyarshi , daya san wannan ranar zata zo da baiyi mata abinda yayi mata a baya ba , Bai ɗauki mace komai ba amma ƙaramar yarinya ta hana mishi sukuni , da girmanshi waishi soyayya zata zo ta dama , kamarshi soyayya zata hana bacci abubuwa suyi ta masa yawo a zuciya , idan An mata tayi fushi ko kuka duk yanaji wannan bala'e kamar asiri..... A ƙofar gida na samu Nana har yanzu bata daina kuka ba da takardar sakinta a hannu , wurinta na nufa dan jajanta ma...... Dikko kuwa yana komawa gida ya ɗauki abinda zai ɗauka suka kama hanyar jigawa...... 12/09/2019 Jamila Musa.... ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 31 *_Gaisuwa ta musamman gareki "yar uwa ta gari fatan alkairi da addu'ar Allah ya ƙara zaman lafiya da ƙauna mai girma tsakaninki da mai gidan ki , RABI MUSA ..._* A damuwance na zauna kusa da Nana dan ina tattare da ɓacin rai da damuwa , ansar takaddar nayi da cewa saki nawa akayi miki ne ? Cikin kuka Nana tace saki ɗaya , tou ina shi mijin naki yake ? Cikin shashshekar kuka tace yanzu ya shiga cikin gida... Tsoki nayi nace tou me yayi zafi haka har ya sakeki ? Ƙara fashewa da kuka Nana tayi saida tasha kukanta har ta godewa Allah nidai ban bata haƙuri ba kuma bance tayi shiru ba saida ta gaji ta rufe bakinta da kanta na kuma sake tambayarta abinda ya haɗa har akayi mata saki ! Aure zaiyi ! Ba tare dana kalli Nana ba nace tou ke ina ruwanki da auren banzarshi da zaiyi ? Saida Nana ta ƙara goge hawaye sannan tace ba auren ya dameni ba matar da zai aura itace ciwona , wace alaƙace tsakaninki da ita da har bakyaso ta zama abokiyar zamanki ne ? Rumtse ido Nana tayi tare da ƙara rurewa da kuka tace *A ` I* zai aura fa , ɗan gajeren tsoki nayi tare da miƙewa nace A ` in banza A ` in wofi ! Da saboda A ` i har kika kashe aurenki ? Kiyi haƙuri Nana gaskiya baki da wayau kuma lokacin dana so na farkar dake daga baccin asarar da kikayi dake dasu A ` i kuka haɗu kuka riƙa cimin mutunci , kin watsa mutuncin aurenki kin lalata rayuwarki kika biye musu suka koya miki maɗigo ,{ Lesbian } ta koya miki kika koya kuma kika iya , gashi yanzu zata aure miki mijin kinga zaki tashi a tutar babu , ba abokiyar iskanci babu mijin aure.. Idan kuma zawarcin kika fuskanta ga "yan mata tsalala sabbin zubi suna yawo a gari suma basu samu sun shige ba , idan maza suna kallon lutsa²n zawarawa wankakki "yan gayu masu ƙamshi da gogewar zaman takewar aure , Nana gaki muguwar ƙaza babu sallah babu salati babu biyayyar aure ki faɗamin wane sakaran namiji zai kalleki bare yayi tunanin jajibar ki ya kaiki gidanshi , Ke kanki baki wanke kanki ba bare namiji yayi tunanin idan ya aureki zaki wanke mishi gidanshi , mazan yanzu sunfi san kwankwashshin mata , masu gogewa wanda zasu gyara masu gida ba su kashe musu gidaje ba , dan mazan yanzu suna kashe kuɗaɗe su gina gida na fita idon duniya , tou yau dake da A ` i wa gari ya waya Nana ...? Kin san zawarci kuwa ? Kai lallai kin tafka babban kuskure aradu... Juyawa nayi zan shige gida Nana ta riƙoni cikin kuka tace ki taimaki rayuwata wallahi ko naje gidanmu korata zasuyi Baba baya san *Zawarci* shi yasa ban tafi ba , tou idan kuma na bashi haƙuri ya mayar dake kika sake jawo matsala fa ? Bazan jawo ba Mother kuma zan ɗauki duk shawarar da kika bani bazan sake tsallakewa ba , Tou zan baki shawara idan har kika ɗauka ba A ` i ba ko uwar A ` i mijinki bazai sake kallo ba bare ya sha'awar aure tunda sun zama maciya amana , Nana tace ngode sosai...., Muje cikin gidan , lokacin da muka shiga har mijin Nana ya gama tattara kayanshi ya fito zai bar gidan , Gabanshi nasha tare da cewa Audu ina so zamuyi magana dakai don Allah , kallona yayi ƙasa da sama yace idan har maganar Nana zaki min bana so , ko Nana autar matace duniya na haƙura da ita , cikin sigar lallashi nace don girman Allah kayi haƙuri ka saurareni , ka bani dama nayi magana dakai na minti biyar kaɗai dan Allah badan halina ba , Tsoki yayi ya koma da baya ya jingina da bango sai haɗe rai yakeyi shi mai gida , murmushi nayi sannan na matsa kusa dashi nace Audu meya haɗaka da Nana ka saketa ne ? Banza yayi ya ƙaleni , ban damu da shirunshi ba naci gaba da cewa tou nidai don girman Allah ina neman alfarma kuma wannan alfarmar ba kowa zaka ma ita ba saini , na roƙeka da girman Allahn daya halicceka ya baka aron numfashi da lafiya , ya baka ji ya baka gani yayi maka hankali , idan har kaji daɗin wannan ni'imomi da ubangiji yai maka kayi haƙuri ka mayar da Nana ... Cikin damuwa Audu yace Sultana Nana bata da mutunci kwata² ina ce duk abinda Nana kemin a gaban idonki , Nana ta rainani itace dakamin tsawa fita ba izini na magana da mazan waje duk wanda nace bana so tanayin tarayya dashi sai ta kafe tayi , rabon da inyi kwanciyar aure da Nana tun muna tsohon gida , na rabata da A ` i taƙi ta rabu da ita , A ` i tana so na kuma tana tausayamin sai in aurota dan ta kwantarmin da hankali na , kuma nace zan auri A ` i sai tacemin bata yadda ba ? Bayan tana san A ` i ta kasa rabuwa da ita tou idan na auro ta ta zama abokiyar zamanta ai duk wata ƙauna ya kare ko ? Duk cikin ɓacin rai yakeyin maganar har wata maganar ma bata fita , haƙuri na bashi saida na tabbatar ya sauka sannan nace tou aurenka da A ` i fa babu fashi kayi aurenka bama hanaka , amma kayi haƙuri ka mayar da Nana dan soyayyar da kake ma manzan rahma S. A. W , Jinjina kai yayi yace in zauna da ita da baƙin halin nata da ƙazantar da duk iskancin da takemin a haka ? Karka damu mayar da ita sauran gyaran duk nawa ne idan bata gyara ba ni da kaina zan ƙaro maka mata sadaki da lefe duk ni zan bayar kuma zan baka jari , tou shikenan na mayar da ita... Godiya nayi mishi sannan nasa Nana ta anshi kayanshi ta mayar cikin ɗaki , nayi musu saida safe , na wuce ɗakina , ina shiga Karima ta shigo tana cewa wallahi banso kika sa aka maida ita ba , banza nayi bance da ita komai ba , ta ƙari kilbibinta naji babu ansa ta fice.... A ɓangaren su Amisty kuwa ina fita Momyn Hafsa ta cire wayar wuta taci gaba da dukansu babu ji babu gani , tana dukansu tana cewa wato na hanaki wannan iskancin bakya bari ko ? Tou wallahi yau saina kashe ki , dama tunda nabar gidan nan na kasa samun natsuwa zuciyata tana saƙamin tunda bana nan nan zaki kawo "yan iska su tarar min a gida , Amisty ganin hankalin Mom ya fita jikinta tana dukan Hafsa har ta daina motsi yasa ta biyo ta bayanta ta fice da gudun tashin hankali , A bakin get ta faɗawa mai gadi Momy ta kashe Hafsa , da gudu ya nufi ɗakin Hafsa , ita kuma ta fice daga gidan , saman Hafsa ya samu Momy tana dukanta tana yaginta duk tayi mata kaca² jini saibin jikinta yakeyi , da sauri ya ciro wayarshi ya kira Yayan Hafsa ya faɗa mishi duk abinda ake ciki dan babu yanda za,ayi ya ɗauke Momy , babu ɓata lokaci ya iso , dakel ya ɓanɓare Momy sannan mai gadi ya kama mishi Hafsa suka tafi asibiti da ita.... A asibiti kuwa likitoci sun tabbatar cewa Hafsa bata mutu ba , dan haka suka shiga bata taimakon gaggawa dan ceto rayuwarta.... Amisty kuwa a gidan Asma'u ta yada zango , tana zuwa wanka tayi Asma'u ta kawo mata abinci taci sannan suka ɗora iskancinsu daga inda suka tsaya ! Tunda safe almajirai suka fara kawo kayan "yan gidanmu a cikin baro , sahu ɗaya yaran sukayi nace idan sun koma suce a samu mota a zubo kayan zan bada kuɗin , Nana na kira ɗakina nayi mata nasiha , cewa ki rufawa kanki asiri ki gyara halayenki , ki zama mai tsabta ki fita daga harkar zaman majalisa kija mijinki jikinki , ki zama mai biyayya da haƙuri a rayuwarki , karki kuskura mijinki ya sake neman haƙƙinshi a wurinki ki hanashi , ko inuwar Audu kika gani ki bashi natsuwa , Tsafta a rayuwar aure itace jigo , kamar yanda baki shiga makaranta dole saida uniform , bazai fa yuwu ba ki gama duk wata fangila taki kisha yawo cikin rana ga kaurin zufa ga warin rana gana haƙi , zaninki na zarnin fitsarin yara ga ƙarnin tunbiɗi babu wanka babu wanke jiki ba sake kaya a haka zakije kice namiji ya kwanta dake ? Wace natsuwa zai samu ? Taya zai samun natsuwar da zai biya buƙatarshi....? To idan zaki gyara ki gyara , ki nemi ruwa da turare sabulun wanka da man shafawa ki fara wanka , ki zama mai biyayyar aure kima mijinki sannu da zuwa idan ya dawo ki masa rakiya idan zai fita tare da addu'ar Allah ya bashi halal inshi , ki gode masa akan abinda ya kawo miki ki kuma yi haƙuri idan bai kawo miki ba , ba kullum ake nema a samu ba , dole wata rana a samu wata rana kuma a rasa , kin dai ga yanda rayuwar take tafiya dan haka ki tashi ki miƙe da gaske ki janye tunanin mijinki daga kan A ` i idan kuwa ba haka ba ta shigo to aradu sai tayi waje dake... Jiki a sanyaye Nana tayi godiya tare da cewa bara in tashi nace da dai kin kyauta ki kuma zuƙe jikinki daga sabgar matan banza , insha Allah Mother ngode sosai , yayi kyau na faɗa tare da cewa zan fita saina dawo , addu'ar a dawo lafiya tamin , ni kuma na irga kuɗi 20K na bata idan an kawo kaya ta sallami masu motar , in an rage canji ta ajiyemin , insha Allah ta amsa min sannan ta fita , nima na shirya na fice ! Anguwar su Amisty na nufa , kafin inkai ƙofar gidansu nayi parking jikin wani shago , amma ina hangen gidansu Amisty , wayata na kallo da take kuka , lambar Amisty ce keta tsalle saman screen in wayata , kamar bazan ɗauka ba na ɗauka dan inje me zatace ! Ina ɗauka ta fara , Tauraruwa mai wutsiya ganinki ba alkairi ba , ciwon tsakar dare mai hana bacci , ance kinje anguwarmu bayan kin sacemin kuɗi me kuma kikaje yini ? Murmushi nayi tare da gyara zamana sannan nace tsauni da ƙaya da tsawon zango maibi da ƙafa sai ya daure , yaro bai ɗaukar yaro dan kansu matsa sai sun faɗi , guguwar tsakar dare ga tsoro ga ban al'ajabi , kura bata cin damisa saidai taci zaki , ki saurari kaidina zuwa gobe kamar yanzu , kashe wayata nayi dan ganin mahaifin Amisty ya fito , Yana wucewa da motarshi nima nabi bayanshi da tawa motar , a hankali yake tuƙi nima a hankali nake binsa saf da ƙafa har ya isa wurin aikinshi , inda yayi parking nima a wurin nayi yana fitowa nima na fita murmushi ɗauke da fuska na nufi wurinshi , Da sallama na isa wurinshi tare da cewa sannu , yawwa ya ansa yana kallona , murmushi nayi tare da cewa naga kamar baka ganeni ba ma ko ? Cikin muryar dattijantaka yace Eh ban gane ba gaskiya , ajiyar zuciya na sauke tare da cewa me yasa baka gane mutane haka ? Murmushi yayi sannan yace to bani sani mana , nace tou sakamin numberka mayi waya dai zuwa dare , babu musu ya ansa ya gwagwaɗamin lambar shi nayi ajiyeta da Lamba shidda , bayan na gama ajiyewa na kirashi yaga tawa sannan nayi masa sallama na wuce , Daga nan ban zame ko ina ba sai Office in Babansu Hafsa , suna da dokoki masu tsaurin gaske dan haka aka hanani shiga , nayi ² aka hanani , lambarshi na tambaya itama dai ban samu ba , dan haka na haƙura na nufi gidansu Hafsa , A wurin mai gadi na samu number bayan na bashi cin hancin 5K , ina ansa na nufi gida , cikin farin ciki nayi sallama dan har "yan gidanmu sun dawo dukansu , amma Inna bata dawo ba , Babana kuma saida dare zaizo , Cikin kulawa nake gaishesu amma kowa sai ya ansa min a wani dusasar , haka nan dai na haƙura na wuce ɗaki na , saida nayo wanka na fito Nana ta shigo ta bani cikon kuɗina tace ta bayar da kuɗin ta sallamesu , godiya nayi mata sannan tace bara ta sharemin ɗakina , nace babu damuwa ta share... Satin "yan gidanmu ɗaya da dawowa amma Babana baizo ba kuma Inna bata dawo ba itama , Baban Amisty da Baban Hafsa munayin waya dasu , kowa ya damu yaushe zamu haɗu dan wayar babu abinda ke cikinta banda zallar sakin layi , har yanzu badai mu haɗu ba kuma sati biyar ya ragemin a lissafin satikan da Dikko yake lissafi.... Mijin Zalifa ma ya matso lamba mu haɗu amma yanzu bashi ne gabana ba , Alaji wato Abbu Afsar shi kuma yana min hidima sosai wacce ta wuce hankali ma , maganar wani abu har yanzu babu wani abu daya shiga tsakaninmu yadai cemin yana so muyi aure na zama abokiyar rayuwarshi niko ba auren ne gabana ba , Zalifa kuma tazo min da labarin mutuwar ƙawar Amisty wacce muka haɗu da ita a station Fadeela wacce tayi cikin shege da aurenta kuma itace ta kawomin Zalifa gidana , ta mutu sanadiyar rataye kanta da tayi bayan tasha gwagwar maya wurin zubar da ciki bai zubu ba , kuma sunje wurin bokaye anyi asiri anyi tsafin amma cikin bai fita ba , kuma anyi ƙoƙarin ɓatar da hankalin mijin dan ya yadda cikinsa ne shima ba'a samu nasara ba , dan haka ta kashe kanta , ... A ɓangaren ango D K yau akayi walima amarya ta tare a gidan angonta Dikko dake G R A { karkara road } , an gina gida na faɗi a faɗin birnin garin katsina , an kashe kuɗi kuma anyi hidima ta kece raini , gida ya tsaru iyakar tsaruwa , iyayen amarya suma sun kashe kuɗi wurin ƙayata ɗakunan amarya da palukanta tunda kuɗi da kuɗi ne suka haɗu abindai sai wanda ya gani , duk inda ka nufa a gari maganar auren Dikko akeyi da gidanshi , gaskiya Dikko mai sa'a ne... Cikin farin ciki ango ya shiga ɗakinshi danshi babu wani abokin daya rakoshi cewa yayi baya so , bayan yayi wanka ya saka jallabi ya nufi ɗakin amarya , itama tayi wanka ta shirya cikin shiga mai kyau da burgewa , a ɗakin amarya yayi alwalla suka gabatar da nafila raka'a biyu dan miƙa godiya ga mai duka , Bayan sun gama sukayi addu'o'in neman zaman lafiya da wanzuwar arziƙi mai ɗorewa tare da addu'ar Allah ya basu zuri'a masu albarka ya kuma kauda sharri da fitina a zaman aurensu , bayan sun gama ya dafa kanta yayi mata addu'a , Bayan ya gama ya koma palo dan ɗaukoma amarya ɗan abinda ya shigo mata dashi kamar dai yanda kowa ya sani anayi , sama ² Sadiyya taɗan lallasa tace ta ƙoshi , shine ya tattara sauran yaje ya zubarwa da karnuka , bayan ya dawo ya wanke hannunshi da bakinshi ɗakinshi ya koma ya sake ciwo ɗama dan shima ya nuna tashi jarumtar a daren farkonshi da matarshi... Itama amarya fitar ango ta ƙara gyarawa ta cuscusa na cusawa ta shafa na shafawa ta kukƙurɓa na ƙurɓawa ta ɗaga katifa ta jera layunta , ango na dawowa itace ta taroshi dan a halin yanzu sha'awar Dikko ta rufe soyayyar da take mishi , Cike da bariki taja Dikko suka sauka saman gado , daga nan labari ya fara canja salo , kowa dai gwanine wurin ganin ya nuna shi wani shege ne , Dikko kuwa a zuciyarshi yake mamakin Sadiyya dan yasan duk macen da bata goge ba a harkar maza tana tsoron namiji bare kuma a daren farkon ta , Yayin da Sadiya kejin daɗin salon Dikko ta yaba mishi ko a haka aka tsaya tasan Dikko namijin duniya ne gaskiya Dikko ya karanci mace yasan duk wasu salo na burge da saka nishaɗi , ya iya sirrika masu tsayawa a zuciya , duk mazan da tayi mu'amula dasu tasan Dikko zakara ne a cikinsu , Soyayya tai nisa ango ya tunkari gidan sarauta , amma me zai samu ? Labari yasha banban domin dai wani ya rigashi hayewa saman kujerar mulki , la'ilaha illa anta sub'hanaka innee kuntu minazzalimeena , lahaula wala kquwwata illa billahi aliyyil azeem , Dikko ya faɗa tare ci gaba da cewa Allah na tuba , Allah ka yafemin , kukan makirci Sadiyya ta fara wani irin kallon tsana Dikko yabita dashi yayin da yake kallonta kamar an mata a daren daya kacaccala mata rayuwa , Yaya DK don Allah ka rufamin asiri yanda Allah ya rufa maka , ka rufe wannan sirrin don girman Allah karka tona min asiri.... Wani irin tashin hankali yazo a zuciyar Dikko ya tsaya yayi ² yayi control in zuciyarshi ya kasa yana ƙoƙarin sauka daga saman Sadiyya matsalarshi tazo , wani iri ihu yayi ya tafi gaba ɗayanshi kafin kace mi ? Tuni lumfashin shi ya tsaya cak..... Wannan itace babbar matsalar dake damunshi da ranshi ya ɓaci sai kawai numfashin shi ya ɗauke.... Cikin ruɗewa ta ɗauki wayarta ta fara kiran Momyn Dikko , babu ɓata lokaci ta ɗauka Sadiyya ta karanta mata halin da Dikko yake ciki , jikin Momy na ƙyarma ta miƙe "ya "yanta suka riƙeta saboda karta faɗi ta samu matsala , kuka ta farayi tana Allah ka tausawa rayuwata idan har Dikko ya samu matsala mijina ya shiga tashin hankali ubangiji ka dafamin a dukkan lamurarra na , meya faɗawa Dikko rai a wannan dare ....? Kai ku sakeni ta faɗi maganar tare da kwacewa ta shiga ɗakinta ta nemo wani magani da ake mishi amfani dashi idan lalurarshi tazo , ko Dadyn bata faɗamawa ba driver ya ɗaukota tayo gidan Dikko dan tasan idan har Dady yaji to idan dai Dikkon bai mutu ba kilashi yana iya mutuwa... Sadiya kuwa tana gama waya da Momy ta sakama Dikko gajeren wando dakel , sannan ta lulluɓeshi da bargo , Babu ɓata lokaci Momy ta iso , Sadiyya ta buɗe mata ƙofa kuma itace tayi mata jagora har zuwa ciki , a ɗakin Sadiyya ta samu ɗanta kwance cikin tausayawa tace meya haɗaku ne ? Sadiyya cikin daburcewa tace ba komai wallahi , Momy tace bazai yuwuwu ba me kikai masa ne ? Fashewa da kuka Sadiyya tayi tana cewa wallahi ba komai Momy , Hmm shine abinda Momy ta faɗa tare da matsawa kusa da Dikko ta buɗe bakinshi ta zuba mishi magani , kamar mai ciwon aljannu haka ya tashi kamar babu abinda ya taɓa faruwa dashi , kallon Momy yayi tare da cewa lafiya kika zo ? Ya ƙarasa maganar yana ma Sadiyya kallon tuhuma , Cikin so da ƙauna Momy tace ba komai yanzu ma zan tafi , zaiyi magana Momy tace ba komai , tana faɗin haka ta fice daga ɗakin da maganinta bata barshi ba , Sadiyya kuma gefe ta koma ta zauna ta rasa inda zata saka ranta dan Dikko ya tsareta da ido.... Tsoki yayi bayan wani lokaci sannan ya gyara kwanciyarshi , idonshi na kallon sama ya rasa abinda ke mishi daɗi , amma yayi alƙawari kamar yanda Sadiya ta nemi ya rufa mata asiri wannan maganar duk duniya babu wanda zaiji kuma babu wanda zai sani , kuma ya zamarshi dole ya zauna da Sadiyya abin family a saketa zuminci zai samu damuwa..... Saukowa yayi daga saman gadon ya nufi ɗakinshi , Sadiyya kuma abun duniya duk ya dameta , sai yanzu take nadamar da bata da rana..... 13/09/2019 Meelat Musa....💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 32 Dikko kuwa yana komawa ɗakinshi wanka yayi , a gaggauce ya shirya bayan ya fito cikin ƙananan kaya , blue in riga da upwhite in wando shima takalmin irin wando ne amma rufaffi ne takalmin , ya naɗe hannun rigar daidai guiwar hannu , turare ya fesa sannan ya ɗauki makullin motarshi ya nufo ɗakin Sadiyya , a bakin ƙofa ya tsaya har yanzu tana nan zaune inda ya barta kamar asara , Kamar ba abinda ya faru dashi ɗazu kuma babu wata damuwa a tattare dashi yace zanje in dawo yanzu ! Cikin jin kunya da kama kai tace ina zakaje yanzu ? Naga har 11:05pm shima kallon agogon yayi sannan yace Ey ai na sani juyawa yayi tare cewa saina dawo bai jira yaji abinda zata ce ba... A wannan dare kai tsaye gidanmu Dikko ya taho ni kuma a lokacin ina zaune saman dakali dani da Alaji muna fira , tun kafin ya fito nasan shine dan tuƙishin yasha banban dana kowa , cikin filinshi yayi parking sannan ya juyo motar ya haskemu da hasken fitila , Alaji dake da matsalar ido ya fara kauce² yana burza idanuwanshi dan gani ke barazanar ƙare mishi... Fitowa Dikko yayi ya zauna saman mota , Alaji kuma miƙewa yayi ya fara laluben hanya dan gaucewa haske , cikin damuwa na kalli Alaji ina gilashin ka ne ? Ba tare da yayi magana ba ya miƙomin makullin mota , da sauri na ansa na nufi motar dan ɗauko masa gilashi , Da sauri na dawo da gilashin a hannuna nace tou saka , bawan Allah hannunshi yana kyarma ya ansa ya saka , ajiyar zuciya ya sauke cewa waye ne ya haska ? Baiga mutane zaune a wurin ba ? Banji daɗi ba gaskiya , haƙuri naba Alaji tare da cewa idan akace kayi hukunci wa mutumin daya haska maka ido me zaka mishi ? Alaji yace wallahi da fitulun motar zan kashe... Shiru nayi ina nazari dan nasan idan har na faso fitulun motar Dikko na sake tarowa kaina fitina , tou amma ai ba gidan haye muke zaune ba , zuciyata ta ingizani in koma cikin gida kawai in ɗauko taɓarya na rusa fitulun kamar yanda Alaji yake sha'awar gani... Kallo Dikko nayi dake zaune a saman mota yana kallonmu tas , gaskiya bana iyawa idan ya riƙeni a wurin can jakin duka zaimin babu wanda yaji kuma babu wanda ya gani , ya dakeni ya daki banza , kallon Alaji nayi tare da cewa barshi ya samu daidai dashi muje ka tafi gida , Rakiya nayi ma Alaji har wurin mota ya shiga , addu'a nayi masa Allah ya tsare hanya Allah ya fisheshi dare , ina tsaye a wurin harya tafi , buzum² na nufi gida dan anguwar ta ɗinke da duhu sosai gashi babu wasu "yan gayu da zasu kunna gen bare su bamu sadakar fitila ɗaya a cikin anguwa muga haske , yanda baki baya ɓace maka a cikin duhu haka ƙofar gidanmu bata ɓacemin dan haka na tunkari gidanmu cikin sauri... Ina ƙoƙarin shiga Dikko ya fizgoni tare da cewa yawwa kwanakin baya kince zaki gauraya dani nine abokin wasar ki yarinya ? Ya faɗi maganar cikin neman fitina idan yaji haushi mi yasa tun a lokacin baiyi magana ba ? Sai yanzu ? Da nayi tunanin babbaka mishi ashariya amma sai zuciyata tace karki biye mishi so yake ya jagula miki lissafi , idan har kika zageshi ko kika faɗa masa baƙar magan akwai wani abu a zuciyarshi , kawai kice masa yayi haƙuri , kinga idan baiba kinsan masifa yakeji... Cike da rashin kunya nace kayi haƙuri amma hakan baya na nuna inajin tsoronka bane a , a , dan ɗan dambe yaja baya ba yana nuni ya tsorata bane gyaran tako ne , a haka zaki gyara takon kina tarayya da makafi ? Baki ba kwalwarki natsuwa ba zance har 11:49pm a haka kike tunanin zaki gyara tako ? Duk macen da tasan abinda take tana cikin gidansu kamar yanzu amma ke kina nan kina balbaɗewa a santa , kindai ji kunya ! Cikin jin haushi nace kaine kaji kunya ƙato dakai kana faɗa da mace , murmushi yayi tare da cewa kindai gane baki iya gauraya da Dikko kenan ? Tunda dai kinji tsorona kin fanshi kanki a daren nan amma dasai na hanaki baccin dare... Jana yayi tare da cewa nima muje kimin rakiya , tirjewa na farayi bazan je ba , kallona yayi sannan yace kifa wuce muje idan ba haka ba kinsan Allah ɗaukarki zanyi , tashi nayi na daina tirje² cikin murya mai saukar da kasala yace muje ya faɗi maganar tare da sakin hannuna , gaba nayi yana bina a baya har wurin mota , buɗewa yayi ya shiga ni kuma na juyo da sauri , shima cin taya yayi ya biyoni da sauri tare da cewa An mata zo zo zo banza nayi na shige gida , saida safe ya faɗa , ko inda yake ban sake kallo ba na shige abu na... 12:20am Dikko ya isa gidanshi zuciyarshi na ƙara azabtuwa da soyayyar Sultana , addu'arshi a daren yau itace yanda yakejin kishin Sultana ubangiji ya sanya mata kishinshi a zuciyarta , yanda yakeji soyayyar ta itama Allah ya saka mata soyayyarshi , yasan dama babu ranar da zata ga girman shi tunda ya gama ɓareshi a wurinta , amma yasan idan dai tana mishi soyayya zatasan girmanshi dan darajar wannan son nashi dake zuciyarta.... Da sallama ya shiga ɗakin Sadiyya har yanzu tana nan inda ya barta tasha kuka har ta godewa Allah , cikin tausayawa ya kalleta yace har yanzu baki kwanta ba ? Dakel ta sauke ajiyar zuciya cikin kuka tace ina kaje ? Kusa da ita ya duƙa ya ɗagota cikin sigar lallashi yace meye ? Ki daina kuka kinji ya ƙarasa maganar tare da rumgumeta , cikin shashshekar kuka tace ina kaje ? Shine ka tafi ka barni , Shiru Dikko yayi , Sadiyya taci gaba da cewa nasan da ciwo a rayuwarka yau kaji babu daɗi kuma nasan duk lokacin daka kalleni zakaji baka ƙauna na , murmushin ƙarfin hali yayi cewa haba keko waye yace miki haka ? Sadiya tace ka daina ɓoyewa Yaya DK nasan babu daɗi kuma akwai ɗaci kayi haƙuri ka rufemin wannan sirri ko bayan babu ni... Lallashin ta Dikko yayi saida ya tabbatar ta samu natsuwa har tayi wanka sannan suka kwanta , har Dikko yayi bacci Sadiyya ta kasa bacci baƙin ciki yazo ta taru a zuciyarta sai kukan zuci takeyi tare da nadamar biyewa soyayyar zuciya... Tunda safe na farajin hayaniyar "yan gidanmu masu abun kuɗi suna ɓoyewa , masu wayoyi na kashewa suna adana abunsu , muryar Naja yayata naji tana cewa wallahi gashi nan yayi parking fa , zai fito , zai fito ya fito , gashi nan zai shigo zai shigo.... Sai kuma naji gidan ya natsu yayi shiru kamar babu masu rayuwa a cikin gidan , tashi nayi na leƙo ta jikin window dan ganin wanda yake shigowa , Babana duniya kenan , kai ina san Babana wallahi dan nafi sanshi fiye da Inna , Da sauri na buɗe ƙofa na nufi wurinshi da gudu ina mai farin ciki da ganinshi , cikin soyayyar da ya saba nunamin ya riƙeni tare da cewa bi sannu Uwar masu gida karki faɗi , yayi maganar cikin jin kunyata ya kasa haɗa ido dani tsaɓanin yadda yakemin a baya , rumgume Babana nayi tare da fashewa da kuka nace me yasa ka tafi ka barni Babana ? Kasan ina sanka banajin daɗin rashinka a kusa dani ? Me nayi maka kayi nisa da rayuwata ? Shiru yayi baice komai ba , naci gaba da cewa idan har akwai sauran wata soyayya bayan wacce nake maka Babana itama na baka ita dan jaddada soyayya da ƙauna a gareka , ina alfahari dakai daka zama uba a gareni , kuma ina addu'a na kasance dakai har numfashin ƙarshena a duniya , kuma ina roƙon Allah yasa kar na wayi gari babu kai a duniyar nan , ɗagowa nayi cikin kuka na kalli cikin idon Babana nace karka sake tafiya ka barni ka kasance dani dan nima na samu duk irin soyayyar da ko wane mai Baba yake samu a duniya Babana... Baiyi magana ba yaja hannuna muka fita ƙofar gida , motarshi ya buɗe muka shiga muka zauna , cike da soyayya Babana ya kalleni yace Uwar masu gida duk wata soyayya ta duniya wacce Allah ya halitta ta bayan soyayyar shi da manzansa da nake a duniya soyayyarki ke ɗaya tak ta goge soyayyar kowa a faɗin duniyar nan , idanuwana basa kallon kowa haka kuma zuciyata bata nunanin wani a duniyar nan idan bake ba ,tun daga ranar dana sameki ubangiji ya ɗoramin jarabtar soyayyarki a zuciyata , ni Allah bai ɗoramin ciwon son "ya "ya ba , wallahi bansan yanda akejin soyayya ɗiya ba saida Allah ya kawo zamaninki... Nayi kukan baƙin ciki nayi nadama da har na kasa samar miki farin ciki , tunda nake a duniya ban taɓa nema na rasa ba , haka kuma babu wani abu na rayuwa daya taɓa kubcemin matsawar inajin soyayyarsa a zuciyata , an cuceni an kuma yaudareni da har aka samu nasarar rusamin farin cikin rayuwata , nayi tir da Allah wadai dana zama sokon uban da ya kasa ceto rayuwar "yar sa.... Mamana ki yafemin ni ban cancanci na zama uba a gareki ba , banso kika zo cikin rayuwar wahala ba , banso ba kuma banji daɗin haka ba , da ana canja uba dana zaɓar miki mafi girma da matsayi a duniya ya zama shine mahaifinki domin kiyi rayuwa mai inganci ba rayuwar dana sani ba , Uba ɗan caca bashi ne ya dace da rayuwarki ba , ba nine ya dace na zama uba a gareki ba bayan ni na kasance bana cikin mutanen kirki , idona ya rufe da duniya bansan duniya bata da daɗi ba saida na kasa magance duk wata damuwa taki , saboda haka ki daina alfahari dani nasan ke da kanki zaki gogeni daga lissafin rayuwarki matsawar kika gane wane irin mahaifi gareki a duniya... Girgiza kaina nayi tare da cewa duk rayuwa sunanta rayuwa , jin daɗi ko rayuwar baƙin ciki baya sa a gane mai rabo a duniya , girman zunubi da saɓo baya sa kakai mutun jahanma domin rabon rahama wannan daga Allah ne , ɗan caca da ɓarawo duk matsayin su iri ɗaya ne a idon al'umma amma a wurin ubangiji azabarsu ta rabauta , manta da abinda ya faru baya kawai mu fuskanci rayuwa , amma waye Bello ? Meye tsakaninka dashi ? Me ka mishi wanda har ya zaɓi nice zaka saka a wasan caca.....? Hawaye ya gangaro daga idanuwan Babana , murmushi nayi tare da riƙe hannunshi ina masa kallo mai tattare da soyayya..... Cikin soyayya shima ya kalleni sannan yace ki jirani ina dawowa yanzu zan mayar da mutane motarsu , idan na dawo zan faɗa miki asalin waye Aliyu Binna , haɗuwata da Bello abinda ke tsakaninmu saka ki a wasan caca duk zakiji , sakin hannunsa nayi ba tare da nayi magana ba na fice daga motar , shi kuma yaci sitiyari yabar anguwar , cikin gida na koma ban damu da hararar da akemin ba naci gaba da sabgogin gabana.... Har yanzu Sadiyya bata daina kuka ba , kuma Dikko yayi lallashin duniya taƙi ta daina kuka kuma taƙi taci abinci , daga jiya zuwa yau ta rame idanuwanta sun kumbura , Dikko ya gaji yace mata kode shine bata so ? Sadiyya tace duniya da tasan zata zama matarshi kwata² da bata ɓata rayuwarta ba , gajiya yai ya fita sabgarta yaci gaba da huɗɗoɗin gabanshi zai bar gari ana rantsar dashi idan Allah ya kaimu gobe... Cikin ƙananan kaya ya fito yayi kyau sosai a cikin coppie brown in riga, da wando ash mai haske , rufaffin takalma brown mai haske yayi stocking yafa ɗauku iyakar ɗaukuwa yayi kyau sosai , ɗakin Sadiyya ya nufa yana ɗaura baƙar agogo a tsintsiyar hannunshi yana cin cigom cikin salo mai ɗaukar hankali... Da sallama ya shiga tana kwance saman gado cikin bargo ƙasa² kakejin sautin kukanta , yaye bargon yayi fuska a haɗe yace waike baza ki daina kukan banzar nan ba ,? Nifa bana san iskanci bana so inyi ta magana abu ɗaya , zan tafi idan kinga dama kiyi shiru idan kinga haggu kiyi ta kuka har masu kuka suzo su sameki.... Murmushi Sadiyya tayi tare da cewa Allah yasa ka sauka lafiya , kuma kayi haƙuri idan har kazo ka samu na mutu to ka yafemin , tsoki Dikko yayi ya fita ba tare daya sake mata magana ba , Al ' Ameen shine yaja su , Dikko ne a gaba mutane biyu kuma a bayan mota , su huɗu kenan , kuma saida suka biyo ta anguwarmu amma yau bamu samu haɗuwa da Dikko ba , kuma ya aiko kirana har gidanmu akace masa bana nan , bayan kuma ina nan , amma banji lokacin daya aiko kirana ba.... , Dikko yaso ya ganni amma haka ta gagara , dole ya haƙura suka ibi hanyar Abuja....... 14/09/2019 Jamila Musa....💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 33 Tafiyar Dikko babu jimawa Nana ta shigo take faɗamin mai gidan dokuna yazo nema na amma ance bana nan... Tsoki nayi ban bata ansa ba , tsintsiya ta ɗauka taci gaba da share ɗaki , ni kuma jakata na ɗauko na buɗe ina kallon abinda nake fesawa mutum ya tafi bacci , jijjigashi nayi bayan naji sauran abinda ya rage na mayar a jaka ina mai addu'ar haɗuwa na da iyayen su Hafsa... Maganar Babana naji a tsakar gida yana cewa duk iya ƙwarewa munafircinku na gano ku baƙaƙen munafikai , wato duk lokacin da kukaji motsina sai ku kashe wayoyi ku ɓoye kar nace ku bani kuɗi kuce babu , idan naji babu zansa wayoyi suci kasuwa , dan ku bani kuɗaɗen , lissafo duk yayuna yayi masu waya cewa kowa ta kawomin wayarta dukanku ancemin har face buk kukeyi , kuma na gani da idona dan babu wacce banga hotonta a cikinku ba... Cike da damuwa suka fara fitowa Babana yana zaune a saman kujera kowa sai ta bashi ta koma ɗaki cike da ɓacin rai , bayan ya gama tattare wayoyin kaf ya kira babban yayanmu yace maza kasuwar tsaitsaye ka siyar min dasu , da guda² yake bashi wayoyin tare da faɗa masa adadin farashin da yake so a siyar da ko wace waya... Shima Yayanmu cikin fargaba yace Baba ai duk kuɗin daka faɗa baza'a siya a haka ba , wata irin harara ya zabgaga mishi tare da cewa wannan kuma damuwarka ne , kai tunani ya rage ma yadda zaka siyar danni duk kuɗin dana faɗa su zaka kawomin a ko wace waya na faɗa maka , yana faɗin haka ya miƙe ya nufo ɗakina... Da sauri Nana ta ajiye tsintsiya saida tayi masa sannu da zuwa ta fice daga ɗakin , bayanta yabi da kallo zuciyarshi tana ƙisima mishi wasu abubuwa , amma bai ansa sannu da ta masa ba... Gefen katifa ya zauna kusa dani cike da soyayya irinta mahaifa yabini da kallona mai tattare da tsantsayar soyayya , murmushi nayi nima ina kallonshi nace Babana baka da kuɗine ? Murmushi yayi bai bani amsa ba , nima murmushin na sakeyi kamar yanda yayi sannan na jawo jakata ina cewa ni ina da kuɗi bara na baka... Ansar jakar yayi tare da rufeta yana mai cewa nifa ina da kuɗi Mamana kinsan mage kota ƙoshi sai ta hari ƙwari , ajiye kuɗinki anjima zan ƙaro miki wasu , ajiye jakar yayi a gefena sannan yace Mamana tun kuna ku hamsin da bakwai har yau an wayi gari kun zama ku sittin ciff, Tsoki yayi tare da kauda kanshi gefe yace tirr , wallahi da za'a tambayeni abinda nake so a musanya min da tulin "ya "yan nan ke kaɗai zan cire a cikinsu sauran a mayar min dasu daga motocin hawa sai ƙayataccin gidaje , ita kuma matar malam bahaushe ita dai burin ta kawai ta tara taron "ya "ya ita dai a mutu kawai taci gado , tou ban ajiye ba kuma bazan ajiye ba duk wacce ta haifi "ya "yanta taji da abunta ni babu ruwana... Uhum Babana kenan mugunta kamar mai tsaron gidan yari , wato karya nema ya ajiye idan baya duniya a ci gado , hmm halin Babana saishi kallo nabi shi dashi ga wayyen mutum kisan boko ɗan gayu mai buɗewar ido yana da ilimin boko mai zurfi amma saboda tsabar baƙin ciki ko aikin gwamnati bayayi , tunda yaga ana ruguwar haifar mishi "ya "ya ya daina aiki ya koma caca... Kallona yayi yace ki ɓoye sirrin mahaifinki koda bana faɗin duniyar nan , ki zama maimin addu'a bayan mutuwa ta ɗaukeni daga kusa dake , ki nunamin soyayya irin wacce nake nuna miki Mamana , ina miki soyayyar da duk duniya bana ma kowa irinta , banajin kunyar kowa idan nayi abinda ban kyauta ba amma Allah ya sani inajin kunyarki Mamana , babu wanda ya isa yasa nayi ko na bari amma idan har kika hanani na hanu , labarin waye Binna kuwa zan faɗa miki ne saboda abinda ya faru dake wanda ba'a san raina hakan ta faru ba , kuma ki yafemin na roƙeki ya haɗa hannayensa biyu tare da ci gaba da cewa kuma bazan sake tafiya na barki ba , ya ƙarasa maganar yana mai min kyakyawan murmushi .... Riƙe hannunshi nayi tare da cewa kayi alƙawari ? Jinjina kai yayi yana murmushi yace nayi miki alƙawari , nima murmushin nayi tare da cewa nima nayi maka alƙawari Babana bazan taɓa tafiya na barka ba , yayi Allah ya albarkaci rayuwarki Uwar masu gida , da amin na ansa tare da gyara zamana , shima gyara zamanshi yayi sannan ya fara.... *ALIYU MUHAMMAD BINNA...* Shine cikakken sunan da kowa ya sanni dashi , *BINNA* laƙani ne dana sakawa kaina shi bayan na shiga harkar wasan caca , dalilin binna kuwa saboda tsabagen neman asiri irin nawa , *BINNA* a binne kenan , dan da anyi magana kaza bazai yuwu ba , zance a binne shi kawai , tou idan nace a binne sai mutane suka fara ankara da abinda nakeyi dan haka sai nayi waiwayen damisa na zama Binna kawai dan ɓatar da mutane lissafinsu , sunan yana firgita kowa haka kuma yake bawa kowa tsoro duk wanda yaji ance *BINNA....* tou binna abin tsoro ne abun firgici tashin hankali ne ga duk wanda yasan Binna da irin rayuwar da nakeyi...! Malam Muhammad shine mahaifina , Maryam wacce ƙauye yasa ake kiranta da mero itace mahaifiyata , matan malam 2 mero da sahura , mahaiyarmu itace ƙarama kuma dake ta daɗe bata samu aihuwa ba , ita kuma Sahura dama tuni ta kwankwatso ɗiyanta goma sha shidda , hmmm Babana yayi tare da cije haƙorashin na gefen dama ya karkace leɓunansa sukayi sama , jinjina kai yayi sannan yaci gaba da cewa "ya "ya sha shidda saboda haɗama sai kace wata kaza , dan tun kafin a auro Mero tuni Sahura tayi haihuwarta ta gama... Mu talakawa ne na abin musali , kaf zuri'armu ba'a taɓa samun mutumin daya mallaki kaza biyar ba , kaf kauyen Ƙarara babu mutane masu talaucinmu , bamu gaji arziƙi ba kuma babu wanda yayi shi , kowa dai yanashan azabar talauci yadda ya kamata , Malam kuwa wutar talauci data isheshi ya rasa inda zai saka ransa saiya fara aikin tsubbanci , kuma sai Allah ya tallafa mishi domin idan yayi aiki kamar yankan wuƙa wuyar dai kafin yayi ne kawai , cikin ƙanƙanin lokaci sunansa ya fara ketawa yana zagawa kunnen jama'an duniya , yayin da mutane suka fara kiransa mai gobe da nisa... Nanfa harka ta buɗe dan Allahn yace masa zama , tun abun bai fita ba har mutane suka fara shigowa daga cikin birni suna zuwa wurinshi , a tsabibincin nasa fa yakai maƙura kuma shekarar arziƙin nasa ya tsaya kalmar zama da Allah ya yaddar masa taci gaba da tabbata akanshi.... Malam fa ya fara tara abun duniya , liƙafa taci uban ta da , dan malam ba mutum bane mai rowa dan haka jama'a suka fara saɗaɗowa zuwa gidanmu cin arziƙi , cin nan 3 a yini tou fa idan mutum yazo zaici ya ɗinke har yayi guziri , shi yasa gidan namu kullum ya koma kamar wani gidan biki ko suna... A lokacin da Mero ta samu cikin farko Sahura kuwa tace ina wuta ta jefata , nan ballin asiri ya fara tashi jefe² tahana mahaifiyarmu zaman lafiya , da ta samu ciki sai ya ɓare , ciwon yau daban na gobe daban , abun dai babu daɗi , Su kuwa malam ba abinda ya damesu da harkar da iyalinsu ke ciki burinsu kawai sudai a kawo musu , kullum matan malam basu da aiki sai wanke alluna , ana haka dai har Allah yasa Mero ta samu cikina , tunda Sahura ta lura Mero tana da ciki taci gaba da wurgago subbancinta , haba ina harta isa ? Allah yace saina zo asiri baya tasiri a wannan lokaci sai hukuncin Allah... Har Mero ta haifeni cikin wahala take da musibar rayuwa , tunda na sako ƙafa duniya dama azababbena aka haifoni , da rana zansha baccina har in gode Allah , amma da zaran an kira sallah magrib na fara kwarara ihu har garin Allah ya waye babu wanda ya isa ya runtsa idonshi kona second a gidan nan saboda kuka na , a haka akayi suna Allah ya cidani da Aliyu , ina wannan masifafen kuka da an kira asubahi kuma zanyi bacci , malam kuwa saida ya rubuce yace abani insha maganin kuka duk ranar da aka bani rubutu kukana sai yafi na jiya , har malam ya haƙura ya daina rubutu ana bani... Haka Mero ta haƙura taci gaba da rainona duk wanda ya ganta yasan tana tattare da damuwa , tabi ta soye tayi baƙiƙƙirin saboda tsabar rashin kwanciyar hankali , dana fara zama kuwa idan ta zaunar dani zan fashe da wani irin ihu mai firgici wanda dole saita ɗaukeni ta goyani , nadai zama fitinanne ta ko wane sashi , Dana fara rai rafe kuma ɓarna harta ƙeta , duk abinda yake na Mero bana ɓatawa amma daga ba ita ba duk abinda na gani saina tadashi aiki , Sahura tace iskanci kesa nakeyi ɓarnar tunda nasan abun uwata bana ɓatawa , da nayi mata ɓarna sai tayita dukana maimakon inyi kuka sai inyi ta dariya... Abun fa ya fara tayar da kowa hankali , har aka yayeni a nono , iskancina kuma sai abinda yayi gaba , tun ina ɗan firiri na , na iya tsakalo fitina saidai idan ban fita ba , masu kawo ƙara kuwa haka zasu jero layi , wasu a biyasu wasu kuma a basu haƙuri... Shekarata 3 Mero ta sake samun ciki , amma har ta haifeshi Allah bai sanar da Sahura ba , tashin hankali wanda tayi ba kaɗan ba , amma bata da yanda zatayi dan duk wanda yazo baya komawa sai idan Allah yaso... Ranar suna data zagayo aka sakawa jariri suna Muhammad , wanda ake kiranshi da ƙarami , ku kuma kuna ce masa Baba ƙarami , haka dai akaci gaba da cakwakiyar rayuwa , har Allah ya kawo wata mace matar wani attajiri malam yayi mata aiki , bayan buƙata ta biya shine ta siyawa malam gida anan cikin garin birnin katsina , a anguwar ƙofan marusa , daga nan muka tattaro mukayo birni ! Shekarar mu biyu da dawowa birni Mero ta ansa kiran mahaliccinta babu jinya haka kuma babu ciwon kai bare na hannu , nasha kuka kamar zan mutu na rashin mahaifiyata , wanda Sahura ko a kwalar rigarta , Bayan anyi kwana 3 da rasuwar Mero Sahura ta samu malam ta kitsifa masa ita bata iya zama dani ga iskanci ga rashin kunya ta taɓani ace dan uwata bata raye take azabatar dani , saidai ya raba mana wurin zama , Ba tare da nazarin komai ko tunani ba , yace in bar mishi gidanshi dani da ƙarami , haƙuri na bawa malam akan ya bari saiya kamani da laifi , amma fur ya ƙeƙashe idanuwanshi saina bar mishi gida , ina ƙoƙarin barin ɗakin malam Sahura tace sai inzo in tafi da ɗan uwana dan so take gaba ɗaya fitina ta fitar masu daga gida , a lokacin shakarar ƙaramin 2 da wattanni , ni kuma ina da shekara biyar da "yan watanni , haka malam yayi mana korar karnuka , ina kuka na ɗauki ƙarami muka fita daga gidan , Ina ɗauke da ƙarami na shiga cikin gari , duk wanda ya ganni ɗauke dashi zaice na mayar da yaron nan bana iya ɗaukarshi , ko sauraron mutane banayi bare na basu ansa , tafiya nakeyi har aka kira magrib , ni kuma a lokacin na isa wata anguwa ita Gambarawa.... Bakin wani shago na zauna na sauke ƙarami dake ta zabgaga kukan gajiya da yunwa , bayan na zaunar dashi naje na ɗauko buta da wani ya gama alwallah ya ajiye na bashi sauran ruwan daya rage yasha , bayan yasha na matsa wurin mai shagon da yake ƙoƙarin buɗewa ya dawo daga sallah nace Baba da Allah ka taimakamin da sadaƙa zan siyawa yaro abinci yaci , Cikin hargowa yace ai sai ka buɗe ka ɗauka mishi ɗan barauniya , dama irinku ne masu sacewa mutane abu idan basa nan , wata irin kwanya yaimin tsakiyar kaina harsai da nayi tunanin kaina ya huje , dariya nayi tare ce masa ka nunamin inda zan ɗauka , kuɗi ya fiddo daga cikin aljihunshi kwaci ² shege ɓarawon banza , kallonshi nayi sannan na duma ma kuɗin wawa , kaf kuɗin na kwace na ruga na cicciɓi karami nabi lunguna ba tare da nasan gari ba , Biyoni yayi da gudu yana a tara ɓarowa , ƙarami kuma sai kuka yakeyi saboda ya wahala , ganin jama'a na ketowa daga hanyoyi da dama yasa na samu wani zauren gida na sake na rufe bakin ƙarami sautin kukanshi ya daina fita... Dube ²n su sukayi basu sameni ba saboda haka suka hakura kowa ya kama gabanshi , saida na tabbatar babu kowa sannan na fito naje na samawa ƙarami abinci yaci muka bar anguwar Gambarawa a daren na dawo Qerau da zama.... Haka rayuwa taci gaba da tafiya , ni na saka kaina makarantar allo kuma na samu gidan aiki , gidan aikin suka sakani makarantar boko , haka dai na haɗa abu goma da ishirin , ga karatun allo ga boko ga gidan aiki ga rainon ƙarami , A daddafe dai nayi ta dafa rayuwar kuma ban sake zuwa wurin malam ba kuma daga Qerau zuwa Ƙofar marusa babu wani nisa , Shima ƙarami daya isa sakawa makaranta boko gidan aiki na suka sakashi , kuma tare dashi mukaci gaba da aikin gidan , daga baya ma suka bamu wurin zama a cikin gidan , Na gama secondry sch Bello ya shigo cikin rayuwata , gidan ƙawar matar da muke zaune gidanta itace take aikena gidan ƙawarta gidan kuma a maƙotan gidansu Bello ina zuwa idan aka aikeni nan ya ganni ya liƙemin , yana zuwa gidan da muke zaune yana yini wani lokaci ma har kwana yakeyi , ya shigeni sosai abota mai girma , Makarantar gaba da secondry tare da Bello muka fara nidai nayi karatu kuma na fito da sakamo mai kyau yayin da Bello ya faɗa harkar mata , a lokacin kuma ƙarami yana secondry sch aji biyar , bayan na gama degree aka fara neman min aiki , yayin da ni kuma nake neman ƙara faɗaɗa ilimin nawa... Har wannan lokaci banje wurin malam ba , kuma malam bai nemeni ba ni kuma naƙi nemansa dan dama ni nasan inda yake , saida naci gaba da karatu na , na faɗa harkar wasan caca daga nan duk lissafi ya jagulemin , dan duk wannan kangarar da nayi a baya tana da dalilinta kuma a gaba zaki ji ta , dan bayan na baro gida naɗan samu natsuwa , amma shigowar Bello rayuwata yasa na ida ƙwacewa...... 16/09/2019 Jamila Musa.....💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 34 *_Fatan na samu kowa lafiya ? Kuyi haƙuri na jina shiru kwana biyu banajin daɗi ne amma na samu sauƙi alhamdulillah ngode da addu'o'in ku a gareni masoyana , gaskiya naga soyayya kuma ngode sosai , na warware zamu ɗaura daga inda muka tsaya , fatan alkairi a gareku masoyana kuyi farin ciki..._* Shiru Babana yayi ya zubamin idanuwa yana min kallo mai tattare da bayaso ya faɗamin , nima ƙureshi nayi da idanuwa amma bance masa komai ba , shiru yayi yana nazari zuwa can ya ɗago ya kalleni , nima kallonshi nake har yanzu zuciyata dai ta bani kila zai ɓoyemin wani abu ne... Gyara zama yayi yaci gaba da cewa , zuwan Bello rayuwata yazo min da al'ajabi mai girma , wanda ya kasance bana iya ƙetare maganarsa , idan yacemin inyi zanyi idan yace na bari zan bari ya rabani da ko wane aboki shi ɗaya ne abokina , Bello shi ɗayane iyayenshi suka aifa , kuma attajirai ne na gaske , soyayyar duniya sun ɗorawa Bello sun sangartashi yadda ya kamata , saidai ya kashe waccan mota ya ɗauka waccan , ba mazaunin gida bane ba , domin duk kayanshi na sakawa yana cikin motarshi , tafiya yake jira kawai yayi gaba , gashi cikakken ɓarawo domin duk ƙarfin arziƙi mahaifinshi saida ya duƙar dashi ƙasa. Tun wancan lokacin Bello ya mallaki bantan baƙin biri , daya ɗaurashi duk inda ya shiga idan dai akwai kuɗi hayaƙi ne zai riƙa tashi , da yaga yahaƙi yasan kuɗi ne a wurin zai buɗe kawai ya kwashe yayi gaba , Bello mashayi ne , ɓarawo ne , ɗan caca ne sannan tantirin mazinaci ne , idan har ya zuƙawa mace masifa tou duk irin kamun kanta da natsuwarta sai Bello ya keta mata mutunci , baya neman zawara baya neman matar aure sai "yan yara ƙasa da shekarunki , shekaruna kenan ni Sultana , kuma daya biya buƙatarsa ya gama da ita wata zai nema... Da nayima Bello magana sai yacemin sa'ar caca malaminshi ya bashi , gabana Bello ke zuƙewa kuma gabana yake kwalbewa , ma'ana a gabana yake shawuwa yasha sigarinshi yasha giya da sauran kayan shaye ²n shi... Ni kuma a lokacin na koma makaranta naci gaba da karatu na , dan zurfafa ilimina dan na fahimci rayuwar idan baka da ilimin zamani mai zurfi tou ka zamo an maido wuta an ɗauke... Banda isashshen lokaci bansan abinda gida yake ciki ba idan na tafi makaranta , gidan da ake riƙemu akwai ɗiyar mai gidan itama yarinya ce ƙarama lokacin tana js3 ashe itama Bello ya ɗora mata alƙalamin kudirinshi akanta wanda ya fake da soyayya ne ni kuma duk ban sani ba , Wallahi babu abinda na sani tunda bana nan , ƙarami ma baya zama gida shima makaranta , Bello idan yazo bama nan zai buɗe ɗaki kawai ya shiga babu mai hanashi tunda abokina ne , Wata rana kwatsam ina makaranta "yan sanda suka zo suka tafi dani , tambayarsu na farayi lafiya ? Babu mai lokacina , haka suka sarkafeni da sarƙa suka tafi dani ofishinsu... Suna zuwa office sukaci gaba da dukana babu ji babu gani , sunma hanani nayi magana bare naji laifina ? Saida suka min lullusar fitar hayacci sannan aka wurgani cikin cell aka rufeni , Saida na dawo hayyacina naga Bello gefena yana kyalkyalamin dariya , ƙarami na gefe sai kuka yakeyi , goge hawaye nayi tare da cewa me mukayi haka abu babu mutunci ? Dariya Bello yaci gaba dayi yana shan lolypop inshi... Ƙarami na kalla nace meye wai ? Cikin kuka yace wai rafe naji dai suna cewa , cikin ɓacin rai nace rafe me ? Miye rafe kuma ? Ƙarami yace nima ban sani ba kawai dai haka naji suna cewa , tsoki nayi zuwa can nace waye yayi rafe ɗin ? Cikin kuka yace mu duka naji suna cewa , har yanzu Bello dariya yakeyi yana shan lolypop , raina naji ya ɓaci na tashi nayi kan Bello naci gaba da dukanshi babu ji babu gani ina cewa me mukayi ne ...? Dariya Bello yakeyi yana cewa wallahi hauka yasa suka kawoku , ni kaɗai nayi kuma yarinyar da kanta tacemin tana so in rantsar da ita , itama ta zama cikakkiyar mace kamar kowa , tou dan nayi abinda takeso sai azo a rufemu , ai godemin ma ya kamata suyi , shaƙe Bello nayi sosai tare da cewa itama ka zuƙe.......? Bushewa yayi da dariya to me ake jira da abun kwaɗayi.... ? Yau taji abinda uwarta keji , da sauri na rumtse idanuwana dan naji kaushin maganar Bello a raina , murmushi yayi tare da cewa kaji babu daɗi ko ? Tou ai itama uwar ta tuni na bata alƙalamin daraja kuma yanzu nan zata zo ta fitar damu dan nace idan har ta bari muka kwana sirrinta a buɗe yake dan ina da babbar sheda , Kallon Bello nayi idona cike da hawaye nace hajiya ma .....? Murmushi Bello yayi yace harda tukwuici take bani ma , kuka naci gaba dayi dan banji daɗin abun ba , daga haka nayi shiru na samu wuri na natsu muna jiran tsammani... Hajiya itace tayi cuku² dan Alhaji shine yasa aka kamo Bello kuma Bellon yace tare mukayi kowa saida ya zagaya sau biyu domin ya buɗe mutuntakar a yarinyar yadda ya kamata ! Saida Hajiya ta saki kuɗi sosai tare da ƙaryata zance mijinta cewa ba Bello ne yayi wannan aika ² ba wasu daban ne sukayi kuma suka gudu haka nan aka ɗaura alhakin tuhuma akansu yara marayu basuji suka gani ba sai Allah ya saka musu... Saida aka kai ruwa rana sannan muka fito , Bello yace mena faɗa muku nace muku zamu fito babu ɓata lokaci , haushin sa kawai nakeji domin naji ciwon wulaƙantawar da yayiwa yarinyar da nake ma kallon ƙanwata , kuma naji ciwon keta mutunci mahaifiyata Hajiya da ta ɗaukeni matsayin ɗa , kuma nima daga wannan lokaci na ɗaura ɗamarar saina masa yaji idan da daɗi ! Alhaji kuwa korar kare yayi mana daga gidanshi bayan yayi maganganu masu zafi da ɓatanci akanmu , kayanmu muka kwashe daga gidan Bello ya bamu mazauni a gidansu... Duk lokacin dana kalli Bello sai naji kamar in haɗiye zuciya in mutu saboda tsabar baƙin cikin abinda yayiwa mutane masu mutunci , koda zai fita da daddare binsa nayi domin na fara harin rayuwarsa , Gidan caca muka nufa dashi , shine zuwana na farko dan kallon wasan da Bello zai buga , bayan yayi "yan al'adunshi ya binne ya ɗaura , hankalina ya tashi ganin tulin kuɗi da aka zuba , cikin ƙanƙanin lokaci aka fara gabatar da wasa , an ɗauki lokaci mai tsayi ana gwabzawa bayan wasan yayi zafi Bello ya lashe wannan makudan kuɗaɗe , Bayan ya kwashe kuɗinshi aka fara shagali , kwalaben giya suka fara wali da dai duk wani mai ɓatar da hankali , ina cikin ɓacin rai dan haka bansha ba , amma Bello yace idan nasha zan rage damuwa , dan haka na ansa nasha cikin ƙanƙanin lokaci na nemi damuwa na rasa ! Uwar masu gida labarin dai bazai buɗu duka ba , dan wasu labaran bai kamata na faɗa miki ba , mu tsaya haka nan , domin nima na zama atsabibin matsafi dan ko magana nayi bata faɗuwa ƙasa na koma kamar wani mai kambun baka saboda tsabar neman asiri irin nawa ! Daga nan na shiga wasan caca nima , naci gaba da harkar mata , shaye² da duk wani abunda ya zama zunubi , nayi nisa banajin kira , sheɗan yaci gaba da busamin sarewar halaka na shi , ga Bello bashi da ƙanne , Bayan ƙarami ya gama secondry sch yacemin bazai ci gaba da karatu ba , nayi juyin duniya yacemin daga haka ya tsaya , to ni na bashi gidan zama wanda a caca na ciwoshi , kuma ni na bashi kuɗi yaci gaba da kasuwanci , kuma duk matan daya aura nine na kashe kuɗi nayi masa hidima , Ƙarami bai daɗe da aure ba Malam ya saki wasan , wato ya mutu , bayan yasha doguwar jinya an girbi abinda aka shuka domin aikin tsubbu ɓata ce , ya lalata maka zuri'arka ga dakon zunubi , wasu an ɓatar an raba an haɗa dan dole an talauta wasu an raba aure an raba uba da ɗa anyi an gama dai duk an tafi an iske Allah.... Bayan ƙarami yayi aure aka barni daga ni sai Bello mukaci gaba da gurza rayuwa , har Allah yasa ya samu yarinyar da yake mugun so , kyakkyawar yarinya mai hankali da biyayya Bello ya mutu akan yarinyar nan , sukaci gaba da soyayya , na tambayeshi ko itama dai kamar sauran ? Yacemin a , a wannan ta aurece gaskiya , naji daɗi sukaci gaba da zuba soyayya sun shaƙu sosai tarayyarsu abun burgewa , Basu wani daɗe suna soyayya ba sukayi aure , lumshe ido Babana yayi sannan yaci gaba da cewa ango na shirin shiga ya angonce Binna ya anshi budurcin matar Bello , Bello yayi kuka saida yayi jinya gashi kuma yana mata san da baya iya rabuwa da ita , uhum tafasha azaba yarinyar nan , bayan Bello ya samu sauƙi akaci gaba da abota , Nima yana nan zai rama ashe , to yanda kasar suri bata cuwuwa ga bakin duk wani bil'adama haka Uwar masu gida tafi ƙarfin Bello dan yasan idan yace akanki zai ɗauki fansa tabbas nima zan rama akan "yar sa , shi yasa ya matsamin na sakaki a caca , hawaye ya cikawa Babana ido , Yaci gaba da cewa yasan duk duniya ya cire soyayyar Allah da manzan sa babu wanda nake so a faɗin duniyar nan bayan ke , tabbas yasan zanci caca shine suka juyarmin da hankali ta hanyar bani asiri cikin abunsha , bayan sunyi galaba a kaina suka rasa abunyi , shawarar abokinmu ya nema shine yace yasan wani da yasan Dikko , yace idan aka kaiki a wurin bazan iya ja da hukuma ba , hankalina ya kwanta da naji wurinshi kike nasan babu abinda zai faru , Ashe shima sun shirya mishi gadar zare , ɗan masu aikin gidansu shine yayi jagoranci , cikin kuka Babana yace aka ciwa "ya ta mutunci , haka na gudu na ɓuya kamar ƙolo na boye saboda kunyarki , duk da nayi haƙuri ban ɗauki fansa akan abinda Bello yayi ba duk da haka bai faru ba , Amma dana biyewa sharrin zuciya gani takaini ta baro ni , murmushi nayi nace ba komai Babana na yafe maka , kuma wannan abun ka ƙaddara babu abinda ya faru , ! Amma me yasa ka bar iyalinka cikin wahala ? Tsoki yayi sannan yace nima haka aka barni a saman titi bansan mai kyau ba bansan mara kyau ba , banda mai nunamin kyakkyawa ko mummuna , babu wanda ya kula dani shi yasa nima na saki kowa yayi rayuwarshi , Baba Allah fa yana kallonka , ka karanta kuma kaji ka gani kuma kasan abinda Allah yace akan iyali , girgiza kai yayi tare da cewa kar muyi haka dake Mamana , banasan maganar su , tou Babana amma me yasa baka aiki ne ? Wannan ra'ayina ne , caca na zaɓa kuma zanci gaba bazan daina caca ba sai numfashina ya ƙare , cike da damuwa nace ko kana da dalili ne ? Uwar masu gida mubar maganar nan , Tou Babana ina Sahura ? Kuma me yasa kayi kangara kana ƙarami ? Murmushi Baba yayi tare da cewa wannan kangara wani aiki ne malam yayi akan wani yaro dan ya lalace , matar Babanshi tazo ayi mata aiki ne , sai abun ya dawo kaina , Matar ta dawo ta faɗawa malam buƙata bata biya ba , can wurin binci kenshi ya gano inda aiki ya sauka kuma ya warware komai , idan dai kayi mugunta tou ka daina saurin rufe ƙofa domin dawowa takeyi , Sahura kuma tana can gidanta bana dai zuwa gaskiya... Tou ita Inna baza ta dawo ba ? Manta da ita gani nan na isheki taje can tayi ta zuciyarta , kallon agogon hannunshi yayi ya miƙe yana cewa bani makullin motarki , miƙa mishi nayi ya fita yana mita ba'a kawo mishi kuɗin wayoyinshi ba , gaskiya Babana bansan irin halinshi ba , dandai yaƙi yadda ya faɗamin komai duk haka ya bani labari nidai a duƙunƙune.... A ƙofar gida ya anshi kuɗin wayoyinshi yayi gaba , "yan gida kuma cewa sukeyi da wani yake da motar nan sai Baba ya siyar da ita amma da yake ta Sultana ce komai daren daɗewa zai dawo mata da abinta , saboda kar yamin faɗa raina ya baci shi yasa baiji a ina na samu mota ko yamin faɗa ina hawa mota ba , Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya , Babana yake amfani da mota ta , Bello ya fita harkata nima na fita harkashi , d c o babu ruwana dashi , Hafsa da Amisty banda labarinsu , su A ` i ma bana shiga sabgarsu , mijin Zalifa da Zalifar duk na daina jinsu , Alaji kaɗai yake zuwa fira danshi ya matsa aurena zaiyi... Haka nan na tsira yin bedday babu gaira babu dalili , nayi i v nasa akaci gaba da rabawa , har a gidan radio nasa Alaji yakai sanarwa , manyan baƙi a wurin Baban Amisty mai yanka cake kuma Baban Hafsa , wurin taron kuma wani zuƙeƙen gidan Baban Hafsa , nayi gayya duk wani lungu da saƙo na zaƙulo manya ² karuwai nakai musu gayyata wanda duk ba ƙawaye na bane nasu Amisty ne , Al'amarin wannan taro ya karkato da hankalin jama'ar gari a kaina dan ban ibo abun da wasa ba , kowa da abinda yake faɗa akai na yayin da wasu mutane suka cewa taron iskanci ne ba wani taron birthday ba , Hafsa kuwa Amisty tayi mata waya ta faɗa mata cewa zanyi birthday amma taga venue gidan shaƙatawar Dady inta ne , yaushe ne ake taron Hafsa ta tambaya ? Amisty tace mata ranar laraba , Hafsa tace tou Allah ya kaimu zata ga yanda zan wulaƙanta ta .... Nima da Nana ta bani labari dariya nayi tare da cewa Nana nima zan wulaƙanta ta yayin da taga Dad inta ya yanko cake ya rungumeni yana bani a baki na , itama Nanar dariya tayi tare da cewa Allah ya kaimu zanje idan har Audu ya barni , Lokacin da Dikko ya samu labarin wannan taro da zanyi zuciyarshi tayi mishi ɗaci domin yasa ana biyayyar mishi rayuwata duk wani motsina da komai nawa babu wanda Dikko bai sani ba , Tsoki yayi tare da kallon agogon hannunshi jinjina kanshi yayi ya cusa "yan yatsun sa ko wane yana gogar ɗan uwansa , laraba , ya faɗa a bayyane tare da sake jinjina kanshi , litinin kuma ya faɗa a bayayyane Allah ya bamu aron rayuwar muje larabar dani dake........ 19/09/2019 Jamila Musa 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 35 Har yaci gaba da cin abinci kuma yaji gaba ɗaya moƙoshin nashi abincin baya wucewa , tsananin ɓacin rai da damuwa suke ta kartar masa zuciya , dakel ya haɗiye yawu mai ɗacin gaske , kallon Al ' ameen yayi yace kiramin Umar.... Wayar ya ɗauka da sauri ya fara kiran wayar Umar , saida Umar ya ɗauki wayar ya miƙawa Dikko cikin ladabi , ansa Dikko yayi cike da ɓacin rai yace har yanzu kana anguwar ko ka fita ne ... ? Magana Umar ɗin yayi , Dikko yace tou kaje ka kaima An mata waya zanyi magana da ita yanzu ² yi sauri karka ɓatamin lokaci , saida ya jira abinda Umar zai faɗa sannan Dikko ya kashe waya , Ina zaune ƙofar gida dani da Alajina muna fira Umar ya faka da machine inshi , kallo ɗaya nayi masa na kauda kaina yayin da na ciro wayana na fara ƙoƙarin kiran Wane Yaro , Sallama yayi suka gaisa da Alaji nima ya gaisheni , ansawa nayi babu yabo ba fallasa , ɗan gyara tsayuwarshi yayi tare da cewa dan girman Allah saƙo aka bani wurinki , daina kiran wayar Wane Yaro nayi na tattara hankalina kaf wurin Umar nace waye ya baka saƙon ne ...? Cike da ladabi ya miƙomin waya bayan ya kira number ya miƙomin yana cewa kiyi magana an ɗauka , cike da wasi² na kara wayar a kunne na tare da cewa Assalamu Alaikum.... Ansa sallamar yayi yana mai ci gaba da cewa An mata kinaso in saka ƙafar wando ɗaya dake ne ? Shiru nayi banyi magana ba , Dikko yaci gaba da cewa na rantse da Allah ki kama kanki wannan iskanci birthday in da kika taro ki warwareshi tun kafin inzo wurinki ina fushi , banda kyau idan na ɓata rai ki roƙi Allah ya rabaki da ganin fushi na amma na rantse da Allah.... Saida yayi rantsuwa mai sa faɗuwar gaba sannan yace idan kunne yaji .... Sai kuma yayi shiru bai ida faɗar maganar ba , ni kuma na ɗaura da cewa idan ka barni na huta baka ƙaunar Allah , tsoki nayi tare da miƙawa Umar wayarshi naci gaba da magana na da Alaji , Cike da masifa Dikko yace Umar ya maidomin wayar , bani yayi nima kuma na ansa , cikin sigar lallashi yace An mata nine bana ƙaunar Allah ? Wai mi yasa kike min magana haka babu ɗa'a , ai kasan gidanmu ba'a koyamin ɗa'a ba shi yasa ma har nayi rashin ɗa'ar a cikin gidan ubana , Dikko yace idan kinajin rashin kunya ki fita daga cikin mutane ki zageni idan kin isa , ni nasan baki isa kimin rashin kunya inda babu kowa ba , dama kin tsaya a gaban waɗanda ko naso nayi miki hukunci zanyi haƙuri a haka kike tunanin bakyajin tsoro na ne ? Idan dai bakijin tsoron Dikko maza ki tashi daga inda kike kice Dikko ƙarya kakeyi nafi ƙarfin ka takuramin ki faɗi haka kiga yadda zanyi wasan kura dake wallahi .... Kamar wata sakara na miƙe na matsa daga inda su Umar suke , ashe shi kuma yayi wayau ne dan kar in riƙa wulaƙantashi ne a gaban yaronshi , saida na matsa sannan nace ƙarya kake ni nafi ƙarfinka kuma nafi ƙarfin ka takurani dan banajin tsoronka kayi duk abinda kakejin zaka iya yi na matsa daga cikin mutanen.... Dikko yace tou babu komai dani dake aga fasashshe , ni zanzo katsina insha Allah gobe talata , ke kuma zakiyi birthday ranar laraba sai nazo , kuma karki sake kiyi mafarkin gemuna na faɗa miki.... Gemun banzar ka gemun wofi , Allah ya sawaƙe min in ganka a barci na , cikin murya mai saukar da kasala yace nifa bana san cika baki bayan nasan komai , kawai yarinyar kirki taga ustaz ta maƙale mishi aidai kina so na ko.... ? Tsoki nayi ban bashi ansa ba na kashe wayar naje na bawa Umar ko sallama banma Alaji ba na shige gida raina a ɓace , Murmushi Dikko yayi bayan na kashe waya tare da cewa An mata rigima , zaki zo kusa dani kuma inaji a jikina wata rana zaki rumgumeni ki kalli cikin idanuwana kice Dikko ina sanka , yana maganar yana nuna yanda Sultana zatayi , cikin farin ciki yaci gaba da cin abinshi bai sake kiran Umar ba , kuma koda Umar ya kira dan ya faɗa masa cewa Sultana ta tafi bai ɗauka ba , Shima Alaji kiran wayana yayi tayi naƙi ɗauka , ya gaji ya tashi yayi tafiyarshi , shima Umar tafiyarshi yayi gida , Ni kuma ina shiga ɗaki saman katifa na faɗa nayi ruf da ciki bansan dalili ba , maganar Dikko yake dawo min a zuciyana , karki sake kiyi mafarkin gemuna , cike da fargaba zuciyata ke cewa kodai Dikko ya gane ina kallon masa gemu ne .... ? Tsoki nayi na gyara kwanciyata ina tuno kyakkyawar fuska Dikko , tunani dai barka tai a zuciyata har bacci ya ɗaukeni.... Da safe Alaji yazo ya kaini kasuwa dan Babana baya nan kuma motana tana wurinshi , siyayya na bada mamaki nayo domin fa Alaji yana da hidima kuma yana da gabata , ya kashe kuɗi duk yanda tunani baya tunani , ko kayan da zan saka wurin partyn zagayowar shekarar aihuwata wallahi masu masifar kyau da tsada ya siyo min abun dai zabburgewa sai wanda ya gani , Bayan mun gama siyayya nace masa ya tafi zanyi kitso idan na gama zan kirashi ya ɗaukeni , Alaji yace to saida ya ƙaramin kuɗi ya tafi ni kuma na shige shagon "yan arna da basa gane yare na , na fara faɗa musu abinda nake so amma dan ubansu wai basu gane ba , saida wata rantsatstsar karuwa maiji da iskanci har iskanci yayi mata sign tayi musu bayani , girar ido za'a sakamin akaifa da kuma atach duk gashina saida nasa aka yimin ƙari saboda tsabagen wawanci irin nawa , A ƙofar gidanmu kuwa 5:00pm Dikko suka kafe motocinsu , aikawa yayi a kirani amma sai akace masa na tafi kasuwa , maimakon ya tafi sai yace zai jirani har na dawo , Duk lokacin da minti ɗaya ya wuce sai Dikko ya kalli agogo ranshi ya ƙara ɓaci , shiru ² babu ni har aka kira magrif , cikin damuwa yace ma Al ' ameen muje zan dawo anjima , Tashin motocinsu sukayi gaba ɗaya suka taho , suna fita anguwar mu kuma muna shigowa hannun riga mukayi dasu wato suna fitowa mu kuma muna shigowa , Babu abinda na sauko daga mota nace ma Alaji ya tafi sai Allah ya kaimu , sallama mukayi dashi ya tafi ni kuma na shige gida , ina shiga na shirya a gaggauce domin Baban Amisty zaizo , naje kasuwa har nayo kawalcin mace zan haɗasu , itace karuwar da muka haɗu ta tambayeni sana'ar da nakeyi nace mata karuwanci nakeyi , tace ashe tafiyar ɗaya ce ? Nace mata Eh musayar number mukayi har na bata labarin iyayensu Amisty tace suna da mai ne ? { kuɗi } nace sosai ma , shine tace a cikin daren nan in bata aron kowa a cikinsu ita kuma tamin alƙawarin zata ɗaukomin su dukansu a cikin yanayi mara kyau tou shine zan haɗasu , duk da dai malami da mawaƙi da karuwa basu da amana amma zuciyata ta yadda da ita 100% , Har ƙofar gida Baban Amisty ya ɗaukeni kuma yanzu ma muna fita Dikko yana shigowa , akace masa yanzun nan muka fita ko bakin titi bamu kai ba , da sauri ya biyo bayanmu ko zai sameni amma bai iskomu ba , ganin baisan ta ina zai samoni ba yasa ya haƙura ya koma ƙofar gidanmu a ranshi yayi alƙawari ko zankai yaushe ban dawo ba zai jirani , Daga gidanmu ƙofar soro muka nufa gidansu Mamy ƙarfe 8:18pm mukayi parking a ƙofar gidansu kamar yanda tayimin kwantance , bayan mun tsaya na kirata a waya , babu jimawa ta fito cikin shiga mai ɓatar da hankali , tana isowa ta kama mota ta buɗe ta kashe a gidan baya , shi kuma yaja mota muka tafi , shegen tsoho kenan yace ina muka nufa ne ? Yayi maganar yana kallona , Murmushi nayi tare da cewa nifa guzirin dare nayo maka itace zaka tambaya bani ba , kaga ni kullum muna saka rana amma abun bai yuwu ba shine dana ga mai buƙatar ruwa a tsakar rana nace tazo ina da ƙatuwar randa { tukunya } a gidana har yoyo takeyi { ɗiga } kaga kuwa idan har ta riƙe babban kofi a tausayawa ruwan nan domin saita ƙare shi kaf hankalinta zai kwanta , juyawa nayi na kalli Mamy sannan nace a ina zakisha ruwan ne .... ? Cike da bariki tace aishi ruwa ko a tsakiyar hanya shanshi akeyi saidai idan ba ƙishirwar ke damunka ba , amma tunda ni mace ce dole zan matse ƙishirwa har mu isa gida , amma ka daure kar kayi tafiya mai tazara dan lumfashina gaf yake da ɗaukewa , ! Karkata mota yayi ya ibi hanya , muka nufi kwaɗo , har muka isa babu wanda ya sake magana , a ƙofar gida yayi parking shida ita suka shiga aka barni a cikin mota , shigarsu babu jimawa na fara kiran Baban Hafsa inda zamu sameshi ya faɗa mana nace muna zuwa babu ɓata lokaci , Mamy kuma da Baban Amisty bansan abinda ya faru ba , sundai share awa da rabi sannan suka fito... Bayan sun fito ta buɗe inda nake zaune tace fito mana haka nan , nace kidai shigo muje , Mamy tace nan zamu sauka , fitowa nayi mukayi sallama dashi tare da ƙara tuna mishi sai mun haɗu wurin party yace in Allah ya yadda , yana tafiya muka samu wuri muka zauna , wayata ta ansa ta tura min vidion data ɗauko nashi abundai babu kyan gani ko ya akayi tayi masa dibara ta ɗaukoshi tasa shi sai iskanci yakeyi , a wayana ta tura bayan ta tura ta shiga whatsapp ta turawa Amisty abinda zata faɗa nake faɗa tana rubutawa... _Salam aminiyata Amisty , Sultana ce ban sani ba ko kin goge lambana shi yasa na baki sani dan kar ki shiga dogon nazari da tunani , kinsan mage bata cin bushiya , idan kuma maciji ya raɓi bushiya noƙe kanta takeyi yana tahowa da ƙarfinshi dan niyar mugunta sai ta noƙe kanta ya soki ƙayoyinta , maciji baya san tabo daga nan sai ya sari kanshi ya mutu , bushiya sai ta fito taci gaba walinta a duniya , tou haka tsaka take mage kaɗai ke cinta ta rayu amma ke in kakaci ta sai sheƙawa lahira , ganin aljanni a siffarshi akwai tsoro da firgitarwa masana ɓoyayyan sirri suna cewa idan kaga aljani a siffarshi kwanakin mutuwar ka ne yazo , nidai naga aljani ban mutu ba kuma naci tsaka ban mutu ba shi yasa na turo miki kema ki gani shin kina da yawancin kwana ko daga yau kwananki ya ƙare ne....?_ Turawa tayi ni kuma na ɗora da voice note cewa kiyi haƙuri kuma kibi sannu ki warware maganganuna kinsan tsarƙesu nakeyi idan kin gani kiba Hafsa ta tayaki gani.... Bayan na tura muka hau napep muka doshi barhim estate acan Baban Hafsa ke jiranmu , shima dai sun shana yadda ya kamata kuma Allah ya bata nasarar ɗauko min mugu , itama Hafsa tura mata nayi da voice note cewa... Duk gudun kare idan yaga kura ɓoyewa yake domin tsira da rayuwarshi , haka mutum idan yaga abun tsoro kuka yakeyi ya rumtse idanuwanshi , irin haka kikaji a lokacin da kika cire towul in dake jikina..... ? Ina gama faɗa na sakeshi ya tafi.... , Napep muka hau muka nufo gidanmu , saida aka fara saukeni aka wuce da ita bayan ta shedamin zasu zo wurin shagalin ita da zugar tata ƙawayen , godiya nayi ina ɗaga mata hannu har suka tafi , Kallon agogon hannunshi yayi yaga 11:35pm , daga ina nake a wannan daren shine tambayar daya fara ma kanshi kuma bashi da mai bashi ansar tambayar , ni kuma cike da farin ciki na tunkari ƙofar gidanmu sai tsalle² nakeyi na jin ɗaɗi na shige gida abu na , Jiki a sanyaye DK yaja motarshi ya nufi gida zuciyarshi tana mishi babu daɗi , amma yayi addu'a gobe tazo mishi lafiya , Yau laraba kuma itace ranar da nake wannan gagarumin taro wanda na samu damar gayyato mutane daga sasoshi da dama , tunda safe ake shiga da fice a gidanmu duk inda ka buɗe idonka zunzurutun karuwai ne kawai suke kai koma , wane yaji ga wane waccen taji ga wance , taron motoci ne burjik a ƙofar gidanmu duk wanda ya wuce sai yayi tir da irin matan da dake ƙofar gidanmu ! Shi kuma Dikko a safiyar nan tayi mishi babu daɗi dan matarshi aka kai asibiti bata da lafiya sosai , kuma taƙi cin abinci ta rame tayi duhu saboda ciwo da damuwa , hankalin Dikko idan yayi dubu ya tashi da guda ² kallo ɗaya zaka mishi ka gane yana cikin damuwa , ga damuwata ga ciwon matarshi .... Taruwa akaci gaba dayi duk yaran Baba Ƙarami sunzo gida ya cika taf kuma na duba har yanzu daga Amisty har Hafsa babu wanda ya hau online dan suma suna can suna shirya tasu gadar zaren , Komai fa anyi kowa ka gani a wurin shima yakai wani babban shege , sai 6:00 aka fara tafiya wurin partyn , Nana dai bata samu zuwa ba mijinta ya hanata kuma ta hanu , Karima itama bataje ba amma A ` i da Saude tare dasu aka tafi duk yayuna maza da mata sunje , Dikko yana duƙe gaban gadon Sadiya riƙe hannunta yayi cike da damuwa yace Sadiya karki kashe kanki don Allah idan baki so na ki faɗamin sai in sahale miki auren nan ki huta , ni ina da damuwa idan naga kina cikin damuwa ko nayi miki wani abu bai miki daɗi ba ne ? Karkata kanta tayi gefe hawaye suna ci gaba da gangaro mata , zama Dikko yayi gefen gado ya tattaro natsuwarshi fuskar Sadiya ya tallafo da duka hannayenshi yace mene ne ? Ki faɗamin wai meke damunki ne ? Dakel ta ɗaga bakinta zatayi magana a daidai lokacin da wayarshi ta fara ringing , cirowa yayi ya duba , Umar ne dan haka ya ɗauka tare da cewa ina ne..... ? Bayani Umar ɗin yayi masa , bayan ya gama Dikko ya kashe wayarshi , shafa gefen fuskar Sadiya yayi ina zuwa , yana faɗin haka ya miƙe ya fito daga ɗakin , ita kuma taci gaba da kuka , bayan ya fito yacewa Mom insha zaije ya dawo yanzu , Allah ya tsare tayi masa Al ' Ameen da sauran tawagarshi suka rufa mishi baya.... ! A bakin get suka ɗauki Umar suka nufo inda muke taro , a lokacin anci rabin shagali itama Hafsa ta taho dan ta wulaƙantani tunda gidan Babanta ne , amma tana zuwa labari yasha banban duk wannan taron jama'ar bai hana uban Hafsa rungumeni ba ya yanko cake yana bani a baki , gaba ɗaya wurin aka ɗauki sowa da ihu shi dama Alaji tunda ya ajiye kayan party nace kawai yaje tunda taron mata ne babu maza , kuma yayi tafiyarshi... Lallaɓawa tayi ta koma da baya ba tare data bari wani yaji koya ganta ba , ihu akaci gaba dayi sakin sauti akayi yadda ya kamata mata sukaci gaba da farantawa sheɗan , Hafsa tana fita taci karo da Dikko ya fito daga mota , da gudu ta nufi wurinshi tana kuka cikin kuka ta fara faɗa mishi abinda Sultana tayi mata niko nace danma baki ga vidio ba , number wayar Sultana Dikko ya ansa a hannun Hafsa ya fara kiranta , Muna ta cashewa wayata ta fara zurzur dan ba ƙara takeyi ba murzawa takeyi sai kaji sautinta yana shiga maka hannu burbur , ɗauka nayi naci gaba da kwantace ba tare dana jira naji ko waye ba , Cikin wata irin murya yace fito gani nan na kasa gane gidan , wallahi banyi tunanin Dikko bane nayo waje , ina fitowa naga Hafsa tsaye da wanda bansan ko waye ba domin ya juya bana ganin fuskarshi sai bayanshi , cike da mugunta nayo wurinta dan a tunani na taga vidio zamu cashe rashin mutunci , Saida nazo gabansu na gane Dikko buɗe baki nayi da zumar nayi magana ya wanka min wani irin gigitaccen mari harsai dana juya kamar ranfa saboda karfin mari kafin in dawo hayyacina ya sake wankamin wani firgitacce wanda saida nayi ɗimuwar tunani na dan wallahi a daidai lokacin da zaka tambayeni suna na bansan abinda zan faɗa maka ba , Ƙara ɗaga hannunshi yayi zai kaimin wani marin a gigice na riƙe hannun cikin kuka nace yi haƙuri don Allah , a tsawace yace tou shiga mota , har yanzu dafe nake da inda ya mareni na nufi wurin motar da kanshi ya buɗemin na shiga sannan shima ya shigo dani dashi ne a baya , rufe murfin motar yayi Al' Ameen yaja sauran motocin suka biyo bayanmu... Duƙar da kaina ƙasa nayi ina kuka cikin sauti mara hayani jikina sai kyarma yake dan har yanzu marin shiga jikina yakeyi , 20/09/2019 Jamila Musa ..... 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 36 Duƙiyar ta isheni na ɗago hannuwana na rumgume kujerar da ake kira da mai zaman banza , ta kusa da Al 'Ameen babu kowa akai dan haka na rumgumeta kawai naci gaba kuka , Kallon hannuna Dikko yayi idonshi ya sauka akan wayata kawai ya miƙa hannunshi da zumar cirota daga wurina , da sauri na ƙara riƙe wayar gam tunda bana saka ma waya wasu malatsan sirri wanda saini na buɗe da kaina zata buɗe a buɗe take zaka iya shiga duk inda kake so... Da ƙarfinshi ya fizgi wayar kafin yayi mata kyakkyawan riƙo na fizgeta a hannunshi dan bai kamata ace anga wannan ɗaukar ba bai kamata ba , miƙo hannunshi yayi tare da kauda kanshi gefe yace bani , Girgiza kaina nayi alamar a , a , cikin tausassar murya ya matso da fuskarshi kusa dani yace bani wayarki nace , matsawa nayi tare da ƙara saƙe wayar a bayana , shima matsowa yayi kusa dani yace zaki bani ko sai kinci cingom ne ... ? Cikin kuka nace dan Allah ka shafamin lafiya , kallona yayi gefe da gefe sannan yace ta ina zan shafa miki inyi sauri dan nafi so kiyi lafiya da nisan kwana ya ƙarasa maganar yanamin kallo mai nuni da rainin hankali , nima kallon raini hankali nayi masa amma banyi magana ba , Shima shiru yayi bai sake magana ba kuma ya daina maganar in bashi waya , daga haka dukanmu babu wanda ya sake magana har muka zo inda zamuzo , duk sauran motocin a waje suka tsaya tamu kaɗai ce aka buɗe ma get muka shiga , bayan Al ' Ameen yayi parking ya fita daga cikin motar aka barni daga ni sai Dikko ! Al ' Ameen na fita Dikko ya sake taro hannu in bashi waya , cikin kalar ban tausayi na maida hannuwana baya tare da cewa dan Allah kayi haƙuri , ni nace kinyimin laifi ne ? Wayarki kawai zaki bani nace ya ƙarasa maganar cikin kausasa murya yana zazzaro idanuwa , Tsoro naji ya kamani sosai dan haka da sauri na miƙawa Dikko wayar , ansa yayi yana mai min ƙwafa tare tare da latso wayar haske ya bayyana , kafin ya shiga inda yake so kiran Amisty ya shigo cikin wayar , badai serving nake da sunan mutum ba lamba ce kawai , dan haka kiran sunan lambar dana ajiye number Amisty yayi sannan ya shafa wayar ya kara a kunnenshi , Dafe kaina kawai nayi lokacin da Amisty ta fara watso kalamai masu zafi da ɓatanci akaina sai ta ciko bakinta da ashariya sannan ta luƙaƙamin tare da furta wallahi idonta idona sai takaini kiyama ta dawo , maganganun dai babu daɗi dan har mahaifina ta saka duka dai abun gwananin ban takaici , tana zurara zagin wayar Hafsa ta shigo , amma bai ɗauka ba saida Amisty ta sauka ta kashe wayar , har ya gama waya da Amisty kiran Hafsa daya tsinke sai ta sake kira.... Itama Hafsa ta tata nata rashin mutunci itama a kalaman nata maganganu tayi masu kyaushi itama dai abun babu daɗin ji , idan tayi magana taji Dikko baice uhum ba , sai tace kina jina ko ? Sai yace Umm itama itace ta gaji ta kashe wayarta... Cikin takaici Dikko ya kalleni tare da cewa fita , ina zanje ? Rumtse idanuwanshi yayi tare da sake cewa fita bana san ganin ki wallahi komai zai iya faruwa ki fita kafin naji miki ciwo , ƙaruwa hawaye na sukayi nace da Allah wai ina zanje ? Ki fita........ Ya faɗa cikin murya maisa firgici babu shiri na buɗe mota na fito , sai yaita yin abun kamar wani shafar aljannu , Ina fita Al ' Ameen yace muje ciki yayi gaba babu musu na bishi muka matsa , makulli yasa ya buɗe ƙofa sannan ya shiga , nima shiga nayi palo ne mai girman gaske sai wasu ƙoƙofofi biyu da bansan ko ina ne ba , makullin ya ajiyemin a saman hannun kujera yamin saida safe.... Banyi magana ba na saki baki kamar lefen wawiya ina kallonsu suka fice daga gidan , dan daga cikin palon zuwa bakin get ba wani nisa kuma daga cikin palon kana hange duk wanda yake bakin get , wuri na samu na zauna ina maijin takaicin rashin kasancewar wayana a kusa dani , A ɓangaren masu party kuwa saidai shagali yayi nisa sannan aka gane bani a wurin , nemana aka farayi amma ina mutane basu ankara ba Dikko yayi layar ɓata dani , wasa ² abu ya zama gaske yayin da wasu ke cewa sunga anmin waya na fita , nemana aka shiga yi amma babu ni kuma babu labarina.... Dikko kuwa asibiti suka fara zuwa ya ƙara duba Sadiya da jiki yayi mata nasiha ya lallasheta , saidai tayi murmushi mai tattare da ƙuna da baƙin ciki tabi Dikko da kallo mai ban tausayi , duk da yawan murmushi ba ɗabi'arshi bane idan tayi murmushi shima sai yayi mata dan ta samu natsuwa domin shi kanshi yasan murmushin shi wani sirrintaccen sirri ne da Allah yayi masa baiwa dashi badan halinshi ba , murmushi yana ma Dikko kyau sosai kuma murmushin shi yana da ɗaukar hankali da burge duk wanda ya gani , Saida Sadiya ta samu bacci Dikko yayi sallama da wanda zasu kwana da ita ya wuce gida , yana zuwa wanka yayi bayan ya fito ya saka riga da gajeran wando na jersey palo ya dawo ya zauna zuciyar shi na mishi babu daɗi , gaskiya tunda yake a shakarunshi bai taɓa cin karo da yarinya mai taurinka da rashin ji kanta cike da iskanci ba irin Sultana , a shekarunta har tasan taje ta ɗauko vidion tsiraicin uban wani ta tura ma ɗiyarshi , Shi kuma Babanta shima dai anyi tsohon banza ka rasa wacce zakayi lalata da ita sai ƙawar ɗiyar daka haifa , kai abu yayi muni gaskiya , jinjina kanshi yayi shi idan shine duk su Sultana ba mata bane a wurinshi , ko iskanci zakayi da sakarci ai ka samu macen da ta cika mace ta ansa sunanta takai mace ta ko ina da ko ina mai cikakkiyar zarra ba wannan jagwalgwalon yaran ba , Ya daɗe yana zaune palo yana tsaƙawa yana kuncewa wallahi zai tsaya saman ƙafafuwan shi ya cusa wa An mata soyayyarshi a zuciyarta idan ya riƙo ragamar rayuwata wato zuciya yasha da ita kuma ya gama da ita har abadan duniya , zata ga girmanshi tasan darajarshi saboda wannan kamun da yayiwa rayuwarta , Wayarta ya buɗe yayi binciken duk da zaiyi bayan ya gama ya rufe wayar gaba ɗaya tare da zamewa saman kujera yaci gaba da bacci ! A ɓangaren Babana kuma yana can gidan caca baisan wainar da ake toyawa ba a gidan , yana can ya shawu an zinatu kuma akaci gaba da caca , baya tunanin komai na ɓacin rai bare kuma halin da iyalinshi suke ciki , sabgar gabanshi ya saka a gaba kuma ita yakeyi baiji duk faɗin duniyar nan ba akwai mai iya dakatar dashi akan abinda ya saka kanshi ba.... Gajiya nayi da tsayuwa na tunkari ƙoƙofin biyu da na gani a jere , ƙofa ɗaya a rufe take ɗaya kuma a buɗe , turawa nayi na shiga da sallama a baki na , ɗan madaidaicin palo ne da kujeru masu kyan gaske na leda , sai labulaye masu kyau da tsada wanda suka dace da kujerun , a gefe kuma ga ƙatuwar talabijin girke a tebirin ajiyarta kamar zata ɓaro ƙasa saboda girman ta , abundai zabburgewa , ciki na shiga wato ɗakin bacci babu gado sai ƙatuwar katifa da "yar ƙaramar talabijin liƙe a bango , labulayen suma irin na palo ne , toilet na leƙa sannan na fito daga ɗakin duka nayo waje inga ko ni ɗaya ce a gidan ! Wasu irin murɗaɗin ƙattin mutane na gani marasa kyan gani yanayin duk ko wane ɗaya kamar ɗan rastilin amma su wanɗan nan baƙaƙe ne , suna gani suka yo kaina suna wata irin magana mai tada hankali wallahi saboda tsoro saida na saki fitsari a wurin , saboda wallahi siffar su bata da kyan gani abun tsoro ce abun firgici ce idan kuma sukayi magana sai kaji kamar ba duniya kake ba , tsaye nayi wurin saboda tsoro na kasa gaba na kasa baya , ruɗewa tasa na manta da ina da ƙafafuwa ... Tunzura babbansu yayi yanayin shi ya nuna yana cikin ɓacin rai dan haka yayi wani irin kuka mai motsa tunani ya ƙara takowa dan ya samu damar matsowa kusa dani , nidai bansan ya akayi na ruga ba saidai kawai na ganni saman katifa har na lulluɓe da bargo ina kuka ! Bansan lokacin da bacci ya ɗaukeni ba , Da safe Dikko daga masallaci asibiti suka nufa daga shi sai Al ' Ameen , har yaje ya dawo Sadiya bacci takeyi , bayan ya dawo gida ne ya kira danjin ita kuma An mata ko ta kwana lafiya , lafiyanta qalau suka faɗa tare da bashi labarin abinda ya faru , mugu yaji mugunta , dariya Dikko yayi sosai tare da cewa zaizo anjima ai , Ba'a mugun sarki sai mugun bafade , Al ' Ameen bayan Dikko ya gama waya yace mai gida dan girman Allah ka kyale yarinyar nan tayi tafiyarta , sai kace dai itace kaɗai mace a duniya ? Yarinya mara kunya mara tarbiyya mara ɗa'a masu gajeren asali wallahi mutuncin gidanku da nasabarku da kai kanka taka mutuntakar ta wuce ace kana sauraren yarinyar nan wallahi , kana da zarrar da duk macen data ganka duniya sai tayi addu'a ta sameka a matsayin abokin rayuwarta. Kana babban asali ga cikar zati ga kyau ga kwarjini me zakayi da yarinya mara tarbiyar ? A hankali Dikko ya lumshe idanuwanshi dan duk duniya idan akwai kalma mafi muni da ɗaci a wurin shi bata wuce ace An mata bata da tarbiyya ba , Al ' Ameen yaci gaba da cewa uwa uba kuɗi kana da cikar arziƙin da zaka iya auro mace ko wace iri ce kai ko babu kuɗin sai ta so ka dan kyan ka , abin kunya daci baya ne ka auri ɗiyar ɗan caca mashayin giya manemin mat.... Hannu Dikko ya ɗaga alamar dakatar dashi , shiru yayi bayan yayi shiru yayi masa nuni da ya fita kawai , Allah ya baka haƙuri mai gida ya faɗa cikin girmamawa sannan yabar ɗakin , Fitar Al ' Ameen Dikko ya fara nazarin maganganun shi tabbas duk abinda ya faɗa ba ƙarya bane ba , ko wane mai asali yana so ya auro mai asali gidan tarbiyar da mutunci amma miye aibun An mata ? Duk dai haɗa jini da mutane banza bashi da wani amfani dan ba'a gane matsalar hakan sai zuri'a sunzo dan iskanci jini yake bi , tou amma mi yasa ita An mata batajin magana ne ? Wani sashe na zuciyarshi yace ba komai wata rana zata daina , idan har mace tana shakkun namiji idan dai ya shata mata doka tou fa tabbas ba zata karyata ba , wani sashe kuma cewa yayi matsalar ba'a nan take ba , tsoki Dikko yayi tare da cewa da Allah ku barni... A ɓangare na kuma , da asuba ina farkawa kayan jikina na cire na wanke su saboda na ɓatasu da fitsari na goge katifar dake da leda a jikinta kila ma sabuwa ce , labule ɗaya na ciro na ɗaura , bayan na gama wanke kayan a palo na shanya saman kujera na kunna fanka , ɗaki na koma na shiga nayi wanka tare da ɗauro alwalla , bayan na fito na sake ciro wani labilen na rufa dashi naci gaba da sallah.... 🤔 Bayan na gama na koma na kwanta , ban daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗaukeni , dan banda wata damuwa saidai kaiwai ina so in tafi gida , Ina bacci Dikko yazo kuma tun a palo na fara jin faɗashi wai waye yace kujera wurin shanya ne ? Da sauri na tashi na ɗauki bargo na ƙara lullube jikina a dai² lokacin da naji Dikko yace maza cire wannan tsumman kaje ka jefar dashi a waje , kutumelesi ? 😭 rigata mai tsada itace za,a yadar ? Amma dai wallahi Dikko ɗan iska ne , kuɗi fa masu yawan gaske Alajina ya siyamin ita shine zaisa a yado ta , Ina cikin kuka naji ƙarar takalminshi yana tahowa ɗakin da nake , ci gaba nayi da kuka ko zai tausayamin yasa a dawo min da rigata , kwance nake cikin bargo fuskata kaɗaice a waje ina kuka , ƙamshin turarenshi ya ƙara matsowa kusa dani haka ya tabbatarmin yana gab dani dan haka na buɗe idona ina kallonshi , Murmushi yayi cikin natsuwa sannan ya fara magana cikin kamun kai da aji , gaba ɗaya jiya da daddare tunaninki nai tayi , da sauri nace me ? Murmushi ya sakeyi sannan yaci gaba da cewa tunanin da nayi tayi cikin dare shine nayi kuskure , sam bai kamata ace na ɗaga hannu na mari mace ba , kiyi haƙuri don Allah idan ma baki gamsu ba zaki iya rama marikin kamar yadda na mareki , ƙoƙarin tashi na farayi dan rama marina , cikin magana mai kama da raɗa yaɗan fiddo kyawawan idanuwanshi yace a haba keko ba'a nan ba kinsan babu kaya a jikinki koma kawai ki kwanta , Babu gardama na haƙura na koma na kwanta , fita yayi bai daɗe ba ya shigo da wani haɗaɗɗen kwando ya ajiye a can gefe cikin magana mai laushi da kalamai masu burgewa yace kiyi kalaci ya faɗi maganar tare da nunamin inda kwandon yake , zai fita nace am da Allah idan babu damuwa rigar nan kada a yadar da ita anjima idan zan tafi ita zan saka , Ba tare daya kalleni ba yace bama buƙatar ita rigar kayanki yanzu zansa a shigo miki dasu palo , wai ance jibi hutun ku zai ƙare idan zan wuce zan ajiyeki makaranta , kallo ni yayi tare daci gaba da cewa kyakkyawar fuska da kyawawan idanuwa irin naki gararin gari ba nasu bane da ilimi suka dace bada taron murnar zagayowar shekarar aihuwarki ba , yana faɗin haka yayi gaba abinshi , ni kuma nace wallahi aiko babu sakaran da ya isa yakaini makaranta tunda ba cewa nayi ina so ba , dawowa yayi tare da cewa kina magana ne ? Banza nayi dashi naci gaba da hararar ƙasa , Murmushi yayi da gefen bakinshi ya fita , yana fita na ƙara cewa kuma ko ka kaini saina dawo dan kaga na kwana nan gidan nan ko an faɗa maka ni ina tsoron waɗanda ka ajiye ne ? Sake dawowa yayi yace kina so ki madani kamar wani sa'ar wasanki ko ? Tou idan kinje makarantar ki gudo mu gani , Dikko ya kaiki saboda haka Dikko zaici gaba da ɗauko ki , ke ɗaya na bayar kuma ke ɗaya za'a bani a ko wane hutu , kuma ko hutu akayi idan ba nine naje ba ko waye wallahi yarinya bazaki dawo gida ba gara ma ki fara kamun ƙafa tun yanzu ko zan riƙa ziyartarki lokaci ² idan kuma kika nunamin yarinta sai ina barki kisha baƙar wahala babu abinci babu kuɗin kashewa , yana faɗin haka ya fice abunshi , Ni kuma ƙasa² nace sai inyi ta iskanci da malam su sa fiddoni , in dawo gida , kuɗinkan banza kuɗinkan wofi ko an faɗa maka ni matsiyaciya ce ? Hahaha niko nace da kanki ma zaki riƙa cewa ya baki bari dai kisha azaba yarinya .... A palon ɗaki na Dikko yasa aka ajiyemin kayana saman kujera , shi kuma yayi tafiyarshi , saida naji fitar motarshi na tashi naje na ɗauko kayan na saka ina sakawa ina mita ni za'a bawa kwance kila ma kayan matarshi ne ya ɗibomin , kona ƙannenshi , niko nace kedai kika sani... Ɗaki na dawo ina cewa shikenan an yado rigar Alajina daya ji kuɗin rigar shi kanshi nasan sai gabanshi ya faɗi , Allah yasa ya dawo yanzu yace in rama marina saina ci abinci na ƙoshi zan zabgaga mishi mari sai yayi fitsari saboda azaba , Gaban kwandon na durƙusa ina ci gaba da surutu babu kai babu misali , kwalin makilin da burosh a gefe da sauri na fara buɗewa dan inga abinda aka kawomin inyi kalacin safe dashi ..... 21/09/2019 *JAMILA MUSA...*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 37 Gayu mutanen Allah shine abinda na furta a lokacin da naga shagalin dake cikin food flarks , murmushin jin daɗi nayi wai duk ni ɗaya zanji daɗi na , miƙewa nayi tare da komawa da baya cikin farin ciki na faɗa saman katifa zanci daɗi yau zanyi kalaci da farfesu , ga doya ga farfesun "yan ciki , wannan daɗi da hawa tsaunin rayuwa har haka ? Ɗaga ƙafafuwana nayi sama ina musu shangululu tare da rumgume duka hannaye na a ƙirjina cikin farin ciki nace wallahi madarar ma duka zan juyeta... Wani irin ihun farin ciki na kurma wanda har na waje saida sukaji ni , da sauri na sauko daga saman katifata naci gaba da aiki dan gani nake idan na tsaya wanke baki a iya shigowa aga kamar na gama a fita dasu , ina ci ina kaɗai kai tare da addu'ar rayuwa ta ɗauremin da irin wannan daddaɗan kalaci , naci komai kuma komai nasha nayi hamdala ga ubangiji da ya bani aron lumfashi ya bani baki da ciki da lafiya kuma ya ruboto min wannan babban rabo da alƙamin kudarar shi... Ina gamawa na tattara komai na fitar palo , labulayen dana ciro na ɗaura na mayar dasu mazauninsu na gyara , saman katifa na dawo tunda dama nayi wanka cike da farin ciki na lumshe idona na tafi duniyar bacci.........! Tashin hankali a gidan su Sultana , cike da farin ciki Baba ya shigo gida ya dawo da kuɗin shi cike da aljihu domin a daren jiya shi ya lashe maƙudan kukaɗaɗen da aka zuwa a wasan caca , ƙofar ɗakin Sultana ya nufa kai tsaye yana cewa Mamana kin ganni sai yanzu ? Kowa yayi cirko² domin "yan gidansu Sultana tun jiya suka dawo da labarin ɓatanta , kowa dai yana cikin jimami da tashin hankali , Baba kuwa bayan ya shiga ɗaki shiru² bai fito ba dan a tunaninshi Uwar masu gida tana bayi ne... Zama yayi har ya gode Allah , komi Uwar masu gida takeyi ai ta isa ta gama ta fito gajiya yayi da zama ya fito tsakar gida yana cewa ina Mamana taje ne ? Shiru kowa yayi ya kasa magana , bin kowa yayi da kallo yanayin fuskar su ta nuna akwai wani abu daya faru , bayan ya gama kallon kowa yayi magana cikin karyewar zuciya cewa ina Mamana...... Take ? Ya ƙarasa maganar yana mai bin bango ya sulale ya zauna ƙasa a hankali , Maman Fa'iza ce tace mu saka Sultana a addu'a domin yanzu ba abinda take buƙata sai addu'armu mu dage da roƙon Allah har ubangiji ya bayyana mana ita domin Sultana dai ta ɓata , lokaci guda zufa ta ɓarkewa Baba ya tsurama wuri guda ido kamar mage ta ɗana tarko , bayan wani lokaci kuma yace haka zakimin Mamana ? Haka mukayi dake ? Wannan shine sakamakon alƙawarin ? Ina kika tafi ne ? Inajin babu jimawa mukayi magana dake baza ki taɓa tafiya ki barni ba , shine kika tafi kika barni..... ? 😭 hawaye ya gangaro mishi daga cikin idonshi , daga nan yayi na wani mawaƙi da yace ayye mata a ƙame ƙam , tou Baba shima ya ƙame kamar wayar da tayi hucking.... Tunda na kwanta bacci babu abinda ya dameni kuma bana wani tunanin komai haka kuma banga komai ba a cikin mafarki na , bacci na nakeyi cikin natsuwa da kwanciyar hankali , sai da aka kira azahar na farka nayi sallah bayan na gama na watsa ruwa na koma nayi kwanciyata amma ba bacci nake ba ! Gidan shiru kamar babu kowa ciki sai ƙarar iska irin mai tahowa da ƙasa , a hankali sanyi ya fara saukowa irin mai shiga ƙashin nan , zuwa bayan la'asar sanyi ya sauko sosai wanda yasa mutane suka fara saka rigunan sanyi, Ni kuma da banda rigar sanyi ina cikin bargo na duƙunƙune , ga azabar yunwa da nakeji na rasa inda zan saka rayuwata , har akayi magrif babu wani labarin abincin rana bare in saka ran na dare zaizo , nasha ruwa har nayi fitsari bansan adadi ba , tun ina daurewa har na fara Allah ya isa a zuciyata... Tunda nayi magrif ban tashi daga inda nayi sallah ba ina zaune na zabga tagumi kuma ni ba addu'a nakeyi ba , ina cikin wannan tunani naji ƙarar buɗe get murmushin jin daɗi nayi nasan Dikko ne kuma yazo da abinci , tabbas abinci yazo ya kawomin , cike da murna na leƙa ta window kuma wallahi shiɗin ne , sanye da tsadajjiyar baƙar rigar sanyi mai kyan gaske da burgewa tana da farin zif daga gaba , an zageye wuyan rigar da farin ado amma ba irin na mata ba ina ganin dibara ce dan kar rigar ta lalace daga saman wuya , sanye da shuɗin wando da takalmi baƙi amma ba rufaffu bane maɗauri gare su kamar sandals , hannun rigar ya ɗan naɗeshi zuwa guiwar hannu , kanshi babu hula kuma fa gaskiya yayi kyau dake baida ƙiba ko kaɗan amma yana da tsayi daidai burgewa bana zarce misali ba... Al ' Ameen ke ɗauke da kulolin abinci shi kuma waya yakeyi , ina ganin sun tun karo ƙofar shigowa palon nayi sauri na kowa saman abin sallah na kalli gabas , Suna shigowa shi Al ' Ameen ya kunna musu kallo , maimakon ya kawomin abinci sai kawai suka zauna sukaci gaba da kallon kwallo , har akayi isha'e suna zaune kamar asara suna kallon kwallo , inajin maganar Dikko lokacin daya shiga ɗaki mai kallon wanda nake ciki yana cewa bari inyi sallah dai , tsoki nayi tare da cewa andai ji kunya sallah a gida , nima tashi nayi nai sallah dan ina da alwallah ... Har na gama sallah banji Dikko ya fito ba , kuma naji palon ya fara cika da maza ga dukkan alamu kila gidan dai matattara ce ta maza , tunani na farayi karfa su cinye abinci ban samu ba , tashi nayi na fita ɗan madaidaicin palon na zauna ina jiran fitowar Dikko idan ya manta da ina nan tou ya ganni ya gane ina nan , Tunda na zauna ƙarar motoci ke shigowa , hayaniyar sai ƙara sama takeyi maza surutu ga magana babu natsuwa , nafa daɗe ina zaman jiran Dikko bai fito ba , kuma bana so na leƙa babban palon bansan ko su waye a wurin ba , na haƙura da niyar komawa ɗakin da aka ajiyeni naji dai bazan iya kwana banci komai ba yunwa nakeji kamar zan mutu wallahi , dawowa nayi kai tsaye na shiga ɗakin , Da sauri ya kallo ƙofar dan yaga waye yake shigowa yana zaune saman abin sallah , murmushi yayi ganina tare da cewa An mata miye ? Ɗan suɓaro baki nayi ina wasa da yatsun hannuna nace dama , sai kuma nayi shiru , ɗauke kallonshi yayi daga gareni yace dama me ? Shiru nayi na kasa magana , shima bai sake magana ba yaci gaba da latsa counter , naci uwar mintuna sha biyar Dikko bai sake kallona ba kuma bai sake magana ba , Saida ya gama abinda yake ya ɗauke abin sallar daga inda yayi sallah ya ɗora gefen gado , zuwa yayi zai wuce ya fita dan yayi kamar ma babu ni a wurin , Ya kusa fita nace yunwa nakeji , yi yayi kamar baiji abinda nace ba ya fice abunshi , biyoshi nayi a lokacin har ya kusa fita daga palon ya shiga babban palon , nace da Allah nace maka yunwa nakeji nayi maganar a tsiwace , naji ya faɗa tare dayin gaba abunshi , Tsoki nayi cikin ɓacin rai na koma ɗaki ina gunguni , shi kuma daya koma kallonshi yaci gaba dayi , sai ihu sukeyi "yan iska kamar mahaukata , amma bana tunanin Dikko yana wurin dan har yanzu ban jiyo maganarshi ba , duk wanda aka ci su sai kuji hayani ta ƙara sama , sai gaddama da magana cikin faɗa² , Sai yanzu naji dariyar Dikko yana shigowa cewa ko gobe da fansar kura saidai garin da babu awaki , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya nace ashe kaima ka iya karin magana ? A dai² lokacin daya shigo yana dariya , Ɗaure fuska nayi kamar ina cikin yanayi damuwa , ko kallonshi banyi ba ya ɓatamin rai ni zai zubowa abinci a gaban bainannasi hmm , ga abinci ya faɗi maganar a daidai lokacin da yake ajiyewa a gabana , kauda kaina nayi na tura abincin na ƙoshi ... Murmushi yayi tare da ɗaukar abinci zai fita , nace kai nifa wasa nakeyi bani nan nayi maganar tare da nuna mishi ya maidoshi gabana , banza yayi ya fice daga ɗakin da sauri na tashi nabi bayanshi amma kafin in fito harya fice ya koma cikin abokanshi yana dariyar mugunta , a ranshi yace daga yau sai kiyi hankali ni ban iya wasa ba kuma ba'amin wasa , Wannan rana saidai na kwana da yunwa nasha kukana har bacci ya ɗaukeni bansan lokacin da suka tafi ba , Koda safe dakel nayi sallah saboda yunwa duk jikina ciwo yakeyi kamar nayi aikin ƙarfi , bayan na gama sallah na daddafa nayi wanka , na canja kaya sannan na koma bacci , Yauma da asibiti ya fara , ya lallashi matarshi kamar yanda ya saba , yau ya samu ya lallaɓata tasha ruwan tea , ya kuma sake tambayarta damuwarta dai tayi masa zurfin ciki har yanzu , dan haka bai wani damu ba ya wuto wurina , Yau shi ɗaya yazo babu Al ' Ameen kuma kai tsaye ya shigo ɗakin , bayan ya ajiye kayan da yazo dasu ya kunna fitila yana cewa anya ma kinyi sallah ? Tashi ya faɗi maganar tare da yaye bargon dana lulluɓe , juyawa nayi na kifa kaina saman katifa saboda haushi ya bani jiya sosai , Yauma bakijin yunwa bara in tafi , ya faɗi maganar tare da ɗaukar kwandon , cikin fushi nace abinci banza gare ka , ko an faɗa maka yunwarshi nakeyi muma gidanmu sau 3 a rana akeci ka tafi na ƙoshi nasan yunwa baza ta kasheni ba an girma ba'asan an girma ba , Dariya yayi tare da zama gefen katifa yace wai nima irin wasan jiya nake miki amma ke naji kalaman naki zafi garesu ai kema da sai kiyi shiru kamar yanda nayi shiru jiya , sai kace dai kina jirana ? Cike da jin haushi na tashi zaune ina cewa jiranka nakeyi kamar yadda ka zanemin rayuwata haka zan zane taka rayuwar babu gudu babu ja da baya ba abinda ke cikin zuciyata face ɗaukar fansa akan ka , Murmushi yayi tare da gyara zamanshi sannan ya ɗaure fuskarshi babu wasa a tare da ita ya fiddo siffofinshi masu tayar da tsikar jiki da saka fargaba yace ke har gobe yarinya ce , amma ki sani ya nuna ni tare da ci gaba da cewa wannan tsarin tamkar sautin radio na ne , na ƙarashi na rageshi yadda nake so , kiyi haƙuri burina kaɗan ne amma sanin ya kamata na yana da ƙarfi , ban iya ba kece kika koyamin kinsa na zama kamar wani sakarai sai biye miki nake ina ƙananan maganganu kamar mace , dakamin tsawa yayi tare da zaro idanuwa sannan ya sassauta maganar shi zuwa sauti mai kama da raɗa yace ki kiyayeni kafin na baki hukunci a karo na biyu , azabar yau sai tafi ta jiya zafi , ina nan kuma namijin ne .... 🤫 ya ƙarasa maganar tare da ɗora ɗan yatsanshi a saman bakinshi yace shitt ya rufe maganar da fiddo idanuwanshi da suka ɗanyi ja... Jiki a sanyaye na koma na kwanta , ba tare daya kalleni ba yace tashi muyi break , da sauri na tashi naje na wanko bakina da fuskata nazo na zauna kusa dashi cikin ladabi , shine da kanshi ya zuba komai amma tea ɗin a kofi ɗaya ya haɗa kuma da kofi ɗayan mukayi amfani yana sha ya bani insha in miƙa mishi , cokali ma ɗaya mukayi amfani dashi , Ba wani damuwa a tare dashi ko kunya ko irin yaji babu daɗi haka dai , tsakaninshi da Allah hankalinshi a natse yake , har muka gama da kanshi ya tattara komai ya mayar a kwandon ya ɗauka kwandon ya fita , ya daɗe sannan ya dawo ya kwanta a gefen katifa , Wayarshi ya ciro yace zo kiga in nuna miki "yan uwana , matsawa nayi kusa dashi amma ni ba kwanciya nayi ba zama nayi , ɗago kanshi yayi tare da bani wayar na riƙe a hannuna yana wuce hotuna , wannan itace wance wannan kaza ce dad ina ne kinga momy kinga wannan itace nake bi mawa , tana aure a gari kaza , haka dai yayi ta wucewa har yazo kan Sadiya yace wannan kuma matata ce.... Kai kalmar namiji yace matata kalmar tana da girma da matsayi , matata saida na maimaita a zuciyata sannan nace ban ƙaunarta har abadan duniya na faɗa a zuciyata , kallona Dikko yayi tare da cewa tayi kyau ko ? Ban sani ba nace masa , baiyi murmushi ba kuma baiyi dariya ba yace kada Allah yasa ki sani "yar rainin hankali , Cike da ɓacin rai nace dakai da matarka duk kune "yan rainin hankali munafikai dukanku , tsareni yayi da ido tare da cewa kishi ko ? Ya ƙarasa maganar yana nunani da san yayi murmushi amma ya haɗeshi , tsoki nayi tare da cewa hmmm Allah ya sawaƙe min niko waye zanji kishin a cikinku kai ne ko ita ? Miƙewa yayi tare da cewa tunda baki son na tayaki fira zan tafi , bazan dawo anjima ba Al ' Ameen zai kawo miki abinci , idan Allah ya kaimu gobe lafiya ki shirya da wuri dan bana san tafiyar rana , yana faɗin haka yayi gaba abunshi.... Abinci rana da dare duk Al ' Ameen ya kawo min , yau babu wanda yazo kallon kwallo ni ɗaya a gida bayan naci nasha na koma na kwanta tare da addu'ar Allah ya kaimu gobe lafiya ! Da safe tun kafin in tashi bacci Dikko yazo , shi ya tasheni tare da ajiye uniform a gefen kati yace maza jiranki nakeyi , kallon kayan nayi sannan na kalli Dikko da yasha manyan kaya hada babbar riga hular kanshi kuwa sai sheƙi takeyi saboda sabinta ko wanki ne ? Koma dai miye sai ka kalli kanka a ciki kayi sakace , kallon ƙafarshi nayi nan ma komai yaji gemu ma dai yasha gyara yana nan dai da jan hankali da yakeyi , gaskiya Dikko haɗaɗɗen namiji ne mai tafiya daidai da zamani , ga kyau ya gayu uwa uba iya saka sutura , Dikko nada burgewa ... Katse min tunani yayi da cewa kin tsaya kina kallona ! Kiyi maza jiranki nakeyi , yana faɗi maganar yabar ɗakin , cikin kuka na nufi toilet nayo wanka sannan nayo alwalla nazo na fara gafatar da sallah asuba da banyi ba akan lokaci , bayan na gama na shirya cikin kayan makaranta ina kallon kaina a madubi na fashe da wani irin kuka wanda har sai da gaban Dikko ya faɗi... Da sauri ya shigo ɗakin fuskarshi ɗauke da damuwa yace a mota zakiyi kalaci , shi a tunaninshi yunwa nakeji , cikin kuka nace ni wallahi bana san makaranta haba Yaya Dikko me yasa zakamin haka abin kunya a ganin a makatanta yanzu , Wani irin kallon rainin hankali yayi min daga sama zuwa tsakiya ta yace lallai yarinyar nan kin rainani nine Yayan naki.... ? Baki da hankali ma da Allah ni wuce mu tafi munatane na jirana , hannu na ɗora saman kai ina cewa dan girman Allah ka kyaleni wallahi bazan sake ba , cikin kwantar da murya yace muje tun kafin kiji babu daɗi , 😭 hijabi na saka nabar kallabin a katifa nayi waje , abun kunya shi ya ɗaukomin kallabin wai hada jakkar makaranta saboda ci baya , waini zan koma makaranta , ina gaba yana bayana har cikin mota , ni kaɗai na shiga baya ya wurgomin jakar da kallabina ya rufe ƙofar ya shiga gaba , Al ' Ameen yaja muka fita daga gidan , kuka naci gaba dayi ina ma katsina kallon ƙauna , tafiya akeyi sosai dan Al ' Ameen yakai mota maleji wurin gudu , kuka na ya ƙaru lokacin da naga an ibi hanya tafiya da gaske babu fashi....... ! 22/09/2019 *JAMILA MUSA CE...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 38 Ƙuramin idanuwa yayi yana kallona ta cikin madubin gaban mota , sai kuka nake ina fyace majina da gefen hijabina , tissue ya wurgomin bai juyo ba kuma bai kalleni ba yace zaki ma mutane shiru haka nan ko kuma dai.... ? Harararshi nayi cikin muryar kuka nace mara zuciya ko mutum baya harkar ka sai ka shiga nashi mutum ba dangin uwa ba na uba kawai ka shigomin rayuwa , kyakyawan murmushi yayi da gefen bakinshi amma baiyi magana ba , kallonshi Al ' Ameen yayi bakinshi ɗauke da magana , murmushi Dikko yayi tare da cewa manta da labarinta ka ƙaddara ma bama nan bare kayi tunanin munji abinda tace , makaranta dai zuwa babu fashi ! Shiru sukayi su dukansu babu wanda ya sake magana , saidai shi Dikko yana kallona ta cikin madubi idan akayi sa'a muka haɗa ido sai yayi murmushi mai tattare da mugunta , matsawa nayi daga saitinshi dan ya daina kallona , ƙara gyara saitin madubin yayi yaci gaba da kallona , kwanciya nayi na lulluɓe da hijabi naci gaba da baccin dole... Har nayi bacci na farka bamu isa ba , kuma tafiya Al ' Ameen yake bata wasa ba dan shima kusan irin tuƙin Dikko yakeyi kamar basa san rayuwarsu , ganin har yanzu a hanya muke yasa na sake komawa na kwanta ina mai ci gaba da kuka , jin kukana yasa Dikko juyowa tare da cewa ke miƙomin kunun nan tunda baza kisha ba , Cikin kuka nace ina sha , Al ' Ameen yasa ya faka a gefen titi da kanshi ya fita ya ɗauko ruwa a but sannan yazo ya buɗe inda nake ya bani ruwan , yana nufi in kuskure baki na , fita nayi na kuskure bakina na wanke fuskata na koma mota na zauna , Ɗan ƙaramin flaks ne na sulba mai kyau cike da kunun gyaɗa tun kafin in fara sha Al ' Ameen ya tada mota ya hau titi yadda ta kamata yaci gaba da gudu , cike da baƙin ciki nake shan kunun , yayi min daɗi sosai ɗan kaɗan na rage na miƙawa Dikko flarks in dan ya ajiye , ansa yayi ya shanye sauran dana rage, a raina kuma tunani nake Dikko ko ƙyamata bayayi yanda yake ɗan gayu mai aji har zansha abu in rage yasha saura na , Har muka isa bakin get in makaranta babu wanda ya sake magana , a bakin get Al ' Ameen yayi parking , muna zaune a mota ga dukkan alamu akwai wanda ake jira , bamu wane daɗe ba , wata irin shareriyar mota tayi parking kusa da tamu , wani matashi ne ya fito daga motar yayo wurin motarmu , Al ' Ameen ya sauke gilashin kusa da Dikko , yana isowa Dikko ya miƙa mishi hannu suka kashe , Sai kuma aka shiga gaisawa bayan sun gaisa yace ina An matan take ne ? Murmushi Dikko yayi yace gata can baya kuka takeyi , dariya matashin yayi tare da cewa tun daga katsina har bakori tana kuka ? Dikko yace ai bata da aikin yi , dariya matashin ya sakeyi tare da cewa sannu dai za'ayi mata , Ba tare da Dikko ya juyo ba yace An mata dani dake waye ya kamata ayi ma sannu ? Banza nayi dashi ban bashi amsa ba , dariya yayi tare da cewa muje sauri nakeyi yayi maganar yana kallon agogon hannunshi , komawa matashin yayi cikin motarshi ya tada , mu mukayi gaba shi kuma yana bayanmu har muka isa bakin ofishin principal , a bakin ofishin mukayi fakin sannan muka fita gaba ɗayanmu muka nufi cikin office in... Bayan gaisuwa akaci gaba da abinda za,ayi duk wani abinda ya kamata ayi anyi , kuma Dikko yace wa principal ko hutu akayi idan bashi yazo ba kar wani ya ɗaukeni , ya ƙara da cewa ko wannan ya nuna Al ' Ameen yace koshi yazo a , a, niɗin dai , tace insha Allah , saboda Dikko ya ɗaukeni ƙarshen kidahuma JS 1 yasa aka ajiyeni , inajin aji ɗaya na ƙara fashe wa da kuka duk da dama kukan nakeyi tun safe har yanzu , Bayan an gama aka ciro kayana daga bayan motar Dikko , a bayan motar abokinshi aka fiddomin katifa , bayan an gama sauke kaya Dikko ya bulale Prcp da kuɗi wanda Al ' Ameen ya miƙa mata su , tayi ta zabga godiya Dikko yace tasa min ido sosai a riƙa zaneni idan nayi abinda bai kamata ba , tace insha Allah ! Ina tsugunne a gefe sai kuka nakeyi , bayan sun gama abinda suke Dikko ya kallo inda nake yace taso ki biyoni , jiki a lalace nabi bayan shi har cikin mota , dukanmu a baya muka zauna , da yanayin tausayi a fuskarshi yace idan kina san wani abu ki faɗawa principal zatamin waya kinji ko ? Nace to , karkiyi rashin ji kiyi karatu kuma ki zama mai haƙuri karki sake ki biyewa abokan banza kinji ko ? Saida na goge hawaye sannan nace tou , Shiru yayi zuwa wani lokaci yace tou kalloni kiga , ba musu na ɗaga idona na kalleshi , murmushin shi mai burgewa yayi tare da cewa idan kuma kikayi , uhum ? Ya nuna idanuwanshi da hannunshi , bansan abinda hakan da yayi yake nufi ba , banyi magana ba ina kallonshi dai , yace to nan ? Ya nuna , girgiza kaina nayi alamar a , a tou zakiyi tunani na ko ? Da kai na bashi ansa Eh , tou idan dai kin tunoni kar kiyi kuka kinji An mata zan riƙa zuwa da wuri ina ganinki ai zaki ji daɗi idan kika ganni ko ? Nace Eh , Bandir in "yan 1k ya bani guda biyu yana cewa karki yi damuwa sosai kiyi farin ciki kullum don Allah kar kiyi kuka da yawa inaji a jikina idan kina cikin damuwa kinji ko ? Jinjina kaina nayi alamar gamsuwa , godiya yayi tare da cewa tou kya iya tafiya , godiya nayi sannan na fita daga motar , ina fita Al ' Ameen ya shiga yaja suka tafi abokinshi yabi bayan su shima cikin motarshi... Aji Principal tasa aka rakani tare da cemin idan an tashi makaranta inzo da "yan ajinmu su tayani ɗaukar kayana , nace tou , kamar wata geliya haka nake ji na , na koma kamar wata sakara , haka na zauna ina bin "yan ajin da kallo , kowa sabgar gabanshi yakeyi babu wani da ya damu da wani , Koda aka tashi ban nemi kowa ya tayani ɗaukar kaya ba na koma ofishin principal , tou Dikko dai ya nemomin mutunci na tunda yayi mata wanka da kuɗi mutane basa abu dan Allah sai dan hatimin nasara , da kanta ta samu yara suka tayani ɗaukar kayana har zuwa ɗakinmu... Bayan munje mun ajiye kayan na samu wuri na zauna ina kallon yanda kowa yake rayuwarshi domin ina so na fahimci yanda rayuwar makarantar take tafiya ! Tunda Baba ya sulale ƙasa ya tsaya cak ya daina aiki , yana da rai amma dashi da matacce basu da banbanci ɗagowar da cikin shi keyi kawai zaka gani ka tabbatar da ranshi , wannnan abu yayi ƙololuwar ɗagawa kowa hankali dan haka aka kwashe shi akayi asibiti dashi... A ɓangaren Sadiyya kuma tanajin jiki sosai dan haka iyayenta suka buƙaci ta koma gida suyi jinyarta , amma daga inda Dikko yake ya murje idonshi tas yace idan dai shine yake aurenta a barta kar wanda ya tafar mishi da mata ko yace ya kasa kula da itane ? Dole suka haƙura suka barta , Amisty kuwa da Hafsa lingu da saƙo sun nemi Sultana basu samu ba , kuma wayarta ma idan sun kira a kashe take dan tuni Dikko ya ƙarya layin , kuma sunje wurin Alaji sun tambayeshi ko yana da labarin Sultana yace shima kanshi nemanta yakeyi , yaje gidansu ance an saceta wurin partyn birthday inta Babanta ma yana asibiti baida lafiya , bawan Allah Alaji shine ke kula da Baba duk wani aune ² da magunguna shine yake biya... Sati na ɗaya a makaranta banda damuwar komai kuma banda wani tunani daya dameni sai Babana da nakejin kewarshi kullum rana , bana tunanin Inna kwata² dan na tabbata itama duk inda take bana rayuwarta kuma bata tunani na amma nasan duk inda Babana yake yana can yanajin damuwa na rashina a kusa dashi ! Har yanzu banyi abokiya ko ɗaya ba kuma bana shiga sabgar kowa tunda babu abinda na nema na rasa , ni ɗaya nake rayuwata idan kuma naje aji idan malami ya shigo zan samu natsuwa na tattara hankali na , rubutu ma ni nakeyin abuna da ɗaiɗaya nake ɗauko ko wane harafi , bana surutu a aji dan ba'a magana da hausa idan kuma mutum yayi za,aci shi tara ne , Tun ranar da nazo ban sake zuwa wurin principal ba , kuma ta aiko a kirani banje ba , harkar gabana kawai nakeyi dan gaskiya naji ciwo da Dikko yasa aka ajiyeni JS 1 kuma naci ɗamara saina nuna mishi ni ba jahila ba ce ba , Dikko kuwa tunda ya ajiye Sultana a makaranta yaci gaba huɗɗoɗin gabanshi , baiyi waya yaji ya Sultana ba kuma baizo makaranta ba da sunan ziyara , duk juma'a yana katsina yana komawa monday tunda safe yana ta zirga² a hanya saboda rashin lafiyar matarshi amma ko so ɗaya bai biyo wurin Sultana ba , Haka dai rayuwa ta taci gaba da tafiya a makaranta , mutane suna ta shigowa rayuwata amma banda lokacin kowa ina so in tsula iskancina amma ba yanzu ba saina san abinda nakeyi , saboda ko magana nayi ma mutum sai kawai inji suna wani min turanci banza shi yasa na fita sabgar kowa nake tawa sabgar.. Wallahi kwata² banajin daɗin zaman makarantar nan a daddafe dai muka fara jarabawa dan hutu za'ayi mana kuma har yanzu Dikko bai zo ba bai aiko ba , kuma kuɗin daya bani har yanzu akwai su kayan provision ina ma akwai sosai dan gaskiya ba ƙananan kuɗaɗe ya kashe ba dan dai kawai inyi farin ciki ! Tunda naga hutu ya fara gabatowa nake neman "yan katsina dan in turasu gidanmu su faɗawa Babana ina FGC nasan zaizo idan muka dawo hutu , na samu "yan katsina amma duk wanda na faɗa masa anguwarmu sai yace bai sani ba dan abinda na lura duk "ya "yan masu kuɗi ne irin wanda basa zuwa yawo kamar yanda mu "ya "yan talakawa keyi... Dole na haƙura gashi ban riƙe number kowa ba dana riƙe tabbas dana samu aron waya na kira nace a faɗawa Babana yazo ya tafi dani , tou ban riƙe ba banda yanda zanyi inba haƙuri ba dan ban samu yanda nake so ba , duk ɗalibai suna farin cikin hutu kowa yana cike dajin daɗi zaije yaga iyayenshi saɓanin ni da bazan samu ganin Babana ba , Anyi jarabawa an gama kuma an bada report ga ko wane ɗalibi nima an bani na saka a jakata na adana abuna , Ranar hutu kowa yana cikin farin ciki ko wane ɗalibi ya samu "yanci kamar sakakken tsuntsu kowa na wali sakamakon ni da principal ta tsare a ofishinta , motoci kuwa sai ɗaukar dalibai sukeyi suna tafiya abin dai gwanin burgewa ina ta kallon ikon Allah har ɗalibai suka ƙare kaf dan principal tacemin tun satin hutu ta faɗawa Yayana za'ayi hutu , kuma jiya ta kirashi tace mishi yau ake hutu yace zaizo insha Allah ! Saida kowa ya watse babu sauran ɓishi²n ɗaliba ko ɗaya saini ina jiran zuwan shi , Dikko baizo ɗaukata ba sai bayan azahar bayan ya iso ya kira principal ya sanar da ita zuwanshi , dan dama lokaci ² tana kiranshi ya kawo ina tana mishi sannu da hanya , tare muka fito da ita har wurin mota muna tare da ita , bayan mun isa suka shiga gaisawa da Dikko tare dajanshi da fira dan kilbibi an fara magana da hausa sai a wani jefo turanci dan munafirci , gajiya nayi da tsayuwa na buɗe mota na shiga na zauna , Yauma ya tunbiza mata kuɗi masu yawa , gaskiya Dikko yana da kyauta sosai zaiyi wuya ka ganshi bai baka ba , ya ganka yanzu ya baka anjima ma idan kuka sake haɗuwa saiya ƙara maka , godiya tayi sosai tare da mana addu'ar sauka lafiya ta wuce..., Saida Al ' Ameen ya fara tafiya Dikko ya juyo dukanshi yana kallona , bayan wani lokaci yace An mata kin rame me ya sameki ne ? Gyara baki na nayi tare da cewa ina yini , na gaishe shi dan kauda waccan maganar , murmushi yayi tare da cewa lafiya qalau , gaishe da Al ' Ameen nayi shima ya ansa , Cike da tausayi Dikko yace kodai baki san wannan makarantar ne ? Dama saida nace bazan kawoki boarding ba kowa yace min wai in kaiki makarantar kwana , a raina nace wato saida kayi shawara kenan , kallon Al ' Ameen yayi tare da cewa ji yarinyar nan ta rame ni gaskiya banji daɗin haka ba wallahi ya ƙarasa maganar yana mai dawo da kallonshi wurina yace An mata ko bakicin abinci ? Murmushi nayi nace ina ci , to baki da kuɗi ? Nace ina da , to meke damunki ? Ko baki lafiya ne ? Yayi maganar tare da nunamin in matso kusa dashi , Matsawa nayi kamar yanda yake so , ƙasa² yayi da murya yace meke damunki ne ? Ba komai nace , tsoki yayi tare cema Al ' Ameen ya tsaya zai dawo kusa dani , parking Al ' Ameen in yayi Dikko ya fito ya dawo baya kusa dani , ansar jakata yayi bayan ya rufe ƙofa yana cewa matso kusa dani , juyar da kaina nayi ina cewa nidai ka gyaleni a dai² lokacin da motar taci gaba da tafiya , Buɗe jakar yayi yana cewa ni wallahi naga duk kin koma "yar ƙarama Allah dai yasa ba masonyo min ke akayi ba , shiru nayi kamar banji ba , kalloni yayi da kallo maisa natsuwa , magana yayi cikin riƙe haruffa yace umm ya nunamin nayi shiru da kanshi , murmushi nayi shima murmushin yayi yace tou kice wani abu mana , Sake maimaita maganar yayi , girgiza kai nayi cewa nice , yace ai banji kin fara kuka ba yau naji kinyi shiru , a daidai lokacin daya fara duba littafai na , haka yayi ta cirosu ɗaya baya ɗaya yana dubawa har yazo kan report ina , warwareshi yayi ya duba , gaba ɗaya annurin fuskarshi ya ɗauke ya ƙurawa report in ido , cikin muryar ɓacin rai yace tsaya , tsayawa Al ' Ameen yayi Dikko yace fita ki koma gaba ki zauna , da sauri na fita na koma gaba na zauna , ina ta mazurai kamar nayi wa sarki ƙarya duk yanda akayi a cikin waccan takarda yaga ɓacin rai... Shiru yayi tun daga nan ba saike magana ba har muka iso katsina , ko waya aka kirashi baya ɗauka , lokacin da muka iso har an fara sallah magrib , Al ' Ameen na tsayawa na fita da sauri zan wuce cike Dikko yace ke zo nan , da sauri na dawo shi kuma Al ' Ameen fita yayi ya ɗauki buta ya zagaya can bayan gida dan yayi alwallah , Buɗe murfin motar yayi ya fiddo ƙafar ɗaya ɗayar kuma tana ciki , tsareni yayi da idanuwa dan haka na sauke kaina ƙasa shiru yayi na wasu mintuna sannan ya ɗago report in yace dan kin ɗaukeni sakarai ni zaki kawo ma wannan abun ? Shiru nayi banyi magana ba , tsawa ya daka min yace baki ji ina miki magana ne ? Cikin rawar murya nace yi haƙuri , fitowa yayi daga cikin motar da sauri nayi baya , shima takowa yayi ya matso kusa dani , da sauri na sake ja baya , ya sake biyoni , yana sake matsowa na ƙara ja baya , idan na sake matsowa kika matsa wallahi saina zaneki , tsayawa nayi jikina ya fara kyarma ina kallonshi , Cike da ɓacin rai yace wannan iskanci zaki kawomin ? Girgiza kaina nayi ba tare da nayi magana ba , cikin tsawa yace shin kinyi rantsuwar magana ne ina miki magana kina girgizamin kai , da sauri nace a , a , jinjina kai yayi tare da tillomin report in yace ɗaukarshi ki shiga gani nan zuwa zaki faɗamin iskanci da kikeyi makaranta har kika ɗaukomin na 20 , na ƙarshe ke jakar da baki kishin kanki ya ƙarasa maganar tare da nannaɗe hannun rigarshi dan Al ' Ameen ya kawo mishi ruwa zaiyi alwallah... Duƙawa nayi na ɗauki report in zan shiga ciki yace kije ki fiddo min jakar banzarki daga mota , da sauri naje na ɗauko jakar na wuce ciki a lokacin shi kuma har ya gama alwalla ya biyo bayana yana ci gaba da faɗa , Ɗakin da yake shiga ya wuce ni kuma na shige ɗakin da nake zama , yana nan kamar dai da babu wani ci gaba a cikin ɗakin , alwallah nayo nayi sallah ina roƙon Allah ya bani mafita Babana kaɗai nake ciwon san gani , Har nayi sallah isha'e Dikko bai fito ba , su kuma uwayen ƙwa² har sun cika gidan sun fara gardamar kwallo , gajiya nayi na kwanta a inda nayi sallah gaskiya rashin ahali masu mutunci bai ba , duk wanda ya rasa iyaye masu daraja ya zama sai a hankali , ita kuma Inna ko wane irin ahalin suka raine ta ? Soyayya tana rufewa mata ido dasan duniya har su kasa gane aibun namiji , irin wannan rayuwar bata dace dani ba , da na fito daga zuri'a masu mutunci da duk haka bata faru dani ba , Inayin rayuwa irin ta dabbobi kuma ni ba dabbar ba , mahaifi ya haifi zuri'a wai ya barsu da cida kansu wannan ba komai bane sai rashin tsoron Allah , caca neman mata shaye² shine wanda na samu a matsayin ubana , rayuwata tazo a garari zata ƙare a raɓe² , na ɓarar da mutuncin da yasa har wani namiji yake da damar shigowa rayuwata ya ɗaukoni daga cikin ahalina ya maidoni cikin rayuwarshi , wannan wace irin rayuwace na samu kaina a cikin ta... ? Dariyar Dikko na jiyo sai kyalkyatawa yakeyi duk yadda akayi waccan dariyar wallahi mugunta yaji , palon yayi shiru sai salati akeyi ƙasa² amma Dikko sai dariya yakeyi yana ƙarawa , maganar Al ' Ameen naji yana cewa mai gida tou ya za,ayi , miƙewa Dikkon yayi yana dariyar mugunta yayo ɗakin da nake kwance , Cikin dariya yace ya miƙo hannunshi yana cewa An mata taso mu tafi , da sauri na taso kallona yayi yace wai duk me kikeyi baki cire kaya ba , ba tare dana kalleshi ba nace ba komai , tou zo mu tafi kina zuwa ? Ya tambayeni , girgiza kai nayi alamar a , a dan Dikko baida saiti abinda na fahimta idan dai yana cikin mugunta zaiso yayi ta zalinci yana dariyar cuta , Dariya ya sakeyi cikin sigar cuta yace da Allah kizo mu tafi , kyaleshi nayi na koma na kwanta , murmushi yayi sannan yace to tunda baza ki ba karki bacci ki jirani yanzu zan dawo kinji ko ? Nace tou , kallona yayi cikin wani irin yanayi sannan yace kinsan yau zan hanaki baccin dare sai kin faɗamin abinda yasa kika je kikayo na 20 , nace tou , har ya fita kuma ya dawo yace kiyi wanka kafin in dawo ga kayanki nan palo ki kwashe su ki dawo dasu ciki naga ma duk sunyi ƙura , yana faɗin haka yayi gaba abunshi , ina kallonsu ta window kowa ya shiga mota amma ba'a fita da motar Dikko ba kuma ba'a tafi da Al ' Ameen ba , saida suka gama fita na wuce bayi dan inyi wanka..... 23/09/2019 *JAMILA MUSA ...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 39 Ina fitowa daga wanka na wuce palo inda kayana suke ajiye , ɗagasu nayi ɗaya bayan ɗaya naga babu wata ƙura da kayan sukayi nidai a gani na dan an lulluɓe su da towel , zani da hijabi kawai na ɗauka na koma ciki , Zanin na ɗaura wato ɗaurin ƙirji , na saka hijabin na nufi palo dan naga Al ' Ameen yana waje har yanzu bai shigo ciki ba , inda kulolin abinci suke naje na buɗe na zuba abinci naci na ƙoshi sannan na dawo ɗaki nayi kwanciyata ! Babana ne yazo ya tsayamin a rai gaskiya ina cike da kewarshi soyayyarshi ta hanamin zaman lafiya , duk duniya ban haɗa soyayyar Baba da kowa ba , ko ina yake ? Ko a wane hali yake yanzu ? Yana tunani na ko shima bayayi... ? Haka nan naji hawaye sun cikamin ido cike da rauni nayi magana a bayyane ina kake ... ? Murmushi nayi mai cike da ɓacin rai zuciyata cike da kudurirrika akan Dikko duk runtsi duk wahala komai daren daɗewa sai Dikko yayi nadamar sani na , yanda ya takura ma rayuwata nima saina takura ma tashi rayuwar saina mishi zargen da bazai iya warware kanshi ba , da wannan tunanin bacci ya ɗaukeni. Su Dikko kuwa sai 12:30am suka dawo hayaniyar shigowar motocinsu ta tasheni daga bacci , tunda suka fara fitowa daga cikin mota suke gaddama har suka shigo palo , bayan kuma sun shigo haya² ƙarar filets da cokula kowa yana zuba abinci amma har yanzu banji maganar Dikko ba danshi baya da ƙoƙari wurin magana saidai dariya itama sai yaji mugunta yakeyi... Zuwa wani lokaci kuma palon yayi shiru bakajin maganar kowa sai ƙarar tv dan sun fara cin abinci , bayan wasu mintuna kuma naji wani yana cewa kai ubangiji ya fishshemu tsaka mai wuya , gaskiya na tausayawa kaina na tausayawa Saminu wallahi , Dariyar Dikko naji yana cewa niko wallahi bai bani tausayi ba aishi ya siya tsautsayi da kanshi maganin ganganci da rayuwa kenan kaga garin neman gira an rasa ido , anso ayi suna sai aka samu matsala... Hayani taci gaba da tashi , yayin da wasu ke cewa wannan tashin hankali da suka gani yau basu iya bacci , Dikko yace badai anan gidan ba ku gama cin abinci kowa ya kama gabanshi wallahi yau babu mai kwana a gidan nan , dariyar wani daban naji yana cewa sai An mata , Dikko yace koma "yar tsohuwa ce sai kunbar gidan nan , Kusan mutum biyu suka haɗa baki wurin cewa wai da gaske akwai mace yanzu haka a gidan nan ? Dikko yace mai maganar zaka tambaya dan nima dai ban sani ba , wai wace ce ita An matan nan ni na daɗe wallahi inaji Dikko yana kiran An mata ko itace ɗiyar ɗan... Sai naji kuma yayi shiru , murmushi nayi nace ɗiyar ɗan caca , Duk yanda akayi wani ya dakatar dashi ta hanyar hanashi yayi maganar shi , gaba ɗaya kuma palon yayi shiru har suka gama cin abincinsu babu wanda ya sake magana , bayan sun gama suka fara saɓewa ɗaya bayan ɗaya , bayan kowa ya gama fita naji Al ' Ameen yana ma Dikko sai da safe , banji abinda Dikkon yace mishi ba , ya fice kuma da motar Dikkon ya fita , Bayan Al ' Ameen ya fita daga gidan Dikko ya fara kirana , ban ansa ba na taso na fito palon daga bayanshi na tsaya nace gani , shima bai juyo ba yace kinajin yunwa ne ? Nace a , a me kikaci ne ? Nace ba komai , a , a ƙarya kike yarinya me kikaci dai ? Nace maka ba komai , tou zo nan yayi maganar a daidai lokacin da yake kwanciya saman kujera , Gabanshi naje na durƙusa cike dajin haushin shi , bai kalleni ba dan hankalin shi nakan tv amma dan tsabar ya ɗaukeni kidahuma yace kinmin kyau fa , zanyi magana ya tsareni da idanuwanshi tare da cewa bafa ina nufin kina da kyau ba ko kin birge ba kawai dai dan bakyajin yunwa nace da kyau , kallonshi nayi amma yanayin fuskata ya nuna banji daɗi ba , murmushi yayi tare da taɓe bakinshi ya kauda kanshi gefe guda yana ci gaba da cewa ni mace mai kyau haushi take bani , dan mafiya yawansu jakuna sunyi yawa a cikinsu kalloni yayi yana tambayata ko nayi ƙarya ? Kallon da yayi mani yasa nace a , a , murmushi yayi yace ɗaukomin report inki , tashi nayi jiki suku² na fara tafiya , tallabo kanshi yayi da duka hannayen shi yana kallona , zuwa can kuma yayi tsoki wai ji mace na tafiya , babu wani tsari mai jan hankali babu wata zarra mai burgewa a tattare dake , shi sakaran waccan rana kome ya gani a tattare dake zance har 12ndare , ya gane sarai banji daɗin abinda yake faɗa a kaina ba , naje na ɗauko report in na kawo mishi , Ansa yayi tare da tashi zaune yana kallona , yace wallahi kina burgeni sosai saboda kina da kyau , murmushi nayi tare da kallonshi , gyara zama yayi yaci gaba da cewa kyawawan idanuwan ki inajin natsuwa yayin da kika kallene ni dasu saboda kyawunsu da sheƙinsu ko a duhu kikayi kallo dasu abun ɗaukar hankali ne , ƙarajin daɗi nayi tare da ɗanyin wasa da idanuwana dan ina so inji an yaba surar da Allah yayi min , kyakkyawan murmushinki yana tafiya da hankali na a duk lokacin da naga kina cikin nishaɗi dan yanayin yana sakani cikin wani irin shauƙi mai wahalar misultuwa , ƙara yashe bakina nayi inajin daɗi , hankalinshi nakan report in yace kike ta wani kwashe baki da ita fa nake ba ke ba , ɗan kama kaina nayi sannan nace wace ce ? Matata mana dan tafi ki haɗuwa yayi maganar tare da ɗaure fuska yaci gaba da kallon report in.. A dibarance na kalleshi shi kuma hankalinshi yana kan report yana kallo ko kyaftawa bayayi sai gemunshi dake motsawa a hankali saboda taunar cingom in da yakeyi cikin kwarewa da salon ɗaukar hankali... Naɗe takardar yayi tare ɗago ƙafarshi ya takamin kafaɗa yana wasa da report in yace tunanin me kike a makaranta ? Kin rame , kuma cikin ku 20 kika yo na 20 , tunanin me kike ? Duƙar da kaina nayi ƙasa ina wasa da kafet banyi magana ba , jijjigani yayi da ƙafarshi yace baki ji wai ina magana ne ? Cikin ladabi nace babu komai , to ko aure kike so ne ? 😳 aure kuma ? na tambayeshi tare da zaro idanuwana ina kallonshi , wani irin kallo yayi min mai tsarga zuciya wanda saida tsikar jikina ta tashi naji wani irin yanayi mai wahalar fassarawa na kasa daina kallon idonshi , Ɗan kauda kanshi yayi cewa tou daina kallona haka nan , gyara bakina nayi na sauke idona daga fuskarshi , yaci gaba da cewa zan miki haƙuri na yau saboda bance miki kar kiyomin na 20 ba , ban faɗa miki irin position in da nake so ki kawomin ba , amma zan faɗa yanzu.. Kalloni yayi sannan yace wallahi ׳ nayi rantsuwa kuma bazanyi kaffara ba , idan har kika sake kawomin 20 bazan dakeki ba , kuma bazan zageki ba haka bazan sakeyin fushi ba , kinga gidan nan dagani sai ke , sassauta muryarshi yayi ƙasa² yaci gaba da cewa babu wanda zaiji kuma babu wanda zai gani , duk lokacin da kika zo min da na 20 nasan abinda kike tunani , duk lokacin da naga 20 ni kuma zan sakaki a ɗaki irin abinda nayi miki a gidanmu ai kin tuna ko ? Ba tare da ya jira na bashi amsa ba yace tou wallahil azim irinshi zan ƙara miki , Kinga idan baki so in miki sai ki dage kiyi karatu , idan kuma kina so sai ki sake kawomin na 20 ni kuma ina ganin 20 tou sai mu shige daga ciki in rufo ƙofa in baki abinda kike tunani kuma ince karki sake ki faɗawa kowa... Lallai Dikko digirarran ɗan iska ne kuma baida kunya ko kaɗan , kasa haɗa ido ma nayi dashi naci gaba da kallon kafet , komawa yayi ya kwanta tare da cewa kashe tv n can kije ki kwanta , simi² na tashi naje na kashe tv in na wuce ciki , Tun daga wannan rana Dikko ya zama siriki na , nafi sati ɗaya ban yadda mun sake haɗuwa dashi ba , idan basu nan zanje in zuba abinci inci , idan kuma yana nan saidai in yini kuma in kwana da yunwa , da kuma naji maganarshi ya shigo ƙaramin palo zan gudu bayi in zamana , idan kuma akayi sa'a ya shigo ɗakin dan ya jira in fito ya ganni to shi da kanshi zai gaji da zaman jirana ya fita , ni kuma idan zasu fita daga gidan zan laɓe jikin window inyi ta kallonshi wallahi bana gajiya da kallonshi kwata² Gidan kuma kullum sai ya cika da maza suci su asha suyi ta gaddama mara amfani , amma zaiyi wahala kaji bakin Dikko , idan sun gama sun tafi kuma zaiyi kwanciyarshi ne kawai a palo , dan yanzu gidan yake kwana tun ranar da abokinshi yace wai da gaske akwai macen dake zama a gidan nan ? Amma naji ranar nan yana waya da wata wai yaushe zata dawo zai kawo mata amanar wata ɗiyar tsintuwa , nidai haka naji daga nan ban sake jin maganarshi ba , shin nice ɗiyar tsintuwar ko kuma wata ce daban oho... Kwance nake saman katifa sai juyi nakeyi saboda azabar yunwa , na rasa inda zansa kaina cikina sai zafi yakemin har na gaji da kwanciya kuma gashi duk yau Dikko bai fita , yanzu haka palon ya cika da mutane kuma wallahi ko jiya babu abinda naci tun daga kalacin safe. Na rasa inda zan tsoma rayuwata inji sanyi , sai hamma nakeyi ga bacci inaji amma yunwa ta hana inyi bacci duk jikina ya mutu bana iya tsinana uwar komai sai kwanciya nake kamar ruwa , Ta dubu nasha na fita ƙaramin palo na zauna ko Allah zai kawo min Dikko , amma mi har 11:30 bai shigo ba kuma babu wanda ya fara tafiya har yanzu dan naji sun tashi daga firar kwallo sun dawo labarin "yan danbe , har yanzu banji maganar Dikko ba kila baya gidan gaskiya , Daga firar "yan danbe suka faɗa maganar Saminu , wani ne yace bawan Allah Saminu wallahi ana maganar danben nan shi ya faɗo min a rai , me ya sameshi ne ? Wani daban ya tambaya , cikin muryar jimami yace bakaji ba ? Yace wallahi banji ba kuma ban sani ba miya faru ? Yace wallahi tsautsayi da rabon ayi , yaje kallon danbe . Dariyar Dikko naji yana cewa babu wani tsautsayi kuma babu rabon ayi , kawai ka faɗa mishi matar wani ya nema , kuma dan hauka ya tashi ya bita har gidanta , Allah yasa mijinta ya ritsasu shine yayi ma Saminu shegen duka har saida idonshi ɗaya ya fita , innalillahi wa'inna ilaihir raji'un wannan masifar Dikko kema dariya ranar da na dawo daga makaranta kenan ? Shima mutumin da ake ba labari salati yakeyi , Dikko yace wato mu mutane muna da wani hali na daban , kai da kanka zaka siyawa kanka matsala sai kace wai Allah ya kawo maka ? Ko ƙaddara ne ko meye ne , kaje ido ya fita wurin zina , kuma abin takaici ma Saminu matanshi biyu amma saboda masifa sai ya nemi mata , waye ya aike shi ? Wa ya saka shi ? Waye ya sashi neman matan aure ni wannan masifa da ta samu mutane bansan irinta ba , wannan tsautsayin dai Saminu shine ya kawo ma kanshi abunshi ba wani ba , Mai tambayar yace wa Dikko ina suka haɗu da matar tou ? Dikko yace an faɗa maka kallon danbe yaje , dariya sukayi dukansu , yace nifa ban gane kallon danbe ba , dariya Dikko yayi yace nanfa aka tsaya , wurin kallon danbe suka haɗu , Shima naci gareshi mai tambayar yace don Allah wai ya wurin danbe suka haɗu ? Tasowa Dikko yayi ya taho ciki , yana shigowa ya ganni zaune saman kujera yace baki bacci ba kenan ? Yayin da naji "yan palo sun ɗauki ihu duk yanda akayi an fassara kalmar dambe , Ba tare dana kalleshi ba nace Eh , zama yayi kusa dani yace mene ne tou ? Nace yunwa nakeji , kallon agogon hannunshi yayi sannan yace kuma wallahi banajin sun rage abinci amma bari su fita mu gani , nace to , wayarshi ya ciro daga aljihu ya ƙura mata ido yana danne ² yayin da nakejin kamar in tambayi Dikko miye dambe ? Dan ina so naji yanda labarin yake tiryan² kuma gashi palo labarin suke amma zuwan Dikko yasa banaji , Haka dai rayuwata taci gaba da tafiya zamana tare da Dikko , kullum da tunanin Babana nake kwana dashi nake tashi , bani da wata damuwa ta rayuwa dan Dikko ya shigo cikin rayuwata sosai kuma babu abinda na nema na rasa , Daren yau kuwa da kanshi yake tayani haɗa kaya saboda gobe zan koma makaranta idan Allah ya kaimu , sai nasiha yakemin cikin lallashi cike da tausayina da kuma nuna tsantsar soyayyar a gareni , kamar ya buɗe kaina ya zubamin ilimi haka yakeji bawan Allah , saida muka gama haɗa kayan muka fitar dasu ƙaramin palo , duk yanayin Dikko yana nuna bayajin daɗi zai rabu dani , duk inda na motsa zai tsareni da kallo mai tattare da tsantsar ƙauna da shaƙuwa. Murmushi yayi yace idan kika koma makaranta zaki riƙa tunani na kuwa ? Ya mutsa fuska nayi tare da taɓe baki nace wai ni ? Na nuna kaina ! Yace Eh , nace Allah ya sawaƙamin mema zaija min nayi tunanin yin tunaninka ma ? So ya bani ansa , murmushi nayi tare da cewa tirr Allah ya sawaƙamin in faɗa Soyayyarka , wani irin kallo yayi min mai tsarga zuciya harsai da naji jikina ya mutu sannan yace ke komai sai kinyi wasa ni banajin daɗin haka , Jan hannuna yayi muka zauna saman kujera ya tattaro duka natsuwarshi sannan yaci gaba da cewe , ni ina sanki , da sauri na tashi tsaye nace me ? Dikko yace ƙwarai ina sanki kuma kema kina so na wannan shine gaskiya ina ta ɓoyewa kwarai , ya faɗi maganar tare da kauda idonshi daga kaina , dariya nayi tare da cewa wasa kakeyi ne ? Yace a , a da gaske ne fa , ba yanzu na faɗa soyayya dake ba tsawon lokaci , duk lokacin da nazo kusa dake sai inyi ta zuba miki ido wannan ai soyayya ce , Idan kina magana ni kuma kawai sai nayi shiru natsaya nayi ta kallonki inajin daɗi wannan shima ai soyayya ne , dakatar dashi nayi ta hanyar ɗaga mishi hannu ya isa , ya isa haka :• Abinda ka bayyana wannan shine ƙimar matashi kamar ka ? Ba shi bane ba , tsawon wane lokaci muka ɗauka da zamu fuskanci juna ? Fari yaro da yarinya ko wannen su yasan damuwar ɗan uwanshi wannan shine so , sannan fahimtar juna , Dikko yace sani da kuma fahimta da kike san ko bakya so kina da damuwa ko bakya da , yayin da kika samu wannan sannan ki so ni ? Wannan shine so ? Soyayya fa ita ba tsarata akeyi ba kawai faruwa takeyi , kinyi waya kuma kina saka mata kati ki siya data sai ta baki duk abinda kike buƙata kinga faruwa hakan yakeyi ba shiryawa akeyi ba , tou wannan shine so , bana so na rasa damata yayin da nace kece sarauniyar mafarkina , kina da damuwa kuma kina da riƙe abu a ranki , Duk da haka inayinki , ina sanki , tsoki nayi tare da cewa kayi haƙuri Dikko ba kamar yadda kake tunani bane ni banma yadda da soyayya ba tun daga farko ma kenan , soyayya tana faruwa ne cikin wani lokaci mai gushewa da wurwuri wannan shine tabbataccen hasashen da babu irin shi , ina kaiwa nan na juya na shige ɗakina , Murmushi Dikko yayi bayan tafiyar Sultana yace yanzu ta gayamun abinda zanyi kenan , duk da abinda na faɗa mata saida tayimin gaddama ta yarinta na faɗa soyayyarta yawancin abubuwa sukan zo da aibi ku tsaya ku gani zata faɗa soyayya ta da wurwuri....... 24/09/2019 *JAMILA MUSA ...*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 40 Miƙewa yayi bayan ya gama surutanshi ya fita babban palo maƙulin motarshi ya ɗauka ya fita , ina tsaye a jikin window ina kallonshi har ya shiga mota ya bar gidan da gudu bansan inda zaije ba , kuma ga dukkan alamu bazai kwana gidan ba , murmushi nayi tare dayin magana ƙasa² nace sauka lafiya. Yana fita na dawo na kwanta saman katifa naja bargo na lulluɓe na rufe idanuwana ina jinjina irin wulaƙancin da Dikko yayi mana shi mai kuɗi , "yar madara dabbace amma duk lokacin da naji an kira sunan mage ko na ganta sai magena ta faɗon min a rai da Dikko yabi ta kanta da mota bataji bata gani ba , Wulaƙancin da yayi ma Babana a ranar daya wankemin ubanda yafi ko wane uba a wurina da ruwan taɓo , lokacin daya bugamin kanshi har na suma , uwa uba ƙarshen wulaƙanci daya keta min mutuntaka ta , idan ma har zuciyata ta bari ƙiyayyar Dikko ta goge a cikinta ban yafewa kaina , ɗaukar fansa ƙudirina ne kuma muradi nane ko ba daɗe ko ba jima saina kafawa Dikko tarihin da bazai taɓa gogowa a rayuwarshi ba , Maganar cewa idan na kawo mishi na 20 zai rufe ƙofa dani nayi masa rata har abada nayi masa nisan da bazai iya kamoni ba , yanda Annabi ya gagari arna haka na gagareka Dikko sa'a ɗaya kawai nake nema fita daga hannunka amma da zaran na zare tou kwankin hararka sun soma... Dukan sitiyarin mota Dikko yayi a daidai wannan lokacin yace wallahi ƙarya kike , dan tunda ya fito daga gidan zuciyarshi tana faɗa mishi Sultana tana sanshi tabbas kuma akwai wannan soyayya domin yaga soyayyashi kwance a cikin idanuwanta ! Da safe tunda nayi sallah asuba nayi wanka na shirya cikin kayan makaranta , jakata na ɗauka da sauran kuɗina da ban kashe ba nayo babban palo , Na daɗe dan nafi ƙarfin awa ɗaya amma babu Dikko babu alamarshi kuma babu mota ko ɗaya a gidan , tun ina zama na marmari har na fara gajiya na kwanta saidai na kalli agogo nayi tsoki dan gani ma nake lokutan basa sauri , raina fa ya gama ɓaci sosai dan har nayi tunanin kila bayau zan koma ba , Ƙarfe 9:46am ya shigo gidan , a kasalance ya fito daga cikin motar ya nufo palo , kallo 3 nayi mishi kafin ya iso na kauda kaina , kamar yayi kuka dan yanayin fuskarshi ya nuna rai a haɗe kamar hadarin tsakar dare , Da sallama ya shigo palon bai ko kalli inda nake ba ya wuce ciki , na ansa sallamar na gaishe shi bai ansa ba ya wuce , murmushi nayi a zuciyata nace kila matarshi taci ƙaniyarshi , mugu kenan sai lahira a gane halinshi... Yayi fata² da awowi biyu sannan ya fito tunda ya fito ƙaramin palon ƙamshin turarunshi ya fara zagaye cikin gidan nan lungu da saƙo bana tunanin akwai inda ƙamshin bai kai ba , ƙamshin turare mai daɗi mai jefa mutum cikin wani irin baƙon yanayi mai wahalar mantawa , Bayan kamar minti biyu ya iso cikin babban palo , wallahi dole tasa na juya dan yanda naji ƙamshi inga wace shiga yayi haka ? Dan nasan bazaiyi wannan ƙamshin a banza ba , yanayin ƙamshin nasan yanayin haɗuwar da zaiyi kuma ba'a magana , dan duk yanda zan musulta muku kyawun Dikko zakuga kamar shiri ne abun , gaskiya Dikko yana da kyau fiye da duk yanda mutum yake zato , tunda nake a rayuwa ban taɓa ganin wayayyen namiji ɗan gayu mai saurin shiga rai kamar Dikko ba , ko ta ina babu inda mutum ya isa ya kushe shi saidai wani halin daban dan ɗan adam 9 yake bai cika 10 ba , Dikko yana da aji yana da natsuwar da ko mace tayi natsuwarshi taci Allah buɗa , Baida yawan dariya haka kuma bai cika murmushi ba , idan kuma yaji mugunta ya fara dariya kai kanka sai abun ya burge ka domin dariya tana mishi kyau , haka kuma murmushi ke ƙara ƙawata kawunshi , kuma yanayin ɗaure fuska ma dai yana mishi kyau gaskiya ! Idona na sauka kan idonshi gabana ya yanke ya faɗi , yasha ƙananan kaya abunshi yayi kyau cikar zatinsa da ƙwarjinsa ya ƙara fitowa sosai , bai kalleni ba ya yayi kamar ma bana nan saida yazo dai² inda nake zaune yace muje , Ajiyar zuciya na sauke na ɗauka jakata nabi bayanshi dan shi tuni ya fice daga palon , lokacin dana fito harya shiga mota , ina buɗe murfin motar zan shiga baya zaune naga shine zauna , fuska a haɗe kamar an aiko mishi da sauƙon mutuwa , Kawai dai naji babu daɗi yanayin yanda yake ta haɗe rai duk na kama kaina haka nan naji duk na takura , jakata na fara sakawa sannan na shiga na rufe na kalli wani gefe daban ba na driver ba kuma bana Dikko ba , yau an sako Al ' Ameen wani mai girman kan bala'e ne , kamar jira yake na rufe ƙofa ya bige mota kamar zai tashi sama , Saida muka fara biyawa Alheri clinic acan matar Dikko take shi kaɗai ya fita yaje ya dubota bai wani daɗe ba ya dawo yana gaba wata kyakkyawar budurwa tana biyoshi baya har suka iso wurin mota , Buɗe motar yayi ya ɗauki wayoyinshi daya bari lokacin da zaije wurin Sadiya , gaba ya koma ya zauna ita kuma ta shigo baya , kallona tayi ƙasa da sama sannan tayi tsoki tare da faɗin wata kalma da turanci amma ko miye tanayin maganar da zafi ne , Ɗaga kaina nayi na kalli cikin madubi inda Dikko yake kallona , sam yau idonshi hankalin shi da tunaninshi baya wuri na , da gudu driver ya sauko daga inda aka tanada dan ajiye motoci ya ibi hanya yaci gaba da falfala gudu babu ji babu gani , Saida mukayi tafiya sosai sannan ta sake faɗar irin kalmar data faɗa daga farko tana hararata , shiru nayi banyi magana ba , bayan wani lokaci tace au na manta ashe da daƙiƙiya nake magana jahila karuwar banza karuwar wofi , wani irin ɓacin rai na haɗeye dakel lumfashina ya fara yawo tsakanin duniya da lahira , taci gaba da cewa karya wacce iyayenki suka kasa baki tarbiya balbaɗaɗɗiya dake ɗiyar ɗan caca , Murmushi nayi mai cin zuciya amma banyi magana ba dan na fahimci tana da sauran magana , ci gaba tayi da cewa ni sweetheart baya ɓoyemin komai ni nace yayimin rainonki zuwa ranar da za'a ɗaura mana aure zaki dawo gidana kuma gidan mijina da zama a nan zan fara baki azabar tausayin da yasa kika shigo rayuwata Sadiya ma da tamin hawan ƙawara ya kikaga lamarinta ya ƙare ? Zata tafi duniyar mutuwa babu jimawa , Murmushi nayi tare da gyara zamana na kalleta sosai sannan nace idan kin isa ki sake maimaita abinda kika faɗa daga farko ! Nace jahila , nace ni ba jahila bace dan abinda na sani ko uwarki bata sanshi ba , ina da ilimin addini sittin ce a kaina sakara izihinki nawa ke ? Tayi shiru nace tou kinga ɗan caca tun nan ya nuna tarbiyarshi tafi irin wacce babanki ya baki , Da kika cemin karuwa tabbas ni karuwa ce bazaki shaida hakan ba saina kasa tallata a bakin titi uban naki idan ya gani zai kwasa , ni da kika gani kamar ɗan silif nake ko mutum baici ba saina burgeshi idan kuma harya taɓa kwanon zai taɓo cikin idan baici ba saiya lashe hannu , tabbas zan nuna miki kaidina da kuma illar kirana da karuwa da kikayi , Matsalarki da Sadiya ba tawa bace amma tabbas sai ubanki ya taɓa nan da nan ya kuma maida miyanshi , na faɗi maganar tare da nuna mata wuraren da idonta ke iya gani sannan nace dake da Dikko duk nafi ƙarfinku kuma kinyi ganganci shigowa rayuwata abun harina ya koma biyu daga yanzun nan zanci gaba da hararki kuma in hari Dikko , mari takaimin , nima na rama daga nan muma cakume da kokowa daga zaune , Da sauri Dikko ya juyo yace miye haka kuma ? Cikin ɓacin rai nace ban sani ba baƙin munafiki dakai , zaro ido yayi yace ai bake nake tambaya ba , cike da masifa nace nima ai bakai nake ba ansa ba , Ashiru yi parking inji Dikko , da sauri ya gurji gefen titi ƙayyyyy yayi parking har lokacin bamu daina bige² ba , Ni Dikko ya fara fiddowa tunda ni nake saitin daya buɗe murfin motar yana fizgoni ya mareni yace nine munafikin An mata ? Kafin ya sauke hannunshi nima na zabgaga mishi mari nace kaine mana munafiki dama akwai wani bayan kai ? Da sauri Ashiru ya kauda kanshi , murmushi Dikko yayi yace An mata ni kika mara ? Nace waye kai ? Dikkon banza Dikko wofi , fitowa tayi daga cikin motar ta kamani da kokowa duk da banda ƙarfi na firgice sosai dan na tsani inji an aibata Babana , kokowa mukaci gaba dayi Dikko ya riƙeni na sake fizgewa mukaci gaba da faɗa , ya ƙara riƙeni sosai hannun damarshi ya riƙo min ƙuguna dashi hannun haggunshi kuma ya ɗagomin fuskata kowa yana kallon kwayar idon kowa , Cikin maganarshi maisa natsuwa yace An mata yau kuma Dikkon ne na banza da wofi ? Ni An mata ? Kinmin adalci kenan ? A gaban mutanen dake ganin girmana zaki tozarni ? Mi yasa bakimin jiya ba ? Me yayi zafi haka haba An matana.... Ya ƙarasa maganar kamar zaiyi kuka , cikin kuka nace cewa fa tayi Babana ɗan caca kuma kaine kace mata ni karuwa ce kuma karya fa 😭 jahila fa 😭daƙiƙiya balbaɗaɗɗiya fa wai Babana bai bani tarbiya ba irin wannan shedar zakuyi ma Baba ? Tsareni yayi da idanuwanshi masu ɗaukar hankali sannan yace tou kiyi haƙuri , rufe idanuwana nayi nace inyi haƙuri a aibata min Babana ? Dikko ya ƙara cewa kiyi haƙuri , buɗe idanuwa na nayi tare da cewa wallahi Babana bai kasa bani tarbiyya ba kuma kai zaka sheda haka wata rana sakeni , sakina yayi baiyi kaddama ba mota na koma na ɗauko jakata nazo gabanshi na zazzageta nace ga jakar ka nan ga sauran kuɗinka nan idan naje gida zan bada cikonka a kawo maka , Ina faɗin haka nayi gaba , Dikko yace ina zaki je ? Juyowa nayi cike da ɓacin rai nace zanje gidan ubanda ya hafeni ne , nasan darajar ɗan caca kuma nasan mutuncinshi , kallon inda budurwar take nayi nace sunana MARYAM ALIYU MUHAMMAD BINNA { Sultana } ki fara kuka tun daga yanzu domin kwanakin baƙin cikinki sun soma daga yau , mafita ɗaya kawai shine ki mutu ki huta amma tabbas bazan goge kuɗina akanki ba wallahi ׳ , Kamar sakarai haka Dikko ya tsaya yana kallona , nunasu nayi dukansu da ɗan yatsa nace gata nan gatanan ku , goge hawaye nayi nai gaba cikin ɓacin rai , Dikko ya sake cewa wai An mata miye kikeyi haka ? Tsayawa nayi amma ban juyo ba nace idan ka sakemin magana saina tona maka asiri....... 25/09/2019 Kuyi haƙuri don Allah wallahi banajin daɗi wannan ma dakel nayi shi , *JAMILA MUSA...*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 41 Dariya Dikko yayi mai shiga zuciya yace tou miye ribarki idan kin tunamin asiri ? Ai asirina da naki a haɗe yake ki tona tunda ban riƙe miki baki ba , amma ki sani idan kin tonashi sai ki fara neman hanyar da zaki rufeshi saboda tabbas wata rana zaki zama ni , ni kuma zan zama ke , kije abunki amma duk abinda zaki kiyi na hankali da tunani , cikon kuɗi kuma da kike magana bake ba da wani abu ya shiga tsakani dake nake ganin mutunciki da ƙimarki saboda kina da wani matsayi na musamma a rayuwata da zuciyata wanda ta dalilinshi kuma nake ɗaga miki ƙafa , duk abinda ya fita hannuna na gama dashi har abadan abada , Kuma zuciyata ta faɗamin cewa ko kin tafi sai kin dawo bata taɓa faɗamin ƙarya akanki ba duk abinda ta faɗamin gaske ne , idan akacemin An mata ta mutu ina da yaƙini zuciyata tacemin a , a tou tabbas idan nazo zan ganki kina numfashi , sauka lafiya amma banda kukan dare dan ina buƙatar bacci a wannan lokacin kiyi kuka da safe kiyi da rana amma idan har kikayi kukan dare gani nan zan dawo , Kallon budurwar yayi ya nuna mata da hannu ke koma mota muje , shiga tayi mota shi kuma ya biyo bayana , gabana yasha yace An mata karki zo kiyi abunda zai zama matsala a rayuwarmu , ki manta da abinda ya faru baya mu fuskanci sabuwar rayuwa , Cikin kuka na kalleshi nace har ƙarshen numfashi na bana fatan na sake kasancewa dakai wallahi , kuma zuciyarka ta faɗa maka gaskiya tabbas zan dawo amma ɗaukar fansa zata dawo dani , Murmushi yayi tare da cewa haba yarinya , Dikko ne fa ! Kin manta nine na koya miki ? Nine nayi kuma nine na fara baki idan daɗi kikaji ko zafi duk nine dai , ruwa idan da rabonka cikin sa ko ka zuba a kwando bai maka yoyo , ni ba abin farautarki bane zaki duk jarumtatai yana ganin ƙimar mafarauci a wancan karon suma kikayi , wannan karon ma haka zata sake faruwa dake ba suma ba har jinya sai kinyi , idan kin dawo ɗauka fansa zaki gane Dikko ba sa'ar wasanki bane domin saina baki azabar da sai kinyi fitsarin wahala bayan kin dawo daga duniyar suma , tsoro na zai shigeki a lokacin da kika kasance dani a shifimɗa ɗaya , idan kuma Dikko baya nan zakiyi kuka bacci ya gagareki gidan biki ko suna Dikko yana tare dake a zuciyarki domin zan zame miki garkuwa , da hannun damarshi ya daki na haggu yace wallahi jarumi ɗaya ake a ƙarni nine jarumin wannan lokaci , Dikko jarumin maza ne kuma ke da kanki zaki faɗa keje ki dawo ina nan ina jiranki , Idan kuma soyayya ta dawo dake , ƙasa ya kalla yana nazari bayan wani lokaci ya kalloni yace tabbas zaki zo zuwa gareni kina roƙon na baki soyayya ta , nace wa ni ? Yace tabbas ranar zata zo , nuna kaina nayi tare daci gaba da cewa yi haƙuri Dikko ka manta da wannan wasan kwaikwayon naka har abadan duniya hakan bazai yuwu ba , murmushi yayi tare da taɓa daidai saitin zuciyarshi yace ina da tabbacin zaki soni kamar dai yadda na faɗa , ko kina da tabbacin cewa baza ki taɓa so na ba ? Nace Eh har abadan abada , murmushi yayi yace ƙarya kikeyi , nace da gaske nake , yace zaki gani nima nace zaka gani , girgiza kanshi yayi yace jeki abunki , Ci gaba nayi da tafiya har yanzu yana tsaye a wurin dana barshi , motoci masu komawa katsina nayi ta ɗagawa hannu har Allah yasa na samu masu ragemin hanya shiga nayi na nufo katsina yayin da Dikko ya shiga suka kama hanyar abuja , Budurwar Dikko kuma ga wayarta a hannuna , domin dana koma mota dama ba jaka na koma ɗaukowa ba waya na ɗauko abinda yasa na fito da jaka dan karsu zargi ni na sace kuma nasan idan sukayi gaba zasuyi tunanin wurin fitowa ta yada ita , Baba da Mama da kowa nata yana cikin waya... Tunda Dikko suka tafi yake kukan zuci daren jiya da An mata tasan irin matsalar daya fuskanta akanta da bata baɗa mishi ƙura ba , abinda ya faru tsakaninsu sirri ne babu wanda ya sani sai shi sai ita sai Allah , yana bata mutuntukar mutuncinta daya ɗauka amma yarinta ta hanata kusantowa gareshi ! Abinda ya faru jiya , bayan Dikko ya faɗawa An mata yana santa tafiyarta kawai tayi ta barshi palo zaune kamar wani sakarai , bata daɗe da shiga ɗaki ba Dady yace yana nemanshi duk abinda yakeyi ya barshi yazo , shine ya tashi ya fita babban palo ya ɗauki makullin mota ya fita kuma a gaban idon Sultana yabar gidan... Bayan yaje gida a palon Dady ya samu Al ' Ameen gurfane a gaban Dady , kallo ɗaya yayi mishi ya ɗauke kanshi tare da samun wuri shima ya zauna can nesa da Dady , bayan ya zauna ya gaishe da Dady ya ansa shima Al ' Ameen ya gaishe da Dikko , Dikko bai ansa gaisuwar ba , kallon Al ' Ameen Dady yace ya kira mishi Ummar , Miƙewa Al ' Ameen yayi kafin ma ya fita daga palon Umar ya shigo saboda dama tuni an kirashi bai samu isowa da wuri bane , bayan kowa ya zauna Dady ya kalli Al ' Ameen yace ga Babana nan ka sake faɗar abinda ka faɗa , shiru Al ' Ameen yayi , Dady kuma ya kalli Umar bayan Al ' Ameen yaƙi magana yace Umar wace yarinya ce take zaune da Baba ? Da sauri Umar ya kalli Dikko amma shi basu yake kallo ba yana kallon wani wuri daban , cike da fargaba Umar yace wallahi Dady nidai ban sani ba , Dady yace tou aini Al ' Ameen yace min ya ajiye mace gidanshi na goroba road bayan ni nasan Babana baya huɗɗa mata shi yasa hankalina ya tashi , Umar sake kallon Dikko yayi amma har yanzu Dikko fuskar nan tashi dai kamar yadda take kullum kuma har yanzu baya kallonsu kawai dai yana saurarensu. Dady yace ƙarya zakamin ne ? Ya tambayi Umar , Umar yayi shiru , Dady yace ma Al ' Ameen yanzu ina yarinyar take ? Tana gidan har yanzu ? Al ' Ameen yayi shiru , gyara zama Dikko yayi yace tana gidan Dady , amma lokacin dana fito na barta tayi bacci , nayi kuskuren rashin sanar dakai amma da Allah kayi haƙuri nayi amfani da maganar ka ne da kace na zama mai kyautatawa duk wanda naga rayuwarshi tana buƙatar taimako , Yarinya ce ƙarama shekarunta bazai wuce 18 ba kuma na baka labarinta kwanakin baya itace yarinyar da mukeyin faɗa tou yanzu mun daina faɗan ne , a tsawace Dady yace ɗiyar ɗan caca ? Karuwar Babana ? Cikin ladabi Dikko ya sauke kanshi ƙasa tare da rufe idanuwanshi , Dady yaci gaba da cewa duk ƙoƙarin kare martabar ka da nake maka ni zaka ɓatawa siyasa ka ɓatamin suna har cikin jahata ? Ni zaka zubarwa da mutunci ? Ka ɗauko karuwa ka ajiye a gidanka ka bar matarka kaje ka kwana da "yar iska mara tarbiya wacce tafi ƙarfin iyayenta itace wacce kake ganin kaine zaka gyara mata rayuwa ? Masifar da tasa iyayenta suka yada ita ba ƙarama bace kai shine kaje ka ɗauko ka dawo da ita rayuwarka kai sarkin imani da tsoron Allah ? Kana siyasa zaka ɓatawa kanka suna , ka zubar da mutuncinka a idon duniya ina amfanin mu'amula da karuwa ? Ko zaka dafa Al ' Qur'ani kayi rantsuwa kace baka neman yarinyar nan babu wanda zai yadda , da yarintar ka baka bi mata ba sai yanzu da shekaru suka fara hawanka ? Tou idan dan rashin lafiyar matar ka ne Momynka ta nemo maka auren ɗiyar yayarta shikenan na kashe maganar... Murmushi Dikko yayi tare da cewa gaskiya Dady ban tsara zama da mace 3 ba a rayuwata itama Sadiyar haƙuri nayi kawai na ansa amma ni gaskiya mata 3 sunmin yawa wannan karon bazan ansa ba kuyi haƙuri , ciki ɓacin rai Dady yace wallahi idan dai ina lumfashi a duniyar nan baza ka auri karuwa ba sakaran banza da baka san macen da ya kamata ka aura ba , shi aure daka ganshi yana buƙatar cancanta mutuntaka asali da nasabar mace , banda kake sakarai ka rasa wacce zaka so sai karuwa ? Karuwar kake tunanin zata zama uwar "ya "yan ka ? Ni wallahi ko jirgi zan siya bana buƙatar na hannu sai sabo shi yasa bazan iya auren zawara ba amma kai dan baka kishin kanka har kake tunanin auren karuwa , wallahi da kasan kanka ko mace baka nema ,na tsani wani yayi amfani da abu nayi amfani dashi saboda tsanar da nayi ma abun yasa bana sauka hotel , duk jahar daka gani babu inda banda gida babu ƙasar da ban mallaki gida ba dan na tsani wani ya shiga a wuri na shiga sakarai wawa dakai idan baka fita harkar yarinyar nan ba zaka haɗu da fushi na , Dady kayi haƙuri kasan.... Tsawa Dady yayi masa yace nasan me ? Ko zaka mutu banajin komai Babana , Dikko zai sake magana Dady yace fita bana san ganinka , jiki a sanyaye Dikko ya miƙe ya fita , ɗakin mom inshi ya nufa itama faɗa ta mishi sosai domin Allah kaɗai yasan abinda Al ' Ameen ya faɗa akan Sultana , Itama wata yayarshi da isowarta kenan nigeria tazo ganin Sadiya ta sako bakinta tayi ta ma Dikko faɗa tare da cewa kadaiji kunya wallahi kuma kayi asara ka rasa wacce zaka so sai ɗiyar ɗan caca , abun kunya duk nasabarka da mutunci gidanku kaje ka auro mana ɗiyar marasa asali , jiƙar matsafi ɗiyar ɗan caca karuwa tou ka faɗamin ita me zata haifa ? Kalli yadda tazo ji yadda take tata rayuwa wace irin tarbiya zata ba "ya "yanta ? Gaskiya Dikko ka bani kunya da ina alfahari dakai amma , Dikko ya tareta da cewa amma yanzu kin daina ko ? Tou kije kiyi ta daina warki kuma ki fitar da bakinki idan ba haka ba kuma duk abinda nayi miki ke kika jawa kanki , Momy tace rufemin baki mara kunya ko itama halin karuwanci zaka nuna mata ? Dikko yace tou ta ƙara aibata ta kiga yanda zanyi da ita ! Wallahi saina zane mata jiki tas idan kuma tana ganin zaki hana na daketa ta fito waje wallahi saina bi ta kanta da mota na wuce , wani irin mari Momy taimishi dan tasan halin Dikko da kafiya idan dai yace zaiyi sai yayi idan kuma ya rantse akan abu ko za,a mutu baya kaffara saiya aikata wallahi , Kallon Yayarshi yayi yace akanki aka mareni ko ? Jinjina kanshi yayi tare da miƙewa yace zan haɗu dake , tace ni ba'a kaina aka mareka ba akan karuwa dai , cikin ɓacin rai Dikko ya nufi wurinta Momy tace idan ka taɓata ban yafe maka ba shanyayye , dariya yayar tashi tayi tare da cewa aikin san karuwa koba asiri akwai bariki mai wahalar goguwa a zuciya , wallahi Dikko ka daiji kunya ɗiyar daka isa ka haifa ai ko baka haihu ba ka kalli ɗan abokinka , fita Dikko yayi daga ɗakin dan idan ya tsaya komai zai iya faruwa , Wurin motarshi ya samu Umar , kuma Umar shine ya faɗawa Dikko cewa Al ' Ameen yazo ya faɗawa Dady komai kuma ya ɗora da cewa idanma aure mai gida zaiyi ga ɗiyar yayarshi , shine ya kawota gidansu Dikko kuma tayi sati tunda tazo Dikko bai taɓa ganinta ba sai yau , kuma Dady shine ta tursasa Dikko yaje asibiti ya ɗauketa ya tafi da ita ya ajiyeta kaduna , tunda tazo itace take kula da Sadiya , tana kyautatawa kowa na gidan , Ita kuma Momy ta riga data yanke shawara kawai Dikko zai auri autar ɗiyar yayarta , kuma duk zagin da yarinyar nan tayiwa Sultana wallahi Dikko baiji ba , baisan sunayi ba dan hankalin shi baya wurinsu yana can ya tafi duniyar tunani , bige²nsu kawai yaji , amma wallahi baiji zage²nsu ba , Al ' Ameen shi yasan komai akan Sultana kuma shine ya bawa ɗiyar labari yace ta faɗawa Sultana tace Dikko ne ya bata labari , amma tayama Dikko zai fara wannan sakin layi ? Bayan bai haɗa Sultana da kowa ba , A gajiye na iso anguwarmu tafiyata babu jimawa anguwar ta samu ci gaba sosai , tun daga farkon layin hannun da Dikko ya sissiye har zuwa gidan dawankashi an bugeshi anyi wani irin zuƙeƙen gini babu wani maƙoci daya raɓeshi baya tare da kowa sai gidajen dake kallon gidanshi , waje kawai aka gyara aka ciccina mishi fulawowi ciki kuma aka watsa dawakuna da wasu irin lafiyayun karnukan turawa masu kama da kuraye , an ƙawata gidan da wasu irin fitulu wanda idan dare yayi aka kunnasu haskensu zai gauraye ko ina da ko ina , Gidanmu na shiga da sallama , Nana tana gani na ta tashi da gudu ta shige ɗaki , Babana na gani kwance saman tabarma yanajin magana na ya karkato da kanshi dakel ya kalleni , Kowa ya tsaya yana kallona babu wanda ya ansa min sallamar da nayi , wurin Babana na nufa na durƙusa na kamo hannayenshi nace meke damunka ? Kallona yayi cike da tsantsar ƙauna sannan ya buɗe baki dakel idonshi ya cika da hawa yace shine kika tafi kika barni....? 😭 Murmushi nayi tare da goge mishi hawayen nace ai gani na dawo ? Kana tunanin zan tafi na barka ne ? Bayan bana iya rayuwa saida kai ! Dare da rana safe da yamma yanayin farin ciki da damuwa halin yunwa ko ƙoshi babu kowa a zuciyata sai kai , farin ciki ya dawo rayuwar kunci da damuwa zata kama gabanta , Har yanzu babu wanda yayi mana magana ga gida cike da jama'a yayin mutane suka fara janye "ya "yansu , matar Baba ƙarami ta kira "yarta gefe tace ki wuce ki tafi gida annoba ta dawo , Wane yaro ne ya shigo gidan cikin farin ciki yana barka da dawo uwar ɗakinmu , ban kalleshi ba kuma ban saurareshi ba ina kallon yadda jama'a suke tsame "ya "yansu saboda zuwana , jinjina kai na nayi tare da cewa wane yaro a kawomin abinci da Allah , saida ya saramin caucau Allah dai ya kare miki sharri yayi maganar cikin muryar dabanci , nace Amin shi kuma ya fice... Fitar wane yaro nabi duk wanda ke gidan da kallo , sannan nace duk sannun ku ? Na dawo ya mai jiki ? Babu wanda ya bani ansa , murmushi nayi na zauna gefen Babana , ban gama zama ba Amisty ta shigo , fitowar Nana daga ɗaki shigowar wane yaro da kwanon abinci , Hafsa A ' i Saude Zalifa Karima sai kuma wata daban wacce nake tunanin itace suke zuwa gidanta wato Asma'u , Murmushi nayi tare da miƙewa tsaye nace dama nasan ranar nan tana zuwa shi yasa na taho gida na dawo kuma a tafe nake da sabon salo na baya ba komai bane ba , ga Sultana ga Amisty ga kuma Hafsa ku kaɗai nake da damuwa daku sauran kuma banma sansu ba , .... 26/09/2019 *JAMILA MUSA....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 42 *_AHUMAGGAH yadda kika fara lafiya ubangiji yasa ki kammala lafiya , ku nemi naku karku bari ya wuceku daga alƙamin SURAYYAHMS haziƙar marubuciya mai tafiya dai² da zamani yana nan yazo..._* Kallon wane yaro nayi nace kai muje ƙofar gida kaji , na faɗi maganar ina nufar hanyar fita , riƙoni Amisty tay ta baya tana cewa babu wani wajen da zakije anan zamu ci uwarki , ban kalleta ba na kalli inda ta riƙeni nace sakemin hijabi , Hafsa tace baza'a saki ba kina nufin mu zaki ɗauka wasu ƙolaye mu barki kuma , murmushi nayi na kalli Hafsa nace sakarar banza ba ƙolaye ake cewa ba kuzo muje ƙofar gida , saboda bana so ayi wulaƙancin a gaban Babana da kuma sauran jama'ar dake gidan gani na ma kawai yasa sun kora "ya "yansu ina kuma ga anyi wannan maganar a gabansu , duk a zuciyata nayi wannan nazarin .... Babana ya karkato cikin yanayin jin jiki yace Uwar masu gida me ya faru ne ? Nace ba komai Babana , a kadarance Amisty ta kalleshi tace ai kasani , a wahalce ya kalleta yace me na sani ne Amina ? Nace Baba da Allah ya isa haka kayi bacci abun ka kada a ruwa ai sarki ne kaja bakinka kawai kayi shiru domin ni wutar kara ce ba'a kwana dani ba saidai idan ba bacci ake ba ! Mamana..... Ya faɗa tare da lumshe idanuwan shi yace mene ne ? Kallonshi nayi cikin ɓacin rai nace wutar da aka daɗe da kashewa ni kuma nake so yanzu ta ruru , cikin hayaga ga , nace ɗaukar fansa da ramuwar gayya a cikin jininka yake Babana , baka gada ba ni kuma na gada ɗan koyo da ɗan gado dukansu idan suka tashi sai sun zarta , Na rantse da ubangiji da ya bani aron lumfashi da rayuwa dawowa ta sai ta zame ma kowa tashin hankali saina firgita kowa saina jinyata duk wanda ya shigo rayuwata , wallahi ׳ Amisty da Hafsa kun sake toƙalowa kanku masifa idan baku kiyayeni ba uwar kowa a cikinkun nan , na nuna su da ɗan yatsa na jinjinashi nace kuma nayi rantsuwa... Da sauri Hafsa ta kalli Amisty suka kalli juna cikin firgici , komawa nayi na zauna tare da cewa har kun firgita kenan ko ? Jinjina kaina nayi tare da cewa baku ga komai ba furtawa kaɗai nayi kuma ban faɗa muku abinda zan aikata ba amma tabbas wani abu zai faru , kallon wane yaro nayi nace kai bani abinci kaji , gabana ya ajiye abinci nace muci shi tare , babu ɓata lokaci yasa hannu mukaci gaba dacin abinci , Kallo Babana ya bini dashi na wani lokaci sannan ya kalli Amisty yace mi ya haɗaku da Uwar masu gida ? Amisty tayi shiru tou maganar dai bata faɗuwa da kunya tace tsiraicin Babanta na ɗauko , tayi shiru ta kasa magana , lashe hannuna nayi tare da cewa bara kaji abinda ya haɗamu Babana , Kafin in ɗago su Amisty sunyi layar ɓata domin dai bansan ta inda sukabi suka fice ba , murmushi Babana yayi mai nuni da yana alfahari dani , kallon wane yaro nayi nace jeka idan Allah ya kaimu jibi ka dawo ina neman ka , godiya yayi ya fice daga gidan , ni kuma ɗakina na nufa ina zuwa na cire kayana , alwallah nayo nazo nayi sallah azahar har saida nayi la'asar sannan na tashi , Komai na ɗakina yana nan yanda yake babu abinda aka taɓa har kuɗin dana sata a jakar Amisty duk suna nan , wanka nayi na saka kaya na fice daga gidan , a napep naje gidan su Mamy wacce muka haɗu da ita a wurin saloon , ban sameta gida ba , saidai nabar saƙo idan ta dawo ace mata Sultana tazo mu haɗu gidanmu jibi idan Allah ya kaimu , Kasuwa na shiga nayi "yan hidimomi na har katifa na siyowa Babana da sabbin zannuwan gado 3 sabuwar ledar tsakar ɗaki sai ƙaton bargo saboda yanayin sanyi ² dake shigowa da labulaye masu kyau , bayan na gama da kasuwa naje na siya sabon sim card na wuto gida... Ɗakin kusa da ɗakina na share na shinfiɗa leda na saka katifar na rataya labululluka na shinfiɗa zanin gado mai kyau a saman katifa , ɗakina na koma na ɗauko fulaluwa nazo na saka musu rigarsu irin na zanin dake saman katifar , ruwan zafi na dafa na kaiwa Babana bayi yaje yayi wanka , Kafin ya fito na ɗauko mishi kayan da zai saka dan naga kayan a gefen katifar ɗakina , ɗakinshi nakai mishi da turare shima a kusa da kayanshi na gani turare mai shegen tsada da ƙamshi , yana fitowa ya saka kayanshi ya shafa turare sannan yayi alwallah dan magrib ta gabato , abin sallah na shinfiɗa mishi ya hau sama , nima na fito nayi alwallah na wuce ɗakina... Duƙe yake saman bayan kujera ya ƙurawa waya ido yana kallon hotunan Sultana , murmushi yayi a bayyane yace da wannan kyakkyawar zan kere sa'a na kasace na daban abina , amma dai ya kamata na bata shawara ta daina ciki baki akan cewa baza ta taɓa so na ... Zagayawa yayi ya zauna saman kujera yana cewa dani dake yau zanga waye tunani zai hana bacci , kwanciya yayi saman kujera ni na kwanta kuma bacci zanyi ya ƙarasa maganar yana murmushi , saida ya lumshe idanuwanshi yace ki kasance cikin farin ciki na barki lafiya.... Saida na gama duk abinda nakeyi na kwanta saman katifa a gajiye , a hankali naja bargo na lulluɓe tare da ƙurawa wayar dana ɗauko ido kira sai shigowa yakeyi babu ƙaƙƙautawa , uhum murmushi nayi tare da kashe wayar gaba ɗaya na rufe idonuwana danyin bacci.... _Ƙarya kike..._ Wannan kalmar itace ta fara zomin a cikin kwalwar kaina , ɗan jujjuya kaina nayi a hankali na gyara kwanciya ta , _Zuciyata ta faɗamin cewa ko kin tafi sai kin dawo , bata taɓa faɗamin ƙarya akanki ba duk abinda ta faɗamin gaske ne_ Murmushi nayi har yanzu idanuwana a rufe nace tou ya akayi ban dawo ba ? _Zaki zo zuwa gareni kina roƙon na baki soyayya ta , tabbas ranar zata zo , murmushin shi yazo ya tsayamin a rai kalmar ƙarya ta sake dawomin a zuciyata..._ Da sauri na tashi zaune nace wallahi ƙarya kakeyi na tsaneka.... Murmushi yayi ya gyara kwanciya , nasan baki tsaneni ba ɓacin rai yasa kike faɗar wannan kalmar , idonshi a rufe yayi magana ... Wallahi a daren ranar banyi bacci ba , tun daga ranar dana fara ganin Dikko har zuwa yau da muka rabu ko ta ina Dikko ya zargemin zuciya , nayi juye² wallahi bai fita ba , ganin dai baccin bazai zo ba yasa na haƙura na fita nayo alwallah naci gaba da sallah ! *** Yau laraba kuma itace jibin da nake jiran zuwanta , bayan hantsi ya ɗaga na dafa ruwan wanka wa Babana , kafin ya fito na gyara mishi ɗakinshi na share na goge fess na zuba mishi turaren wuta , bayan ya fito wanka ya shirya cikin shiga ta kamala ya baɗa ƙamshi , Sama ² ya yagi abin kalacin dana kawo mishi , bayan ya gama ya umurceni dana fitar dashi ƙofar gida saman dakali , ɗakina na koma na ɗauko kafet na naje na shinfiɗa mishi sannan na dawo na kamashi dan har yanzu yanayin abu irin na wanda yasha jiya harya gaji , A hankali muka fito dani da Babana muna lallaɓawa , saman dakalin na samu Amisty zaune ita da Hafsa , ko inda suke ban kallaba na taimakawa Baba ya zauna , a dai² lokacin da Umar yake tsugunniya a gaban Baba yana gaishe shi cikin girmamawa tare dayi masa sannu da jiki , Naji daɗi sosai dan haka nima na gaishe shi , ya ansa cikin kulawa tare da cewa wurina yazo ya faɗi maganar yana miƙewa , bayanshi nabi mukayi nisa da Baba , bayan mun samu madakata yace mai gida ya aikoni wurinki , kallonshi nayi banyi magana ba , wayarshi ya ciro daga aljihu ya kira Dikko bayan ya ɗauka yace mai gida gata , ya faɗi maganar tare da miƙomin wayar , Cikin jin daɗi na ansa na kara a kunne na tare dayin sallama , ansawa yayi cewa ya kike ? Lafiya qalau kaima kana lafiya ? Alhamdulillah , tun shekaran jiya nake so nai miki ya hanya Umar yace yazo ² bakyanan ina kike zuwa ne ? Banje ko ina ba , tou da kyau , na sake cewa banje ko ina ba , yace ai shine nace hakan yayi kyau sai anjima , shiru nayi dan bana so wayar ta tsaya hakanan , shi kuma kashe wayar yayi abunshi... Miƙa mishi wayarshi nayi , shi kuma yace min yana zuwa , mota ya koma ya ɗaukomin wata "yar ƙarama leda mai tambarin waya a jiki yace gashi yace a kawo miki kuma akwai layi a ciki anyi mata caji , Uhum ni da zanma Dikko cikon kuɗi saina ɓige da ansar waya , cikin farin ciki mukayi sallama da Umar , ban koma wurin Babana ba nayi cikin gida ina zuwa na shige ɗakina na zazzage ledar na ciro "yar kyakkyawar wayata na dudduba bansan sunan wayar ba anma an rubuta a jikin wayar , ban damu da sanin sunanta ba nidai tamin kyau kuma ta burgeni sosai , ajiyewa nayi na koma ƙofar gida wurin Babana dasu Amisty dana baro waje , Ina fitowa a daidai lokacin da Mamy ta faka da tsadajjiyar motar ta , tasha wani irin dakeken gilashi wanda ya cinye kaf rabin fuskata , karuwa ce data ansa sunanta karuwa , ba karuwar muje mu dawo ba , ba karuwar wahala ba , ba karuwar ya zanyi ba ? Kana ganin zubin iskancinta kasan karuwanci takeyi mai aji kuma mai matsayi ba iskanci cini inci tuwo ba , Tana fitowa ta fara bi bi biyyy 👍🏻 cikin yanayi mai nuni da "yar hannun ce , murmushi Babana yayi cikin jattako da gogewa , wata alama yayi mata da ido irin tasu ta "yan bariki , dariya tayi tare da cire gilashinta tace *BINNA* 👍🏻 , Binna kaci dubu ka binne dubu , binna zaki binna kura binnan ƙarshen ƙarni binna ka taushe ..... Sai kuma ta fasa ƙarasawa ! Dariyar "yan duniya Babana yayi tare da ɗan kauda kanshi gefe cikin jin kunyata , Mamy ta sake cewa Binna wuta , wuta na wurina.... Ba tare daya kalleta ba yace ga Mamana nan da nake baki labari ku gaisa , gaba ɗaya tabi mu da kallo dani da Amisty da Hafsa a wani irin yanayi tace wace ce Uwar masu gida ? Kakkaɓe idanuwa na nayi nace nice , ƙwalalo idanuwa tayi tana kallona sannan ta sake kallon Babana tace Binna Sultana ɗiyarka ce ? Jinjina kai Babana yayi alamar Eh , ƙara kallona tayi sannan ta sake kallon Baba ta juyo ta tsareni da ido.... Kusa da ita na matsa na duƙa ƙasa² nace matsayin kura daban amfanin labule sirri , huɗɗakir da Babana daban nima tawa dake daban , Murmushi tayi tare da kallon Amisty tace Amina kuma tsaf ta kira sunan Hafsa , tace ke kuma Sultana ? Nace sosai suma mu'amular ki dasu daban nima har yanzu nawa daban da nasu..... Kallon Babana tayi shi kuma yayi murmushi tare da cewa mijinki ya dawo ne ? Miji kuma ? 😳 wane irin miji na tambaya a bayyane , kallona Mamy tayi tare da cewa ya dawo ya koma ta ƙarasa maganar tana murmushi , Babana yace sai kuma yaushe zai dawo ? Har yanzu ni take kallo tace harsai na kirashi.... ! Dama kina da aure ne ? Na tambayeta tace Eh amma auren jeka nayi ka kawai idan yazo miji idan baizo ba sauka lafiya , ƙara duƙawa nayi nace ina kika san Amisty da Hafsa ? Wurin Babanki na sansu , Babana kuma kamar ya ....? Dariya tayi tare da cewa amfanin labule sirri yanzun nan kika faɗa Sultana , saboda haka a sake labulen muje ciki inji neman da kike min , Amisty tace Aunty Mamy amana don Allah , cikin rashin fahimta na kalli Amisty nace amanar uwarki .... Dariya Mamy tay tare da cewa ai kinsan ba haka nake ba , kowa da wurinshi , Murmushi nayi na nuna mata da "yan yatsuna biyu manuni da mai bi mishi 🤞🏻 kamar ina datsa abu nace kema ...? { lesbian } Tace ina yaran wata ƙawata ne , nace baƙar magana kika faɗamin kenan kikace wurin Babana kika sansu ko ? Tace wallahi tare da Babanki nake ganensu kullum rana , Kallon idonta nayi tare da cewa kuma fa da gaske kike ba ƙarya kika faɗa ba , tou amma idan na gano akwai wani abu tsakaninsu da Babana tabbas zaune da tsaye bata ƙare ba , murmushi Mamy tayi tare da cewa ki kiyayi Binna duk macen da kika ga tana manneshi ki mata uziri idan ya gaji da kanshi zai wulaƙansu wallahi babu asiri ba komai idan dai kika faɗa tarkonshi fitarki sai Allah , matan yanzu da kansu suke bibiyarshi , kuma duk mutanen da kika sa nayi musu vidio kwanaki kinsan ko su wayen Babanki ne ? Nace sai kin faɗa , jinjina kanta tayi tare da cewa gaba zaki sani amma Allah yasa dai wani abu bai shiga tsakaninki da Baban Hafsa ba , ni babu abinda ya taɓa haɗani dashi saidai munayi waya ana maganganu dai irin na gyaran kasuwa , so ɗaya kawai ya taɓa rungumeni ya bani cake a bakin partyn birthday ina , Mamy tace gaskiya an samu matsala shi kanshi Binna da yasan waye Hafsa a wurinshi daya haɗe zuciya ya mutu , itama bata san wayenta ba , shima Baban Hafsa baisan ke wacecen shi ba , kowa iskanci ² gaba ɗayan ahali sun zama *KWARATA...* Cikin rashin fahimta nace su waye ahali ɗayan ? Murmushi tayi tare da cewa wai dani da mijina shima neman matan bariki yakeyi , murmushi nayi nima dan ban taɓa daukar akwai wani abu ba , saidai tacemin da Baban Amisty da Baban Hafsa na fita hanyarsu tsohuwar motace su koda mai sai an tura , na gane karatunta kalami ne na matan bariki , Kallon inda su Amisty suke suna fira da Babana cikin tsantsar soyayya akwai soyayyar Babana mai zafi a cikin kwayar idon ko waccensu , sun tsareshi da ido daga gani sunajin daɗin kallonshi dan Babana yana kyau sosai gaskiya kuma ɗan gayu ne ƙirƙirar farko yana da aji kuma yanayin komai nasa cikin tsari da burgewa , tabbas saboda Babana su Amisty suka ƙyaleni amma da ba haka ba idan duk katsina dangina ne babu wanda ya isa ya kwaceni a hannun su Amisty... Cikin gida muka nufa da Mamy amma zuciyata tana tamin tariya akan maganar Mamy , _Gaskiya an samu matsala shi kanshi Binna da yasan waye Hafsa a wurinshi daya haɗe zuciya ya mutu , itama bata san wayenta ba , shima Baban Hafsa baisan ke wacecen shi ba , kowa iskanci ² gaba ɗayan ahali sun zama *KWARATA...*_ Juyawa naji kaina nayi kwalwata na zakuɗawa wasu abubuwa sunamin yawo a cikin kai da sauri na rufe idanuwana jikina ya fara kyarma lokaci guda zufa ta ketomin kaina da tunanin da nake dashi da wani sauran sani ya juye kwalwata ta sake toshewa , na sake tashi wata kidahuma ta karfi da yaji..... Gaba ɗaya saina manta maganar da nayi da Mamy nayi ² na tuno amma sai zuciyata tacemin bamuyi wata magana ba , duk yanda naso na tuno wallahi gaba ɗaya komai ya goce daga cikin kaina , amma ban manta na fitar da Babana waje ba kuma na riƙe nabar su Amisty kuma na tuna nayi waya da Dikko amma sauran maganganun sun ɓacemin , Ina ƙofar ɗaki tsaye Mamy ta miƙomin waya cewa ana kiranki , da sauri na ansa na ɗauka , An mata Dikko ya kirani a cikin wata irin murya yace meke damunki ne ? Ba komai na bashi ansa , yace karki min ƙarya meke damunki ne ? Tunani na fara yi , sassauta murya yayi yace me kikeyi yanzu ? Ba komai , kina yanayin tsayuwa ko zama ? Nace tsaye nake , An mata zaki iya faɗamin ko wane iri ne Dikko ? Shiru nayi ina tunani , yace tuna ² An matana , har yanzu kaina juyawa yakeyi , yace kin tuno ko wane iri ne Dikko ko ? Wallahi Dikkon ma ya ɓacemin , An mata tsaya kiji kin tuna nine mukayi fada dake har kika mareni , kin tuna ? Eh na ganeka , amma me yasa kamin wannan bayanin ne ? Murmushi yayi tare da cewa kawai mafarki nayi wai kin manta dani shine nayi sauri na tashi a baccin na kiraki dan Allah kimin adalici karki manta dani kinji An mata , nace tou yawwa An matana..... Muah yai sumbata , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya na kashe wayar.... Ɗaki na shiga na ɗauko wayar budurwar Dikko ina zama kusa da Mamy nace ciro layin ciki ki saka a wayar nan..... 27/09/2019 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 43 *_Ina miƙo saƙon ta'aziyya gareki HALIMATU SADIYYA MUHAMMAD { Leema } Allah ya bada haƙuri ya jiƙanta yasa ta huta mu kuma ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo..._* *_Don Allah dan Annabin rahma kuyi haƙuri yadda labarin yazo min kenan haka nake rubuta shi_* Me za'ayi da layin idan an ciroshi ne ? Shine tambayar da Mamy tayimin , kallo nabi Mamy dashi yayin da nima nake tambayarta wane irin layi kuma...? Mamy tace kina miƙomin waya ne kince na cire layin ciki na saka a wannan wayar shine nace meye ? A ni ban wani faɗa ba ko dai kin fara ƙarya ne Mamy ? Nifa bana san ƙarya da kika ganni ƙatuwa dake bakyajin kunyar Allah bare kunya na kike nema kijamin sharri ko ? Tou tashi fitar min ɗaki , kamar sakara haka Mamy ta tsaya tana kallona , a hayagagance nace fita....... Da Allah malama , na faɗi maganar ina nuna mata hanyar fita , kallona Mamy tayi sosai tace ke Sultana anya kina da lissafi kuwa ? A , a banda shi sai ke kika iya malamar lissafi , kila ma kece makarantar boko gaba ɗaga ko ? Murmushi Mamy tayi tabi Sultana da kallo cikin yanayin tausayawa , shi yasa ramuwa ga ramuwar abinda akayi maka babu kyau ka rama sharri ga sharri , Binna kuma idan har na faɗa mishi komai tabbas rayuwar yarinyar nan zata ƙare a gariri ne kawai , tun farko da bai anshi buduricin matar Bello a daren farko ba duk da haka bata faru da tilon "yar shi da ya ɗauki soyayyar duniya da ƙauna ya ɗora mata , dogon tunani Mamy ta tafi , tunanin abinda ya wuce shekaru da yawa shine wani sashe na daban yazo mata a kanta... _Cikin farin ciki Binna ya shigo gidansu , dan dashi da Bello kowa baya ma kowa iyaka da shiga gidan kowa , kowa kai tsaye yake shiga..._ _Bello yana zaune tsakar gida Binna ya rungume shi cikin farin ciki da in ina yace kai banzan abokina an haifomin balarabiya yanzu na aihu a duniya duk na gaba hoton banza ne , kaga yarinyar kuwa ? Kyakkyawa da ita gata fara , burina akan ta zai sauka , itace Uwar masu gida dama nace sai an haifomin mai kyau zansa sunan mahaifiyata , zan gina mata rayuwa mai kyau dan ina so inyi alfahari da ita..._ _Murmushin yaƙe Bello yayi tare da cewa wane irin farin ciki kake ji a yau ɗin nan ? Binna yace baya musultuwa , Bello yace yanzu alal misali yarinyar nan sai kawai ayi mata fyaɗ...... Ai bai gama faɗa ba Binna yakai mishi wani irin duka harsai da Bello ya suma , duka ɗayan da Binna yayi masa yasashi tafiya duniyar suma , da gudu Mamy ta ɗauko ruwa ta yayyafawa Bello ya dawo , kallon Binna yayi tare da cewa alal misali fa kawai nace ! 👌🏻 Binna baiyi magana ba sai huci yakeyi kamar ɗan matashin zaki , jinjina kai Bello yayi tare da cewe hakan ya nunamin irin soyayyar da kake yi wa yarinyar nan , tsoki Binna yayi ya fice daga gidan..._ _Fitar Binna Bello yayi dariya tare da kallon Mamy yace wallahi tabon da Binna yamin yana nan bazai taɓa gogewa ba , shi a tunaninshi yaci banza , ya amshe min budurci mata a daren farko kuma yake tunanin zai gujeni , kyaleshi nayi kawai ni da kaina naje na bashi haƙuri duk da ni yayi ma laifi , na lallashe shi muka dawo muka koma ɗaya , tun kafin Binna yai aure yake bada labari akan zuwan Uwar masu gida , yau tazo kuma ta faɗo a dai² lokacin da Bello ke jiranta , ɗaukar fansa ba'a kan "ya "yanshi yake ba akan zuciyarshi yake wato Uwar masu gida mu tafi wasan daga yanzu Binna dani dakai wanda ya fasa shi ba ɗan iyayenshi bane ba..._ _Mamy tace haba dan Allah wai harsai yaushe zaku daina wannan ɗauke ²n fansar naku ne ? Ya kamata abu ya riƙa wucewa a wurinku don Allah , kayi haƙuri don Allah karka cutar da yarinyar ku daina jefe² da tsafe²n nan Bello , Bello yace na rantse da ubangiji daya aiko annabi da gaskiya sai yarinyar nan tayi karuwanci , shine abinda ya tsana tayi , kuma sai tayishi wallahi , namiji ɗaya ne zai buɗe mata ƙofa daga nan zata firgice ,kuma yaci buri akan sai ta zama malamar asibiti wallahi har a busa ƙaho ita da ilimin zamani , zan cuɗanya "yan uwa su halaka zan ɓata zumuncin su ,.... !_ Murmushi Mamy tayi tare da kallon Sultana tace tou zan wuce , kallonta nayi nace kai tun yanzu ? Haba dan Allah karki tafi ki zauna muyi magana , Mamy tace ba komai zan dawo zuwa asabar in Allah ya yadda , ansar wayata tayi ta sakamin numberta , tace kinga number na nan , idan kika tuna abinda zaki faɗamin to ki kirani kinji ko ? Jinjina kaina nayi alamar gasuwa , zan wuce ta sake faɗa , miƙewa nayi dan in mata rakiya... Har ƙofar gida tayi sallama da Baba tahau motar ta tayi tafiyarta , wurin Baba naje na zauna dan Amisty bata nan kila tana gidan Asma'u , kallon Hafsa nayi dake muguwar matsoraciya ce kamar ni , nace da Allah ba mutane wuri zasuyi magana da Babansu , babu gaddama ta miƙe itama ta wuce gidan Asma'u... Kusa da Babana na matsa sosai ina kallonshi nace Babana , yace Mamana ya akayi ne ? Runtse idanuwana nayi kwalwata tanamin wani irin zafi kamar zata fita daga cikin ƙoƙon kaina , hawaye ya cikamin idona cikin kuka na sake cewa Baba , riƙeni yayi tare da cewa wai miye ne Mamana ? Buɗe idona nayi tare da cewa zaka iya misulta irin soyayyar da kakemin ? Murmushi yayi tare da kafeni da idanuwanshi , faɗamin Baba , hannunwashi ya buɗe kamar zai rumgumi wani abu , kallon yanda ya buɗe hannuwan nayi nace ɗan haka Babana ? Ƙara buɗewa yayi na sake cewa wannan kaɗai ? Murmushi ya sakeyi tare da buɗe ko wane hannu saida ya taɓa bango iyakar buɗewa sannan yace ina miki soyayyar da bata da farko bata da ƙarshe , Murmushi nayi tare da kamo hannayenshi na riƙe nace nima ina sanka , ina kuma tausawa rayuwata ranar da za'a waye gari babu ɗaya a cikin wa'annan masoya , idan na rasa ka zanyi kuka Babana harsai na haukace , idan kuma na rigaka mutuwa nasan kaima zaka zare kamar dai yadda zanyi idan baka duniyar nan .... Murmushi yayi tare da cewa haba Mamana idan har na mutu karki sake kimin kuka kimin addu'a itace kawai zata tabbatarmin da irin soyayyar da kikemin , tou mudaina maganar mutuwar nan Babana... Yace tou an daina , nace to wai Babana ina kasan Mamy ? Yace tsohuwar matar Bello ce , murmushi nayi tare da kallonshi nace kaima ka zagaya zawarci ba .... ? Na ƙarasa maganar ina nunashi ina dariya , dariya yayi shima cewa ita dai tayi zawarci na , tou mi yasa baka aureta ba ? Ba tsari na bace ba , ya bani amsa , murmushi nayi nace to wai kuma da gaske tana da aure ? Eh mana tana da aure hada yaranta amma bata aihu da Bello ba , tou Baba amma kuma naga kamar karuwa ce ! Yace Eh me yasa kika ce haka ? Shiru nayi dan dai babu dama na bashi labarin abinda ya faru tsakani na da ita akan iyayensu Amisty , Share maganar nayi da son nayi mishi maganar su Amisty amma sai kawai zufa taci gaba da kwararomin , kaina ya ci gaba da tafasa zuciyata tanamin wani irin zafi , lokaci guda kuma ɗimuwar tunani ta sake zuwa min , kallona Baba yai yace ya akayi kuma kinyi shiru ? Saboda hijabi ne jikina da yaga irin zufar da nakeyi... Miƙewa nayi kawai na koma cikin gida , ina shiga Nana ta nufoni tana magana ko saurarenta banyi ba bare insan abinda take cewa , ina zuwa ɗaki na faɗa saman katifa na dafe kaina wai meke faruwa dani ne......? Gaskiya Bello baka da mutunci kuma kaci amanar amintaka Allah bazai barka ba , Mamy ke faɗawa Bello magana dan daga gidansu Sultana wurinshi ta nufa kai tsaye , dariya Bello yayi yace umm dama nasan sai kin hallara ai mayya , wai me yasa kike san Binna da yawa haka ne ? Murmushi Mamy tayi tace duk abinda yasa ma nake maitar tashi ka sani kuma maitarshi yanzu na fara , dariya yayi yace iska na wahar da mai kayan kara kuma wallahi kika sake dawomin da hannun agogo baya saina shafe babinki a saman doron ƙasa ... Dariya Mamy tayi sannan tace ina jiranka , tana faɗin haka taja motar ta tayi gaba... Ranar juma'a da daddare bayan na gama sallar isha'e na fito da makullin mota ina sauri dan jirana Baba yakeyi sai kira yake kwalamin , ina fitowa Nana tace Alaji yazo nemanki bansan kina nan ba aka ce masa bakya nan , ko inda take ban kalla ba , muka fita daga gidan dani da Baba majalisarsu zan ajiye shi yacemin yanajin sauƙi naje na kaishi yaga abinda ake ciki , Ina ajiyeshi na dawo gida ban biya ko ina ba , ko parking ban gama gyarawa ba na hango wata mota a gabana kamar ana kokowa a ciki sakamakon haskasu da nayi da fitilar mota ta , da sauri na fita daga cikin mota ta na tun karesu ina zuwa na buɗe motar wai in rabasu , me zan gani.... Haka ? Ƙanwata na gani ana iskanci da ita a cikin motar watanni biyar na bata da aihuwa , kallon saurayin nayi sannan na kalleta nace me kukeyi haka ne ? Babu damuwa ko fargaba a tare da ita sukaci gaba da abinda sukeyi , jiki a sanyaye na rufe musu ƙofar na koma motata na zauna ina jiran su gama , Hawaye naji ya cikamin ido nasan duk yadda akayi kila ta nemi wani abu ta rasa kuma ta tambayi Baba kawai zaice taje saurayinta ya bata , kwantar da kaina nayi saman sitiyarin mota ina goge hawaye , zata fito zan mata faɗa nace duk abinda take so ta faɗamin zan riƙa bata , Ai ban gama tunanin ba kaina ya juye , zuciyata tace karki wani yi mata nasiha kinga kin samu ƙarin fasinja daga nan zaki samu tayo miki yaƙi da "ya "yan gidan Baba ƙarami kawai kuci gaba da sha'aninku tunda kun rabu dasu Amisty , murmushi nayi tare da cewa tabbas haka za'ayi... Dama ranar dana dawo naga kowa sai janye ɗanshi yakeyi karna gurɓatashi , zuciyata tacemin Eh kiyi ƙoƙari ki yaƙi duk wanda ya kyamaceki kinga idan kowa ya zama ɗan iska abun zai miki sauƙi wurin gori , Haka ne fa , ina ƙoƙarin fita a mota shima yayi parking in tashi daga bayana ya riƙa wasa da fitilar motarshi , ta kashe ta kunna , rufe mota ta nayi na nufi saman dakali inda zan jira fitowar "yar uwata , Ina zuwa dai² motar zan wuce ya buɗe murfin motar ƙamshin shi da sanyi a c suka lulluɓemin kaf ilahir ɓargon jikina , a kasalance na tsaya tare cewa ashe kaine ? Ey mana nine nazo gaishe shi , murmushi nayi na kunna fitilar wayata dan idanuwana sun ƙagara suga fuskar Dikko , haskashi nayi yaɗan shanye idanushi saboda hasken fitilar... Sai ya ɗan rufesu ya buɗe su yayi haka yakai sau biyar sannan yace kinasan ki ganni ne ko ? Bara na kunna miki fitila ki ganni sosai , da sauri na kashe fitilar wayata na taɓe baki nace wa ni ? Tirr Allah ya sawaƙemin me zan kalla fuskarka , a dai² lokacin daya kunna fitilar motarshi yana cewa kinfi kowa sanin abinda kike kallo.... Murmushi yayi tare dayimin wani irin kallo yace ya kika gannin ne ? Ya ƙarasa maganar yana kashemin ido ɗaya , juya mishi baya nayi ina murmushi cikin jin kunya , gyara zamanshi yayi yana cewa bari in tafi zuwana kenan nace saina fara ganinki yakai hannunshi ya kashe fitilar daya kunna , Harararshi nayi tare da cewa kuma bakai kyau ba , dama banda abinki meya haɗa namiji da kyau ? Kece dai mai kyau kuma daga yanzu idan na kiraki saima na riƙa cewa ya kyau ? Zan tafi yayi maganar yana rufe motar , shiru nayi banyi magana ba dan bana san ya tafi kuma shima ya gane haka , Sauke gilashin motar yayi ya kwatar da kanshi saman murfin motar yana kallona ta sama yace ko kar in tafi ne ? A , a , a , a kawai kaje abunka , cikin sigar zaula yace kedai....... In tsaya ki ƙara gani na ko ? Matsawa nayi ina cewa wuce , murmushi yayi tare da cewa to na wuce sai Allah ya kaimu , nace amin , ɗage gilashin motarshi yayi ya fice da rubos tun daga ƙofar gidanmu har bakin titi , yana fita yaci taya ya ɓace abunshi , murmushi nayi komai na Dikko burgeni yakeyi , Cike da soyayyarshi na isa bakin dakali na zauna , ban daɗe da zama ba ta fito zata shige gida nace yaki Hamida , zuwa tayi tace gani , cikin tausayawa na kalleta dan itama babu uwarta a gidan , nace Hamida kin tambayi Baba wani abu bai baki ba ko ? Shiru tayi tana kallon ƙasa , nace kimin magana kinyi shiru , yanayin ta ya nuna bata san ta faɗamin abinda ya faru dan sunsan bana san laifi Babana , tou tun yaushe kika fara wannan harkar ne ? Tace an daɗe gaskiya , nace yanzu har kinsan daɗin namiji kenan ko ? Daga gefenmu naji maganar Fa'iza na cewa wai na cikin masai ke cewa na waje ya taka kashi , nawa kike Sultana ? Kema kinsan daɗin namiji bare ita ko an faɗa miki ita dutse ce ba mutum ba ? Duk yadda kikeji itama irin abun takeji , ko nufin ki kiyi mata nasiha ? Keji Sultana da buƙulu zatama yarinya baƙin ciki , Ba tare dana kalleta ba nace ke kuma ina ruwanki da firarmu ? Da ruwana mana idan bata samo kuɗinta ba kece zaki riƙa cida ita ne ? Fita sabgar Fa'iza nayi nace nawa ya baki ne ? 150 zaro idanuwa nayi nace 150 sai kaci yaci yaɗi ? Fa'iza tace waike Sultana ina ruwanki da rayuwarta ne ? Ko ke wani ya shiga taki sabgar ne ? Banma Fa'iza magana ba naci gaba da cewa aiko kina karuwanci wahala gaskiya , janyeta Fa'iza tayi tana cewa kyaleta idan kika biye mata sai yinwa ta kamaki a gidan nan , tunda Allah ya baki kin samu na kalacin safe... Suna gaf da shiga gida nace Hamida idan zaki iya huɗɗa dani kizo zan kaiki inda zaki samu kuɗi karki kuskura ki bari a koya miki toya awara a ƙofar gida hayaƙi ya kashe miki ido , kizo in haɗa da wani Alhaji ki biya buƙatarki kuma ga tulin kuɗi , Fa'iza tace naje na toya awarar dan uwarki , dama habaici ne nake mata kuma taji haushi tunda ta tanka , Fa'iza taci gaba da cewa kuma ita bata bin manyan Alhazawa ta bar miki kije kija , nace kece shedar inaja tunda kinga motar da nake hawa , danni ba sakara bace bana barin namiji ya hauni ya a banza ya sauka ni kuma in tashi a 150 ko doki namiji zai hau sai bada kuɗi da yawa bare kuma mace mai daraja.... Idan dai ka murza tou tabbas nima saina murje aljihunka fess , janta tayi sukayi shige gida , dariya nayi nima nabi bayansu , ina cewa 100k idan kin shirya ki sameni ɗakina... 29/09/2019 *JAMILA MUSA....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 44 Ina ƙoƙarin shiga ɗaki Nana ta taho wurina a firgice jikinta yana kyarma tace Uwar room zo kiji wani abun tashin hankali , a firgice na kalleta nace kai miye haka har kin bani tsoro wallahi , magana ƙasa² tace zo muje ƙofar gida tayi maganar tana jan hannuna har muka fito waje... Muna fita ta fara waige² irin yanda magulmata keyi idan zasuyi kilbibi , bayan ta tabbatar babu kowa tace da Amisty da Hafsa suna asibiti , a nutse nace meya samesu ne ? Ƙara matsowa kusa dani Nana tayi kamar zata koma cikin cikina tace gidan matar da suke zuwa... Meya faru a gidan ? Nana tace mijinta yazo ya samesu suna maɗigo , { Lesbian } Asma'un tana ganinshi ta fara kuka ashe sun manta basu rufe ƙofa ba ya rutsasu duk sun haye mishi mata , Asma'u tace ya rufa mata asiri tana cewa ita wallahi ba halinta bane cutarta kawai akayi tana bashi haƙuri , Bai mata magana ba ya koma ya kulle ƙofa , bayan ya kullo ya dawo yace kiyi haƙuri my wife ba wani abu da zai faru sukadai yi miki haka ko ? Tace Eh yace tou koma gefe yanzun nan zan rama miki abinda sukayi miki , wayarshi ya ciro daga aljihu ya fara kiran abokanshi yana cewa suzo gidanshi yanzu akwai babban aiki kuma kowa ya shawo ta dubo ya taho dan yau a gidanshi za'ayi kwana ana wasan *DANBE...* shagon mada da shagon gwaggo zasu buga babbar lamba... Bayan ya gama waya ya hunce tare da jawo ƙarfar Hafsa yace kece kika sha mata nan ko ? Ya ƙarasa maganar tare da taɓa inda yaga tana ma matarshi , cikin kuka Hafsa tace dan Allah kayi haƙuri tsautsayi ne , mijin Asma'u yace ai nima tsautsauyin zan nuna miki , Hafsa zata sake magana ya haɗe bakinshi da nata , wata irin ƙara Asma'u tayi ba tare daya kalleta ba yace Swry madam rama miki zanyi.... Cikin kuka Asma'u tace dan Allah kar kayi , har yanzu bai kalleta ba yace tou ni banza ne inzo in samu wasu na ƙwaƙulemin mata in barsu su tafi a haka ai wallahi ko waccensu saina bata tukwuici , kowa a cikinsu sai taji nauhi na , ihu Asma'u takeyi tana ba mijinta haƙuri baya ji kuma baya gani , kusa dashi ta matsa ta riƙoshi wani irin mari yayi mata wanda yasa tayi zaman dirshen dole a katsa , Haka ya farke Hafsa tas kuma bashi ne farko ba shima akan hanyar wani yabi ya wuce , bayan ya gama ya jawo Amisty itama ya kaita , yana gamawa da Amisty ya sake jawo Hafsa saidai ya zagaya ko waccen su so 3 sannan abokanshi suka shigo suma sukaji yanda kowa keji , bayan sun gama yace itama Asma'u suyi mata , ke a gidan dai haka aka kwana bala'e ana zagaye ² har gari ya waye , da safe kuma ya bawa Asma'u saki 3 gaba ɗaya , kai naga cikakkin *KWARATA...* Wato a gabanki akayi komai kenan ko ? Na tambayi Nana , tace a , a ina ni ayi a gabana ? Ita Amisty tamin waya na taro musu mai napep , dani dasu Zalifa mukaje dan har muka isa asibiti Hafsa bata farko ba , itama Asma'u taji jiki sosai dake Amisty jar wuya ce ita bata wani damu ba , Shiru nayi ina kallon Nana zuwa wani lokaci nace mata miye wasan *DANBE... ?* Nana tace wani sabon iskanci ne maza ke zuwa su saka kuɗi a jera musu layin mata , ko wane namiji zaibi mace goma wanda yakai ba tare daya gajiya ba kuma ya gamsar da ko wace a cikinsu tou dama kuɗi ake zubawa , idan ko wace ta samu biyan buƙata kuma namiji bai huta ba tou wannan miliyoyin kuɗin nashi ne shi zai lashe su , tou ai irin *DANBEN...* mijin Asma'u yakeyi, shine sana'arshi... Haka nan naji raina ya ɓaci wato Dikko kallo yake zuwa shima shi yasa naji yana cewa Saminu a wurin wasan danbe ya haɗu da wata ya bita baisan matar aure bace ba , Cike da ɓacin rai na koma cikin gida , ina shiga ɗakina na ɗauki wayata na fara kiran lambar Dikko , na kirashi yafi sau a irga amma bai ɗauka ba , zuciyata tacemin yana can kallon Danbe , raina ɓace na koma ƙofar gida na ɗauki mota ta na ibi hanyar goruba road , dan nasan irin wannan lokacin suna can suna kallon kwallo , 10:29pm na isa , inayin horn aka buɗemin get na shige... Motoci sunfi goma a harabar gidan , dama nabar wasu a waje ma , cike da ɓacin rai na sauko ko ganin gabana banayi na tun kari palon , ashe ina fitowa mota ya ganni dan haka ya taso da sauri dan ya tareni , a bakin ƙofa ya tsaya ya raba hannunwa shi ya tare ni , kwantar da kanshi saman kafaɗarshi ta dama yace An mata lafiya ? Cikin ɓacin rai nace ashe kai ɗan iska ne , da sauri ya buɗe bakinshi cikin yanayi mamaki yace me kuma yayi zafi haka ? Nace ban sani ba , ɗan buɗe idanuwanshi yayi sosai yace tou ai kin bani dunƙule bansan abinda nayi miki ba , kince ni ɗan iska ne nace me akayi kuma kince baki sani ba , Rufe idanuwana nayi hawaye na zubowa nace ashe danben ranar nan da kake magana iskanci ne , dariya Dikko yayi tare da sauko hannayen shi daga inda ya ɗorasu , jan hannu na yayi muka koma cikin mota ta , bayan mun zauna yace waye ya faɗa miki ? Banyi munafinci ba na kwashe kaf na zayyanawa Dikko labarin da Nana ta bani , dariya yayi sosai yace tou ni bana zuwa kallon danbe ban taɓa zuwa ba , ina da labari dai kuma abinda yasa kikaji nayi maganar danben a waccan rana shi Saminun abokina ne , kuma shine ya kirani yake faɗamin abinda ya faru dashi , kuma nace kizo muje kikace baza ki ba , da wannan abun yasa kika taho ? Da Allah baisa na ganki na tareki ba da haka zaki zo ki ɓara maganar gaban mutane ? Tou ni ban taɓa kallon danbe kowa ba sai nawa da naki , kuma ina addu'a ubangiji ya tabbatar min dake a matsayin mata ta naci gaba da miki kina alfahari dani , yanzu kin yadda kinajin soyayya ta ko ? Ya ƙarasa maganar yana leƙo fuskata , kauda kaina nayi saboda kunya , Dikko yace kinga kinyi kuka dan kina tunani DK n ki yana zuwa kallon danbe , ki kwantar da hankalinki Dikko naki ne ke ɗaya da izinin ubangiji , ni bana zarginki har abadan duniya anma dan Allah karki sake ki bari zuciya da sharrin shaiɗan yasa aimin wasan danbe dake , ni ɗaya tak na isheki bana gajiya kuma bazan taɓa gajiya dake ba har ƙarshen numfashi na , Kwantar da fuska ta nayi saman sitiyari nace to me yasa gwamnati baza ta hana wannan saɓon ba ? Dikko yace tou waye yasan sunayi ? Bayan sun ɓoye babu wanda yasan inda suke sai su kaɗai , muna tare dasu muna cuɗanya bamu sansu ba tunda ba rubutawa akeyi a jikin mutum ba , yanzu dani dake da muka ɓoye mukayi waye ya sani ? Babu wanda ya sani daga ni sai ke sai Allahn daya haliccemu kuma kullum ina neman ya gafarta min kuma ai kin yafemin An mata ko ? Shiru nayi banyi magana ba , kallon agogon hannunshi yayi yace kizo ki tafi gida dare yayi ya ƙarasa maganar yana ƙoƙarin fita daga motar , nidai bana so ya tafi banƙi mun kwana muna magana ba , dan wallahi maganar Dikko daɗi gareta ga sa natsuwa wani irin harshe yake amfani dashi wurin magana nidai tunda nake ban taɓajin irin yanayin maganarshi ba , amma shi na lura baya san yana daɗewa tare dani , ƙara maido maganar baya nayi cewa , Tou baka san Saminu ba , yace An mata ƙungiya ce fa , kuma daga jin irin kuɗaɗen da ake zubawa ai kinsan ba talakawa bane ba , can matsalarsu suyi rayuwarsu muyi namu rayuwar manta da sha'anin wasan danbe kin fara so na yanzu ko ? Shiru nayi , yace tou nidai ina sanki kuma kullum saina faɗa , Maganar abokinshi naji yana cewa DK wace "yar yarinya ce ka ƙurmusa a mota ? Fita yayi yana cewa An mata ce zo ku gaisa da ita , a tadai zo ta gaisheni baka faɗa mata ni yayanka bane ? Ya ƙarasa maganar yana zama saman bayan mota , ba tare daya bashi ansa ba ya maidai fuskarshi kamar yadda take wato ya ɗaure tare da rufe murfin motana yana cewa Allah ya tsare hanya , Kunna mota ta nayi zan fita , gaba ɗaya mazan dake palon suka fito suna cewa mai gadi karka buɗe yau sai munga "yar matan da yake ɓoyewa , cikin ɓacin rai Dikko yace kai buɗe mata hanya ta wuce , da sauri ya fara ƙoƙarin buɗewa su kuma suna cewa idan ka bari ta fita bamu ganta ba wallahi ubanka zamuci , Dikko yace wai da Allah mi yasa kukeyin abu wani iri ? Koma ce mana kayi mahaukata wallahi sai mun ganta , Dikko yace ashe kuwa zakuyi kaffara , kallon mai gadin yayi cikin tsananin fushi yace na rantse da girman Allah ka buɗe get in nan idan kuma baka buɗe ba na rantse da wanda rayuwata ke hannunshi saina taka ka da mota in take ka mutu kamar ɓera kuma babu abinda za'ayi na kashe banza , sanin hali yafi sanin kama , da sauri ya buɗe get in duk zagin da ake mishi ni kuma na fice da da gudu... Sultana tana fita sukayi kanshi suna zagi dan ubanka ba cewa mukayi karka buɗe mata ba ? Mu da bama bi takanka da mota ko ? Faffala mishi mari kowa yayi sannan suka bi bayan Dikko daya koma palo ya kira Sultana yace karta sake zuwa idan tana san ganinshi zaizo ya sameta ko tana ina , tace insha Allah , bayan ya gama wayar yace hmm An mata ta rainani , bata ganin girmana ko kaɗan , tacemin ɗan iska munafiki hada mari , idanma ban auri yarinyar nan ba ai ta gama dani duk lokacin data ganni tana min kallon sakarai na nasha dakai , duk borinki na waje ne bari dai in lallaɓaki kizo hannu zaki gane ruwa ba sa'ar kwando bane... Saida na biya ta majalissa akacemin Babana sun tafi wasan caca , raina ya ɓaci naji banji daɗi ba ace daga fara fitowarshi harya fara zuwa caca , ƙaraurawar kaina ta buga dan haka na manta da ɓacin rai nayi gida abina... Washe gari ranar asabar tunda safe Mamy tazo gidanmu , kuma har yanzu Babana bai dawo ba , da murna na tareta muka shige ɗaki abunmu , bayan mun gaisa ta tambayeni na tuno abinda zan faɗa mata ranar laraba data zo ? Nace mata Eh , wayar na ɗauko na bata nayi mata dukkan bayani amma ban faɗa mata Dikko bane ba , Layin kawai ta cire daga cikin wayar ta bani wayar ta saka layin a jaka , nace da Allah Mamy wai da gaske kina da aure ? Tace ina da aure Sultana , nace keko me yaja miki bin mazan waje ? Bayan ga naki a gida ? Naga wasu ma basu samun ƙoshi ɗaya a bayan wasu shekaru { wanda basu da mazaje , basu da masu kwantar musu ko sauke musu sha'awarsu } kuma sunayin haƙuri keko naga kamar kin girtse da yawa... Kici abincin gidanku kuma kici na gidan wasu , murmushi Mamy tayi tare da cewa aike yarinya ce bakya gane inda aka dosa gashi kuma kwalwarki tana tafiyar ɗimuwar rabin sa'a , murmushi nayi tare da cewa gaskiya ne inajin ƙaraurawar hauka tana bugamin duk bayan wasu "yan mintuka , Mamy tace da yanda idanuwanki da zuciyarki suke ganewa haka kanki ke ja da anyi alfahari dake , kauda kaina nayi gefe nace kwantar da hankalinki ina da ayyuka ne a gabana amma nasan komai zai warware , Mamy tace Allah yasa , zatayi magana kiran Hafsa ya shigo wayarta , ɗauka tayi tare da cewa Hafsa ya jiki cikin murna Hafsa tace Aunty ai jiki ya warke matar Dikko ta mutu , shegiya an gaji da ƙwaƙwar duniya an tafi anya mayyar matar nan baza tayowa mutane fatalwa ba , Mamy tace innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , ke waye ya faɗa miki ne ? Tace Mom ina taje ganinta safiyar nan tana can ma ta rasu amma tace Dikko yaji mutuwar saboda yana zaune kusa da ita tana bashi labarin abinda ya faru da ita bata gama bashi labarin ba ta zuge gilashi ta kama gabanta , Tou Allah ya jiƙanta ubangiji yasa mu cika da imani ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo amin , Hafsa tace yanzu tashin hankalina kuma ɗaya kinaji saura sati ɗaya a daura mishi aure , Mamy tace Hafsa bari anjima zamuyi magana , tana faɗin haka ta kashe wayarta , Wayoyin mutane ta fara kira tana tambayar da gaske ne matar Dikko ta rasu ? Abunka da masu jaha magana ta karaɗe kaf gari , kowa Mamy ta tambaya sai yace mata Eh ta rasu , kallona Mamy tayi tace kodai maganar mutane ta tabbata ? Nace me mutanen suke cewa ne ? Ƙasa² da murya tace kinsan kuɗin gwamna suna firgita al'ummar , ɗanshi kuma ya taso da ƙarfin dukiyar da ubanshi kanshi abun tsoro yake bashi , Anyi itifaƙi kaf gwamnonin nigeria babu mai kuɗinshi , danshi tunin duniya dama yayi kuɗinshi ba'a siyasa ya samesu ba , siyasa daya shiga kawai neman suna yasa ya shigeta amma badai kuɗi ba , to shi kanshi daya haifi Dikkon yana tsoron dukiyar shi , mutane cewa akayi wai ɗan nashi matsafi ne , dama tunda matarshi ta fara rashin lafiya akace ya tsafeta mutuwa zatayi , Wata irin mummunar faɗuwar gaba naji , yayin da zuciyata tace ki rufe idonki ko sau ɗaya ne kiyiwa Dikko adalci Sultana , rufe idona nayi gaba ɗaya a halin Dikko babu ɗaya na zaɓe , Mamy tace da zan baki labari amma gaskiya tashi zanyi na sake dawowa , nace tou , har ƙofar gida nayi mata rakiya saida ta tafi na dawo gida , Tunda Mamy ta tafi nake saƙawa nake warware , me yasa Dikko ya zaɓi tsafi ? Me zaiyi da kuɗi dattin duniya da za'a koma ga Allah a barsu a duniya ? Tsikar jikina sai tashi takeyi , Har akayi kwana bakwai da mutuwar Sadiya ban daina tunanin maganar nan ba , Dikko kuwa ya kirani har bansan adadin kiran ba amma naƙi ɗaukar waya , daga ƙarshe ma kashe wayar nayi gaba ɗaya , Marecen yau kuwa ina ƙofar gida duk abin duniya ya dameni na rasa ina zan saka rayuwata naji sanyi , tunani ya dameni na babu gaira babu dalili , tsayuwar mota a gabana tasa na ɗago kaina da sauri dan a tunani na Baba ne , Dikko ne dan haka na tashi da sauri a daidai lokacin daya sauko daga saman mota , yana fitowa na taga ƙafa ina ƙoƙarin rugawa , a zuciyata nace an cuci sunna gaskiya ga gemu ga tambarin sallah wallahi ka ɓata kyanka , Ya kusa isowa inda nake na ruga da gudu ina wayyo Allahna...... 29/09/2019 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 45 Tsaye yayi yana kallona , ni kuma da gudu nayi cikin gida har na kusa faɗuwa , a mamakince Dikko yabi Sultana da kallo a ranshi yana cewa ko lafiya ? Mota ya koma ya gyara parking , yayi zamanshi ciki bai fito ba ranshi ɗauke da tunani daban ² , ga zafin mutuwar matarshi ga ciwon auren da za'a ɗaura mishi wanda rasuwar Sadiya yasa aka ɗageshi , ga iyayenshi sam² sun rufe idanuwansu akan aurenshi da Sultana... Ya ɗan rame har yayi duhu saboda damuwa da tunani , a gajiye ya fito daga cikin motar ya nufi gidanshi , kafin ya ida shiga Baban Sultana ya faka tashi motar daga can gefe dan kar yayiwa Dikko laifi... Dikko yana ganinshi ya dawo suka gaisa , bayan gaisuwa yace am dama ina san ganin wannan yarinyar ne , cikin damuwa Baba yace ta sake janka ne ? Fuska dai a murtuke babu fara'a yace a , a zanyi magana da ita ne kawai ! Baba yace tou Allah dai yasa lafiya , a ɗan rashin jin daɗi Dikko yace ba komai fa , shi baya so yayi ta nanata magana kuma anajinsa amma a kasa fahimta , Cikin gida Baba ya nufo zuciyarshi cike da damuwa , tunda ya shigo gida yake kwalamin kira kamar ranshi zai fita daga jin yanayin maganarshi babu daɗi a zuciyarshi , Da gudu na fito ina tambayar Baba lafiya , cikin faɗa yace me ya sake haɗaki shiga sabgar yaron can mara mutunci kuma ? Ɗan iskan yaro da baya ganin kowa da mutunci , ya raina arziƙin duk wani mai farin gashi dake doron ƙasar nan , fitinanne yaro dako bakin duniya baya tsoro ga rashin mutunci da masifa kamar kishiyar ɓarauniya... A ruɗe nace ni babu komai , dakamin tsawa Baba yayi yana cewa babu komai inji waye ? Gashi can ya kafe mota ƙofar gida yana ɓacin rai duk abinda nace bana so sai kinyi Mamana kina so dai ki samin ɓacin rai idan na mutu kin huta , Hannuwa na duka biyu na ɗaga alamar bada haƙuri nace a , a Babana kayi haƙuri don Allah , dan bana so naga Baba yana fushi akan komai bare kuma ni daya ɗauki soyayyar duniya ya ɗoramin , Sassauta murya yayi cikin tausayi yace tou kije ki bashi haƙuri nidai bana so kina jawoshi faɗa uwar masu gida , nace tou Baba , a tsorace na fita ƙofar gida gabana sai faɗuwa yakeyi , Dikko yana tsaye ya jingina da mota , da gudu na isa inda yake na riƙe hannayen shi , na irin gani karka kasheni , kallona yayi cikin sigar so da ƙauna yace tou kin kama min hannaye ai gara ki riƙeni gaba ɗayana tunda abin har yakai ga riƙe hannu , Sakin hannuwan nashi nayi na ɗaga kaina na kallo cikin kwayar idonshi , wani irin kallo yayi min kwayar idonshi tana motsawa a hankali wanda idan baka iya saka ido ba baka gane motsi takeyi , Hmmm me yasa kika gudu da kika ganni ? Ko na zama dodo ? Bansan abinda yasa bana iya ma Dikko ƙarya ba amma da nauhi wannan kalma mai muni ta fito daga bakina , Tou tunda baki da abun faɗa ni zan faɗa nawa , shiru nayi ina saurarenshi , yace zanyi tafiya kuma bana tunanin idan na tafi zan dawo yanzu , bana so na shiga haƙƙinki da yawa dan ina baƙin ciki kiyi damuwa a rayuwa , ina so miki farin ciki bana so kiyi kuka haka kuma bana so ki kasance cikin damuwa ko ƙunci , Na baki daga yau zuwa jibi kwana biyu kenan ko ? Ya tambayeni , ina kallonshi banyi magana ba , yace tou kije ki natsu kiyi sharawa da zuciyarki shin kina so na ko bakya so na ? Cikin yarinta nace ni bama sai nayi shawara ba gaskiya bana sanka , kallona yayi sosai yace karkiyi ƙarya An mata zakiyi nadamar hakan wata rana , nace wai ni ? Na ƙarasa maganar ina masa kallon rainin wayau nace Allah ya sawaƙemin ai baka cikin tsarin mazan da nake so , cikin damuwa yace . Kina da matsaloli fa daban ² An mata , saurara samar da farin ciki a domin ɓatawa wani ba dai² bane , haka zafin murmushi a yayin da wani yake baƙin ciki da takaici hmm baya da amfani , karki damu kawai cewa zakiyi ina sanka , shi kenan fa babu wani wahala , uhum kana ba kanka wahala kaji , ince ina sanka ? Allah ya sawaƙemin , Murmushi Dikko yayi maicin rai yace tou ni kuma na san a cikin kwanaki biyu da wannan taurarin idanuwan naki zaki zamo masoyiyata babu jayayya , zaki zo ki rumgumeni , numfashinki zai shiga kwalwata, zaki kalli idanuwana , ina sanka , idan har baki faɗa kina so na ba , shiru yayi yana kallon fuskata , zuwa wani lokaci yace sai kin faɗa , yana faɗin haka yayi tafiyarshi ya barni a wurin... Cike da damuwa na koma gida yayin da zuciyata ke shawarta ta ince ina san Dikko wata zuciyar tace karki sake ki faɗa ko zaki mutu ki barshi kawai kuje a haka , kina mace kice kina san namiji haba ai kinci ƙasa , Lokacin da kwana biyu ya cika zuciyata ta gama tabbatarmin da bata san Dikko , dan haka kuma na yanke shawarar sanar dashi bana sansa yayi haƙuri , Da daddare bayan yazo ya aiko aka kirani dan har yanzu ban kunna wayar ba tunda na kashe ta ban sake buɗewa ba , bayan na fita muka gaisa dashi , bayan gaisuwa yace ina saurarenki , nace gaskiya ansar dana baka tun farko itace har yanzu , Shiru Dikko yayi , bayan wani lokaci yace , wannan rana ta kasance min ranar juyayi ne , bana fatan wannan ranar ta sake zomin , ranar ƙarshe kenan banda wani ƙwarin guiwa , An mata ce kaɗai abin alfaharina , umm abinda bana so ya kasance duk lokacin dana runtse idanuwana nakan iya ganin kyakkyawar fuskarki , bansan mace ba sai a kanki idan har na taɓa san wata mace a rayuwata to kece An mata , Zan tafi idan har naci gaba da ganinki to zan ɓata miki , kiyi haƙuri bazan sake kiranki ba , haka ma zuwa ba zaki sake ganina ba An mata , kin daɗe kina ƙonani inajin kamar na rasa wani abu , me zanyi ? Bazan iya koda dariyar ƙarya ba , jawoni yayi ya rumgumeni duƙowa yayi ya kwantar da kanshi saman kafaɗa ta , cikin wata irin murya mai tsayawa a zuciya yace sai wata rana , ki yafemin don Allah karki riƙeni zan fita daga rayuwarki dan ina so kiyi farin ciki , zan tafi ki huta koda kuwa ni zan shiga halin damuwa , Bayan wani lokaci ya ɗago ya kalleni , cikin kallonshi mai ɗaukar hankali yaɗan ɗauki lokaci yana kallona sannan yazo dai² bakina lumfashin shi yana fitowa saman fuskata , gashin gemunshi yana shafar dai² saitin bakina , lokaci guda jikina ya canja tsikar jikina ta tashi ban taɓa jin irin wannan yanayi ba , bafa haɗa bakinmu yayi ba , daga waje ya sunbace ni wani abu naji ya shiga jikina da gudu saida ya gama zagayawa ya dawo zuciyata ya shiga da ƙarfi , ajiyar zuciya na sauke yanajin nayi ajiyar zuciya ya sakeni da sauri daga jikinshi yaɗan turani baya yace ki tsaya da kyau karki faɗi , zan bada saƙo Umar ya kawo miki kafin in wuce , Kasa magana nayi nabi shi da kallo da sauri ya shiga mota ya bar ƙofar gidanmu da gudu , har ya fita daga anguwarmu ina tsaye a wurin daya barni , yana ɓacewa na kyalkyale da dariya , na zabgaga wani irin ihu , daga cikin gidanmu Zainab ta fito da gudu tana tambayata lafiya ? Sai dire² nakeyi kamar anyi ma doki allura ƙarfi , Zainab tace wai miye yake faruwa haka ? Goge hawaye nayi nace har yanzu na kasa yadda da wannan , Zainab tace miye ne kika kasa yadda dashi ? Nace masoyina ya faɗamin dukkan na kasunsa , shi da yace zan rungumesa sannan na faɗa masa cewa ina sanka DK , Zainab tace waye DK murmushi nayi nace baki sansa ba , Zainab tace tou ki faɗa masa kina sansa mana , nace ke jinan ya nunamin yatsansa yayin da yake ƙalubalanta ta cewa a cikin wasu kwanaki zance ina sansa , murmushi nayi tare da rufe idona , nace kamar dai yadda yace naji ina sansa , ƙara ɗaga murya nayi ina sanka mutumi na , ina sanka , Zainab tace to me yasa baki faɗa a gabansa ba ? A , a , a , a , idan na faɗa masa tou zaiyi ta jamin ƙafane har abada , Zainab tace zakiyi duk abinda kike so amma kuma idan kika makara a soyayyarshi fa ? Nace sam ² ki rabu dashi kawai yayi kuka na wannan daren nasan bazaiyi zuciya ba da safe zai sake zuwa , ni kuma yana zuwa zance barka dai DK idan ba tare dakai ba ina ne zanje .....? Cike da farin ciki na shiga gida , Zainab ta rufomin baya , alwallah nayi na shige cikin ɗakina ina farin ciki , Dikko kuwa yana isa gidanshi wanka yayi , bayan ya shirya ya ɗan faffaka abu mai mahimmanci ba kaya ya ɗauka ba , wasu takaddu ne kawai ya tattara , layinshi ya cire ya ajiye , dube² yayi na irin banyi mantuwa ba kuwa ? Sannan ya fita daga cikin ɗakin , Wajen da aka tanada dan ajiye motoci ya samu Umar kamar yadda yace su haɗu , Ashiru a gefe sai Al ' Ameen , duk gaisheshi sukayi cikin girmamawa , bai ansa ba , makullin mota ya miƙewa Umar tare da nuna mishi mota yace ka kaima yarinyar nan akwai kuɗi a but in tasha mai , Umar yace mai gida wace yarinya ? Yarinya nawa kasan ina tare da ita ? Haƙuri ya bashi tare da cewa tou ai naji bakace An mata ba , murmushin baƙin ciki Dikko yayi a zuciyarshi yace tace bata so na , kuma fa ba'a soyayya dole Allah ma yasa bansha wahalar shawo kan kowa ba dasai nasha wahala na shawo kan iyayena tace bata aurena , gara kawai na haƙura nayi nesa da rayuwarta na barta ta huta , Umar kallon motar yayi Al ' Ameen ma ƙwalalo idanuwa yayi cikin tashin hanki yace mai gida wannan motar zaka bata ? Cikin ɓacin rai yace Ey ita zan bata , cike da hassada yace ko ka manta nawa ka siyota ne ? Dikko yace kila babanka ya nemomin kuɗin shi yasa na manta , dan wani irin haushin Dikko yakeji kuma Dady yace idan yayi masa wani abu bai yafe masa ba , Al ' Ameen ya kalli motar ya ƙiyasta kuɗinta tou ai wallahi kaf garin katsina wannan motar ita ɗaya ce tak , bazai manta ba lokacin da Dikko ya siyo motar wallahi ganinta ake zuwa yi ana mata hoto ko wata motar batayi ba kuma Dikko bai taɓa hawanta ba , shine zai ɗauka ya bawa karuwa ? Kai amma yarinyar nan ta shanye mai gida da yawa , motar miliyoyin kuɗi haka ? Kaf ma'aikatan gidan nan suka haɗu suna ma Dikko addu'a Allah ya tsare , wallahi game da kyauta dai Dikko baisan darajar kuɗi ba , yana kyauta maisa mutum ya kasa gane bacci yake ko idonshi biyu ? Bayan ya gama sallamarsu ya shiga mota Ashiru yaja suka bar gidan , Al ' Ameen kuwa sai ƙara kallon motar yake hada kukan baƙin ciki ina ma ɗiyar "yar uwarshi ta samu wannan mota ? Mai gida baisan abunshi haka nan yake neman kuɗin baisan darajarsu ba wallahi , yo wannan mota ai daya sani siyar da ita yayi ya sayi gidaje masu kyau kawai ya ɗauki mota ya ba shegiyar yarinyar da Z bata tantancewa , lallai zaima Yayarshi waya idan har Mai gida ya dawo nigeria Haneefa taje Abuja wurinshi... Daga gidanshi gidansu ya wuce kai tsaye , danyi musu sallama , momy tace idan an ɗaura aure matarka zata isko ka , cike da biyayya yace tou , bedroom ta koma ta ɗauko maganinshi tace gashi nan saura idan ka tafi ka yadda shi , ansa yayi ya saka a aljihun wandoshi , addu'a tayi mishi tare da mishi fatan alkairi harya fita , Dady kuma baya nan , Cike da soyayya tabi bayanshi da kallo , haka nan taji dai bari ta mishi rakiya , bayanshi tabi har inda ya ajiye motarshi , saida zai shiga mota yaga Momy ta biyoshi , kallonta yayi yace inzo ? Murmushi tayi tace a , a , kusa dashi ta matsa tace karka zo rakiya nayi maka , taci gaba da mishi addu'a Allah ya tsare tana ɗaga mishi harya shiga mota suka tafi , Tun a mota ya goge hotunan Sultana , bayan yayi musu kallon ƙarshe dayi mata addu'a Allah ya bata miji na gari , ya kuma sa ta yafe masa karta riƙeshi a zuciyarta , shi kuma Allah ya bashi haƙuri da dangana akan ta... Bayan ya gama goge ²nshi da addu'a shi ya anshi tuƙin motar dan gani yakeyi Ashiru ma baya sauri , tuƙin ganganci da wauta Dikko na fama da iskanci cike da kwalwarshi , ga raini ga rashin ganin mutuncin mutane amma yana da tausayi da taimakon wanda baya dashi , 10:09pm suka isa kano , anan aka canja abokan tafiya , saida jirginsu Dikko ya tashi Ashiru ya juyo katsina bai kwana ba , sauka lafiya mai gida Dikko Allah ya tsare.... Cikin farin ciki na wayi gari kuma nayi alƙawari yau zan faɗawa Dikko nima ina sansa , duk wanda ya ganni yasan inajin daɗin wannan rana , saida hantsi ya ɗaga na sheƙaƙa wanka na , naci gayuna dan nasan yau Dikko yayi kwanan haƙuri nasan ya ƙagara gari ya waye zai fara zarya ganin dokuna , Cike da farin ciki nayo ƙofar gida na zauna ina jiran isowar jarumina , har lokacin zuwanshi yazo ya wuce babu Dikko babu labarinshi , gida na koma na ɗauko wayata na kunna , bayan ta gama kunnuwa na fara neman layinshi , amma dai inajin maganar ɗaya ce kodai wayar tana kashe ko kuma babu kuɗi a wayata , Gida na koma nasa aka dubamin ko banda kati , kowa sai yacemin akwai idan nace nawa ne sai su kasa lissafomin , Babana na bashi ya dubamin yace akwai kuɗi , nace nawa ne Baba ? Yace dubu ɗari biyu ne , nace tou kiramin wannan lambar na ƙarasa maganar kamar zan faɗa masa , Duba sunan da akayi saving in number yayi yai murmushi tare da cewa iye Mamana ta fara soyayya ya ƙarasa maganar yana kallona kuma cikin zaulaya yayi maganar , cikin jin kunya na zauna kusa dashi ina dafa kafaɗarshi nace aini bana soyayya , yace ai ba wani ne ya bani labari ba nine na gani da idona , tou me yasa kace haka ? A dai² lokacin da yacemin wayar a kashe take , Cikin rashin jin daɗi na anshi wayar kaina ya fara min ciwo haka nan naji ɓacin rai ya lulluɓemin zuciya , cike da damuwa na fito tsakar gida , amma sai naga gidan kamar yana juyawa , Baba kuma yana min magana daga bayana wallahi kwata² banajin abinda yake faɗa , Wai ance ana kiran Sultana , da sauri na fara kakkaɓa idona daya cika da hawaye inayin dariya cikin farin ciki , nayi ƙofar gida da gudu Babana ya fito da sauri ya biyo bayana yana lafiya ? Turus na tsaya ganin Umar , nayi tunanin zanga Dikko babu shi , sake cika da hawaye idona yayi nace ina yake ? Miƙomin makullun mota yayi a dai² lokacin da Baba ya fito yace gashi yace a kawo miki kuma akwai kuɗi a but wai kisha mai , sai ki bani tukuwici in wuce , nace tou ina shi Dikko yake ya aiko ka ? Umar yace yayi tafiya , Kallona Baba yayi yace waye ya kawo wannan motar ? Hawayen da suka taru a idanuwa na suka samu damar gangarowa daga saman kumatu na , da sauri na juya na rumgume Babana ina kuka , ɗagoni yayi daga jikinshi yace wai miye ? Waye ya baki wannan motar ? Cikin kuka nace Dikko ne , kallon motar Babana yayi sannan ya kalli Umar yace wai wane Dikko ne ? Da hannunshi yayi mishi nuni da doki , kallona Baba ya sakeyi yace meke tsakaninki dashi ? Goge hawaye nayi na anshi makullin na buɗe but in motar , bandir in "yan dubu² ne guda goma , guda biyar na ba Umar nayi godiya , shima godiya yayi ya wuce abunshi... Umar yana tafiya Babana yace wai Mamana ke ya akayi ya baki wannan motar ne ? Nace shi yaga dama ya bani ita ba roƙarshi nayi ba , kallon motar Babana ya sakeyi yace aiko wannan motar bata hawuwa wurinki garin nan saidai a siyar da ita kuma duk ma garin nan bana tunanin akwai mai siyenta shima ƙuruciya tasa ya siyeta , { ba rashin kuɗi baba yake magana ba da yace baya tunanin akwai mai siyenta } babu dai wanda zai ware wannnan kuɗaɗen ya siyi wannan motar kawai dan dai ya hau , murmushi nayi kaɗan nace baza'a siyar da ita ba gaskiya , Baba yace ki hauta ace miki wa Mamana ? Nace idan na hauta kaji yadda za'a kirani , tou ina zaki ajiye wannan mota ? Nace gidan dokunanshi zata riƙa kwana ... Allah ya tsare Babana ya faɗa , na ansa da Amin , Da kaina nakai ma masu gadin gidan ajiyar mota , suma kansu mamaki ya kamasu ya akayi motar mai gidansu tazo wurina ? Saboda kowa ya sani tashi ce shi ɗaya yake da ita duk kaf cikar faɗin garin katsina , dan anyi surutun motar sosai a lokacin daya siyota kuma har yanzu ba'a gama ba , wannan ansa basu da mai basu ita.... Na shiga cikin ɗimuwar rayuwa nayi kukan rashin Dikko nayi harna gode Allah , na rasa ina zan saka kaina naji daɗi , "yar jakar daya bani a lokacin da muka kama shago dasu Amisty na ɗauko na zazzage , cingom in daya bani nashi na ɗauka nayi ta ci ina haɗiyewa , saida naji zan mutu na haƙura na tattara sauran na mayar , Na faɗawa iska ina san Dikko bansan adadin kalamai nawa suka fita daga sautin bakina ba , baida wani amfani dan Dikko dai baya nan kuma bazaiji ba , nayi kukan rashin Dikko har tsawon sati ɗaya ina zubar da hawaye duk nabi na rame na susuce , na kira wayarshi kullum dai maganar ɗaya a kashe , duk lokacin dana kira wayarshi naji kashe sai nayi kuka kuma bazan daina kukan rashin ka ba Dikko har abadan duniya.... Bayan wata ɗaya , Abubuwa da dama sun faru , Babana ya warke tas kamar bai taɓa wani rashin lafiya ba , su Amisty kuma an ƙaro iskanci domin dai suma a anguwarmu suka sayi gida , Ta siyi motar hawa ta baro iyayenta tana zaman kanta , Nana ma ta tashi daga gidanmu ta koma nasu Amisty , Saude A ` i Zalifa Karima ma duk sun tare a can , Hafsa ma nan take yini amma bata kwana , itama Asma'u anyi mata register kuma suna faɗa cewa yanzu zanga yanda ake shugabar duk wani ɗan iska daya kwana a katsina suna da masaukinshi , idan inajin nima wata ƙwaro ce na kafa manya ²n karuwai kamar nasu... Lokacin da naji saƙon su Amisty dariya nayi , bana san komawa ruwa dan naji kwata bana sha'awar karuwanci dan zuciyata bata da lokacin sauraren kowa saboda Dikko yabi ya mamayeta da soyayyarshi , kafin inyi wani nazari na yanke hukunci naji gam × ³ a cikin kaina , kamar wacce aljannu yake shiga jikinta haka jikina ya fara fizge² idanuwana sunamin zafi sosai , kaina ya juye , nace tabbas zasu san nawa ba kalar nasu bane mu zuba mu gani dani dasu. A wannan halin Mamy ta sameni , bayan mun gaisa ta fara rattafomin bayani akan Baban budurwar Dikko , wacce mukayi faɗa da ita a mota..... 30/9/09/2019 *JAMILA MUSA....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 46 Tsare Mamy nayi da ido na kasa magana duk saida ta gama buɗemin komai ta ƙare da cewa harma ta gayyato shi zaizo katsina jibi , har ta gama kallonta nakeyi saida takai nunfashinta ƙarshe nayi murmushi amma har yanzu idona akanta yake , kuma banyi magana ba , Mamy taci gaba da cewa tou ya kike ganin za'ayi idan yazo ? Zance gaki ko kuwa ? Shiru nayi na ɗora wayata a saman goshina na rufe idona na dama ina nazari , _Kije abunki amma duk abinda zaki kiyi na hankali da tunani ,_ _Ni bana zarginki har abadan duniya anma dan Allah karki sake ki bari zuciya da sharrin shaiɗan yasa aimin wasan danbe dake , ni ɗaya tak na isheki bana gajiya kuma bazan taɓa gajiya dake ba har ƙarshen numfashi na,_ _Jarumi ɗaya tak akeyi a ƙarni nine jarumin wannan lokaci , Dikko jarumin maza ne kuma ke da kanki zaki faɗa kije ki dawo ina nan ina jiranki....!_ Hawaye ya gangaromin daga cikin ido nace a ina kake jirana inzo ....? Murmushi Mamy tayi tare da cewa soyayya ? Shiru nayi ina hawaye , dariya tayi sosai tace har kin bani tausayi Sultana uban waye ya shiga zuciyarki har kike kuka ? Saida nayi shashshekar kuka sannan na kalli Mamy da ido ɗaya nace ni kike tausayi ? Tace Eh ai soyayya babu abinda ke cikinta sai wahala da dana sanin da bashi da amfani , murmushi nayi mai ƙuna nace gara ki tausayimin dan a halin yanzu banma san a babin da nake ba , Yana so na har yanzu ko ya goge ni daga zuciyarshi banma sani ba , dama yace idan bana sansa zai tafi kuma bazai sake dawowa ba , yazo a lokacin da bansan waye shi ba , kuma ya tafi ya barni a dai² lokacin daya koyawa zuciyata soyayyarshi , bazan gaji ba , ba kuma zan daina faɗa ba har kalma na ƙarshe a duniya , ina sanka ׳ Na ƙarasa maganar ina goge hawaye , Tsoki Mamy tayi tare da cewa yanzu kinji abinda na faɗa miki , sai magana na gaba , akwai wani mijin ƙawata yaga wata anan anguwar yana so ya ɓata dare ɗaya tak da ita , tou na biyota bayan nayi bincike sai akacemin matar aure ce , dana faɗa mishi sai yace min dama matar auren yake nema shin zaki iya kawo mishi ita ? Akan wane farashi ? Na tambayi Mamy , tacemin 50k nace kai haba zunubin fa akwai girma , yadai ƙara wani abu... Mamy tace Sultana haka zai baki , kallonta nayi ido cikin ido nace gaskiya ƙarya kikeyi ke kika rage kuɗin da za'a bani , Sultana ni nake ƙarya ? Nace yo wace ce ke da baki ƙarya ? Mamy tace dama naga kin raina ni ko girma na baki bani ? Murmushi nayi da gefen baki na , nace babu wanda ya kawoni bariki ni na shiga da kaina , bana ƙarƙashin kowa ina bisa ƙarƙashin ikon zuciyata ne , banda uwar ɗaki haka kuma banda ubangida , bana nema wurin kowa dan kowa baida abin bani , wannan harkar ra'ayina ne yasa na shiga badan ra'ayin kowa ba , abuna yana jikina naki yana jikinki , tayuwu ke ki bada naki a baki 1k wannan ra'ayinki ne kuma kinji kina iyawa ne , niko babu dalili na buɗewa namijin banza ƙafata ya hauni ya sauka ya bani kuɗin da bazasu kashemin kwarnafi ba , Ban kawo ki bariki ba baki kawoni ba ,baki koyamin ba haka nima ban koya miki ba , a rana tsaka muka haɗu kin gama gogewarki nima idona biyu kika ganni ba bacci nake ba , tuni na bushe fitilar idona , banda Aunty banda Yaya banda Mama haka kuma banda uwar ɗaki a bariki wallahi , ta yuwu ma kila namiji ɗaya ya nemu a tare yana gamawa dake ya jawo ƙafata , wane girma gareki a wurina ? Sana'ar fa iri ɗaya ce , uwar data haifeni ma data ga bata iyawa kayanta ta tattara ta kama gabanta tou bare fa ke banzar bazara kashi a masai , na faɗa kuma zan sake maimaitawa idan bakiji ba kiji , idan kuma kin manta ki sake fahimta , Matar aure bana kawota a dubu 50k wallahi idan dai yana so tou dubu ɗari biyar zai bani nayi miki alƙawari kuma ki mishi albishir a cikin sati ɗaya tak zan kawota babu asiri babu bori , idan haka yayi miki to idan bai miki ba a daina cinikin dan bana san rainin hankali da yawa.... Shiru Mamy tayi tana kallona ni kuma naci gaba da gwada layin Dikko , can kuma tace tou za'a baki rabin kuɗin idan an gama sai a cika miki , ba tare dana kalleta ba nace ni bana da sasshen jikin mutum , Mamy tace kamar ya kuma ? Nace tou kamar yadda zaki bani rabin kuɗi ! Me zan ciro na fara kawo mishi ? Mamy tace Sultana zan baki rabin kuɗi idan aka gama na cika miki , tsoki nayi nace kinga da Allah ki tashi kina ɓatamin magana a banza , kije idan kun shirya ansar mace kuzo da dubu ɗari biyar na gama magana.... Jakarta ta buɗe ta ɗauko dubu ɗari biyu tace gashi zan cika miki anjima , ai banma da lokacinta bare kuma tayi tunanin naji abinda tace , can kuma tace kin cika kafiya gasu bara na ranta cikin kuɗin ƙawata idan naje banki na cire ita saina bata , da gefen idona na kalli kuɗin , miƙomin tayi na ansa na tusasu fes sun cika , hoton matar ta turamin a wayata tace gata nan kuma bama so sai tazo tayi ta wani noƙe ² nace inki so kije abunki , Har zata fita nace , maganar mai zuwa katsina kuma jibi akwai Hamida akwai yaran gidan Baba ƙarami ki taimakamin suma su shigo sahunmu tafiyar zatamin dai² , Mamy tace baki da damuwa , godiya nayi mata ta wuce abunta , ni kuma naci gaba da nazari akan hanyar da zan fiddo matar aure a kaita wurin mijin da ba nata ba kuma banma taɓa magana da ita ba ina dai ganinta tana wucewa ! *America...* Mai gida Dikko ne kwance a gefen gado , ya ƙurawa waya ido ko kiftawa bayayi , daga can ƙarshen gado kuma amaryace sanye cikin wata irin tsadajjiyar alkebba , mutum biyar suka kawota kuma kwanansu biyu yau suka juya bayan sun ƙara gyarewa ango amarya suka shiryata cikin shiga ta alfarma da ɗaukar hankali , bayan tafiyar "yan rakiyarta ta dawo ɗakin da take tunanin nan ne ɗakin mijinta ta tsareshi da kallo kamar kwarton namiji yaga wawan zama.. Tafi minti 15 zaune bataji yayi magana ba , dan haka ta tashi tsaye ta zare alkabbar ta ajiye a gefen gado , cikin gogewa da buɗewar ido ta fara tafiya cikin natsuwa ta zagaya inda Dikko yake kwance. Kafin ta iso Dikko ya tashi da niyar shiga toilet , da sauri tasha gabanshi tace haba ina ne kuma zakaje ne bayan kayi wanka , kallonta yayi sannan yace zan tsaya kiyi ta kallona ne kamar banda aikin yi ne ? Haba Yayana aiko kaine kake da aikin yi a gabanka , nuna kanta tayi daga sama har ƙasa tace mai wannan zundumemiyar mace inashi ina bacci a daren nan ? Ga kallo kuma ga aiki , kasan yanzu ba'a sake da miji mai mummuna ma ta tattala abinta ina gani mai tsadajjiyar fuska da ƙira mai ɗaukar hankali kamar ka ? Ai banga ta zama ba aiki ya sameni harsai na goge tambarin ɗiyan ɗan caca a zuciyarka... Wace ce ɗiyan ɗan caca ? Dikko ya tambayeta yana mata kallo mai nuni da zaici ubanta ! Haba Yaya DK kana tunanin bansan komai ba ? Kaf labarinta a hannuna yake , me zakayi da wannan yarinyar ? Yarinya mara tarbiya , marar asali jahila da bata gane komai sai karuwanci.. Murmushi Dikko yayi maicin rai dan duk duniya ya tsani a famo mishi ciwon tunanin An mata , haka kuma ya tsani a soketa , cikin ƙunar rai yace ni na sanki tun baki san kanki ba , haka kuma nasan waye ahalin babanki ciki da waje , idan har zan duba girma da tsatson ahali da tarbiyar iyaye ke ko matsayin mai aikin gida na baki ba , da cancanta aka bimin wurin auren da aka yomin ke kinsan baki kai cikin layin matan da zanbi hanya ɗaya dasu ba , An mata bata sanki ba kuma baki gabanta dan bata san da zuwanki ba , tana can tana rayuwarta bake ba ko ni bata da lokacina bana san munanan kalamai yana fitowa daga bakin ki akanta , ba ƙoƙarin gogeta zakiyi ba domin bata gogowa har abadan duniya a zuciyata , idan dai zaki iya kiyi ƙoƙari ki kafa soyayyarki a zuciyata shine abinda zakiy farko kenan , Sassauta muryarshi yayi sannan yaci gaba da cewa , tana da tarbiyya , nine zan bada wannan shedar , asalinta kuma yana tare da asalina , tabbas bata gane komai sai karuwanci , nine na yanka mata tikitin karuwanci nace ta koyo dan tamin riƙo da bazan taɓa tunani wata mace a duniya ba sai ita , ta shafe kaf illahirin zuciyata , tabi cikin kwalwata da jinin jikina , yarinya ƙarama mai tafiya dai² da irin rayuwar da nake so , zan bata labarin ki , kuma ince kina mata gori itama ta goranta miki tunda dai uba baifi uba , sa'arki ɗaya ma da mamanki ta haɗo da momy ai da ina ganinki sai nayi amai... Goge maganar tayi dai tare da nunawa Dikko ya bata haƙƙinta , shareta yayi ya shige toilet, bai daɗe ba ya fito da alama alwallah yayo , itama shiga tayi tayo alwallah ya gabatar da komai kamar yadda yayi a daren farkonsu da Sadiya cikin natsuwa , bayan sun gama suka koma gado anan Dikko ya farke sabuwar amaryarshi kuma ya sameta a cikakkiyar budurwarta , Yayi farin ciki dan a tunaninshi yadda take ta nuna haɗama tana zalama baiyi tunanin zai sameta a cikakkiyar mace ba , komai yaji gaskiya amma Dikko yace gishiri yayi yawwa , { tasha kayan mata sosai } dan shi Allah ya bashi ilimin gane tsurun mace idan ta haɗa da "yan dubaru ya sani , amma wallahi An mata itadai ta dabance... Sai kukan kissa matar Dikko keyi , cikin nuna tasha wahala , Dikko kuwa ɗan jirgiwa yayi ya kifar da kanshi saman katifa tunanin yadda darenshi ya kasance da Sultana yakeyi , wallahi ya cuci budurcin An mata daya karɓa ta ƙarfi da yaji , ƙaramar yarinya da ƙananan shekaru ya saki ƙarfinshi ya haɗa da magunguna yaje mata a gigice , bata taɓa gani ba kuma bata taɓa ji ba sai a gareshi , me yasa ....? Me yasa? Me yasa haka ta faru ? Dole kice bakyasan Dikko saboda Dikko ya zama mugu a wurinki , An mata da kinyi haƙuri kin bani dama a karo na biyu da kinyi alfahari dani , da bazan barki kiyi kuka ba , bazan barki kiyi baƙin ciki ba , shi kenan kin fita a hannuna zaki tafi wurin mai rabo ya ɗaukeki ya dasa wasan sa daga inda na tsaya... A hankali ya lumshe kyawawan idonuwanshi a bayyane yace Allah ya sanyaya miki zuciyarki , a tunaninta da ita ake tace amin mijina , har yanzu idonshi a rufe yace kin yafemin kenan ? Ummm ai bakamin komai ba ma , kenan babu zafi ? Umm umm , to me yasa ki key kuka ? Ba komai , sai yanzu ya gane bada Sultana yake maganar ba , buɗe idonshi yayi da sauri ya ganshi kwance akan sabuwar amaryar shi , kuma "yar uwa a gareshi... Ko tsakar dare dana farka haka naci gaba da gwada wayar Dikko wanda ya zamarmin kamar hauka dan ƙaranci ban kira wayarshi ba a rana na kirashi sau 200 da wani abu , Ina zaune tsakar daren nan ina ta aikin neman wayar naji maganar Baba ƙasa² daga bayan ɗakina dake daga tagar ɗakin sai a fice zaure a fita ƙofar gida , bana iya jiyo abinda Baba yake cewa saidai naji maganar Amisty cikin shagaba tana cewa nidai Dady don Allah... Ta ƙarasa maganar kamar tana kuka ! Da sauri na haska fitila na duba agogo naga 3:45am cikin sauri na miƙe na sake matsawa da kunnena jikin window naji shin da gaske Amisty ce ko kuwa dai wata ce daban ! Wallahi Amisty ce dan duk duniya babu mai irin wannan muryar sai ita , me suke cewa ? Me ya haɗa Amisty da Babana a wannan salasunan daren ? Me ke tsakanin Amisty da Baba ? Duk wannan tambayar banda ansoshinsu nayi yunƙurin yin wani abu tunani na ya tsaya cak domin kaina ya riga da ya juya... Buga kaina nayi da ƙarfin bala'e a jikin bango na kurma wani irin ihu duk wanda ke cikin gidan saida yayo waje saboda ƙarfin ihun da amonshi ni kuma na fito da gudu nayo hanyar fita , babu Amisty domin tuni ta fice , ina ƙoƙarin fita Baba ya riƙeni da ƙarfi yana lafiya ? Fizge ² na farayi na kwace nayi waje , da gudu ya bini ya riƙoni nafi ƙarfin riƙonshi domin na sake zuƙewa daga riƙon da yayimin , cikin tashin hankali zugar gidanmu suka yo kaina dakel suka kaini ƙasa suka daddanne ni na birkice gaba ɗayansu na watse su , na yanki santa , yayuna maza suka taimaka aka kamani aka mayar dani cikin gida , Kowa tambayar abinda ya sameni yakeyi ? Murmushi nayi mai ciwo na kalli Baba nace ina ka ɓoyeta ne ? Cikin rashin fahimta yace wa ? Kafi kowa saninta me takeyi a gidan nan a wannan lokacin me tazo yi me take nema...? Baba yace wai wace ce ? Ga sunan Amisty a zuciyata amma ƙiri² ya gagara na faɗa a baki na , nace ita mana ita wace ce ? Kai ji nan na nunashi da ɗan yatsa nace tana ina karfa ka ɗaukeni mahaukaci nasan abinda nake ina ka ɓoyeta ne ? Amma Baba sai ya fara tofa min addu'a yana cewa aljannu sun kama uwar masu gida , a taimakamin da addu'a , inaji ina gani Baba yasa aka mayar dani mahaukaciyar ƙarfi da yaji , kowa yayi ta tofamin yawu , banda yanda zanyi dole nayi shiru amma wannan abun bai gogemin daga zuciya ba kuma saina bi salsala na gano abinda ke tsakanin Baba da Amisty , maganar Mamy ta dawo min a kaina kamar yanzu take faɗamin maganar... _Gaskiya an samu matsala shi kanshi Binna da yasan waye Hafsa a wurinshi daya haɗe zuciya ya mutu , itama bata san wayenta ba , shima Baban Hafsa baisan ke wacecen shi ba , kowa iskanci ² gaba ɗayan ahali sun zaman *KWARATA...*_ Lallai akwai alamar tambaya a wurin nan amma waye zai fiddo maganar daga cikin zuciyata ? Waye ? Waye zai taimakeni ne ? Wai wace ce ni ? Anya kuwa ni mutunce ? Mutane kuwa suna gani na ? Wai meke damun rayuwata ? Me ke damun kwalwata ? Wannan wane irin masifa ne ? Wace irin rayuwa nakeyi ? Ina mahaifiyata wai me Baba ya ɗaukeni ? Me nene ׳ na ƙarasa maganar ina ɗaga muryata wanda ina tunanin duk mutumin dake anguwar nan yaji irin hayagagar da nakeyi... Fashewa nayi da wani irin kuka nace tabbas ko wace ce ni da sanin wace irin rayuwa nakeyi amsar tana wurinki , kuɗin da Mamy ta bani na ɗauko na irga suna nan yadda ta bani su , maidasu nayi na aje , amma a zuciyata nayi alƙawari zan bautata mata tiƙuru kuma zan bata girmanta kamar yadda take so zan nemo matar nan kuma zan kaita zan bawa Mamy kuɗinta kuma zanci gaba da farauto mata duk wanda take so adalci ɗaya zatamin ta warwaremin sirrin rayuwata wannan shine kawai mafita.... Gari na waye nayi wanka yau ko inda Babana yake ban kalla ba kuma ban gaishe shi ba , makulin mota ta na buƙata ya bani amma sai yacemin wai anci motar a caca , kallonshi nayi nace ni bansan caca ba mota ta kawai na sani kuma sai ka biyata , Mamana ni kike cewa saina biyaki mota ? Kaine ka siyata ne ? Ai ko ban siya ba naci albarkacin haihuwarki da nayi , ka maidani ciki idan kaji munin maganar amma sai ka biya wannan motar babu gudu babu ja da baya kuma ba abinda ya dameni na baka daga yanzun nan zuwa bayan sallah isha'e ... Ina faɗin haka nayi waje abuna na barshi ta tagumi... Ina fita na shiga maƙota na nuna hoton matar da Mamy ta turomin a wayata nace da Allah ina neman gidanta , matar tacemin lafiya dai ko ? Nace lafiya qalau gwamnati tace a taimakawa masu ƙaramin ƙarfi wanda suke shan wahala a gidan aurensu , an ɗauko jaddawalin sunan ko wace macen aure da ƙaramin katin hotonta , sai naga ita kamar tafi kowa shan wahala shine nake so ita a taimaka mata da yawa , mata da kuɗi sai Allah kuma nayi haka dan in rubzata rami itama , ta haka zanji wane irin hali matar take nasan komai nata kafin na isa gidanta , ! Murmushi matar tayi tare da ɗaukomin kujera na zauna tace amma Sultana kunsan kuna da hanyar taimako shine mu ba'a saka sunanmu ba ? Jakata na zuge na fiddo damen "yan dubu² nace kin gansu nan kowa da sunanshi ai bansan kuna buƙata ba , itama banda tabbacin da zataje ko bazata ba , Tace zuwa kai , muje na rakaki gidan ta amma don Allah nima kisa a rubuta suna na don Allah , nace baki da matsala , saman ƙyaure ta ɗauko hijabinta tana ba yaranta umarni karsuyi mata ɓarna idan Babansu ya shigo ta shiga maƙota baza ta jima ba , Ta gaban gidan Amisty muka wuce gaba ɗayansu suna ƙofar gida hada Asma'u an saka kujeru na roba Amisty kuma tana ta tofi da hayaƙin sigari , yayin da wata tantiriyar "yar iska ke shan shisha tana murza hayaƙin cikin ƙwarewa da gogewa a cikin harkar , Har mun wuce naji bana iya haƙuri na dawo da baya , dai² Amisty na tsaya na ciro sigarin daga cikin bakinta na kasheta a saman goshinta , wata irin ƙara tayi saboda zafi ta riƙo hannuna na , da hannun damata na riƙe hannunta saboda dana haggun na kashe mata tabar sannan nace na rantse da Allah duk ranar da hasashena ya zamo gaskiya yadda na murje wannan sigarin a goshinki haka zan murje miki rayuwa.. Gaba dayan su sukayo kaina suna kee.... Nace heeee ku saurara na kaso daku sannan ku ɗauka domin yanzu babu sauran muradin ɗaukar fansa a zuciyata ina neman rayuwata ne amma idan kuka bari na ɗauki zafi anbaliyar wuta zan fara hattaranku domin ni fetir ce kuma sai cikin wuta nake amaina ! Kallon Amisty nayi nace ki fara addu'ar kuɓuta daga sharrina domin na yanzu ba irin na baya bane , na yanzu maciji zansa ya cinye kwansa { uba ne zai kwanta da "yar sa } ki kiyayi haɗuwa ta da ke domin abin bazai miki kyau ba , Sakinta nayi na kalli matar nace mata muje... Wuce su mukayi muka tunkari gidan matan , da sallama muka shiga , ta amsa mana cikin sakin fuska tare da shinfiɗa tabarma tace ku zauna sannunku da zuwa , Zama mukayi , baiwar Allah ta dama ɗan kokonta da ɗumamen tuwo suna ci ita da yaranta tana ma Allah godiya , amma dole tayi haƙuri domin Sultana ta shigo mata rayuwa , mijinta ya fito daga cikin ɗaki muka gaisa dashi ita kuma tabi bayanshi danyi mishi rakiya , wayyo bawan Allah kayi haƙuri Sultana tazo yanzu zan firgita maka iyalinka ka kasa gane gabanta bare bayanta... 01/10/2019 *JAMILA MUSA....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 47 Cikin sakin fuska ta shigo cikin gidan bayan ta dawo daga rakiyar mijinta , a mutunce ta zauna kusa damu saman tabarmar da muke aka gaisa a mutunce suka ɗan taɓa fira a tsakanin su da matar da muka zo tare mai nuni da akwai sanayya mai girma tsakaninsu , Bayan sun gama gaisawa da Maman Sadiq itace wacce muka zo da ita , ita kuma mai gidan naji Maman Sadiq in tana kiranta da Ummu Affan , Maman Sadiq tace tou Sultana wannan itace kike nema ko ? Murmushi nayi cikin jin kunya nace itace , kallona matar tayi tace lafiya dai ko ? Nace lafiya lau , Ummu Affan tace ya akayi ne ? Nace dama ƙungiyace gwamnati ta buɗe domin taimakawa matan aure marasa ƙarfi , an ɗauki sunayen wasu matan da kuma yawan "ya "yansu , mai girma gwamna ya bada izini dan gyara siyasar shi , shin kina da wata sana'a da kikeyi ko bakya da ? Ummu Affan tace gaskiya bana sana'ar komai , tou mi kike buƙata wannan gwamnati mai adalci ta taimaka miki dashi wanda zaki taimaki kanki da kuma iyalinki a cikin gida ba tare da kinsha wahala ba ? Tace Eh tou gaskiya idan dai san samu da gaske za'a taimakamin a siyamin injin markaɗe da kuma injin taliya domin shine abinda yayi ƙaranci a wannan anguwa tamu , tou amma bashi za'a raba kayan ko kyauta ? Nace haba wane kuma da gaske Ummu Affan ? Kinga ai ban taɓa zuwa gidanki ba sai yau , kuma duk mutumin daka gani a gidan ka ai da dalili , gwamnati tsaye take a kan ƙafafuwanta dan ganin ta taimaki talakanta , idan zaki amince ma ai sai a naɗaki shugabar ƙungiya ki tattaro mana matan aure waɗanda suke san taimako kinga ke sai ki zama shugabarsu idan yaso sai a baki kuɗin da kuma kayayyanki da gwamnati zata bayar ke kuma saiki riƙa raba musu ya kika gani ? Maman Sadiq tace to ni me za'a bani ne ? Nace ke kuma sai a naɗaki matemakiyar Ummu Affan amma ban sani ba ko mazajenku zasu riƙa barinku kuje wurin taro ? Dan naga duk lokacin da ake taro dubu goma ² ake bawa duk wacce ta halacci taron , Maman Sadiq ta zaro ido tare da cewa dubu goma ? Nace sosai ma idan ma gwamna yazo wurin taron dubu ishirin ake rabawa ga duk mace ɗaya ga lemu ga ruwan roba hada naman kaji ga abinci mai kyau kici ki ɗaurowa yaranki a leda... Ummu Affan tace dubu ishirin ? Nace sosai ma , tace idan dai taron bana dare bane wallahi sai muje ko ƙawata ? Suka kashe da Maman Sadiq , Maman Sadiq tace aini ko na daren ne wallahi ina iya zuwa uwar me ake baka auren ƙaddara auren ya zanyi ? Auren cida kai ? Kana gida zaune kullum kamar mai takaba babu wani ci gaban rayuwa sai tsofewa kakeyi kai baka mori rayuwarka ba kazo a wahala ka rayu a ƙunci ka koma a alakoro , nidai gaskiya ina zuwa , Nace tou ki bari muji ta bakin shugabar ƙungiya mana ? Na ƙarasa maganar a dai² lokacin dana zage jakata na fiddo irin kuɗin dana fiddo a gidan Maman Sadiq dubu biyar² naba ko wace a cikinsu nace idan kunyi shawara ku neme ni , gaba ɗayansu dubu biyar² ta ruɗasu dan yanayin fuskarsu ya nuna haka , ina basu nayi sallama dasu na wuce gida abuna... Fitar Sultana daga gidan sukaci gaba da tattaunawa yayin da Ummu Affan tace ni zan faɗawa Abbu Affan idan ya yadda , Maman Sadiq tace ki rabu dashi kinsan mazanmu baƙin ciki garesu su kaɗai suke so su ƙaru da sunga hanyar da zaka samu sai su nemi bulo da suminti su yaɓeta , kiyi shirunki kici gaba da sabgar gabanki gaki shugabar ƙungiya kinga idan aka baki kayan ki raba kina iya danne abunki kice ance za,a kawo amma har yanzu bai iso ba , idan kuma kina ganin zai hana taron sai a riƙayi a gidana , ni nafi ƙarfin mijina dan bai tsaremin ci 3 a rana ba bare ya juyani wallahi. Ummu Affan tace tou idan kuma akace an ganni a wurin taron fa ? Tsoki tayi tare da cewa banda kike banza ai niƙaf zaki saka waye ya isa ya ganoki ? Ey fa haka ne , tou Allah yasa karta juya tunaninta akanmu ta samu wasu daban , Maman Sadiq tace ai gobe idan Allah ya kaimu sai muje gidansu muce munzo gaisheta sai mu sake tuna mata muce karda ta manta damu , Ummu Affan tace haka ne zanzo , bara na bada a siyomin cefane yau a gidan nan miyar ja kowa zai sha... Dariya sukayi tare da cewa sai sun haɗu goben ta fita a gidan... A ƙofar gida na samu Babana yana zaune ya zagba tagumi ga dukkan alamu akwai abinda yake damunshi , gaskiya ina san Baba kuma wallahi yana bani tausayi bawan Allah , daga nesa dashi na tsaya nace mike damunka kake tunani kamar macen data rasa miji ? Ba tare daya kalleni ba yace ba kince saina biyaki motarki ba , nace idan nace sai ka biyani mota kuma sai ka zauna ? Ka tashi kaje ka nemomin kayata , nifa saidai kawai in siya miki wata tunda ba ɓacewa tayi ba nace miki a caca aka cita , Kiyi haƙuri Mamana , nace idan na ƙyaleka baka biya motar nan ba gobe gidan zaka saka shima a cinyeshi sai mu koma kuma muna raɓe² tunda cacar ta daina yinka basai kayi haƙuri ba ? Baba yace insha Allah nama daina cacar daga yau idan dai hakan zai miki daɗi , zanyi magana naji ƙaraurawar kaina ta buga da ƙarfi , addu'o'i naci gaba dayi dan na fara fahimta sheɗanci na yana cikin kaina , Ƙarfin hali nayi cewa daka hutama kanka ina faɗin haka nayi cikin gida , ina tunanin anya kuwa kaina ɗaya ? Koma dai miye Allah yana tare dani , Al ' Ameen durƙushe a gaban mai girma gwamna yana gulma , Allah ya taimake ka har yanzu mai gida bai rabu da yarinyar nan ba , kai kace in saka ido sosai kuma duk abinda yake faruwa a tsakaninsu in faɗa maka , tou wallahi wannan motar daya siya kayi mishi faɗan siyenta ita yama ɗauka gaba ɗaya ya bata ita , kuma hada kuɗi yace tasha mai amma kuɗin bansan ko nawa bane , Dady yace tou ai ya kyauta ni bansan yadda zanyi dashi ba , mai ɗaki shi yasan inda ruwa ke zubar mishi sai yaje yayi ta tarayyar da ita , ƙara duƙar da kai Al ' Ameen yayi yace Allah ya taimake ka a gani na bai kamata a zuba ido abarshi da ita ba ya kamata a sake dakatar dashi kafin abun ya wuce misali , Dady yace idanma gidansu zai koma da zama yaje ya koma tunda ba yaro bane shi ai yasan abinda yakeyi , Al ' Ameen yace ranka ya daɗe ai bazaka so a kaishi a baroshi ba , gara a tari abun tun wuri basai yayi nisa ba a kasa taroshi ba , Dady yace wai ba Dikko bane ba ? Yace Eh , yace tou ka ƙaleshi tasu ta haɗosu kasanshi baida gwani ka basu wasu kwanaki zakasha mamaki , ba haka Al ' Ameen yaso ba amma baida yadda zaiyi dole ya haƙura amma zai faɗawa Momy ita kaɗai zatayi maganin Sultana , daga nan shi kuma ya samu ɗiyar yayarshi ta shigo babu ɓata lokaci , Da daddare bayan na gama abinda nakeyi Alaji na kira { Abbu Afsar } ya kaini gidan Mamy tunda banda mota , motar da Dikko ya bani kuma ba yanzu zan fara hawanta ba akwai tanadin da nayi mata nasan duk ranar dasu Amisty suka ganni da ita sai sunyi hawan jini , Da sallama na shiga gidan , daga cikin ɗaki ta ansa min sallamar tare da cewa shigo Sultana har ta ɗauki miryata , nace tou ɗakin na shiga da sallama na samu wuri saman daka²n kujerunta na zauna , bayan na zauna na gaisheta cike da biyayya sannan na gaishe da wani mutum dake zaune yanacin abinci , kallonshi Mamy tayi cewa tou ɗauki abinci ka koma waje zamu tattauna da baƙuwa , yace tou Hajiya ya ɗauki abincin ya fita daga ɗakin... Bayan fitarshi nace Aunty kiyi haƙuri da Allah akan abinda ya faru dani dake jiya , nayi miki rashin kunya wanda haka bai kamata ba kuma ba tarbiya bane ɓatawa na gaba da kai ba , kiyi haƙuri kuma insha Allah bazan sake ba , jakata na buɗe na fiddo kuɗin data bani nace kuma gama kuɗinki na dawo miki dasu , maganar matar kuma zan kawota kiyi haƙuri bazan sake ba , Murmishi Mamy tayi tace ba komai Sultana ni dama banji komai ba , Allah ya haɗani dake kuma yasamin soyayyarki a zuciyata kuma nayi ɗamarar taimakonki in Allah ya yadda , Godiya nayi tare da matsawa gabanta zan ajiye kuɗin , tace ki barsu ki riƙesu , nace a , a Aunty ki barsu wallahi , tace bani nace ki barsu ba ? Bana so muna jayayya dake ki maida kawai a jaka , nace tou , jakata na buɗe na saka kuɗin , daga nan muka ɗan taɓa fira har take cemin kece kike mamakin ina da aure ko ? Murmushi nayi amma banyi magana ba , mutumin data fitar yanacin abinci shine ta kira , bayan yazo tace tou kinga mijina nan , Kallonshi tayi tana cewa wai mamaki take ina da aure , cike da biyayya yace Allah sarki , Mamy tace tou jeka tunda ta ganka , kamar sakarai kuma ya juya ya fita , a kunyace nace tou Aunty ya maganar baƙonmu na gobe ne ? Tace zaizo yanzu ma muka gama waya dashi , nace tou ya maganar yaran gidan Baba ƙarami ? Mamy tacemin komai ya tafi dai² karki damu amma ina ganin tunda ita Hamida tahau layi kawai mu fita safgarta , nace da ina so ta samu kuɗi , Mamy tace manta da "yan gidanku domin dama su tuni suna cikin sahun *kwarata...* tuni sun daɗe a harkar bariki tunda sune suke kula da kansu ki rabu dasu kowa yayi sabgar gabanshi , nace tou , Mamy tace yawwa akwai wani Uncle Al ' Ameen lokacin dana saka layin da kika bani yana ta kira babu ƙaƙƙautawa , gajiya nayi da nacinsa na ɗauka waya , bayan mun gaisa yacemin da Allah wannan wayar ta doughter inshi ce aka yadar da ita , ko ina zai sameni ya ansa ? Sai nace masa ni ba waya na samu ba layi na tsinta , Gaskiya da nayi niyar mu haɗu na bashi layin dan naji shima yacemin a katsina yake , abinda yasa na fasa yamin burga da cewa zaisa a kamani , nace masa shi ɗan uban waye a garin katsina shine yacemin daga gidan gwamnati , nace gwamnan ya tsaya maka ko waye ? Shine sai yacemin layin wayar matar ɗan gwamna ne , cika bakinsa yasa na saka number a wayata na duba ta whatsapp hoton Dikko ne na gani a d pn inshi , abinda na fahimta wato shi yaron Dikko ne , amma idan na tuna da labarinki kuma idan na fahimta Dikko shine kukayi faɗa a motarshi ! Me ya haɗaki dashi kuma miye tsakaninku ? Ajiyar zuciya na sauke tare da gyara zamana nace tou kila sato wayar tayi amma ita wannan ai bata taɓa aure ba , shi kuma mai maganar yace miki layin wayar matar Dikko ne , ko kin manta matar Dikko ta mutu ne ? Tace min haka ne kuma fa , nace gaskiya shiri ne abun , naci gaba da cewa yanzu wayau ɗaya zamuyi mishi shine kice masa ya turo miki lambar wayar da za'a iya samunta , domin akwai wasu tambayoyin da zamuyi ma mai layin idan ta bada ansa za'a bata wayarta da layinta wannan shine mafita , nayi haka ne dan na samu ta hanyar da zan turawa yarinyar nan vidion da zamu ɗauki ubanta , naƙi yadda kuma na faɗa mata nasan Dikko saboda gudun bita da ƙulli , bayan kuma Sadiya ta rasu babu wanda yasan Dikko yayi auren ... Miƙa hannuna nayi tare da cewa Mamy inga hoton , miƙomin wayarta tayi bayan ta kamomin hoton Dikko a wayarta tana cemin yanzu lambar wayar yarinya zansa shi Al ' Ameen in ya turo mana kenan ko ? Banajin ta domin hankalina da duk natsuwa ta ya tafi wurin kallon kyakkyawar fuskar mutumina , Wallahi bana gajiya da kallon kyakkyawar fuskar Dikko , yayi min kyau sosai a hoton kuma yayi hoton a cikin yanayin fushi ya ɗan soɓaro leɓonshi na ƙasa , yayi kyau sosai kuma shima Al ' Ameen in yasan hoton ya haɗu shi yasa ya sakashi a whatsapp inshi , idona ya cika da kwalla a zuciyata nace shine dai kayi fushi dani ko ? Kiran waya ya shigo a wayar dan haka na miƙawa Mamy wayar na miƙe ina cewa sai mun haɗu goben idan Allah ya kaimu , tace tou Allah ya kaimu ki gaida gida , banyi magana ba na fice buzum² zuciyata namin babu daɗi , A gajiye na isa gida , koda Alaji ya ajiyeni kawai ce masa nayi saida safe dan banajin daɗi kwata² kuma yaso na tsaya muyi fira na nuna masa bana buƙatar hakan , Ina shiga gida ɗakina na shige , saida na kwanta sannan naci gaba da tunanin Dikko , inayi ina hawayen baƙin ciki naci gaba kuma da kiran layinshi , har na gaji nayi bacci.... Washe garin ranar kuwa tunda safe Maman Sadiq da Ummu Affan a gidanmu suka bayyana , lokacin ko baccin safe ban tashi ba , dan tunda nayi sallah asuba na koma bacci , zuwansu ya tasheni , saida na fita na wanko fuskata da bakina sannan nazo muka gaisa dasu , bayan gaisuwa Maman Sadiq ta fara cewa dama cewa nayi bari muzo muji yaushe ne taron ? Shiru nayi tare da tsaresu da idanuwa dukansu , bayan na gama fahimtar wani abu daga garesu nace gaskiya shugaban ƙungiyar munyi magana dashi yacemin in ƙyaleku danshi baya san azo a samu matsala dan basaso a ɓatawa siyasar su suna , matan aure basa iya basu gudumawa yadda ya kamata akwai matsalar mijina yace karna fita , ko kuma ina zan bar yarana ? Ko kuma ni bana zuwa hotel ko kuma inane za'ayi taron ? Saboda jiya bayan na rabu daku naje wurinshi nayi masa bayani yadda mukayi daku bayan na nemi alfarma dan yaɗan ƙara muku wani abu saboda na lura iyali sunyi muku yawa gashi babu wata sahihiyar sana'a kuma yaran naku duk basu kawo ƙarfi ba , na samu dai yayi muku ƙarin budu goma tunda kune shuwagabannin ƙungiya , Sai yace na kawo mishi shugabar ƙungiyar ya gani shine nace ai matar aure ce , kinji faɗa ? Yace mi yasa kika naɗamin shugabar ƙungiya matar aure ? Bayan kinsan meeting na gaggawa zai iya tashi na kirata tacemin bata shirya ba ? Nidai ki mayar min da budurwa ko zawara , dakel dai na bashi haƙuri yace min ai matsalar matar aure wai kina iya zuwa kice aike bakya zama wuri ɗaya da mijin da ba naki ba , bayan dole zaku riƙa ɗan warewa ku tattauna abinda ya shafi ƙungiya , Ummu Affan taji zance kuɗi dan haka tace anyi ma aikin kishiya bare na uwar miji ? Daga magana sai mi kuma ? Nace kinsan wayayin maza basa so ayi ta wani dunkumewa a hijabi kinsan "yan boko basa san suga ana sha''ani da hijabi , Tacemin ai bansan wurin taron ko za'a nuna a talabijin ba , nace a , a ba'a sakawa a TV , Maman Sadiq tace tou Sultana ai sai mu tafi tare kice nice matemakiyar Ummu Affan , nace kibi sannu duk za'aje da kowa , tace a , a abari ya huce fa shine ke kawo rabon wani , nace aiko bai hucen ba idan rabon wani ya shiga tun yana kan wutar wani zaizo , kinga kuwa ai dole zakuci tare ko ? Tace haka fa , nace tou kudaije ku sake tunani shin zaku iya huɗɗa da maza ? Dan duk zama ɗaya ko wace zata tashi da dubu ishirin idan kuma gwamna yazo ko wace tana da dubu talatin idan kuma kin iya gogayya da maza zama ɗaya ma da hamsin zaki tashi , Zasu sake magana wayar Mamy ta shigo , nace tou anyi ma sa'a ga shugaban nan yana kirana ku jira muji me zaice ne ? Ɗaukar wayar nayi bayan mun gaisa da Mamy tacemin in shirya gata nan zata taho , nace tou , sai nace yawwa Alhaji maganar matan auren nan ina dai ƙara baka haƙuri yanzu haka ma muna tare dasu kuma sunyi alƙawari babu wata matsala , shiru nayi bayan wani lokaci nace dubu ɗari da keken ɗinki ? Allah ya ƙara arziƙi wallahi godiya suke , kallon juna sukayi suka ƙyarawa junansu ido , ni kuma na sake shiru bayan wani lokaci kuma nace kai Alhaji dani da ita zamuje har a gaban mai girma gwamna ? Tou muna godiya sai munzo goben , nagode ׳ , yawwa sai anjima na kashe wayata , Mamy kuwa cewa tayi kai wannan yarinya batajin magana , Ummu Affan har sauri take wurin cewa wai waye za'a ba keken ɗinkin da dubu ɗari ? Nace shugabar ƙungiya wai cewa yayi idan Allah ya kaimu gobe duk shuwagabanni zamuyi zama da mai girma gwamna shin zaki samu damar zuwa ko kuwa yadai ? Tace zuwa ma kai zanje , nace tou kidaiyi shiga mai kyau dan kinsan shiga gidan gwamnati bana yara bane , kiyi wanka ki ɗauro kallabi ƙarshen layi kizo muje amma kuyi shiru da bakinku karku sake ku bari wani yaji idan ba haka ba "yan zidaƙuiy zasu zo su anshe ma ɗan tama doki , Ummu Affan tace haba wallahi bama faɗa , nace tou yayi kuje sai mun haɗu goben , Maman Sadiq tace ai wallahi baku bari na wannan ai baƙin ciki ne taya ni na rakaki gidanta kuma a gabana aka haɗa komai sai ku tafi gidan gwamnati ku barni dan baƙin ciki ? Nace kema hada ke za'aje , tace tou yanzu naji magana , murmushi nayi tare da cewa kuje zan shiga wanka , Maman Sadiq ce ta fara fita ɗakin dan haka na riƙo hijabin Ummu Affan nace karki faɗa mata ƙarfe biyu na rana zamu tafi , idan ba haka ba keken ɗinkin nan da dubu ɗari tare zaku rabasu , tace bazan faɗa nace tou ku gaida gida , Kwando na ɗauka naje nayi wanka , bayan na fito na fara shiri ina saka kaya Mamy ta iso , bayan mun gaisa nake bata labarin yadda mukayi da matan aure , na ƙara da cewa kinga goben idan mukaje sai muyi ta zama ace gwamna yana meeting , ni kuma ina ci gaba da gyara hanya cikin sauran kwana shiddar daya rage har an kaita an baro ta , Mamy tace gaskiya ne , nace tou shi mutumin saiki faɗa masa idan munje muka tashi tafiya ya bata dubu hamsin kinsan ita mace da kuɗi ake tafiya da imaninta , Mamy tace haka ne karki samu damuwa nace dama banda ita , Bayan na gama shiri na ɗauki jakata da abinda nake shafawa mutane su tafi bacci , saida muka fita ƙofar gida nake tambayar Mamy ko Al ' Ameen ya turo lambar yarinyar ? Tace yace babu waya a hannunta sai dai ta Mamanta take amfani dashi kuma ya turo nace shikenan magana ya ƙare mata tacewa mijinta shege.......... 02/10/2019 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 48 Ni naja motar muka tafi Mamy kuma tana gefe na tana waya , dama ta shigo tanayin abunta kuma har yanzu bata gama ba , hanya na iba ɗoɗar saboda ta nunamin hanyar da zanbi da hannunta ta kuma nunamin kawai in tafi miƙe kar in kwanta , Munyi tafiya mai nisan gaske sannan Mamy ta gama waya , sawa tayi nayi parking ta anshi tuƙin motar mukaci gaba da tafiya har muka iso inda muka zo Mamy bata sake magana ba , Get in gidan buɗe yake dan haka muma muka samu damar antayawa daga ciki , tun kafin Mamy tayi parking Allah ya nunamin Al ' Ameen , haka nan naji gabana ya yanke ya faɗi gaba ɗaya sai guyawuna sukayi sanyi nama kasa fitowa daga cikin motar , ni kaɗai nasan Al 'Ameen Mamy bata sanshi ba , sannan kuma numbershi da ta saka a whatsapp inshi ba shine ba Dikko ne , Dogon nazari na shiga to me ya kawo Al ' Ameen wurin nan kuma ?Tunani nayi sosai firata da Mamy ta daren jiya ta dawo min , to duk yadda akayi yarinyar da mukayi faɗa da ita kenan tana da alaƙa da Al ' Ameen ? Na shiga tunani sosai amma na kasa fahimtar ya abun yake , Mamy kuma fita tayi daga motar tabar harabar gidan ta koma ƙofar gida , bayan wani lokaci kuma ta dawo ita da wata matashiyar yarinya shekarunta da kamanunta duk bana iya ganewa saboda ta saka niƙaf ta lulluɓe fuskata , ciki suka wuce ta barni zaune a mota kamar mage na dakon tsuntsu , Shiru² babu Mamy ba labarinta , ni kuwa sai sassada kai nake ƙasa dan bana so Al ' Ameen ya ganni , gashi ina so na fita nima na shiga amma dole banda yadda zanyi saboda Al ' Ameen zaune yake kuma baida alamar tashi , Har su Mamy suka gaji da daɗewarsu suka fito , yarinya bata shigo motarmu ba ficewa tayi Mamy kuma ta shigo mota taja muka tafi , saida mukayi nisa nace mata wai mutumin dake zaune a wurin nan shi kuma waye ? Ko gadi aka sashi ne ? Mamy tace ƙanin matar Baban yarinyar ne , jinjina kaina nayi sannan nace tou wace ce da niƙaf kuma ? Tace "yar uwarki ce da kika ce na farauto , Nace Hamida ? Tace ɗiyar ƙanin Babanki ce , dariya nayi sosai nace tsakaninki da Allah tace wallahi kuwa , tou ya akayi kika farauto ta da wuri haka ? Mamy tace wallahi ina zaune gidana Allah ya kawo minsu ita da ƙanwata , ashe ita ɗiyar ƙanin baban naki aure zatayi ? Mamy ta tambayeni nace mata Eh Safiyya ce zatayi aure , Mamy tace to ai kinsan "yan matan zamani sun saka kansu ƙarya basa haƙuri da abinda iyayensu sukayi musu , basa da gashin wance sai suce dole zasuyi kitso irin nata , Ƙanwata tacemin tana naima wa ƙawarta aiki a ƙarƙashi na , na taimaka wannan ƙawarta ce zatayi aure iyayenta basuyi mata wani abun kirki ba na kayan ɗaki , shine ta kawota wurina ko zan taimaka na ɗauketa aiki ita kawai talabinjin in bango da kayan sautin ta take so ta siya sai labulaye masu tsada ta gyara palon ta dan bata so ƙawayenta su raina mata gidan aurenta , Saina tambaye su bikin kwana nawa ya rage ? Shine tacemin wata 3 nace tou yarinya banda abinki wata3 taya zaki samu kuɗin da zaki sayi talabinjin in bango da kayan sautinta ? Kona ɗaukeki aiki na baki kuɗi da yawa a wata baifi na baki albashin 3k ba , kinga 3k sau wata3 ya kama 9k ba talabinjin ba ko labule bazai siya miki ba , Tacemin haka ne , tou bayan nayi bincike naji daga inda ta fito kuma naga kina nemansu da karuwanci ruwa ajallo yasa nayi mata tayin karuwanci bayan munyi ciniki dashi baban ƙawar faɗan taki akan zai bayar da dubu hamsin , nayi ² ya ƙara wani abu akai umm lusarin a haka ya tsaya , bayan mun gama ciniki dashi ya kafe kai da fata haka zai bayar , Kodai yane tunda na samu an farketa shikenan kinga ta tsaya zaman jiran talabinjin dan ubanta saidai kawai taji a salansa tamin hauka akan na bata kuɗi ga vidio na ɗauko ta ƙarasa maganar tana dariya , nima dariyar nayi tare da cewa yaro inya iya ruwa ai bai iya laka ba , dariya Mamy tayi sosai tare da tambayata meye ruwan kuma miye lakar ? Nace zancen sai wanda ya kwana a bakin gabi.... Mamy tace ina ne gabi kuma ? Nace wata matattara ce ta karuwai dake can wajen gari ! Haka dai mukayi ta taɓa fira har muka iso ƙofar gidanmu , bayan Mamy tayi parking ta fara kiran wayar Maman budurwar Dikko da mukayi faɗa da ita wacce bayan an ɗauki wayar naji Mamy tana cewa da Allah Momy ko Mardiyya tana kusa ne ? Eh tana nan Mardiyya kizo anyi miki waya , Tazo ta anshi wayar , bayan gaisuwa Mamy tace mata kin gane ɗiyar ɗan caca wacce kukayi faɗa da ita a motar saurayinki akan haryar ku ta zuwa Abuja ? Wacce bayan kunyi faɗan tayi zuciya ta barku a hanya ta samu mota ta dawo katsina kin tuna har kikace mata jahila daƙiƙiya kidahuma jaka kin tunota ? Tace Eh na ganeta ya akayi ne ? Mamy tace yawwa dama cewa tayi ki riƙe wayar Mamanki a hannu ki duba ta whatsapp zata turo miki saƙon ta tashi daga jahila ta koma ma... Da sauri na anshi wayar daga hannun Mamy nace. Mai ilimi barka da tsakiyar rana , barka dai ta amsa a daƙile , nace suna na *SULTANA ALIYU MUHAMMAD BINNA...* ina miki albishir da mummunan gani , salona ne yin albishir da mummuna ga abokin gaba sai kuma nayi albishiri da kyakkyawa ga masoyina , idan baki manta ba a waccan ranar nace mutuwa kaɗai zaki ki huta da ganin baƙin cikina , tou yanzu muka fara ki fara yininki da wannan anjima ma zan turo miki na kwanciya bacci kisha kallo lafiya...... Gashi nan zuwa , ki gani ke ɗaya idan uwarki ta buƙaci gani itama ki bata ta gani muna da maganin ciwon zuciya na hausa idan kina buƙata kallon Mamy nayi tare dayin dariya nace masu magani kasuwa ta buɗe .... Ina faɗin haka na kashe wayar , Mamy kuma ta ansa ta tura vidion data ɗauko kuma hada Safiyya a cikin hoton tana ta kwarara ihu saboda azaba yayin da Baban Mardiyya ke kwarara wani irin gurnani kamar kura tayo kamu , na raka vidion da voice note cewa mi yasa ya faɗa ruwa bai iya iyo ba ? Dariya mukayi dukanmu , saida muka tabbatar an buɗe saƙon kuma ya ɗauki lokacin da ya isa Mardiyya ta gama gani sannan naba Mamy Umarni data goge shi daga wayar mamanta , wato ta saka delete 4 everyone , bayan an goge duka hada voice note in da nayi nasa Mamy ta rubuta cewa ta kawo kuɗi masu yawa sai mu goge idan kuma ba haka ba ta tara a tashar yanar giza gizo. Bayan mun gama nayi sallama da Mamy na wuce gida akan sai mun haɗu gobe idan Allah ya kaimu , tace Allah ya kaimu lafiya , a gajiye na shiga gida dan haka ruwa na watsa kawai nayi sallar la'asar na kwanta ina hutawa. A ɓangaren Ummu Affan da Maman Sadiq kuwa fitarsu suka yanke shawara cewa idan na kaisu so ɗaya bazasu sake tafiya dani ba dan abinda suka fahimta zan riƙa ci musu aljihu , ma'ana idan aka basu zan riƙa ragewa ni inci da yawa su abasu kaɗai , ummm kuji ɗan adam butulu , Yayin da Maman Sadiq ke bayar da shawara cewa suyi wayau muna zuwa su lallaɓa su anshi lambar shugaban ƙungiyar sai suce masa idan ana taro ko yana nemansu karya kira Sultana ya nemesu kai tsaye , Ummu Affan tace gaskiya haka ne , dan kinga idan aka bamu dubu ɗari zata saka rai a cikin kuɗin ta, ga, tunda itace ta haɗani dashi zata jira na bata wani abu a cikin kuɗin , Maman Sadiq tace haka ne , ai tana nuna mana hanya mun gama da banzar , haka dai suka yanke shawarar su , Bayan sun rabu kuma kowa ya yanke shawarar saiya koro abokin tafiyarshi dan kowa yaci shi ɗaya , yayin da Maman Sadiq take tunani idan gwamnati ta bada mai da sabulu da magi da rigunan siyasa da ake rabawa zatayi samayya fiye da tunanin mai tunani , Itama a ɓangaren Ummu Affan haka ne dan har ta kasafa dubu ɗari yadda zata kaya mata tun kafin akai inda za'aje har sun yada Sultana a gefe , Ummu Affan ma tana tunanin yadda zata yada Maman Sadiq yayin da itama Maman Sadiq in take tunanin yadda zata kora Ummu Affan taci ita ɗaya ba tare data samu mai tayata ba. Washe gari kuwa tun 7:22am Ummu Affan ta bayyana a gidanmu , tasha wanka ta ɗauko jagira irin ta zamani sai baɗa ƙamshi takeyi anci jaka da takalmi masu kyau ta ida rufe wankan da wani irin tsadajjen gyale tayi kyau fa abunta , Tana zuwa ta ganni ban shirya ba , tacemin da Allah muje kafin wacce mayyar tazo , nace tun yanzu ? Tace Eh na samu na ajiye yaran a maƙota muje mu dawo , nace tou ki bari itama Maman Sadiq in tazo basai mu tafi tare ba ? Tace nidai karmu jirata da Allah ki tashi mu tafi , nace tou yanzu gwamna ma kanshi ai bai tashi bacci ba , tace haba ai da a jiraka gara kai ka jira , dan Allah ki tashi mu tafi , nace kai gaskiya ni ko shara banyi ba , kuma ban wanka ba , tace jeki kiyi wankan ni kuma sai in tattara miki ɗakin kafin ki fito , nace to amma mi yasa bakya so aje da Maman Sadiq , na tambayeta ? Danni dama bana so aje da ita , Ummu Affan tace kinsan mutanenmu da baƙin ciki sai kaja mutum inuwa ƙarshe kuma yakai ka rana , nace tou ba aminiyarki bace ba ? Tace wa ni ? Ta nuna kanta sannan taci gaba da cewa ba aminiyata bace ba kawai dai muna gaisawa cikin anguwa , nace tou ina kika cewa mijinki zakije da wannan safiyar ? Saida tayi murmushi tace tambaya kamar "yar jarida , ce masa nayi ƙawata bata lafiya za'a tafi da ita asibitin zariya zanje na dubata kafin su tafi , nace to misali idan mukaje bamu samu ganin gwamna ba fa sai akace gwamna abubuwa sun mishi yawa mu dawo gobe tou sai muka dawo idan zaki fita goben sai mijinki yace baza ki fita ba tou ya zakayi ? Tace ina ai dabara ma bazata ƙare ba , idan yace bazan je ba nasan hanyar da zan biyo masa , nace Allah ya taimaka ina faɗin haka nayi waje dan inje inyi wanka , kafin in fito wankan ta share ɗakin tas ta goge shi ta shinfiɗamin zani a katifa , ina fito na shirya a gaggauce ko kalaci banyi ba muka bar gidan kafin Maman Sadiq tazo. A napep muka je gidan Mamy , a ƙofar gida muka same ta cikin motar wani namiji ga kuma wanda ta nunamin da sunan mijinta yana zaune saman dakali yana kallon ikon Allah , gaisawa mukayi dashi na umarci Ummu Affan da ta shiga ciki na nuna mata gidan tare da cewa shiga muna zuwa , Tana shiga ni kuma nayi wurin Mamy muka gaisa na gaishe da baƙon nata , bayan mun gama gaisawa Mamy tacemin in shigo mana , baya na buɗe na shiga bayan na zauna muka ƙara gaisawa , Shiru na wani lokaci sannan Mamy tace Sultana ga mutumin ki yaga mutuniyarshi kalli iskanci da yakeyi leƙo ta nan ki gani , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya nace ni basai na gani ba , tace dan girman Allah leƙo kiga yadda bironshi ki rubutu babu takarda , dariya nayi sosai nace nidai bana san gani , Mamy tace haba so ɗaya fa zaki gani kawai , nace ba komai idan ya rubuta a takardar zan gani danni bana gane rubutu bisa iska , Dariya akayi gaba ɗaya , bayan wani lokaci kuma mukaci gaba da maganganu dai na sakin layi , bayan an gama mutumin ya tambayeni yadda mukayi da sabuwar sheƙar tashi , na goga mishi bayani duk yadda mukayi da su Ummu Affan hada Maman Sadiq duk ban ɓoye masa ba ! Yace babu damuwa ba hamsin za'a bata ba dubu ɗari zan bata yanzu sai ince mata gwamna yaje Abuja sai jibi zai dawo , kinga tana dawowa jibin ke Mamy sai ki bamu aron ɗaki mintuna 30 sun ishemu sau ɗaya kaɗai zan sa mata hannu kuma in bata kuɗi daga nan da kanta zataci gaba da zuwa ana mata singing , Shiru nayi sukaci gaba da firansu da Mamy , bayan wani lokaci kuma ya juyo yace Sultana kirata na sallameta tafiya zanyi na ansa da to tare da fita daga motar na nufi cikin gidan babu jimawa muka dawo tare da Ummu Affan bayan sun gaisa yace mata gwamna yaje Abuja wurin shugaban ƙasa amma zai dawo jibi idan Allah yasa muna da rayuwa , tace tou Allah ya dawo mana dashi lafiya... Ya ansa da amin tare da karkacewa ya fiddo bandir in "yan ɗari biyar² masu zafi ya bawa Ummu Affan da kwalin sabuwar waya yace kuma da akwai layi a ciki , ruɗewa tayi ta duƙe har ƙasa tana zabgaga mishi godiya tare da cewa Alhaji kasa min lambar ka a ciki ? Yace zan kiraki zuwa gobe yadda mukayi da gwamna zan faɗa miki , godiya tayi sosai kamar zata faɗa mishi sai ƙara godewa take godiya irin ta maroƙa , Wani irin kallo ya bita dashi yana lashe loɓonshi na ƙasa mai nuni da zan kashe wuta dake , Mamy kuwa fitowa tayi daga mota mukayi mishi sallama bayan muma yayi mana wanka da ruwan naira ya tafi ya barmu da ɗaurewa da ruwan godiya , Ai Ummu Affan kuwa cewa tayi bazata koma cikin gida ba lokacin da Mamy tace mu shiga ciki , juyin duniya nayi mu koma ciki tacemin tabar yaranta suna jiranta gida zata tafi , babu ko tayin kuɗin bare ta jira taji munce ko mun ƙoshi , haka ta saɓe abunta tabarmu da kuɗinta da wayarta tai tafiyarta , mu kuma muka koma gidan Mamy , gaba ɗayanmu a palo muka zauna inda Mamy take cemin Al ' Ameen ya kirata ya zageta fess dan Mardiyya ta kirashi ta faɗa mishi babu daɗi yace duk sai yaci uwarmu dagani har ke kuma ya faɗawa mai gida abinda mukayi ma matarshi kuma shi mai gidan yace duk sai an tattaremu an ɗauremu , ni kuma jin haka yasa na kira wannan mutumin na faɗa mishi tunda naga yana cikin gwamnati shima. Nace to yanzu ya ake ciki ? Mamy tace sai munemi mafita , nace shi Alhajin ya yace miki ? Mamy tace yace mu jira idan anyi ƙararmu zai ɗaukar mana lauya , idanuwa na zaro nace wane irin lauya kuma na shiga 14 nidai gaskiya bana san huɗɗa da koto ƙarshe akai mutum gidan yari ni banda wanda ya tsayamin , kawai saina fashe da kuka , Mamy tace haba Sultana tou miye abun kuka muna fa da bakinmu ki barshi ya yanko sammacin kiga yadda alƙalin zaiyi idan yaga lafiyayun katifu , Cikin kuka nace shikenan kullum mai makon katifa tahau saman gado sai gado yai ta hawan katifa nidai na shiga 3 , Mamy tacemin da Allah ke banza ce ki kwantar da hankali babu abinda zai faru domin na sake kiran yarinyar nayi mata baraza na da zan saki vidion a social media idan Al ' Ameen ya sake magana kuma ta kama kanta sosai , Dakel dai Mamy ta lallashe ni ta kwantarmin da hankalina ta sake bani ƙwarin guiwa , a gidanta na yini saida nayi sallah isha'e ta kawo ni gida , Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya , yanzu tsawon watanni 3 kenan da kafa su Ummu Affan da Maman Sadiq a ƙungiya kuma tun daga ranar dana kaita bata sake bi takaina ba , yanzu tama ƙwace sosai wuta kawai takeyi abunta a cikin anguwa , Mijinta kuma tuni ta wanke ta bashi dan tunda ya taso ya fara hayagaga ta kwantar da banza da asiri , Maman Sadiq itama tuni an mata register amma bata ƙarƙashin ƙungiyata tana ƙarƙashin ƙungiyar su Amisty ne , Safiyya kuwa ɗiyar Baba ƙarami ciki gareta , gashi biki yazo Mamy ta hana talabijin bare labulaye , fitina sukayi ta rashin lissafi akan rashin talabijin da labulaye , ga rashin lafiya ya taso ta gaba tun Safiyya tana boyewa har abu ya fara damunta dan haka ta faɗawa Mamy cewa bata lafiya wata 3 bata ga jinin al'ada ba , kai tsaye Mamy tace ciki gareki sai kawai kije ki zago bedi ki saɓa kisha , Safiyya kuwa ta gaji da ɓoye ²ta rasa ina zata soka rayuwarta gashi Mamy bata , bata sahihiyar mafita ba , dan haka kawai ta haƙura ta faɗawa mahaifiyarta komai bata ɓoye mata ba , da Mamy da mahaifiyar Safiya akaci gaba da musayar harshe tsakanin Mamy da Uwar Safiyya , tashin hankali naƙin ƙari , ni ko kada Mamy ta faɗamin cewa nayi ai ba danneta akayi ta ƙarfi aka ƙwata ba lokacin da Alhaji yake bata tana ta tanɗewa tare da wa suka tanɗene ? Taje can taji da abunta sakaran banza tunda bata iya shan gishiri ba , Ƙarshen film in dai mahaifiyar Safiyya zama akayi aka sasanta suka fuskanci juna ita da Mamy daga ƙarshe dai a asibiti aka wanke cikin tass , ta tashi babu talabijin ba labulaye babu budurci kuma babu albashin kuɗin aikin da alhaji yayi , bayan wanke ciki da sati biyu aka ɗaurawa Safiyya aure , kwanata biyu a gidan miji ya korota tare dayi mata shegen duka rashin samunta da baiyi ba a matsayin budurwa , itama daga nan ta yanki nata tikitin na shiga sahun jerin *Kwarata...* kuma buƙata na ya biya. Rayuwa mukeyi dai tsakanin ni dasu Amisty kowa naji haushin kowa , har yanzu ban sake ganinta da Babana ba , ta sake faɗaɗa ƙungiyarta da manyan mata masuji da duniya kuma duk matan aure sunfi yawa a cikinta domin yanzu kasuwar sutafi ja ba'a neman "yan mata kuma bata zawarawa akeyi ba matan auren dai , Ƙungiyar Amisty ta samu karɓuwa fiye da tunanin mai tunani ta samu kuɗi ta goge ta zama lafiyayyar hajiya , nima kuma inata bakin ƙoƙarina wurin ganin na kafa tawa ƙungiyar amma wallahi taƙiya daga ni sai Mamy a ƙungiyarmu , itama Ummu Affan ta kafa tata tana bada hayar matan aure ko a hanya ta ganni batamin magana saboda tana ganin tafi ƙarfina , al'amirin duniya ya fara bani mamaki dan haka na fara sanyi da rayuwata. Mazan kuma nabi su² amma da an fara ciniki dai kalmar ɗaya ce 1k gani ni kuma haɗama gareni bana iya iba kaɗan sai in kantamo dubu ɗaruruwa , zuwa wannan lokaci kuma al'amura sunjamin baya sosai tun ba'ayi nisa ba duniyar ta ajiyeni bani ake yayi ba lokacin ba nawa bane na wasu ne , kenan tun kafin na ajiye bariki tana neman ta ajiyeni , dan har alaji su Amisty sunyi gaba dashi ! Ina cikin wannan tararrabi Allah ya kawomin wani zazzafan matashi maiji da kanshi ga kuɗi ga gayu amma matsala ɗaya wallahi mummuna ne , Naji daɗin zuwanshi kuma mun antaya soyayya shi ya wankoni daga talauci yayi ta yayyafin ya cidar hadarin naira da anyi tsawa saidai kiga yana ɓarin naira , cikin ƙanƙanin lokaci nima na farfaɗo na fara dawowa hajiyata , Naci gaba yanzu har hotel nake kwana amma matsalar ɗaya abunda na fuskata bayada alƙamin rubutu , kullum haka zanje in kwanta salaf in taso babu wani ɗan shafe² ko ɗan lashe ² ko ɗan tsotse² idan kuma na tashi tafiya haka zai bani kuɗi masu sa mutum ya kasa gano hanyar gidansu , abun a dameni dan haka na tambayeshi nace shin wai kai bakajin kanajin sha'awata ? Saidai yayi dariya yace yana da sha'awa in kwantar da hankali ranar hawa na zuwa , Ina kwance ina bacci a saman gadon hotel nayi guda² ina sararawa abuna idanuwana a rufe amma ba bacci nake ba , a tunaninshi nayi bacci dan haka ya tashi saf² ya fita daga bedroom in , wallahi haka nan naji tsikar jikina ta tashi jarr hankalina ta tashi ƙararrawa ta doka hayani ta riƙa tashi cikin kaina , da sauri na sauko daga saman gadon nayi bakin ƙofa , Da sanɗo na shiga palon ya bada baya yana waya cikin harshen turanci , hakanan na tsargu dan haka zuciyata tace kiyi masa vidio ko recording kamar yadda kika saba wannan da ganinshi baida gaskiya , da sauri na latso recording na fara ɗauka saida ya gama wayar tas sannan ya juyo da wata irin siffa mai ban tsoro dasa firgici tunda nake duniya ba taɓa ganin irin siffar ba , dakewa nayi banji tsoro ba kuma ban firgita ba naci gaba da addu'a nima na tsareshi da ido , A hankali siffarshi ta dawo siffarshi da nasanshi da ita , murmushi yayi yace ke matar aure ce ? Na girgiza kai da a , a , yace tou ki wuce daga yau karki sake dawomin matan aure muke nema , murmushi nayi tare da cewa ngode kuma na barka lafiya , ina faɗin haka nayi gaba abuna ko ciki ban koma ba bare na ɗauko gyalena , saida na fita daga ɗakin na ruɗe na firgice na kwarara wani irin ihu mai tada hankali , Hmmm _Ƙalu bake gareku matan aure......_ 04/10/2019 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 49 Gaba ɗaya na firgice na fita hayyacina kururuwar da nakeyi ta karaɗe kaf girman hotel in , hayagagata ya jawo hankalin mutane akayo wurina ana lafiya ? Duk wanda na gani sai inga fuskar mutumin nan gareshi wayyo Allahna na shiga 3 🙆🏻 na lalace shikenan mutuwa zanyi na bani ׳ na ƙarasa maganar tare da faɗuwa ƙasa ina burgima. Baiwar Allah lafiya ? Meke damunki ? Shine tambayar da mutanen da suka zagaye ni sukemin amma maimakon naji maganarsu sai naji muryar mutumin cikin muryar tsoratarwa da firgitarwa yana cemin da hantarki da ƙodarki ko zuciyarki wanne kika bamu.... Da sauri na dafe cikina na tallabo saitin zuciyata amma har yanzu wayata na riƙe ram a hannuna , cikin kuka nace wallahi bazan bayar ba , nawa ne ni ɗaya , cikina ne da zuciyata hantana da ƙoda Allahna ya bani ba wani ba , kuma ubangiji bazai baku damar rabani da ko ɗaya ba , wata irin gigitacciyar dariya akayi tare da cewa kina nufin kinci kuɗinmu a banza ? Tou wannan kuɗin ki sani jinin wasu ne da wasu sassa na jikin ɗan adam dole ki bayar da naki kema domin a bawa dodo ya bamu kuɗi zuciyarki zata shiga kwarya , bankwana da duniya sai wata rana.... Gaggaɓewa akaci gaba dayi da dariya data gigitani a karo na biyu , addu'o'e naci gaba dayi da ƙarfi idan ina addu'a bana gama wata saina saketa na kamo wata , dai najin sautin muryar dariyar nayi sai sautin kuka har zuwa wannan lokacin ban daina addu'a ba , bayan wani lokaci kuma na dainajin sautin kukan gaba ɗaya... Da sauri na miƙe ko jikina ban tsaya kakkaɓewa ba nayi gaba , mutane suka bini da kallo yayin da wasu ke tunanin ko ina da taɓin kwalwa ne , da gudu na fita daga hotel in , ina na fita na samu napep sai gidan Mamy amma har yanzu hankali na baya jikina gaba ɗaya a ruɗe nake , napep na tsayawa na fita da gudu nayi cikin gidan Mamy , bata nan sai yara na samu nace musu ina Mamarsu ? Sukacemin yanzun nan ta fita tace idan kinzo ki kirata , Jikina yana ƙyarma na fara laluben wayar Mamy babu ɓata lokaci ta ɗauka , gaisawa mukayi nace mata kina ta ina haka ne ? Sunan hotel in dana baro ta faɗamin tare da cewa wani sabon sauna ne na samu ki jirani na wankoshi cikin mintuna kaɗan zan dawo , kaina ya juya a gigice nace karki je , ki dawo hotel in nan akwai wani gahurtaccen matsafi daya bayyana karki shiga ɗaki ki dawo , Mamy tace wane ɗaki ? Nace ɗakin dana shiga wallahi matsafi ne karki shiga ki dawo akwai zama na musamman , Mamy tace tou lamba nawa ne ɗakin , Da sauri na dafe kaina duniyar ta riƙa juyamin kamar nahau shillo mai wanawa , gafa lambar ɗakin ina gani a idona bana iya faɗa dan na iya lissafin lambobi tunda dasu nake sarving numbobin mutane a cikin wayata , ganin na kasa faɗa kawai nace .... Ki dawo........... Na faɗi ki dawo cikin wata irin murya hawaye suka gangaro daga cikin idona ina cewa nidai kawai ki dawo matan aure yake nema ko wane ɗaki bana so ki shiga ki dawo Auntyna bana san na rasa ki adaidai wannan lokacin ki dawo dan Allah na ƙarasa maganar ina durƙushewa ƙasa naci gaba da kuka , amma duk wannan maganar da nayi sam Mamy bata jini ta riƙa hello , hello idan kina jina kawai ki jirani , tana faɗin haka ta kashe wayarta , Da gudu na fita daga cikin gidan , mai napep in daya kawoni shi nace ya maidani inda ya ɗaukoni dan dama ban sallameshi ba , nace kayi gudun bala'e ka kaimin motar nan maleji karka tsaya kuma karka kauce ina so kawai na buɗe idona na ganni a hotel in nan kamar kyaftawar ido , Gudu mai napep yakeyi amma ce masa nake ya ƙara ina kiran wayar Mamy amma ba'a ɗauka , saidai na daki napep in nace wuta mai mota nace karka tsaya kaucewa ababen hawa muje kayi tuƙin nan kamar babu koma bisa titin nan saimu , gudu yake balbalawa na tashin hankali amma gani nake kamar baya tafiya , wayar Mamy kuwa saidai ta ƙari ringing inta ta tsinke amma ba'a ɗauka har muka isa hotel in ban daina kiran wayar Mamy ba kuma bata daina shiga ba haka kuma babu wanda ya ɗauka... A harabar hotel in naga dandazon mutane , da gudu na tunkari inda suke kamar wata mahaukaciya na riƙa ture mutane , hasahsena ya zama gaskiya domin Mamy ce yashe a ƙasa mutane sun zagayeta ga "yan sanda har sun rigani hallara a wurin , jini ne kawai ke ɗiga daga cikin idon Mamy kamar babu ƙwayar idonta dan baka gani hasken idon ko sai jini dake ɗiga ɗis ² , A wurin mutane ke cewa yanzu wata ta fita itama tana ihu ita Allah yasa tana da sauran shan ruwa a gaba , goge hawaye nayi a zuciyata nace ba ni suke so ba matan aure , mutane sukaci gaba da cewe lallai akwai abinda yake faruwa , jiki a sanyaye na na isa gaban Mamy nace Aunty na ƙarasa maganar ina mai kamo hannuwanta , bata iya magana ma kwata² dan haka na rungumeta naci gaba da kuka , bayan "yan sanda sun gama bincikensu kuma basu samu wata sahihiyar sheda ba haka aka ɗauki Mamy da wayarta akayi asibiti da ita... Nima napep na koma nace masa mubi bayansu. Bayan mun isa asibiti "yan sanda suka danƙamu a hannun likitoci babu ɓata lokaci aka shiga duba Mamy , tashin farko dai likitocin sun tabbatar da babu idon Mamy kuma har yanzu jini bai gama fita ba , ni kuma hankalina yafi karkata akan wayarta dan haka naje wurin ɗan sanda nace ranka ya daɗe wayar zaka bani na kira Babanmu , Kallona yayi sama da ƙasa sannan yace wace ce ke ? Nace ɗiyar mara lafiyarce ni , dan bana nan na dawo gida "yan uwana sukace Mama tace ta fita amma idan na dawo na kirata , bayan na dawo suka faɗamin na kirata mun fara magana da ita a waya daga baya kuma saita nunamin batajina , ka duba jerin kira kuma zaka gani dan daga baya nayi ta kiranta bata ɗauka ba , Miƙomin wayar yayi domin wayar Mamy ba'a buɗeta sai an zana pattern yace buɗeta tou tunda kince ta Mamanki ce , lafiya lau na zana na buɗe wayar domin kullum a gabana take zanawa kuma baida wahala , bayan na buɗe ya duba yaga kiran da nayi mata kamar dai yadda nayi masa bayani , yana cikin dubawa kira ya shigo dan haka ya ɗauka , bayan gaisuwa naji yace muna genaral , yana faɗin haka ya kashe ya miƙomin wayar , Babu wani daɗewa mijin Mamy ya iso asibitin , yasha kuka kamar ranshi zai fita duk iskancin da Mamy ke zubawa baya gani yana san matarshi , jikin gadon Mamy ya matsa cikin kuka yace Mamy Allah ya tsinemawa wanda yayi miki haka , Allah ya baki lafiya mata ta ubangiji yasa ki warke , A wahalce Mamy tayi murmushi ta lalabo hannun mijinta tace kayi haƙuri mutuwa zanyi amma ina roƙonka daka yafemin , cikin kuka ya rungume Mamy yace Hajiya baza ki mutu ba wallahi baki mutuwa , Mamy tace naji amma kawai kace ka yafemin , cikin in'inna yace na , na na ya.... Ya fe miki , godiya tayi masa tare da cewa naji muryar Sultana tana ina ? Yace gata nan hajiya ya kamo hannuna ya haɗa da nata , Umarni ta bashi cewa da Allah ya fita zatayi magana dani , cike da ladabi ya fice daga ɗakin , Sultana ta kira suna na , nace na'am tace dubamin babu kowa a kusa dani ? Babu Aunty na faɗa cikin girmamawa magana ta farayi bayan na tabbatar mata da babu kowa a wurin :• Sultana ta kira suna na , nace na'am Aunty , tace tou ki saurareni dakyau , nace inajinki Aunty , Mamy tace kinga whatsapp in nan da kike ganinta ? Wallahi ba ƙaramin haukata mata takeyi ba , shiru nayi ban sake magana ba naci gaba da sauraren Mamy . Aurena biyu a duniya , ina da shekara 39 akamin auren farko bayan nasha gwagwar mayar rayuwa , iyayena ba masu kuɗi bane suna dai da rufin asiri na ci da sha da sutura , mahaifina ba ɗan kasuwa bane kuma ba wani shahararen ɗan boko bane ba , yana aiki a ƙarƙashin kamfani wani attajiri , Matan Babana biyu daga mahaifiyata sai abiyar zamanta , muna da yawa sosai mu "ya "yan babanmu , cikin hukuncin Allah matan gidanmu suna auren mazaje masu rufin asiri , duka matan gidanmu saida aka aurar dasu kaf har ƙanne na ni ban samu mijin aure ba , Na tayar da hankalina sosai domin auren nake so ido rufe amma ban samu mai aurena ba , abin ya dameni sosai saina ma daina fita kwata ² kullum ina gida ko a familynmu daina shiga nayi domin na ganɗame sosai saina farajin kunyar shiga mutane ko baƙi akayi gidanmu sai in ɓoye , Ina wannan ɓoye ²n ne Allah ya kawomin Bello a rayuwata , Bello abokin Yayana ne duk duniya baida aminin daya wuce Bello shima Bello baida aminin daya wuce Yayana , kowa yana san kowa kuma kowa baya ɓoyewa kowa sirrin junansu , sun yadda da juna fiye da tunaninki domin dai Bello zai iya tarawa da matar Yayana shima Yayana zai iya tarawa da matan Bello , Tunda Allah yasa ya ƙyalla idonshi ya ganni ya liƙemin , nasan baƙin halin Bello sosai nasan illarshi kuma nasan miyagun halayyarshi dan haka koda ya furtamin kalmar so ban ansa ba nace bana sansa , shine ya faɗawa Yayana yana so na amma nace bana sansa , shine Yayan nawa yazo ya sameni yayi min kaca ² , nace ni bashi ne bana so ba halinshi ne bana so , kuma kaji tsoron Allah kai kanka baza ka iya bashi auren "yar uwarka da kuke ciki ɗaya , Yaya yace tou ko kinso ko kinƙi sai kin auri Bello idan baki aureshi don Allah ba zaki aureshi dan dole , saikin nemo Bello da kanki , yana faɗin haka yayi gaba abunshi , Tun daga wannan ranar sukayi ta kusatsamin asiri na firgice na fita hayyaci na da kaina nake nemo Bello , idan na fita ban ganshi ba ko zankai gobe ban dawo gida ba saina ganshi hankalina zai kwanta , A taƙaice dai Bello na aura aurena na farko , ranar da aka kawoni gidan Bello bayan mutane sun watse shima Bello ya shigo da abokanshi da suka rako ango ɗakin amarya kamar dai yadda akeyi , Kowa fatan alkairi yaimin da addu'ar zaman lafiya , bayan an gama Bello ya bayyanar min da abokanshi kowa ya faɗamin sunanshi , saida yazo kan *BINNA...* ya dafashi cike da soyayya yace kinga wannan nace Eh yace Binna kenan Bello baya rayuwa saida Binna kamar yadda mutum bai rayuwa saida lumfashi , ina san Binna fiye da yadda nake san kowa a duniya , Binna nawa ne nima nashi ne , murmushi Binna yayi cike da izza amma baiyi magana ba , gaskiya Binna ya shiga zuciyata kuma duk duniya ban taɓa ganin wanda nake so a daidai wannan lokacin ba kamar Binna , Sun ɗan daɗe dai suna fira amma har akayi firar aka tashi Binna bai saka baki ba har suka gama suka tafi , bayan Bello ya dawo daga rakiyar su yacemin na tsani Binna na nuna miki shi domin ki ganshi , hawaye ya cika a idon Bello yace tsinan Allah kawai ranar da zan zama ango Binna ya ɗauke budurci ya gudu , saboda kawai nayi ma yarinyar gidan da suka ɗaukoshi a bakin titi suna taimaka mishi , Nayi alƙawari saina ƙafa babban tarihi a zuciyar Binna saina tagayyara mishi rayuwa saina zama silar rushewar kaf ahalinsa wanda suka gabata da wanda basu zo ba , saina jefa ƙiyayya mara gogewa tsakaninshi da "yan uwanshi da suke uba ɗaya , nayi alƙawari kuma babu gudu babu ja da baya ko duniya zatashi saina cika muradina , Wani irin nishin wahala Mamy tayi har yanzu jinin bai daina ɗiga ba , a wahalce taci gaba da cewa.... Bayan Bello ya gama alkaba'inshi ya hawo gado babu wata sallar godiya ga Allah babu wani abunda ya shigo min dashi irin wanda ango yake zuwa ma amarya dashi a daren farkonsu , haka ya hayeni yaita sassaƙa kamar mai faskare ya samu babban bedi , haka kuma babu wata addu'ar tarawa da iyali , Sam banajin daɗin zaman aure da Bello dan na fahimta mugun atsabibi ne , babu sallah bare salati haka kuma bai yadda da ƙaddara ba komai dai malamin tsibbu , ina haƙuri dai ina zama amma sam bana sansa dauriya ce kawai , Tun daga ranar da aka kawoni ina amarya ban sake ganin Binna ba saida yazo faɗama Bello an haifeki , Duk ƙudirin da Bello yayi akan Sultana da burin mahaifinta akanshi ta faɗawa Sultana , tace wannan shine silar abinda ya rabani da Bello domin na nuna ban yadda ba ya aiwatar da ƙudirinshi akan Binna ba domin gaskiya ina sansa kuma bazan bari a cutar masa da rayuwa ba ,abun yayi ma Bello ciwo dan shine ya sakeni , Bayan mun rabu nayi ² Binna ya aureni yaƙiya ina sansa kuma ina sha'awarshi dan haka nayi masa tayin kaina kuma Allah ya taimakeni ya ansa , da sauri na runtse idanuwana , Mamy bata gani na dan haka taci gaba da cewa kullum ni nake isko Binna ko ya nunamin baida buƙata sai nayi yadda za'ayi ya kwanta dani danni kaɗai nasan yadda nakeji idan ina kwance dashi , Har na shekara 2 ina zawarci Binna fa ya kame akan bazai aureni ba , dole na haƙura na samu miji nayi aure , tunda nayi aure na daina zuwa wurin Binna , ina zaune da mijina lafiya babu abinda na nema na rasa , saidai zaman kaɗaici yana damuna , wannan dalili yasa na saya babbar waya na fara chating.. Banda friends sosai a whatsapp dan haka dana duba naga wanda ke online saina dameshi da surutu , idan nayi magana sai mutum ya ɗauki tsawon lokaci bai bani ansa ba , na gaji dai nacema wata ƙawata wai sai inyi magana kuyi kamar baku gani ba , dariya tayi sannan tacemin haba hajiyata yaushe rabon duniya da ayyaraye , ni bana cht da mutum prvt ina can group inmu na mata masu duniya , wayayyin mata masu aji masu faɗa a gidan aurensu aji ina ƙaruwa ina zan tsaya saurarenki. Koda na tambayeta me ake koyawa a group in sai tacemin bara tayi adding ina gani ya kori ji , nace tou , bayan tayi adding ina ta gabatar dani tare da tura hotona , kowa dai yaimin fatan alkairi , a hankali dai nake rayuwa da "yan group in ina fuskantar su , Basu da aiki sai turo style na ɗinki , idan sabuwar atamfa ta fito sai an turota , wasu takalman yayi masu zafi suma a turo jukkuna gyaluluwa "yan kunne tsarƙa , bawai na siyarwa bane ba , a , a sune dai na zamani su matan idan suka gani zasuje kasuwa su siya , Mace kuwa idan tayi lafiyayen girki saita gama tsara abunta kaf a tebirin cin abinci sai ta ɗauko hoto ta turo a group , idan wanka kikayi kika kai ƙarshen adaka zakiyi hoto ki turo matan group in suna zugaki , Shin da Allah mace ta dafa lafiyayyen abinci komai yaji banda bala'e kina kallon yadda naman kaji ke wali ga lemuna masu kyau da tsada an jera ki faɗamin ke kinyi ɗan wake da miyar ƙuli ko kinyi zazafen tuwo kin ɗauka ki tura ? Mace ta share ƙaton fili ga filawowi ta ɗauko hoto tasha kafirarriyar shadda ko wani ƙaton leshi ko super ke kuma mijinki baida halin ɗinka miki super atamfa rober yake da halin ɗinka miki kuma ita gareki shin kin ɗauka hoto ki tura a group in mata masu duniya ? Banda ko sisi amma ina da style na ɗinkuna a wayata yafi dubu , duk wata jikkar da ake yayi ko atamfa sabuwar fitowa tana cikin wayata , banda sisi mijina baya dashi na manta da hatta yatsun hannuna ba ɗaya suke ba , duk lokacin da wata ta ɗauko hoton palonta ta turo sai ince ya zanyi na maida nawa haka ? Kafin wani lokaci na fara tadawa mijina hankali cewa duk mazan duniya suna kishin matansu suna musu sutura sun wadatasu da komai amma duk lokacin da nayi maka magana sai kacemin kai babu , Idan yayimin nasiha ya bani haƙuri sai kuma in haƙura , kullum dai abu ci gaba yakeyi dan haka na fita daga group in , amma kash ina fita admin in ta biyoni prvt tacemin taga nayi left lafiya ? Ban ɓoye mata komai ba nace gaskiya ina ganin kayane hankalina yana tashi zuciyata tana min wasi² kuma mijina baida kuɗi shi yasa na fita , dan na lura idan aka turo kayan yayi duk wacce ta sawo idan ta ɗinka hoto takeyi ta turo kowa ya gani , Tacemin bara in kiraki nace tou , babu ɓata lokaci ta kirani bayan mun gaisa tacemin duk wanda na gani a group in nan matan aure ne , kuma yadda nake tunanin mijina ma baida hali yafi na wasu a cikin group in , kinsan yanzu ana zamanin rayuwar "yanci kina da aurenki amma kina da abokinki a waje , wanda zai ɗauke miki duk wata hidima taki , "Yanci shine babban mutunci da zaran kin rasashi taki ta ƙare , cikin mintuna biyar kacal abokinki zaiyi ya miki abinda mijinki da kike aure bazai miki irinshi ba , yanzu an daina duhun kawai rayuwar ƙyaunci ta gushe , ki riƙe babbar waya kici mai kyau kisha mai kyau ki ɗaura mai kyau ki gyara muhallinki babu wanda yaji kuma babu wanda ya gani , Nace tou idan kuma mijina yace ina na samu kuɗin da nake wannan hidimar fa ? Tace dama ai kafin ki shiga zaki rufe banza a tulun ƙasa zaki riƙa juya rayuwarshi kamar remote sai yadda kikace dashi babu shi babu magana kuma idan "yan uwanshi sukayi mishi magana tou fa ko uwarshi ce zai iya rabuwa da ita akanki , nace tou abokinki me ake bashi yake bada kuɗi haka kuma a ina zan samu abokin , tace abinda zaki bashi yana nan jikinki samun shi kuma nine zan haɗaki dashi , nace tou zanyi shawara , Sati ɗaya ina neman mafita kuma kullum saita kirani ta ƙara bani shawara , ƙarshe dai na haƙura nima na antaya a duniyar kwaratanci , social media tana da amfani tana gyara amma illolin sunfi gyaratanta yawa kusan irin mutanen da kuke huɗɗa dasu , tari tayi sosai cikin yanayin wahaltuwa tace ki riƙe wayata a hannunki akwai wata ƙawata dana haɗa da Bello akwai wasu maganganu da nayi da ita akanki kuma na haɗasu domin ina so duk wani shiri nasa ya lalace ƙarshenshi tazo , naso na kafa rayuwa mai inganci a gareki amma lokaci ya ƙuremin , cikin kakari tace kuma Baban Hafsa da Baban Amisty da Binna ...... Daga nan lumfashin Mamy ɗauke , Shikenan Mamy tata , ta ƙare ina da tulin tambayoyi da zan mata amma ta tafi inda bazan sake ganinta har abadan duniya , me mutumin yayi mata ? Ya akayi aka ƙwaƙwale idonta ? Ina ƙawarta data haɗu da ita a sanadin whatsapp ? Ya akayi Babana bai aureta ba ? Cikin abokan Bello waye Yayan Mamy a ciki ? Ina iyayenta suke ? Wayyoni Allahna na shiga 3na , tou wai meye take san faɗamin data kira sunan Babana dasu iyayensu Amisty ? Wai ya rayuwata take tafiya a taltala ? Wani irin juyi kaina yayi na saki wani irin gahurtaccen ihu tare da faɗuwa ƙasa somammiya , Ihun Sultana yasa mijin Mamy ya shigo da gudu , da taimakon likitoci aka samu aka farfaɗo da Sultana daga duniyar sumar data tafi , a lokacin dana farko har an fita da gawar Mamy waje an sakata a mota , Mijin Mamy ya bani wayoyi duka domin duk firar da mukayi da Mamy yaji komai , yace min kije gida sai Allah ya kaimu gobe za'ayi jana'izar Hajiya , mai napep in da kika zo dashi na sallameshi kije kar a nemeni , Yana faɗin haka yayi gaba , kamar wata doluwa haka na riƙa tafiya irinta sakarkari har na fito waje , napep na samu na faɗa masa inda zai kaini , har na iso gida kuka nakeyi haka na sauka daga napep in nayi cikin gida abuna , shima Babana ya sallameshi ya tafi , Wanka na farayi har na fito kuka nakeyi , zuwa wannan lokacin kuma labarin mutuwar Mamy ya fara zagawa a cikin gari , har su Amisty sunji labari kowa so yake yaji dalilin da yasa aka ƙwaƙwalewa Mamy idanuwa , bayan na fito wanka ina zaune a gefen katifa na kunno recording in da nayo bana gane komai amma fa ga murya nan lafiya zaw kanajin komai , aje wayar nayi na fita nayo alwalla ina dawowa na saka kayana ban shafa mai ba , hijabi na saka nayi sallah la'asar da ban samu yi ba ina gamawa na maida magrib bayan na sallame na ɗauki alkur'ani naci gaba da karantawa dan har yanzu bana cikin natsuwata ga tsoron da naji daga farko ga kuma mutuwar Mamy da aka zare ranta a gaban idona .... Tsaye yake gaban madubi yasha ƙananan kaya cikakken namiji kenan tsawonshi ma kanshi abun burgewa ne , sanye yake cikin farar riga da bakin wando rufaffen takalmi baƙi yasha stocking da bakin belt ƙamshin turare mai daɗi da dasa farinci mai jefa mutum yanayi marar gogewa a rayuwa sai tashi yake , murmushi yayi yayin daya fara sharce gemunshi yana cewa , sa'a da kanta take kwankwasa mana ƙofa ga duk nasarar namiji mace ce jigonshi , cingom yasaka a bakinshi saida ya ɗan tattauna yace gani nan zuwa gareki An matana...... 05/10/2019 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 50 Cike da farin ciki ya juyo , amma me ? Sai yaga *Jiddah* tsaye ta zarge hannuwan ta , wayoyinshi ya ɗauka sannan ya tunkaro ta dan ta hanyar da zaibi ya wuce ta tsaya , cike da kissa tace haba Yaya daga dawowa kuma ina zakaje haka da daren nan ? Inda raina yake so zanje , haba Yaya gaskiya haka an shiga haƙƙina , kallon raini wayau yayi mata tare da cewa a haba ? Umm gaskiya ina so mu kwanta mu huta duk gajiyar jirgi tana damuna , ta ƙarasa maganar tare da san kwanciya a jikinshi , zamewa yayi da sauri ya karkata ya fice daga ɗakin. Ni kuma bayan nayi sallah isha'e tunanin duniya yazo ya tokaremin zuciya , ikon Allah wato ita rayuwa haka take , Mamy bata taɓa tunanin mutuwa ba kwata ² a "yan wa'annen lokuta , hawaye ya gangaromin daga cikin idona nace shikenan anyi zamaninta an gama , duk saɓawa ubangiji da tayi saboda samun duniya kuma Allahn ya yaddar mata ta samu kuma ta tara , amma ta tafi ta barshi domin ansa kiran mahaliccin ta , Me ake ma haɗama a duniyar ? Bayan babu wanda yazo dashi kuma babu wanda zai tafi da komai , anan aka samu kuma anan za'a tafi a barshi , haba mata meke ruɗarmu a cikin duniya ? "Yar uwa ko kunyi yar jejeniya da mala'ikan mutuwa ga lokacin da zaizo miki ? To kisani mutuwa bata sallama bata jira sai kin gama sharholiyarki wallahi zata iya riskarki a duk yanayin da kike ciki , ba ruwanta da kina aikata alheri ko akasin haka , ya ubangiji ka karɓi rayuwarmu muna masu aikata alkhairi ka sada mu da aljannar ka dan darajar fiyayyen halitta S. A. W , am3n. Gadai Mamy nan an tafi neman duniyar amma an haɗu da mala'ekan mutuwa a hanya , kai ubangiji kasa muyi kyakkyawan ƙarshe , ko waye ma ya haɗa Mamy da wannan ibilishin ? Ƙarar wayata naji a gefena a firgice na juya inda take na miƙa hannuna na ɗauko , lambar Dikko naga ta bayyana a saman screen in wayata , ajiyar zuciya na sauke da sauri na ɗauki wayar tare da miƙewa tsaye na karata a kunnena , Sai sauke wani irin wahaltaccen numfashi nakeyi mai nuni da nasha wahala , cikin muryarshi maisa natsuwa yace har kin fara bacci ne ? Kukana ya ƙara kwacewa ban bashi ansar tambayar shi ba nace shine ka tafi ka barni.... ? Murmushi yayi mai sauti cikin murya mai kashe jiki yace in dawo ne ? Da sauri nace Eh , dariyar mugunta yayi yace An mata taji a jikinta tou fito gani nan ƙofar gida , da gaske ? Na tambayeshi sai kin fito zaki tabbatar da haka , da sauri ya ajiye wayata nayi waje da gudu , Dikko yana tsaye ya jingina da mota ya rungume hannayenshi a guje na isa inda yake tsaye da niyar in rungumeshi , a wayance ya matsa daga saitina ni kuma na ɗan sassauta gudu na saboda na iso ina ganin ya kauce nima na basar na rumgumi mota , Kauda kanshi yayi gefe tare da cewa ya kike ? Nima juya mishi baya nayi ina wasa da ƙasa da babban ɗan yatsana na ƙafa nace aini dana san kaine ma da ban fito ba , buɗe mota yayi ya shiga yana cewa ai dan nasan dama idan nine baza ki fito ba shi yasa nace miki ga Dikkonki ya dawo , ya ƙarasa maganar a daidai lokacin da yake zama a mota , Juyowa nayi dan a tunani na tafiya zaiyi , murmushi yayi yace ba tafiya zanyi ba banajin daɗin tsayuwar ne shigo mu tafi , da sauri na zagaya na buɗe mota na kame a gaba , ina rufe murfin motar ya taka motar muka shiga gidan dawakan shi , Kusa da motar daya bani yayi parking , ajiyar zuciya ya sauke tare da riƙe sitiyarin da duka hannayen shi biyu yayi miƙa cikin yanayin gajiya tare dayin hamma yace An mata na gaji wallahi yayi maganar cikin murya mai ladaftar da zuciya , Murmushi nayi amma banyi magana ba , dan idan inajin muryar Dikko sai inji tawa wata iri shi yasa ban cika magana a gabanshi ba , wayarshi ke ringing dan haka ya ɗauketa daga gefenshi daya ajiye yana cewa tou fa , karkace kaina nayi ina kallon fuskar shi yayin da hasken wayar ya haskaka fuskarshi dan duba mai kiranshi waya , Ɗan kallo yayi mai kyau yayin da idanuwan shi ke duba daga saman wayar zuwa ƙasa , zai ɗauka yace nifa bana san kallo da yawa , ki daina kallona haka nan tunda bakya so na , a dai² lokacin daya ɗauki wayar yana cewa inajin ka , Tou haka yace kuma ? A , a gaskiya bana kusa kawai kuje idan na dawo Ashiru zai tattaro minsu , ba komai fa kawai kaje abunka , to yayi kyau , ya kashe wayarshi , Bayan ya gama wayar ya juyo ya fuskance ni sosai yace An mata mi yasa kika bar mota tayi datti bakya hawanta ? Nace haka nan , hmm tunda bakyasan Dikko motar da ya baki ma bata burgeki ko ? Nace tana burgeni mana kuma ai nahau ta ma , Dikko yace haba An mata ai da kin hau wannan motar da naji a jikina , zansa a wanketa a daren nan ko baki so na ki hau motar nan don Allah inji daɗi kuma ko bakida inda zakije gobe kiɗan hau ta , Nace tou , yace yawwa ngode sosai , bayan wani lokaci kuma ya sake kallona yace An mata wai dan Allah mi yasa kike da kunne ƙashi ? Mi yasa bakyajin magana ? Nace me kuma nayi yanzu ? Bama kisan abinda kikayi ba ko ? Nace Eh , jinjina kanshi yayi yace yanzu ina amfanin irin rayuwar da kika koyama kanki don Allah ? Kullum baki da aiki sai ɗaukar tsiraicin mutane , Idan an taroki nan sai ki koma nan kina rayuwa kamar baki da kwalwa a kanki , shiru nayi banyi magana ba , cikin ɓacin rai yace ki kiyayeni ranar da nima zan miki tsirara in miki irin abinda kike ma mutane , bana san ɓacin raina akan ki saboda fushi na baida kyau idan har nace zanyi miki hukunci dai² da irin abinda kike aikatawa lafiyayen duka ɗaya zan miki ki mutu , cike da ɓacin rai nace tou ni yanzu waye kuma nayi ma vidio , Ƙanƙance idanuwa yayi yace Baban Mardiyya dama shine baƙin cikin da kike cewa zaki dasa mata a zuciya ? Ki bari bana so , nace tou , sake maimaitawa yayi cewa bana so ׳ idan kuma kuma kika sake zakiji babu daɗi , nace tou , Hararata yayi cikin salon so , yace to me kuma akayi miki kikayi kuka naga fuskarki duk sai a hankali , ban bashi ansa ba na canja maganar da tambayarshi wanda ya faɗa mishi nayi ma Baban Mardiyya vidio ? Cikin lallausar murya yace babu ruwanki da wanda ya faɗamin idan nace bana san abu kawai ki bari idan baki so mu ɓata , a ɗan zuciye nace tunda baza ka faɗamin ba bari in tafiyata , hannuna ya riƙo yace yi haƙuri An mata , tou faɗamin , yace ni bana san ɓacin ranki Al 'Ameen ne ya faɗamin , gaskiya An mata Al ' Ameen bai jitu dake ba kullum burinshi ya nemo aibunki ya faɗa a gidanmu duk da kince bakya so na ina so ki zama mai mutunci a idon "yan uwana da kuma iyayena kinga idan aka tashi bada labari cewa za'ayi ƙawar Dikko bata da hali mai kyau ni kuma kinga ai bazanji daɗi ba ko ? A kunyace nace Eh , yace tou da Allah ki baryin abu mara kyau duk ki barbaɗawa "yan baƙin ciki yaji a ido ya ƙarasa maganar yana kashe min ido ɗaya na dama , nace tou , Tada motar yayi yana cewa bari in ajiyeki haka nan kar ace kin ɓace , a dai² lokacin daya fara tafiya a hankali , yau da natsuwa yakeyin tuƙi yana ƙara jamin kunne na daina shiga sabgar kowa nayi rayuwata ni ɗaya idan banji bari ba kuma zanji hoho a jikina , a ƙofar gida ya ajiyeni yana cemin idan Allah ya kaimu gobe zai dawo , nace tou Allah ya kaimu ya kuma hutar da gajiya , ya ansa da amin ni kuma nayi cikin gida da gudu , murmushi yayi ya wuce cikin farin ciki , Yau zuciyarshi ta ƙara tabbatar mishi da akwai soyayyar shi a zuciyar An mata tunda har tasan idan ya daɗe bai zo ba idan yazo zata zo da gudu ta rumgume shi , kuma yace ko tana so ya dawo tace Eh , babu abinda ya kawo haka idan ba soyayya ba , yau kam yana cikin farin ciki. Washe gari sai 9:30am na fita daga gida domin zuwa wurin jana'izar Aunty Mamy dan naji ance 10:00am za'ayi mata sallah domin kaita gidanta na gaskiya , doguwar hijabi nasa mai hannu ta saukar min har ƙasa mai ruwan jinin kare , dake ina da haske sosai sai hijabin ta matuƙar martabamin fuskata , babu abinda na shafa domin yau ranar ta jimami ce , makullin mota na ɗauka nayi gaba abuna , Ina fita naga su Amisty suma sunsha nasu hijaben cikin mota suna tahowa , ganin zan shiga gidan dokuna yasa Amisty tayi parking dan ganin abinda zanyi , a natse na shiga da jakata a hannuna saboda riƙon wayoyin zaimin yawa a hannu , A gidan na iske Dikko da kayan training jikinshi ya cire takalma rufaffi ya jiye a gefenshi ya naɗe kafafuwan wandonshi , silifas ne a ƙafarshi ɗorowo { Yellow } masha Allah shine abinda na furta lokacin da na kalli ƙafarshi , hutu dajin daɗi ya tabbata a gareta har wani hurhurun haske takeyi tsabar tasha madara ta ƙoshi "yar gayun ƙafa da ko mai ba'a shafa mata sabar hutawa , ga wani gargasa ya sauko saman ƙwaurinshi "yan yatsunshi masu kyau dan dani keda ƙafafuwan shi babu abinda zaijamin saka wasu takalmi idan ba irin silifas in daya saka a ƙafarshi ba domin yafa burge , Yana gani na ya tashi tsaye ya tare da ɗauko takalman daya ajiye a gefenshi ya tun karo inda nake yana cewa ina zaki tunda asuba haka ? Nace rasuwa akayi , Allahu Akbar Allah Allah ya sawaƙe , nace ba rashin lafiya ba mutuwa , yace Ey ai na sani ina nema ma ahalin gawar sauƙi ne , Allah ya kiyaye hanya nace amin , biyoni yayi bai sake magana ba shima ya nufi wurin motarshi ya buɗe but in mota ya watsa takalman ya rufe ya shiga motarshi nima na shiga wacce ya bani wanda yau itace ranar farko da zan fita da ita , Tasha wanki tayi kalar ɗaukar hankali , saida na shiga harna sauko daga inda na ajiyeta shima ya sauko yana cewa mintuna 15 na baki ki dawo , tsayawa nayi nace ya kuma minti 15 sai kace kai ka aikeni ? Ban aikeki ba amma wallahi kika wuce lokacin da nace saina ɓata miki rai za'a faɗamin lokacin da kika dawo ai , haba wai mi yasa kake yin haka ne ? Ki wuce lokacin da nace miki sai kiga dalili , cikin hayani nace aure na kakeyi da zaka tsaramin yadda zanyi rayuwata ne ? Murmushi yayi ba tare daya kalleni ba yace ai da ina aurenki babu abinda zaisa na barki kije gaisuwar wacce aka kwakwale ma ido tirr ya ɓata baki tare da ficewa ya barni cikin mota kamar sakarai. Da sauri na kalli agogo naga 10:19am , kenan zan dawo gida 10:34 ? Gashi kuma har naci minti 1 , ina da sauran minti 14 yaushe naje har nayi musu ta'aziyya na dawo ? Tsoki nayi kamar kar naje wata zuciyar tace kije kawai kina ɓata lokaci , Da gudu na fito daga gidan kamar zan tashi sama , su Amisty suka rufowa motar baya dan a tunaninsu Dikko ne a ciki , lokacin da suka fito bakin titi tuni na ɓace musu ko ƙurata basa gani , hanyar da motar tabi ta wuce suka gaza gano ta ina motar tabi ta wuce , Da nasan haka hawan motar nan zai jawomin tashin hankali wallahi da ban hauta ba , ni kuma na hauta ne kawai dan Dikko yayi farin ciki saboda tayi wata huɗu da "yan kwanaki da bani ita amma ban taɓa hawanta na fita sai yau , Ina isa ƙofar soro har an dawo daga kai Mamy dandazon mutane kamar ƙasa gaskiya Mamy tayi jama'a a hankali na shiga mutane suka riƙa darewa suna bani hanya duk wanda ya kauce saiya bi motar da kallo kowa ya ƙagara yaga Dikko ya fito dan nace muku lokacin daya siyo motar anyi ihunta a gari duk garin katsina wannan motar Dikko kaɗai keda ita , Daga Qerau zuwa ƙofar soro minti biyu kacal ya kaini shima dan nabi a hankali dan motar tana da tafiya sosai , nabar gida 10:20 , na iso ƙofar soro 10:22 harda parking da nayi , manyan mutane suka fara yayyaɓe motar dan cikawa Dikko sheda ba'a iya gane waye a motar saboda gilashin motar duhu gareshi , wa za'a gani ta fito daga motar ? Ɗiyar ɗan caca , Tunda na fito kallo ya koma sama a dai² lokacin dasu Amisty suka iso , banbi takan kowa ba na ɗauki jakata na wuce jama'a suka bini da kallo yayin da surutu ya fara tashi ƙasa² danni taron mutane baya hanani tafiya kuma bai ruɗani bai firgitani haka kuma yawansu basa gigitani kuma banayin tafiya inji kamar zan harɗe na faɗi ,saida nakai gaf da zan shiga gidan Mamy naga Bello , kallona yayi ƙasa da sama yace wai Sultana ce haka bakya ko gane mutane ? Murmushi nayi tare da cewa ya za'ayi lafiya ta kasa gane mai bata damuwa ? Magana ce na faɗa masa ina faɗin haka na shige abuna na barshi da dogon nazari , Gidan mutuwar sai koke ² akeyi yayin da tabarmin zamar gaisuwar suka rarraba kashi ² , dangin Mamy da tasu , sai dangin mijinta makota sai kuma wasu lafiyayun karuwai suma sunyi nasu mazauni , ahalinta na farawa ta'aziyya sannan "ya "yanta , sai dangin mijinta , ko inda karuwan suke ban kalla na miƙe zan fita wata mata tacemin nan zaki zauna ke ? A dai² lokacin dasu Amisty suka shigo gidan , miƙewa nayi banyi mata magana ba , tace ke Sultana take ko wa ? Ta tambaya , aka ce mata Sultana , tace nan ne mazaunin mu , juyawa nayi da niyar feƙe mata uwa saidai banda isashshen lokaci dan ina so nayiwa mijin Mamy ta'aziyya , ina ƙoƙarin fita matar ta biyoni ta cakumoni ta baya tana cewa akace ina zakije ? Baki ga inda karuwai suke zaman gaisuwar su ba ? Ban mata magana ba na fiddo wayata daga cikin jakata nace ki duba zaki ga an rubuta Sultana itace lambar wayata , Kallona tayi sosai kuma kome tayi tunani Oho sai ta sakarmin hijabi ba tare data anshi wayar ba , ɗan gajeren murmushi nayi da gefen bakina na juya na fito ba tare dana sake mata magana ba , a ƙofar gida nayi ma mijin Mamy ta'aziyya da "ya "yanta maza Bello kuma sai kallona yake , murmushi nayi mishi na miƙe shima ban mishi magana ba , Tunda na fito daga barandar ƙofar gidan Mamy ake nunani nice nazo a motar Dikko , wasu kuma na cewa ni karuwa ce amma meya haɗashi dani bayan baya harkar mata , wasu kuma na cewa ɗiyar ɗan cacar nan ne shege mashayin giya ya haifo wannan kyakkyawar , wani yace ai yarinyar shegiya ce tana burgeni domin tanayin karuwancin cikin tako ne , kowa dai da abinda yake faɗa akaina abundai babu daɗin saurare , Murmushi mai ciwo nayi yayin dana tunkari mota ta , wato shi karuwanci babban tambari ne da baya gogewa har "ya "ya da jikoki kayi ƙoƙari ka zama na gari domin gori akan karuwanci ciwo gareshi yau mutane da sun san zasu taɓani su kwana lafiya inajin dasai sunci ubana kafin na fito , mota na shiga na karce duk wanda bai ga zuwa na saida yaga fita ta , Wuta ² na iso anguwarmu , a ƙofar gida naga motar shi , lokacin 10:33am kai tsaye inda na ɗauko motar na maida ta , lokacin dana fito ban sameshi ba kenan yazo da kanshi yaga lokacin da zan dawo ? Da sauri na wuce cikin gida dan inada abinda zanyi , Wuri ɗaya naje da mota amma yau gari magana ta kawai akeyi wata karuwa take tare da ɗan gwamna ta gama dashi ta tsafeshi har ya bata motar daya siyo ta miliyoyin kuɗi , duk inda ka saƙa a gari Sultana ɗiyar ɗan caca kafin wani lokaci kuma hotuna na sun fara yawo a social media da motar dana hau ɗiyar ɗan cacan da yafi ko wane ɗan caca sa'ar rayuwa , Al ' Ameen kuwa tuni yaje ya samu mahaifiyar Dikko ya faɗa mata halin da ake ciki dan yaga Dady yayi sanyi , Momy kuwa tayi zafi har ta wuce tafasashshen ruwa , matar Dikko data zo gaisheta itama ta cika ta kawo wuya , tace ma Al ' Ameen ya bari Dikko ya tafi a kamo Sultana zata ƙagi azabar da zata bata , Al ' Ameen yace ai ko yanzu ina iya kawota , Momy tace kudai bari yabar katsina dan koni baya so kamar yadda yake san mayyar yarinyar nan , Wane dalili yasa Dikko ya matsamin nahau motar daya bani yau ? Tabbas dan yasan za'ayi magana ne kuma haka yake so dama kowa yasan ina tare dashi shima yana tare dani dan idan babu wata alaƙa dani dashi mai girma me zai haɗani da motar shi.... ? Yau kuma idan akwai wanda yafi *Jiddah* baƙin ciki bai wuce Momy ba kuma sun tanadin shaglin partyn wulaƙanta ni , Jiddah bata ƙara jin takaici ba saidai Dikko ya tura Ashiru ya maida ita gida , tace bata komawa , koda Ashiru ya faɗawa Dikko tace bata komawa cewa yayi ya barta idan ta gaji ta koma da kanta , Tunda naje gidan rasuwa ban sake komawa Dikko ya hanani , sai yau sadakar 3 yace inje amma yau mintuna 10 ya bani , Umar ya aiko ya kawomin kuɗi in bada sadaka idan naje , kuma har yanzu yana gari bai tafi ba saboda kullum rana muna tare , Ina ta shiri zan fita saiga Ummu Affan wai tazo min gaisuwa , bayan ta gama ta'aziyyar tacemin ashe kuma sai kikayi mota ? Murmushi nayi ban bata ansa ba naci gaba huɗɗar gabana kenan ba gaisuwar ta kawota ba dan kawai taji labarin mota , saida na gama shirina kaf nace tou zan rufe ɗakin , tace tou bari in tafi idan kika dawo na dawo , fita tayi nima na fita na rufe ɗakin . Ina fita naga Baba zaune a tsakar gida duk yayi wani kalar ban tausayi , nace Baba baka lafiya ne ? Kallona yayi yace wallahi Mamana gabana keta faɗuwa , nace miya faru ne ? Yace nidai nayi miki alƙawari nabar caca har abadan duniya nace Eh Baba , yace tun daga ranar da mukayi maganar dake da na saka motarki a caca wallahi ban sake zuwa koda wurin caca ba haka duk abokai na bana tare dasu tun ranar ban sake shan giya ba haka kuma ban sake neman mata ba , Nace to yanzu meya faru ne ? Yace abun ya dameni ne tun ranar da nayi wannan maganar idan na kwanta bacci sai inga wani mutum tsaye a gabana yana cewa idan baka koma caca ba ajalinka ne zaici gaba da fuskantar ka , ka koma caca kaci gaba da neman mata kasha giya idan ba haka ba zamuyi maka kisan wulaƙanci domin zaka lalatamin duk wani tsari na , Shine nace bazan koma ba , jiya itace rana ta ƙarshe daya bani kuma yace yau idan banje gidan caca ba wallahi kasheni zaiyi , murmushi nayi nace Baba kenan wannan ai duk shirmen bacci ne , yace Mamana ba shirme bane da gaske ne dan har sunanki naji an kira a mafarkin yace shine ya toshe miki rayuwa wai ya rufe ƙwalwarki a bakin mataccen kwaɗo , dariya nayi sosai nace ji wani magana Babana ni na tafi saina dawo , Saida na fita daga anguwarmu zuciyata ta fara tabbatarmin da ba shirme bane , maganar Baba abin dubawa ce da tunani iri ² na isa gidan rayuwa , ban jima ba na fito bayan na basu kuɗin da Dikko ya bani duka ban rage komai ba , Jiki a sanyaye na dawo gida ban samu Baba ba , dan haka na shiga ɗakina kaina sai juyawa yakeyi , wayata na ɗauka na kira Dikko kaf na rattafa mishi abinda Babana ya faɗamin , yace baya nan yaje kano amma idan yayi magrib zai taho in Allah ya yadda , nace tou don Allah daka dawo kazo wurina , yace insha Allah An mata ki kwantar da hankalinki babu abinda zai faru sai alkairi , nace tom saida ya kwantarmin da hankalina sannan ya kashe wayar , Ina gama waya da Dikko wayar Mamy ta fara kuka , da sauri na ɗauki wayar ba tare dana san mai kirana ba , ina ɗauka nace Hello , mai magana a waya tace Mamy na samu duk bayanan da kike buƙata , kila bata san Aunty Mamy ta rasu ba , akwai wani kwaɗɗo da aka rufe gawarshi a kwalbar lemu kuma gawar kwaɗon saida aka zuba kwata a cikinta , akwai bokan dake gyara aikin kullum amma yace abu ya warware komai zai iya faruwa tunda har Binna ya fita a caca , Anyi ƙoƙarin juya al'ƙamin tsafi ya sauka akan yarinyar da kike magana bokan yace sai ta tsallake sallar isha'e da asuba idan har batayi su ba tana dai cikin tsarki ba jinin al'ada ba itace zata maye gurbin ubanta , yarinyar tana da addu'a gaskiya kuma bata wasa da sallah , kiyi sauri yanzun nan suka kira Binna zasu kashe shi.... Kwalbar da akayi asiri gata a hannuna , amma kiyi gaggawar zuwa gidan........ Ihun matar naji ina ta hello ׳ amma cikin wahaltacciyar murya tace kiyi gaggawa zuwa bayan gidan caca acan za'a kashe Binna ni kuma zanci da sauran.... A firgice na fara kiran wayar Dikko amma sai akacemin a kashe take , wayar Babana na fara kira sai ringing take amma ba 'a ɗauka , wayyoni Allahna na sake faɗawa wata rayuwar , me yasa Dikko ya kashe wayarshi ? Su waye suka kirashi ya fita ? Me akayi ma wacce nake magana da ita a waya ? Wayyo Allahna rayuwa me yasa zakiyimin haka ne .....⁉ 😭 06/10/2019 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 51 *_Godiya ta mussaman gareku ma'abota mutunci da mutunwa , ngode ׳ ina godiya sosai wanda idan nace zanyi ta rubuta ngode ² sai cajin wayana ya ƙare ban gama rubuta godiyar ba ,_* *_Hassan 80k_* *_Hassana Masko_* *_Hafsat Sa'idu Galadima_* *_Muhammad Musa Muhammad { Na Allah... }_* *_Halimatu Musa { Uwa }_* *_Gaba ɗayan shafin nan na yau sadaukar wane ga masoyana a duk inda kuke a faɗin duniyar nan ina sanku ina ƙaunarku kuma ina alfahari daku , fatan alkairi a gareku_* *_Kuma na gaishe ku..._* *_Abdulrahman & Ja'afar , Allah ya tabbatar da farin ciki da kwanciyar hankali a gareku ubangiji ya jiƙanku yasa ku gama da duniya lafiya , Am3n_* Juyawa ɗakin yakeyi dani kamar anayin hajijiya dani , wayyo Allahna ina zan dosa ? Mi zanyi ? Ya Allah ka kawomin mafita ka tausayawa rayuwata kuma ka tabbatarmin da alkairin ka , banda zaɓi sai naka banda wurin gudu ko tsira sai yadda kayi dani ya ubangiji al'arshi taimakon ka nake nema bana san taimakon kowa sai naka , duk abinda ya faru da Babana dani haka yazo a rubuce kuma babu wanda ya isa ya goge, Da gudu na fito daga cikin ɗaki ina cewa yaku taron "yan uwana kuzo kowa ya biyoni domin dai yau wata baƙuwar rayuwa tana tunkaro mu , ciwon ba nawa bane ni ɗaya , babu babba ba yaro ba matar Baba ba mace ba namiji yau tashin hankalin gaba ɗayan gidan ya tunkaro ku taho Baba yana buƙatar taimako ! Ina faɗin haka nayi gaba da gudu , namiji ɗaya ya biyoni shine babban yayanmu yana ke Sultana ina zaki ? Banda lokacin bashi ansa gudu nakeyi kamar taɓaɓɓiya shima da gudu ya biyoni ina fitowa bakin titi na samu napep nace muje , Yaya yana fitowa tuni mun tafi , shima dafe kai yayi tare da riƙe ƙugu , ganin hakan ba mafita bane yasa ya tari mai machine yace yabi mishi bayan napep inmu. Muna isa tun kafin napep inmu ta tsaya na dire na tun kari inda nake hango mutanen da basu wuce su biyu ba , sunyi rami sun saka hannun takobi cikin ƙasa tsinin kuma yana sama , bayan sunyi wa Babana wani irin duka a kai ya tafi duniyar ɗimuwa jini sai bin jikinshi yakeyi , bana iya gane fuskar kowa a cikinsu saboda rufe take idanuwansu kaɗai ake gani , Mai napep yana ganin haka ya gudu babu shiri dan tsira da rayuwarshi yayin da ni kuma na tunkari wurin haiƙan ina cewa kai na rantse da Allah idan wani abu ya sameshi gaba ɗayanku sai tsinuwar Allah ta tabbata kanku , ku barshi me yayi muku ne ? Me rayuwar shi ta tsone muku ko kune kuka bashi aron lumfashi ne ? Ubangijin al'arshi shine ya bawa Babana aron numfashi kuma shine ya bashi lafiya ku ɗin nan banzaye da ku baku isa ku fitar da ransa ba sai Allah yaso , Dariya sukayi sosai tare da cewa tou Allahn ne yaso shi yasa ma ya kirashi kuma yanzu zai tafi domin ansa wannan kiran idan kina iyawa ki kamo ran ki dawo dashi cikin jikinshi , suka ƙarasa maganar tare da ɗauko Babana suka birkitashi saitin zuciyarshi suka ɗagashi sama suka dakoshi saman takobin da ƙarfi , sai kuma suka ɗagoshi suka juyashi yana kallon sama suka sake sokeshi... Da gudu na isa wurin Babana na durƙusa saman guyawu na , nace Babana karka sake ka rufe idanuwanka babu abinda zai sameka kallarni gani nan nazo Mamanka Uwar masu gida jikina yana ƙyarma na fara ƙoƙarin ɗago Baba amma na ƙasa idan kuma nace zan juyoshi ina tunanin inda bai yanku ba ma zai yanku , Babu abinda ke ɗiga daga cikin idanuwan shi sai hawaye yana lunshe ido nace kar kayi bacci ka rufamin asiri karka rufe ido idan ka rufe ido tawa ta ƙare , waye ? Waye wai waye mutumin da kake gani a baccin ka ? Waye ya kiraka wurin nan ? Karfa ka rufe ido yi murmushi yimin murmushi Babana , dakel ya ɗago idonshi ya kalleni cike da soyayya sannan yayi murmushi da gefen bakinshi la'elaha illallah muhammadur rasulillah ya ƙarasa tare da rufe idanuwanshi , nice na ida da S. A. W , Kai........ Na shiga 3 na bani na lalace wayyoni Allahna wayyo rayuwa ina zan sa kaina , nace kar kayi bacci shine kayi bacci me yasa ? Me yasa kayimin haka haba Babana , shine zaka tafi ka barni ? Bayan kamin alƙawari baza ka tafi ka barni ba , shine ka tafi ka barni ? Ya ubangiji ka farkar dani wannan mafarki ka tausayamin badan halina ba dan darajar manzan tsira kasa bacci nakeyi , Isowar Yayana shima da gudu ya iso wurin cikin tashin hankali yaga Babanmu soke a saman takobi dan suna soke Baba suka gudu , shima wani irin ihu ya kurma hakan ya jawo hankalin jama'a , kafin kace me ? Wuri ya cika sai kuka nakeyi ina ƙarawa tare da cewa wai Allahna , wai Allahna , Allahu Akbar , Sauko Baba akayi daga saman takobin har yanzu murmushin da yayimin yana nan akan fuskarshi bai goge ba , kamar kace taso ya taso sai kayi tunanini bacci yakeyi , duk wanda yazo saiya haskashi saboda duhu yayi sosai , ganin ana ta kallemin Babana yasa na cire hijabina na lulluɓeshi a lokacin har Yayana yayi waya an kawo mota , Allah mai girma da ƙafafuwan shi yazo wurin nan amma gashi yanzu baya iya tafiya sai an ɗaukeshi , bayan an saka Baba a mota Yayana ya kamoni nima ya shigar dani duk muna zaune a baya yayin dana kwanta saman gawar Baba inaci gaba da kuka , Zuwan Mamy gidanmu na tuna ranar data zo ta samu Baba zaune a saman dakali tana bi bi biyyyy , murmushin da Baba yayi mata na tuno da alamar da yayi mata da ido , yau gashi daga Baba har Mamy duk basa cikin wannan duniyar , kai.... Wani irin ihu na sake kurmawa daga nan ban sake sanin abinda ya faru dani ba saidai na farko na ganni a ɗakina Dikko durƙushe a gabana idanuwan shi sunyi jajir Ashiru da Umar suna tsaye a bayanshi . Tashi nayi cikin kuka na rungume Dikko nace me yasa ka kashe wayarka ? Kiyi haƙuri har yanzu wayar a kashe take banda caji , kauda maganar nayi da cewa kaga Babana ko ? Ranar da nayi faɗa dakai na dawo gida shine Baba yayi kuka yace Mamana shine kika tafi kika barni ? Ni na goge mishi hawaye da wannan hannun nawa na nunama Dikko hannun naci ga da cewa nace masa ai na dawo , Nace Baba kana tunanin zan tafi na barka ne ? Bayan bana iya rayuwa saida kai ! Dare da rana safe da yamma yanayin farin ciki ko damuwa halin yunwa ko ƙoshi babu kowa a zuciyata sai kai , farin ciki ya dawo rayuwar ƙunci da damuwa zata kama gabanta , cikin kuka nace shine ya tafi ya barni , ni in rayuwar ƙunci da ɓakin ciki wayyo Allahna , wai Allahna.....? Inajina kamar inayin rayuwar da bana cikin sahun mutane yayin da farin ciki yake tunkaro rayuwata sai mutuwa tazo ta shafe wannan farin ciki , duk wanda yazo da niyar ya taimakeni sai a shafe labarinshi a duniya , bana so ka rasa rayuwarka ka tafi daga rayuwata kada kaima su kashe ka.... Juyawa Dikko yayi yace ma Ashiru ku jirani waje , fita sukayi , Dikko ya ɓanɓareni daga jikinshi ya zauna kusa dani yace ina Mamanki ne ? Cikin kuka nace ta gudu tabar rayuwata banma san ita ko "yar gidan wane ahalin suka haifota ba , ni ɗaya nake rayuwata a wannan ɗakin babu ruwan kowa dani nima banda ruwa da kowa babu mai so na sai Allah banda wanda zai nunamin kyakkyawa ko mummuna duk rayuwar dana ɗauko ita nakeyin abuna gani yau na zama marainiya..... Kallona Dikko yayi yace ke ba marainiya bace Allah yana tare dake kuma Dikko yana tare da rayuwarki , duk wanda kika ga ya mutu kwananshi ne ya ƙare ki daina mishi kuka kiyi mishi addu'a , nace to , Dikko yana gidanmu shi ya tayani zama a ɗakina yana min nasiha sai 1:39am yabar gidanmu , Bayan tafiyarshi ma na tuna banyi magib ba bare isha'e , fita nayi nai alwallah nazo nayi sallah nayi karatun al'qur ani mai girma tare da roƙawa Babana rahma a wurin ubangiji , har gari ya waye banyi bacci ba kuma banje ɗakin da aka kwantar da gawar Babana ba , Tunda safe gidanmu ya fara ɗaukar mutane su Amisty da suka zo ɗakina suka sauka , suna shigowa ni kuma na tattara wayoyina da tawa data Mamy na fita , ɗakin da aka kwantar da gawar Baba na nufa , har anyi masa wanka an shiryashi yana kwance a mankara , ina tsuguniya abinda ya tunomin shine , Ranar da muna zaune dashi a ƙofar gida nace Babana ina sanka ina kuma tausayawa rayuwata ranar da za'a wayi gari babu ɗaya a cikinmu , murmushi yazo ya tsayamin a rai da maganarshi da yace min ai bazai tafi ya barni ba , a bayyane nayi magana cikin kuka nace shine ka tafi ka barni... Naci gaba da kuka mai tada hankali , ina Allah ya jiƙanka ubangiji yasa ka huta , Allah yasa can yafiye maka nan Allah ya sadaka da mala'ekun rahma ubangiji ya kauda kai akan duk laifukan da kayi masa ya yafe ma ya gafarta maka ya baka aljanna dan arziƙin annabi muhammadur rasulillahi sallallahu alaihi wasallam.... Zainab ce ta riƙeni duk gidanmu Zainab tafi kowa tausayi na tana so na , tace Sultana kiyi shiru don Allah , cikin kuka na rungumeta nace don girman Allah ki tasheni daga baccin nan haka nan wallahi zuciyata ta kusa ɓarewa , Haƙuri kawai take bani , ina nan zaune a ƙasa kusa mankarar Baba sai kuka nakeyi , bayan wani lokaci kuma maganar Baba ta faɗomin a rai da yace idan har na mutu karki sake kimin kuka addu'a zakimin shine kaɗai zai tabbatarmin da soyayyar da kike min , shiru nayi naci gaba da gumji ina addu'a wa Babana , Misalin 08:50am gidanmu ya gama cika duk ta inda baka tunani , 09:00am aka ɗauki mankarar da Babana yake sama kwance za'a fita dashi domin salla tar gawarshi shi , shikenan Baba zai tafi inda bazan sake ganinshi ba bazan sake jin muryarshi ba har abadan abada duk soyayyar da yakemin ya tafi da gaske ya barni.... Sake ɗaukewa nayi na ƙara somewa ! Har akayi ma Baba sallah aka kaishi gidanshi na gaskiya Sultana bata san inda kanta yake ba , zata dawo² shiru har la'asar babu Sultana babu labarinta , duk wani taimako daya kamata ayi mata anyi amma har 5 na yamma bata dawo ba , Dan haka yasa Dikko yace a fito da ita a kaita asibiti , Zainab ce akan Sultana sai firfita take mata dama itace ta kula da ita a asibiti lokacin da Dikko ya farke mata mutuntakarta , da taimakon wasu matan aka fitar da Sultana aka sakata a mota da Zainab kaɗai aka tafi sai Ashiru dake tuƙi saishi Dikkon. Asibiti mai kyau aka kai Sultana likitoci suka rufa akanta dan ceto rayuwata , amma duk yadda akayi saida Sultana ta kwana huɗu bata cikin hayyacinta , ga dai ido tana kallon kowa amma ƙiri² bata iya magana , bata ci bata sha sai kuka , hankalin Dikko idan yayi dubu ya tashi ya lallashi Sultana har ƙarfinshi ya ƙare amma Sultana taƙi tayi magana da kowa , da tsiya² Dikko ke bawa Sultana ruwan tea shima idan tasha saita amayar dashi , Zainab itace ta bawa Dikko shawara ko a riƙa ba Sultana fura duk tsiya dai ko tayi amai wata zata tsaya , Dikko yasa Ashiru ya samo fura ake ba Sultana amma ko tasha sai ta dawo da ita , Dikko yace haba An mata wai me yasa kikeyin haka ? Gaskiya banajin daɗin abinda kike yi ko nima so kikeyi in mutu shikenan sai ki huta ? Kiji tsoron Allah ki tausayawa rayuwata haka nan mana , ke shikenan abu baya wucewa wurinki ? Kina nufin ke Allah bazai jarabce ki ba ? Ko akanki ne aka fara rashin iyaye ? Ba'a fara a kanki ba , ba kuma za'a gama akanki ba , mutuwa tana nan tana zagayawa tsakanin rayuwar kowa kuma babu bararre a duniya duk wanda yazo sai ya koma , ina ilimin naki da kike alfahari kina dashi ? Wannan shine sakamakon da zaki sakawa rayuwa dashi ? Shi kukan mutuwa da kika ganshi ba'a gamashi kuma baya ƙarewa har sai ranar da rai ya ƙare kiyi haƙuri don Allah . Murmushi Sultana tayi mai ciwo dan gani takeyi Dikko baima da hankali , ya za'ayi ta daina kukan rashin Babanta ? Ubanda ya ɗauki soyayya duniya ya ɗora mata , cikin "ya "ya sattin da wani abu itace kaɗai ya ɗauki duk soyayyarshi ya bata , taya ma zata manta Baba ? Taya zata daina kukan rashin shi ? Duk ma wanda yace tayi haƙuri ta daina kukan rashin shi wallahi mahaukaci ta ɗaukeshi , Banyi magana ba na sauko daga saman gadon na fice daga ɗakin , Dikko ya biyo bayana yana ina kuma zaki ? Banza nayi dashi ban juya ba kuma bansan abinda ya sameni ba bana iya magana sai hawaye , da sauri ya iskoni yasha gabana ina zaki nace ? Kaucewa nayi daga inda ya tsaya na tun kari hanyar fita asibitin , Zainab ma tambayata takeyi ina zanje duk banza nayi dasu nayi wurin mota na tsaya dan gida nake so inje , murmushi Dikko yayi mai nuni da baya san abinda nakeyi amma bai sake magana ba ya buɗemin mota na shiga na zauna ya rufe itama Zainab shiga tayi Ashiru ma haka amma yanzu Dikko yaja motar rashin a matuƙar ɓace , Har muka iso ƙofar gida babu wanda yayi magana , bayan yayi parking Zainab ta fita nima na fita Dikko kuma bai mana magana ba yaja motarshi yabar anguwarmu ranshi a ɓace , jiki a mace na shiga gida Zainab tana bina baya har ɗakina dan "yan gidanmu sai sharholiya sukeyi yadda kukasan ba mutuwa akayi ba , wayoyina Zainab ta kawomin tare damin bankwana tace Allah ya ƙaddara saduwarmu , Taci gaba da cewa yau kwanan Baba 5 da rasuwa ke kuma kina asibiti tunda aka ɗaga mankarar shi baki sake sanin abinda kikeyi ba , wannan gida naki ne babu maishi duk duniya saike tou a cikin kwanaki biyar da rasuwar Baba har sun siyar da gidan sun raba kuɗinsu an bani nidai gaskiya ban ansa ba , kuma wanda ya sayi gidan yaba kowa daga yau zuwa gobe ya tashi . Murmushi nayi tare da jinjinawa Zainab kai , ansar wayoyi na nayi ta fice ɗakin , tashi nayi na dudduba , kayana masu kyau da tsada duk an sacemin su kaf har kuɗaɗene gaba ɗaya an dauke su , tsoki nayi na fita nayi wanka na wanko bakina nazo nayi sallah magrib na gamesu da isha'e , ƙarfe 10 na dare kuma Dikko baiyi zuciya ba yazo , A saman dakali muka zauna , ya ƙaramin gaisuwa tare damin nasiha yacemin kuma idan Allah ya kaimu zaije Abuja kwana biyu zaiyi ya dawo idan ya dawo zai tafi dani , cikin kuka nace to kuma kayi haƙuri ɗazu da nayi maka shiru , jawoni yayi jikinshi cikin sigar rarrashi yace ba komai An mata ai kinsan bana iya zuciya dake , Murmushin ƙarfin hali nayi cikin shashshekar kuka nace Allah yasa kaima kar a kashe ka , yace shima da suka kashe shi sai kuma ya kauda maganar da cewa tunda har An mata tayi rashin lafiya nima banajin daɗi , Bai dai wani daɗe ba mukayi sallama dashi har mota na rakashi ya bani kuɗi masu yawa yace in ajiye mishi nace ni sata akemin yanzu , yace idan an sace ba komai idan baki da kuɗi na arami ki , nace nidai bana ajiyewa haba yi haƙuri ki ajiyemin , nace kuɗin sunyi yawa bazan iya ajiyewa ba , kallona yayi yace tou ibi wanda zaki iya ajiyemin , nidai ko ɗaya bana iya ajiyewa , Tou ɗauka na baki duka , zaro ido nayi banma yi mishi magana ba na wuce da sauri gida , An mata zo , da Allah kizo kiji , ban dawo ba , murmushi Dikko yayi yaja motarshi ya tafi... Jiya Dikko ya koma Abuja kuma munata waya dashi yana gayamin ya ƙagara gobe tayi ya dawo kuma yacemin yanzu idan zan koma makaranta Abuja zai tafi dani bazan sake makarantar kwana ba , yace shine zai riƙa kaini yana ɗaukoni wai sai muzo katsina juma'a da daddare mu riƙa komawa lahadi da daddare , bawan Allah shi kaɗai ke lissafin shi , haka dai ya ƙari surutunshi yamin saidai safe. Muna gama waya da Dikko aka aiko kirana , dan haka na ajiye wayar na fita , Al ' Ameen na gani ƙofar gidanmu bayan mun gaisa yacemin mai gida yace nazo na ɗaukeki ki gano wani gida idan yayi miki yana so acan zaki koma da zama , murmushi nayi nace aiko yanzu muka gama waya dashi bai faɗamin zaka zo ba , Al ' Ameen yace nidai shine ya aiko ni , ni kuma nace tou bazanje ba na juya da niyar komawa gida , matan dake bayan mota suka fito kaca² muka fara kokowa har sukayi nasarar dannani a mota Al ' Ameen aja muka bar ƙofar gidanmu... 07/10/2019 *JAMILA MUSA....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 52 Ina zamu je yanzu ? Al ' Ameen ya tambaya ? Muje gidana Momy tana can tana jiranmu , juya kan sitiyarin yayi muka kama hanyar gidan Dikko , babu wacce nayi ma magana a cikin su kuma banyi ta wani fizge² ba kawai na tsaya ne naga iya gudun ruwansu nasan dai bana kasuwa a wurinsu saidai su dakeni , murmushi nayi mai sauti tare da binsu dukansu da kallon rainin hankali , Jiddah harararki takeyi , wacce aka kira da Jiddah ta juyo tare da yankamin wani irin lafiyayen mari harsai da gefen bakina ya fashe , murmushi nayi cikin takaici nace wallahi kinyi sa'a rayuwa taimani duka amma da yanzu²n nan na kifar da motar nan kowa ya mutu , me nayi muku kuka shigo rayuwata a dai² lokacin da nake kukan mutuwar mahaifina ? Ɗayar tace munafika ji tana nuna kamar bata san komai ba , idan kin manta bara a tuna miki , ai kinsan Dikko ko ? Wannan matarsa ce ta nuna Jiddah ke ɗin banza ɗiyar mashayin giya jikar matsafi ki haɗa ƙirji da mijin ɗiyar masu wankakken asali , da sauri na rufe idona amma kafin ta rufe bakinta tuni nakai mata kaina da ƙarfi hancinta ya fashe jini yaci gaba da kwarara , cikin tsananin ɓacin rai nace ita jakar da kike magana itace baƙuwar Dikko , Da tun farko kun faɗamin ko suwaye ku da ba'asha wahala ba , domin ido na a buɗe yake inga macen da zata kalli mai girma Dikko in tsiyaye mata kwayar idanuwa ke dan ganganci ma aurenshi kikayi ko ? Hmm hawan doki ba linzami muguwar kasada ne domin in baka faɗo ba kasha wahala , idan kin isa ki kira Dikko a waya na kirashi dani dake a ga wayar waye zai riga ɗauka , matar sadaka dake , Gaba ɗayansu suka rufeni da duka a dai² lokacin da muka iso cikin harabar gidan , dukana suke tun daga cikin mota har waje suka jawoni , matar Dikko ta bugamin kai a jikin mota sai dukana sukeyi babu ji babu gani kamar an kama musulmin ɓarowa a chochie , murmushi nayi cikin wahaltuwa nace kinji haushi ko ? Nace miki matar sadaka ! Kiyi haƙuri mace ɗaya ce a zuciyar gwarzon namiji idan har akwaita to ba kowa bace nice , haka yake faɗamin kullum rana , kuma yacemin babu wata mace a duniya saini domin zuciyarshi da idanuwan basa ganin kowa saini , kunnen sa bayajin maganar kowa sai tawa , A dai² lokacin da Umar ya iso wurin yana ranki ya daɗe lafiya ya tambayi matar Dikko , sai kuma ya kalleni yace Sultana ya akayi kika zo nan ke kuma ? Goge hawayen baƙin ciki nayi sannan nacewa Umar Al ' Ameen ne yaje har gida ya ɗaukoni da ƙarfin tsiya , a gigice Umar ya kalli Al ' Ameen tare da zaro idanuwa yace da kanka ? Wayarshi ya ciro daga aljihu yana wallahi saina faɗa mishi , ka kamo An mata da tsiya² ka rungumar mishi An matar shi ? Hmmm lallai akwai matsala dan nasan idan har naga mala'enka mutuwa tabbas nasan tafiya tazo wallahi yau babu abinda zai hana mai gida dawo katsina cikin daren nan , Jiddah tace ka kirashi ka faɗa mishi ni banajin tsoronshi , Umar yace yau zaki fara ji ki jirayi zuwanshi a dai² lokacin daya fara cewa ranka ya daɗe Al ' Ameen yaje har gida ya ɗauko Sultana kuma da ƙarfin tsiya ya jawota gata nan sai dukanta sukeyi kamar agola yaci zarafin ɗan masu gida ! Banji yadda Umar da Dikko suka ƙare ba suka jani mukayi ciki , a gaban mahaifiyar Dikko suka gurfanar dani tare da cewa Momy gata nan , kallona tayi sosai irin yanayin kallon da Dikko yakeyi irin kallon takeyi , itama dai kyakkyawa ce kamar buzuwa hutu ya tabbata ga kyakkyawar matar nan , Ɗan zamowa tayi daga cikin kujera tace yarinya ya sunan ki ? Ɗan kauda idona nayi dan bata girmanta nace suna na Sultana , meye tsakaninki da ɗa na ? Cikin ladabi nace babu , miye dalilin da yasa ya ɗauki mota ya baki ? Shiru nayi dan banda ansar bata , dake nake , nayi shiru , tace tou saurara kiji da farko zaki bada makullin motar nan aka kawomin shi , na biyu kuma ki fita daga harkar Dikko idan ma yana miki ƙarya yana sanki tou ƙarya yake miki baya sanki , ya faɗamin bakina da nashi yace halakar dake zaiyi da soyayyar shi ya kaiki ya baro ki , kuma tun yanzu ya kaiki ya dawo domin kin tafi kuma Dikko ya dawo , dama in banda baki da lissafi ya za'ayi a haɗa doki da jaki ? Siga ko a faɗar sunan ba iri ɗaya ne ba , ina ke ina zinari ? Matsayin Dikko ya wuce naki ki tuna idan kin manta , gidajen da kuke haya gaba ɗaya ya tattara ya siye ya mayar dasu gidan kiwon dokunan shi , "Yar talaka waye ya kaiki kiwon doki ? Jidda tace kuma ita ba jinin sarauta ba , Momy tace duk dinari sunanshi dinari akwai na talaka akwai na masu kuɗi wallahi Dikko babban zinari ne koda kuɗinka saida rabonka kuma ba'a saka irin kaɗɗararshi a caca tsaftatacce ne shi baida sirki ba'a haɗashi da komai ba ko goro baya ci bare yasha sigari ke ko naki uban kwalbewa yakeyi kuma saiya raba titi biyu tirrr da sanin zuri'ar da ubansu baya ciyar dasu , Tadai wulaƙanta ni sosai ta faɗi duk wasu sirrika na gidanmu abun dai babu daɗin ji , ta tozartamin Babana bawan Allah da yana can lahira duk a gaban Jiddah tayi min wannan wulaƙancin sannan ta rufe da cewa in tattara inbar garin katsina saboda jahar mijinta ne idan taji labarina kusa ² wallahi zata ɓatar dani , Al ' Ameen maida banza ka taho da makullin motar ɗana , Jiki a sanyaye na miƙe na kalli Al ' Ameen dake gefena nace mu haɗu gidanmu in baka , Momy tace ku haɗu a ina ? Ki bishi ku tafi tare , ko inda take ban kalla ba nayi gaba abuna yau banda inajin mutuwar Babana tana yagarmin zuciyata da babu abinda zai hanani na faɗawa matar nan miyagun kalamai masu zafi . Da sauri na fita daga gidan zuciyata tana tafarfasa kamar zata zubo ƙasa saboda azabar zafi , nayi tafiya mai nisan gaske sannan na samu abin hawa , gashi banda ko sisi kuɗina an sace su duka , a ƙofar gidanmu na samu Al ' Ameen nacewa mai napep in ya jirani ina zuwa yace to , Gida na shiga na ɗauko mukulin mota na bawa Al ' Ameen ya tafi , shi kuma mai napep nace masa kana san katifa ? Dan gidan babu kowa duk kowa ya kama gabanshi , mai napep yacemin hajiya siyarwa zakiyi ne ? Nace Eh idan na samu masu siya dan siyar idan ban samu ba sai na bayar kyauta tashi zamuyi .... Dame ² zaki siyar ne ? Nace katifa labulaye sai gas sai tukunya ɗaya bokitin wanka da dai sauran tarkacenmu na mata idan kuma kana da kuɗi kawai ka bani dubu 3 ka kwashe duka , da sauri ya warwaro 3k ya bani , muka koma dashi gida har ledar tsakar ɗakin saida ya cire ganin katifar mai mutunci ce yace hajiya bara na ƙara miki ɗari biyar nace ngode , Yana cikin kwashe kayan wayar Mamy ta fara ringing da sauri na ɗauka cikin wahalalliyar murya tace Mamy mu haɗu dake general yanzu ² tafiya za'ayi dani gida a daren nan , wane ɗaki kike ne ? Emargency da kinzo ki kirani amma karki daɗe nace tou , a wurin nabar mai napep na fice daga anguwarmu ina mai cike da kewarta. Napep nahau babu ɓata lokaci muka isa general a lokacin har an fiddo matar za'a sakata a mota ina kiranta ta ɗauka na faɗa mata na iso , tace ta ganni itace aka kamo in matso inda suke , da sauri na matsa wurin duk na gaishe su suka ansa tacemin ina Mamyn take ? Cike da damuwa nace mata Aunty ta rigamu gidan gaskiya , ni nice Sultana , salati matar tayi tare dayin kabbara tace tou Sultana shiga mota muje , nace tou babu wani wasi² ko kokonto na shiga mota ahalinta suka shiga muka fice daga asibitin bansan garin da zamu ba.... 01:30am ihun Al ' Ameen ya karaɗe kaf ilahirin girman gidan gwamnati , a ɗakinshi ya farayi mishi wata irin azzalimar shaƙara bayan an ƙwaƙwale Al ' Ameen daga hannunshi dakel , shine Al ' Ameen in ya fito da gudu ya nufi inda zai haɗo da Dady dan yasan duk girman gidan nan babu wanda ya isa ya hana Dikko yayi mishi wani abu saishi , kuma duk Umar ne ya ƙara zuga Dikko yadda ya kamata kuma duk zagi dacin zarafin da akayiwa Sultana saida ya laɓe yaji kuma ya faɗawa Dikko , tsakanin Abuja da katsina ji yayi tayi mishi nisa yaci titi yadda ya kamata Allah dai kawai ya kawoshi katsina dan Ashiru ma baiyi tunanin zaizo katsina da rayuwa.... Ihu Al ' Ameen yakeyi a taimakeni zai kasheni yayin da Dikko ya koma mota cikin ɓacin rai yabi Al ' Ameen da gudu , na bani na lalace gefe² ya riƙe hayewa inda mota bata hawa amma hankalin Dikko ya fita daga jikinshi duk mai lumfashin dake gidan nan babba da yaro babu wanda bai fito , cikin tashin hankali Dady ya tunkari motar yana Babana meye haka kakeyi wai ? Da gudu Al ' Ameen ya ɓoye a bayan Dady cikin tsananin ɓacin rai Dady yace meya haɗaka dashi ne ? Al ' Ameen yace babu abinda nayi mishi kawai ina ɗaki kwance yaje yaita dukana da ya gaji kuma shine ya shaƙeni , Dikko da aka fito daga mota dakel yace babu abinda kamin ko ? Dady yace Babana wai meke damunka ne ? Cikin tsananin ɓacin rai yace saifa na kasheshi matsalata kafin na gano kanamun munafinci ne amma da zaran na gano ka tou babu sauran amfaninka a duniya da ƙarfin bala'e zan shaƙeka saina kashe ka hankalina zai kwanta , Momy data iso yanzu tace ka kashe tunda kai mahaukaci ne , kamar jira yake tayi magana ya fizgo Al ' Ameen yayi mishi kyakkyawar shaƙa yana zaka sake shiga sabgata ? Ina makullin mota ta dan ubanka ? Dady yace sakarshi Babana ! Dikko yaci gaba da cewa tunda kake kaga ina shiga sabgar wani a gidan nan ne ? Ubanka ne ya bata motar ko ni ? Har kaine ka isa ka taɓa An mata , Saida Al ' Ameen yayi fitsari a wando saboda azaba kuma anyi a cire Dikko daga riƙon da yayi mishi an kasa , saida Dady yasa hannu aka ciroshi dakel bayan Al 'Ameen ya suma , wani irin ihu Dikko yayi mai tada hankali yayi wata irin jijjiga ya sake tattaka Al ' Ameen zaiyi magana lumfashin ya tsaya , Su Ashiru suka ɗaukeshi aka shiga dashi ciki kamar yadda Dady ya bada umarni , cikin bedroom aka kai Dikko saman gado aka kwantar dashi , koda Momy ta shigo Dady cewa yayi ta fita baisan ganinta kuma wallahi idan bata fita harkar Baban shi da yarinyar nan da yake magana wani abu ya sameshi wannan Jiddah da kika matsa kika auro mishi wallahi saina sashi ya saketa , Dady yaci gaba da cewa ai nima ina da "yan uwa kuma suma suna da"ya "ya sai yaje ya auro yarinya mai ɗa'a da tarbiyar. Kullum kina gidan yarinya ke ko kunya bakyaji kin hana yarinya ta zauna ɗakin mijinta kullum tana gidan surukai , tou kayi mata gori tazo ta kwana kuma ko Dikko baya aurenta nan gidan uwarta ne saita kwana kaje ka koreta tana can ta kwanta , tsoki Dady yayi mai nuni da bata da hankali , Nan yabar Momy tsaye ya ɗauko maganin Dikko ya zuba mishi a baki , da sauri ya buɗe idonshi maganar Umar taci gaba da dawo mishi wai Jiddah ta bugawa An mata kai a mota , ta daketa har ta fasa mata baki , kuma ka faɗawa Dikko saboda ni banajin tsoronshi , murmushi yayi ciwon mugunta ya tashi da sauri ya diro daga saman gadon ya fita Momy tabi bayanshi da sauri , kafin ta fito harya ɓace mata ya nufi part inta , Kwance ya samu Jiddah saman gado tayi ɗai² tana shan iskan A C bata da wata damuwa hankalinta kwance , ƙafarta ya riƙo ya jawota ƙiyyy a firgice ta buɗe idonta wayyo Allahna Yaya me nayi maka ? Dake da waye kuka je gidansu An mata ? A tsorace ta nuna mishi ƙanwarshi dake kwance gefenta tana bacci , kallon ƙanwar tashi yayi sannan ya sake kallon Jiddah yace bana dukanki amma ki tattara ki kama gabanki ki tafi gidan babanki babu wanda yaji babu wanda ya gani har sai na gano An mata , Idan baki tafi ba na rantse da Allah sakinki zanyi kuma saki na wulaƙaci da tozarci amma in kika haɗa ya nayi ² sai ki ɓace abinki babu wanda yaji babu wanda ya gani , idan wani ya kirani ya bani haƙuri zan sakeki ne , idan kika sake dawowa gidan nan ba tare da An mata ta dawo ba saki ne , idan har kika bari Momy taji ta zageni ko tamin faɗa saina sakeki ya ƙarasa maganar yana fizgo ƙanwarshi itama da sauri ta buɗe idonta wayyo Allahna na shiga 3 tasan haukan Dikko Yaya wallahi Momy ta aikeni itace tace naje , wani irin mari yayi mata saida ya bata kashin bala'e yace idan ta aikeki gobe sai kije , Kuma a gidan nan An mata zata dawo da zama idan akwai wanda ya isa saiya hanata zama na gani , wasu kwashe ² ma sunzo bare kuma matar ishashsshe , wallahi idan dai na ganta a daren nan saita kwana gidan kallon banza ko harara wani yayi mata saina makantashi har abadan duniya , Momy data shigo yanzu tace da Allah rufemin baki sakaran banza ka kawota gidan nan kaga yadda zanci mutuncinta a gaban idonka , baiba Momy ansa ba yace ma Jiddah kuma ki anso mata makullin motar ta kafin kiji babu daɗi , Momy tace makullin mota yana hannuna Jiddah zata riƙa hawa motar , taɓe baki Dikko yayi yace ba komai An mata dai ta hau ta bata kwance yana faɗin haka ya fita yaci gaba da kiran wayar An mata... Dikko na fita Jiddah tace Momy idan Allah ya kaimu gobe zanje gida , Momy tace lafiya ? Jiddah tace tunda muka dawo daga america nake cewa zanje ² Allah bai bani ikon zuwa ba , Momy tace sai kuma cikin dare zaki faɗamin zaki ? Jiddah tace kiyi haƙuri Momy ai kwana biyu zanyi in dawo , Momy tace tou Allah ya kaimu , sun dai daɗe suna ɗan firarsu sannan kowa ya kwanta yayin da Jiddah tayi ƙudirin warware soyayyar Sultana daga zuciyar Dikko , Wurin Dady ya koma har yanzu yana kiran An mata amma taƙi ɗaukar waya ita ai dole tayi fushi , shi kuma bai daina kiranta ba , a gaban idona kiranshi yake shigowa kuma a gaban idona yake tsinkewa dukan kiraye ²n da yayi min ina ganin su, Dan sai 10:58pm muka iso garin Daura , kuma tun muna hanya Dikko yake kiran wayata har yanzu kusan biyu da rabi yaƙi daina kirana , ni ɗaya ce kwance a ɗakin da aka bani gidan "yan gayu komai dai yaji bakin gwargwado matar da ta taho dani tace na kwanta da safe zamuyi magana , Hawaye ya cikamin ido tausayin Dikko ya kamani sosai dan abinda na lura idan za'a kwana a haka bazai daina kirana ba haƙura nayi na ɗauki wayar cikin kuka nace ka daina kirana mayaudari mai yaudararin kalamai , Dikko yace An mata wai mi yasa ke birkitaccen tunani gareki ne ? Kaine mai birkitaccen tunani ashe da kake cewa ka ƙagara gari ya waye kazo gareni duk yaudara ce , ka shirya munafircinka shine kasa aka wulaƙantani aka tozartani aka zage Babana da baisan irin rayuwar da nakeyi ba a halin yanzu , to na bar katsina sai ka zuba ruwa ƙasa kasha kuma daga nan gaba naci kada Allah yasa na sake ganinka ko a mafarki na , a haka dama kake tunanin zance ina tsanka ? Tou bana sanka na tsanake ׳ , Cikin hayani Dikko yace kada Allah yasa ki soni An mata idan baki so ni ba zan mutu ne ? Sai lallaɓaki nakeyi kin ɗaukeni kamar wani sakarai sai gagari nake tsakanin rayuwata da taki , baki saurarawa kiji abinda zan faɗa miki kije kiyi duk abinda kika ga dama idan kin tashi ma kibar Nigeria ƙarewar katsina nima kada Allah yasa na sake ganinki a barci na sai me , ƙaramar yarinya dake , sassauta murya yayi yace kiji tsoron Allah An mata domin ubangiji yana iya jarabtarki da irin soyayya da ya jarabeni da ita taki , me nayi miki haka kika tsaneni don Allah ? Haba An matana nasan kina san Dikkonki kuma kina tausayina kiyi haƙuri yanzu kina ina inzo ? Fashewa nayi da kuka idan har nace bana san Dikko nayi ƙarya ina sanshi ׳ amma nasan babu yadda za'ayi gidansu su bari ya aureni saidai kawai mu dawwama muna soyayya , duk soyayyar da babu aure a cikinta ta zama shirme ni haka rayuwata zata ƙare tsanin sama da ƙasa ? Saina hau sai na sauko ? Me yasa zuciyata ta cuceni ta koyi soyayyar wanda tasan yafi ƙarfinta , A gajiye Dikko ya kwanta saman kujera 2siater yace inajinki kina ina ne ? Ina ina sai kuma nayi shiru , kina ina Nidai kayi haƙuri bazan faɗa ba , cikin sigar lallashi yace ai nasan zaki faɗa irin ɗan jan ajin nan ne na mata kuma duk a rasa wanda za'aja ma aji saini An mata ni ko bana iya ja miki aji wallahi saboda baida wani anfani inja miki aji ince na jawa wa aji ? Da kinsan yadda na ɗaukeki wallahi da baki fara tafiya kika barni ba , amma nasan kema wasa kike kina katsina , Ina katsina amma bana cikin katsina , yace ai na sani saboda wallahi inajinki kusa dani amma zaki ɓatamin rai a daren kuma dole sai kinyi saboda yarinta , baza ka sake samuna a waya ba , kuma baza ka sake gani na har abadan duniya ba , murmushi yayi tare da cewa ƙarya kikeyi , zaka gani shima yace kema zaki gani , yana faɗin haka na kashe wayata gaba ɗaya , Koda Dikko ya sake kiran wayar Sultana yaji ta kashe cikin ihu yace Dady ta kasheni , dan dama a gabanshi yake wayar , wallahi idan bata buɗe layin nan nima zan rufe rayuwata kowa ya huta , Cikin tashin hankali Dady ya dafe zuciyarshi yace Babana idan dai ka kasheni ka huta , shima Dikkon yace nima idan na mutu kowa ya huta wallahi idan bata buɗe wayar nan ba zan zama shafaffen a cikin "yan kwanakin nan , cike da iskanci ya sauko daga saman kujerar yana layi kamar yasha giya ya ƙoshi wurin firij ya nufa yana Allah kasa inyi kyakkyawan ƙarshe ashe iyakar ibar da nayo kenan , Da sauri Dady ya tashi ya nufi wurinshi a lokacin harya ɗauko ruwan sanyi ya fara sha hawaye na fita daga idonshi Dady ya riƙeshi yana cewa Babana wai miye kakeyi haka ne ? Ɗora rober ruwan yayi saman firij yace kaima ka fara jiyo ƙanshi mutuwar ne Dady ? Ka riƙe wannan daren domin zai riƙa ebe maka kewa idan bana raye , riƙeshi Dady yayi yana cewa baka dai so ka bar in zauna lafiya ko ? Dikko yace gangar jiki kaɗai ake tattali ba ruhin ba , idan akwai wani wanda ba'a so ya zauna lafiya to ba kowa bane nine , Wai me An mata tayi muku ne kuka tsane ta haka da yawa ? Naga shege ma mara uba ana aurenshi bare ita ba shegiya bace ba , kuma nasan namiji yana zuwa gidan karuwai ya auro mata ita a gidan wane karuwan take zaune ? Caca ² kowa saboda Babanta yayi caca sai ace bana aurenta ? Tou nima zan zama ɗan caca kuma na fara neman matan na sha giya shikenan sai ta zama matar mashayi , sassauta murya yayi cikin kuka yace na wahalar da An mata na bata azabar da duk lokacin dana tuna abinnan sai naji kunyar kaina.... Cike da damuwa Dady yace a , a Babana da hannu Dikko ya dakatar dashi bai sake magana ba ya ɗauki robar ruwan daya fara sha ya matsa wurin kujera ya ɗauki makullin motarshi ya fice , a lokacin har 3 na dare yayi , shida Ashiru suka fita daga gidan suka koma g r a gidan Dikko , Fitar Dikko Dady ya zauna ya zabga tagumi yana tunanin da bashida da gaira bare dalili , Ni kuma bayan na kashe waya na fashe da kuka nima wanda bansan dalilin yinshi ba , ji nake kamar in taho katsina in haɗu da Dikko zuciyata ta tabbatarmin cewa Dikko bazai taɓa wulaƙantani ba har abadan duniya , kwana nayi ina kuka kafin gari ya waye fuskata tayi jajir saboda kuka , idanuwana sun kumbara saboda rashin bacci , ko kalaci kasa cin komai nayi ina ta tunanin Dikko , Kwance yake yayi ruf da ciki ya kifa kanshi a katifa shi kaɗai yasan masifar da yakeji , bayan wani lokaci kuma ya juyo shima dai yaji masifar so yayi kuka har ya gode Allah , shi mamakin da yakeyi duk girmanshi a shekarunshi wai yake ma mace kuka , macen ma "yar ficiciyar yarinya wahalallen murmushi yayi mai ciwo a bayyane yace An mata baki da adalci kanki kaɗai kika sani , kema Allah sai kamaki bazai barki ki huta ba tunda kika hana marawuta zaman lafiya , A hankali ya lumshe idanuwan shi ya fara tunanin tun farkon haɗuwar shi da An mata , da abinda yayi mata da gishirin daya zuba mata ya korashi da ruwa , wayyo Allahna me yasa nayi haka ? A lokacin ina hankalina ya tafi ? Ina tunani na ? Dama baya zata dawo dana gyara wannan kuskuren wayyo Allahna , me yasa ² ? Wai me yasa sai nine aka zaɓa ? Wai wane hauka ya kani ? Kai An mata me ya sa kin cika taurin kai haka da yawa insha Allah ubangiji bazai barki kimin wasa da rayuwa ba wallahi sai kin nemo Dikko ina nan ina jiranki bazan sake zuwa ko ina ba sai kin dawo kuma sai kin kirani nima bazan sake ɗaukar wayarki ba sai kinzo kin bani haƙuri , yafa san baya hanani kuma baya ɗaga murya shine yakeyi , Ashiru yace mai gida dan girman Allah kayi haƙuri , Dikko yace kai baka da hankali na cuci yarinyar nan babu wanda yasan abinda ke tsakani na da An mata daga ni sai ita sai Allah , murmushi yayi yace An mata manya duk duniya inba ita ba waya isa ya mari Dikko ya kwana lafiya sai ita ta ɗaga hannunta mai daraja ta zabgagamin mari kuma nace ina santa tace na tsanake Dikko inba Ubangiji ba waya isa yayi wannan tsarin ? Saishi ubangijin samman da ƙassai , a hayaniyance yace sai kin dawo wallahi........ Tari yayi yaci gaba da cewa kema Allah ya zargeki tunda na dawo daga america na gani sama lumfashin ya farayi , a wahalce yace kuma wallahi bazanyi shiru ba saina faɗa , riƙeshi Ashiru yayi cikin damuwa yace mai gida don Allah , idon Dikko cike da hawaye yace shitttttt🤫 ya karasa yana fiddo kyawawan idanuwanshi , Ashiru yace don Allah , cikin hayani yace kaimin shir bai ƙarasa faɗa ba lumfashin shi ya ɗage. Ƙarfe sha ɗaya da rabi na safe Al ' Ameen ya ɗauki Jiddah suka fara laluben hanyar kaduna ranta a ɓace amma babu yadda za'ayi ta faɗawa wani ayi ma Dikko magana kuma tasan wallahi kamar yadda yace zai saketa zai saketa addu'ar ta Allah yasa aga Sultana da wuri , kuma ko ta ƙarƙashin ƙasa saita shiga ta fita ta raba wannan tarayya...... Murmushi Zaune nake a gaban matar da tazo dani , kwalbar data faɗin a waya ajiye a gefenta babu abinda ke cikinta sai tsutsotsi da wasu irin mahautan layu mataccen ƙwaɗon da Babana ya faɗa gashi ina kallo , gyara zama tayi tare da cewa jira Yayata tazo tacemin ta kusa isowa , cike da ladabi nace to Aunty , ji nake dama Dikko yana tare dani shima yaga abinda nake gani yana tayarmin da tsikar jiki........ 08/10/2019 *JAMILA MUSA....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 53 *_ƊAN MACE...! Sabon abinci yafi ɗumame daɗi 😋 na zaune makahon duniya , wasan kokowa bana gurgu bane hanzarta ki nemi naki karki sake ki bari a baki labari , tsohon hannu ce tuni ta shahara wannan marubiciya kuwa itace HAWWA MUH'D USMAN {{ real smasher }} ina tayaki murnar fara sabon littafinki ubangiji yasa yadda kika fara lafiya ki gama lafiya , Am3n..._* Cikin tashin hankali Ashiru ya fara kiran wayar Momy dan ya sanar da ita halin da mai gidanshi yake ciki , koda ya faɗa mata cewa tayi ko nazo ba abinda zan mishi dan maganinshi yana hannunshi ka nema ka zuba mishi a bakinshi , Kallon Dikko yayi yace Hajiya wannan ba irin waccan ciwon bane ba , tsoki tayi tare da kashe wayarta tana masifa cewa ni mutuwarshi bata wani hanani nayi rayuwata dan wanda ya mutu shi jin daɗi ya ƙare mawa danni a halin yanzu banda wani abinda ya isa ya tashi hankali na , mijina kawai zai kwanta ya mutu in tashi hankali ba Dikko ba , Ƙanwar shi daya zane jiya tace Momy miye ? Cike da masifa tace Dikko ne kinsan shi idan bai ɓatawa mutane rai ba hankalinshi baya kwanciya ni yanzu bazai sake tayarmin da hankali ba saidai ya tada ma ubanshi danni na gaji da iskanci shi , tunda na haifi Dikko duniya ya hanani in zauna lafiya dan yaga bana so ya shiga damuwa shi yasa duk hanyar da yasan zaibi ya tadamin hankali yasanta , Meya sameshi yanzu kuma Momy ? Ta tambayi mahaifiyarta cikin damuwa , tashi Momy tayi daga palon tana cewa koma miya sameshi cansu ta dama ba abinda ya dameni , ɗan uwa da ɗan uwa sai Allah duk dukan da Dikko yayi mata jiya ta manta dashi ta ɗauki wayarta ta fara kiranshi , Ashiru ya ɗauka tace ina Yaya ? Ashiru yace baida lafiya , Bashi waya mana , cikin damuwa yace ai baya iya magana , kamar ya baya iya magana ne ? Tayi maganar cikin tsawa , shiru Ashiru yayi tare da kashe wayar , wayyo Yaya...... Momy Yaya fa baya magana kuma an faɗa miki zakice ba ruwanki ? Daga ciki Momy tace ba ruwan nawa ke mai ruwa sai kije kiyi. Cike da tausayin ɗan uwanta ta fara kiran wayar Dady amma bai ɗauka ba ta kirashi yakai ×3 baya ɗauka kawai ta tura mishi text Yaya bashi lafiya ! Ashiru kuwa ya ɗako magani ya zuba² amma kamar ana zubashi a ƙasa Dikko ya ɗauke gaba ɗaya sai hawaye dake gangarowa daga gefen idonshi , cike da tausayi Ashiru yabi mai gidanshi da kallo yana tunanin tou wane irin sirrin ne yakeyi da Sultana da yace Allah kaɗai yasan tsakaninsu yace babu wanda yasan abinda ke tsakaninsu daga shi sai ita sai Allah , wannan wane irin sirri ne mai ƙarfi haka......? A wannan hali Dady yazo ya samu Dikko , fuskarshi ɗauke da damuwa yace ma Ashiru ya koma palo , fita Ashirun yayi Dady yabi Dikko da kallo bayan wani lokaci ya saka hannunshi a aljihu ya ɗauko wani garin magani ya shaƙa mishi a hanci tari Dikko yai tayi yana atishawa , saida ya ɗauki wani lokaci yana tari da atishawa sannan ya dawo dai². Cikin natsuwa Dady ya kalleshi yace Babana kana neman dai ka kasheni ko ? Ka hanani in zauna lafiya kullum jini na a saman akaifa ko wadataccen bacci bana samu kullum zuciyata a takure take banda walwala bare kwanciyar hankali wannan fitinar daka tsiro da ita ba kanka kake wahalarwa da ba , ni kake ba wahala duk duniya baka da jigon daya wuceni idan har ka bari wani abu ya sameni ko na mutu taka ta ƙare , Cike da ladabi yace kayi haƙuri na bari , Dady yace kai zan ba haƙuri , Dikko yace insha Allah bazan sake ba , Dady yace da ka taimaki rayuwata , saida ya tabbatar Dikko ya dawo hayyacin shi sosai ya tafi tare da jaddada mishi ya daina fushi da tunani tunda yasan baida cikakiyar lafiya , kuma yaje gida da daddare yana nemanshi , da kanshi yayi ma Dady rakiya har wurin mota saida ya tafi sannan ya dawo palo wurin Ashiru ya kwanta. Ni kuma ɗaki na koma na cire wayata daga jirgi na fara kiran wayar Dikko , duk kiran da nake mishi yana gani yaƙi ɗauka dan yayi alƙawari cewa sai nazo da ƙafafuwana na sameshi idan dai ya furta zaiyi ko zai mutu saiya yayi , tun ina kiranshi yana basarwa ƙarshe sai ya riƙa rejecting , nima na daskare naci gaba da kiranshi bayan wani lokaci ma kashe wayarshi yayi gaba ɗaya , Murmushi nayi maicin rai a bayyane nace ni zaka wulaƙanta ina kiranka ka kashe min waya nima har abadan duniya bazan sake kiranka ba na ƙarasa maganar tare da maida wayata a jirgi. Ranshi a ɓace ya kalli Ashiru yace zanyi tafiya zakaje ? Dariyar jin daɗi yayi tare da cewa mai gida zanje mana amma kace baza ka sake zuwa ko ina ba sai Sultana tazo , hmmm manta da An mata Dikko ya bashi ansa... Saida na ƙara yin kuka sosai sannan na sake cire wayata daga jirgi na ƙara kiran Dikko , har yanzu wayar a kashe take ci gaba nayi da kira har matar da ake jiran zuwanta ta iso amma Yaya DK bai buɗa waya ba , yayi fushi dani yayi tafiyarshi London ya manta dani , Sultana ....! Aka kira suna na daga palo da sauri na tashi na fita ba tare dana ansa kiran ba , gaishe da matar nayi bayan na samu wuri na zauna , ansawa tayi cikin sakin fuska tace sannu baiwar Allah , murmushi nayi mai ciwo dan yanzu duk duniya banda damuwar da tafi rashin Dikko a tare dani... Auntyn da tazo dani tace Yaya kinga kwalbar nan kallo ɗaya tama kwalbar ta kauda idonta tare da neman tsari daga azaluman mutane a wurin ubangiji , abin babu kyan gani gwanin tashin zuciya da tashin hankali , Auntyn da tazo dani tace tare da ita za'a tafi ne ? Yayar ta tace a , a cewa yayi kawai na anso kwalbar na kai mishi , Aunty tace gata nan , kwalbar matar ta ɗauka tare da cewa saina dawo zuwa jibin insha Allah , godiya Aunty tayi sosai wa "yar uwar ta , ita kuma ta tafi tana mai addu'a ubangiji ya yanke wahala. A daddafe nayi kwana ukku , ga ciwon mutuwar mahaifina dake nuƙurƙusar min zuciya , ga maraicin Dikko dake damuna gashi banda abokin fira kuma gidan ba'a fita gashi ni ban saba da Auntyn da tazo dani ba , abubuwa dai duk sun dameni na rasa inda zan saka raina naji sanyi , duk alƙawarin da nayi bazan sake kiran Dikko ba na kasa kullum saina kirashi kuma har yanzu wayarshi ya rufeta. Al' Ameen da yakai Jiddah ƙin dawowa yayi wai sai ranar da zata dawo zasu taho tare , haɗuwa sukayi sukaci gaba da gulmar Sultana yayin da Al ' Ameen ke cewa ai Sultana asiri tayi ma mai gida ta gama dashi danshi tunda yake duniya ma bai taɓa ganin mai gida yana shiga sabgar mace ba sai akan yarinyar nan , tayi mishi asiri na gani kasheni , idan dai kina san zaman lafiya ki miƙe tsaye ki fitsare ƙafafuwanki. Jiddah tace aini bansan ta ina zan fara ba , Al ' Ameen yace ina da malami a zaria zan kaiki amma karki fara neman mai gida dan ɓannar kuɗinki zakiyi saboda yana da addu'a sosai , banda toshewar basira irin na Jiddah yanzun nan Al ' Ameen ya gaya mata cewa Sultana ta nemi Dikko da asiri fa , amma ita yace mata kar ta nemi Dikko da asiri wai ɓannar kuɗinta zatayi , yaci gaba da cewa saidai ita yarinyar a firgitata a saka mata shakkun mai gida a zuciyarta , idan ta ganshi tayi kamar taga cici , Jiddah tace tou haka yayi yaushe zamu je ? Al ' Ameen yace bara inyi waya dashi saiya fitar mana lokaci da kanshi , Jiddah tace ngode Al ' Ameen da Allah ya haɗani dakai da na shiga gararin rayuwa , tayi godiya sosai shima ya gode tare da fitowa daga palonta , Bayan ya fito yayi dariya yace sakarar banza zan kaiki malam yayi ta ɗirka miki asirin da ke da kanki zakice mai gida ya sakeki , ina ansar taimako ina kaiwa Mardiyya insha Allahu sai mai gidana ya auri Mardiyya zuri'armur zasu fita daban yarinyar "yar uwata ta samu sa'ar rayuwa , ita kuma Sultana zamu goge labarin mai gida daga zuciyarta , shi kuma mai gida soyayyar da yake ma Sultana sai a juya sunan Mardiyya a kan soyayyar da yake ma Sultana , sai ya koma san Mardiyya wannan shine mafita , Yeeee wannan shawara tayi , yayi "yar rawa tare da taɓawa cikin farin ciki. *_London_* Dakel ya juya kwanciyar shi cikin yanayin gajiya idanuwan shi a rufe , miƙa yayi sosai yace An mata , saida ya gyara kwanciya yace duk ki gama yarintarki da duk abinda kika ga dama insha Allahu duk duniya baki da miji saini , buɗe idonshi yayi a hankali yaci gaba da cewa ni wallahi tausayi kike bani dana tuno na tattara fushi na da ƙarfina na sauke a kanki sai tausayinki ya kamani , tsoki yayi tare da saukowa daga saman gado yana cewa banso ranar tazo a haka ba , amma ya na iya yadda ubangiji ya tsara kenan. Toilet ya shiga bai wani daɗe ba ya wanko bakinshi da fuskarshi ya fito , Ashiru ne ya shigo cikin bedroom in ya miƙawa mai gidanshi waya wai Jiddah tana kira , ansa Dikko yayi ya kara wayar a kunnenshi tare da cewa inajinki , Cikin soyayya da gogewar kalamai tace haƙuri na kira in bada ranka ya daɗe , sai yanzu na gane nayi kuskure kishinka ne ya rufemin ido har na aikata abinda bakaji daɗi ba , amma ka gafarceni insha Allah haka bazai sake faruwa ba kayi haƙuri don Allah , waye ya faɗa miki bana nan ne ? Cike da ladabi tace Momy ta kira Hajiya tace kayi rashin lafiya , sai tace zata zo ta ganka shine Momy tace baka nan amma zata turo mata number ka ni kuma data turo saina ɗauka in bada haƙuri. Ajiyar zuciya Dikko ya sauke shima cikin kulawa yace ba komai ya wuce , tou Yaya zan koma dan Allah , a , a , haba Yaya ka rufamin asiri don girman Allah ka barni na koma , Dikko yace keyy..... Jiddah tace Allah baka lafiya yasa kaffara ne , yayi kyau ya ƙarasa tare da kashe wayarshi. Kallon Ashiru yayi bayan ya gama wayar ya nuna mishi hanyar fita da hannunshi , da sauri Ashiru ya fita shi kuma yaci gaba da tunanin An mata...... Kwance nake saman gado na ƙurawa wayata ido dan yanzu na cireta a jirgi kwata² ina tsammanin kiran Dikko ko wane lokaci , Yayar Aunty ce ta shigo dan sun daɗe suna kirana banji ba hankali ya tafi tunanin Dikko , dan na kalli hotonshi dake cikin wayar Aunty Mamy wanda Al ' Ameen yasa a d p inshi Aunty kuma ta ajiye hoton a ma'ajiyar hotunan cikin wayarta , nasha kuka har na gode Allah dan idan zan kalli hoton shi so goma sai nayi kuka sau adadin kallon da nake ma hoton. Dafani tayi na dawo a firgice tare da goge hawayen idona ina sauke ajiyar zuciya , murmushi tayi mai haɗe da cewa sannu , nima murmushin nayi na sauko daga saman gadon na gaisheta , ansawa tayi cikin sakin fuska tace muje tayi gaba nabi bayanta , A palo , Auntyn da tazo dani ce a saman keken guragun ta , sai Yayar Aunty sai wani babban mutum yasha rawani zubinshi dai irin na malam zaure ne , duƙusawa nayi na gaishe su cikin ladabi , cike da kulawa ya ansa tare da cewa sannu baiwar Allah , nace yawwa, Shi kuma yaci gaba da cewa cikin hukuncin ubangiji abinda ya faru shekaru da dama da suka wuce Allah ya bada iko cikin hukuncin sa da yaddarsa ya warwareshi , bamu yi ƙoƙarin bincike ba saidai nayi amfani da bayanin da Hajiya Suwaiba tayimin ya nuna Auntyn da tazo dani yaci gaba da cewa. Hajiya Mamy kafin ta rasu tace duk musabbabin abinda ya janyo wannan rikici da tashin hankali da jefe² duk sanadin ɗaukar budurcin matar Bello ne wanda shi Binna yayi a matsayin ɗaukar fansar abinda akayi ma yarinyar da ya zauna gidansu , Wannan dalili yasa shi Bello ya ƙwallafi marigayi Binna a zuciyarshi wannan itace ƙiyayyar dake tsakaninsu , kafin haka kuwa abinda ya shigo da Bello a rayuwar Binna shi ɗan uwan Binna wanda suke Baba ɗaya shine ya turo Bello a rayuwar Binna bayan mahaifiyarshi ta haɗa tuggun da mahaifinshi ya korashi daga gida , Taga ya tafi bai lalace ba shine ta tashi hankali su kuma "ya "yanta suka taimaka mata wurin ganin sun cika mata muradin ta na ganin Binna ya lalace dashi da ɗan uwanshi kuma babu abinda sukayi mata haka kuma mahaifiyarsu Binna batayi mata komai ba , da sukaji labari su Binna sun samu gidan aiki da ake kula dasu , shine suka nemi hanyar lalatashi wannan dalilin yasa suka tura Bello ya shigo rayuwarshi ya shanmace shi da sihiri ya samu damar afkashi a wasan caca kuma suka fidda ma Binna tunanin waiwayar gida , ana cikin haka ne kuma Bello ya lalatawa yarinyar gidan dashi Binna yake zaune rayuwa sai aka korasu , Bello kuma yajasu suka zama suna ƙarƙashin ikonshi har Allah yasa shi Bello yayi aure Binna ya ɗauki budurcin matarshi a daren ranar da ango zai shiga ɗaki. Daga nan sukayi faɗa na tashin hankali suka rabu , bayan rabuwarsu ne "yan uwan Binna suka tura Bello akan kar ya sake ya yadda ya nemi Binna ya bashi haƙuri idan ya dawo rayuwarshi shima ya ɗauki fansa akan kaff ahalinshi , Haka yabi kaf ahalin Binna yaci gaba da jifarsu , amma saiya lura hankalin Binna baya kansu bai kuma damu da lalacewarsu ba , yaci gaba dai bai daina ba har Allah ya kawoki kuma mahaifinki ya ci buri akanki kuma yaso kiyi ilimi mai zurfi ganin Binna dai ya ɗauki soyayyar duniya ya ɗora miki yasa Bello ya juya akalar tsafinsa akanki shine yaje yayi wannan tsibbacin nasa wanda kuma ubangiji ya kawo ƙarshenshi da izininshi da yaddarshi kuma an warwareshi , ga magunguna nan Hajiya zata faɗa miki yadda zakiyi amfani dasu. Gyara zama nayi na kalli Hajiya Suwaiba nace Aunty da kika kirani kince an tafi a kashe Babana su waye suka tafi kashe shi ? Kuma ke me kikeyi a wurin lokacin da kikemin waya me yasa kikayi ihu bayan ke kuma na ganki baki da ƙafafuwa ya akayi kika je wurin..........? Cike da damuwa tace bani bace kikayi waya dani , yadda kika ga wannan kwalba da wannan waya da na kiraki da ita ina kwance a saman gadon asibiti Allah ya kawo min matar da kikayi waya da ita batamin bayanin komai ba tadai bani wayarta tacemin amana ce aka bata kuma itama ta bani amana , tabbas tamin maganar Mamy idan baki manta ba da kika zo asibiti ai kinji nace miki ina Mamyn take ? Bansan Mamy ba amma matar ta nunamin hoton Mamy a cikin wayarta , Wannan bawan Allah kuma da kike gani itace tace in duba cikin wayar ta zanga lamba an rubuta malam ɗayyu inyi ƙoƙari na nemeshi shine zai kawo karshen matsalarki domin tamishi bayanin komai , ni banda ƙafafuwa shi yasa na kira "yar uwata bayan ni nayi waya dashi malam ɗayyu ya faɗa mana mazauninshi shine na tura Yayata takai mishi kwalbar , Idona cike da hawaye nace shin ina ita matar data baki wayarta da kwalbar nan take ? Aunty Suwaiba tace bansan inda take ba domin tana saƙamin a cikin bargon da nake lulluɓe dashi naga wasu mutane sun shigo suna nemanta ita kuma tabi ta wata hanya ta fice , ba'a sallameni ba gudun bi baya yasa nima na baro asibitin dan bana san rayuwata ta sake komawa cikin matsala. Kai ׳ innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , Allah ngode maka ubangiji ya bayyani min duk masumin wannan bita da ƙulli , an kashe Aunty Mamy , an kashe Babana ita kuma wannan tana raye ko tana mace oho ? Ya zamar min dole nabar gidan baiwar Allah nan da bata san sake mayar da rayuwata a damuwa ita kuma meya faru da nata rayuwar ? Kallon malam ɗayyu nayi tare da cewa shin ko kasan inda gidansu Babana yake ne ? Yace yasan gidan a katsina yake ƙofar marusa , nace kai a wane gari kake ne ? Yace katsina yake , miƙewa nayi tsaye tare dayi ma Aunty Suwaiba godiya na koma ciki na tattaro wayoyina ina dawowa palo nace ma malam ɗayyu muje katsina. Miƙewa yayi tare da tattara magungunan daya zo min dasu yayi gaba , ni kuma na duƙa a gaban keken guragun ta nace Aunty ngode sosai zan tafi amma zan dawo domin ina sha'awar jin wace irin rayuwa ce kikayi ta baya wacce har baki so ki sake komawa cikinta , miƙewa nayi tare dayi ma Yayarta sallama na fice daga palon ina kewar mutanen kirki irinsu Aunty Suwaiba amma tabbas akwai dawowa bayan kowa ya ajiyewa kowa lambarshi a cikin wayarshi...... Ƙarfe 7:43pm acikin garin katsina tayi mana wanda malam ɗayyu shine ya jawo motar tun daga daura har zuwa cikin birnin garin katsina , kai tsaye ƙofar gidan su Babana muka tsaya , ina ƙoƙarin fita daga motar naga Baban Hafsa ya fito , kallonshi nayi sosai yayin da Bello ke biye bayanshi , kallon malam ɗayyu nayi nace lallai² nan gidansu Babana ? Yace shakka babu wannan shine . Dogon nazari na tafi anya Baban Hafsa yasan ni ɗiyar ɗan uwanshi ce kuwa ? Da babu Bello dana sauka nayi masa magana na gani ko zai ganeni ? Kenan wannan shine dalilin da yasa Mamy tace da Binna yasan wace ce Hafsa a wurinshi da ya haɗiye zuciya ya mutu , a bayyane nace ummm tare da taɓe bakina naci gaba da cewa ƙaddara da ajali ba'a kauce musu tou amma kuma meke tsakanin Hafsa Amisty da Babana ? Wannan ansa banda mai bani ita itama. Daga gidan su Baba gidan Baba Ƙarami muka nufa na nuna masa zan zauna ne zuwa wani lokaci amma saboda tsabar shi butule ne ya manta da irin karamci wanda mahaifina yayi mishi ya shafawa idonshi kwallin rashin mutunci yayi min wulaƙanci na ƙarshe tare damin gori karuwar banza karuwar wofi wacce ubanki ya mutu a gidan caca. Kallon Baba Ƙarami nayi ƙasa da sama nace aiko caca ta gama maka komai tunda harya ciyo gida ya baka kake zaune dan na tabbata da "yan uwana sunsan wannan magana wallahi da sai sun ƙwace gidan nan sunce na magada ne , kuma da kake cewa ya mutu a wasan caca kai kaga yadda taka ƙarshen tazo maka ne ? Kuma da kacemin karuwa inda na gode Allah tambarin ba a kaina kaɗai yake ba kaima kana da taka karuwar zaune a gida. Cikin hayani yace ni ban haifi karuwa ba kuma bazan haifeta ba har abadan duniya idanma nasan ina da karuwa a gidana saina kashe ta ko an faɗa miki ni lusarin ubana ne ? Nace shima uban nawa ba lusaranci ya janyo mishi haka ba ƙaddara ce kuma babu wanda ya isa ya goge ƙaddara , haka kuma shiriya ba iyawar kowa bace ba daga Allah ne kuma na rantse da Allah idan baka barni na zauna gidan nan ba saina nemo "yan gidanmu sun anshi gidan ubansu tunda ba takadda ya rubuta ya baka shi daga duniya har lahira ba , Matanshi suka sako baki wallahi bazan zauna musu gida ba na lalata musu tarbiyar "ya "ya inji maman safiya , kallonta nayi nace aike taki ta daɗe da lalacewa ko kina tunanin bansan komai ba ? Naci gaba da cewa ƙofar soro , asibitin da akayi komai ke hatta gidan da aka samo tukuicin da niƙaf taje , da sauri Safiya ta tashi tayi cikin ɗaki , uwarta ko ta kama bakinta bata sake magana ba gudun kar in tona mata asiri a gaban kishiyoyi , Tunda abokan zama sukaji haka kowa ta fara ɗakinta zan zauna sarai na gane dan suji labarin abinda Safiya tayi amma sam nace ɗakinsu Safiya zan zauna , uwar Safiya kuwa bata sake magana ba shima Baba Ƙarami ɗaureren azumin magana ya ɗauka , waje na koma wurin malam ɗayyu na anso magunguna na bayan yamin bayani duk yadda zanyi amfani dasu , godiya nayi masa na anshi lambar wayarshi tare da cewa saina shigo. Satina biyu a gidan Baba Ƙarami na kammala kaf magungunan da Malam Ɗayyi ya bani , natsuwa ta shigo cikin kaina tsoron Allah da gudun duniya ya dawo amma kaf iskancin da kuka sani yana nan ɗibge akaina saidai idan ba'a latsomin wurin ba , Ranar dana cika sati biyu cif ranar na ɗagawa Baba ƙarami hankali saiya maidani makaranta , yace min baida kuɗi nace aiko ni ba'a gayamin babu duk inda zai samo kuɗi saiya samosu ya maidani makaranta , yacemin wallahi baida inda zai samosu , dole na haƙura amma na yanke zan kira Alaji in jaraba sa'a na gani ko an dace amma kafin nan zan koma islamiya in fara hadda. Da daddare na tambayi Baba Ƙarami ƙarfe nawa yake rufe gida ? Yace min ƙarfe 10 idan har goma ta wuce koda minti ɗaya ne saidai mutum ya kwana waje , nace tou babu damuwa , saida nayi alwallah sallar isha'e na kira Alaji nayi masa kwatancen gidan Baba ƙarami nace mu haɗu dashi yanzu da Allah ina san ganinshi yace yana zuwa. Ban daɗe da gama sallah ba yazo , bayan na fita ko gaisawa bamuyi ba nayi masa kwatancen wurin da Baban su Hafsa yake zama nace masa can zaka kaini , ya tada mota muka tun kari wurin kai tsaye.... 12/0/10/2019 *JAMILA MUSA...*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 54 Har muka isa daga ni har Alaji babu wanda yayi ma wani magana a cikinmu , kuma munyi sa'ar samun Baban Hafsa kamar dai yadda nayi tunanin dama zamu sameshi , gabansu nasa Alaji yayi parking ban fito daga cikin motar ba na sauke gilashin gefe na tare da cewa Assalamu Alaikum.... Cikin farin ciki ya ɗago daga latsa wayar da yakeyi jin muryana , ba tare daya ansa sallamar ba yace Hajiyata da kina duniyar nan ? Kin kama waya kin rufe ruff , saboda kunsan layina na farko Dikko ne ya karya shi , nace Ey wallahi , tasowa yayi daga cikin mutane yana kaucewa inda babu jama'a cewa fito kiji mana. Fita nayi daga cikin motar nabi bayanshi bayan wata container dukanmu muka tsaya , kusa dani ya matso sosai ya riƙemin ƙuguna magana ƙasa² yayi cewa haba ina kika ɓoye haka kika barni ina ta garari a garin nan na rasa ina zan samu labarinki ? Shiru nayi ban bashi ansa ba kuma ban cire hannunshi daga riƙo da yayi min ba , Yace ya na ganki duk rai a haɗe ko anyi miki wani abu ne ? Ajiyar zuciya na sauke tare da cewa Binna , me Binna yayi miki ne ? Neman sa nake saina ga bayanshi , kashe shi zakiyi kenan ? Nace tabbas kuma ba gudu babu ja da baya , amma me yayi miki haka da ciwo wanda kikayi ƙudirin ɗaukar fansa rayuwarshi haka babu sassauci.....? Cikin ƙunar rai nace shin ko kasansa ne ? "Yar dariya yayi ta duniyanci sannan yace ai wani ya rigaki shafe labarinshi a duniyar nan , ɗago kaina nayi na kalleshi nace wane mai zarra ne haka wanda yafi mace zafin nama ? Baban Hafsa yace abin duhu ne amma ke wane irin duhun ya baki na rayuwa haka ? Sauke hannunsa nayi daga riƙon da yayi ma ƙuguna nace , shin wai da kake tambayana duhun da Binna ya bani kama san waye Binnar tukunna ? Ni kuwa nasan Binna domin Babanmu ɗaya dashi , kamar walƙiya haka naji duniya ta juya , cikin dakiya nace amma kasan ɗan uwanka ne ka barni nake furta kalmar kisan sa daga bakina ? Sake rungumoni yayi ya rumgumeni sosai , kunsan akwai runguma akwai rungumewa tou rumgumewa yayi ya kwantar da fuskarshi a saman ƙafaɗata , hawaye ya cikamin ido wato wannan shi Yayan Babana ne ? Goge hawaye na nayi tare da saita muryata nace me yasa bakwa zuminchie da Binna ne ? Har yanzu yana kwance a saman jikina , cikin disashshiyar murya yace aishi kanshi Binna bai isa yasan ni wayen shi ba bare kuma "ya "yanshi , banma san gidan da yake zama ba amma kaf rayuwarshi da duk wani motsinshi a tafin hannuna yake , Amma me yasa ka sakawa rayuwarshi ido bayan kuma ya fita daga rayuwarku ? Ai bashi ya fita daga rayuwarmu mune muka fitar dashi , akan wane dalili ? Ɗago kanshi yayi tare da sunbata ta yace labarin yana da tsayi ni kuma na yanke miki wahala tunda an sheƙar miki da Binna zuwa duniyar mutuwa... Murmushi nayi mai nuni ina farin ciki amma a baɗinance ina cikin tashin hankali , ƙarfin hali nayi tare da cewa labarin yana da tsayin gaske amma duk meye musabbabin fitinar taku ne.... ? Murmushi yayi tare da shafa gefen fuskata yace keko kuɗi ne silar komai , yanzu dai zamu ɗan rage dare ne ko yadai.... ? Share maganar nayi da cewa wai kasan "ya "yan Binna kuwa ? Taɓe baki yayi cewa shi kanshi Binnar dakel na sansa bare wasu "ya "yanshi can na wahala , dariya nayi nace tou ina da sharaɗi ɗaya tak zanyi tarayya dakai amma duk wata so ɗaya ka yadda ? Yace Eh na yadda , nace yau nawa ga wata ne ? Ya faɗamin , nace tou ni bana zini a farkon wata da tsakiyar wata sai ƙarshen wata kuma shima ƙarshen wata sai daren da wata zai fita haka yayi maka ne ? Eh na yadda nace tou idan Allah ya kaimu gobe dani dakai mu haɗu a *Erudite comprehensive sch*. Me zamuyi a makaranta kuma ? Zubin adashe zaka fara dan zan koma makaranta ne kuma itace makarantar da nake so , sabon machine uniform littafai da duk abinda makaranta ta buƙata zaka biya ne sai ka biyamin kuɗin makaranta tun daga aji 1 zuwa aji 3 idan haka yayi maka mu ƙulla tarayya dakai bana san surutu ka kame bakinka kayi shiru abinka kamar yaro ya kama nonon uwarshi.... Zai sake magana nace yi haƙuri 9:44pm zan tafi gida ana rufe mana ƙofa 10:00 , mu haɗu makarantar idan Allah ya kaimu gobe misalin 12:30pm kuma karka zo da aboki ko ɗan rakiya , ina faɗin haka na wuce da sauri na koma cikin mota Alaji yaja muka tafi... Tunda na shiga motar wasi² nakeyi kenan Hafsat "yar uwata ce da Baban Hafsa da Babana babansu ɗaya ? Tou wane irin sirri ne kuma Aunty Mamy ta ɓoyemin wanda tace da Binna yasan matsayin Hafsa a wurinshi daya haɗiye zuciya ya mutu ? Tunani nayi mai zurfi zuciyata ta faɗamin cewa ko shima Baba kwarto ne ? Da sauri nace astagafurillah , ita kuma Amisty ya muke da ita ne ? Hmm Allah ka iya mana , 9:57pm a ƙofar gidan Baba Ƙarami tayi mani nacewa Alaji yayi haƙuri yaje zamuyi waya idan na shiga ciki yace tou , kuɗi ya bani har 10k ina san Alaji ko ba komai akwai kyauta , godiya nayi na shige ciki , ina shiga Baba Ƙarami ya fara banbamin bala'e daga gidan uwar wa kike a tsohon daren nan ? Balbaɗaɗɗa irin iskanci da kika saba a gidanku idan kikace zakimin shi nan saidai ki tattara ki kama gabanki "yar iska karuw...... Kuɗin hannuna na miƙa mishi duka sai yaci gaba da cewa Allah yayi miki albarka ubangiji ya ƙara koro kasuwa yasa kifi haka matsayi. Ban mishi magana ba nayi cikin ɗaki , maman safiya kuma tace sai ki kwashe duka ki bashi ai ya kamata ma ki riƙa biyan kuɗin hayar ɗakin nan , ko inda take ban kalla ba na kwanta tare da saka airpiace a kunne na ina sauraron firata da Baban Hafsa , bayan na gama ji tass nayi murmushi tare da kiran wayar mutumina amma a kashe take har yanzu , saida na kalli hotonshi sannan nayi bacci. Jiddah da Al ' Ameen zaune a gaban bokansu ya kwarara ihu tare da ɗirkaka uwar ashariya bayan duk sun kora mishi bayani , roƙo na farko abinda aljannu suka buƙata shine a basu jinin jariri sabuwar aihuwa , matakin farko kenan , mataki na biyu kuma idan ba'ayi wannan ba ita Jidda zata kawo jinin al'adarta , mataki na ukku shine za'a kawo maniyin Dikko , wane kuka zaɓa ne ? Boka ya tambaye su , Cikin rawar jiki Jiddah tace haba a ina za'a samu wani jinin jariri ne ? A daina maganar jariri gaskiya , wata irin dariya bokan yayi mai firgitarwa , yace arne zaisha jini ne shine zai shiga zuciyar ita yarinyar ya sanya mata wasi² , idan kuma kika bayar da jinin al ' adarki duk duniya yadda Dikko zaiji maganarki ko ta uwarsa bazaiji haka ba , idan kuwa aka kawo maniyinsa labarin yarinyar ya goge a zuciyarshi kwata² har abadan abada zaima manta daya taɓa sani wata yarinya wai ita Sultana , bazai sake san wata mace ba sai ke , ke ɗaya ke ya sani kuma ke zaiyi ta ƙauna har a mutu , Hahahahaha..... Jiddah tace boka aini yanzu bana tare dashi ya koroni gida yace sai yaga ita Sultanar zan koma kuma babu wanda yasan ma inda take zaune a halin yanzu dan ita mahaifiyar Dikko tace tabar katsina kwata² , dariya bokan yayi sosai sannan ya ɗaga hannunshi daga gefen shi yace tana katsina gata nan , lafiya lau aka nuno hoton Sultana kwance , Jiddah tace Eh wallahi itace , itace boka , dariya yayi tare da ɗaukar kaza ya wurga sama cikin seconds ta dawo ƙasa har an tsotse mata jini , Jiddah ta firgice sosai boka yace idan har kika faɗa masa tana katsina sai ya dawo , idan ya dawo daga nan komai zai tafi mana a sauƙaƙe , Al ' Ameen yace haka za'ayi ranki ya daɗe kinga idan kika samu kika samo sai ki bani ni kuma sai nazo na kawo ko ? Jiddah tace Eh , tadai daɗe tana faɗawa boka yadda take san aikin ya tafiyar mata yadda take buƙata , da suka tashi tafiya ta yayyafawa boka ruwan kuɗi shi kuma ya watsa kuɗin sukayi sama..... Koda suka koma gida Al ' Ameen sai ƙara jaddadawa Jiddah yake tayi ƙoƙarin samo sperm in mai gida idan aka goge ko wace mace a zuciyarshi aka sakata ai taci lafiya , Jiddah tace ai yanzu wanka zanyi na kirashi , Al ' Ameen yace ki bada himma dai karki tsaya sanya , tace insha Allah , sallama yayi mata ya fice daga palon , Yana fita ya kira Mardiyya , bayan ta ɗauka yace doughter nasara tana ƙara tunkaro ahalinmu , lallai ke mai nasara ce kuma kece tauraruwarmu gaba ɗaya , fitila mai haskawa amarya a gidan mai gidana , dariya Mardiyya tayi tare da cewa Uncle ya ake ciki yanzu ? Al ' Ameen yace boka yasa a samo masa sperm in mai gida kuma na faɗawa boka yadda zaiyi kinga ina kai masa za'a goge Jiddah a goge banzar Sultana , filin zuciyar mai gidana naki ne ke ɗaya my doughter , Mardiyya tace godiya nake Uncle Allah ya taimake ka ya bada sa'a , Al ' Ameen yace am3n. Sukayi sallama ! Koda Jiddah ta faɗawa Dikko Sultana ta dawo katsina cewa yayi da kyau , ta tambayeshi ranar da zai dawo yace shi daga nan ma gaba yaci , tace haba Yaya nidai tunda an ganta ya kamata kayi haƙuri ka dawo , Dikko yace kiyi wata maganar bana san wannan , Jiddah tace dawowa na ne baka so ko kuwa zancen Sultanar ne yanzu baka so ? Tsoki yayi ba tare daya bata ansa ba ya katse kiran , Yana katse kiran Jiddah ya fara kiran mai gadinsa na goruba gidan daya ajiye Sultana , bayan sun gaisa Dikko ya tambayeshi ko An mata tazo nemansa ne ? Yace A , a , gaskiya bata zo ba , katse kiran yayi ya kira Umar yace masa An mata ka ganta ne a katsina ? Umar yace gaskiya bata dawo ba , shima katse kiran yayi tare da cewa "yar ranin hankali ashe kinga dama kin dawo , hmmm kedai kika sani mara aikinyi kuma aradu bazan kiraki ba. Washe gari bayan na gama duk abinda nakeyi na kira Aunty Suwaiba muka gaisa , nayi mata sannu da jiki ta ansa cikin farin ciki da faɗamin tayi kewata , nace mata insha Allah ai zanzo , tace Allah ya yadda , nace ko Aunty ta kira waya ne ? Aunty Suwaiba tace har yanzu dai shiru gaskiya bata kira ba saidai wata number ake ta kiran wayar da ita , nace kin ɗauka ne ? Tace tunda naji namiji ne ban sake ɗauka ba , ki turomin number , Aunty Suwaiba tace a , a gaskiya Sultana kiyi sabgar gabanki ki fita daga rayuwar wani zaƙule² , Aunty turomin number da Allah , Aunty Suwaiba tace gaskiya bazan turo ba , juyin duniya nayi amma taƙi haka nan na gaji na haƙura mukayi sallama. Dani da Baban Hafsa dukanmu 12:30pm a cikin makarantar tayi mana , a napep nazo bayan na iso na anshi kuɗi a wurinshi na sallami mai abin hawa , daga nan kuma muka ɗunguma zuwa Ofishin shugabar makaranta , bayan gaisuwa Baban Hafsa da kanshi yayi bayani tare da nema min gurbin karatu a makarantar , duk dai abinda ya kamata shine yayi , duk wani rubuce² shine ya cike komai da hannunshi da sunan MARYAM ALIYU , Bayan ya gama ya tambayi shugabar makaranta shin ko zai iya biyan kuɗin makaranta na daga aji 1 har zuwa 2 tace anayi zai iya kuma ta ƙara masa da cewa ana shiga aji dan koyon karatu na musamman bayan ɗalibai sun tashi , extra lesson , tambayana yayi ko ina ra'ayi nace masa ina so , gaba ɗaya akayi lissafi yayi mata transfer kuɗin zuwa cikin asusun makaranta , Ranar da zan fara zuwa makaranta aka faɗamin fita nayi daga ofishin na basu wuri domin su ida abinda suke san kammalawa , bayan sun gama ya fito dani dashi duka wurin motarshi muka nufa , bayan munje muka buɗe kowa yayi ma kansa mazauni. Bayan mun zauna yace min Hajiyana gaskiya baza ki hau machine ba wurin zuwa makaranta , motar makaranta zata na zuwa tana ɗaukarki , sch bus , nace kuɗi ne baka da ko a ina matsalar take ne ? Yace ina da kuɗi kawai dai girmanki ya wuce ki hau machine , faɗuwa gabana yayi kardai yaga hotona a lokacin da akayi ta yamiɗiɗi dani a social media lokacin da Dikko ya bani motarshi ? Dakewa nayi nace shin wane irin girma ne kake gani ina dashi wanda har kake tunanin nafi karfin hawa machine ? Jawoni yayi jikinshi yana cewa aike babbar ƙaddara ce samunki sai namiji mai babban rabo , tarayya dake kuma sai jarumin namiji irina , matsayinki da darajarki saima kin ɗora mutum a linzaminki zai tabbatar da haka nine zan tabbatar idan har muka keɓe na samu nasarar taka ruwan cikinki , murmushi nayi tare dayi mishi kallon ɓatacce. Lalube jikina ya farayi , kallon sakarai nayi masa tare da ƙara ƙureshi da ido sosai yanzu na tabbar da ɗan uwan Babana ne dan naga kamarshi da Baba harta ɓaci wallahi kuma sai yanzu na fahimci maganarsu iri ɗaya sukeyi yanayin kallonsu da komai dai iri ɗaya saidai shi Babana yafi shi haske sosai kuma yafishi hanci da ƙaramin baki amma gadai jinin nan yana yawo a jikinshi. Hannunshi ya tura cikin rigata tare da ƙoƙarin haɗa bakina da nashi na riƙe hannunshi na kauda fuskata gefe ɗaya idona ya cika da hawaye dan wallahi kallonshi nakeyi kamar Babana , cijewa nayi cikin jarumta nace kar ka manta da nace maka bana ci sai ƙarshen wata , ƙara riƙoni yayi yana cewa tou ai ba cewa nayi zanyi ba koma zanyi kina tunanin zanyi a mota ne ? Kuma a motar ma tsakar gari da tsakiyar rana ? Murmushi nayi tare da cewa ai ba matsala bane ba ra'ayinka ne cin duk abinda kake buƙata yayin da yunwa ta taso maka dan ba'a tarar abinda za'aci a dai² irin lokaci buƙata ɗaya kawai aji ciki yayi nauhi , Kin san da haka tou kike ta wahalar da rayuwata ? Kika ɓace min ɓat kuma da kika dawo sai kika zo da wani tsarin banza , jifa yanzu ko hidimar da nayi miki ai ya isa ki bani tukwuici mana , tou kayi min gori ka biyamin kuɗin makaranta , a , a ba gori nayi miki ba ina so dai kisan yadda akeyin halakkaci da sakayyar farin ciki yayin da akayi maki karamci ya ƙarasa maganar tare da haɗe bakina da nashi wuri ɗaya zuyzuy ya riƙa lashewa yana tsotsewa wani irin ihu nayi tare da cewa nace bana so wai kai maye ne iye ? Dariya yayi irin dariyar Babana yace maye ne ni mana , kin taɓa ganin namiji ba mayen mace ba ? Duk uztazancin namiji duk imanishi duk haukarshi ko hankalinshi duk talaucinshi ko arziƙinshi duk wani matsayi da yake taƙama dashi mace ce remote control inshi , ke yaufa duk masifarki saina sha wannan dadɗan bakin naki wallahi , matsowa yayi daga saman kujerar da yake zaune yayi sosai dan sai zuƙewa nakeyi inayin baya amma maye ɗan mayyar saida ya jawoni ya ƙara lasar bakina , cikin kuka nace haba Bab..... Kimace Baban ai na isa in haifeki tunda yarinyata ta huɗu ma nasan zata girmeki amma dady suke cewa. Kema sai kice Dady daga yau.... Cikin kuka nace dan Allah ka daina irin wannan abun mana ! Ai yanzu na fara miki irin wannan abun dan ni daɗi nakeji idan inayi miki , haka zamuyi dake ƙarshen watan iye ? Haka zaki ta ihu kina kiran Dady har maƙota suji kukanki ? Fuskata kaca² da hawaye nace tou ka bari sai ƙarshen watan yayi mana ka bari ƙarshen wata yazo idan bakayi abinda kake so ba sai kacemin marowaciya ce ni mana , Allah ya taimakeni yace Allah ya kaimu yayi maganar tare da gyara rigarshi ya gyara fuskarshi dana daƙune hawaye , Ajiyar zuciya nayi a lokacin daya fara tafiya da motar yana cewa ina zan ajiyeki ne ? Ajiye ni kasuwa , me zakiyi kasuwa ? Yayi tambayar yana kallona nace hijabi zan siya , sai me kuma ? Nace shikenan , yace tou a siyo hada niƙaf dan banasan ayi ta kallemin wannan kyakkyawar fuskar mai ɗaukar hankali ya karasa maganar tare da shafo fuskata nace tou , Har muka zo kasuwa daga haka babu wanda ya sake magana sai shashshekar kukana dake tashi kaɗan² , bayan ya ajiyeni kasuwa ya bani 30k yana cewa sun isheki ? Da sauri na buɗe mota nayi gaba ko ansa ban bashi ba , murmushi yayi tare da bin Sultana da kallon mai tattare da tsantsar so , saida ya daina hangota ya wuce yana mai addu'ar Allah ya bashi sa'ar "yar yarinyar can ya more abunshi..... Ta bayan kasuwa nabi na fice daga kasuwar ina ta kuka tare da goge bakina wai Yayan Babana shine yake haɗa bakina da nashi har yake addu'a Allah ya bashi sa'ar hawa saman ruwan cikina ? Wayyo Allahna wai meya haɗa wannan bala'e wanda yasa "yan uwa suke cuɗanya da "yan uwansu babu wanda yasan matsayin kowa , wayyo Allahna Aunty Mamy me yasa tun farko baki faɗamin abinda ke tsakanin Babana dasu Amisty ba ? Juyawa naji garin yanamin , Malam Ɗayyu ya faɗomin a rai dan haka na fara kiran wayarshi ! Bayan ya ɗauka muka gaisa nace Malam kamin bayanin abinda ka sani akan abinda ke tsakanin Babana da Bello tou ko kasan dalilin da yasa matar Babansu Babana ta kori su Baba daga gidansu ? Malam Ɗayyu yace a , a , nace Aunty Mamy ta faɗa maka tsakanin Amisty Hafsa da Babana ? Karka ɓoyemin komai ka faɗamin abinda ya riga ya wuce ya wuce ka faɗamin meye tsakanin Babana dasu don Allah........? Malam yace Eh gaskiya abinda mariganya ta cemin shine , tace shi Bello yace yana san ya jefe ƙiyayya mai girma a tsakanin ahali ɗaya duk akan fansar budurcin matarsa da Binna ya ɗauka a ranar da yake tunanin itace ranar sa ta farko a angwanci , shine yayo dillacin ita Hafsa da Amisty wadda ita Amistyn da Baban shi Binna da Kakan Amisty suke Baba ɗaya , da sauri nace tirrr da wannan ahali , malam bana san sanin zuminchie su sauran bincike da sanin dalilin da yasa aka kashe min Babana da wanda suka kashe shi bana kowa bane nawa ne , miye tsakanin Babana dasu Hafsa ? Malam yace muradi ne , nace wayyo Allahna wane irin muradi Malam ? Malam yace muradi wanda baya buƙatar kawaici kunya ko kara , tirrrr Allah ka tsinewa Bello albarka tsinannen Allah ubangiji ma bazai barka ba kuma nima bazan barka ba da zaran na gama haɗa abinda nake buƙata ƙaryarka ya ƙare aihuwar asara ban yafe maka ba kuma kada Allah yaba uwarka ladar aihuwarka , kashe wayata nayi tare da dafe goshina da hannun damata kaina naji yanamin ciwo kamar zai faɗo ƙasa , Aunty Mamy tayi gaskiya da tace gaba ɗaya ahali sun zama *KWARATA...*. Baba ya nemi Amisty kuma ya nemi Hafsa , ɗiyar Yayanka , da ɗiyar shi ta zumincin Allah , kowa mayunwanci ne duk wanda aka bashi saiya ansa yaci babu mai haƙuri inama anfanin irin wannan muradi , yanzu nima gashi Baban Hafsa yana muradina a hayaniyance nace ni kuma ba muradikanka nakeyi ba dukiyar da tasa mahaifiyarka ta lalata zuminchie itace muradina kuma saina ga bayanta kaf saina mayar daku faƙiran ƙarfi da yaji , tunda har tayi sanadin lalacewar zuminchie ta fasa kan "yan uwa saina tarwatsa komai har gobe dai zata rayu da taƙaicin *BINNA* kuma saikin mutu da nadamar sanin *BINNA* , kun kashe maciji amma baku sare kanshi ba , kun kashe *BINNA* amma baku sani ba *BINNA* yana nan a saman doron ƙasa na ƙarasa maganar tare da buga ƙafata ƙasa , sai kun mutu dukanku da baƙin cikin *BINNA* domin Binna ya dawo daga duniyar mutuwa......... A sassauce nace koma miye yasa kuka korashi daga duniya kuma sai kun tafi baku ci koma miye ba kuma haka zaku tafi ku barshi kunaji kuna gani... A gajiye na koma gida zuciyata cike da masifu iri² , a ƙofar gida na samu Baba ƙarami zai fara magana na bashi kuɗina kaff amma bai ansa ba yace ki tattara naki ya naki ki kama gabanki domin zamanki a tare dani babban haɗari ne da kuma barazana a rayuwata , cike da ladabi nace yanzu kuma laifin me nayi maka ne ? Idonshi cike da hawaye yace babu abinda kikamin amma yau duk mutumin dake anguwar nan babu wanda bai shiga tashin hankali ba da ɗimuwar rayuwa ba sanadinki , Ƙara tausasa muryata nayi cikin kuka nace sanadina kuma Baba ? Nida bana nan me kuma ya faru ? Baba yace wasu mutane ne suka zo ni banma taɓa ganin irinsu ba sai yau suka shigo anguwar nan sai hauka sukeyi sukayi ta harbe² suna nemanki duk gidajen anguwar nan babu gidan da basu binke ba suna nemanki , nace su waye su ? Hukuma ce ko kuwa "yan gani na iya ne ? Baba yace koma "yan waye ki tafi daga anguwar nan dan zasu iya dawowa ko wane lokaci , murmushin ƙarfin hali nayi tare dayi ma Baba godiya na wuce...... Ina tafiya ina nazari , babu yadda za'ayi Bello ya fito fili yasa a nemo mishi ni saboda ta ƙarƙashin ƙasa yakeyin cutarsa kuma idan ma banda wata sahihir sheda babu yadda za'ayi nayi shara'a da Bello , tou wane sabon abokin gabar ne ya ɓullo haka a lokacin da abubuwa sukayi ma kaina yawa ? Wata zuciyar tacemin Mardiyya ce , kaina na girgiza tare da cewa a , a , Ummu Affan ce ? Ba ita bace , su Amisty ne ? Um ummm basu bane ,Momy ce , tabbas itace tunda dama tace idan aka sake gani a garin katsina aka faɗa mata zatamin tire² tabbas itace ba kowa ba , wallahi itace ma , dariya nayi tare da cewa nayi gidan ɗanki kije can ki kamoni , na karasa maganar a dai² lokacin dana tsaida napep nace mishi kaini goruba road. Tafiye muke a napep ina kiran wayar Dikko a kashe dai take har yanzu , amma ina mamaki ya akayi Momy tasan nazo katsina ? Murmushi nayi koma dai miye na tafi wurin Dikko naga yadda za'ayi dani dan na lashi takobin zama katsina ko za'a kasheni , tunani dai iri² a zuciyata muka isa goruba road 1k naba mai napep saboda babu canji , yana wucewa nima na shige gidan , Gidan a buɗe yake , gaisawa nayi da mai gadin na wuce ciki , palon kuma abokan Dikko ne cike wasu nacin abinci wasu kuma hankalisu yana kan tv suna kallon boll duk yadda akayi Dikko yana nan ko kuma zaizo dan ba'a irin wannan zaman sai idan yana nan ko kuma idan zai dawo daga tafiya , Banma kowa magana ba na wuce ciki kuma suma babu wanda yayi min magana dan ko sallama banyi ba , ɗakin da nake zama na wuce na shiga da sallama , yana nan dai yadda nasanshi tun farkon farko , kayana a gefen katifa lulluɓe kamar dai yadda aka saba lulluɓesu , zama nayi gefen katifa na rufe wayata na ɓoyeta dan idan har Dikko yazo nasan zaiyi bincike , kuma bana buƙatar yasan matsalar data shafi ahalina da rayuwata saboda wata rana dan bansan inda abun zai tsaya ba , kuma babu wanda yasan abinda gobe zatayi sai Allah , Rufe ɗakin nayi na wuce bayi nayi wanka bayan na fito na canja kaya , kwanciya nayi naci gaba da tunanin rayuwa irin tawa , sai kuma su Amisty suka faɗomin a rai ko sun daina karuwanci yanzu ? Allah sarki Hafsa har tasan Babana ya gogeta taso ita da Amisty su gurjeni suma , hmmm ko ina labarin Ummu Affan ? Ina san sanin rayuwar Aunty Suwaiba duk yadda akayi cire mata ƙafafuwa akayi tou fa , naji dai da rayuwata naga wannan irin rayuwa. Dariya nayi tare da cewa kema uwar Dikko har yanzu baki gano inda nake ba ? Tou zo kiji in faɗa miki ina nan gidan ɗan rainin wayan ɗakin a ɗakinshi kwance saman katifa an tada man gen ina shan iskkan A C babu abinda ya dameni da zafin gari , kuma yazo ya bani abinci mai kyau inci ga masu gadi suna gadina duk ɗiyar ɗan caca da kika raina ɗanki kuma yasan darajata tou nice na samu wannan matsayin , ummm turo bakina nayi tare da gyara kwanciyata nace bacci mai daɗi......... 13/10/2019 *JAMILA MUSA....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 55 Tunda na samu na kwanta bacci har gari ya waye ko fitsarin dare ban farka ba , wadataccen baccin dana samu shine ya bani damar tashi asubahin farko , kuma tunda na tashi nayi sallah asuba ban koma bacci ba , wayata na ɗauka saidai na kunno maganar mutumin nan da nake tunanin shine ya kwakwalewa Aunty Mamy ido ta mutu , Allah ɗaya gari ban² shi nan magana yake , da , da yare na yakeyin magana zanji abinda yake cewa to banaji saidai na saurara amma ba damar na fihimta , hmmm ya zamar min dole na miƙe da zuciyata da kwalwata nima nayi ilimi kodan ceton rayuwata daga duhun jahilci.... Bayan na gama saurare na kashe wayar na saƙata a gefen katifa na koma nayi kwanciyata ban daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗaukeni , na ɗauki lokaci mai tsayi ina bacci hankalina kwance banda wata damuwa data wuce yunwa , sai ɗaya saura na farka , Koda na farka wanka nayi nayo alwalla kaya na canja ni "yar gayu dan ina cire kaya na ajiye a palo za'a ɗauka a wanke a gogemin shi yasa ni kuma kullum saina canja kaya sau biyu , idan nayi wankan safe na saka idan nayi na marece ma na sake ! Bayan na gama sallah azahar na ɗauki kuɗi na fito da zumar in ba mai gadi ya siyomin abinci , amma ina shigowa palo naga ɗika²n kulolin abinci da filets da cokula kamar dai yadda aka saba ajiyewa a kullum idan Dikko yana gari idan har yana nan haka ake ajiye wannan abinci da rana da daddare shi yasa ko wane lokaci gidan baya rabuwa da mutane kalacin safe ne dai bana tunani ana kawowa gaskiya dan bana gani saidai iya wanda zan karya dashi. Saida na zuba abinci dai² wanda zai isheni nakai ɗaki na ajiye sannan na dawo nace ma mai gadi wai Dikko baya nan ne ? Yace min yana nan mana , nace tou ai ban ganshi ba , yace min yana nan ciki tun ɗazu ya shiga kila bacci yakeyi , nace yayi mishi kyau , na juyo na dawo a raina ina cewa miya faru bai nemeni ba ? Wurin mai gadin na sake komawa nace yasan nazo kuwa ? Yace Eh na faɗa masa , ya yace maka ? Baice komai ba , daya zo yace ina ne ? A , a bai tambayeki ba , tou ya yanayin fuskarshi ? Yayi farin ciki ko yayi yanayin damuwa ne ? Yace ni bansan ya yayi ba. Ban sake magana ba na koma na ɗauki abinci na naci gaba da ci , bayan na gama nazo na ajiye filet in a inda na zuba abincin , ban daɗe da komawa ɗaki ba gidan ya fara ɗaukar taron mutane kamar yadda ya saba a ko wace rana , wannan zama haka zasuyi tayinshi har sai dare yayi sannan kowa zai kama gabanshi. Hayaniyar sai ƙara ƙaruwa takeyi palon sai ƙara cika yakeyi harabar gidan kuwa an cika ta da motoci , aikin gardamar suka fara kenan basu da aiki sai maganar "yan kwallo , ƙaramin palon na fito na zauna inga ta ina Dikko zai fito amma har akayi la'asar naje nayi sallah na dawo banji Dikko ya fito ba , gajiya nayi na koma ɗakina naci gaba zaman jiran tsammani. Yau ko abincin dare banci ba inayin sallah isha'e nayi kwanciyata jiya banga Dikko ba yauma ban ganshi ba haka nan na haƙura na kwanta , amma ba haka naso ba naso mu haɗu ko so ɗaya , tou ko baiso nazo masa gida bane shi yasa yake ta ɓoyewa kila yayi haka ne idan na gaji da zama in kama gabana , Bandai yi bacci ba ina kwance ina ta tunanin duniya har 11:05pm a hankali gidan ya fara ragewa har yanzu banyi bacci ba , wurin misalin 11:49pm gidan yayi shiru gaba ɗaya , yau gaskiya sun tashi da wuri dan wani lokaci suna kai har 1:30am suna fira ! Duk masu fita gidan akan idona suke fita amma har yanzu babu Dikko a cikinsu kuma har akayi zaman nan aka tashi banji an kira sunashi ko so ɗaya ba , kuma banji maganarshi ba , saida gidan ya zama babu kowa na haƙura nayi bacci. Wasa² har nayi kwana 3 gidan banga Dikko ba kuma mai gadi ya tabbatarmin yana nan ya dawo , na duba ɗakinshi ban ganshi ba , kuma idan na kira wayarshi yanzu tana shiga amma baya ɗauka , haka nan naji duk na takura gaba ɗaya na kama kaina saima na daina cin abincinsu kwata² saidai in tura a siyomin abincin da nake so naci lashe ² da duk wani abun kwaɗayi da zuciyata take sha'awar ci ko sha da kuɗin da Baban Hafsa ya bani, Ranki ya daɗe yau kwananki 2 da dawowa amma har yanzu shiru nakeji , gyara zama Jiddah tayi tare da cewa waini tayama zan fara samoshi ne ? Kwantar da murya Al ' Ameen yayi cewa haba ranki ya daɗe duk wayewarki da gogewarki kice baki san yadda zakiyi ki samo ba ? Tou taya akayi kika kwanta da shi ? Jiddah tace kwanciya daban maganar samun abinda boka yake magana daban ya bani "yar ƙaramar kwalba yace a ciki zan matso taya zan fara tara kwalbar nan na matso bayan kuma yana kallona. Al ' Ameen yace ranki ya daɗe idan ya kwanta dake bayan kun gama abinda kukeyi sai kiyi kamar irin kina masa wasa naku na ma'aurata saiki lallaɓa kiyi dabara ko a hannunki ki samu , dama kin ajiye "yar kwalbarki a toilet kina matsowa sai ki tafi toilet kamar zaki wanke hannunki kina shiga sai ki zuba a kwalbar , ki maida hankali kinga abun kullum gaba yakeyi , kuma anje kamo yarinyar nan ta gudu yanzu babu wanda yasan inda take ma , Jiddah tace gaskiya wannan shawara haka tayi , tou insha Allah zanyi , Al ' Ameen yace dadai kin taimaki rayuwarki , haka yaita ɗora Jiddah yana kaita yana baro. Da marece bayan na gama abinda nakeyi na fice daga gida , kasuwa na fara zuwa na siya niƙaf kamar yadda Baban Hafsa yace , banyi hijabi ko ɗaya ba saboda ina da hijabai sunkai goma a gidan Dikko , ina sayen nikaf in na lulluɓe fuskata na haye napep , ban sharce ko ina ba sai majalissar su Baban Hafsa , mai napep na sallama ya tafi ni kuma na isa wurin tare da sallama. Gaba ɗaya suka ansa sallamar yayin da Baban Hafsa ya taso fuskarshi ɗauke da yanayin kishi yana cewa sai ki kama kizo nan kuma bazaki faɗamin ba ? Wurin motarshi ya nufa ya ɗauko leda yana cewa da Allah kada ki sake zuwa nan kinji ko ? Nace tou , yawwa ga kayan makarantarki nan da littafanki komai akwai a ciki , nace ngode Dady shi kuma yacemin idan Allah ya kaimu goben zanzo makarantar taku nace Allah ya kaimu lafiya , ya ansa da am3n da kanshi ya tsaida min napep ya biya kuɗin , saida na samo abinda zanci da daddare da wanda zanyi kalaci da safe idan Allah ya kaimu sannan na wuce gida. Yauma gidan ɗinke yake da mutane babu masaka tsinke ko dana tunkari palon dole tasa na dawo saboda babu ta hanyar da zanbi in wuce , gaba ɗaya palon ya gauraye da ƙamshin turare iri² har baka iya gane na wani , kowa dai ɗan gaye ne babu sakarai kuma babu ƙazami dan duk "ya "yan attajirai ne , kowa dai yanaji da kanshi dan babu wanda yake so a fishi , Bayan gida na zagaya wurin masallacin dake cikin gidan , a ƙofar masallacin na samu wuri na zauna sannan na fara duba kayan da nazo dasu , hada waya a ciki da layin waya kila Dady yana tunanin banda waya shi yasa ya haɗomin da ita , ƙaramar waya ce nokia ko kwali bata da sai caja , murmushi nayi tare da maida wayar na fiddo abinci naci gaba da ci saboda yunwa nakeji , Ban daɗe da gama cin abinci ba suka fara fitowa danyin sallah magrib dan haka na tashi na zagaya ta ɗayar hanyar dan gaba ɗaya a wurin ƙofar masallacin suke alwallah , lokacin dana zagayo gaba ɗaya babu kowa a wurin sai Dikko kaɗai dake alwalla a ƙofar palon , gaishe shi nayi tare da mishi sannu da zuwa kallona yayi amma baiyi magana ba , Sake gaishe shi nayi ya ƙara basarwa , raɓashi nayi zan wuce ciki a dai² lokacin daya gama alwalla ya ciko bakinshi da ruwa kamar da yayi niyar watsamin su sai kuma ya zubar a gefe yana warware hannun rigarshi daya naɗe yace ina kikaje tun ɗazu ? A daburce nace ina ina ta can na nuna mishi baya da hannuna , kina ta can ko ? Yayi maganar tare da jinjina kanshi yace yayi kyau, Daga haka bai sake magana ba ya wuce nima na shige ciki , ina shiga ɗaki na ajiye kayan dana zo dasu nayo alwallah nayi sallah , ina gama sallah na fara haɗa littafaina a cikin jikkar makaranta wani irin farin ciki nakeji naga Dikko kuma naji daɗi dana ganshi kullum nidai ƙara burgeni yakeyi addu'a ta ɗaya Allah yasa idan ya gama sallah yazo , ni kuma ince masa me yasa baka ɗaukar wayata idan na kiraka......? Zuciyata tace karki sake ki tambayeshi raina ki zaiyi , a bayyane nace ko yane gaskiya ya kamata nasan miye dalilin da yasa baya ɗaukar wayata , zuciyata ta sake gargaɗina a karo na biyu cewa ki kama kanki shi namiji ma ya riƙe ajinshi sai ke banza zaki damu dashi , murmushi nayi a bayyane nace ina wani maganar aji kuma bayan ina zaune a gidanshi , anya akwai wanda ya taɓa shiga rayuwa irin tawa ? Nidai ko a labari ko littafi ban taɓajin wanda yayi bahaguwar rayuwa mai tattare da ƙalu bale ba kamar tawa , Babana ya rasu , gidana kuma dana siya "yan uwana sun siyar dashi , ƙanin Babana kuma yace min zamana a tare dashi babban riskine , Yayun Babana kuma basu ma sanmu ba , Mamana ta gujeni ta tafi ta barni ina ta gararin rayuwa me nayi ma duniya ta juya min baya haka da ƙuruciyata ? Dole in cire wani girman kai inbi Dikko in zauna lafiya idan ba haka ba shima ya juyamin baya bansan ya rayuwata zata koma ba , ga mahaifiyarshi ta ɗanawa rayuwata tarko idan kuwa har nayi kuskuren bari ta kamani kashina ya bushe , "Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" Allah ngode maka ubangiji ka yafemin ka yaye min ƙunci da damuwa dan alfarmar sayyadis sadati , ka tausayamin ka karkato da hankalin mahaifiyata gareni kaji ƙaina badan halina ba , Inna kina wace duniya haka kika manta dani ? Niko duk halin dana shiga bana mantawa dake har abadan duniya kuma ina sanki Allah ya dafa miki ya jiƙanki a duk inda kike a faɗin duniyar nan kuma ya huci zuciyarki , Allah kaji ƙan Babana kasa ya huta.... 7:19am a cikin makaranta tayimin , ina cikin ayarin ɗalibai har a wurin taron assembly ko a wurin taron komai da turanci ake faɗa kuma abinda na fahimta kowa idan zaiyi magana da ɗan uwanshi bayayi da yaren hausa saidai da harshen bature , Bayan an gama ko wane ɗalibi yayi ajinshi nima nayi nawa ajin JSS 1B shine ajina , duk "yan ajin nafi su girma kuma sai dariya sukemin suna kallona , wuri na samu na zauna ina tunanin idan har yaran nan nabar suka shiga gabana a karatu raini zasumin bana wasa ba , idan har na bar wani ɗalibi yayi na 1 a ajin nan bani ba naji kunya , dan haka na tattaro hankalina da natsuwata na fara ɗaukar karatu yadda ya kamata domin malamai sun fara shigowa. Babu laifi ina fahimta dan ina da ilimin addini sosai shi yasa nake ganin karatun boko bazai wani bani wahala ba , lokacin da aka fita break banje ko ina ba ina cikin aji ina ta naci , bayan an dawo malamai suka ci gaba da shigowa har aka tashi daga makaranta , bayan an tashi saida nayi azahar tare da addu'a ubangiji ya dafamin sannan na shiga ajin koyon darasi na musamman , Saida la'asar muka tashi muna tashi saida nayi la'asar nabar makaranta kuma Dady bai zo ba , daga makarantar boko tsohuwar islamiyarmu na nufa na siya form na shiga ajin harda kuma ni na cika abuna da kaina da larabci , daga islamiya na wuce kasuwa na ɗinka hijabi da wando na islamiya sai gab magrib na isa gida. Yau duk taron su bai hanani wucewa ba , tunda na shiga kowa yabi ni da kallo har na shige , ina shiga wanka nayi tare da ɗauro alwallah na saka kayana ko mai ban shafa ba nayi sallar magrib dan an kira sallah , ina gama sallah wayar da Dady ya bani ta fara tsuwa tashi nayi na ɗauko ta a inda na ajiyeta , bayan na ɗauka muka gaisa yacemin kiyi haƙuri don Allah yau baƙi nayi a Office amma ina san ganinki yanzu ina zan sameki ne ? Nace saidai kai ka faɗamin a inda zan sameka , inda zan sameshi ya faɗamin nace tou gani nan zuwa yace sai kinzo , Daga saman abin sallah dana miƙe wayata kawai na ɗauka wanda zanyo recording idan an taɓo labarin daya shafi Babana , haka na sake ratsowa na fito ina fitowa Dikko yace ina kuma zaki ? Nace yanzu zan dawo ina faɗin haka nayi gaba , yace ke karki sake fita daga gidan nan sai kuma gobe idan Allah ya kaimu , banma saurareshi ba na fice abuna. Ina fitowa daga palon na samu wuri na ɓoye dan nasan dole saiya biyo bayana , ina ɓoyewa kuwa ya fito yana kirana amma abun mamaki ya fita waje ko sahuna bai gani ba na ɓace kamar walƙiya , mai gadi ya tambaya ta wace hanya "Yar mata tabi ? Yace mai gida banga fitarta ba , Dikko yace baka ga fitarta ba ? Yace Eh , tabi ta gabanka ta wuce kace baka ga fitarta ba dan ka ɗaukeni sakarai ? Cikin girmamawa yace wallahi mai gida ban ganta ba , kallonshi Dikko yayi yace amma ai duk wanda zai shiga ko fita a gabanka idonka , kusa dashi ya matsa yace ta wace hanya tabi ? Mai gadi yace mai gida wallahi bata fita ba , Dikko yace to rufe ƙofar karka sake kabar wani ya sake shigowa kuma karka sake ka bar kowa ya sake fita yace tou , daga ƙofar palon ya koma ya tsaya bayan wani lokaci kuma ya taho da sauri ya tunkari hanyar fita daga gida bayan yaje ya sake komawa ƙofar palon ya tsaya , magana yayi ma mai gadi cewa lokacin dana fito ƙofa a buɗe take ko a rufe ? Mai gadi yace a buɗe , Dikko yace buɗemin ƙofar , buɗewa yayi Dikko ya sake tahowa saida yazo fita yace tabbas bata fita ba tana cikin gidan nan dan ko da gudu ta fita fitowa ta ya isa na hangota ko yane , zanga ta inda zaki bi ki fita yarinya , yana faɗin haka ya koma motarshi ya zauna , dariya nayi a raina tare da cewa mu zuba wallahi babu wanda ya isa ya hanani fita a daren nan saina fita. Har aka kira sallah isha'e ina tsugunne cikin filawowi Dikko yana cikin mota , gaba ɗaya suka fito suka zagaya hanyar masallaci Dikko yace ma mai gadi karka sake ka bar wani ya shigo kuma kar wanda ya fita bari muyi sallah , dariya nayi nace aiko na fita na gama kuma tunda har ka bar motarka buɗe da ita zanje , Yana zagayawa na fito na shige motarshi tunanin mai gadi Dikko ne ya buɗemin get na fice da gudu sakarai ya manta Dikko yace mishi zaiyi sallah , ina fita na kira Dady nace har yanzu kana wurin ne ? Yace min yabar wurin daya ji shiru kuma ya kira wayata a kashe , nace tou yanzu kana ina ne ? Yace ina nan asibiti , nace lafiya a asibiti ? Yace Hajiyarmu ce batajin daɗi , nace wace asibiti haka ? Yace min fmc nace wane ɗaki yacemin zuwa zakiyi ne ? Na gane wayanshi idan zanzo bazai faɗamin ba , dan haka nace aini tsoron asibiti ma nakeyi Allah ya bata lafiya dama ko nazo sauƙi zan nema mata daga nan ma nayi mata addu'a Allah ya bata lafiya , yace amin , cikin nuna damuwa da tausayin matar nace amma dan Allah da kun sake mata asibiti , yace ai anan likitan ta yake , nace tou Dady ai kuma da ɗakin sarakai kuka kaita tunda Allah yasa kana da iko , yace ai nan take nace tou Allah ya sawaƙa yace amin , sallama mukayi dashi na dawo gida , Ina dawowa nayi horn ya leƙo yaga Dikko ya buɗe na shige a inda ya ajiye motar na ajiye na shige ciki da sauri , ina shiga nace fmc ɗakin sarakuna , gani nan zuwa gareki muguwar tsohuwa , hayaniyar Dikko najiyo yana cewa waye ya fita kuma waye ya shigo ? Ina alwallah naji ka buɗe ƙofa yanzun nan ina fitowa naji ka sake buɗewa , mai gadi yace mai gida ai kaine ka fita , Dikko yace na fita naje gidan wa ? Mai gadi yace na rantse da Allah kaine ka fita , Dikko yace idan ka sake cewa nine na fita saina mareka wallahi , mahaukaci ka ɗaukeni ko kuwa me ? Shiru yayi yana nunawa da hannunshi wallahi Allah kaine , Dikko yace aiko ubanka zanci , abokanshi suka bashi haƙuri tare da cewa ya canja mai gadi kawai , mai gadi yanajin za'a canja shi ya fara wallahi ײ Dikko yace idan bakaimin shiru ba saina harbar maka baki da ƙafata , duk inajin hayaniyarsu na koma nayi kwanciyata na ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya ina ɗigawa bakina fura ina lashewa , Motarshi ya koma yayi "yan dube² sannan ya rufeta bai ciro makullin ba yayo ɗakina , kwance ya sameni ina ta ɗiga fura a bakina hankalina kwance kuma ko inda yake ban kalla ba na ƙaddara ma babu shi kawai a wurin , An mata ina kikaje ? Ban kalleshi ba nace naje saman katifata ne kuma gaka ka ganni kwance ina shan fura ko zaka sha ne ? Bana san sakarci ina kikaje ? Tashi nayi zaune nace to ko nima mai gadin zaka maidai ni ne ? Rufe idonshi yayi yace ina kikaje nace ? Shiru nayi na koma na kwanta naci gaba da shan furata , har yanzu idonshi a rufe yake ya maimaita ina kikaje ? Ni nace maka babu inda naje sai tambayata kakeyi ina naje idan naje wani wuri zaka sameni ina kwance wai ? Shigowa yayi cikin ɗakin ya shaƙoni ya ɗagani tsaye yace zaki faɗamin inda kikaje ko saina buga miki kai da bango ? A tsorace nace babu inda naje ina nan tunda kace karki in fita na dawo na faɗa mishi duk yadda sukayi da mai gadi da lokacin da zai tafi sallah nace idan bana nan taya na san haka ? Naji kina nan amma dana tafi sallah ke kuma sai kika fita da mota ta , nace wai na fita naje ina ? Murmushi yayi tare da sakarmin wuya daga shaƙar da yayi mini yace Allah ya sawaƙe miki ganin ɓacin raina , wallahi dan ina tausayinki amma yau dasai kinsan kinmin gardama , Fita yayi daga ɗakin yana magana ƙasa² , ajiyar zuciya na sauke daga tsaye na ida shanye furata na wuce nayi alwallah nayi sallah isha'e , ina gamawa nayi kwanciyata dan yanzu bana daɗewa banyi bacci saboda makaranta dan banda lokacin baccin safe kona rana ! Yau da kanshi ya kaini makaranta kuma bai tambayeni wanda ya sani makarantar ba haka kuma bai tambayeni dalilin da yasa na koma makaranta ba , kawai dai tunda safe yazo dana fito zan tafi yace muje in saukeki , kuma daya saukeni yacemin zai dawo ya ɗaukeni , nace masa idan na gama zan kiraka saboda munayin lesson banza yayi yai tafiyarshi bai cemin komai ba , Caf lallai ni zaka sakawa rayuwata ido ? Hmm idan kasan wata baka san wata ba malam Dikko , wallahi sainaje asibiti naga kishiyar kakata , yauma "yan ajinmu dariya sukemin hada wanda bama aji ɗaya dasu an gayyatosu suzo suka ƙatuwa a JS 1 , nima dariya abun ya bani dan haka basu bani haushi ba , Ana tashi makaranta na fice saida naje fmc nayi waya da Dady nace masa yamai jiki ? Yace da sauƙi , nace kana asibitin ko kana office ? Yace idan ina asibitin miye ? Nace wai da ka haɗani da ita in mata sannu da jiki jiya da tunaninta na kwana ko da nayi sallah dare saida nayi mata addu'a Dady , murmushi yayi tare da godiya sannan yacemin yana Office ! Nace Allah ya sawaƙe ya bata lafiya yace am3n ya gode , mukayi sallama dashi , Bayan mun gama waya da Dady nace ma mai napep muje , tada motar yayi muka isa ɗakin , da tambaya na gano ɗakin da take a nuste na shiga da sallama , suka amsa min cikin sakin fuska tare damin sannu da zuwa , wuri na samu na tsugunna na gaishesu cike da ladabi tare da tambayarsu ya mai jiki ? Sukacemin da sauƙi nace Allah ya bata lafiya yasa kaffara ne , suka amsa da am3n , wurin tsohuwar na matsa nayi mata sannu ta ansa da yawwa nace ni ƙawar Hafsa ce , tace Allah sarki aiko yanzu ta tafi ita da ƙawayenta nace Allah sarki , 5k na bata cikin kuɗin da ɗanta ya bani nace ayi haƙuri daga makaranta nake , godiya sukayi tayi tare da tambayata idan Hafsa tazo wa za'ace mata , nace ace mata uwar ɗakinsu ce , sukace da ance haka shikenan nace Eh kuma ai zan sake dawowa sukace Allah ya yadda , godiya sukayi sosai ni kuma na fito abuna. Kai tsaye makaranta na koma saidai nayi sallah na shiga aji kuma malam yamin faɗa kar na sake na sake makara nace insha Allah . A asibiti kuwa abinda yasa nace musu su faɗawa Hafsa uwar ɗakinsu ce dan kada a faɗa Dady yana nan idan yaji Sultana kila hankalinshi zaikai kaina , tou dukansu babu wanda yasan nasan kowa a cikinsu , Dady nasanshi ya sanni , Hafsa ta sanni na santa amma gaba ɗayansu babu wanda yasan ina tare da wani a cikinsu , Hafsa tasan ni ɗiyar Binna ce amma bata san ina da zuminchie da ita ba , Dady kuma bai sanni ba kuma baisan daga ina na fito ba yasan Binna amma baisan ni ɗiyarshi bace ba , su kuma asibiti basu san ko wace ce ni ba ni kaɗai nasan ko suɗin su waye. Yauma sai gab magrif na koma gida saboda naje islamiya , kuma Dikko yayi masifa sosai yace har makaranta bokon bazan sake zuwa ba duk abinda nake idan ban sani ba motsina ɗaya a waje wallahi saman tafin hannunshi yake kuma ya faɗamun naje asibiti saboda kin ɗauke ni bansan abinda nakeyi ba ni zaki gayamin idan kin gama zaki kirani , wallahi kallonki kawai nakeyi amma ki sani koda gira kikayi magana nasan ƙafar dake miki ɗingishi , Na fiki hankali na fiki wayau nafi sanin rayuwa shekaruna da naki ba ɗaya ba gogewa ta da taki ba iri ɗaya ba duk wani wayau da kike tunanin kina dashi ni a wurina Xeyro , mu zuba dani dake tunda kin rainani zanyi miki maganin rashin kunya. Nace yi haƙuri don Allah kuma dama ai kasan zan faɗa maka kuma saida na faɗawa mai gadi nace nabi ƙawata zan gano kakarta ko Yayana yazo , ki rufemin baki ke ɗaya kika shiga napep sannan kuma kika fito daga cikin makaranta kina waige² yaushe kikayi magana da mai gadi ? Ba mai gadi ba malam na faɗa mawa , tou malam kika faɗa mawa koma dai waye na soke makaranta daga yanzu , dan girman Allah kayi haƙuri wallahi bazan sake ba , na gama magana yana faɗin haka ya wuce ɗakinshi , binshi nayi naci gaba da magiya ina bashi haƙuri , banza yayi dani ya wuce toilet yana alwallah , saida ya fito nace dan Allah kayi haƙuri Yaya Dikko , murmushi yayi yana maida agogonshi yace da kince Yaya cuta na zakiyi ya ƙarasa maganar yana kallona , nima murmushi nayi ina kallonshi cike da soyayya , shima cike tsantsar ƙauna yake kallona kowa ya kasa daina kallon kowa. Dafa kujera yayi yace An mata wai a haka baki so na ko ? Ɗan turo baki nayi banyi magana ba , yace Hmm irin wannan kallo haka idan kuma kika fara so na wane iri zakimin kenan ? Kunya naji dan haka na juya na fice da sauri daga ɗakin murmushi yayi tare da cewa Allah ka kamamin zuciyar yarinyar nan kasa mata tsantsar sona da tausayin rayuwata , ubangiji ka ƙaramin haƙuri akan duk abinda zatamin ka wadatani da tausayinta ka bani ikon riƙeta da gaskiya ka kauda sharrin shaiɗan tsakani na da ita dama duk ko wane namiji dake zuwa gidan nan har ta gama zaman ta a gidan nan , ya ubangiji ka ɗauke idon duk wani namiji akanta , ka janye mata tunanin ko wane irin namiji saini , Ina shiga ɗaki saman katifa na faɗa tare da rufe idanuwana na kwantar da fuskata a saman bargo daɗi kawai nakeji Dikko yayimin murmushi kuma nasan wasa yake bazai hanani zuwa makaranta ba dan yaɗan latsani ne , wallahi Dikko ɗan gayene mai kyau na burgewa yanayin magana cikin salo mai ɗaukar hankali , ihu nayi tare da murginawa nace ina sanka mutumina , ina sanka ׳ , juyowa nayi na kwanta rigingine fuskata tana kallon sama na rungume hannaye na a ƙirji na lumshe idanuwana cikin yanayin jin daɗi nace kuma wallahi bazan sake tafiya na barka ba dan ina shan wahala idan bana tare dakai , Jiddah tsaye a gaban Al ' Ameen duk ta fita hayyacin tace ni wallahi na kasa , Al ' Ameen yace haba ranki ya daɗe kamar dai ba wayayya ba ? Saboda rashin wayau aiko ƙawarka mace bakya faɗa mata yadda kike kwanciya miji ba bare yaron mijinki , Jiddah tace ai idan ya kwanta dani baya sauka daga jikina sai bayan mintuna 15 , Al ' Ameen yace basai ki saukeshi da dabara ba ? Jiddah tace wallahi baya sauka , tsoki Al ' Ameen yayi yace haba Aunty Jiddah karki bari kiyi wasa da wannan damar ki sake jarabawa a ƙaro na ƙarshe mu gani , Jiddah tace to saidai idan ya dawo ya tafi Abuja Al ' Ameen yace Allah yasa ya dawo lafiya ta ansa da am3n , Haba Jiddah waye ya faɗa miki Dikko na Abuja.......? 14/10/2019 Taku a kullum mai san farin cikinku 👇🏻 *JAMILA MUSA...*💅🏻 ⚜*BRILLIANT WRITERS ASSO🖊~{{-pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}} *KWARATA* {{kalu bale gareku matan aure}} *JAMILA MUSA* {Meelat musa} sadaukar wa gareku,👇🏻 *ASMA'U ZAYYANA{{Asmeenat}} & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿-----56 ```kuyi hakuri yau baxaku samuba saboda matsalar charge da banda amma insha Allah gobe zakujini``` ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 56 *_MAIMOUNATH O . G {{ Mahnoor }} ni bansan da irin kalaman da zanyi amfani dasu wurin miƙa saƙon godiya ta a gareki ba , idan zanyi ta rubuta ngode² sai cajin wayana ya ƙare ban gama cewa ngode ba , duk da haka dai ngode sosai Allah ya saka da alkairi ubangiji ya ƙara arziƙi ya ƙara zaman lafiya tsakaninki da naki master ya kawo zuri'a masu albarka..._* *_Ummu Farhana ta sake zagayo muku da wani sabon salon labari nata mai taken FANNAH {{ marainiya }} hanzarta ki samu naki karki sake ki bari a baki labari , ina miki barka da fara sabon littafinki Allah ya taimaka yasa yadda kika fara lafiya ki kammala lafiya...!_* Saida Al ' Ameen ya tafi sannan Jiddah ta koma ɗakinta cikin tashin hankali , ta zagaya ƙaton palon ta bata san adadi ba , mafita ta farko da zuciyarta ta yanke mata shine duk yadda za'ayi kawai a fara kamo mata Sultana , shawarata ta biyu kuma sai gata ga Dikko... Wayarta ta ɗauka ta fara kiran Momy bayan ta ɗauka suka gaisa tun kafin a gama gaisuwar Jiddah tace Momy har yanzu dai kin kasa wani abu akan yarinyar nan , Momy tace waye yace miki na kasa.....? Jiddah tace to ai naji shiru har yanzu babu wani ci gaba , murmushi Momy tayi tare da cewa kwantar da hankalin ki an gano komai nata tana shiga makaranta kullum da ƙarfe 7 da wani abu na safe , Tana fita daga makaranta kullum karfe 4 , daga nan tana wucewa islamiyya , tana zuwa a napep idan aka tashi kuma ta shiga motar makaranta ta sauka islamiya , yau ba'a napep taje ba ance wani yakaita kuma basu san ko waye ba , Momy tou mi yasa basu kamata ba ? Kinsan komai yana san bin diddiƙi kuma har yanzu sun kasa gano gidan da take zaune , saboda sunce daga Islamiya kullum take ɓace musu saboda tana amfani da abun rufe fuska { niƙaf } mafiya yawan ɗalibai dashi suke amfani , Momy basai an gano gidan da take zama ba nidai burina kawai a kamota idan ba haka ba zata iya sake sulɓewa , Momy tace babu damuwa , Sun dai daɗe suna saƙawa yadda zasu ci mutuncin Sultana idan aka kamota daga baya sukayi sallama , Jiddah kuwa taci alwashi idan har aka kamo Sultana tunda dai har take tarayya da mijinta tou tayi alƙawari sai tayi mata tsarki da ruwan tsidagu bayan ta jajjaga attaruhu ta zuba abonaki a cikin ruwa zafi zata zaunar da ita a ciki , sai taci ƙaniyarta yadda gobe ko ance tayi iskanci da Dikko sai tace ta tuba.... Kamar yadda na saba fita daga gida yauma haka na fito sanye cikin kayan makaranta na , a palo na samu Dikko zaune saman abin sallah ya jingina da kujera ya miƙe kafafuwanshi ɗaya saman ɗaya yana karantun al'qur'ani mai girma , Kallona yayi amma baiyi min magana ba , hannu na ɗaga mishi alamar saina dawo nayi gaba , gab da zan fita daga palon yace An mata nace karki je makarantar nan ko , cikin muryar lallashi nace haba Yayana na ƙarasa maganar ina kwantar da kaina nayi kalar ban tausayi , rufe al'qur'anin yayi yace nidai banajin daɗi , jikina yana min wani iri inajin kamar wani abu zai faru dake wallahi , nidai dan Allah kiyi haƙuri da makarantar nan ! Nidai zanje a haka , a kasalance ya lumshe idanuwan shi yace a , a , nace dan Allah , kallona yayi tare da cewa kiyi shiru zanyi fushi , zama nayi saman hannun kujera ina magana ƙasa² cewa kayi fushin mana ko an faɗa maka nima banda zuciyar ne ? Na ƙarasa maganar ina hararar bango , Ɗan kintsa bakinsa yayi ya kallo inda nake yace banji abinda kika ce ba , ai dama bana so kaji , saboda kinajin tsorona ko ? Sallamar Ashiru ya hana na bawa Dikko ansa , gaishe shi nayi bayan na ansa sallamar da ina kwana , maidomin gaisuwar yayi da ina kwana ranki ya daɗe , kunya naji dan haka na kwantar da kaina jikin kujera banyi magana ba , Daga inda yake tsaya ya haɗa hannayen shi ta baya tare da rusunawa cikin girmamawa yace mai gida barka da safiya , yawwa Dikko ya faɗa a taƙaice , Matsawa yayi ya duƙa kusa da Dikko yana magana , ya daɗe sosai kuma banajin abinda suke faɗa amma duk yadda akayi gulma sukeyi , bayan ya gama maganar ya fita , shima Dikkon tashi yayi ya maida al'qur'an inda yake ajiyewa ya fita , nima na tashi nabi bayanshi... A ƙofar fita mukaci karo , shi yana ƙoƙarin dawowa ni kuma ina ƙoƙarin fita , cikin faɗa yace ina zaki je ne wai ? Komawa nayi na zauna banyi magana ba , ciki ya koma bai wani daɗe ba ya fito , yana fita yace jeka kawai zanzo bayan la'asar in Allah ya kaimu , Saida Ashiru ya tafi Dikko ya dawo , ba tare daya tsaya ba ko ya kallo inda nake yace fita zanyi idan kina zuwa ki cire uniform in sai in tafi dake , kaje bazan je ba , sai kinje ya faɗa a dai² lokacin daya shige ciki.... Tunda naga ya daɗe bai fito ba raina ya bani wanka yakeyi zaman toilet sai kace mai jego , tashi nayi na ɗauki jikkar makaranta ina na koma ɗaki , Wayoyina na ɗauko na fara dubawa , tarin miss calls a wayar da Dady ya bani ya kira sau adadin da bazan iya ɓata lokacina wurin faɗar su ba , Alaji ya kira Aunty Suwaiba , Malam Ɗayyu da baƙin numbers wanda banda su a cikin wayana ! Cikin baƙin numbobin na fara kira , ana ɗauka naji ya fara babbaka min ashariya tare da cewa duk inda kike a faɗin duniyar nan idan na kamoki kwanakin rayuwarki ya ƙare , Lahaula wala kquwwata illa billahil aliyyul azeem , waye kai ...? Tsoro , tsoro ne , ni tsoro ne mai ban tsoro kuma na duƙufa akan cewa saina ɗan ɗana miki ɗanɗano tsoro sannan na kasheki , Na ganki nasan inda kike ƙoƙarinki ya ƙare kuma na tiso rayuwarki gaba saina ga kin shaƙe kinbi iska hankalina zai kwanta wuƙa zan caccaka miki a zuciya a wurin zaki mutu ko harbawa bazakiyi ba yau zan kashe ki....... Yanzu ne ? Ko anjima koma dai yaushe ne kici abincin bankwana gani nan tahowa..... A firgice na juyo zufa ta tsatsanfomin dan ya faɗi kalaman nashi da kaushi , a wahalce nake fitar da lumfashi dan wanda baya cikin ɗakin yana iya jin sautin fitar numfashi na , zufar goshina na goge da sauri na juyo Dikko na gani tsaye yace me ya sameki ne ? Mutuwa zanyi..... Na bashi ansa kai tsaye , cikin rashin fahimta yace wace irin mutuwa kuma ? Cikin kuka nace nima zasu kasheni kamar yadda suka kashe Babana kuma suka kashe Aunty Mamy suka kashe wata Auntyn wacce ma bata samu damar isowa wurina ba suka shafe labarinta , Tsoki Dikko yayi ya juya yana aike kanki rawa yakeyi kullum baki gajiya da sakin layi kamar zararriya , yadda yayi min sai abun ya tunomin ranar da za'a kashe Babana daya faɗamin nace masa shirmen mafarki ne ni kuma yau gashi na faɗa amma ni an danganta ni da mai rawar kai. A tsorace na sake lalubo wata baƙuwar lambar na sake kira , itama wata murya ce daban ta tabbatar min da mutuwa ta yau babu gudu babu ja da baya , kashewa nayi na kira wayar Dady bayan ya ɗauka muka gaisa na tambayeshi mai jiki yace da sauƙi , ya akayi baki je makaranta ba yau ? Ya tambayeni , Cikin faɗuwar gaba da dakiya nace naje mana , abinda naje makarantar ban sameki ba , nace da wane lokaci kaje ne ? Tunda safe ina bakin get in makarantar ban ganki ba , jinjina kaina nayi tare da cewa amma me yasa kaje kai tsaye bayan baka saba zuwa ba saika faɗamin zaka zo , yau shawara na sake shi yasa naso yi miki bazata kawai , yanzu kina ina ne ? Kai kana ina haka ? Har yanzu ina bakin get in makarantar ku ? Ka jirani gani nan zuwa , ina faɗin haka na kashe waya , lambar Alaji na kira bayan na gama waya da Dady , tana shiga ya ɗauka ko gaisawa bamuyi ba yace Sultana kina ina ne ? Ina Lokoja na bashi ansa kai tsaye , wace irin Lokoja kuma ? Nace lokoja nawa ka sani ? Tou ke meya kaiki lokoja ? Idan aka ga kuɗi katsina aka gansu a lokoja abin mamaki ne ? Ai kuɗi yawo sukeyi babu inda basa iya zuwa a cikin ƙanƙa lokaci , nace to karkayi mamaki domin karuwa da kuɗi duk ɗaya suke yanzu nan zaka ganni anan zuwa anjima kuma in ɓace , nabar katsina ina lokoja , zai sake magana na katse kiranshi na kira Aunty Suwaiba , bayan ta ɗauka muka gaisa nayi mata sannu da jiki ta ansa cikin kulawa tare da cewa Sultana kina ina ne ? Aunty ina kaduna , yaushe kika tafi ne ? Tunda muka rabu da malam ɗayyu a katsina ranar nabar katsina da daddare ! Amma me yasa baki faɗamin ba , murmushi nayi sannan nace kiyi haƙuri Aunty , tsoki tayi tare da kashe wayar bata sake magana ba , tana kashewa na kira malam ɗayyu shima mun gaisa muka ɗan taɓa fira sannan yace min kina katsina kuwa ? Nace masa kana san gani ne ? Yace Eh nace ina Abuja , yaushe kika tafi ? Nace jiya da daddare , yaushe zaki dawo ? Sai bayan wata ɗaya ina faɗin haka na katse kiran malam ɗayyu. Lallai kawai abinda zai faru , tabbas akwai masu farautar ruhi na , mutum ya bashi da tabbas kuma yakan iya canjawa a cikin ƙanƙanin lokaci , kuɗi sunkan canja mutum tsoro yana canja mutum , nacewa Alaji ina Lokoja , Aunty Suwaiba nace mata ina Kaduna , na faɗawa Malam Ɗayyu ina Abuja , Dady kuwa na faɗa masa ina Katsina....... Murmushi nayi tare da ajiye wayoyi na a gefen katifa dani daku mu zuba lumfashina yana hannun ubangiji idan mutuwa ta yazo wayau ko tsimi da dubara bazai hanani ansa kiran mahalicci ba , fatana Allah yasa inyi kyakkyawan ƙarshe. Amisty da Bello zaune a mota , bayan ya kora mata wani birkitaccen sharhi ya ɗora mata da cewa yayi tarayya da Sultana ne ta ɗauki hoton videon abinda mukayi tana ta bazashi a social media gashi yanzu ta durƙusar dashi a harkar wasan caca idan Amisty zata iya tou da Allah ta kawo mishi Sultana ko ta faɗa mishi wurin da Sultana ke zama idan kuma bata sani ba ta binkico mishi inda Sultana take a cikin sa'o'e 24 zan bata naira dubu ɗari , Su Amisty anji zancen kuɗi dan haka tace ai sanin inda take ba abu bane mai wahala dan nima haƙe nake da ita saboda ta ɗauki tsiraicin mahaifina ta turomin , naso na ɗauki na ubanta nima na tura mata dan kai kanka kasan nidai Binna Allah kaɗai yasan iyakar abinda ke tsakaninmu , ina san Binna tunda nake ban taɓa huɗɗa da wani namiji ba sai akan Binna , shine ya koyamin ya gogar dani tun ban iya ba har na ƙware dan Binna aharkar mata yai zarra , na jaraba bin wasu mazan amma banji daɗinsu ba nayi niyar ɗaukar videon tsiraicin shi sai nayi tunani idan har ya sani nice nayi masa zai rabu dani ni kuma idan ya barni bansa ya zanyi rayuwata ba , kwatsam kuma sai ga mutuwarshi dan da na lashi takobin auren Binna dan in dasawa Sultana baƙin dafi mai wahalar amayarwa amma sam Binna yace bazai aureni ba. Murmushi Amisty tayi mai cin rai tare da cewa Hmmm Allah ya jiƙan "yan maza a ƙiyama , Binna namijin duniya jajirtaccen namiji mai kafawa mace soyayyar shi a zuciyarta mai wahalar goguwa ya tafi ya barni da maraicinsa , na tsine kuma bazan daina tsinewa wanda yayi sanadiyar mutuwar Binna ba , amma a tsaye nake saman ƙafafuwana saina wulaƙanta rayuwar Sultana idan dai har ina numfashi a duniya... Ta ƙarasa maganar tare da fara kiran wayar Sultana , ni kuma lokacin da kiran wayar Amisty ya shigo cikin wayata a lokacin muna gidan abokin Dikko su suna saman tebirin cin abinci sunayin kalaci dan tunda Ashiru ya kawo abin kalaci Dikko bai fito dashi daga mota ba yace idan yazo nan zamuyi kalacin tunda jiranshi akeyi wai wasu dokuna ne aka kawo mishi zai gansu , shi kuma abokin nashi ya uzira mishi wai zai tafi ɗauko matarshi , Ko ina zai ɗaukota Oho mishi , ɗaukar wayar nayi muka gaisa , bayan gaisuwa Amisty tace uwar room gaba ɗaya kin manta damu , miye duniya dake abu baya wucewa wurinki ? Da Allah kiyi haƙuri idan dai akan abinda ya faru baya ne muyi haƙuri abinda ya wuce ya zama labari muyi haƙuri dukanmu mu fuskanci sabuwar rayuwa , Labarin Babana ne ya dawo min a kaina da yace bayan nayi fushi da Bello saida yayi yadda ya yaudareni ya sake dawowa dani cikin rayuwarshi ya jagwalgwalamin rayuwa , murmushi nayi cewa ba komai Amisty ya wuce , to kina ina ne yanzu dan ina so inzo har gabanki in durƙusa a saman guyawuna in baki haƙuri , ina kano aiko yanzu ma sa'a kikayi kika sameni gab nake da kashe waya kiranki ya shigo , Amisty tace me kikaje yi kano uwar ɗaki ? Zanje Lagos ne kuma a jirgi zan tafi , tou yaushe zaki dawo ? Ƙarshen wata ina faɗin haka na kashe wayata murus , Shiru Bello yayi bayan ya gama jin wayar Sultana da Amisty , bayan wani lokaci yace ma Amisty jeki kawai zan dawo anjima , fita Amisty tayi daga cikin motar tana mishi addu'a Allah ya dawo dashi lafiya ta wuce , Fitar Amisty Bello ya dunƙula uwar ashariya yace lallai yarinyar nan ta ɗauki mutane "yan iska , dan duk wanda sukayi waya da Sultana banda Dady a gaban Bello akayi ta , saboda Bello yaje gidan Baba Ƙarami ya tambayeshi inda Sultana take a matsayinshi na aminin mahaifinta , Baba Ƙarami yace baisan inda Sultana take ba tunda shi Baba baisan baƙin halin Bello , Bello yace masa ko kasan mutanen da take huɗɗa dasu ? Kai tsaye Baba ya faɗi Alaji da malam ɗayyu , kuma duka mutanen nan babu wanda yasan Bello sunansa kawai sukeji , kuma babu wanda yasan akwai tsama tsakanin Bello da Baba , koda yaje wurin malam ɗayyu cewa yayi shi aminin Baban Sultana ne kuma yana nemanta dan ta tattaro mishi kan "yan gidansu ya taimake su , kuma ya kira wayar Sultana bata ɗauka kila bata ɗaukar baƙuwar number , shine yace malam ɗayyu ya kira Sultana suji ko tana ina ? Tunda shi tana da number shi , Da malam ɗayyu ya kira bata ɗauka ba shine ya kira Aunty Suwaiba , kuma duk da suka samu damar yin waya da Sultana ta rarraba musu , tacewa Alaji tana lokoja , ta cewa Aunty Suwaiba tana Kaduna , ta kuma faɗawa malam ɗayyu tana Abuja da sukayi waya da Amisty kuma tace tana filin jirgin kano a cikin jirgi zasu tashi yanzu zuwa Lagos , Itama Momy da aka faɗa mata cewa Sultana bataje makaranta ba cewa tayi karsu sake su dawo sai sunganta , Shi kuma Bello bokanshi yace dole sai an kashe Sultana idan ba haka ba masifa da balbalin bala'e tsutsar magana zata cizar mishi harshe zai tonawa kanshi asiri duk abinda yayi zai faɗa da bakinshi makarin wannan masifa shine kisan Sultana.... Dikko kuwa bayan sun gama kalacinsu da kanshi ya tattara komai ya bani yace in mayar a mota , ansa nayi naje nakai mota na dawo na samesu a inda suke ta tattaumawa , maganar dokunan kawai akeyi a hankali abokansu suka fara cika gidan sai an zakuɗa doki yayi sama yana haniniya sai ayi mishi hoto , hanayi kawai ke tashi ganin inda muke tsaye mutane sun fara yawa Dikko yace in koma mota in jirashi yana jiran Umar yazo ne , dan abinda na lura shima gidan babu mata a ciki, Wurin mota nazo na tsaya ina neman sa'a inyi waje , ina tsaye ina neman sa'a nake ganin rashin aikinyi na maza ko kuwa rashin sanin darajar kuɗi ne , dan naji wai duk doki ɗaya ana maganar miliyoyi gaskiya Dikko baisan darajar kuɗi ba , wato rayuwarshi zata ƙare a mota ne da dokuna sai yawon tsiya kamar kuɗi , na daɗe a wurin sannan Umar yazo. Umar na shigowa na samu nasarar fecewa daga cikin gidan , da gudu na fita ina gudu ina ɗaura niƙaf ina ,gidan baya da nisa da titi saidai kawai ace anguwar gayu ba'a samun abin hawa tunda mafiyan su kowa da mota yake amfani , Wayar da Dady ya bani na ciro na kirashi yafi a irga amma bai ɗauka ba , na kirashi har na gaji yaƙi ɗauka , ganin bai ɗauka ba kawai nahau napep na nufi makaranta dan a tunanina yayi fushi na ɓata mishi lokaci , Ina fitowa napep da Al ' Ameen na fara cin karo ina ganinshi na nufi napep da gudu da zumar komawa , dan tunda Dikko yacemin Al ' Ameen baya so na yana biye da rayuwata dan ya ɓatamin suna yasa ina ganinshi na nufi hanyar komawa dan karya bawa Dikko labari ya ganni tare da wani , yawwa gata can ku kamota , inajin ance a kamoni ai banma yi gigin komawa napep ba na ibi santa nabi ta lunguna na yanki fili naci gaba da gudu , ai kamar kura taga kare haka suka biyoni da gudu , ganin da gaske ni suke bi yasa na sake tattarewa naci gaba da gudu kamar raina zai fita. Dikko kuwa bayan Umar yazo ya dawo mota bai samu Sultana ba , idan hankalinshi yayi dubu ya tashi da guda² cikin palon ya koma dan a tunaninshi ko ta gaji da tsayuwa ta koma ciki , ya duba bai ganta ba ya dawo ya duba iya inda yasan mutum zai iya lafewa a gidan babu Sultana babu ma mai irin siffar mata a gidan kawata² , Wayarshi ya ciro daga cikin aljihu ya fara kiran wayarta amma a kashe , dan tunda ta gama waya da Amisty ta kashe wayar , cikin tashin hankali Dikko ya shiga mota ya fita daga gidan da gudu wallahi kai tsaye makarantar su Sultana ya nufa dan a iya fahimtar da yayi mata tana da taurin kai da kafiya abinda tasa kanta shi zatayi bata jin bari kuma bata san yi haƙuri ba , tunda tasawa ranta zuwa makaranta yasan sai taje can wallahi. Shi kuma yau yayi alƙawari idan harya kamata sai taji babu daɗi saiya jagula mata rai yadda ko baya nan idan yace mata kar tayi abu zataji tsoron fushinshi , Ta wata ƙatuwar santa na ɓullo ina ta raba idanuwa kamar nayi ma sarki ƙarya , ina ta murna na samu wurin ɓoyo , duƙawa nayi tare da cire niƙaf ɗina ina fita da hijabina dan nasha gudu zafi ya tasomin , ɗan lumfashe idona nayi ina maida numfashi bayan na sarara buɗe idon da nakeyi mukayi ido huɗu da Bello , kamar a mafarki da sauri na ƙara buɗe idanuwana wata irin harara ya zabgagamin bara'uban nan wani irin tsalle nayi na haura wata katanga na tsula da gudu Bello ya biyoni , tashin hankali abinda na ambata kenan yayin dana juya naga rundunar da suka biyo bayana , ga masifar yunwa da nakeji duk yau babu abinda naci gashi juwa ta fara ibana , har bana ganin gabana sosai saboda wahala...... Dikko kuwa bayan yaje makaranta yayi bincike ce masa akayi Sultana bata zo ba , jinjina kai yayi cikin tsananin ɓacin rai wallahi idan har An mata ta bari ya kamata yana cikin fushin nan kashin ta ya bushe , Bello kuwa cewa ya farayi wayyo jama'a ku tare ku taremin ɗiyata ku agazamin don Allah , dariyar mugunta nayi tare da addu'ar Allah yasa masu bin bayana su riƙe Bello suce tunda shine ubana su bashi azaba mai tsanani......... 13/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 57 Follow me on wattpad meelatmusa Muryar Al ' Ameen naji yana cewa daga duniyar mutuwa ka dawo bayan ka mutu kuma kowa ya sani , Bello yace wallahi nine ubanta ni na haifi abuna ku baku lura da kamin mu ba shi wancan ai uban riƙonta ne , cikin shashsheka ta wanda yasha gudu harya gode Allah ya ɗaga murya cewa ki tsaya mu tafi gidan Sultana , muryar wani daban naji shima cikin haki yace kai kuma neman me kake mata ? Allah ya kama bakin Bello yace wasu ke harinta kuma kasheta zasuyi shi yasa zan tafi da ita in ɓoyeta , shi a tunanin shi wannan wayau ne , domin gani yake idan ya kamani ko wani abu ya sameni baza'a zargeshi ba , a gajiye na kurɗo ta wani siririn lungu na sake bullowa bakin get in makaranta mu , kai tsaye na hawo titi yayin da Al ' Ameen ya ɗauki wani irin lafiyayen dutsi ya saitani ya jefoni da ƙarfi , na tafi tangal² zan faɗi kafin in gama saita kaina ya sake dan ƙaromin wata jifar , Jama'a suka fara kai ׳ lafiya ? Al ' Ameen baya saurarar kowa gaba ɗaya sukaci gaba da jifata kamar muslmin da yayi ridda yayin dana raba tsakiyar titi biyu na kasa gaba na kasa baya , tsayuwar da nayi ne na kasa tafiya saboda jifar dasu Al ' Ameen sukayi min suka samu nasarar riƙeni sukaci gaba da dukana wai na basu wahala yayin da suka kasu gida biyu wasu suka riƙe Bello suna kai ɗan iska kaine ka ɗaure mata ƙugu take abinda taga dama ko ? Kai tsaye yace Eh , saida suka bashi kashin bala'e ko motsi baya iyayi sannan suka ɗaureshi suka jefa banza mota kamar kare , lokacin da aka kai Bello mota aka dawo neman Al ' Ameen aka farayi amma tuni yayi layar ɓata babu wanda yaga ta inda yabi ya wuce. Gaba ɗaya hankalin kowa ya koma wurin Dikko dake zaune cikin mota yana kallonmu , a tunanina ni bai ganni ba , dan haka ina ganin sun juya hankalin su ya tafi wurinshi nima na samu sa'ar ɓacewa daga wurin , cikin ƙanƙanin lokaci na isa gida jikina sai ciwo yakemin ina zuwa wanka nayi da ruwa masu ɗumi , bayan na fito na canja kaya naje na zuba abinci naci nayi kwanciyata , Gaba ɗayansu wurin Dikko suka nufa cikin farin ciki dan ba saboda Dikko suka saki Sultana ba sundai tafi maularsu ne kawai , kuma shi kullum ranshi a haɗe yake shi yasa baka iya gane a wane irin yanayi yake farin ciki ko damuwa , Sudai umarni kawai aka basu su kamo Sultana saboda haka basu san komai game da ita ba , sundai ga Dikko kawai sunzo su gaishi dan sun san zasu samu kuɗi ne a wurinshi shi yasa suka saki reshe suka kama ganye , suna isowa suka fara kirarashi irin dai yadda "yan maula sukeyi , kallo ɗaya yayi musu ya ɗauke kanshi yana so yaga ta ina Al ' Ameen zai ɓullo , Shi kuma Al ' Ameen bayan wasu mintuna a tunaninshi Dikko ya tafi dan haka ya fito daga maɓoyar shi , fitowar da zaiyi yaga Dikko dan haka baiyi gigin komawa wani wuri ba ya nufi mota da gudu ya shiga yaja ya tafi a haukace , da gudu Dikko yabi bayanshi dan yayi alƙawari yau da Al ' Ameen da An mata babu abinda zai hana ya tabbatar da baƙin ciki a zukatansu ba , Abinda yasa zai ci mutunci Al ' Ameen saboda yadda yaga yana jifar An mata ya wulaƙanta mishi "Yar matanshi kuma shima sai ya wulaƙanshi ko da kuwa haka zaiyi sanadiyar gogewa farin ciki daga rayuwarshi har ƙarshen numfanshin shi , in banda ƙasƙanci "Yar mata ma zai jefa ? Kuma saman titi kowa yana wuce yana gani sai kace ta aikata wani babban zunubi....? Ita kuma yau zai nuna mata shi cikakken mai zuciya ne in bata san haukarshi ba yau zata sani kuma zatayi baƙin gani da dana sanin saninshi tunda yana tausaya mata bata sani ba , ya ɓarar da farin cikinshi da komai ya zauna tare da ita dan dai ya sama mata farin ciki da natsuwa , yabar matarshi ya taho wurinta shi zata maidai baisan abinda yakeyi ba , zuciyarshi kuma sai ƙara tunzurashi takeyi tana hasko mishi irin balbalin azabar da zai horar da ita da ita. Ai jima yayi bazai iya bin Al ' Ameen ba saiya fara da An mata , wani irin mahaukacin burki ya taka ya fara ƙoƙarinyin kwana saman tsakiyar titi yayin da mutane suka fara kaucewa dan kar ya gogar musu abin hawa , aiji yayi ma bazai iya tsayawa ɓata lokacin yin kwana ba , da ribos ya fita daga titin yana kai ƙarshe ya juya sitiyarin motarshi ya yanki hanyar goruba , yanda yake tuƙin ne yasa hankalin jama'a ya tafi wurinshi , yayin da wasu ke cewa ko lafiya wancan wasu kuma na cewa ai shi dama haka yake wannan iskanci babu abinda ya dameshi da rayuwar da wani zai shiga shi kanshi kawai ya sani dan Allah ya basu damar duniya shi yasa basu san darajar kowa ba , a , a gaskiya sun san darajar mutane shi dai kaɗai keda wannan halin , waye wai ...? Wani ya tambaya. Dikko ne ai shi kaɗai keda wannan baƙin halin mahaifi shi ba haka yake ba , wasu kuma cewa sukeyi ai ɗan iska ne , yayin da wasu kuma suke cewa aini burgeni yakeyi ko nine matashin da na samu irin damarshi saina fishi iskanci kasan su kuɗi jigo ne masu nuna isashshen iko ku barshi yayi Allah ya bashi gara yaji da ƙuruciyarshi wata rana ko ance yayi shekaru sunfi karfinshi baya iyawa , wani yace gaskiya izzar kuɗi da ƙarfi take muma Allah ka bamu masu amfani dan idan kana da kuɗi ji kakeyi kai kafi karfin kowa ka taka wanda kake so ka murje wanda ya shiga gabanka , magana dai ce ta kuɗi su zasuyi bayani kuma da kansu kuɗin zasu baka hakuri kuma ka haƙura , niko dai nace hmm ita dai rayuwa duk abinda mutunci baiyi ba rashin mutunci bazai yi ba , idan an ciza dai a busa dan ita duniya bata da tabbas yanzu takeyin ka anjima ta barka , idan ka raga sai ta raga maka dan duk abinda kake tunani kafi karfinshi sai a wayi gari ya gagareka Allah dai yasa mu dace , Bansan ta inda ya biyo ba kuma banji shigowar shi ba ina kwance dan har na fara bacci saboda gajiya , bansan yadda akayi ba kawai dai na farfaɗo naga ana ta riƙe Dikko yana wata irin zabura yana magana da turanci saidai inji yace An mata sai yace Momy yace Dady , Jini na gani a jikina bansan ta ina ya biyo ba , duk inda na shafa fuskata jini ne bansan da ina da ina ya fasamin ba , tunda nake ban taɓa ganin irin masifa ta Dikko ba ɗan bala'e ne na ƙarshe duk taron abokanshi sunfi su nawa amma wallahi girgiza ɗaya yakeyi ya zuddasu sai su sake riƙoshi so kawai yake ya iso wurina amma sun san idan ya sake riƙeni tawa ta ƙare , Ciƙin ɓacin rai yaci gaba da magana da hausar shi irin kamar bata riƙe mishi baki sosai ba wata irin magana yakeyi , kuma ba irin ta yare ba wata irin murya dai gareshi cikin sanyi yakeyin magana ko yana fushi maganarshi bata canjawa yarinyar can saboda ta ɗaukeni ɗan iska har marina tayi , yana nuna inda na mareshi yaci gaba da cewa idan aka buɗe min fili da irinki dubu duk wanda nayi ma duka ɗaya ya tafi bazai sake dawowa ba har abadan abada ko kina ganin tsoronki nakeji ? So hauka ne ? To ki sani bani na ɗora ma kaina ba Allah ya jarabceni kuma kema idan ya juya alƙamin sa akanki naki ya ƙare ƙaramar yarinya dake babu abinda ke cikin kanki sai wawanci da ƙuruciya , ke banda ƙaddara da hukunci Allah har kin isa kisha inuwa ɗaya dani ina ɗaga miki bakya gani tou yau ƙaryarki ya ƙare saina raba gangar jikinki da ruhinki , badai ina cewa kada Allah yasa kiga fushina ba ko ? Yau yazo kuma bazai tafi ba kin bani ׳ ya ƙarasa maganar yana nunani da ɗan yatsa , kwacewa yayi daga riƙon da sukayi mishi ya fita , Wani abokinshi da naji yana cema Yazeed yace ke An mata kike baki kyautawa abinda kikeyi ba'a rayuwa haka yana ƙoƙarin kare miki mutuncinki da martabarki bakya gani , tunda yace karki je dole sai kinje , yace miki bayajin daɗi yaji wani abu zai faru dake ai sai ki tausaya mishi kamar yadda yace miki jarabta ne daga Allah kiji tsoron jarabta ya dawo kanki , ke da kinsan halin DK da kuɗi idan yace kar kiyi wani yace kiyi zakiji tsoron fushin shi , Allah ma ya rufa miki asiri da mutane a gidan yau da kin gwamce ma aya zaƙinta , A tsiwace nace dan naje kawai sai ya dakeni ko ni baiwa ce ne ? Da mamaki Yazeed ya kalleni yace tou ai da yake yanzu zai dawo sai ki tambayeshi abinda yasa ya dakekin yama iya saka suna da yace miki An mata... "Yar ƙaramar yarinya dake sai tsattsaga masifa Dikkon ne ma dai² dake. Dama nace kaine dai² ni ? Dariya yayi yace ai riƙon mahaukaci sai sarki , nice mahaukaciyar ? Yace ah ah karin magana ne ni na isa ince miki mahaukaciya ai ke da ss kikayi kama sarkin bincike , dariya sukayi tare da tafawa suka koma palo sukaci gaba da kallon boll insu. Wallahi Allah yau sai an faɗamin abinda yasa ba'asan An mata a gidan nan , laifin me tayi muku ne wai ? Momy tace na tsani yarinyar nan Dikko idan zakayi rai kayi rai idan zaka mutu ka mutu dan ubanka bansan yarinyar nan kuma har abadan duniya bazan taɓa santa ba , kuma har gobe har jibi ina nan zaune akan bakana sai an kamo min ita kuma saina wulaƙanta mata rayuwa kamar yadda nayi alƙawari bazan fasa ba , Haba Momy wai me tayi miki haka da ciwo don Allah ? Me tayi min ma kake tambaya ko ? Tou ubanka tayi min kaji ko ? Momy bana so ayi abinda za'azo aji babu kyau ki sauƙaƙa zafin ƙiyayyarki akan ta kafin aji wani iri wata rana , ko wata ranar tazo banajin komai kuma babu abinda zai faru idan wanda ya mutu zai dawo naga yadda zakayi ka auri karuwa ina numfashi , Wai waye yace karuwa ce ? Abinda kowa ya sani duniya da mutane sunyi mata tofin Allah barbaɗe , murmushi Dikko yayi mai ciwo yace duk bakin daya tofawa An mata Allah tsine insha Allah saiya tofa mata albarka babu daɗewa , Momy tace mahaukacin banza ka taɓa ganin albarka ta sauka akan tsinuwa ? Ko ka taɓa ganin iccen da tsawa ta faɗa ma ya sake tofowa ? Ai tsawa so ɗaya take faɗawa icce ya mutu shikenan ya gama rayuwa a duniya dai , juyawa Dikko yayi bai sake magana yana tafiya cikin yanayin mai wahalar fassaruwa , Yace gaskiya ne nine tsawar da na sauka akan An mata , kuma Allah zai taimakeni ita bazata mutu ba zata rayu cikin farin ciki kuma zatayi ganye tayi rassai zata zama alfahari a wurinki Momy idan har na auri An mata zaki sameta mai biyayya , ajiyar zuciya ya sauke dakel tare da lumshe idanuwanshi a bayyane yace Allah dai ka taimakeni a gano min inda mahaifiyarta take da wuri in miƙata cikin aminci da salama. Harya taho bai samu nasarar ganin Al ' Ameen ba amma ya ja mishi layi zasu haɗu komai daɗewa kuma wallahi yadda ya jefi "Yar matanshi sai yayi mishi wulaƙanci na kafa tarihi marar gogewa a rayuwa. Da tunanin Sultana ya isa gidanshi baiji daɗin abinda yayi mata ba amma ya zama dole ya koya mata tsoronshi dan idan harya aureta da wannan taurin kan nata matsala za'a samu , dole ta yadda shine a samanta kuma dole ta koyi bashi girma idan dan tana ganin murmushin shi zaisa ta rainashi zai tsare girmanshi bazai ma sake mata wasa ba tunda ita bata da wayau , Cike da tsantsar sha'awar kasancewa da Jiddah ya shiga gidanshi , shi baisan abinda yasa idan harya haɗa jiki da An mata yakanji yawan buƙatar kasancewa tare mace ba , dakel yayi wanka yana fitowa ya samu Jidda zaune a gefen gadonshi tasha wanka na ɗaukar hankali sai zabgaga ƙamshi takeyi mai tada hankali duk mai wata "yar guntuwar sha'awa , Cikin bariki ta fara mishi sannu da zuwa dakel ya ansa dan rabi da kwata hankalinshi baya nan ya tafi wata duniyar , yau tafiyar safe kayi my excellency ? Kallonta yayi tare da tambayarta ina naje ? Murmushi tayi mai ɗaukar hankali tace Abuja mana , waye yace miki ina Abuja ? Ai naga kwana biyu baka nan nasan kuma idan kana gari ina zaka je bayan gani ta ƙarasa maganar tare da "yar karairaya dai ta matan da suka san hannunsu wurin iya tattalin miji , Wani irin kallo yayi mata mai tayar da tsikar jiki cikin salon tafiya da hankalin mace yayi magana cewa Ey to miye ? Yayi maganar tare da miƙa mata hannunshi , tasowa tayi bayan ta bashi hannun nata saida ya sumbaci bayan hannun sannan ya buɗe tafin hannun yayi tsini da harshenshi yayi mata wata irin lasa a tsakiyar tafin hannun nata ya ƙare da sumbatar inda ya lasa ciki tako mai nuni da yayi rashinta , lumshe idanuwanta tayi tare da sauke ajiyar zuciya cikin yanayi mai nuni da saƙonshi yazo. Jiddah fa ba'a baya ba shima Dikko jajirtacce cike da kulawa da junansu suka shiga masayar soyayyar ta hanyar ƙoƙarin dasawa junansu farin ciki irin na ma'aurata daga baya aka koma saman gado domin doguwar tafiya dole saida guziri , suma dai sunyi ma kansu guzirin gado , a sama aka caskale yadda ya kamata saida Dikko ya tabbatar ya kore duk wata tsohuwar ƙishirwar dake tattare da ita sannan shima ya samu natsuwa , amma wani abu da Jiddah tazo dashi shine , Kai tsaye ta nunawa Dikko kwalbar da bokansu ya bata cike da rashin wayau tace Yaya da Allah ka ɗan taimakamin , idonshi a rufe yana samanta bai sauka ba yace wane irin taimako ? Wani magani ne zan haɗa kuma da sinadirin namiji ake amfani dashi dan Allah ɗan kaɗan zaka zubamin anan ta miƙa mishi kwalbar , jin kwalba a hannunshi yasa ya buɗe idanuwanshi yace wane irin magani ne ake haɗawa da najasa dan tsabar ƙazanta , Nidai don Allah , tou ke me zai hana baza kiyi da naki ba tunda kece kike ra'ayi , ai na namiji akace , um umm aini ba namiji bane ba , nidai haka nan don Allah murmushi Dikko yayi a rashin shi yace kila wani fahami aka bata ta jiƙamin a soɓo mata ni sharrinku ai sai in rubuta littafi tunda cikinku nayi rayuwa , kallon agogo yayi ya jinjina kanshi yace da 15 yanzu zan koma 20 duk masifarki lokacin ya tafi bazai dawo ba , wato harma na namiji , Jiddah taci gaba da dan Allah dan Annabi , banza Dikko yayi bai mata magana ba , saida lokacin daya iba ya cika ya sauka daga saman gadon ya nufi toilet , bayan mintuna 30 ya fito , ƙananan kaya ya saka bayan ya feshe jikinshi da turare ko inda Jiddah take bai kalla ba ya ɗauki wayoyinshi ya fice. Yana fita ta ɗauki wayarta ta kira Al ' Ameen ta rattafa mishi yadda sukayi da Dikko , faɗa yayi mata cewa haba ranki ya daɗe ya akayi kikayi wannan kwaɓar kinja ma kanki nayi imani da girman Allah mai gida ya taso ki gaba da bin bincike kinja mana kuma ki rubuta ki ajiye wallahi ko ruwan gidanki bazai sake sha ba , ke kina wasa da mai gida ? Wai kin kuwa san yadda yakeji da rayuwarshi ? Kai gaskiya kin ɓata wallahi mi yasa kikayi haka ??? Jiddah tace no ka gane Al ' Ameen wannan ba damuwa bane ba idan haggu taƙi kawai mu dawo dama , ka bari saura sati ɗaya na fara period sai in zuba kawai ka kai mishi , tunda malam yace idan akayi amfani da jinan al'adata sai yadda nayi da Yaya , sperm in nashi ne yace idan anyi amfani dashi za'a goge mishi ko wace mace daga zuciyarshi saini ɗaya... Ba haka Al ' Ameen yaso ba kawai dai yace to , bayan sun gama waya da Jiddah ya kira Mardiyya tana ɗauka yace Doughter zan shigo kaduna zuwa cikin sati na gaba yaushe kike fara al'adarki ? Uncle meya faru ? Boka yace a kawo sperm in mai gida tou naso ace an samu amma matar tashi wata aljihun gefe ce ta kasa , wai dan wawanci irin na sakakkin "ya "ya kawai taba mai gida kwalbar wai ya zuba mata maniyinshi kiji hauka da ɓacewar hanya , dariya Mardiyya tayi tare da cewa Uncle ni zanzo in kawwo ƙarshen film in nan haka nan , Al ' Ameen yace karki zo dan in faɗa miki yauma nemana yake saboda tsigaggiyar yarinyar nan , yanzu dai yaushe kike fara naki jinin ? Mardiyya tace jiya na fara , Al ' Ameen yace tou zan shigo kadunar gobe in ansa in kaiwa boka , dan dama nama boka bayani akan ki zai haɗa maganin kinga idan akayi sai a kawo ma Jiddah sai mu samu tayi mana amfani dashi wurin ba mai gida , tana jiran taji soyayya sai kawai tajita a out... Cikin jin daɗi Mardiyya tace na gode Uncle Allah ya kawo ka lafiya yace amin my doughter ki gaishe da Yaya saina zo , zataji sukayi sallama. Wallahi ni ba Babanta bane ba , wani irin mari aka wanka mishi harsai da haƙorinshi na ƙurya ya fita , cikin kuka yace wallahi ranka ya daɗe ɗiyar abokina ce , wani ne yakai mishi duka a ciki tare da cewa idan tafi ƙarfinka batafi karfin hukuma ba , Bello cewa yakeyi wallahi ranka ya daɗe ba "yata ce ba , saida sukayi ma Bello lullusar fitar hayyaci sannan suka wurgashi a cell suna cewa idan ka kawota sai mu fitar dakai. Nayi ² na tuna abinda ya faru dani ban sani , na kasa sanin ta yadda akayi Dikko yayi min wannan dukan har yajimin ciwo ba tare dana sani ba , ko dami ya dakeni ? Duk yajimin ciwo fuskata kuma duk sahun mari ne lallai duk yadda akayi bugun bala'e yayi min tou meya ɓata mishi rai haka .... ? Dakel nayi sallah isha'e kafin in tashi daga inda nayi sallah masarar ta lulluɓeni kasa komawa nayi saman katifa duk jikina ciwo yakemin na kasa wani ƙwaƙƙwarar motsi gaskiya nasha azaba ta ban mamaki a ranar nan ! Tunda na kwanta ban iya wani isashshen motsi ba har gari ya waye , haka na tashi jikina yayi tsami dakel na iya yin wanka nayo alwallah dan yau na makara tunda na kwanta sai 8:39am na farka , Bayan nayi sallah ko mai ban shafa ba na saka kayana na fita palo , kamar jiya yauma yana zaune a inda ya zauna jiya ko inda nake bai kalla ba ya ƙaddara ma baisan Allah ya ajiyeni ba , daga nesa dashi na tsaya nace ina kwana , Bai ansa ba , kuma bai kalleni ba hankalin shi nakan wani littafi yana dubawa , wuri na samu na zauna kamar an sani na zame gefen hijabin nace duk wanda jamin ciwo anan ban yafe mishi ba , kuma tafiyata zanyi tunda bansan abinda nayi maka ka dakeni ba , na ƙarasa maganar ina kuka , Ba tare daya kalleni ba yace An mata zo nan , tashi nayi na tafi kusa dashi ina kuka , wuri ya nunamin na zauna , cikin tausayi ya kalleni yace nine baki yafe mawa ba ? Ni badai nake ba , to dawa kike bayan dagani saike a palon , aini ba kai nake jama Allah ya isa ba , to kin yafemin ni ? Kaina na ɗaga alamar Eh , yace kiyi haƙuri ni bana iya sarrafa fushi bansan abinda yake damuna ba idan nayi fushi saina sauke ki daina ɓatamin rai kinga dai ina sanki bana so kina shiga rayuwa mara kyau , kowa dariya yakemin wai An matar ma da nake taƙama da ita abida batajin magana kuma bata so na , kinsan me nake cewa ? A , a , na bashi ansa , kyakkyawan murmushin shi yayi tare da tsareni da idanuwanshi masu ɗaukar hankali yace ai nasan zaki faɗa ya ƙarasa maganar yana min hararar so , murmushi nayi cikin jin daɗi na gyara zamana ina kallon kyakkyawar fuskarshi gaba ɗaya sai naji masassarar da nake ji babu , yace ko nayi ƙarya ? Girgiza kaina nayi alamar a , a , Shi kuma yaci gaba da cewa ni ko nace zanyi fushi dake wallahi ƙarya nake bazan iya ba , da kinsan yadda kike da mutunci da daraja a wurina da kin daina wahalar da zuciyata da taki , kina ta fama da wahalar dakon so bayan nasan yanzu idan har zamu rabu sai kinyi kuka , tafiya zata iya riskata a ko wane lokaci zan tafi na barki da tunanina babu dare ba rana , zaki kasa bacci dare zai miki nisa wurin kwanciya zai miki girma zaki ga rana ta daɗe bata faɗi ba yayin da kika tuna Dikko baya tare dake , kawai ki daina wani ɓoyewa ki faɗi abinda ke cikin zuciyarki nidai tuni na faɗi nawa , ya ƙarasa maganar tare da miƙomin ɗan yatsan shi mu shirya , dan kinsan jiya na ɓata dake.... Miƙa mishi ɗan yatsana nayi ya lanƙwashi shi da nashi yace faɗamin me yasa bakya so na ? Shiru nayi yace amma ai kina so na mi yasa kike ɓoyewa ? Rufe idanuwana na nayi yace yi haƙuri An mata faɗamin matsayaina a wurinki me yasa kike min wasa da zuciya , Cikin kuka nace a wata rana kayi magana akan idanuwa na , to wannan ranar tayimin naji kamar in rungumeka a wannan ranar sannan nace ina sanka , Wata irin ajiyar zuciya ya sauke da sauri tare da dafe dai² zuciyarshi da duka hannunshi biyu ya kwantar da kanshi saman kujera tare da lunshe idanuwanshi yace me yasa baki faɗa ba a wancan lokacin An mata ? Shashshekar kuka nayi tare da cewa saboda ina tsoron kada na rasa ajina , sauko kanshi yayi ya kalleni yace wallahi Allah babu ranar da ajinki ko wani mutuncinki da zai rage a idona ko a zuciyata , ki taka yadda kike so ina tare dake tsakanin rayuwa da mutuwa , waccan ranar kinji kamar zakice kina so na , yau fa ? Yauma kinajin kamar kina so na............? Su Yazeed ne suka shigo palon , cikin zaulaya yace An mata an shirya kenan a dai² lokacin daya iso yaba Dikko hannu suka tafa , bayan sun tafa Dikko yace aimu bama faɗa ko An matana ? Jiya ma sheyɗan ne yazo kuma mun koreshi bazai sake dawowa ba ko ? Shiru nayi zan tashi ya riƙoni tare da turani saman kujera shima ya dawo kusa dani ya zauna su Yazeed suka samu wuri suka zauna , Yazeed yace zakaje ko ka fasa ne ? Ya tambayi Dikko , ɗan gyara bakinshi yayi ya riƙe leɓonshi na ƙasa dana sama yace gaskiya banajin zanje , a , a kar kayi haka kayi haƙuri ko daga ƙarshe ne muje ai yafi bamu je ba , kallona Yazeed yayi yace ai kema zakije ko "Yar mata , dogon kallo Dikko yayi mishi sosai sannan ya kalleni tare da nunamin inda makullin mota yake yace jeki ki ɗauko abinci a mota , saura idan kinje ki ƙara gaba...... Ɗaukar makullin nayi na fita........ 17/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 58 Follow me on wattpad meelatmusa Ina zuwa jikin motar na buɗe na kame a mazauni driver na tada mota na gyara parking kawai dan neman magana , Yazeed yace ga mutuniyar ka can zata fita , murmushi Dikko yayi tare da cewa wai dan in fita inta hayani so take ta maidani lusarin namiji , fitowa nayi na buɗe but in motar na fara fiddo ƙattin food flakes ina ajiyewa ƙasa. Ban gama fiddowa ba Dikko da Yazeed suka fito a dai² lokacin da aka buɗe get Umar ya shigo saman doki wasu motoci biyu kuma suka biyo bayanshi , ɗaukar ta miya nayi na nufi hanyar shiga palon ina zuwa na tsaya kusa da Dikko nace ka ɗauka fita zanyi ko ? Kallona yayi bainin magana ba , murmushi nayi tare da cewa dama dan inji yadda zaka ce , yadda zance ai a jikinki zakiji idan kin fita zaki dawo ki sameni ni kuma zan ɗora miki a inda na tsaya bazan gaji ba , yana faɗin haka ya gangare yana ba Umar umarni ya ida shigar da abincin ciki. Ina ajiye miyar ɗaki na koma na kwanta , shi kuma Dikko mota ya koma yana cema Umar ka taho da allurar ne ? Innalillahi bara in koma in ɗauko ya faɗi maganar yana mai lalabu aljihunshi ya fita da sauri daga gidan. Umar yana fita Yazeed yace DK yarinyar ka fa ta koma , gaba ɗaya hankalinshi yana cikin mota yana dube² yace ai zata fito yanzu , Yazeed ya fara ƙwala min kira An mata Dikko yace me zata maka ne ? Dariya yayi tare da cewa da Allah barta ta fito insha dariya , tsoki Dikko yayi yana fitowa daga cikin mota yace to ita abokiyar wasanka ce ? Yazeed yace dan Allah barta ta fito , Dikko yace to ai bani ne na hana ta fitowa ba ita idan tanajin yunwa ragguwa take zama ya ƙarasa maganar yana leƙowa ta window ɗakina yace me ye ? Ba komai na bashi ansa ba tare dana kalli inda yake ba , taso ki zo ina kiranki , ba tare da nace tou ba na tashi na fito wurinsu. Yazeed yace ke "yar yarinya sai kiyi ta zama a ɗaki sai kace mai jego ? Ki fito kisha iska sai fama kike da hijabi kamar matar mamaci , murmushi Dikko yayi yana kallona yaɗan shafo gemunshi da bayan hannunshi ta ƙasa yana cewa kai wallahi wannan matar ustaz ce ko An matana ? Ya ƙarasa maganar yana ɗagamin gira , murmushi nayi tare da matsawa kusa da Dikko hannu na yaja ya maidani mota yana cewa wani wuri zamuje kina zuwa in tafi dake ? A , a , ni banajin daɗi , tou meya sameki ko kema in miki allura ne ? Wace irin allura ? Allura nawa kika sani ne ? Idan mutum baya lafiya akeyi , Dikko yace to aikema kince bakyajin daɗi idan nayi ma doki kema sai in miki amma bazan miki da zafi ba , ni doki ce ? Nayi maganar ina harararshi , murmushi yayi yace An mata kenan kanki baya ɗauka dana faɗa miki wata magana idan ma dokince ke da kanki zaki faɗamin , Ɓata raina nayi nace kaina baya ja ? Dikko yace ba haka nake nufi ba ina nufin kinyi "yar ƙarama ni babba dani in zauna in ta sakin layi , idan na faɗa miki baza ki bani ansa yadda zanji daɗi ba ina iya faɗa ki dangana abun da wani shirme daban ki bani ansar da zata ɓatamin rai shi yasa kikaji nace haka......! Tou amma sai kace kaina baya ɗauka , Dikko yace a , a karfa muyi haka dake wai me yasa kikemin bahagguwar fahimta ne ? Kanki yana ɗauka mana abinda nake nufi maganganuna ni idan nayi miki sun girmi kwalwarki da lissafinki , fashewa nayi da kuka nace nice banda kwalwa banda lissafi , ɗaure fuska Dikko yayi cikin ɓacin rai yace An mata naje nace kiyi yadda zakiyi dani idan zaki iya mtsww ya fita daga motar yana sabbatu , Yazeed dake sauraren firarmu yayi dariya , tsoki Dikko ya sakeyi tare da ansar allura a hannun Umar ya nufi palo. Bai daɗe ba ya fito da wata "yar madaidaiciyar kwalba a hannunshi ya soka sirinji ciki yana tsotsowa , hararar inda nake yayi cikin yanayin jin haushi , fitowa nayi daga cikin mota nima cikin ɓacin rai na tsaya ina kallonshi yana ma doki allura. Bayan ya gama yake ma Umar bayani yadda zaiyi amfani da allurar yana ci gaba da cewa mantawa yayi da ya taho da ita kai kuma cewa nayi kawai kazo ka ansa ka kama ka taho doki ni bana san kuna hawan dokin nan tunda baida lafiya , wata takadda ya ciro a aljihunshi ya bashi yana cewa yayi sauri ya anso mishi , Yazeed kuma palo ya koma zaici abinci , wanda suka zo a mota suma fita sukayi tare da Umar , filin wuri ya rage daga ni sai Dikko. Ciki na koma na sako dogon wando tunda har naga ya ɓata rai akan rashin san hawan dokin saina hau na ɓata mishi rai nima , ban daɗe ba na fito Dikko yana cikin mota yana waya , motar Yazeed na taka saboda dokin a kusa da ita yake , cikin fargaba Dikko yace An mata ki bari karki faɗo kiji ciwo wai me yasa kikeyin haka ne ? Idan an taroki ta nan sai ki koma tanan wai meke damun kanki da Allah......? Banza nayi na ƙyaleshi na tattara hijabina na haye saman dokin , murmushin mugunta yayi ya koma palo makullin motar Yazeed ya ɗauko tare da rufe palon da makulli ta waje ya rufe gidan , ɗauke motar yayi daga inda take ya matsa da ita kusa da tashi , bayan ya kaita ya dawo kusa dani ya dafa dokin yace kinyi kyau bari in miki hoto ko kuma ba yanzu ba bari sai anjima , bakin dokin ya buɗe ya tura mishi wani abu bansan ko miye ya bashi ba , lokaci guda dokin ya firgice ya riƙa wata irin zabura yana jijjiga sai wata irin samarya yakeyi yana haniniya gaba ɗaya kukanshi ya cika kaf gidan... Kallona Dikko yayi yace ai dan ki ɓatamin rai ko ? Kema naki zai ɓaci sai naga mai sakoki duk sai jikinki yayi ciwo , idan kuma kin bari kika faɗo wallahi ta samanki zaiyi wannan haukan kuma ko sannu bazan miki ba , Allah ya taimaka a sauko lafiya , yana faɗin haka ya koma mota ya kunnata ya ɗage glasses yaci gaba da wayarshi cikin kwanciyar hankali ya barni saman dokin daya haukata.... Kallon nisan ƙasa da saman da nake nayi lallai idan na kuskura na faɗo wuyana karyewa zaiyi in mutu , gaskiya Dikko mugune , riƙe dokin nayi sosai gashi yaƙi tafiya wuri ɗaya ya tsaya yana hauka , Riƙe wuyan dokin nayi sosai ina kuka , saboda abinda na fahimta duk bayan wasu seconds ƙara haukacewa yakeyi , saiya jirgoni na rabo daga samanshi sai inyi sauri na ƙara riƙewa , tun ina dauriya har ƙafafuwana da cinyoyina suka fara ciwo , dani da doki haka kowa yaita kuka , Yazeed kuwa da yaji ihun doki ya taho dan ya fito yaji ƙofa rufe , ta window ya leƙa yaga Sultana ta haɗa zufa da hawaye waya ya buga ma Dikko bayan ya ɗauka yace haba DK karfa yarinyar mutane ta faɗo taji ciwo , Dikko yace yarinya tace bata kowa ba duk faɗin duniyar nan nine nake da ita , inajin daɗine kawai tana wahaltuwa a sauƙaƙe ita kangara ni kuma cuta , idan ma ta faɗo taji ciwo nine zanyi jinyarta ba wani ba , dan Allah zo ka buɗe tafiya zanyi , idan na gama abinda nakeyi ai kasan dole zan buɗe yana faɗin haka ya kashe wayar. Kwanciya nayi saman dokin na riƙe wuyanshi sosai naci gaba da kuka dan kawai na haƙura idan ma na faɗo duk abinda ya faru haka yazo a rubuce , tausayi na bashi ya fito yaje ya buɗe ƙofar ya saukoni da kuka na wuce da gudu na tafi ɗaki. Cikin kuka nayi wanka ina fitowa na saka kaya ko abinci ban samu naci ba na kwanta sai bacci , Saboda azabar duka da fitar da haƙorinshi yayi har fuskarshi ta kunbura , fito dashi akayi dan ya anshi na safe , wato duka , bayan an fiddoshi akace ina take ne ? Cikin kuka yace wallahi ranka ya daɗe bansan inda take ba , saida suka sake mishi lullusar fitar hayyaci sannan suka sake tambayarshi ka tuno inda take ne ? Cikin kyarmar jiki yace Allah ya taimake ka wallahi bansan inda take ba , cire mishi rigar jikinshi sukayi suka bashi azaba saida sukayi ma jikinshi kaca² suka rufe sahun dukan da gishiri , wata irin ƙara Bello yayi kamar ana cire ran kafiri yace oficer bansan inda take ba , Saida aka sake tattaka Bello wanda ya takashi yace lallai soyayyarta mai girma ce a zuciyarka , wannan ɗiya kanaji da ita sosai ya ƙarasa maganar tare da halbashi ya tafi suuu ya shige cikin magarƙama ya kullu yana cewa ka tuno inda ka ɓoyeta kafin nan da wayoyi biyar..... Cikin farin ciki Al ' Ameen ya ɗauki hanyar Kaduna , bayan ya gama zabgagawa Jiddah ƙarya ya anshi dubu ɗari biyar a hannunta kuma yasa tayi mishi full tank da motar da aka kwace daga hannun Sultana yace boka yayi kira na gaggawa za'a anso mata saƙo kafin zuwan jininta... Yana isa Kaduna ko hutawa baiyi ba ya ɗauki Mardiyya suka dawo zaria wurin mushiriki , bayan ya baje kayan tsafinsa yaci gaba da koro musu jawabi maganar dai ɗaya akan Sultana kuma ya tabbatarsu da rabuwar Dikko da Sultana babu jimawa ya ƙara da cewa kuma sai Dikko ya ɗiga ma Sultana ruwan rashin mutunci bayan yayi mata wulaƙanci da gori na rashin arziƙi zai korata... Bayan ya gama bayani ya anshi jinin hailar Mardiyya ya wurga kwalbar sama cikin ƙanƙanin lokaci ta dawo babu jinin a ciki sai garin magani yace Mardiyya ita da kanta zata zubawa Dikko a abunci ko abunsha idan dai tayi wannan tou magana ya ƙare , saboda Dikko zai zama nata ita ɗaya idan ta ajiye masa ƙara tace karya tsallaka bazai wuce ba saboda gudun ɓacin ranta , amma da sharaɗi a kiyaye kar wanda ya sake ta taɓa kwalbar nan saike idan kuwa wani ya taɓa bake ba tou kashinki ya bushe ya ƙarasa maganar yana nuna Mardiyya da ɗan yatsa ! Ansa tayi tare dayin godiya Al ' Ameen ya bashi dubu ɗari da hamsin tare da cewa dubu ɗari na aikin Mardiyya dubu hamsin kuma ayi mishi aiki akan mai gida ya maidashi bakin aiki dan gaskiya yana fama da talauci kuma gashi Dikko zaiyi tafiya yana so yaje dashi waccan tafiyar da Ashiru aka tafi , tafiya da mai gida kuɗi mutum yakeyi akafin a dawo.... Boka yace ya dawo sati na gaba ya anshi saƙo , godiya sukayi suka tafi har suka bar wurin boka basuyi maganar Jiddah ba , bayan ya maida Mardiyya gida ya bata cikon dubu ɗari 3 ya riƙe dubu hamsin yace ki sayi kaya masu kyau da turaruka wani satin idan na dawo sai in tafi dake wurin Momy ince kinzo gaisheta ta , ke kuma daga nan sai kici gaba da gyara aikinki har mu samu nasara , godiya Mardiyya tayi ma Uncle sannan sukayi sallama ya kamo hanyar katsina.... Sai bayan la'asar sakaliya na tashi daga bacci , shima bani na tashi da kaina ba Dikko ne ya tasheni wai in tashi haka nan inci abinci kada yunwa ta kama mashi ni , koda na buɗe idona na ganshi ɓata rai nayi na juya da niyar ci gaba da bacci , ke ki tashi haka nan nace fita zamuyi , basar wa nayi na rufe idona dan gajiya nakeji sosai tsakanin jiya da yau duk banji daɗi ba... Hawowa yayi saman katifar ko takalminshi bai cire ba tsabar wulaƙanci yana janye abinda na lulluɓe , kallonshi nayi sannan na kalli ƙafarshi , shima kallon ƙafar yayi yace palo mota kawai naje babu wani datti a jikin takalmina , Tashi nayi na sauka daga saman katifar nace na tsanaka , wannan ai ba baƙuwar kalma bace wurina , kin tsaneni bakya so na duk nasansu , Dikkon banza Dikkon wofi shima wannan ai na sani sai me kuma ? Baka burgeni , to aini kina burgeni ba lallai saini na burgeki ba , tunda ni ina sanki kuma kina burgeni kinmin a haka , fushinki da duk wani kunburinki bai damuna dan banma san kinayi ba ko aure mukayi kika ɓatamin rai sai nayi miki hukunci dai² da abinda kikayi kuma ko yanzu na zaneki miki jiki tass bazai hana in miki magana ba ko inƙi ansar haƙƙina a wurinki idan na biya buƙata ta kije can kita kunburinki , gara ki iya ki kuma koyi kauda fushinki ki koyi haƙuri dani ko kuma ki kiyaye ɓatamin domin da zaran nayi fushi bani ne ba gara ki koyi kaucewa fushina kawai sai ki zauna lafiya , wuce kiyi wanka kuma karki ɓatamin lokaci jiranki nakeyi. Wanka na shiga ina tunanin rashin kunya ta Dikko wato shi ɗan iska ma har tunani yakeyi zai dakeni kuma yayi tunanin kwanciyar aure dani , to wai waye ma yace yana san sa bare yasa ran zan iya aurenshi zuciya akamar ahalin kutare..... Koda na fito wanka a ɗakin na sameshi sai tattara duk wani abu daya shafeni yakeyi yana jibgawa a cikin trolley bag , jikina a sanyaye nace Yaya me yasa kake zubasu anan ko baka so ina ajiyewa a gefen katifa ne ? Shiru yayi baiyi magana ba yaci gaba da tattarawa amma yanayin fuskarshi babu daɗi , Cike da damuwa na matsa kusa dashi na duƙa nace D-kow wai miye ya faru ? A dai² lokacin daya zage ziff in jakar ya ɗago yace An mata dole rabuwa zamuyi , cikin damuwa nace mi yasa ko nayi maka wani abu bakaji daɗi ba ? Ba abinda kikamin kuma bana tunani har mutuwa ta zanji babu daɗi daga gareki , tou me nayi maka zaka rabani da kanka a dai² lokacin dana ke farin ciki kasancewa dakai , me yasa ka koyamin sanka kuma zaka rabu dani yanzu ina zaka kaini......? Me yasa kakemin irin wannan wasan nidai bana so dan Allah , na ƙarasa maganar tare da duƙawa na buɗe jakar na zazzage kayana ina cewa babu inda zanje , ina ne kake tunanin zanje bayan kasan kaine hatimin sa'ata sai kawai lokaci ɗaya ka rusa min sa'ar rayuwa tou wa kake so ya zauna dakai idan bani ba.....? Sake tattara kayan yayi ya maida cikin jakar ya rufe , cikin kuka nace wai me yasa kake min bana so bara na sake fiddo kayan idan ka mayar dasu nima zanyi fushi , riƙeni yayi yace gida zaki tafi , cikin hayagaga nace wane irin gida ? Dama inda zakuje dani kenan kaida Yazeed munafikai ne ku tou bazanje ba ɗin sai inga mai fitar dani haba da Allah , An mata , kafin yayi magana nace An mato Allah babu inda zanje sauƙaƙa kuka na nayi na rungume Dikko nace a gaban idonka jiya mutuwa tayi wasa da rayuwata , kuma kaga yadda tayi wasan kura da Babana , kowa baya so na Baba ƙarami ya koreni Aunty Mamy ta rasu , wata Aunty ta mutu ban ganta ba , shashshekar kuka nayi tare da sakin Dikko nace ita kuma Aunty Suwaiba cewa tayi in tafi dan bata san damuwa ta sake zuwa a rayuwarta , nazo wurinka shine zaka korani shikenan ka daina so na , goge hawaye nayi tare da ɗaukar kayan daya ajiyemin na saka ina kuka.... Cewa shikenan ba komai zan tafi amma ka bar kayanka bana so , dama ai badasu nazo ba , kusa dani ya matso zai riƙeni cikin hayani nace karka taɓani bana sanka , Allah ya gogemin kai a zuciyata na tsaneka , riƙe ƙugu yayi yana kallona cikin yanayin mamaki yace wai baza ki tsaya nayi miki bayani ba ko kuwa ke kaɗai kika iya fushi wai ? Ki bari bana so muyi rabuwar fushi dani dake ki tsaya ki natsu , bana san ayi rabuwar arziƙi ta bala'e nake so ayi , tsoki Dikko yayi tare da kiran Ashiru , babu ɓata lokaci yazo yace ɗauka jakar ina zuwa , ɗauka Ashiru yayi ya fita yana fita Dikko ya sake matsawo nace karka taɓani bana sanka... Zuƙewa nakeyi amma da ƙarfi Dikko ya riƙeni tare da rungumewa a jikinshi ya sauke wata irin wahalalliyar ajiyar zuciya mai saukar da kasala , tunda ya haɗani da jikinshi nayi shiru na kasa wani wadataccen motsi na kwantar da kaina saman ƙirjinshi na rufe idanuwana , shima rufe nashi idanuwan yayi tare da cewa An mata kiyi haƙuri kinsan ina sanki kuma ba wani abu kikamin ba , zan rabu dake ne dan sadaki da farin ciki na gaba tun ranar rasuwa Baba dana tambayeki Mamanki kikacemin bata nan ta tafi ta barki , tun daga wannan lokacin na duƙufa wurin nemota , bayan wanda nasa sun mun samota dakel suka mata bayanin ki cewa tayi ta yafe ki wa Babanku , Da suke nemi ba'asi , shiru Dikko yayi ya kasa ƙarasawa , abinda Inna tace shine taji baƙin cikin lalatamin rayuwa tayi kuka kamar ranta zai fita tun lokacin da abokan zama sukaji Baba ya sakani a wasan caca suka farayi mata gori da habaici suna cikin farin ciki , bayan sun samu labarin abinda akamin aka yadani a ƙofar gida shine kunya tasa ta gudu dan bata iya haɗa ido da kishiyoyi , bayan ta tafi shine Baba ya aika mata da saki har saki 3 yace shi mace bata mishi yaji kuma ba'a kome a gidanshi.... Shine ta nemi ya bata ni amma yace ai bai gagara riƙe Uwar masu gida ba , ko dan tana ganin suna da kuɗi a gidansu take tunanin zai bata "yarshi shi jininshi baya zuwa kwaraka dan su basu gaji kwakwa ba , Ko baki faɗa ba nasan kina so na An mata , ina sanki bazan iya zuwa rakaki ba nima cikin daren nan zan bar katsina bansan zamu rabu a dai² irin wannan lokacin ba , karkiyi rashin ji banda yawo kinji ko ? Duk wani bincike ² ki daina kibarma Dikko komai tsaye nake babu dare ba rana akanki An mata ko bacci nake kece a saman idona , kece mafarkina komai na kece rayuwarki kaf a raina take ki natsu dan Allah dan annabi , idan kuma kikayi taurin kai zanzo kuma kinsan abinda zai faru , Kwanaki na ce bana zarginki , kinsan abinda yasa nace miki haka ? Shiru nayi banyi magana ba , yace kinga ya nunamin tafin hannunshi yace duk motsinki yana nan ciki kuma na yafe miki abinda kikayi a baya nasan ɓacin rai ne da ƙaddara karki ƙara kinji ya ƙarasa maganar yana ɗagoni daga jikinshi ƙara komawa nayi na kwanta murmushi yayi mai sauti har cikin zuciyata ya soka , yace insha Allah zamuyi aure babu jimawa An mata zan dasa farin ciki a rayuwarki nima ki haifomin wata "yar matan , amma bamai taurin kai irin naki ba ya ƙarasa maganar cikin zaulaya..... Dakel ya ɓanɓareni daga jikinshi ina kuka ya kamo hannuna muka fito , muna shigowa palon gaba ɗaya abokanshi suka taso suna Allah sarki An mata tafiya zakiyi ? Yazeed ne yake cewa sai munzo zance , ko zaki hau dokin bankwana , dariya sukayi dukansu Dikko yace kadaiji kunya , Yazeed yace kaine kaji kunya daka ɗora An mata a doki har tayi kuka , murmushi Dikko yayi tare da cewa Allah yasa ma banji abinda kace ba ! Har wurin mota suka rakani , Yazeed yace yana zuwa , gaskiya sunmin halakci suna cewa basu san zan tafi ba , yawansu da daloli suka sallameni Yazeed ne ya bani kyautar zoɓen zinari mai kyau amma Dikko ya ƙwace shi ya ƙaryashi tare da cewa suma dan karsuce wani abu na barta ta ansa kuɗinsu sai kai ɗan haɗama zaka bata zobe ? Tou har yaushe ma ka siya ka ajiyeshi ? Wato kana jira idan bana nan ka saka mata ko ? Ko ni na taɓa ba matarka kyautar zobe ne ? Cikin yanayin rashin jin daɗi Yazeed yace aikai ba matarka bace ba kuma dan na bata zobe miye duk su da suka bata kuɗi baka ansa ka zubar ba saini ? Dikko yace kaima ka bata kuɗin kaga idan ban barta ta ansa ba , ai ni ban fito da kuɗi ba , sai zobe ka fito dashi ? Allah dai yasa ta tafiya zatayi ɗan iska ƙaton banza kadaiji kunya wallahi , ashe da anci amanata..... Dariya sukayi gaba ɗayansu hada Yazeed banda Dikko amma maganar dai cikin sigar zaulaya yayi ta dan dai bai cika dariya ba kawai ke baiyi ba , Yazeed yace ba komai An mata zanzo jibi , Dikko yace Allah ya kaimu , kallona yayi yace An mata Yazeed zaizo jibi idan muna da rayuwa amma idan yazo ya baki zo be a , a , kinji nace tou , to ku tafi muyi bankwana yace , wani ne daban yace to ku tafi tare kawai mana , murmushi Dikko yayi tare da fita daga cikin motar yace sai munyi waya ya ƙarasa maganar yana rufe motar... ! Ashru yaja muka tafi daga gidan suna ta ɗagamin hannu , kukana ƙara yawa yayi ina cike da kewar Dikko , tunda muka hau titi na duƙar da kaina naci gaba da kuka ina maraicin Dikko da duka zuciyata..... Da malami da karuwa ba abin yadda bane ba dan basu da amana , Al ' Ameen kuwa saida yazo malumfashi ya tsaya wurin wani gahurtaccen malamin tsubbu ya anshi asiri , abinda yasa bai anso wurin boka ba saboda Jiddah taga wurinshi taje tayi mishi ɓarin kuɗi ya kwashe komai ya faɗa mata , asirin farko Jiddah karta riƙa jin maganar kowa sai nashi , na biyu kuma Dikko akayi ma ya maidashi aiki na ukku kuma , Sultana rabuwa ita da Dikko , na huɗu kar Jiddah ta aihu dan so yakeyi duk wannan tulun dukiyar ta Dikko su lasheta idan Mardiyya ta aihu sai su kashe shi su cinye komai nashi.... Bayan yazo katsina ya bawa Jiddah yace inji boka kuma duk ya faɗa mata yadda zatayi amfani dasu hada wanda zata zubawa Dikko a abinci godiya tayi sosai ta bashi dubu ɗari 3 tace yasha maganin gajiya , godiya yayi sannan ya fita... Dikko kuwa tafiyar Sultana bayan kowa ya tattara abinda yake buƙata government house suka nufa bayan ya shirya ma abokanshi abinda ya shirya dan ya kuɓutar da Sultana daga tarkon Momy ta shafawa An mata lafiya tayi rayuwarta free. Tare ya shiga da zugar abokanshi da sukayi amfani da motoci huɗu , bayan ya fara bincika Al ' Ameen bai samu ba , daga inda yake tunanin zai samu Al ' Ameen babu kai tsaye ƙofar palon Momy suka nufa bayan sunyi parking ya zame ya rufe idonshi , gaba ɗaya suka fito daga cikin motoci suka fara ƙoƙarin fito da Dikko daga cikin mota , jin tsayuwar mota yasan ƙannenshi mata suka fito dan sun san shi kaɗai ne ke zuwa da irin wannan tuƙin kuma sunji an ɗauki lokaci bai shigo ba suka fito , su dai Allah yasa musu san ɗan uwansu kodan shi ɗaya ne namiji ? Da mamaki sukaga ana fito da Dikko daga mota sai kakkafawa yakeyi , wayyo me ya samu Baban Dady sukayi wurin suna kuka dasu aka fiddo da dikko daga mota aka shiga ciki ! Momy na zaune a cikin ƙaton palon gidan gwamnati tanajin daɗin ta bata da wata damuwa ko tashin hankali na duniya tana shan iska yadda ya kamata taga an shigo da Dikko sai kakkafewa yakeyi , ciwon da bata taɓa ganinshi da irinshi ba gaba ɗaya ta ruɗe cikin tashin hankali tace meya sameshi ne ? Wanda Dikko ya ɗaura a matsayin lawyer n shi yace wai kasashi akayi ne ? Gyara zaman kallabin kanta tayi tace miye kasawa ? Wata yarinya yakeso shine akayi mata aure , cikin hargowa Momy tace wace yarinya ? Yazeed yace muma bamu santa ba kawai dai muna zaune ya faɗi yana cewa An mata , dariya Momy tayi tare da cewa shikenan Allah ya raba faɗa , yaushe akeyin bikin ? Yau aka kaita gidanta , Momy tace babanta yaci uwashi shi yasa yayi sauri yasa akayi mata aure , Bedroom ta nufa ta ɗauko magani tazo ta zuba mishi amma saiya watsoshi maimakon ya miƙe , ƙara zuba mishi tayi ya ƙara fesewo , cikin ruɗewa ta koma ciki "ya "yanta suka bita suna kuka , tana shiga Dikko yayi murmushi tare da ɗagawa su Yazeed gira ya kashe ido ɗaya ya koma yanayin da yake kamar baya , a firgice ta sake dawowa da wani maganin tana ni maganinshi kamar yana wurinshi , a ruɗe ta fita dan wannan ciwon ya tadawa Momy hankali da gudu ƙannenshi sukabi bayanta dan sunga mahaifiyarsu tana cikin tashin hankali , tana fita Dikko yace ko idan ta sake zubamin maganin ince bazan tashi ba sai an kawo An mata , wani yace a kawo ta daga gidan ubanwa bayan kace muce an mata aure , zaro ido Dikko yayi cewa innalillahi na rantse da Allah da nasan hankalin Momy zai tashi haka da ba wannan dabarar akayi ba , wayyo Allahna gani gareka , shigowar Momy wata irin zabura yayi tare dayin harbe² danma karta ga kamar yana magana shi yasa ya birkice su Yazeed suka fara ƙoƙarin juyoshi amma duk yawansu suka kasa firgito Dikko , Yazeed yace karfa ƙaramar magana ya zama babba..... Duk wani shaƙe² Momy tayi amma Dikko yaƙi tashi gashi Dady baya nan , ciki ta koma ta kira Dady ta sanar mishi abinda ke faruwa , inda zata samu maganin da yayi mishi amfani dashi a gidanshi ya faɗa ajiye wayar tayi ta fita da sauri ta daɗe sosai sannan ta dawo ana shaƙa mishi ya miƙe yana tari da atishawa Yazeed yace ashe da gaske....? Momy tace da gaske mana ai dan ubanshi yasan baida cikkar lafiya yake so kashe kanshi , dan anyi mata aure miye ? Ba rabokan bace shi yasa baka sameta ba , nasiha Momy tayi ma Dikko daga ƙarshe tace ai An mata hadari ce kuma tazo ta tafi kawai ya manta da ita , Tashi yayi baiyi magana ba ya fita suma abokanshi suka bi bayanshi , suna fita suka fara kai daga wasa sai kawai kayi mana haka ? Ai ka sake ganin mai rakoka kayi ƙarya , bai basu ansa ba suka ga ya shiga mota da gudu , ashe Al ' Ameen ya hango , Momy data fito dan taga yanayin jikinshi ko ya warware tana ganin Dikko a mota ta hango Al ' Ameen cikin tashin ta nufi wurinshi ta ciro makullin dakel yayin da Dikko yayi tsalle ya tsallake motar dake gefenshi , tace su Yazeed su riƙeshi suna riƙeshi yayi wani irin ihu yace saina kashe shi , ya watse su gaba ɗayansu suka faɗi ƙasa , cikin ruɗewa Momy tace ku rufamin asiri ku riƙoshi , da gudu suka tashi suka bi Dikko yana wata irin zabura , Momy kuwa fashewa tayi da kuka tare da cewa ya Allah kayimin sakayya tsakanina da duk wanda keda sa hannu acikin lalurar Dikko , an maidamin ɗa mahaukacin ƙarfi da yaji , wani irin ihu Dikko keyi yana wani irin gurnani mai tada hankali dasu Yazeed sun riƙeshi saidai ya ɓaresu yana wata jijjiga , yayin da Al ' Ameen ya haye saman wani ƙaton tanki yana fitsarin tsoro , dakel aka kai Dikko ƙasa da taimakon duk wani maiji da ƙarfi dake gidan , cikin kuka Dikko ya ɗaga ido dakel ya kalli Al ' Ameen a hankali idanuwanshi suka rufe Momy tasa aka dawo dashi ɗaki.... Sai 1:30am su Yazeed suka tafi amma har yanzu Dikko bai dawo ba , momy tasha kuka kamar ranta zai fita wasu matan basu da adalci ita ba ita taba kanta Dikko ba Allah ya bata shi dan kawai an nemi namiji a gida ba'a samu ba ita ta aifa sai kawai a hana yaro ya zauna lafiya , tou wallahi bata yafe ba kuma bazata yafe ba duk wanda yayi ma Dikko wannan abun ubangiji ya saka mishi Allah kuma ya bashi lafiya duk da dai tasan yana da baƙar zuciya da rashin ɗaukar iskanci abun yayi yawa , shikenan da rai ya ɓaci sai kawai mutum ya riƙa ɗaukewa kamar wutar nepa , ai kowa yanajin fushi kuma kowa yanayin zuciya su duk masuyi me yasa basa suma sai Dikko so kawai akeyi ɗanta ya mutu kuma insha Allah Dikko bazai mutu yanzu ba... Bayan ta gama kokenta ta kira mutanen da suka kama Bello tace suyi mishi dukan leƙa lahira ya dawo kuma su faɗa mishi idan ya fita ya nemi dafa'in zaman aure ɗiyarshi ta zauna karta fito daga miji idan kuwa ba haka ba to wallahi aka sake mamoshi na gobe saiya fishi jin daɗi... 19/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 59 Uhum wai ashe duk abin nan inna tana cikin garin katsina ita da iyayenta "yan gayu dasu sun wani shige cikin ƙaton gidansu sunayin farin ciki basu da wata damuwa abun su a cikin ɓarkeken gidansu dake cikin anguwar layout , yanzu Inna suna da wannan gidan wace ƙaddara taja mata auren Babana taja mukaje mukayi ta rayuwar cin ƙanzo da garin kwaki , wannan irin ƙaton gida an ƙawatashi da ciyayi ga ma'aikata an baza ta ko ina , amma dan mugunta suka bar Inna tayi rayuwa a gidan haya ina ma amfanin arziƙin da baka samma wanin ka..... Ashiru da kanshi ya shigar min da kayana har cikin ƙaton palon gidan da aka ƙayatashi da wasu irin azababbin kujeru masu kyau da tsada tayils in palon yasha guga duk dare ne sai ɗaukar ido yakeyi tvn bango da sifiku umm amma yanayin palon ya nuna tsohuwa ce ke rayuwa a gidan , wuri Ashiru ya samu ya ajiyemin jakata ya zauna gefen jakar...! Nima rakuɓewa nayi ina tunanin Dikko Allah yasa karya tafi yabar katsina tsakanin layout da goruba road ai ba wani tashin hankali bane kawai sai in riƙa zuwa ina yini wurinshi in dawo nan in kwana ! Murmushi nayi cikin yanayin jin kunya na rufe idanuwana tare da kwantar da kaina gefe ina tunanin yadda na kasance a jikin Dikko , Hannunshi mai laushi baya da wata wahala a cikinshi kamar ba'a amfani dashi , ƙara sinsina jikina nayi turaren Dikko a jikina kamar nice na shafashi , murmushi na sakeyi ina ƙara tunano yadda ya kamani dakel a jikinshi ya rungumeni , ajiyar zuciyarshi dana tuno itace tasa naji tsikar jikina ta mimmiƙe gaskiya Dikko yayi ya gama haɗuwa tako ina , ga aji ga natsuwa ga kyau ga wayewa ga gayu sai maganarshi mai sa mutum cikin halin tunani babu dare ba rana... Maganar Ashiru ta dawo dani daga duniyar tunanin dana lula , buɗe idona nayi naga wata dattijuwa mai cikar kyawu da asali kame a saman kujera tasha lulluɓi da gyale mai kyau kanta babu kallabi ta ɗora gyalen a saman kanta ta fiddo kunnuwata waje kodan ta nunawa mutane tasa "yan kunne zinari oho , kila kuma nata ra'ayin ne haka... Gaisheta nayi yayin da nakeji dama ahalin Babana ne dan duk cikar arziƙi ko asali na uwa tou wallahi na uba ne a sama dan uba dashi ake tunƙaho shine ado ga kowa ɗa , duk cikar arziƙi irin na mutum da duk wani mulki ko sarauta da yake taƙama dashi da bazar uba yake taƙama , da zaran ka rasa ahalin Baba na gari tou ka zama sai a hankali , cikin sakin fuska ta ansa gaisuwa daga nan na kama bakina nayi shiru sukaci gaba da fira da Ashiru , a cikin firarsu ne naji tana cewa wai inna ta tana Dubai kunji fa..... Sun daɗe suna fira da Ashiru kuma har sukayi suka gama ban saka musu baki ba , da Ashiru ya tashi tafiya saida na rakashi har mota ina cewa ya gaishemin da Dikko sosai kuma yace masa idan na kirashi waya ya ɗauka zanyi magana dashi yace insha Allah , saida ya tafi sannan na dawo ciki , Lokacin dana dawo har an shigar da kayana ciki , tsohuwar da nake tunanin itace kakata tayi min jagora zuwa ɗakin da zan zauna tana ta jana da fira cikin soyayya amma ni wallahi banajin maganar kowa saita Dikko domin duk ilahirin hankalina da tunani na yana wurin tunanin shi , abinda yafi tsayamin a rai kawai rungumar da yayi min da kuma fitar sautin ajiyar zuciyarshi... Gajiya tayi da surutu ta fita dan dai Sultana bata ita take ba , tana fita na shiga toilet nayi alwallah nazo nayi sallah bayan na gama kawomin abinci akayi naci ina gama cin abinci na soke saman gado na fara kiran wayar mai gida Dikko......! Na kirashi bansan so adadi ba amma bai ɗauka ba , tun inayi daga kwance har na tashi zaune haka kira zai shiga yaje ya dawo Dikko baya ɗauka , faɗuwa gabana yayi shikenan ƙarshe kawai zai kashe wayarshi ne daga nan sai ya manta dani , bansan yadda akayi ba kawai naji hawaye na gangaromin daga cikin idanuwana saida nasha kuka har na gode Allah bansan sadda bacci ya ɗaukeni ba na kwanta da tunanin Dikko a zuciyata , Yauma horon safe akayi ma Bello yaci ubanshi cikin farashi mai tsada , yayi kuka harya gode Allah , bayan an mishi kashedi akan karya kuskura ya bari auren Sultana ya mutu saida suka haɗa mishi jini da majina sannan suka sallameshi , yana fitowa ya faɗi a wurin da taimakon wasu tsirarun mutane suka ɗauki banza suka wuce dashi asibiti suna zuwa gado aka bashi dan lalubo mishi sauran rayuwa. Dikko kuwa sai asuba ya farko kuma da ihun saiya kashe Al ' Ameen ya dawo , dakel Momy ta rarrashi Dikko akan ya fita hanyar Al ' Ameen cikin gamsuwa yace mata ya barshi bazai mishi komai ba , Momy ta ƙara da cewa dan Allah uban masu gida kar na sake jin wani maganar kisa ya fita daga bakinka kar kuma ka sake ka dakeshi , jinjina kanshi yayi alamar bazaiyi ba ya ƙare ajiye kan da murmushi , Momy da kanta ta rakashi ɗakinshi , acan yayi wanka ya canja kaya ya fita masallaci , daga masallaci gidanshi ya wuce ko Jiddah bata san ya shigo ba kai tsaye ɗakinshi ya wuce dan har yanzu gajiya ke murzar mishi jiki . Tunda nayi sallah asuba naci gaba da kiran wayar Dikko amma sam bai ɗauka ba , ganin baya ɗauka na haƙura na kwanta bacci tunda na kwanta kamar jaka ko motsowa banyi ba sai bayan azahar , dan nima ina tattare da nau'en gajiya , akwai gajiyan gudu da jifar dasu Al ' Ameen suka min , dukan da Dikko yayi min sai gajiyan hawa doki... Ina tashi da wayata na fara na duba ko Dikko ya kira babu miss call inshi , saida na sake kiranshi bai ɗauka ba ni kuma nayi alƙawari daga nan har a busa ƙaho idan ba shine ya kira ba bazan sake kiranshi ba. Yinin ranar yau dai har dare Dikko bai kirani ba kuma nima na basar da lamarinshi , da daddare kuma kaka ta haɗani da gyatima mukayi waya wai nace Inna ni zata dake ma kashedi kar na sake ce mata Inna , nace gwaggo zance miki ko me ? Dariya tayi tare da canja maganar da wata fira ta daban , mun daɗe sosai muna waya da ita cikin farin ciki daga baya mukayi sallama na maida ma kaka wayarta danni dama ban wani san wannan kakar ba gaskiya sai a hoto nake ganinta dan Babana baya bari ina zuwa ko ina kuma duk inda zanje tare muke tafiya dan abinda na fahimta a can baya akwai "yar tsama data faru tsakanin Inna da iyayenta da kuma Babana ɗan uwan Inna ɗaya kawai na sani shima saboda yana mana hidima ne lokacin muna tare da Inna a gidan Baba ! Bayan nayi sallah isha'e ina shirin kwanciya mai aikin Kaka ta shigo wai nayi baƙo a waje , cikin farin ciki na tashi na ƙara gyarawa na fesa turare gyale na ɗauka da sauri na fita , Ina fitowa motar Yazeed na gani parke a wurin da aka tanada dan ajiye motoci , cikin farin ciki na isa wurin dan a tunani na shida Dikko ne kuma jiya da zan taho Yazeed yace min zaizo jibi , kenan sai gobe ne ranar da zaizo , cike da farin ciki na isa jikin motar ina zuwa Yazeed ya buɗe motar ya fiddo ƙafarshi ɗaya waje yana kallona cikin yanayin farin ciki , Gaishe shi nayi ina leƙa cikin motar ko zanga Dikko , murmushi yayi irin na wayayyin maza yace An mata ni bada DK nazo , me yasa baku zo tare ba ne ? Nima bansan zanzo ba kawai hanya ya kawoni nace bara in biyo miki da mamaki kafin zanzo gobe , a yatsine nace kazo yau gobe ka dawo ? Yace Eyy mana jibi ma zanzo kullum zanyi ta zuwa har sai bana nan ne kaɗai bazan zo ba.....! Kallon rainin hankali nayi mishi nace to meye nasabar hakan ? Kula mana , meye halaƙar ka ta san kula dani ? Neman kusanci ! Ta wane dalili kusanci zai ƙullu tsakanin namiji da mace ? Abokanta ka , ai babu abota tsakanin mace da namiji , murmushi yayi tare kauda maganar ta hanyar cewa tou ya kike ya gajiyar kuka da hawan doki ? Ya ƙarasa maganar yanamin kallon ƙarƙashin ido.... Lafiya qalau na faɗa a ƙagare , fitowa yayi daga cikin motar ya jera dani , ja baya nayi sannan na juya mishi baya , murmushi yayi tare da cewa haba An mata miye kikeyi haka ? Babu kyau kinsan yana daga cikin ɗabi'u masu kyau martaba baƙo irin wannan tarbar zakimin haba An mata yadda ya ƙarasa faɗar An matar sai naji kamar maganar Dikko , ba tare dana juyo ba nace yi haƙuri bacci nakeji ne , Iyya yi haƙuri na tuna kinayin bacci da wuri to zan tafi zanzo goben fa , Allah ya kaimu ina faɗin haka nayi gaba abuna , da gudu na isa ɗakina cikin ɓacin rai ina shiga wayata na duba dan ganin ko Dikko ya kirani , ya kuwa kira amma miss call ɗaya ne , shine duk kiran da nayi masa bai ɗauka ba ni zaima wannan miss call ɗin ɗaya dan ya maidani bansan abinda nakeyi ba ? Tsoki nayi tare da kiran wayarshi dan da bai kirani ba nayi alƙawari bazan sake nemanshi har abadan abada. Saida kiran ya kusa ƙarewa ya ɗauka , cikin disashshiyar murya kamar wanda mura ya kama yace An matana ya kike ? Ban ansa ba nace me ya sameka muryarka wata iri , gyaran murya yayi irin dandai maganar ta tafi dai² yace babu daɗi ko ? Murmushi nayi tare da kwanciya saman gado nace da daɗi mana , yace wallahi muryar shaƙewa tayi bansan abinda yasa ba kinga kuma ni bana huɗɗa da abu mai sanyi da sai ince mura ya kamani , sannu nace masa yace yawwa yaci gaba da cewa wallahi wayar a mota na barshi sai yanzu dana fita naga tulin miss calls kuma ke na fara kira An mata... Yayi maganar a sakace, Murmushi nayi cikin yanayin jin daɗin yadda yayi maganar nace tou amma yanzu ka fasa tafiya ko ? Yace zanyi tafi amma sai wani satin banajin daɗi ne duk jikina ciwo yakemin , ni kuma nace ciwon tunani nakeyi , murmushi Dikko yayi tare da cewa Allah ya baki lafiya saida safe... Yana faɗin haka ya tsinke kiran, Cikin jin haushi na sake kiranshi amma yaƙi ɗauka , ni bansan abinda yasa yakemin irin wannan abun ba , ko wurina yazo baya so ya daɗe , idan inayin waya dashi a ƙagare yake ya barni anya Dikko zai soni kamar yadda nake sansa ......? Murmushi yayi bayan ya tsinke kiran yace An mata kenan itafa nan a wayan ta so take ta ganni amma bazata iya faɗa inzo ba sai ta fake wai tana ciwon tunani tou ai sai kisha magani ko kin samu sauƙi..... Daga G R A kai tsaye tsohuwar anguwar su Sultana ya taho inda gidan da yake kiwon dawakai yake , tunda ya shigo anguwar ya ganta cike da taron jama'a maza da mata kuma duk wadda ka gani kasan cikakken ɗan iska ne maza "yan daudu mata karuwai duk wacce ta ansa sunanta tanaji ita wata shegiya ce a cikin iskanci ta hallara a wurin gaba ɗaya anguwar ta karaɗe da kiɗa ko wane ɗan iska da iyayenshi suka ce jeka ka gani su Amisty sun hallarar dashi a wurin , Da gudun bala'e ya shiga cikin santar saboda tsabar gudu motarshi har wani tsalle takeyi , kamar fari haka mutane suka riƙa tashi da gudu dan keɓe rayuwarsu daga faɗawa mummunar rayuwa , a ƙofar gida yayi parking ya fita ya shiga ciki rai a haɗe , shigarshi hayani ta fara tashi kowa dai da abinda yake faɗa akanshi , Bayan ya gama abinda yakeyi zai fito Umar ya biyo bayanshi yake cewa mai gida yau kaga anguwar namu cike ? Banza Dikko yayi dashi bai bashi ansa ba shi kuma yaci gaba da cewa wata karuwa ce take ajo na cika shekaru biyu da fara barikinta sai kuma shagalin samun "yan cin kai na zaman kanta watanni bakwai , Dikko dai baiyi magana ba yana fitowa ya shiga motarshi ya fice da ribos har ƙarshen santar yana kaiwa titi ya juya sitiyarin motar shi ya wuce inda suke majalisarsu , Hafsa kuma tabi bayanshi , Umar kuma mamaki yakeyi ko akwai abinda yake damun Dikko duk dai haka yake amma kamar wani abu ya taɓashi , ko wani abu ya ɓata mishi rai idan an gaishe shi zaice yawwa , ko lfy ko da kyau ko yayi amma yau duk wanda ya gaishe a gidan nan bai ansa gaisuwar kowa ba kuma baiyi magana da kowa ba har ya shigo ya fita... Har yanzu ban daina kiran wayar Dikko ba , duk kiran daya shigo wayarshi na Sultana yana kallo saida yazo goruba gidanshi sannan ya ɗauki wayar cikin tsananin ɓacin rai da hayani yace wai me ye ne............? Ni bana san maita sai kirana kikeyi kin dameni bansan masifa da kwakwa da Allah mayya kawai , cikin tashin hankali na tashi zaune tare da sake kallon lambar wani abu naji yazo ya tokare min a zuciya nace Dikko nice mayya....? Eyyy kece nace mayya ko ba mayyar bace , nima kamar an sakani cikin ɓacin rai nace kaine maye marar tunani wanda baka san ina duniya ya nufa ba , kamar ƙaramin yaro haka Dikko ya biyemin mukai ta zage² duk abinda yace min saina rama , Daga ƙarshe ya zageni tass da turanci , cikin kuka nace Dikko An mata ce fa , tsoki yayi ya kashe wayarshi , wayyo Allahna meke faruwa haka ? Yanzu na gama waya da Dikko lafiya qalau sai kuma in sake kiranshi ya zageni me yayi zafi haka don Allah ? Wayyo Allahna , da sauri na kalli agogo 9:24pm zuciyata kamar zata tsage saboda tashin hankali idona kuwa banda aman hawaye babu abinda yakeyi , da gudu na fito har bakin get , wanda nake tunanin shine driver naje gabanshi a rikice na fara magana cikin rawar baki nace da Allah ka kaini goruba road taimakeni don girman Allah na ƙarasa maganar ina jan hannunshi.... Lafiya ya tambaye ni ? Babu lafiya muje don Allah zan baka kuɗi idan muka dawo yanzu zamu je mu dawo yi sauri don Allah na ƙarasa maganar ina goge hawaye idona , muje ya faɗa yayi gaba nabi bayanshi , Ko a mota a gaba na kasance ina ce masa yayi sauri , sauri ׳ malam driver , gudu yakeyi sosai amma kayi sauri kawai nake cewa har muka isa goruba road , a harabar gidan na haɗu da Hafsa Dikko ya bata kashin bala'e ana ta riƙonshi ya haukace gaba ɗaya , cikin tausawa na kalli "yar uwata dake duƙe tana kuka Dikko sai ruwan rashin mutunci yakeyi ana bashi haƙuri kamar ana ƙara tunzurashi yana sai ya tattaka ta , Wurin Hafsa naje na kamata na miƙar da ita ina bata haƙuri tare da tambayarta meya faru ? Kallona tayi amma bata ce wani abu ba sai kuka takeyi , sakinta nayi zanyi wurin Dikko aka tareni cike da iskanci yake cewa kizo ku barta tazo yayi maganar yana kirawoni da kanshi , turesu nayi na tunkari Dikko kai tsaye ina isa ya yankamin wani irin mari saida na wurwura kamar ranfa na dawo gaban Hafsa ko gabana bana gani sai duhu , kafin in dawo hayyacina na sake komawa inda nakejin sautin muryar Dikko dan kawai ji nake gara in mutu da masifar da zan fuskanta a gaba dan rabuwa ta da Dikko a halin yanzu na dangana abun kawai da mutuwa ta , Riƙeni akayi cikin ihu nace ku sakeni saiya kasheni , ka kasheni Dikko kasheni bana so ka barni da raina gani na matsa gabanshi ina kuka , da ƙafarshi yayi min wani irin halbi saida aka ɗagani sama sannan na faɗo ƙasa ruf da ciki , da sauri na sake tashi cikin kuka na sake tafiya wurin Dikko wani irin tsalle yayi ya ɗaga hannunshi sama rigarshi ta ɗage har kana gani cibiyarshi yace idan taurin kaine ɗabi'arki nine kangara zai kaimin duka saman kai Yazeed ya riƙeshi birkicewa Dikko yayi yana saina kasheta , andaiyi tashin hankali sosai munyi zage² da Dikko abun dai babu daɗi dakel Yazeed ya sani mota muka dawo gida can na baro Hafsa kuma bansan abinda ya haɗata da Dikko ba kuma babu wanda yasan abinda ya jawoma Dikko wannan haukar ba, Sultana tana tafiya Dikko yace zancen banza zance wofi yau duk wani mai tsohon laifi a wurina an famomin ciwon dana daɗe ina raino a cikin zuciyata saura waccan ɗayan ɗan iska yau duk wanda ya hawoni saina lalata mishi rayuwa , yana faɗin haka ya shiga mota ya nufi gidansu , Yau duk wanda yaga Dikko lafewa yakeyi saboda tsoro , wurin mahaifiyar shi ya fara shiga itama da yanayin tsorata ta kalli Dikko tace kai lafiya kuma ? Banda lafiya kuma yau duk wanda yayi gigin shigomin rayuwa ko waye saina mishi babu daɗi ba ruwanki yau saina kashe Al ' Ameen a gidan nan kar wani yayi gigin taɓani ko zuwa kusa dani idan ba haka ba yau zan tara majiyyata da yawa a gidan nan , Dikko badai zaka barni na zauna lafiya ba ko ? Cikin hayani yace da ko wane daƙiƙi na rayuwata shi nake jira yau bana iya bacci saina kasheshi yana faɗin haka yayi waje..... A tsorace Momy tabi bayan Dikko amma lokacin data fito ko sahun ƙafarshi babu tuni ya ɓace , tsayuwa tayi tana tunanin mafita taji gaba ɗaya gidan ya gauraye da hayani da sauri ta nufi inda take jiyo hananiyar tana zuwa Dikko ta gani shaƙe da wuyan Al ' Ameen ya riƙeshi duk wanda ya matso wurinshi halbi ɗaya yake mishi sai mutum yayi sama ya dawo ƙasa somamme... Ƙatti majiya ƙarfi sunfi nawa amma sun zagaye Dikko an kasa samun wani da zai sake matsawa kusa dashi , cikin ɓacin rai Dikko yace har so nawa zan faɗa bana san wani ya sake zuwa kusa dani idan akwai mai sha'awar jinya ko mutuwa yazo..... Ya faɗi maganar a dai² lokacin daya ɗaga Al ' Ameen sama ya dakashi da ƙasa , Momy tace ku riƙe minshi mana , wani yabi ta bayanshi dan ya kamashi amma yana isa Dikko ya halbeshi ta baya shima saida yayi sama ya dawo some , cikin ɓacin rai yace har sau nawa zan faɗa bana so azo kusa dani kuci gaba da shigowa duk saina ƙarar daku a dai² lokacin da yayi wani irin tsalle ya dira akan ruwan cikin Al ' Ameen dako motsi bayayi yace zaka fita harkata ne ko zakaci gaba da shiga ? Kun hanani na zauna lafiya yayi maganar yana ɗaukar Al ' Ameen kamar ya ɗauki kaza yayi jifa dashi jikin wani ƙarfen fitila , yanayin jifa dashi gaba ɗaya suka rufa kanshi dan su riƙe shi , wani irin ihu yayi kai...... Wayyo wai...... Yaci gaba da dukansu babu ji babu gani duk wanda ya hawo saida Dikko ya kwantar dashi yau kam saida ya tsamama ma duk wanda ya hawo layin shi jiki ya kama gabanshi..... Goruba road ya koma a daren yana neman wayarshi , kowa ce masa yake baya kyautawa abinda yake yi , baima kowa magana ba yace ina wayarshi , cikin girmamawa Ashiru yace gata mai gida , cikin ɓacin rai yace kiramin An mata , kallonshi Yazeed yayi yace "Yar matan daka wulaƙanta kake tunanin zaka kirata ta ɗauka , ai saboda wannan lalurar yasa na sakata a tarko , Yazeed yace dan kayi ta zalincin ta kana ɗaukar alhakinta ka ɓata rai kayi ta rashin mutunci warware hannun rigarshi yakeyi yana cewa dole sai tasan fushina kuma ta riƙa kiyayeshi na faɗa mata idan nayi fushi bani ne ba , ɓatamin rai tayi data kama hanya ta taho kuma nace bana so tana yawo ita sarkin soyayya dan nace mata mayya taji haushi tayimin zagin rashin mutinci. Wani ne yace to kai me yasa kace mata mayyar ne ? Raina ne ya ɓaci a dai² lokacin da fushi ya hau kaina ita kuma taita kirana dana ɗauka na sauke fushin a kanta , tunda har zan zama mijinta dole ta koyi ansar laifin da ba nata ba , domin da zaran nayi fushi tofa ko kaina bana saurara..... Tambayar shi suka sakeyi meya ɓata mishi rai haka da yawa har ya daki Sultana da yake iƙirarin ko wani ya taɓata saiya rama mata , cike da damuwa Dikko yace karuwai ne na gani ƙanan yara wanda shekarunsu bai dace da karuwanci ba "yan kuci²n yara wai su nan har sun giga sun tafasa har sun ƙone sun bushe fitilar idonsu wai sunsan daɗin maza , sun gagari iyayensu abin ne ya tadamin hankali , bansan masifar dake damun mutanen wannan zamani ba , wallahi wata "yar ƙaramar yarinya na gani sai kuma yayi shiru hawaye ya cika mishi ido a dai² lokancin da Ashiru ya miƙo mishi waya Sultana ta ɗauka , An mata miye kike kuka kina tunanin zan iya fushi dake ? Cikin kuka nace shine ka zageni kace min mayya kuma ka dakeni , haba An mata ki riƙa min uzuri don Allah ai kinsa bada gangan na faɗa ba fushi ne , tou nidai kazo in ganka , kallon agogo yayi yace dare yayi ki bari da safe zanzo , nidai kazo yanzu , cikin sansanyar muryarshi yace gani nan zuwa.... Gaba ɗaya kowa yace sai yaje yaga yadda za'a ƙare , yayin da wani yake cewa Allah yasa itama tasa ayi maka shegen duka , murmushi Dikko yayi a dai² lokacin da suka fito daga palon yace An mata bata iya fushi dani har abadan duniya domin wannan lalurar ne yasa na sanya mata maitata a zuciyarta , babban muradin ta a yanzu na aureta kaga idan na aureta ta zama tawa , idan har na auri An mata ba maganar yaji dan babu inda zata iya tafiya tabar Dikko muyi faɗa mu shirya danma tana da ƙananan shekaru har yanzu ta kasa kullema 20 , motoci suka shiga suka nufi gidansu Sultana... 11:52pm a gidan Kaka tayi ma su Dikko kuma duka ciki suka shigo da motocinsu , ba waya yayimin yazo ba kukan motarshi kawai naji nayo waje , saida na gaishe da duk abokanshi na shiga mota yana baya zaune ina shiga Ashiru ya fita , fashewa nayi da kuka na rungume Dikko cikin kuka nace shine kacemin mayya ? Yace ai mayyar ce ko ke ba mayyar Dikko bace ba , nima ai mayenki ne kuma ba kin rama ba , to ai har zagina kayi da turanci , murmushi Dikko yayi da gefen bakinshi yace ni wallahi ba zaginki nayi ba , iyakar mayya dana ce ban wani ɓoye da wani harshe na aibataki ba , gaki kin fara zama jajirtacciya soyayyata ta hana ki gano matsalata , haka zakiyi ta haƙuri dani An mata har Allah ya bani lafiya kinji , ya ƙarasa maganar cikin sigar lallashi. Nace to me kacemin da turanci ? Saida yayi dariya yace cewa nayi "yar ƙaramar yarinya kin hanani zaman lafiya , duk wannan doguwar maganar a "yar wannan kalmar ya tsaya ? Ajiyar zuciya ya sauke baiyi magana ba , Shashshekar kuka nayi tare da cewa tou me nayi maka haka da ciwo don Allah , riƙeni yayi da hannunshi na haggu har yanzu ina kwance a jikinshi shi kuma ya kwantar da fuskarshi a saman kaina ya fara magana cikin sanyinshi , yace An mata taron karuwai na gani abun ya gigitani wata "yar ƙaramar yarinya ba zata wuce shekarunki ba kinsan abinda na gani anayi da ita , shiru nayi ba tare dana bashi amsa ba , cikin kuka Dikko yace to maza ke layi akan yarinyar yadda kika san ana ɗaukar mutum a abun hawa a anshi kuɗi haka maza ke hawan yarinyar suna sauka suna bata kuɗi , ɗimuwar rayuwa ta sameni duk taron mutanen da aka tara An mata batajin kunya wai ta keɓe gefe ɗaya tayi ma maza masauki a jikinta , mata basu san illar namiji ba duk mayatar mace da masifar maitar namiji bata iya kashe namiji 2 a bariki , namiji kuwa sai ya kashe mace sama da goma yana nan zamzam , rayuwar mace taƙaitacciya ce amma rashin tunani ya hana su gane haka tunda na shiga anguwar da wanda ke gefe na da wanda ke gabana da duk wanda yake bayana zan iya baki labari , kallo ɗaya zanma abu na gama dashi yanayin mutum na kalla zan iya faɗa miki komai akanshi, Ni mamaki ma nayi duk wa'an nan "yan iska ina ita wacce ta tarasu ta samo su ? Wai ke kinga taron ? Ya ubangiji ka tsare mana imaninmu ka shirya bayinka daga faɗawa tarkon zina , ina cikin jimami ke kuma kin dameni da kira a lokaci ni kuma ina so na samu natsuwa na kiraki ke kuma kin gagara daina kirana ne ina cikin tashi hankali bana so ban ɗauka kiranki ba kuma kiji babu daɗi ina magana dake raina ya ɓaci nayi ta faɗar maganganu babu daɗi , ita kuma wannan yarinya ta wani kama hanya ta biyoni bayan itama na ganta maza sai rumgumarta suke , Ai banma san na cire belt na zaneta ba ina cikin wani fushin ke kuma kika zo , ƙara riƙeni yayi sosai a jikinshi hawayenshi ya ɗigo a saman wuyana ya sassauta murya yace dan Allah An mata idan kika kirani ban ɗauka ba ki daina zuwa wurina kuma ki daina kiyi ta kirana idan kin kira sau ɗaya ban ɗauka ba kinji ko ? Nace tou haƙuri ya bani saida ya tabbatar na samu natsuwa ya gogemin hawayen fuskarta nima ya umarceni da in goge mishi nashi da hannushi yayi min nuni goge mishi nayi tare da shafa gemunshi najashi dan yana burgeni , murmushi yayi mai kyau tare da gogamin gemun a fuskata , a kasanlance na sake komawa jikinshi na kwanta , dariya yayi cewa jeki zanzo gobe insha Allah , dakel na iya fita daga cikin motar na wuce ciki kamar wacce bata da lakka a jikinta , cike da tausayin Sultana su Dikko suka bar gidan.... Bayan Dikko ya gama ci musu uwa motarshi ya hau yai tafiyarshi , haka akayi ta ibar mutane ana tafiya dasu asibiti , Momy bata faɗawa Dady ba amma dan sharrin mata aka samu wacce ta sulalewa Dady waya ta fesa mishi komai , shima daya tashi bai kira Momy ba ya kira Dikko bayan sun gaisa yace Babana duk abinda kakeyi ka barshi zuwa jibi ka sameni , wato kaga bana nan shine kake duk abinda kaga dama ko ? Na taho ganin likita ban dai tsira ba saidai ka kasheni hankalin ka zai kwanta ? To ka taho ka sameni zuwa jibi na baka yana faɗin haka ya kashe wayarshi. Tunda na shigo ɗakina nake tunanin wannan wace yarinya ce ? Bansan mutanen su Hafsa ba amma naji a raina inasan sanin yarinyar da Dikko yayi ma kuka saboda tausayin ta , kuma inasan nasan dalilinta na shiga karuwanci , Dikko yana da tausayi amma baida mutunci ko kaɗan da wannan tausayin nashi Allah ya kamamin zuciyarshi akan abinda yayi min a baya , tabbas ina san sanin ya rayuwarsu Amisty take yanzu , ina san sanin a wane hali Ummu Affan take matar auren da nayi silar zuwanta bariki , ina san sanin abinda yasa matar Baban Babana ta korasu daga gidan mahaifinsu , ina san sanin labarin Aunty Suwaiba , ina san karatu kuma ina san Dikko sannan ina san sanin abinda ya kashe matarshi ko da gaske tsafetan yayi ?.... Kuma gaba ɗaya sai nayi babu wanda zan fasa a ciki ! Sai kuma rashin lafiyar Dikko da abinda yake sashi cusa ɓacin rai a cikin farin ciki wani , tabbas saiya faɗamin meya jawo mishi wannan lalurar da fushin wani yake shafar wani... Asibiti mai kyau aka kai su Al ' Ameen duk wanda Dikko ya daka babu wanda baima rauni ba , ya gota wasu ya karya wasu Al ' Ameen duk yafi kowa shan wahala dan har safiyar yau bai dawo ba , amma likitoci suna ta bakin ƙoƙarinsu wurin ceto rayuwarshi... Duk azabar dake damun Bello bata barshi ya zauna a asibiti ba guduwa yayi domin ya kudiri ganin bayan Sultana , dan haka yabar asibiti ya koma gida , Da sauri ya fito daga toilet yasha wanka a gaggauce ya saka kayanshi bayan ya shafa mai ya wanke jikinshi da ruwan turaruka dan yanzu yake so ya wuce akwai abinda zaiyi Abuja kafin yabar nigeria , cike da kissa ta shigo ɗauke da kofi ta haɗoma Dikko tea data barbaɗeshi da garin maganin da Al ' Ameen ya kawo mata , cike da kwarkwarewa tace my excellency kasha wannan kafin ka tafi , da sauri ya ansa ya ajiye a saman madubi yana ɗaura agogo bayan ya gama ya saka takalminshi wurin ɗaukar wayarshi kofin ya biyoshi ya faɗo ƙasa ya watse , cikin kyarmar jiki Jiddah ta dafa goshi tace bara in kawo maka wani , kallo ɗaya Dikko yayi mata yai murmushi yace haka nake ni da zaran gishiri yayi yawa abunsha ko abinci ɓarewa yakeyi haka rayuwata take tunda safe kina so ki ɗuramin masifa babu gaira babu dalili , yana faɗin haka yayi gaba , Ko wurin Sultana bai biya ba kuma bai kirata ba haka kuma baije gidansu ba danyi ma Momy sallama suka kama hanya daga shi sai Ashiru... Bayan la'asar Yazeed yazo ciki muka shiga suka gaisa da Kaka aka kawo mishi ɗan abun taɓawa bai taɓa komai ba muka shiga firar duniya , ya daɗe sai gab magrib ya tafi bayan na faɗa mishi zanje daura gobe idan Allah ya kaimu yace zaizo ya akaini , yayi hauka da kuɗi wa duk wani ma'aikaci dake gidan itama Kaka ya bata kuɗi masu yawan gaske , ni kuma wasu irin jikkuna yasa aka shigo min dasu masu ɗauke da kaya iri daban ² kuma nima ya bani kuɗi gaba ɗaya ma'aikatan gidan maganar Yazeed sukeyi da irin kuɗin daya bada , tou wai me hakan yake nufi........? 20/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 60 Ɗan bubbuɗawa nayi na lalleƙa gaskiya Yazeed baida hankali wannan irin haukan duk me ya jawoshi ? Duk abinda ya shafi na sakawa a jiki babu abinda Yazeed bai sako ba , turaruka mayuka gyaluluwa takalmi jikkuna materials masu kyau da tsada lessess shaddoji masu tsada atamfofi ƙarshen iskanci hada breziya da fants ondy da sabuwar waya cikin kwalinta mai tambarin apple a bayanta , nima dai ya zubo kuɗi wanda saida suka bani tsoro , Salati nayi naja baya da sauri banma sake gigin ko kallon inda kayan suke ba bare na sake tunanin taɓasu , ɗakin Kaka na nufa na samu tana waya da Inna wuri na samu na zauna cike da mamaki , ina zama tace ga Maryam nan ta faɗi maganar tare da miƙomin wayar , Ansar wayar nayi tare da kallon Kaka ita tana san lulluɓi bata san ɗaura kallabi sai a wani fiddo kunne waje kome hakan yake nufi oho , Hajiya Inna haka na faɗa a dai² lokacin dana kara wayar a kunne na , ya kike ? Lafiya qalau wai yaushe zaki dawo ? Idan na dawo me zan miki ne ? Haba kema da Allah ki dawo Inna , zan dawo ai bai gama abinda yakeyi ba , waye ? Mijina mana , cikin in ina nace Inna miji......? Ey mana yanzu aure kikayi saboda Allah ? To kar inyi ? Wani irin kishin Babana naji ya kamani nace kawai sai kikayi aure haba Inna ke me zakiyi da aure da Allah ? Dariya tayi sosai naji tana cewa Sultana ce , Sultana zaku gaisa da Alhaji , nace ki gaishe shi sallah zanyi , ina faɗin haka na maida ma Kaka wayarta na shige toilet nayo alwallah sallah magrib bayan na fito ɗakina nai tahowa ta , ina shigowa naji wayata na tsuwwa da sauri na isa wurin wayar , murmushi nayi tare da ɗaukar wayar cikin farin ciki, Na koma saman gado na kwanta cike da shaƙun so zuciyata nata tsumama da soyayyarshi nace hello , ke yarinya me kike nufi ne yau baki kirani ba ko kinyi fushi da nine ? Murmushi nayi tare da ɗan murginawa na lumshe idanuwa na gaskiya ina jin daɗin muryar Dikko tana sakani ciki wani irin yanayi dani kaina bana iya ganewa , nima irin abunda yakemin nayi cewa zanyi sallah idan na gama zan kiraka , tou kimin addu'a , nace me zan roƙar maka , ki roƙarmin Allah yasa miki soyayyarta wadda bata gogewa har abadan duniya , ubangiji yasa nine mijinki , duk wanda baya san aurenmu Allah ya sanyaya masa zuciyarshi shi da kanshi yace Dikko ka auri yarinyar nan kana santa tana sanka , Nace zan maka amma ni bazan aure ka ba , murmushi yayi yace ni ko zan aureki in Allah ya yadda kuma inaji a jikina lokaci yana kusa , ai nace bazan aure ka ba , Ey dama ai nine zan aureki bake ba , kinsan Allah ki daina min abinda bashi da kyau idan ba haka idan na aureki duk abinda kikai min saina rama , ka rama idan na aurenka mana... Haka kika ce ? Nace Ey , aiko yarinya zaki ga ramuwa hada ta gayya kice zaki je gida in koma daga gefe in haɗe rai ince baza ki ba , kice dan Allah...... Wata magana yaso yayi amma ganin nayi masa "yar ƙarama kamar yadda yake faɗa saidai yayi dariya yace An mata Allah dai yasa ke rabona ce , a cikin zuciyata nace amin tare da tsinke kiran.... Wani irin ihun jin daɗi nayi na miƙe saman gado nayi rawa Allah yasa haka mutumina Allah yasa muyi aure , ina sanka ׳.............. Da tsalle na sauko daga saman gado ina rawar jin daɗi , rumgume hannuwana nayi nai juyi An mata.... Wai me yasa kake cemin An mata......? Banda mai bani ansar wannan tambayar.... Murmushi Dikko yayi tare da gyara kwanciyar shi yace An mata kenan kinga irin yarintar taki wai zakimin addu'ar amma baza ki aureni ba , hmm yarinya kenan kinaji da ƙuruciya sosai har yanzu kanki ɗanye ne amma zan dafa miki shi gaki ga Dikko ubangiji yasa nine mijinki am3n , Har yanzu Al ' Ameen bai dawo ba , likitoci suna ta bakin ƙoƙarinsu amma shiru kake ji kamar an aiki karuwa ɗakin kwarto , yauma abiyar zaman Momy ta kira Dady ta faɗa mishi har yanzu fa Al ' Ameen babu wani ci gaba sai ƙasa yake ƙarayi kuma Momy ko ganinshi bataje ba , kuma ta sani sarai ɗan ta yayi wannan iskancin tunda a gaban idonta ya doki Al ' Ameen bata ce komai ba tunda daga wurinta ya fito duk yadda akayi ma itace ta tiroshi sai Dikko ya zauna yaita iskanci amma ba'a iya ma yaro magana kamar ɗan ido , Tuni nace ka kaishi gidan mahaukata sai kace ɗanka lafiyarshi qalau yanzu mai hankali zaiyi abinda Dikko yayi ? Cikin ɓacin rai Dady yace ni ban haifi mahaukaci ba , lafiyar Babana qalau kuma Maryam babu yadda za'ayi tasa Babana ya daki wani tunda tasan abinda yake damunshi , duk dai abinda mutum yayi shida Allah kuma ba Maryam aka cuta ba ni aka zalinta duk mai sa hannu a lalurar Babana nakai ƙararshi wurin ubangiji kuma sai Allah yayi min hisabi dani dashi wallahi ban yafe ba kuma bazan taɓa yafewa ba , yana kaiwa nan ya tsinke kiran ya fara kiran Dikko. Gaisawa sukayi bayan ya ɗauka Dady yace Babana har yanzu me kakeyi ne ? Dady ni ina Abuja , tou duk abinda kake ka kasance tare dani idan Allah ya kaimu gobe na faɗa maka , insha Allah , me ya haɗaka da Al ' Ameen kayi mishi duka haka ? Wai bana hanaka wannan doke²n ba ? Badai zaka zauna da rayuwarka lafiya ba ko ? Sai kayi ta abu ana dan ganaka da zararre , Cikin kwantar da murya yace Dady kasan bana iya sarrafawa , tsohon laifi ne na daɗe ina ba zuciyata haƙuri jiya ne taji bata iyawa shi yasa haka ya faru , Allah ya kyauta ya baka lafiya , ubangiji ya yaye maka abinda yake damunka , da am3n ya ansa saida Dady yayi mishi nasiha sosai sannan yace kuma karya zo da kowa yazo shi ɗaya yace insha Allah , cike da soyayyar Dikko Dady ya ajiye waya yana mai tausayin ɗanshi da lalurar dake damunshi , gashi cikakken mutum mai cikar zati da ƙwarjini amma saboda haukan kishi na mata an birkita mishi kwalwar ɗa , matsalar dai kawai yayi fushi idan har yayi fushi tofa nan ake samun matsala danma ana ta roƙon Allah , kuma roƙon Allah gaskiya ne baya faɗuwa ƙasa dan ubangiji maji roƙon bayinsa ne.... Dikko yana da mutunci kuma yana da kirki Allah yasa mishi tausayi amma yafi tausayin mata a rayuwarshi , kuma tun kafin matsalar nan ta sameshi bai ɗaukar raini kuma da an taɓoshi sai anji babu daɗi bai iya zuciya ba haka kuma sai laifin wani ya shafe wanda baisan anyi mishi ba , dariyar mugunta dama haka Allah ya halicceshi tun fil'azal baya dariya kuma shi bai cika murmushi ba , Koda Dady bai samu namiji ba ya tashi hankali sosai kuma duk matanshi kowa addu'a take Allah yasa itace zata haifo , shi kuma a tunaninshi duk wacce ta haifa duk ɗaya tunda suma "ya "yanshi mata baice baya sansu ba kuma kowa tana da , amma tunda aka haifi Dikko sai wutar kishi taita ruruwa sai jefe² har suke ganin kauda Dikko daga duniya shine kawai kwanciyar hankalinsu , tun yana ƙarami suke asirinsu kuma basu gaji ba daga ƙarshe aka tura mishi aljannu su shanye jininshi ya mutu , yasha wahala sosai babu wanda yayi tunanin zai sake rayuwa amma ubangiji yayi alƙawarin rayayye ne , Ganin ba'a samu nasarar hakan ba yasa akayi amfani da fushinshi wurin saka wani fushin idan har yayi zuciya sai ya fita hayyacinshi yayi ta hauka bayaji baya gani ya riƙa kiran saiya kashe sai yabi takan mutum da mota , tou kalmar kisan itace ba'aso yana faɗa idan yana fushi dan idan yace zaiyi kawai sai yayi yake samun natsuwa , to idan yace saina kashe ka daga nan yake tafi sai ya ɗauke wuta ya faɗi , tanan ake neman sa'ar sa ake farautar numfashin shi a haka aljannu ke so suyi nasarar raba gangar jikinshi da ruhinshi su shanye mishi jini ya mutu.... Shi yasa ya faɗawa Sultana idan yayi fushi bashi bane ba ta kiyayi fushin shi saboda baya da kyau , tayi ta haƙuri dashi har Allah ya bashi lafiya ! Ana ta neman taimako dai , wannan magungunan da ake mishi amfani dashi na cikin baki dana shaƙawa abokin Dady ne ya nemosu dan ya tausayawa Dady akan lalurar Dikko saboda Dikko ke ciwon amma Dady ke jinyar bawai jinya ta kula ba , jinyar kar Dikko ya mutu shi yasa duk abokanan shi suka miƙe suka tayashi neman taimako , kuma har yanzu ba'ar nema ba , yanzu haka ma idan Dikko ya samu Dady a inda yake idan ya gama ganin likita zai wuce saudiyya suyi umara tare sai ya dawo dashi inda wani amininshi yace mai maganin yace sai an kawo mishi Dikkon , dan da Dady ya bari saiya dawo amma haukan da yayi jiya yasa Dady yace ya sameshi. Dikko ganin Sultana bata da niyar kiranshi yasa shi ya kirata , har na fara bacci kiran wayar shi ne ya tashe ni , cikin gigin bacci na ɗauki wayar na gaishe shi da muryar wanda bacci yafi ƙarfin shi , cikin murya mai nuna da fushi yace har yanzu baki gama sallar ba ? Bacci ya riga yafi ƙarfina kawai na kashe wayar banma san na kashe ba , ƙara kira yayi har yanzu bacci bai sakeni ba , dakel na ɗauki wayar na ɗorata a saman kunne nace inajinkan , ni zaki kashe ma waya har kin isa in kiraki ki kashemin waya An mata......? Da sauri na buɗe idona dan namayi tunani ko a mafarki nake wayar wallahi , yi haƙuri don Allah wallahi na fara bacci ne tsoki yayi tare da kashe wayarshi gaba ɗaya , da sauri nabi bayan kiranshi amma har ya kashe wayarshi akace a kashe take.... Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un haba ina amfani halin Dikko dan Allah anyi mutum rayuwarshi babu uziri , kwata² bayamin adalci bayan yasan da kaina ina kiranshi , shi so nawa na kirashi bama ya ɗauka tou idan ka kira kai baka cika Dikko ba , kuma nima har abadan duniya bazan sake kiranka ba da Allah can tsamiyar biri dakai mtsww.... Komawa nayi nai kwanciyata cikin ɓacin rai , shi wannan Dikko baida haƙuri ko kaɗan sai zafin kai shi ɗan zafin zuciya ko an faɗa maka bana iya rabuwa dakai , ko zan ragu ne idan na ɓata dakai duk abokanka ma sunfi ka kirki masu haƙuri kaiko komai fushi duk namiji shi ke sarrafa fushin mace amma kai ƙato dakai saini zanyi ta haƙuri dakai ? To bazanyi haƙurin ba kuma an ɓata babu ranar shiryawa..... Wuri ɗaya ya ƙurawa ido yana kallo , ajiyar zuciya ya sauke mai tattare da ɓacin rai , murmushin ƙarfin hali yayi a bayyane yace wai Allahna , wai..... Wayyo ya ƙarasa yana mai kwanciya dakel cikin yanayi mai nuni da wahaltuwa , lumshe idanuwanshi yayi ya ƙara cewa wai........ Wai Allahna , kukan Sultana ya riƙaji a zuciyarshi idonshi ya cika da hawaye yayin daya tuno yadda yayi da ita a safiyar daya anshi budurcinta ta ƙarfi da yaji ya ɓata mata , gangarowa hawayen yayi daga cikin idonshi saida ya sake wai..... Wayyo har yanzu idonshi a rufe a zuciyarshi yace Allah na tuba ׳ , Allah ka ƙaddara aure na da "yar yarinyar nan ya ubangiji kasa An mata rabona ce duk abinda zanma yarinyar nan nidai nafi so kawai na aureta ta samu natsuwa dani , ya Allah kaji ƙaina ka tabbatar da auren mu , zan nunawa An mata tsantsar soyayya mai tsafta zan gatanta ta kuma zata samu natsuwa daga gareni mai sa natsuwa , Ashiru ya kwalawa kira bayan ya samu natsuwa , da sauri ya shigo cikin girmamawa yace mai gida , ran Dikko a haɗe yace wani tunani nayi me kake tunani game da Yazeed da yace zaije zance.....? Cikin girmamawa Ashiru yace mai gida kila wasa yakeyi , Murmushi Dikko yayi tare dayin shiru yana nazari , bayan wani lokaci yace tabbas sai yaje wallahi sai yaje wurin An mata , nasan halin Yazeed ciki da waje , yanzu nayi wani tunani idan ka fahimci rayuwarshi ya cika leƙe² aiko idan har ya leƙo An mata saina tada katsina da bala'e , Tun bansan meye iskanci ba nakejin kalmar iskanci a bakin Yazeed , idan kayi tunani goruba ba majalissar shi bace tunda yaga An mata ranar dana daketa ya dawo da zama gidan nan , jinjina kai Dikko yayi yaci gaba da cewa lallai akwai abinda zai faru , miƙewa yayi tsaye yace zafa a samu matsala ya ƙarasa maganar yana ma Ashiru wani irin kallo , da sauri yaja da baya yana cewa mai gida haka bazai faru ba , Dikko yace abun yakemin yawo a zuciya yace An mata ta cika zama ɗaki kamar mai jego , yawan zama da hijabi kamar mai takaba , ya gajiyan hawa doki ko zaki hau na bankwana , kyautar zobe a maimakon kuɗi kamar yadda sauran sukayi mata , duk haka yana nufin wasa ne.....? Me yasa su sauran basuce haka ba ? Mahaifiyar An mata bata nan tayi tafiya zuwa Dubai ita da mijinta da mukayi waya da ita nace sai ta dawo zan dawo da An mata , abinda yasa na mayar da ita shine , Washe garin ranar dana bata kashi su Yazeed su suke riƙeni lokacin dana bigawa An mata kai da bango , tayi ƙara sau ɗaya mai tsananin tayar da hankali , ihunta shine ya jawosu suka shigo ciki da gudu a lokacin ita kuma ta suma.... Gaba ɗayansu sun riƙeni , ni kuma ina zabura cewa saina kasheta , kowa haƙuri yake bani hankalin kowa yana kaina amma idon Yazeed yana saman An mata , abinda tayi min suka fara tambaya ina cikin wani yanayi saina ce na hanata fita shine ta fita maza suka daketa to da wani ya daketa gara ni da hannuna in kasheta , ko ina cikin yanayin fushi duk abinda akeyi ina sane kuma kar nake bana mantuwa , tabbas naji Yazeed yace wannan tafassar fa.......? A dai² lokacin na kwace na fita daga gidan , ranar a gidan ya yini har 1:21am yana nan a tunaninshi zan tafi baisan tunda na dawo da An mata goruba na daina kwana gidana nake kwana tare da ita , ita kanta bata san gidan nake kwana ba saidai kawai ta ganni da safe , Yazeed yace min DK yaushe zaka wuce ne ? Nace masa aini bana fita sai kowa yabar gidan nake fita , sai yacemin tare zamu fita , nace masa bana zuwa da kowa kuma bana fita da kowa , yace zai bini a haka dai saida nayi mishi gatso² ya tafi , misalin 2:09am ya kirani na ɗauka yace wai na wuce ko ina goruba ne ? Nace masa ya akayi ne ? Murmushi Dikko yayi tare da cewa waini za'a ɗauka sakarai bayan har "yan cikin Yazeed ina kallo. Kallon Ashiru yayi sosai tare da buɗe duk girman idonuwan shi masu ba mutane tsoro yace , kawai Yazeed cewa yayi wai "yar yarinyar nan nake tausayi an barta ko yata ƙara jin jikinta ne ? Sakaran banza sai na rubza shi a rami mayen kuma saiya faɗa , { bai faɗi maganar da yayi da Yazeed ba haka kawai yacewa Ashiru } Dikko yaci gaba da cewa , Da safe sai An mata ta fito palo ta sameni tana kuka , bata yafe ba duk wanda yaji mata ciwo a gefen fuskarta , na kirata tazo kusa dani na bata haƙuri kuma na lallasheta ta saki ranta mun fara magana Yazeed ya shigo , ni kaɗai nasan fassarar kallon da yayi mata , ta tashi na zaunar da ita saman kujera , kallon da yake mata yasa nace ta ɗauki makullin mota ta ɗauko mana abinci , tana fita ya matsamin muka fita , bayan takai miya ta kwanta yasa na fiddota , nayi niyar zuwa da ita wani wani taron da zamuyi a ranar daka maida ita gida bayan shine ya matsamin naje , na yadda yace inje da An mata nace masa bazani da ita ba , hmmm waini zaima wayau sai ya zuƙe da matarshi kaza ² ya kawo wani makirci ya raɓa , da naga zai maidani wani ruwan tsakar dare kawai na maida An mata gida wurin kakarta bayan na faɗawa mahaifiyarta , yaga gidan shine yace zaizo zance , kawai na ɗauka yana wasa ne amma naji a jikina kamar yaje , ko zaije Allah ya tsallake shi a tarko fitinata , Ashiru yace mai gida anya zaiyi haka duk halakcin da kayi mishi , Dikko yace manta da wannan matsayin dana ajiyeshi daban kuma idan ya kuskura yace zai shiga rayuwar An mata zanci ubanshi ne kawai kuma dan naci mutunci shi bazaisa na rabashi daga inda na ajiyeshi ba jeka kawai , fita Ashiru yayi Dikko kuma toilet ya shiga dan yayi wanka..... Ashiru kuma tunani yake akan maganganun Dikko idan ko har Yazeed ya shiga rayuwar Sultana za'a samu matsala , kuma yayi ƙaton butulci dan Dikko ya suturashi ya farfaɗoshi daga masifar talauci ya kwato mishi "yan cinshi a cikin abokansu , yana zalincin Dikko amma dake shi abun duniya bai rufe mishi ido ba bayajin komai , domin Yazeed yana wulaƙanta dukiyar Dikko da ƙeta an faɗawa Dikko sai yace ai idan Allah ya baka arziƙi tou ba naka bane ba kai ɗaya , yace kuɗinshi na kowa da kowa ne duk yadda Yazeed ke facaka da kuɗin Dikko baya mishi magana kuma ko abokansu da sukayi ma Dikko magana ya kori Yazeed daga dukiyarshi karya talautashi kamar yadda ya lalata arziƙin mahaifishi Dikko cewa yayi ko haka ya tsaya ya daina neman kuɗi nan da shakaru dubu baya talauci.... Ajiyar zuciya Ashiru yayi tare da cewa gaskiya mai gida yana da haƙuri addu'a yayi Allah ya tsare arziƙin Dikko domin shi bangone ga duk wanda ya raɓeshi dan Allah yayi ma Dikko kyauta kuma kyauta mai ɗauke lumfashi hannunshi buɗe yake shi yasa Dady ke cewa yasan koya mutu Dikko zai zama uba ga "yan uwanshi , gaskiya Dikko yana da kirki sosai saidai matsalarshi fushi sai mugunta da ƙeta... Yazeed abokin Dikko ne , kuma shima Yazeed ɗin babanshi cikakken attajiri ne sai Allah ya kawo mishi karayar arziƙi kuma duk Yazeed shine silar lalacewar komai na ubanshi dan shima yana harkar wasan danbe ya daɗe sosai a cikin harkar , da abokai suka ga bashi da wani kuɗi a hannunshi sai suka cireshi daga cikinsu shi kuma lokacin Dikko baya nan..... Bayan ya dawo daga tafiya yaga baya ganin Yazeed daya tambaya sai sukace gaskiya DK mun cire Yazeed a cikinmu , bashi da ko sisi zai zama mana damuwa , Dikko yace ba'a rayuwa haka kar a barshi rashin kuɗi yasa ya shiga wani hali na daban gaskiya a ceto rayuwarshi dan duk wanda ya saba mu'amula da kuɗi idan ya rasa yana samun damuwa , a tausayawa duk wanda ya samu ya rasa.... Sai sukace sudai basa zama dashi gaskiya zai rage musu matsayi ne kuma ana ganin girmansu a gari duk wani matashi addu'a yakeyi ya zama kamarsu sai kuma su fara rage zafi gaskiya basa iyawa , amma sai kuma suka ɓoyewa Dikko Yazeed yana wasan danbe..... Shine Dikko ya farfaɗo da rayuwar Yazeed ya bashi manager a wani companyn shi , yaga kuɗin banza ya shiga daddagar musu uwa , mutane yadda suka ga Yazeed lokaci guda ya zama mutum yana wulaƙanci da kuɗi sai sannan suka cewa Dikko ai yana wasan danbe Dikko yace ai basu faɗa ba shi kuma ya wuce wurin dan idan ya tafi baya dawowa , duk wulaƙancin da yakeyi da kuɗin Dikko shidai Dikkon bai taɓa nuna mishi komai ba , koda ya fara mai gida Dikko yace baya so ya kirashi kamar yadda ya saba tun farko , Sai ki haɗa mace 20 zakiji duk sunce su "yan matan Yazeed ne , ɗan neman matane na bala'e , duk macen daya gani saiya lasa ta , tunda yaga Sultana tsutsar masifar jarabarshi ya tashi kuma ya ɗana mata tarko itama so yake ya lashe ya wuce , idan har mace ta kuskura ta faɗa tarkon Yazeed nata ya ƙare...... Cikin farin ciki na wayi gari , a murnace nake ta huɗɗoni na sai shiri nake na tafiya Daura , tun ina wanka ake cemin nayi baƙo a waje , dan gaskiya rayuwar gidansu Inna babu takura zan fita duk lokacin da nake so in dawo babu wani tsanani , idan zan fita Kaka tana nan zatace min Allah ya tsare kuma idan na dawo taga dawowa na zatamin sannu ! Ina fitowa daga wanka hijabi na saka nayi waje , a harabar gidanmu naga motar Dikko , da farin ciki nayi wurin motar ina zuwa Ashiru ya sauke gilashi ya gaisheni , ansawa nayi cikin halin ko in kula , yace ranki ya daɗe mai gida yace inzo in zauna dake harsai ya dawo kuma duk inda zakije nine zan kaiki , Cike da masifa nace kamar ya ka zauna dani ? Ko ance neman wanda zai tayani zama nakeyi ni bana san kilbibi kawai ka kama gabanka , Ashiru yace babu inda zanje ko a napep zaki fita yace kawai in riƙa bin bayanki shine abinda yace , to me yake nufi da abi bayana , Ashiru yace nima haka yacemin , aiko sai inga wanda ya isa yabi bayana , Ashiru yace mai gida ya isa kuma sai nabi bayanki saidai ki fasa fita amma ina nan daga nan har Allah ya dawo dashi lafiya , Cike da masifa na nuna Ashiru da ɗan yatsa nace kasan sharrina kuwa ? Banza yayi ya ƙyaleni , nace tou bakai ba ko ubangidan naka bai isa ya sakawa rayuwata ido ba dani dakai mu zuba , nayi wanka yanzu zanje daura ka biyoni idan ka isa kuma ta gabanka zanbi in wuce lusari kawai dakai , ina faɗin haka nayi ciki , Murmushi Ashiru yayi tare dabin bayan Sultana da kallo , tunanin Dikko yayi da yace masa , An mata tana wayau sosai kuma haɗarinta yawa gareshi tana anfani da wani abu take sa mutane bacci dashi sai ka kula , mai gida ya akayi ka sani , wurin "yan daban da take amfani dasu domin saida nasa aka tattaromin su akan wani binke daya shafeni ka kula tafiyata ta zama dole saboda Dady yana jirana Yazeed sharrinshi yana da ƙarfi na baka amanar An mata Ashiru idan har wani abu ya faru da ita bazanyi kuka da kowa ba sai kai , Ashiru yace mai gida bana tunanin zata fita ta tsorata dakai , Dikko yace batajin tsoro na irin An mata duka baya mata amma zata tsorata dani da zaran na aureta dan irin su An mata hukunci ɗaya ne maganin su kuma dashi zan horata kowa zaiyi mamakin natsuwarta dan yadda nasan zan mutu haka nasan sai An mata ta fita , Ashiru yace lallai kuwa gata ita daura zata tafi ma , zanga ta gidan ubanda zaki bi ki fita , fitowa yayi daga cikin mota ya fara duba saman katangar gidan da aka zagayeta da wayoyi masu raba mutum gida biyu su tsisstige masa hanji , zagaya gidan ya farayi ko zai samu wani wuri daya buɗa inda zai ba mutum damar fita , Dariya nayi nace ga ɗan boko wanda ya zaga duniya ga jahila wacce ba ilimin boko kuma babu inda taje tana rayuwarta ne a cikin birninsu yau zanga yadda zamuyi wannan wasan dakai malam Ashiru dan wallahi ko min bala'e sai naje daura kuma sai naje na dawo kana nan banza kwance a mota kana baccin asara............ Muyi wasan..... 21/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 61 Ina saka kayana ina mita cewa naga yanda za'ayi wani ƙaton banza ya hanamin nayi rayuwana yadda na tsara abuna , zanje daura dole saina san dalilin da yasa aka yankewa Aunty Suwaiba ƙafa , a madubi na kalli kaina kamar ina ma wani kashedi na nuna da ɗan yatsa duk wanda ya shigo da takura a rayuwata , abuna da nake fesawa na bacci na ɗauko dan yana cikin jakar makaranta na tuni nake neman sa'a akan Dady dan ina da ƙudiri akan shi sosai a zuciyata , ta cikin madubi na fesashi fesss dariya nayi tare da cewa haka zan feshe ka kamar na watsawa sauro magani maimakon kai ka mutu sai kawai ka tafi duniya bacci..... Ina gama saka kayana na yafa gyalena na ɗauka jakana dan a lokacin har Yazeed yazo wayata na ɗauka da kwalbar abuna na fice daga cikin ɗakina dan ko Kaka ban faɗawa Daura zanje ba kuma ban leƙa mata ban kwana ba ! A harabar gidan na samu hayaniya ya gauraye tsakanin Ashiru da Yazeed kowa sai ɗaga murya yakeyi kamar zasu buga , wurin Yazeed na nufa nace masa ya akayi ne ? Cikin ɓacin rai yace wannan jakin ne zai ɓatamin rai , wai me yace ne ? Nayi tambayar ina kallon Ashiru amma Yazeed na tambaya , Yazeed yace cemin yayi ni ɗan iska ne ina leƙe² nazo zan leƙaki , ɗauke idona nayi daga kan Ashiru nace ma Yazeed miye leƙe² ? Duk shiru sukayi , murmushi nayi a raina na kalli Ashiru nace Dikko yace idan ka bari na fita zaka bini ko ? Yace Eh , nace idan Yazeed zai ɗaukeni fa ? Shima sai naje , kallon Ashiru nayi sosai ƙosashshen ƙato ne mai sigar "yan restyling ya ƙoshi sosai Dikko yayi mishi horon ƙarfi ko ina ya cika kamar anbi jikinshi an tsatstsaga mishi dutsina saboda cikarshi , Ajiyar zuciya na sauke na kalli Yazeed nace wai miye leƙe² ? Kowa shiru yayi , to tunda baza kuyi magana ba kai Yazeed muje kafin rana yayi , juyawa Yazeed yayi da niyan tafiya Ashiru ya shaƙoshi ta baya , murmushi nayi a bayyane tare da cewa kai yaro sakar mishi wuyan riga kafin inci uwarka , na ƙarasa maganar ina nuna mishi da kaina , Ni zaki ci ma uwa ? Ya tambayeni , nace ba kai kaɗai ba hada Dikko naci uwarka naci uwar wanda ya turoka ka zauna dani , gyara tsayuwata nayi sosai tare da nuna Ashiru da ɗan yatsa nace ai saboda so duk za'a sakawa rayuwata ido ko ? Shiru Ashiru yayi yana kallona a nutse baiyi magana ba , naci gaba da cewa ni dama inda na gode Allah ban taɓa cewa ina san Dikko ba , tou wai waye ma zai so mahaukaci ? Yanzu mutum anjima aljani , a haukan nashi yake tunanin zan iya aurenshi ? Bashi da aiki sai zafin kai da doke² idan har baka fita harkata ba saina tona maka asiri , ke ni zaki tona ma asiri.....? Tabbas nasan ahalinka kaf kuma nasan abinda ya raboka daga gidanku ka dawo rayuwa ƙarƙashin mahaukaci , { kuma ƙarya nakeyi bansan komai game da rayuwarshi ba , } Ashiru yace ke yarinya bamu da sata bamu da maita kuma bamu gaji iskanci ba duk duniya wannan abu 3n dana faɗa ɗaya daga ciki mutum zai samu kanshi yaji takaici kuma shi ubana baya taushewa.... Nima ban gaji iskanci ba hayenshi nayi kamar yadda kaima baka gaji kwaraka ba kake rayuwa a ƙarƙashin wani , kuma idan ubana ya taushe kaima ai naka ya taushe saboda kunne ya girmi kaka yaro idan baka san asalinka ba yanki fili ka shiga siyasa , Sultana bata siyasa amma rayuwar kowa da labarin gidan kowa yana a tafin hannuna saboda ɓacin rana , kasan duk wanda baisan kanshi ba daya shiga siyasa duniya zata faɗa mishi koshi ɗin waye , nima siyasa ce duk wanda ya shigoni zan warware mishi dan nidai ubana bai taɓa murƙushe surikarshi da ɗiyar maƙocinshi ba , { kuma haka nan kawai na faɗa dan in ɓata mishi rai bansan komai game da rayuwarshi ba , } cikin ɗaga murya Ashiru yace ke...... Ki gyara kalamanki akaina tun kafin in ƙera miki rayuwa , a sanyaye nace malam Ashiru ai yanzu muka fara , zama fa tare dani zakayi anshi wannan kafin in dawo , kafin ya ankara na feshe banza ya ƙame a wurin , Da taimakon masu aiki da kuma Yazeed aka sakashi a mota bayan na faɗa musu ciwon farfaɗiya yake , haka ciwon yake taso mishi lokaci² , ina ƙoƙarin rufe motar naji wayar Ashiru tana kuka a aljihunshi , Yazeed nasa ya cirota nace waye yake kira ? Yace mai gida , saida nayi dogon nazari sannan nacewa Yazeed ya maida mushi wayarshi a jikinshi muje , Maida wayar yayi jikin Ashiru mu kuma muka shige mota mukai tafiyarmu , tunda muka kama hanya bana tunanin komai sai tunanin irin halin Dikko , ga zuciya kamar kumburƙuma , mema Dikko yayi min na rayuwa wanda ya kamata ace na so shi ? Bashi da aiki sai doke² so biyu yana dukana na farko saida na suma , na biyu dakel aka riƙeshi umm gaskiya bana san namiji da zuciya gashi bashi bada uziri ko kaɗan na rayuwa jiya daga ya kirani na fara bacci kawai ya hauni da masifa , na sake kiranshi ya kashe wayarshi gaba ɗaya.. Dai² saitin zuciyata na dafa a bayyane nace kiyi haƙuri dan Allah dan annabi kiyi haƙuri ki goge wannan mutumin daga cikinki , a sirrance na sake cewa me ma Dikko yayi miki na rayuwa ? Mota ce kawai ya baki sai miliyan ɗayan kuma dan ƙaranta daci baya mahaifiyar shi ta ansa , gashi bata so na , kallon Yazeed nayi da wutsiyar idona , zuciyata tace kalli Yazeed shima dai lafiyayyen matashi ne jini yana motsawa ko ina ajikinshi , yana da ƙirar burge mace kuma shima dai ɗan kwalisa ne , me ake nema na rayuwa ? Idan dai namiji yana da "yan canjinshi kuma ya iya soyayya ai shikenan , kawai ki watsar da Dikko duk da dai badai wata makusa shima dai kyakkyawa ne gashi ɗan gayu uwa uba ya iya magana mai daɗi amma yanayin Dikko yafi na Yazeed nuna gogewa a wurin iya ɗagawa mace hankali ƙwayar idonshi ya nuna haka giraren shi kawai ka kalla kasan zaiyi jarabar masifa duk macen da Dikko ya damƙa zataji a jikinta bare kuma ni da yakeji ma haushi nayi imani da Allah irinsu Dikko sune masu horar da mace da azaba a wurin kwanciya matsawar tayi musu laifi , mace taita ƙarewa a rasa abinda ke damunta , ai dama yama taɓa faɗa min da bakinshi cewa idan harya aureni sai nasan shi ba abokin wasana bane ba bare ga Dikko da ƙeta , umm manta da Dikko kawai ki auri Yazeed na tabbata zakiyi rayuwa mai inganci dan shima jajirtaccen namiji ne tunda har baiji tsoron Dikko ba ya shiga soyayya dake wannan namiji yakai jarumi... Ajiyar zuciya na sauke na sake kallon Yazeed da wutsiyar idona , kallon siffarshi nayi sosai domin Allah Dikko yafi shi zarrar cika cikakken namiji nesa ba kusa ba , duk baƙar hassadar ka babu yadda ka isa ka kushe Dikko wallahi , domin cikakken namijine jajirtacce yana da zarrar da duk macen data ganshi mai lafiya da sanin duk wasu qualitative na namiji tasan Dikko yakai kuma wallahi babu yadda za'ayi yaba kanshi kunya wurin mace a gado , mutum ɗan tara ne bai cika goma ba , ni gaskiya na haƙura da Dikko dan bansan ranar da zai samu lafiya , idona ya cika da hawaye gaskiya ina san Dikko sosai wallahi idan har nace bana sansa nayi ƙarya , domin duk yadda zan faɗa muku Dikko gani nake baza ku gane ba , Da wata irin ƙara ya farfaɗo wayyo Allahna mai gida karka kasheni kayi haƙuri na bari , wayyo Allah ku taimakamin zai kashe ni wayyo............. Wani irin ihu ya sakeyi wanda ya jawo duk hankalin wanda ke cikin asibitin yana cewa gashi nan ku riƙeshi wayyo kakkafawa Al ' Ameen ya sakeyi yana fizge² idonshi a rufe saboda tsabar tsoro , dole tasa akayi mishi allurar bacci dan ya cikawa mutane asibiti da ihu kuma ga marasa lafiya sosai masu buƙatar natsuwa. Me wannan yaron yake nufi zanyi ta kiranshi baya ɗaukarmin waya ne ? Ƙaton banza kila ma yaje ya miƙa mata fuskar tayi mishi feshi , shi uzirinshi idan ya kiraka so ɗaya baka ɗauki waya ba zai maka uziri har zuwa lokacin dakai zaka nemeshi da kanka , akan Sultana kaɗai yake maimaita kira dan idan ya kirata bata ɗauka ba duk bayan mintuna saiya sake kira yaji ko zata ɗauka , hardai ya samu sa'ar barin nigeria Ashiru bai kira ba bare yasan a ina aka kwana....! Duk wani shiri daya kamata tayi , tayi ta tattara duk wani abu da tasan idan taje tayi zata tafi da imanin Dikko , duk wani tsafe² saida ta haɗo kanshi , turarenta da man shafawarta da powder har kwallin da zata shafa a idonta duk anbisu an barbaɗesu da asiri , kaya masu azabar² ɗauka hankali ta ɗauka , wai ita zataje jinyar ƙanin mahaifiyarta wato Al ' Ameen , shiri tayo mai kyau da makaman yaƙinta tayo garin katsina bata san sunyi hannun riga da Dikko ba..... Ni yanzu ina zansa kaina komai ya fara warwaremin kayi wani abu haka nan mana ai bana tunanin akwai abinda ya gagareka , ya ina neman mafita kuma ɗan gwamna zai shigo rayuwarta , yaron nan ɗan iska ne ya raina mutane duk garin nan babu wanda baisan halinshi ba baida mutunci kuma ya raina mutane dan baya ganin girman kowa a garin nan , dan gaskiya idan aka aike ka neman tantirin ɗan iska daka ga Dikko ka tsaya ka samu saboda wannan dalilin ne yasa nasa kayimin aiki akan ya lalatawa ɗiyar Binna rayuwa dan nasan idan har Binna yace zaiyi wani abu Dikko kawai zai iya bi ta kanshi da mota ya wuce , dan na tabbata daba Dikko ne ya farke yarinyar nan ba da har yanzu zaune bai ƙare ba. Bello ne zaune a gaban bokanshi duk ya koro wannan sharfin tare da fashe mishi da kuka cewa tuni kasa ni nabar sallah azahar da asuba da isha'e amma ka kasa wani abu ? Wata irin dariya bokan yayi cewa akwai sauran mafita ɗaya , jikinshi na kyarma yace wace mafita ce ? Saura la'asar da magrib zaka dakatar , Bello yace na ajiye 3 biyun kake tunanin zai gagareni ne ? Na daina sallah dama ai ba kullum nakeyi ba ni koma miye zanyi amma duk yadda za'ayi nidai a raba yarinyar nan da Dikko ko kuma in aureta kawai kaga sai in ida cika burina tana gidana , hahahahaha bokanshi yayi dariya tare da cewa idan dai kana san ganin burinka ya cika na auren yarinyar nan yanzu sai ka auri mahaifiyar , zaro idanuwa Bello yayi tare da cewa kamar ya in auri mahaifiyata kuma boka ? Wata irin dariya yayi mai ansa kuwwa gaba ɗaya dajin ya karaɗe da ƙarar dariyarshi bayan ya samu natsuwa yace yarinyar tana da ibada tana sallah akan lokaci kuma tana da karatun littafin Allah babu dare ba rana , kuma kasan munyi² mu rabata da sallah abun ya gagara idan har zaka iya auren uwarka duk daren duniya zaka kwanta da ita ne ka riƙa samun natsuwa daga gareta shikenan Sultana zata aure ka kuma duk duniya babu wanda ya isa ya hana auren , saboda sai mahaifiyar taka tayi bacci zaka kwanta da ita , tou yadda ka sadu da ita tana bacci bataji bata gani ba haka za'ayi aurenka da Sultana mutane bazasu ankara ba bare ayi ta surutu.... Shiru Bello yayi bayan wani lokaci yace wannan kauce hanya tayi yawa da wane idon zan tsaya a gaban Allah uwata fa.......? An zan samu rahama ranar gobe ƙiyama ? Boka yace wanda yayi kisa me ya rage mishi daga rahamar Allah a duniya da lahira ? Bello ga kisan kai ga zinace ² ga caca kawai kayi sai ka tuba idan ka kusa mutuwa tunda kana san rahamar , Bello yace to a rabata da Dikko basai na aureta ba , Boka yace ko ka aureta ko a rabata da Dikko saika auri uwarka , idan haka baiyi ba tou kisanta shine mafita kawai.... Bello yace shikenan zanyi shawara.... Har muka isa Daura ni banyi magana da Yazeed ba sai shi daya kunna wata waƙa ta "yan siyasa yakebi , wannan ta shiga ta fita , nidai hankalina da zuciyata ya tafi yayin da nake jinjina auren Yazeed sai kuma tunanin yadda zanyi ma in cire Dikko daga raina tun farko ma kenan. Haka nan naji gabana ya yanke ya faɗi ina tunano lokacin da Dikko ya sumbaceni a ƙofar gidanmu ranar dazai rabu dani , tashi tsikar jikina tayi yayin dana tuno yadda na kasance a jikinshi da maganarshi da yake cewa zamuyi aure bada daɗewa ba , Haukanshi na tuno yadda yake fizge² yana zabura kamar anba doki ƙwaya idan an riƙeshi , kai gaskiya ina san Dikko amma idan har na aureshi ranar da nayi mishi lafiya waye zai riƙeshi idan zai dakeni....? Murmushin Dikko na tuno a ranar da mukayi faɗa dashi hanyar tafiya bakori lokacin da muka tafi da Mardiyya maganar da yayi na tuno , Haba yarinya Dikko ne fa ! Kin manta nine na koya miki ? Nine nayi kuma nine na fara baki idan daɗi kikaji ko zafi duk nine dai , ruwa idan da rabon ka a ciki ko ka zubashi a kwando bai maka yoyo , ni ba abin farautarki bane zaki duk jarumtatai yana ganin ƙimar mafarauci a wancan karon suma kikayi wannan karon ma haka zata sake faruwa dake ba suma ba har jinya sai kinyi idan kika dawo ɗaukar fansa zaki gane Dikko ba sa'arki wasanki bane domin saina baki azabar da sai kinyi fitsarin wahala , bayan kin dawo daga duniyar suma tsorona zai shigeki a duk lokacin da kika kasance dani a shimfiɗa ɗaya , Wallahi jarumi ɗaya akeyi a ƙarni nine jarumin wannan lokaci , Dikko jarumin maza ne kuma keda kanki zaki faɗa kije ki dawo ina nan ina jiranki , murmushi nayi a bayyane nace wannan gaskiya ne mutumina Allah ya baka lafiya..... Fita nayi daga cikin motar ina fita da Yayar Aunty Suwaiba na fara haɗuwa muka gaisa da ita take cemin yanzu nan aka tafi da Suwaiba Zaria wai sunje zasuyo wasu aune² , cikin rashin jin daɗi nace yaushe zasu dawo ne ? Tace insha Allah barasu wuce kwana biyu ba , nace tou dan Allah akwai wata waya a hannunta wacce aka bata a asbiti shin ko zan samu wayar ne da Allah ko kuma ta tafi da ita.....? Shiru tayi irin na masu nazari tace me zakiyi da wayar ne , murmushi nayi ba tare dana bata ansa ba na buɗe jakata na ɗauko kuɗi na bata tare da cewa bani wayar ke kuma ki riƙe wannan , cike da farin ciki ta anshi kuɗi tare da cewa ina zuwa , mota na koma ita kuma ta shiga gidan Aunty , bata wani daɗe ba ta dawo da wayar ta bani , godiya nayi mata sosai tare da cewa zan sake dawowa godiya tayimin sosai har muka tafi tana godiya tare da ɗaga mana hannu har saida muka ɓace... Har yanzu banyi magana da Yazeed ba amma na fahimci wasu ɗabi'u nashi , ina wani tunanin ne wayar da Dady ya bani ta fara kuka da sauri na fiddo wayar daga jakata na ɗauka tare da cewa Dady barka da wannan lokacin , na nunawa Yazeed yayi parking , yana yin parking na fice daga mota... Barka dai kin wani manta dani ko ? Haka kin kyauta kenan ? Haba taya zan manta dakai bayan kullum kana raina kamar kuɗin haya kayi haƙuri ban manta dakai ba kullum tunanin ka nake yanzu haka ma tunaninka nake kawai sai ka kirani , dariya yayi cewa tou yanzu kina ina ? Kallon titi nayi tare da cewa ina gida , ina ne gidan naku wai ? Zaka zo ne ? Saidai ke kizo , kana ina ne ? Ina nan Ambasada kinsan wurin ne ? Nace Eh hanyar Shinkafi ko ? Yace Eh kizo to , gani nan zuwa amma zanzo sanye da niƙaf da hijabi wurin ina kake ne ? Kinsan Fesra hotel ? Eh na san wurin tou ina a wajen da Allah karki ɓatamin lokaci , baka da damuwa ina faɗin haka na katse kiran ! Kwanan wata na kalla a wayata nai murmushi cewa hawan ruwan ciki na fa sai mutum ya shirya baka da zarrar da zan miƙa maka linzamina rayuwata , wahalar banza zansha bayan ka haɗamin da "yan dabaru kayan maza , tsoki nayi tare da cewa anya ma muradin kake nema ? Ko kuwa dai......? Kiran dana ansa a baya da baƙuwar number da akace za'a kashe ni na fara kira a kaina nake cewa zan gane yanayin iskan inda ake magana dani dan ranar dasu Al ' Ameen suka bini da gudu har muka haɗu da Bello naga motar Dady a ƙofar get in makarantarmu , kila Dady ya ganni Bello yana bina daga baya zasu haɗu sai yace meya haɗaka da wannan yarinyar da kake binta ? Kawai zaice ai ɗiyar *BINNA ce...* , ko kuma sunyi magana na shi yasa na ansa wayoyi daga mutane daban² kowa yana so yasan inda nake , tou idan wani abu bai faru ba taya akayi Bello ya kasance a wurin bayan Dady kaɗai yasan zanzo makaranta tunda shine kaɗai na faɗawa ina katsina ? Kuma wurin baiyi hanya ɗaya da majalissar su ba kwata² gidan Bello ba'a hanyar yake ba ? Murmushi nayi tare da cewa haba tsofaffi na gano makircinku amma idan ma nemana kukeyi yanzu zan gane ta hanya mafi sauƙi , a dai² lokacin da aka ɗauki wayar , ba mai maganar nake saurare ba yanayin iskan wurin nake so na fahimci ko a inda Dady yayi waya dani ne yake magana.....? Shi kuma cewa yakeyi , Zaki mutu mutuwa irin ta karnuwa wallahi saina kashe , dariya nayi tare da cewa baka iyawa , yace zaki mutu fa , nace ƙarya ne , sai na kasheki wallahi , wallahi kana iya kasheni ? Na tambaye shi , yace Eyyy , nace tou idan ka isa kai jarumin ne a harkar kisa ka kashe ni a Ambasada zanzo wurin Fesra hotel yanzu sanye da niƙa da hijabi bana kasuwa fa , sai kin mutu kuma kafin mu kasheshi sai kowa ya zagaya ki , gani nan ka kasheni in gani , ina faɗin haka na katse kiran na fara kiran wayar Hafsa... Ba ɓata lokaci ta ɗauka muka gaisa da ita , nace Hafsa kina ina ne yanzu ? Cikin muryarta ta sakarkari tace ina Qerau gidan Amisty , nace kina da hijabi da niƙaf ? Me za'ayi dasu ne ? Nace Dikko ne naji yana maganarki yanzu yace baiji daɗin abinda yayi miki ba da zai ganki da zai baki haƙuri amma sai ya ganki cikin niƙaf da hijabi dan ranar nan ma abinda yasa ya dakeki wai saboda kinzo ko gyale babu shi yasa kika ɓata mishi rai dan kishinki yakeyi sosai , Hafsa tace muna da niƙaf mana wanda muke amfani dashi idan zamu shiga wurin da bama so asan mune , nace to ki saka niƙaf da ƙatuwar hijabi ki shiga napep karki tafi da wani ya rakaki kinsan su "yan siyasa basa san surutu shi yasa sukeyin komai nasu cikin sirri , kicewa mai napep ya kaiki Fesra hotel dake hanyar shinkafi idan kinzo wurin ki kira wayar Dikko kinji ko ? Tace to , nace yawwa kiyi sauri kinsan baya san jira , tace yanzu fa , tana faɗin haka na kashe wayata na sake kiran Dady , Bayan ya ɗauka nace ya kamata kaɗan sirrinta motarka a cikin hotel in dan wani ne zai ajiyeni a mota ban sani ba ko ya sanka , Dady yace ai dama ba'a mota nake ba ina zaune a ƙarƙashin wata bishiya ne ba da mota ta nazo ba , kashe kiran nayi tare da cewa lallai ka shiryamin zagon ƙasa da yawa , Wayar mai cewa saiya kasheni na sake kira bayan ya ɗauka nace wallahi ku dukanku baza ku iyamin fyaɗe ba , na rantse da Allah duk yawanmu sai munyi wasan danbe dake wallahi ׳ sannan mu kashe ki , idan kuma kinyi sa'a kin mutu kafin mu gama kin huta , dariya nayi tare da cewa aiko rijiya ta ƙafe da zaran anyi yasa wasu ruwan ne zasu sake ɓulɓulowa ƙananan kwartaye daku nice uwarku gani nan zuwa... Kashe wayar nayi na koma cikin mota inda Yazeed keta jirana , ina shiga yaja muka nufo cikin babban birnin garin katsina ta Dikko ɗakin kara , kunya gareku badai tsoro ba , A motar Yazeed na saka cajin wayar dana anso a wurin Yayar Aunty dan wayar a kashe take ba caji , bayan na saka naci gaba da sauraren waƙar da Yazeed kebi ta mai girma gwamna , A zahiri nake sauraren waƙar amma a baɗinance ina tunanin yadda zan ƙare da masifar da nake san haɗawa dariya nayi a bayyane a zuciyata nace ai basu iyawa dan basu da shedar da zasuyi shara'a dani harkar karuwanci dai kowa yasan anayi ko sunkai ni ƙara kawai zancewa alƙali ni karuwa ce kuma kawaliya ce , inayin karuwanci ne saishi Dady ya kirani yace inzo , sai ince ya mai girma mai shari'a da ya kirani to dama wayata ta kwana biyu kashe babu caji , shine ina buɗewa kiranshi Dady ya shigo bayan na gama waya dashi akan yana da muradi munyi ciniki nace na sallama , bayan na gama waya dashi sai na fara bin kiran miss calls in da aka ajiyemin a wayata bayan ya ɗauka shima dai muradin ne sai naji shi wannan zai bani kuɗi da yawa to kaga tunda ina kawalci kawai saina tura Hafsa taje wurin Dady nace mu raba ƙafa taje can ni inje wurin masu yawan dan danbe zasuyi tunda ni nafita kuzari da kuma daɗewa ana ɓarin wuta a gado , Sai Dady yace ya mai girma mai shari'a ai Hafsa ɗiyata ce , sai Alƙali yace ke Sultana me yasa kika haɗa uba da ɗiya sai ince ai ranka ya daɗe ni badashi na haɗa ta ba a tambayeta Dikko nace mata , wata zufa naji ta ketomin duk da a c dake cikin motar , yayin dana hasko har an kirawo Dikko ya fara wannan ihun nashi ana riƙeshi yana wannan zaburar yana saiya kashe kowa... Wayyo Allah ba Dikko ba kai ba , Ajiyar zuciya na sauke tare da sake tunanin Alƙali zaice kince Dikko to ya akayi kikace bashi ba kuma ? Shikenan sai inyi shiru inta mazurai banda mafita dan idan an tambayi Hafsa zatace ai cewa tayi Dikko yace in sameshi a Fesra hotel , na shiga 3 , ina cikin wannan jimamin sai Alƙali yace to ya akayi kika samu miss call na wasu kwanaki , sai in nuna mishi miss call in wanda aka taramin ranar da akace za'a kasheni , bayan alƙali ya gani sai kuma yaga nabi kiran babu daɗewa , da sauri na goge wancan tsohon kiran , sai Alƙali yace ya akayi duk kwanakin baki bi kiran ba sai yau ? Kuma kinga miss call , sai ince yamai girma mai shari'a ai nazo zan ɗauki wayar ta mutu saboda rashin caji , idan alƙali ya irga kwanaki sai yace har kwana kaza bakiyi caji wa wayarki ba ? Shafa kaina nayi tare da cewa ai cewa sukayi zasu kashe ni.....? Meye shedar ki kin shigo da wani zance a wani , kai aiko ubana zanci. A , a bazanci ba tsautsayi sai yasa suce ai ranka ya daɗe ta kirani bayan na kirata , dama ina da record in kiran sai in faɗawa alƙali sai yace in kunno aji , zufa nagoge lokacin dana kunno amma ba m card a wayar an cireshi wani irin ihu nayi tare da cewa Dikko me yasa ka ciremin abuna ? Wallahi Dikko ya cireshi da sauri na zura ƙafata na taka burki tare da kaɗa kan sitiyarin motar kamar sakarai haka Yazeed ya sakar min motar dan mun shigo cikin gari kallo Yazeed yabini dashi tuni na juya kan sitiyari na tun kari goruba road Yazeed ya zuƙe gefe ɗaya dan rabi na a saman jikinshi nake shi tuni ya ɗauke kamar an ɗora kura saman kare , banma san yanayi ba , ina tuƙin nake tunani anya ma Dikko yana garin nan gaskiya baya nan dan daya nan bazai turo min Ashiru ba , Ai banma tsaya ba dana isa goruba yadda naga duk an watse gidan ana rusashi aiki ake mishi kuma baya zama , cikin hayaniya nace Yazeed ina Dikko yake zama banda nan ? Banza yayi dani dan baya iya magana , kai tsaye gidanmu na nufa a wurin Ashiru zan samu wannan ansar ,..... Ilimi ake nema baiwa kuma samunta dace ne. 23/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA.....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 62 Tunda na shigo anguwar na danna horn biyyyyi , ina isowa bakin get in gidanmu tuni an buɗe min get na shige ko parking in kirki banyi ba na fito , ina fitowa Ashiru na gani tsaye jikin mota , kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannuna nayi da mamaki ya akayi ya tashi tun yanzu ? Kamar yasan abinda nace yayi dariya yace shi kuma wannan wasan ya kika ganshi ne "Yar mata ? Ashiru ba wannan ba ina Dikko yake ? Murmushi Ashiru yayi yace mahaukaci bari kiga saƙon daya bari a baki idan kin dawo , wayarshi ya ciro daga cikin aljihu yana cewa bani ɗaya bane nake tare dake irina da yawa mai gida ya watsa kina tunanin kin barni ina bacci tunda kika fita a gidan nan akazo aka dawo dani daga duniyar baccin da kika turani , saboda anga fitar motar Yazeed amma ba'a ga fitowa ta ba wannan dalilin yasa aka zo dubawa ko lafiya , amma abun kunya wai kin mameni na tafi doguwar suma , hmmm Yadda sukayi tunani kuwa haka ne ina kwance a mota ina bacci kamar wani kolon namiji , irin abinda nake amfani dashi ya ɗauko a mota tare da wurgomin na riƙe yace mai gida yace a ƙara miki dan yasan naki ya ƙare daga yanzu , kinga wannan ya nunamin wani abu a baƙar leda yace dashi aka maidoni hayyaci na , ya kika ga wannan hotunan ya nunamin lokacin dana fita daga cikin motar Yazeed da lokacin dana koma cikin mota , har kuɗin dana bawa Yayar Aunty zuwana goruba , dariya Ashiru sosai tare da cewa kina ja da mahaukaci ne yarinya , tou bari kiji abinda majnun yace......{ mahaukaci } Record ya kunno na maganar Dikko , "Yar yarinyana barka da hanya fatan kin dawo lafiya ? Ya gajiya ? Allah ya huta gajiya , am An mata nine mahaukaci dai ko ? To wai sai yanzu kika gane mahaukaci ne ni ? Aini tunda nake ban taɓa hankali ba kullum cikin hauka nake kuma wallahi ׳ zan nuna miki ni cikakken mahaukaci ne ina nan dawowa babu jimawa idan na dawo zan nuna miki babban haukana , duk fita ɗaya da kikayi ki sani ko wace da irin azabar dana tanadar miki wallahi saina zane miki jiki tass idan na dawo kinji nayi na rantse kuma wallahi saina rufeki a ɗaki zanga wanda ya isa ya kwaceki a hannun mahaukaci , kinyi ɗaya Allah ya baki sa'a kuma kada Allah ya sanyaya miki zuciyarki ubangiji ya ƙaro miki taurin kai da kangara ni kuma yabarni da fitina na dani dake wanda ya fasa shi ba ɗan baban shi bane , wato maganar dana taɓa faɗa mishi lokacin dana kashe mishi doki , Juyawa naji cikina yayi ƙuww maida wayarshi yayi a aljihu yace tou ni zan tafi dan mai gida yace in tafi in barshi dake tunda ke yarinya ce shi da izininshi bai yadda in fitar dake ba , yace kawai inje abuna inyi huɗɗoɗi gabana , har ya shiga mota ya fito ya sake cewa kalli wannan dan ki koyi yadda zakiy faɗa da mai gida , Dukan da yayi ma Al ' Ameen ne a wayar Ashiru , abiyar zaman mahaifiyar shi tayi video dan sharri ta turawa Dady , shine Dady ya turowa Dikkon shima dan ya gani Dady yace ina anfanin wannan ? Kaga irin abinda kakeyi Babana miye haka dan Allah ? Ta ɗauka dan tayi ta yaɗashi a duniya ta ɓata maka siyasarka , tou ka kiyaye wannan doke²n , amma nace mata wallahi idanma tasan ta tura ma wani vidio nan tasan yadda zatayi dasu su gogeshi idan har na naji labari ko ganshi yana yawo a duniya tasan abinda zai faru da ita , Dakel na haɗi wayun bakin na zufa ta ketomin , Ashiru yace ai finafinan yawa garesu wannan talla ce idan kika kalli cikakken film in fitsari zakiyi tsiii a wandonki , cike da ɓacin rai nace ya akayi banyi ba ? Ashiru yace sauri kike ? Ki fara lissafi daga yanzu duk ranar da mai gida ya riƙeki a hannun shi idan kikayi ni zaki fara tunowa kice ashe Ashiru da gaske yake , dariyar mugunta yayi tare da cewa an kunna wasan mudai Allah ya taimakemu mun fita lafiya , 1 ya faɗa tare da nunawa da ɗan yatsanshi yace ki daure ki fita ko so ishirin ne yarinya kiga yadda zai miki lullusar fitar hayyaci saiya maida ke gari muna gefe muna kallo , na barki lafiya yana faɗin ya shiga motarshi yayo wurin Yazeed , Saida ya kalleshi sosai yace kai kuma ni da kaina zanci uwar data haifeka idona idon ka saina baka kashin bala'e saidai in ka daina yawo a cikin garin katsina , murmushi Yazeed yayi tare da cewa nima idan har ka ganni ka gudu ka ɓoye dan sanyi da ruwa bazai hanaa inci uwarka ba , Ashiru yace mu zuba sakaran banza anyi maka rana kana nema kayiwa mutane dare gara ka tuba tun kafin kayi biyu , ko da yake ni nasan yadda nasan mutuwar da zata ɗaukeni mai gida bazai koreka ba danshi ba matsiyaci bane irinka amma nasan saiya ci ubanka cikin farashi mai tsada , sakaran banza butulu kawai mutum mai manta alkairi da akayi mishi a baya jaki ne , ka tabbata jaki , jakinma mai ɗan guntun bindi , kuma wallahi saika bar comparny tunda ba filin tsakar gidan ubanka bane ba , ko mai gida bai koreka ba wallahi da kaina zan kora maka uwa....... Yana faɗin haka ya fice da gudun tashin hankali , Wurin Yazeed na nufa nace da Allah ƙyalesu mahaukatan banza daga shi har Dikkon , murmushin ƙarfin hali Yazeed yayi lallai Sultana yarinya ce wato tana ganin wannan abun a rabu dashi ne , idan har yaran Dikko sukaji wannan wallahi sai sun ciccirashi idan har aka bajeshi a saman faranti akace su cinyeshi wallahi wani ma bazai samu inda zaici ba , dan Dikko yana da kirki yana musu hauka da kuɗi kuma shike cidasu sun tirku kamar karnukan turawa kuma an basu horo mai kyau na faɗa , idan har Ashiru ya faɗa musu halin da ake ciki ya tabbatar fita ya gagareshi har gida ma suna iya zuwa su ɗaukoshi kuma basujin yi haƙuri bare ku bari Dikko kaɗai ya isa ya dakatar dasu , Dady ya samo su dan su kula da tilon ɗanshi kuma Dikko baya fita sai tare dasu rabon dai Allah ya haɗashi da Sultana yake fita shi ɗaya zuwa wurin dawakai , kuma ranar daya fara zuwa shi ɗaya Allah yasa ya watsawa su Sultana ruwan dake kwance saman ƙasa ta bishi tana zaginshi zagin da tayi mishi yasa yayi mata mark tun daga wannan ranar bata sake ɓace mishi ba , kuma ai ita Sultana tasan irin yaran Dikko tunda shi Dikkon ya taɓa zuwa da ɗaya anguwarsu lokacin daya taka mata mage , dan Dikko ya tafi dashi yaci uwar Sultana amma yadda tayi magana cikin sanyi cewa da Allah cikinku waye yake tuƙar motar nan ? Ya takamin magena , sai Dikko yaji ta bashi tausayi kuma "yar ƙarama da ita amma ta cika taurin ido shi yasa yace mata itama gobe idan ta tsaya a hanya haka zaibi ta kanta da mota ya wuce , sai ya hana a daki Sultana dan gani yake duka ɗaya zai mata a shafe tarihinta a duniya... Ajiyar zuciya Yazeed ya sauke wallahi baisan zai haɗu da Ashiru ba a dai² wannan lokacin da bai shigo ba , da yanayin gajiya ya kalleni yace bara in ɗanje in huta zan dawo anjima , sai ka dawo na faɗa tare da cewa ngode.....🙏🏻 , saida ya tafi na wuce cikin gida a tsorace. Napep na sauketa ta fiddo wayarta ta fara kiran wayar Dikko wannan layi da ake kira a kashe yake , shine ansar da ake bawa Hafsa , tana tsaye tana ta kiran waya taji an nanɗeta ta baya , kai su waye haka ina zaku tafi dani wayyo Allahna , wani irin mari Bello yanka mata tare da cewa wurin ubanki zamu kaiki , kai ku sakeni mana a , a wai miye kukeyi haka ne ? Wayyo Allah bana so jama'a ku taimakeni masu satar yara , ku buɗemin fuskana kun shaƙeni da niƙaf numfashina zai ɗauke , Mota suka danna Hafsa da ƙarfin masifa , tana ihu suka daɗe dai² saitin bakinta dole tayi shiru dan sautin ihunta baya fita , basu dawo cikin garin katsina ba suka kama hanyar kaita da ita , Wayyo Allahna me zan gani haka ? Uncle waye zai kashe ka na shiga 3 ƙaryana zai ƙare karka mutu ka tashi don Allah , kallon rainin wayau Jiddah tayi mata cewa ke kuma wacece ? Cikin kuka Mardiyya tace Mardy beb mai dogon zamani , Jiddah tace ke kuma ya kike da majiyancin ne ? Mardiyya tace Uncle ...... Saida tayi shashshekar kuka tace Ubana ne Uwa na ne shine komai nawa , ke kuma wace ce ? Nice Jiddah , Mardiyya tace wace ce Jiddah ? Jiddah tace ni Jiddah Matar Dikko.... Cike da makirci Mardiyya ta rungume Jiddah tana cewa mun shiga 3 Aunty namu ya ƙare Allah yaba Uncle lafiya , Jiddah tace am3n , Aunty Yaya DK yasan Uncle baida lafiya kuwa ? Cikin ɓacin rai Jiddah tace ai shine ya dakeshi , Mardiyya fa tasan Dikko yayi dukan saboda Umar da kanshi ya bugawa mahaifiyar Mardiyya waya cewa Al ' Ameen baida lafiya kuma mai gida ya bashin kashin bala'e , danshi Umar komai da ruwanka ne haka "yan gidan gwamnati suke kiranshi shi yasa ko abu akeyi da an ganshi sai a bari idan kuma magana akeyi da an ganshi sai ayi shiru inba haka ba yanzu zai ɗauketa yayi gaba da ita , ita kuma Mardiyya tanayin magana da Jiddah dan su samu kusanci saboda so take ta zauna gidan Jiddah. Sai wani shishshige ma Jiddah take , bayan sun gama jimamin Al ' Ameen cikin kuka Mardiyya tace Aunty Uncle yana sanki sosai kuma yana bakin ƙoƙari wurin ganin yayi maganin "yar iskar yarinyar nan dan kinsan ni dashi bama ɓoye ma juna komai , yana ƙoƙarin yadda zaiyi ya raba Sultana da Yaya DK yarinyar tsinanniya ce kuma karuwar ijece ita , karuwa ce mai zaman kanta amma tanayin karuwancin nata da tako ne domin ijin wuta takewa mutane sai ta akisu ta barosu , ƙara fashewa da kuka Mardiya tayi cikin kuka tace harfa girman Dad ina tasa wata matatta ta ɗauko mata ta turomin , kuma duk yadda akayi itace tura Yaya DK yayi ma Uncle dukan nan , Cikin rashin fahimta Jiddah tace harda matattu take huɗɗoɗinta kenan ? Ita kuma abinda Mardiyya ke nufi kafin Mamy ta mutu shi yasa tace wata matatta , a fahimtar Jiddah ita kuma wanda suka mutu dasu Sultana ke huɗɗoɗinta dasu , bata gane ba kuma bata tambayi Mardiyya tayi mata bayani ba , sukaci gaba da neman mafita yadda zasuyi maganin Sultana yayin da ita Mardiyya ke tunanin anshe goruba hannun kuturu ba wuya take ba , ita kuma Jiddah ta saki baki taci gaba da rattafawa Mardiyya bayani , ta kasa yadda zata samo sperm in mijinta , Mardiyya taci gaba dai da warware mata tunani tana ɗorata a hanyar halaka.... Wani irin ihu Hafsa keyi yayin da aka fara gabatar da wasan danbe a saman ruwan cikinta , wani gidane suka kaita a can cikin garin kaita yayin da Bello ke cewa ba kince ke jar wuya bace ba , ai zaki iya damu ko ? Ba kince ke rijiya bace ba ko kin ƙafe da an yasa wasu ruwan zasu sake ɓulɓulowa ? Ai kince mana mu ƙananan kwartaye ne ba ? Yau zamu nuna miki mun manyan *KWARATA...* ne , a dai² lokacin da wani ya sauka wani ya taka saman Hafsa Bello yana cewa nine Bello aminin ubanki kiji da kyau yadda kikamin video tsirara haka zanyi miki kema , ni na koyama ubanki iskanci amma dan iskan ya lashe min matata a daren farkon dana shigo ina murna zan buɗe ta a leda amma ɗan iskan ya yage min mata ya gudu saboda kawai nayiwa yarinyar gidan da suke zama fyaɗe ba dangi uwa bana uba , amma banza ina gama dafuwata ya cinye kafin inci yasha ruwa ya kama gabanshi , Na saka banzan a tarko na amma ranar dana ɗana masa ɗan banzan ya tsalleke , idan baki sani ba nine nayi asiri wa Babanki kuma na haɗashi yake tarayya da ɗiyar Yayanshi wanda suke uba ɗaya , kuma nine nayi asiri na haɗashi yake iskanci da ɗiyar Yayanshi wanda da Babanshi da Baban yarinyar suke uwa ɗaya uba ɗaya , kuma nine nayi asiri ya sakaki a wasan caca nine na maidake kidahumar ƙarfi da yaji nasa kika antaya a ruɗun rayuwa , Wani irin ihu yayi tare da cewa naji baƙin ciki yau da ubanki bai duniya naso ya gani yadda zanyi zazzagar da yayi a saman matata yau zanyi akan "yarshi amma nasan soyayyar da yake miki duk da yana cikin ƙasa yanaji yana kallo yau ni Bello zan cinyye yadda ka kayimin nima zan rama idan zaka iya fitowa daga duniyar mutuwa kazo ka ƙwaci "yarka a hannuna , Dady dake gefe tsaye ya kasa gane inda maganganun Bello suka nufa , kamar ya yake nufi yayi asiri ya haɗa ahali ɗaya sunyi wannan gauragaurayar haka ? Yana tunani yaji Bello yace masa kaima Alhaji Binna yabi naka ya lashe baka da burin daya wuce ka lullusa akan wannan tsinanniyar yarinya a dai² lokacin da Bello ya afka magunguna a bakinshi ya kora da ruwa akaci gaba da video shi kuma yaci gaba da sharar fage yana ihu yau shine yake lalata "yar Binna ashe dai muradina zai cika ? Dady yace nifa duk ban gane abinda kake nufi ba , Hafsa jin maganar mahaifinta yasa tayi magana cikin wahala cewa Dady zasu kasheni , Dady jin muryar Hafsa yasa yayi wurin ya yaye niƙaf in bawai yana dan yana tunanin Hafsa bace ta kasance a wurin ba hasashe ne , yana yaye niƙaf in Hafsa ya gani tasha azaba sai zaro ido takeyi kamar ɓera yaci guba tasha kuka harta gode Allah saboda azaba , cikin hayani yace ma Bello dan ubanka ɗiyata ce sauka yana ɓanɓaro Bello amma Bello ya dafe Hafsa sosai yana cewa ba'a buga ƙaraurawa ba , Dady yace ƙaraurawar ubanka ince maka ɗiyata kana min maganar ƙaraurawa , Bello yace ai nasan ɗiyarka ce ka koma gefe kaima za'a buga naka zaizo , da ƙarfin bala'e Dady ya fizgo shi amma Bello ya ƙadaddabe Hafsa yana cewa ba so kike kisan su waye *KWARATA* ba ? Tou buɗe kunnenki da kyau , Bello kwarto ne , ubanki Binna shima kwarto ne , Yayan ubanki gashi nan tsaye a gefe yana so na sauka ya hau to shima kwarto ne , kowa kwarto kwarto kema kwartuwa dani dake dasu da kowa *KWARATA...* ne , Bello yace ku janyemin mutumin nan kumin baya dashi ni kuma inyi gaba da ita mu ci gaba da fafatawa , kama Dady sukayi suka riƙe suna cewa Alhaji ba haka akeyin wasan danbe ba kaima idan ka hau babu mai saukoka sai ka gaji da kanka ka sauka , Dady yace ba Sultana bace Hafsa ɗiyata ce dana haifa da kaina itace ya akayi kuka kawomin ɗiyata bayan munyi daku ɗiyar Binna shine kuma kuka cuceni kukaci amanata wallahi duk saina tsine muku albarka , cikin kuka Dady yace Allah ma bazai barku ba kuma nima bazan barku ba , da sauri Bello yakai dubanshi ga Sultana amma maimakon Sultana sai yaga Hafsa da tuni suma , shima cikin tashin hankali yace ina Sultana take ne.........? Misalin ƙarfe 3:12am ƙaran wayata ya farkar dani daga ƙatoton baccin daya daɗe yana morar gangar jikina da idanuwana , dakel na lalubo wayar ba tare dana duba ba na ɗauka na ɗora a saman kunne na , nace hello , Dikko ne ya faɗa kai tsaye , cikin faɗuwar gaba na buɗe idona da sauri na tashi zaune nace ina kwana , lafiya lau ya kike ya rashin ji da taurin kai ? Kayi haƙuri don Allah , ai nayi haƙuri shi yasa na kiraki wannan kiran bana rarrashi bane ko yasa ki nemi afuwa ra'ayi nane yasa na kiraki kuma kiran nan bazai hana na zaneki ba wallahi saina zane miki jiki tass idan na dawo kuma bazanyi kaffara ba , kuma ban kiraki dan ince ki daina fita ba duk ba wannan ya shafeni ba yanzu soyayya ne , haka nake laifinki bazai shafi soyayyarmu ba , na faɗa miki ko munyi aure kikaimin taurin kai saina baki azaba kuma mu koma gado nanma in nuna miki girma na , kinsan mahaukaci baida zuciya... Tou ya kike ? Fatan kinajin daɗin bacci , faɗamin kinyi missing ina ne ko ya ? Dan Allah kayi haƙuri , cikin muryar shagaɓa yace ke kina san mahaukaci ko ? Nidai dan girman Allah kayi haƙuri wallahi bazan sake ba , ah lallai abu ya girma An mata hada mafarkina ? Nidai ba haka nace ba cewa nayi kayi haƙuri , Ey wallahi ai haka nake so kullum nayi ta zuwa miki a baccinki , a , a ba haka ba cewa nayi kayi haƙuri , duk maganar dana faɗa sai yayi wata magana daban , tsoki nayi shi kuma yace ke karfa ki sunbaci ni yayi maganar yana yin wata irin dariya mai kama zuciya , naja miki gemuna An mata tunda baki gaishe shi ba , ki duba a whatsapp inki zaki ga Dikko yana gaishe ki , ni ina ruwana da gemunka , kai wannan gemu ya tsare miki zuciya Allah dai ya nunamin ina da rabon gani ranar da zaki ritsa uztaz a ɗaki kija gemu , yaƙi ya ida maganar yace bara dai in barki karki kasa komawa bacci , cikin wata irin murya mai saukar da kasala yace ina san ki...... Murya mai kama da raɗa ya maida maganar shi cewa mahaukaci ya barki lafiya , saida yayi muah da yanayi mai shiga zuciya ya kashe wayarshi ya barni da tunaninshi... Buɗe data ta nayi saƙonni suka shigo , na Dikko na buɗe ina duba hotunshi , duk yayi su a cikin yanayin farin ciki hada Dadynshi ya rumgeshi cikin soyayya duk su dukansu suna cikin farin ciki , murmushi nayi tare da cewa an gaishe da mai kyau , idan yayi murmushi yanayin kyau an sharce gemu yayi kalar ɗaukar hankali , voice note yayomin to ya kikaga mutumin naki ne ? Nima voice note nayi masa cewa wai kai shakarunka nawa ? Na tura , cikin magana mai haɗe da dariya ya maidomin cewa ke yarinya yo ai da kaɗan kika girme ni , bayan naji na tura mishi nine ma na girme ka ? Ey mana baki ganni ɗan yaro ba , ko gemuna ne yake buɗe miki ido ? Amma ai cewa kake kai babban mutum ne , haba An mata nima fa ɗan saurayi ne ko nayi miki tsufa kike tunani ? Karki ja da baya duk abinda kike tunani a wurin marar gemu a wurina zaki samu yarinya , to daga nan muka koma faɗa saida Dikko ya tabbatar nima ya ɓatamin rai akayi rabuwar baran² yace kuma naja ma kaina bazai sake kirana tunda banda wayau , Cike da sanyi jiki na koma na kwanta , nidai ina san halin Dikko ina sanshi matsalarshi saurin fushi , hotunanshi naita kallo kamar banda aikinyi , idan na kalli hotonshi sai in hararo siffar Yazeedu kai gaskiya jirgi yafi mota ko a tafiya ma akwai banbanci , murmushi nayi cikin yanayin ɓacin rai nace mutumina kenan ko harsai zuwa yaushe zaka dawo.....? Murmushi yayi cikin yanayin jin daɗi yace An mata kenan na hayaƙaki ko ? Saina dawo zakiga yadda zanyi dake saina ɓata miki rai gaba ɗaya , hmm yarinya kin rainani da yawa wallahi , amma duk saina sauke miki duk wata rashin kunyarki dake ɗauwaniya da rayuwarki dole sai kinsan nine gaba dake , idan ba'a share masallaci ba za'ashare kasuwa ko wattuba dan wuya ba lada , kuma saina sake kiranki anjima ki gama fushinki saina hana ma zuciyarki zaman lafiya da tunanina.....! Mardiyya gidan Jiddah ta kwana suna ta tattauna yadda zasu shawo kan wannan matsalar , yayin da Jiddah ta buɗe baki taita tonawa Dikko asiri duk yadda yake kwanciya da ita take bawa Mardiyya labari wai dole take ɗan haɗawa da kayan mata Dikko fitina gareshi kafin safiya tayi sai ya buƙace sau3 , wai ko wucewa tayi tana ɗan murzawa sai yace wai a likitance idan mace tana irin wannan tafiya tana buƙatar namiji ne , kai wasu matan dai wawaye ne wallahi mijinki ya kulle ƙofa dake yayi sirri ki fito duniya kina barbaɗawa , wacce kike ba labarin duk lokacin data ga mijin naki sai wannan maganar naki yazo ya tsaya mata tana kallonshi da wannan maganar da kika faɗa haka babu kyau kuma zunubi ne mai girma , Idan kuma kikayi sa'a da "yan iskan mata idan suka gano logon mijinki suka san yanayin sha'awarshi idan ɗan iska ne can zasu zagaye su riƙe miki wuyan miji suyi ta lalata dashi , ke kuma abarki ki zama hoto sunje sun riƙeshi sun zazzage miki shi ya dawo ya kasayi miki komai ke kuma daga nan zaki fara tashin hankali bayan ya riga ya gama horaki da irin yadda yake kwanciya dake , aikinki surutu daga nan saiki ce ai mijinki yanzu baya gamsar dake , dama sunajin haushin kin samu namijin dasu basu samu irinshi ba , naki ya iya gamsar da mace nakine yasan sirrin kwanciya da mace sunajin baƙin ciki basu samu kamar naki ba sai su koya miki bin mazan waje , daga ƙarshe kuma ya ganoki saiya sakeki kije kiyi auren kuma wanda kika aura yazo ya kasa miki irin wanda mijin da kuka rabu yake miki , kila mijinki ya saba kwanciya dake sau 2 ko 3 yadai danganta da yanayin ƙarfin sha'awarshi sai ya nemiki sau adadin lambobin dana faɗa kafin gari ya waye wasu kuma sai suyi 4 kofin haka kafin safe , kuma zai baki su lafiyayyu masu daɗewa suna miki yawo a zuciya , tou shi sabon mijin sai ya kasa baki ɗaya ƙwaƙƙwara daga nan kiji baki iyawa ki ɓallo , kina dai cin abinci mai kyau kici ki ƙoshi jini yana zagayawa ko ina a jikinki ƙarya kike kice baki buƙatar namiji saidai yanayin sha'awa kowa da irin nashi , haka zaki koma kiyi tabin maza kina ganin ina zaki samo kamar wanda kuka rabu , sai Allah yasa ki kasa samo kamar tsohon mijin naki , Itafa mace kamar tanda haka take horar da ita ake horon da namiji yayi mata tun tana toya waina jagwalgwalalla zata fara fiddo mai kyau , dan Allah mata mu riƙe ɓoye sirrin mazajenmu wallahi kanmu muke zubarwa da mutunci , Allah yasa mu dace..... Jiddah taci gaba da cewa gashi kuma idan nasha magunguna ya sani duk lokacin danasha maganin mata ya kwanta dani zai faɗa , idan kukawa kikaji yana faɗin sunan kaya zakisha mamaki kodan ya tashi cikin mata ne ? Wai shi shine ɗan mai ganye idan ina so wai zai haɗamin wasu sirrika masu kyau inyi amfani dasu kuma duk haɗamata bazan iya ƙureshi ba , a yadda yakemin ma tausayi na yake fa , yana da rauni akan mace sosai , yace ita mace abun tausayi ce kuma abun daratawa ce shi yasa ko da yahaniya baya ma mace magana karta firgita , { amma saida Sultana ta ƙure Dikko harya ke dukanta....} tasha dai rashin wayanta ta ƙoshi Mardiyya kuma ta nannaɗe a haɓar zani ta shirya tayi asibiti dan yau Dikko yace ma Jiddah karta fita yawonta yayi yawa... Wallahi gaba ɗayanku saina sa an ɗaureku...... 24/10/2019👇🏻 *JAMILA MUSA....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 63 Bello yace kamar ya a ɗauremu ? Dady yace saboda ka lalacemin "ya a gaban idona har ina tsaye inabin layi a doka ƙaraurawa in hau saman ruwan ciki ɗiyar dana haifa , taya kake tunanin bazan sa a ɗaureka ba ? Bello yace gafara can itama ai wacce kake tunanin taka ruwan cikin nata itama "yar taka ce sakaran banza ka lalatamin duk wani tsari nawa ai duk cikar garin katsina da batsewar ta babu ubanda ya isa yasa a ɗaureni , bana ɗauruwu a wurinka kaidai sakaran banza mayen mace , to idan baka sani ba ka sani idan kuma ka sani ka ƙara sani Sultana ɗiyar Binna ce , wani irin juyi Dady yaji duniyar tayi mishi kanshi ya sara , cike da tashin hankali yace wane Binnan ? Bello yace Binna nawa ka sani ɗan uwanka da kuke Baba ɗaya dashi ƙaninka.... Saida Dady ya sakejin duniya tayi mishi ƙundubale yace Hajiyata ɗiyar Binna ce .....? Bello yace tabbas , wani irin haushi Dady yayi hafhaf kamar kare yace shikenan na kashe kaina shegiyar yarinyar nan tazo har majalissa ta sameni wai tana so taga bayan Binna dan wawanci da kidahumanci irin nawa ni idona ya rufe akan mace nace mata ai wani ya rigaki dan tuni an daɗe da tura Binna zuwa duniyar mutuwa , girgiza kai Dady yayi tare da cewa amma shu'umar yarinyar nan tacemin wane mai zarrar ne wanda yafi mace zafin nama....? Tabbas mutuwar ki ta zama dole abun kunya na rungumi ɗiyar ƙanina na farfaɗa mata maganganu masu girma na lashi bakinta na tura hannuna a cikin rigar nononta , na kamo hannunta nakai a girma na kai , idan har duniya taji wannan abun kunya sai tsinuwar mutane tahau kaina........ Wato a wancan lokacin taso na faɗa mata wani abu , tabbas nace mata ni Yayan Binna ne , tana tare da wani ƙuduri a ranta tuni tasan wani abu ko kuma wani abu ya faru ya akayi ta shigo rayuwata ..? Wannan shine abinda ya kamata na sani farko kenan kafin inyi mata hukuncin daya dace da rayuwarta , shiru yayi yana nazari zuwa wani lokaci yace an kira Sultana nan ya akayi Hafsa ta bayyana wurin a maimakon Sultana ? Sultana tace zata zo sanye da niƙaf ya akayi Hafsa ta sako niƙaf tazo....? Mu kai Hafsa asibiti saita dawo dole duk zamu samu ansar wannan tambayoyin namu. Cikin ɓacin rai Dady ya kalli Bello yace tun can baya boka yayi magana akan Sultana me yace wanda yasa muka toshe kwalwarta a kwalba....? Cikin tashin hankali Bello yace bayan Binna yazo yana farin ciki a gidana an haifar masa yarinya mace yace nasarar rayuwa yazo mishi , na tayashi murna sosai yayin da yake cewa ya samu mai share mishi hawayenshi tabbas nasara ce tazo , sai yace kuma yanaji a jikinshi ko baya raye "yan uwanshi zasuyi alfahari da jaririyar da zai sakawa sunan mahaifiyarshi. Na taya Binna murna sosai bayan ya tafi daga gidana nazo na sameka na faɗa maka duk yadda akayi , a wancan lokacin sai kace muje a faɗawa boka yayi bincike akan ita yarinyar , abinda boka yace mana bayan yayi bincike shine kawai a toshe kwalwar yarinya shine mafita , Bello yace da muka tambayi dalili boka yace idan yarinyar ta girma zatayi ilimi tunda Binna yana da ƙudirin haka akan ta , yarinya tana kishin mahaifinta idan ta tashi ta ganshi a harkar caca zatayi faraucin fitar dashi a caca ku kukace ya dawwama a caca da zinace² idan yana yinsu ya gama lalacewa a mantar dashi tunanin mahaifinshi bare yayi tunanin dukiyar da aka bar muku na gado... Dady yace ya akayi tasan Hafsa ɗiyata ce ? Ya akayi tasan cewa nine baban Hafsa ya akayi ? Ya akayi Bello tasan ina tare dakai ? Bello yace bata san muna tare ba gaskiya nidai nine nayi mata waya cewa saina kasheta , shine tacemin idan na isa zan iya kasheta in kasheta a wurin fesra hotel , yayin da zata sauko daga napep sanye da niƙaf , muna zuwa sai muka ganka a wurin sai muka tsaya muna gaisawa saiga napep ya sauke mai niƙaf bayan dama wacce muke nema tace mana zata zo sanye da niƙaf bamu tsaya bincike ba muna ganin mai niƙaf muka rufa mata tunda dai ta sauka a inda Sultana tace zata sauka , ka tambaya lafiya ? Sai nace maka Sultana ce , kace wace Sultana sai kawai nace maka ruwana ne , kace kana sha ba tare da sanin ko wace ce ba , ni kuma naga abokin cin mushe ba'a nuna mishi sai nace maka ni kasheta zanyi bayan mun gama morewa kai kuma kace muje bayan ka kira wacce kake jira bata ɗauki wayarka ba , sai muka haɗu gaba ɗaya muka taho nan dan bamu da isashshen lokacin da zamu tsaya muyi magana mun barshi akan sai mun gama zamuyi magana , Dady yace to bana tunanin Hafsa tasan Sultana muje asibitin munyi magana daga baya... A wahalce yace mai gida... Hawaye ya gangaro mishi daga cikin ramin kwarin idanuwan shi yace na bari kayi haƙuri insha Allah bazan sake ba , tashi Mardiyya tayi ta matsa kusa da Al ' Ameen ta kama hannunshi ta riƙe tana kuka , cikin muryar kuka tace Uncle wallahi tunda har ya dake akan Sultana wallahi kafin in bar katsina saina korata zuwa duniyar mutuwa , dakel Al ' Ameen ya haɗiye yawun bakinshi cewa karki kuskura ki fara tunkarar yarinyar nan dan wallahi idan har mai gida ya sani naki ya ƙare farko ma kenan , gara ki koyi yadda zaki kyautatawa Sultana idan har mai gida yaga kina santa wallahi sai yaso ki har cikin ransa saboda yana ma yarinyar nan soyayyar dashi kanshi baya san kanshi , yana san Sultana fiye da yadda yake san rayuwarshi , ko wane awa ko wane minti ko wane daƙiƙa wutar santa sake ruruwa take a zuciyarshi , Batajin magana karuwa ce mai lasi da take karuwancinta cikin tako da ƙwarewa , duk inda bakya tunani sansanin yanki garin nan tayi suna amma a ɓoye take huɗɗoɗinta , tunda ta samu ta dafe mai gida ta watsar da ko wane namiji ta koma zama gidanshi tana kwantalarshi , mafita ɗaya shine mu nemi inda Sultana take sai ki shiga rayuwarta sosai a fili ki nuna mata soyayya , a ɓoye kuma sai muci gaba da ɗirkaka mata asiri har mu samu muga mun shafe babinta daga duniyar masu rayuwa , Mardiyya tace haka zamuyi Uncle Allah ya baka lafiya ya ansa da am3n suka ci gaba da tattaunawa. Mai gida ina ganin yarinyar nan sai an haɗa mata da roƙon Allah ko zata samu natsuwa sai inga kamar ba ita ɗaya bace ba , Ashiru ne yake magana da Dikko a waya , Dikko yace ita ɗaya ce tsabar iskanci ne kawai da raina mutane ka barta kaga yadda zan dawwarata idan na dawo , Ashiru yace to ai duk dai firgicin da nayi mata jiya wallahi yauma ta fita , Dikko yace ai dama nasan saita fita An mata halinta sai ita amma wallahi nine maganin rashin kunyarta , yau kuma ina taje , Ashiru yace wallahi mai gida tunda duhun asuba yarinyar nan ta tafi sabon layi can wurin one way layi ne na tsofaffin karuwai maza da mata , idan kana neman duk wani feƙaƙƙen ɗan iska daya ansa sunansa a harkar iskanci kaje wurin saika sameshi indai ya cika karuwa mai "yanci , tsofaffin karuwai ne da sukayi karuwanci shekaru da yawa da suka wuce sune suke rainon wasu ƙananan masu tasowa , Salati Dikko yayi tare da cewa innalillahi wa'inna ailaihir raji'un , wallahi saina zane An mata idan na dawo , wallahi ko zata mutu saina daketa saina dira kanta , cikin ɓacin rai Dikko yake magana shin mema tajeyi ne a wurin ? Ashiru yace mai gida wallahi ban sani ba , Dikko yace kenan tana nuna itafa duk duniya babu wanda ya isa ya dakatar da ita akan duk abinda tasa kanta, wallahi ׳ nine na isa na dakatar da ita duk duniya baki da mai maganinki iskancin ki saini , kashe waya Dikko yayi bayan yacema Ashiru bara zan kiraka. Da sauri na kwanta saman gado tare da jan bargo na lulluɓe gyara muryata nayi na maida ita yanayin muryar bacci na ɗauki wayata dake tsuwwa saboda kiran Dikko dake shigowa , ina ɗauka nace kai mai zuciya ya akayi ka sake kirana bayan kace baza ka sake kirana ba tunda banda wayau , Murmushin ƙarfin hali Dikko yayi tare da cewa key kina tunanin zan iya fushi dake ne dama ? Wai kamar ya kakejin girman soyayyata ne a zuciyarka , An mata yanzu ba lokacin maganar so bane ina kika je ? Ni ? Na faɗa tare da dafe ƙirjina nace kaji sharri ni kuwa ina zanje bayan saman gadona , ke ina kikaje ? Dikko ina kuwa zanje bayan bacci ma nakeyi kiranka ne ya tasheni , An mata ina kikaje nace , cikin kuka nace wai wannan wane irin masifa ne bayan ɗazu wurin 3 da wani abu na dare ka kirani kuma ka tabbatar ina gida , ke ji nan na rufe idanuwana yanayin fushi ya fara hawa saman kaina kafin in faɗa miki magana mai muni ina kikaje yayi maganar cikin murya mai tada hankali , saida naji wani fitsari²n tsoro ya kamani cikin rawar murya nace ƙofar gida kawai na leƙa na dawo , Waye yace ki leƙa ? An mata baki so dai ki zauna lafiya ko ? Dole dai sai kin ɓatamin rai ? Nidai ko An mata ? Dikkon naki ? Haba An matana faɗamin wai meke damunki ne don Allah , duk cikin lallashi yayi maganar , shiru nayi na kasa magana ina shashshekar kuka , cikin murya maisa natsuwa yace dole dai saina dakeki zaki natsu ? Ya tambayeni , cikin kuka nace kayi haƙuri don Allah , wallahi An mata bazanyi haƙuri ba saina zaneki faɗamin ina kikaje ? Sabon layi naje , tou waya aikeki ? Babu , badai zaki kiyaye fushin mahaukaci ba ko ? Idan har kika sabar wa da kanki "yan doke²n nan ko aure mukayi hankalin baya kwanciya sai na dakeki banda kyau ne idan ina yanayin fushi kuma na faɗa miki idan na ɓaci ba nine ba , me yasa kin raini da Allah ? Ban raina ka ba , wallahi kin raina ni har kin faɗawa duniya kowa yasan kin raina Dikko , kayi haƙuri , hmmm banyi ba kuma wallahi bazanyi ba idan dai taƙamarki taurin kai da kafiya nace miki nine kangara idan har bazaki gaji ba nima bana gajiya tunda kema so kike ki zama kamar doki ko anhauki sai an dakeki ina nan dawowa babu daɗewa...... Yana faɗin haka ya tsinke kiran. Ajiyar zuciya na sauke tare da goge "yar guntuwar zufar data tsattsafomin a goshina bayan Dikko ya kashe wayarshi , lallai wato duk safko na su a wajen suka kwana , kaje ka dakenin wallahi bazan daina fita ba , kai ƙarewar fitar ma ai barin ƙasar kayi baki ɗaya ko kai nace karka fita ne ko karkaje ? Ɗan rainin hankali kawai , Abinda ya kaini sabon layi neman wanda yasan Mamy nakeyi , kuma na samu wanda suka santa , kuma na tambayesu ko akwai wanda yasan wata babbar aminiyarta amma ta ɓace kuma ni bansan sunanta ba amma nasan shaƙiƙiyar Mamy ce sosai shin ko akwai wanda yasan aminanta , lissafi akamin nace to sun san wacece aka kwana biyu bata nan ? Sai sukacemin *Raga* ce , nace tun yaushe basu ganta ba ? Lokacin da suka faɗa yayi dai² da lokacin dana san tamin waya cewa inyi sauri na samu Binna za'a kashe shi. Ina ne iyayenta suke ne ? Na tambaye su amma sai sukacemin gaskiya Raga babu wanda yasan daga inda tazo , wata tace amma naji ance bata lafiya tana asibiti , dana tambayi asibitin cewa sukayi gaskiya basu san asibitin ba , nace to waye yace musu tana jinya a asibiti ne ? Sai sukacemin gaskiya jinyar sirri takeyi , na nemi sanin asibiti sai sukacemin wani karuwanta ne kaɗai yasan inda take , wato kamar wanda suke iskanci dai , sai anjima zaizo nima kuma anjimar zan koma , matar data tunkari mutuwarta saboda ceto rayuwata saina ganta kuma sai naje babu wanda ya isa ya hanani fita , Dikko daga kan Sultana wurin Jiddah wayarshi ta sauka me yasa wata ta kwana gidanshi bada izininshi ba ? Ko an faɗa mata gidanshi gidan gwamnati ne ? Ita har ta isa ta daki ƙirji tayi iskancin data ga dama ba tare da saninshi ba ? Shike aurenta ko itace take aurenshi ne ? Daga yau idan Mardiyya ta sake kwanar mishi a gida sai yaci ubanta sakarar banza wacce ƙwalwata ke ƙallon gusin..... Jiddah tace Yaya ni kwalwata ke kallon gusin ? Dikko yace to akwai wacce nake magana da ita bayan ke ? Aike inama tantama anya kina da ƙwalwa a kanki ? Sakarar banza saboda wannan surutun banzar naki sai kin wahalar da rayuwarki , cikin kuka tace Yaya baki zakaimin ? Ba baki zanyi miki ba Jiddah surutunki yayi yawa gaki baki da sirri ko kaɗan , tou wani abu akace maka nayi ? Wallahi babu abinda akace kinyi sanin hali ne yafi sanin kama surutunki na sani zama ɗaya sai kin warwarewa mutum komai na rayuwarki anyi mutum babu sirri ina ma amfanin halinki da Allah , Wannan Mardiyya da kike gani sai tayi cinikin ki a gaban idonki ta sayar dake , Yaya wani abu tace wai ? Babu abinda tace nasan ke ba'a sakaki a kwana ba kinyi surutu kamar kamun hauka bare ita kuma mai wayau ta sakaki a lungu taita dukan cikinki kina bata labari , tunda Umar yacemin a gidan ta kwana nasan yau kin kwana ɗimi { surutu } wai anyi mace babu aji haba Jiddah wasu matan kamar ka biya kuɗi ka siya magana a wurinsu ni gaskiya bana san mace ba aji ki kama kanki tun kafin inyo miki abiyar zama.... Kishiya zakamin ? Tabbas wallahi aure zanyi kuma dana dawo zanyi shi in Allah ya yadda , kam bala'en nan ni zaka ma kishi ? Dikko yace tabbas kuma babu gudu babu ja da baya aure fa babu fashi ko a yadda ko kar a yadda idan dai har banyi auren nan ba tou ki tabbata mutuwa nayi......... Yana faɗin haka ya kashe wayarshi. Dikko yana kashe waya Jiddah ta kira Momy ta fashe da kuka , cikin tashin hankali Momy tace me akayi miki ne ? Momy wai Yaya aure zai ƙara , Momy tace ƙarya yakeyi babu auren da zaiyi , cikin kuka Jiddah tace wallahi da gaske yake duk abinda yayi rantsuwa akanshi ba wasa yake ba Momy tabbas aure zaiyi , Momy tace wace ce zai aura ? Jiddah tace Momy ban sani ba kuma yace min wai kar Mardiyya ta sake kwanar mishi a gida bakiji zagin da yayi min ba har cemin yayi ƙwalta tana kallon gusin , Momy tace gidan banza gidan wofi gareshi har kema baki sake kwana ki tattaro kayanki ki taho , Jiddah tace Momy cewa zaiyi nayi yaji kuma kinsan bazai ce in dawo ba , Momy tace ki barshi dan ubanshi zai dawo ya sami ki taho , kamar dai Jiddah bata yadda ba amma ƙarshe dai ta haƙura Momy ta turo driver ya ɗauketa su Jiddah an sauka a gidan gwamnati. Misalin ƙarfe 12:30pm na fito harabar gidanmu zanyi aike , Ashiru na gani shida wasu irin tiƙa²n mutane harda waɗanda suka zauna dani a goruba lokacin da Dikko ya saceni a wurin bikin birthday ina , shima ɗayan na sansa Dikko yaje dashi anguwarmu ranar daya takamin mage wanda nace jikinshi har wani mai² yake saboda girmanshi kamar an shafa mishi mai , ashe Ashiru ɗan ƙarami ne ma akansu , nafa firgita da ganinsu amma saina basar na kira mai ba filawowi ruwa na aikeshi , zan juya naji suna cewa aiko mun kamashi ba'a nan zamu dakeshi ba tafiya zamuyi da ɗan iska , ji nai cikina ya juya ƙulululu irin kukan nan da yakeyi idan yaji tashin hankali , da sauri na fara tafiya saboda wallahi basu da kyan gani naji wani yana cewa kun gane karmu daki Yazeed muyi masa kashedi idan mukayi saurin dukanshi mai gida zaice mun daki abokinshi kawai dai mu fara worner shi idan baiji ba sai muci uwarshi kawai. Da gudu na shiga cikin palo har ina faɗuwa da sauri na miƙe nayi cikin ɗakina a tsorace , Kaka ma kanta da take zaune tamin magana bana jinta , ina shiga ɗaki wayata na ɗauka na fara kiran Yazeed babu ɓata lokaci ya ɗauka babu ko gaisuwa nace masa su Ashiru suna nemanka zasu dakeka fa , murmushi Yazeed yayi tare da cewa ki kira DK ki faɗa masa cewa yaranshi su fita hanyarki dake dani idan ba haka ba zaku samu matsala keda shi , nace ai nima yace zai dakeni ne idan ya dawo , Yazeed yace ba komai faɗa masa haka kawai , ba tare da tunanin komai ba na katse kiran Yazeed na kira Dikko. Shima babu wani ɓata lokaci ya ɗauka nace Dikko ya ansa da na'am yaja na'am in a cikin murya irin ta sakakkin "ya "ya nace kaga yaranka su fita hanyar ni da Yazeed idan ba haka ba dani dakai zamu samu matsala , murmushi Dikko yayi yace wannan ba tunaninki bane yarinya ashe har yanzu kina wasa da mahaukaci to ki sani da abinda zakiyi da kanki da wanda aka sakaki kiyi komai naki na sani kuma ni halinki da rayuwarki sai in rubuta littafi akanki , Cikin ɗaga murya nace to me yasa suke binshi me yayi musu ne ? Murmushi mai sauti Dikko yayi tare da cewa bana cikin yanayin faɗa yanzu amma ki bari idan ina fushi saiki taɓoni ko kuma ki bari idan na riƙeki ina baki wahala ki tambayeni anan ne zan baki ansar tambayar da kikemin zararra kawai dake , kaine zararre , ai ni dama tuni na zare , Dikko yanzu me Yazeed yayi ma yaranka ne ? Duk abar maganar zare². An mata yarana kenan wanda nakan ɓata musu a ko wane lokaci kuma sukeyin haƙuri dani , na saka baƙin ciki a zukantasu yayin da su sukeyin farin ciki , kuma suyi haƙuri basa zuciya dani , kinga su kansu suna kishina tun kafin ni inyi kishin kaina , suna jin baƙin ciki tun kafin ni inji baƙin ciki , suna tayani kishinki tun kafin ni nayi kishin naki , sunji baƙin ciki na samun kishiya a soyayyarki tun kafin ni mai san naki nayi kishin rabamin zuciyarki da kikayi gida biyu , ni ɗaya nake ko a gidanmu kuma duk zuciyar macen dana shiga bana gogewa har abadan duniya amma ke har kina tunanin jinjina soyayya ta data wani Yazeed , ni zaki ma soyayyata kishiya ko ? Hmmm idan har na barki kin huta dai² da saƙon ɗaya da tunanina kice ba Dikko nake ba. Yana faɗin haka ya ajiye wayarshi. Cikin tashin hankali na sake kiran Yazeed bayan ya ɗauka na faɗa masa Dikko yace bazaiyi haƙuri ba , Yazeed yace sake kiranshi kice masa yayi haƙuri yaranshi su fita hanyar Yazeed , nace tou , wayar Dikko na sake kira amma sai bai ɗauka ba , nan fa na samu aikinyi , Har aka kawomin saƙon dana aika a siyomin ban daina kiran Dikko ba , ganin bazai ɗauka ba yasa na kunna data ta yana online kuwa kenan yaga kirana ɗauka ne bazaiyi ba , voice note nayi masa cewa Dikko kana ganin kirana bazaka ɗauka ba , ya gani kuma na tabbata yaji amma bai bani ansa ba , Whatsapp video call na kirashi ya ɗauka yana kwance saman gado yana cin cingom cikin salo mai ɗaukar hankali , murmushi nayi dana ga fuskar Dikko a kusa dani nace mutumina kaine a kwance haka ? Wani irin kallo yayi min amma baiyi magana ba , cikin sakin layi nace Dikko kai kana da kyau sosai wallahi kana burgeni matuƙa , har yanzu idonshi akaina yake amma baiyi magana ba yana kallona cikin wani irin yanayi , Dikko kayi haƙuri don Allah tsoki yayi tare da cewa ai kina so dai yarana su fita harkar Yazeed ko ? Nayi shiru , tunda kina san Yazeed na bar miki shi kuma insha Allah duk wani wanda ke ƙasana bazasu sake rabaki da Yazeed ba , na haƙura dake An mata na fita harkarki kuma ki goge number na a wayarki nima zan goge naki kowa yaje yayi sabuwar rayuwa , Dan kinga ina sanki zakiyi tamin wasa da rayuwa to na daina sanki ko diamond ce ke na haƙura dake bana so aje akaima Yazeed , yana faɗin haka ya kashe , wani irin tashin hankali naji kamar an tsinkemin jijiyoyin lumfashina , musulta irin tashin hankalin da naji akan kalaman Dikko bana iyawa , cikin kuka na sake kiran wayar Dikko amma yaƙi ɗauka wayyo Allahna kardai mutumina da gaske yake ? Murmushi Dikko yayi da yaga Sultana tana ta kiranshi yace haba An mata ai tuni kin faɗa tarkona na , tuni na dana saka miki maitata a zuciyarki , murmushin mugunta yayi cewa bari in barki saina gasaki dayi miki rowar muryata nima yanzu zan ɗana irin iskancin da kikemin idan kikaji azaba dana dawo ke da kanki zakiy ta haɗani da Allah muyi aure , "Yar yarinya kawai dake kin maidani abokin wasanki , da girmana kin maidani kamar ƙaramin yaro in biye miki inta sakin layi ko girmana baki gani haba An matana so hauka ne .....? Tun wurin 12 da wani abu nake kiran Dikko bai ɗauka ba har zuwa yanzu wurin 3 na kasa daina kiranshi kuma ko tausayina Dikko bayaji yaƙi ya ɗauka wayana ni kuma na kasa haƙura , Saida aka kira la'asar na ajiye wayar naje nayi wanka nayi sallah na shirya na fita daga gidan na nufi sabon layi..... 25/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 64 Lokacin dana isa sabon layi ban samu ganin matar da tacemin na dawo anjima ba , dana tambayi wacce ke bani ansar inda matar taje cemin tayi wai sun tafi wurin taron siyasa , kuɗi na fiddo a jakata saida na shaƙa mata su dai² hancinta na maidasu a jakata nace zan tafi ni suna na Sultana , kuma ni ɗiyar Binna ce ai kin san Binna ba.....? Zaro ido tayi tare da cewa Binna....? Murmushi nayi da gefen bakina tare da shanye idona na dama nace Eh nice na gajeshi masu iya magana nacewa kyan ɗa ya gaji ubanshi na gaji Binna ban gaji uwata ba na ƙarasa maganar ina yatsina fuska , jinjina kai tayi tare da sake kallona ƙasa da sama tace Binna ? Nace tabbas. Dariya matar tayi ta zira hannunta cikin breziya ta fiddo sigari ta bata wuta , saida taja ta sosai ta miƙomin , ansa nayi ina murmushi na riƙeta a hannuna , ita kuma taci gaba da cewa lallai ai Binna namu ne , bara a kawo miki kofinshi kiyi mishi nayau tana faɗin haka tayi gaba , babu jimawa ta dawo riƙe da ƙofi a hannunta ta miƙomin cewa wannan da kike gani duk daren duniya Binna goma yake sha , kuma yabar wasiyya cewa duk daren duniya saboda san da yake ma giya koya mutu a zubar da kofin giya goma a saman ƙasa , ansar kofin nayi na riƙe a hannuna na ƙura mishi ido , hawaye naji ya cikamin ido bansan lokacin da suka fara gangarowa ba , ɗaga kofin nayi na kai bakina amma kafin in samu damar shanshi an ɓareshi , da sauri na ɗago kaina dan inga waye amma babu kowa kuma babu matar data bani kofin , Da sauri na kalli hannuna saboda sigarin hannuna ta cinye wutar har ta taɓomin hannu , yadawa nayi na duba mutanen dake zaune suna wasan lido nace ina matar dake tsaye a gabana da Allah , wasu ne suka ɗauketa a mota , wannan shine ansar da suka bani kawai , da sauri na rufe idona na girgiza kaina gefe da gefe na kalla ba kowa dan haka na juya na tare napep saboda wurin bisa titi ne na nufi gidan cikin ɗimuwa wato har yanzu akwai sauran masu bibiyar min rayuwata ina da sauran lale. Kai...............Wayyo Allahna saina kasheta , shine kalmar da Dikko ke faɗa yayin da yaga hotunan "Yar matanshi ta riƙe sigari , watsi ya farayi da kaya yau sai ya koma nigeria , da sauri Dady ya dafe dai² zuciyar shi ya umarci a riƙe Dikko amma duk wanda yazo sai Dikko ya duƙe ya naɗa mishi hannu so ɗaya saiya koma da baya ya kwanta , wani irin gurnani yayi tare dayi ma Dady wani irin kallo kamar zaki ya ritsa mutum a dokar daji , cike da fargaba Dady yace ku kamamin shi , wani irin ihu Dikko yayi tare da halbin wanda yazo gaba shima ya kwanta , idon Dady cike da hawaye yace ku kwantar dashi mana gaba ɗayanku kuje , kai......... Saina kashe ku ya fara wannan zabure²n nashi taron mutane da yawa Dikko ya haukace gaba ɗaya yana saina kasheta.... Dakel aka kaishi ƙasa yana wai... Wai Allahna .... Wayyo idonshi yana zubar da hawaye yake kallon Dady duk wanda ke wurin saida Dikko ya bashi tausayi har a ƙasa harbe² yake yana An mata ni zaki tonawa asiri me yasa kike min haka saina mutu tunda baki san Dikko saina mutu wallahi , shaƙe wuyanshi ya farayi tunda bazan kasheta ba ni zan mutu kawai Dady mutuwa zanyi An matana take taɓa kofin... Sai kuma yayi ihu sosai tare da watse mutane dasu ka danne shi , Dady yace karku barshi ya miƙe danne Dikko akeyi amma abun yana nema ya gagara , Da ƙarfi ya miƙe ya watsar dasu ƙasa , Dady yace ku rufamin asiri ku maidashi ƙasa , ƙara kama Dikko akayi dakel aka sake kaishi ƙasa a karo na biyu cikin kuka yace idan har na mutu rayuwarki ta zama walawala duk wanda kike tunanin zaiso ki da gaske ƙarya ne nine nake sanki da gaskiya , nine kaɗai zan riƙeki da amana nine kaɗai bazan cuta rayuwarki ba haba "Yar matana karki kuskura ki bari Dikko ya fita a hannunki , birkicewa yayi yana kallon sama yace idan kina ganin munayin faɗa wannan tafiyar babu dawowa har abadan abada idan na tafi babu waiwaye ki natsu mana An mata gaki "yar yarinya ƙarama kina so ki ɓata rayuwarki wai meke damunki da Allah , surutunshi yayi yawa Dady yasa aka zuba mishi maganinshi a baki lokaci guda ya ɗauke ya tafi baccin wucin gadi... Ganin har yanzu Hafsa bata dawo ba yasa Dady ya shaƙi wuyan Bello yace ka tabbata idan har ɗiyata ta mutu wallahi saina kashe ka har lahira ya ƙarasa maganar yana tura Bello baya , murmushi Bello yayi tare da matsowa shima ya shaƙi wuyan Dady yace ni kuma idan har wannan tsinaninyar yarinyar ta rayu sai na tona maka asiri kuma saina kasheta dan uban daya ci uwarka.... Kokowa ta rikice tsakanin Bello da Dady yayin da Dady ke cewa kai har ka isa kaci kwalar rigata kai waye ? Nan fa Dady ya ƙwance ya fara aman turanci yana zage mashayin giya ɗan wasan caca Bello ba'asan komai ba irin kan Sultana ne haka nan akai ta wanka ana zuwa makaranta , empty brain. Rabasu akayi dakel Dady yana kiran stupid , Bello yace kai kaima stupid olowa ƙwaira dakai shima dan dai ace wani shege ne , Dady ya sake shaƙo wuyan Bello saida yayi mishi lullusar fitar hayyaci sannan yace ina Sultana take dan uwarka ? Dariya Bello yayi hihihihihi kamar mahaukaci da bakinshi daya fashe jini yana binshi yace nima nemanta nakeyi , wani irin mari Dady yayi masa tare da cewa ina Sultana take ne ? Bello yace ai kana da numberta ka kirata mana , ganin Bello zai raina masa hankali yasa yayi waya polisawa suka zo suka tafi da Bello yayin da Bello kema Dady kallon idan na fito sai naga bayanka... Ana tafiya da Bello Dady ya fara kiran wayar Sultana , ni kuma a tsorace na shigo cikin gida gabana sai faɗuwa yakeyi kamar banda lafiya haka naji yanayin jikina suku² da sallama na shiga cikin palon gidan , Kaka tana zaune a palo tayi baƙi gaishesu nayi na wuce har zan shiga ciki Kaka tacemin "yan uwanki ne "ya "yan kawunki ne , murmushin ƙarfin hali nayi cewa sannunsu na wuce ciki da sauri. Ina shiga na fara cire kayana bayan na gama nayi ɗaurin ƙirji dan har yanzu kiran wayar Dady bai daina shigowa ba , saida nayo alwalla na ɗauki wayar Dady cewa barka dai alawar zuciyata , murmushi yayi maicin rai tare da jinjina kanshi yace Hajiyata kina ta ina haka.....? Cike da iskanci nace ka ganni ina nan hotel tun shekaran jiya wani Alhaji ya tafi dani ana wasan danbe dani... Shiru Dady yayi ni kuma naci gaba da cewa ko zaka zo ayi dakai ne kaga wata yazo ƙarshe , ciki² yace ummm nace tou kayi sauri ka sameni ina nan hanyar shinkafi a cikin fesra hotel ɗaki na 10 , gani nan zuwa , nace kai saurara ba zafin zuwa ba kazo da kuɗi ai zanzo dasu nace mintuna biyar na baka idan ka wuce babu kai a lissafi Dady yace to ina faɗin haka na katse kiranshi na fara kiran wayar Dikko , bai ɗauka ba kaima kayi fushi da yawa haka mutumina Allah ya sawaƙe , ina faɗin haka na ajiye wayar na kabra sallar magrib. Mota Dady ya hau ya bata wuta ya ibi hanyar shinkafi gudu yakeyi sosai yanayi yana kallon agogo cikin ƙanƙanin lokaci ya isa dan bashi da nisa da wurin yana isa ya fara kirana a dai² lokacin dana sallame sallah na ɗauki wayar yace Hajiyata na iso , ina ka iso ? Fesra hotel ! Ina ne kuma Fesra ? Inda kika ce na sameki ? Ni ? Ni nace ka sameni a Fesra Dady ? Ashe manyan mutane ma suna ƙarya kai amma kaji kunya , da ciwo ya jinjina kanshi tare da cewa tou kina ina yanzu ? Ƙasa² da murya nayi cewa zaka ganni ne ko kaima zakayi wasan danben ne.....? Na ƙarasa maganar ina dariyar mugunta , Ey tou yi sauri ka sameni ina nan ƙofar ƙwaya mintuna shidda na baka , Mintuna 6 daga shinkafi zuwa ƙofar ƙwaya ? Idan ka shirya kawai ka taho idan kuma ka ƙoshi in kakkaɓe zani na in rufe abuna inyi gaba mabuƙata da yawa ai , kallon agogo yayi ya hasko tafiyar dake tsakanin shinkafi zuwa ƙofar ƙwaya yace kidai ƙara zuwa mintuna goma , bana jira , Dady yace aiko baki nemi mu haɗu ba Hajiyata , murmushi nayi tare da cewa tou shikenan indai tayin banza wulaƙanci ne albarka ma amsa ce , dariya Dady yayi mai ciwo cewa gani nan zuwa , yana faɗin haka na ajiye wayar banza na ɗauki wayata da nake kiran kowa da kowa da ita. Yazeed na kira har ta shiga ta fito bai ɗauka ba , wai meke faruwa ne haba da Allah , shi wannan sarkin zafin kan baya ɗaukar wayana , Yazeedu kuma me ya faru dashi kardai su Ashiru sun dafe shi ? Aiko idan har sun kamashi ni wallahi basuyi min adalci ba. Haka nan na zauna jigum ina tunanin duniya , gaskiya nima dai wasa² "yar iska ce mai lasisi , tabbas duk wanda ya ganni yasan karuwa ce ni amma har yanzu dai karuwanci bai huda jikina ba dan kunsan akwai karuwar da ka ganta kasan karuwa ce , akwai kuma wacce ko ance maka ita karuwa ce sai kace ƙarya ne nima dai yanayi na kawai zaka kalla farkon kallo zaka kirani karuwa amma sanin fili akayi min sirrin ɓoye kuma ni marowaciya ce ga mazan bariki , nayi danfara wa mazaje da dama na feshe na kwashe kuɗi na gudu , na ɗauki tsiraicin maza nayi amfani dashi wurin ansar kuɗaɗe a hannun su , naɗanyi dai suna kaɗan kasancewar shagon da muka so buɗewa na kafa ƙungiyar kwarata a halin yanzu Amisty ta fini suna a harkar bariki ni kuma nayi suna sanadin tarayyata da Dikko dan mutane gani sukeyi ni karuwarshi ce ! Hmmm nifa na buɗewa Amisty hanyar zaman "yanci , ta daina zaman karuwanci a gidansu ta dawo zama tare dani har tayi gidan kanta amma wai ni zatafi suna a harkar bariki , kiran wayar Dady ne ya dawo dani daga duniyar tunanin dana lula , ina ɗauka yace Hajiyata nazo ƙofar ƙwayar , tsoki nayi tare da cewa wai kai Dady wace irin kwalwa gare ka ne ? Ba tare dana jira ya bani ansa ba naci gaba da cewa me kuma ya kaika ƙofar ƙwaya kai da nace maka ka sameni ƙofar ƙaura ? Jinjina kai Dady yayi cikin tsananin ɓacin rai tare da danne zuciyarshi yace Hajiyata ai tsakanin nan da ƙofar ƙaura na kusa zuwa ma , Tou cewa nayi ka taho ? Ai nasan cewa zakiyi mu haɗu wurin shi yasa na taho yanzu haka na iso , Dady kenan nifa ina filin jirgi yanzu haka , me kikaje yi a filin jirgi ? Hoto naje ɗauka yanzu mun gama kawai mu haɗu Qerau , ina faɗin haka na tsinke wayata nayi kwanciyata. Saida yaje airport sannan ya nufi Qerau ɗan wahalar , duk inda ya duba bai ga Sultana ba , haka ya haƙura ya tafi station yasa akayi Bello jakin duka yace duk a ɓare mishi haƙoran bakin Bello na gaba idan dai har bai faɗa masa inda Sultana take ba , Bello yace shi wallahi baisan inda Sultana take ba , Dady yace suyi ta dukanshi harsai yaje maƙabarta ya dawo... Haka akai ta dukan Bello harsai daya suma kuma basu daina dukanshi ba har ya farfaɗowa , Dady yace ka tuno inda take ? Cikin kuka Bello yace a , a , Dady yace kuci gaba saiya koma ya ɗauko kwalwar inda ya ajiyeta , haka akayi ta ma Bello gwalagwala yana zuwa duniyar suma da duka kuma yana farfaɗowa saboda azabar duka... Su Ashiru sune suka ɗauki matar data bawa Sultana kofin giya , sune suka tafi da ita bayan sunci ubanta sosai suka ɗauki bayanai a wurinta kamar yadda da suka faɗawa Dikko ya umarcesu , bayan sun gama kuma ba sakinta sukayi ba umarni daga Dikko aka ajiyeta a wurin daya basu umarni , bayan sun gama ne suka tura mishi hotunan da sukayi ma Sultana wanda shine yace duk inda suka ganta da abinda takeyi su ɗauko mishi ita su tura mishi , Su Jiddah an samu abinda ake so ana wurin Momy kuma sai ƙara tunzura Momy takeyi yayin da ita kuma Momyn take ta daɗa hawa kamar kashin safe , Dady kuwa bayan ƙura ta lafa ya fara doke²n waya cewa a ƙara saka shi da addu'a lamarin Dikko fa gaba yakeyi , yanzu banda furunci zai kashe , shi da kanshi yake cewa zai kashe kanshi kuma yana shaƙe wuyanshi , itama Momy haka ya faɗa mata itama dai tasha kuka kamar zata mutu , kuma haka itama tayi ta doke²n waya tana faɗawa "ya "yanta mata Yayun Dikko su biyu ne wanda suke ma'auri tace su saka ɗan uwansu a addu'a. Bayan Dady ya gama yake tambayar Dikko meya ɓata mishi rai ? Cikin kuka Dikko ya rungume Dady yace Dady nidai ka yafemin badan halina ba kayi haƙuri kabarni aure zanyi idan kana san farin ciki na da kwanciyar hankali na , Dady yace haba Babana kana ɗan yaronka zaka fara taretaren mata ? Nidai Dady a haka dan Allah , Dady yace Babana kayi haƙuri kar kayi aure yanzu lalurar mata biyu kanka baya ɗauka gaka baka da lafiya ka bari ka samu sauƙi mana , Ɗagowa yayi ya kalli Dady cewa amma ka manta fa lokacin Sadiyya kafin ta rasu aka fara maganar auren Jiddah nidai Dady gaskiya aure zanyi kuma saura wata ɗaya kawai na faɗa maka dan in fita haƙƙinka , Dady yace ba umarni na kake bi ba ? Kayi min addu'a dan Allah Dady kuma bana so ka faɗawa Momy tace saidai in mutu bazanyi kishiya wa Jiddah ba , Shiru Dady yayi yana kallon ɗanshi daya ɗauki soyayyar duniya ya tattara akanshi , kyakkyawan murmushi Dikko yayi ma Dady tare da ciro cingom a aljihun wandon shi ya cireshi a takardarshi ya rabashi gida biyu yasa rabi a bakinshi rabi a bakin Dady yana ma mahaifinshi kallo mai tattare da tsantsar ƙauna yace ai nasan ka yadda Dady shi yasa nake alfahari dake ya ƙarasa maganar yana ƙara rumgume shi , murmushi Dady yayi cikin yanayin damuwa ya fara tauna cingom in da Dikko yasa mishi a bakinshi yace ina bayanka Babana , tafawa Dikko yayi da duka hannayen shi biyu yace na gode Dady. Shi kuma Dady shiru yayi amma bai tambayi Dikko dalilinshi na abinda yasa yake so ya ƙara aure ba , yadai ansa kuma har a zuciyarshi ya yadda amma dake bayahude ne Dadyn na bugawa a jarida babu abinda ya dameshi da wani auren Dikko kawai dai yana ganin wani ra'ayi ne nashi na daban tunda bai faɗa ba shima kuma bazai tambayeshi dalili ba , kuma bazai hana Dikkon yayi aure ba , dan sanin da yayi ma Dikko a baya babu abinda yake ɓoye mishi kamar aboki da aboki haka suke faɗawa juna damuwar junansu sakamakon Dikko yanzu daya fara zurfin ciki , ajiyar zuciya Dady ya sauke yabi Dikko da kallo shi baya gajiya da kallon Dikko saboda soyayyar da yake mishi , Bayan sati 4, Abubuwa da dama sun faru , kuma duk cikin kwanakin nan babu ranar da bana fita kullum rana saina fita kuma kullum sai anyi hotuna an turawa Dikko , kuma ni ina kiranshi kullum baya ɗaukar waya , nadaiji babu daɗi kuma inayi tunani sosai nakan tuno masu abubu sai inyi murmushi. Inna har yanzu basu dawo ba , tana can ita da mijinta sunma bar Dubai sun ƙara gaba abunsu , kullum sai sunyi waya da kaka ni kuma sai lokaci² nake kiiranta mu gaisa dan idan ban kirata ba bata kira tana daiyin kara haka ta fulani saidai ta kira mahaifiyarta kuma idan ta kira bata cewa ina Sultana , Al ' Ameen ya samu sauƙi sosai an sallameshi daga asibiti ya dawo gidan gwamnati da ƙudurika da dama a zuciyarshi , kuma har yanzu Mardiyya tana nan bata tafi ba , Jiddah ma tana wurin Momy har yanzu bata koma gidanta ba , kuma tuni Umar ya biga waya ya faɗawa Dikko Jiddah tayo yaji tana nan gidan gwamnati , Hafsa ma ta samu sauƙi babu laifi an sallamota amma dake kanta irin na Sultana ne ta gagara gane yadda abun ya faru kwata² , Bello kuwa har yanzu yana can ana gana mishi azaba yanki² , Dady kuwa ido rufe neman Sultana yakeyi kuma har gidansu taje wurin mahaifiyar Dady wato kakarsu Hafsa , Yau tunda gari ya waye da faɗuwar gaba na tashi , idan abu na ɗauka saidai ya kubcemin ya faɗi ƙasa , ko magana akayi sai in firgita , da sauri na fito wanka zanje wurin Yazeed ne dan ya daina zuwa gidanmu saidai muyi waya kuma duk yawan kwanakin nan bamu haɗu ba dan shima yaje tafiya jiya ya dawo shine yau yayi min waya cewa na sameshi company , Saida nayi sallah isha'e na fara shiri , Yazeed sai kirana yakeyi kila na ɓata mishi lokaci , ɗauka nayi yacemin kin taho ne ? Nace a , a yace ni nabar company yanzu ina tafiya zuwa G R A mu haɗu dake a wurin , idan kin hau napep wurin wanki motoci na cikin G R A za'a ajiyeki , nace sai nazo ina faɗin haka na ajiye waya naci gaba da shiri , Ina gamawa na fice babu wanda ma yaga fita ta a gidan ina fitowa na samu napep na faɗa mishi inda zanje mukayi ciniki na faɗa yaja muka tafi , Da sauri ya sauko daga saman gado jin wayarshi tana ringing kuma ya ajiyeta nesa dashi , kafin ya isa inda wayar yake harta tsinke yana isa wurin a dai² lokacin da wani kiran ya sake shigowa , ɗauka yayi tare da kara wayar a kunnenshi mai gida tana nan cikin G R A , baiyi magana ba ya tsinke wayar , makulin mota ya ɗauka ya fita daga ɗakin cikin tsananin ɓacin rai.... Hajiya nifa na kasa gane inda zan ajiyeki wurin wanki motocin biyu ne ke baki san sunan companyn ba ne ? Kiran Yazeed nayi cewa nifa ban gane ba gashi ina tare da mai napep muna ta yawo , cewa yayi in ba mai napep in waya na bashi ya faɗa mishi inda zai kawoni , Baya muka koma muka sha wata kwana mai napep sai masifa yakemin wai tun farko ban iya kwatance ba , da tuni nace masa majalissar Yazeed ai da baisha wahala ba , banza nayi dashi dan bana cikin yanayin fitina yau gabana faɗuwa yakeyi har yanzu , Mai gida yanzu napep yayi parking da ita a majalisa , kashe waya yayi har yanzu baiyi magana ba , ya tafi wurin kai tsaye zuciyarshi tana ƙara ruruwa da zafin masifa , A gaban wani irin makeken wuri yayi parking an ƙayata wurin da wasu irin fitilu masu ɗan bara'un haske , anyi parking motoci masu zafin bala'e daga waje har cikin wurin da aka zagaye shi da wata irin waya mai kyau amma kana ganin wanda ke waje shima na waje yana ganin na ciki , wurin ya haɗu duk matasa ne zaune a saman fararen kujerun rober wasu da ƙananan ƙofinan nan irin wanda ake shan shayin nan na maza duk shekarunsu bazai wuce kamar su Yazeedu ba , duk wanda ubanshi ya tara wasu manyan kuɗi na tashin hankali gashi ya hallara a wurin. Mai napep na sallama na tun kari wurin kai tsaye , wurin bashi da banbanci da rana kowa yana ganin kowa haka zaka iya gane duk wanda kuka sake haɗuwa a wani wurin daban , can gefe ɗaya kuma ga "yan mata zafafa suma an parkersu sai sheƙi sukeyi dan ubansu gayunsu irin ɗaya babu wacce tafi wata haɗu suma dai cikakkin "yan iska ne kowa tasha karuwanci ta ƙoshi duk "yan yara ² ne sunsha atach sunci bilicing har sunce wayyo Allah sai jin kansu sukeyi , Amma ina shigowa wurin wallahi duk macen dake wurin saida ta shiga taitayinta , gaba ɗaya wurin ya anshi ƙamshina ya fara yawo zuwa cikin ƙoƙofin hanci duk wanda ke wurin , ba mazan ba suma kansu matan na zama abun kallo a wurinsu , wurin Yazeed na nufa amma kafin in ida isa tuni ya shigo a haukace wurin da mota , motocinsu Ashiru a bayan tashi , Gaba ɗaya wurin ya karaɗe da hayani haba DK kowa DK yake faɗa yana magana da turanci , ɗan duniya uban Yazeed zaici amma sai yayi murmushi a dai² lokacin dasu Ashiru suka fito daga cikin motocinsu fuskar kowa babu imani , Da sauri na juya zan fita amma Dikko yace Ashiru riƙemin An mata karka barta ta fita wurin nan , da gudu na wuce Ashiru cikin hayani Dikko yace na rantse da girman Allah idan har ka barta ta fita zakaji ni da ɗaci , tsoro ya kamani a dai² lokacin da Dikko ya taɓa Yazeed amma ba dukanshi yayi ba yanayin dana ganshi na firgita matuƙa , ga Ashiru ya ɗaure fuska kamar bai sanni ba dole na kama kaina na tsaya nabi Dikko da kallo. Yazeed har so nawa nace bana so kana tara mun mata a wurin nan ne wai ? Shima kanshi Yazeed zufa ke zobo mishi kanshi ƙasa ya kasa magana , murmushi Dikko yayi tare da cewa ba abinda zan maka idan har nayi faɗa dakai akan mace ni na zama sokon namiji , salon soyayyata a zuciyarta baya buƙatar dukan abokin takara wurin lashe zuciyarta , gani gaka ga An mata macece ita kuma zuciyarta tana da rauni na baka dama dani dakai kowa yaje yayi fira da ita ta bani lokaci naje kaima ta fitar maka da lokaci kaje na baka nan da wata ɗaya idan har ka samu ƙarɓuwa a zuciyarta na baka ita duniya da lahira amma karka sake fiddota waje , yana faɗin haka ya ciro hula daga saman kanshi irin tashi da kwakwar nan ya goge ma Yazeed zufar dake saman fuskarshi bayan ya goge mishi ya kamo hannunshi ya ɗora mishi hular a hannunshi , Yazeed yabi Dikko da kallo , duk saida yabi abokansu ya gaisa dasu sannan yaja hannuna ya sakani a mota yana cewa muje in baki tsaraba.. Ya faɗi tsaraba yana min kallo mai nuni da kasheki kaɗaine bazanyi ba , zagayawa yayi ya shigo cikin motar ni kuma na fashe da kuka , murmushi yayi tare da cewa baki farin ciki na dawo lafiya ? A dai² lokacin daya fara tafiya da mota , ni kuma naci gaba da kuka yace wallahi ki rufemin baki yayi maganar yana kallon madubi ko su Ashiru shi suka biyo , tsayawa yayi ya sauke gilashi yace Ashiru kuje kawai zamuyi waya , banji abinda Ashirun yace masa ba naji yace a , a barshi kawai amma dai goruba zanje yanzu , Yana faɗin haka ya ɗage gilashin yana cewa An mata kinsan bugun rabani da yaro ? Kuka nakeyi har yanzu banyi magana ba , Dikko yace wallahi yau mai ƙwaceki a hannun majnun { mahaukaci } sai Allah kawai miƙomin wayata inga waye yake kirana , ɗauka nayi na miƙa mishi , Jiddah ya faɗa tare da cewa lafiya ita kuma wannan ? Yayi maganar yana ɗaukar wayar yace inajinki , banji abinda tace ba yace Ey naje zance yana faɗin haka ya ajiye wayar yana cewa wallahi An mata yau na raina miki wayau , aini ko mace ce banga ranar da zanbi namiji ba , Namijin mi Allah na tuba ina mace ? Namiji ma ya biyoni yana so ai sai yaga yanga da kisisina , macen da aka santa da kwarkwasa da ƙwalisa aji da ɗauka kai ke kuma gaki nan sake dan wawanci kin taho kin biyo namiji sakarar banza dake da baki san namijin so ba , wallahi ni da macece ni dana ba maza azaba ko zance namiji yaje wurina dan ubanshi saina daɗe ban fito ba dan yasan yes wannan tasha banban da sauran mata a cikin mata dubu sai yasan ni ɗin ta daban ne , kuma in fito ina isa ina riƙe aji , namiji yayi magana goma ansa ɗaya zan bashi , nidai a tsarina ina mace ko driver bana yadda Yazeed yayi min bare dan ubanshi harya ɗaukar min jakata , ashe hakanan nake tun ƙaho "Yar mata tana da class nan ma ashe zero kin ban kunya kuma kinci baya , saboda Yazeedun banza da wofi kika hau napep ƙarshe ya wulaƙantaki yayi miki masauki inda suke ajiye karuwai nan yace ki sameshi ke kuma wawiyar kika kama hanya kika taho wallahi ji nake kamar in wurgaki waje in take ki da mota ki mutu in huta da takaici , mtsww haba inama amfanin mace ba aji ? Gunguni nayi mishi yace me kika ce ne ? Shiru nayi ban sake magana ɗaure fuska yayi cewa bari haushinki nakeji da yawa wallahi , tsoki nayi cewa to ai sai ka kasheni nayi maganar ina miƙa mishi jikina wani irin mari yayi min wanda yasa na ɗauke lunfashina lokaci guda... 26/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 65 Jin nayi shiru yasa yace ki sake cewa wani abu mana marar kunya da kika raina mutane , ke "yar mitsitsiya dake nan har kin iya masifa da ƙure rai wanda idan nayi zuciya ina iya haɗiye ki ba tare da nasan naci komai a bakina ba wawiya "Yar matan Yazeed dake, Tunda na taho daga inda naje wallahi bana tunanin kowa sai ke , na taho cikin farin ciki ina kyarma inzo in ganki amma kika lalata min lissafi , maimakon ki tareni da farin ciki sai kika tareni da hawaye. Cikin kuka nace ba kawai dai kanajin zalinci kazo ka kamani kana ta dukana babu abinda nayi maka tsabar ƙwarewa da zalinci ai dama ba so na kake ba kullum baka da burin daya wuce kaga kana zalinci na. Haba An mata ke harni zaki faɗa ma bana sanki ? Idan har bana sanki ke har kin isa ki kalli tsabar idona ki zageni ? Na baki tayin soyayya na maimakon kalami mai daɗi sai mummunan sakamako , kicemin mahaukaci kuma ƙarshen ki wulaƙanta ni ki faɗa a gaban yara dake ganin girma na , duk a bana sanki ne kika ɗaga hannu ki zabgagamin mari na gyaleki ? Na rantse da girman Allah da bake ce kika mareni ba idan basai nabi ta kan ko waye da mota na wuce ba Allah ya tsinemin albarka , tou wai taya ma mutum zai kalleni bare kuma har yayi tunanin faɗar mummuna akaina ? Ko bakya so na ko albarkacin darajar wannan bazanci ba ? Yayi maganar yana taɓo gemunshi yaci gaba da cewa ba'a zagin mutumin daya ajiye shi amma ke sam baki da lissafi. Shashshekar kuka nayi ina cewa kana so na kake dukana ? Har so biyu ka dokeni , kaji min ciwo a gefen fuskata ka farfasa min jikina wannan duk soyayya ne ? Ai na faɗa miki kema so kike ki zama kamar doki ko an hauki sai an dokeki har so nawa na faɗa cewa bana san kina fita ai ke sai kin fita ki nunamin kunne ƙashi gareki ai dai yau jikinki zai baki labari... Wayyo Allah dama nasan wallahi ba so na kake ba yauma dukan nawa zakiyi ? Duk duniya zuciyata da kwakwalwata ko Dikko basu sani ba sai An mata , haka wayata ma bata san wani Dikko ba itama kanta An mata ta sani amma Dikko ke amfani da ita , ki ɗauki wayata password ina ki rubuta Dikko wallahi zata ce miki a , a amma kina rubuta An mata saita buɗe miki , Banda hoton komai a wayata sai doki amma zuwanki yasa na zama zararre ki duba ki gani babu hotunan kowa a wayata na mace sai naki , duk inda kika shiga a wayata An mata zaki gani amma wallahi yau mai ƙwaceki a hannuna sai Allah addu'a ɗaya zaki dage kiyi shine Allah yasa har in gama dukanki ina cikin hayyaci na... A dai² lokacin daya shigo kwanar da zata sadashi da gidanshi tunda ya shigo santar ya kwace da gudu na tashin hankali kamar zai tashi sama motar har wani lilo take ya danne horn , gabana sai faɗuwa yakeyi cikina sai juyawa yakeyi hawaye kuma basu daina zubowa ba , koda muka iso har an buɗe get in hancin motarshi ya saka ya raba get in biyu ya sauke gilashin motar cewa kai Amadu zo nan... Da gudu yazo Dikko yace kai buɗe nan baya ka ɗauki wata foodflarks na nan kaje ka samun murfinta , matsawa yayi ya buɗe ya ɗauka yace mai gida ai ba'a siyar da ware² a idan za'a siyar da murfin tou dole da uwar ake siyarwa ba'a rabasu , ta cikin madubi Dikko ya kalleshi yace ni ba abinda ya dameni murfi kawai nake so ka samomin irinshi. A tsorace na kalli Dikko murmushi yayi min tare da ɗaga min gira yana min kallon rainin wayau ya taka motar muka shiga cikin gidan da gudu , gidan an ƙara mishi wani irin girma na tashin hankali an maidashi gidan "yan gayu anyi mishi bene hadaɗɗe gidan ya ginu sosai gwanin burgewa amma ba'a gama aikin ba , ko me yasa yake sha'awar sissiye maƙota yayi gini......? Malam Amadu yace mai gida wallahi ba'a siyar da murfi , da sauri Dikko ya fita daga cikin motar bayan yayi parking ya koma wurin get , Amadu na ganin Dikko ya fito a hayaƙe ya wuce da sauri yabar gidan yana kallon rigima irinta Dikko ya za'ayi wai ya samo murfin wannan abun ne ? Ko a kasuwa ba'asiyar da ware² to kodai mai gida yana so yaɗan sha iska ne da macen daya zo da ita shi yasa ya korashi ? Saida ya kalli kular ya kallo gidan da Dikko ya rufe get in da kanshi ! Cikin tsananin ɓacin rai ya dawo da sauri na fito daga cikin motar faɗuwar gabana ya ƙara tsananta yayin da Dikko ya ɗage but ya ɗauko wata irin zureriyar dorina irin wacce ake bugun dokuna da ita yace wuce muje , cikin fargaba nayi gaba Dikko ya biyo bayana ina tafiya ina waiwayenshi , cikin hayani yace ki kalli gabanki ki daina kallo na ya ƙarasa maganar yana zazzaro min duk iya girman idanuwan shi. Wata irin kyarma na farayi ta tsoro na shiga cikin palon na samu wuri na rakuɓe kamar asirin mayya ya tonu , shima wuri ya samu ya zauna a gajiye tare da cewa zo nan , ƙin tafiya nayi kamar banji shi ba , bakiji ina miki magana ne ? Basarwa nayi na nuna mishi ƙangara da yarinta , cikin hayani yace idan na sake cewa kizo baki zo ba saina tuɓe miki kayan jikinki zan zaneki , Kamar ina iyayin wani abu nace ai sai kazo ka tuɓemin dama tuɓeni kake so kayi shi yasa kazo dani ko ni zaka nuna ma hauka ? Kai kaɗai ne mahaukaci kowa mahaukaci ne ? Naci gaba da zagin Dikko yace dama nan nake so kizo , ajiye dorinar yayi ya cire belt yazo yaci gaba da zabgamin shi kamar yana dukan "yar shi yana dukana yana cewa zaki sake zagina ne ? Cikin kuka naci gaba da zaginshi ina Allah ya isa mugu munafiki azzalimi , Yanayin fushi ya fara zuwa ki daina zagina....? Ya ƙarasa maganar yana rufe idonshi daya rufe ido komai zai iya faruwa , cikin kuka na matsa daga wurin da sauri nace yi haƙuri don Allah kayi haƙuri 🙏🏻 kafin in rufe bakina ya fara zabura cewa saina kashe ki....... Cikin ruɗewa na fara gudu zan fita waje amma kafin in fita har Dikko ya ɗauko wata wayar wuta da aka sauke ƙasa ya wurgota ta naɗoni ya fizgo da ƙarfi na faɗi ƙasa ya jawoni na dawo cikin palon , saina kashe ki tunda kin rainani , dorunar ya ɗauka yaci gaba da dukana zaki sake zagina ko bana nan ? Yaya dan Allah kayi haƙuri zaki sake fita idan nace bana san abu zaki sakeyi ko bana nan ? Wallahi na bari ƙarya kikeyi sai kin sake kawai kasheki zanyi inje in wurgaki a ruwa , Malam Amadu kuma ganin Dikko ya rufe gida ya lura kamar baya hayyacinshi sai yanzu ma ya gane Sultana ce bayan yayi dogon nazari , da sauri ya fiddo wayarshi ya fara kiran Ashiru , da farko Ashiru kamar bazai ɗauka ba dan yasan dama Amadu zai ce masa mai gida yana dukan Sultana ne shi kuma yana so Sultana taji yadda Dikko yake yarinyar bata da mutunci kwata² ga raini ga rashin kunya yauko zataci ubanta tunda ta raina mai gida , har wayar ta tsinke bai ɗauka ba Amadu ya sake kira saida ta kusa tsinkewa Ashiru ya ɗauka yace ya akayi ne ? Amadu yace mai gida ya rufe gida kuma ya aikeni wai na nemo mishi murfin kula kuma kamar yana yanayin fushi yazo da Sultana , Ashiru yasan komai dan haka yace to ka sani ko soyayya sukeyi ne ? Amadu yace duk dai yanayin fushi da farin ciki irinsu ɗaya a wurinshi bana tunanin soyayya da Allah kuzo , Ashiru yace ai kaima namiji ne ka shiga ka bashi haƙuri dan yacemin yau sai saɓa mata kamannu ai ta raina mutane barta taci ƙaniyarta yana faɗin haka ya tsinke kiran... Bayan Ashiru ya ajiye wayar yace kai gaskiya fa za'a iya samun matsala kunsan mai gida matsalarshi da yake duka yana buga mutum da wani abu , itafa ba namiji bace ba duk da bana tunanin zai bata wahala sosai kai ku tashi mu tafi kada rayuwar yarinyar nan ta samu matsala dai , gaba ɗayansu suka fito suka taho goruba cikin motocinsu , Zuwa wannan lokacin ni kuma Dikko tunda ya ɗaga ƙafa zai takamin wuya ya kare in mutu kamar yadda yace na riƙe kafarshi na kalli idonshi cikin kuka nace karka kasheni ina sanka don Allah , murmushi yayi tare da takani da ƙafarshi a hankali yace ƙarya kike , da gaske nake ina sanka wallahi , duƙawa yayi ya ɗagoni daga ƙasa ya rungumeni yace da gaske kina so na An mata ? Cikin kuka na ƙara rungume Dikko kaina kamar zai ɓare saboda ya buga min a bango yayi wasan kura dani ya bani wahala sosai duk jikina ciwo yakeyi kamar jirgin ƙasa yabi takaina ya wuce , kwantawa nayi jikinshi sosai ina kukan wahala. A dai² wannan lokacin da aka fara dukan gida ni kuma daga nan ban sake sanin abinda ake ciki ba , cire Sultana ya farayi daga jikinshi amma ya kasa , An mata tsaya inje inga waye , ina Sultana ta tafi batajin Dikko dakel ya ciro wayarshi daga cikin aljihu saboda cakumar da Sultana tayi mishi Ashiru ya gani yana kiranshi , bai ɗauki wayar ba yace An mata sakarni in buɗo gida , tuni Sultana ta daina motsi dakel Dikko ya ɓanɓareta daga jikinshi ya kwantar da ita ƙasa har yanzu hawaye bai daina fita daga idonta ba amma gaba ɗaya ta tsaya , Fita yayi daga cikin palon yazo ya buɗe gidan , Ashiru ya gani tsaye yace ya akayi ne ? Ashiru yace naji shiru ne nace bara inzo inga lafiya ? Lafiya lau Dikko ya bashi ansa , Ashiru yace mai gida to ina Sultana take ne ? Tayi bacci , Ashiru yace bacci ? Umm ya bashi ansa da kanshi , ɗan gyarawa Ashiru yayi yace tou amma ai kayi haƙuri ko ? Na daketa amma kaɗan yayi maganar yana yatsina fuskarshi , Ashiru yace mai gida kuma duk da ka daketa sai tayi bacci ? Murmushi Dikko yayi tare da cewa ko ina cikin yanayin fushi nasan abinda nakeyi naso na bata gwalagwala amma sai tayi sauri tace tana so na , wannan kalmar ya ceceta daga azabata kuje kawai zanzo idan na maida ita gida , Ashiru yace bara dai mu jiraka daga ciki , ba tare da Dikko yayi magana ba ya dawo ciki ya bar musu gidan buɗe , Ɗaukar Sultana yayi ya fito rungume da ita a jikinshi ya kaita mota , idan mutum ya suma a wurin faɗa ko duka ba'a fesa mishi ruwa , idan mutum ya suma a ruwa ba'a zuba mishi ruwa saidai a buɗe bakinshi a busa mishi lumfashi idan kuma yasha ruwa sosai sai ake danna ƙirjinshi a hankali , idan kuma mutum ya suma a faɗa ko ana dukanshi firfita ake mishi , idan mutum ya suma haka nan babu gaira babu dalili shine ake yayyafa mishi ruwa. A mota Dikko ya riƙe ruwa a bakinshi ya fesawa Sultana tunda ita dai ba lokacin daya doketa ta suma ba tana kwance a jikinshi ta ɗauke , ajiyar zuciya ta sauke ta sauke a wahalce , rufe motar yayi ya zagaya ya shigo ya rufe , ba tare da yayi magana ba ya tada motar muka fita a gidan. A waje yaga Amadu tsaye da kular daya bashi ya samo mishi murfinta , yana ganin fitowar Dikko yayo wurin cewa mai gida ba'a samo ba , ba tare da Dikko ya kalleshi ba yace maidata inda ka ɗaukota , buɗe bayan motar yayi ya ajiye ya rufe mukayi gaba su Ashiru suka rufo mana baya , Har muka isa gida babu wanda yayi ma wani magana , fita nayi daga cikin motar dakel banyi magana ba , har zan wuce yace An mata zo , dawowa nayi banyi magana ba na tsaya , baki gode ba ? Nayi shiru , shigo , komawa nayi cikin motar a wahalce na zauna , rashin godiya ba ɗabi'a mai kyau bane dana kawo ki gida ai sai kicemin kin gode waike baki iya irin ɗan makircin nan na mata ba ? Gaskiya aikin yawa zaimin in koya miki hankali kuma in koya miki zaman takewa na rayuwa ya zama dole ki koyi kissar zama dani danni bazanyi haƙuri dake ba ke ya zamar miki dole kiyi haƙuri tunda nine samanki fita ki ban wuri , Ƙoƙarin fita na farayi yace kuma tafiyar zakiyi da gaske ? Komawa nayi na zauna , kwantar da murya yayi sosai yace kin yafemin ? Da kaina na bashi ansa Eh , zaki aureni aiko ? Shiru nayi ina nazari , yaci gaba da cewa insha Allah ƙarshe watan nan zamuyi aure kuma idan munyi aure bazan miki ko kallon banza saidai ki anshi hukuncin ki a gado , wannan dukan insha Allah shine na ƙarshe bazan sake ba abinda yasa ma na dakeki nayi rantsuwa so adadin da bazan iya gane ko so nawa na rantse ba, ina sanki har abadan duniya bazan taɓa goge ki a zuciyata ba , kuma ai kema kina so na ko ? Yanzu ma da kaina na bashi ansa Eh , ngode zanzo da safe insha Allah kije , fita nayi ina masa godiya kamar yadda yace na wuce , Cike da tausayi Dikko yabi Sultana da kallo a bayyane yace duk wannan ɗa'ar wallahi ta banza ce bazata bar abinda take ba , motarshi yaja ya fita daga cikin gidan yana mai ƙarajin soyayyar An mata a zuciyarshi. Tsaye nayi a gaban madubi bayan na fito daga wanka ina kallon yadda Dikko ya farfasamin jiki sahun bulala babu inda bai fito ba , a fuskata kuma har yanzu akwai sahun marin da yayi min , murmushin ƙarfin hali nayi tare da cewa saidai ka kasheni wallahi bazan daina fita ba idan har baza ka gaji ba nima bazan gaji ba. Washe gari da wani irin masifar zazzaɓi na tashi ko sallah asuba kasawa nayi ina kwance a gado na rasa abinda yakemin daɗi har 11:15am , ga gidan namu yau cike yake baƙi "ya "ya da jikoki sai hayani sukeyi ɗan uwan Inna zai dawo daga tafiya shi yasa suka taho tararshi , dan abinda na fahimta shine gaba ɗayan ragamar su bana tunanin akwai wani mai kuɗi idan bashi ba , Murmushin ƙarfin hali nayi yayin da naji murya wata mata akan ita babu yadda za'ayi a cuci rayuwata a gauraya mata zuri'a da jinin Aliyu , sunan Inna ta faɗa tana ci gaba da cewa har sukayi aurensu suka gama ni ban taɓa zuwa ko anguwar daya zauna ba bare nayi tunanin taka ƙofar gidanshi , ɗan iska mashayin banza mashayin wofi duk ma wanda yasan kanshi taya za'ayi ya bari a gauraya mishi zuri'a da gurɓataccen ahali. Maganar Kaka naji cikin rawar murya tana cewa ai hannunka dai baya ruɓewa ka cireshi ka yar ko kina tunanin asalin ɗanki yafi ita Maryam ne ? Cikin bala'e tace nidai babu wanda zai haɗamin ɗa aure da wannan yarinyar wallahi , yarinya "yar iska jahilar banza jahilar wofi , sai cin mutunci takeyi wa Babana , abun yamin ciwo amma banda yadda zanyi , Ci gaba sukayi da caccar Babana suna gulmarshi suka tado da tarihin auren Inna ai saboda baƙar kafiyarta taje ta aureshi ta zaɓi namiji tabar iyayenta gashi yanzu taje ta haifo ɗiya ɗaya kwantilkwal ta rasa ubanda zai aure ta , ai tasan a zuri'armu auren zuminci kowa keyi jakkar banza taje ta rasa namijin da zata aura sai ɗan caca , shima ɗayan marar zuciyar dake sakarai ne aka sakota har ya dawo ya aureta , wato mijin da Inna take aure yanzu ko ? Kaka tace to ina za'a kai rabon Maryam ? Cikin ɗaga murya tace rabon wahala ? Hajiya ku hausawa wani abune daku wai sai kuzo kuyi abu idan ya samu damuwa wai sai ku riƙa dangana shi da rabo ne sai kaji mutum na cewa wai rabo ko na abincine sai kaje kaci ka dawo babu wani maganar rabo tsabar kafiyace saboda haka ai itama ɗiyarta ta tana da ahalin Babanta taje can suyi auren zumincisu su haifo masu bakin hali "yan caca karuwan banza. Ikon Allah wai waye ma yace musu auren "ya "yan nasu zanyi ? Aikin banza anba makaho kyautar ido yace banso wari yake dan yasan baya samu ne nima bana san "ya "yanku kuje can kuji dasu nayi maganar a dai² lokacin dana sauko daga saman gado ina tunanin wato ita Inna auren Babana tayi "yan uwanta basa so ? Toilet na shiga dakel ina cewa mune karuwan banza karuwan wofi.....? Ku fiddomin shi Dady ne yake magana a fito mishi da Bello , bayan an fiddoshi Dady yace ina Sultana.....? Bello yace ban san inda take ba , Dady yace wai kunji har yanzu bai tuna inda take ba , tou ku sake markaɗashi muji , saida Bello yasha juyin alalar gero akace ka gano ko tana ina ? A wahalce yace tana tare Dikko , Dady yace wane Dikko ? Cikin nishi yace Dikko U DK , Dady yace kai kana da hankali kuwa ? Idan har ka bari DK yaji ma kana danganta shi da wannan yarinya tou ka sani saiya yanke maka harshe wallahi , ko kana tunani DK zai saurare ta ne ? Bello yace wallahi yana tare da ita , kuma tana zaune a gidanshi na goruba road , Duƙawa Dady yayi kusa da Bello yace ya akayi kasan yana tare da ita bayan shi kowa yasan baya harkar mata , murmushi Bello yayi ya fara cewa. Bincike na ya nunamin cewa tana zaune a gidanshi bayan dogon lokaci dana ɗauka ina nemanta , duk inda naje bata nan nasa an kirata da wayoyi da dama daga mutane daban² amma duk wanda ya kirata saita banbanta inda take , Da naga rainin wayan nata yayi yawa saina duƙufa wurin ganin na samota ko ta halin ya ya ! Nayi binke a wurin ƙanin mahaifinta bayan nayi masa ƙarya cewa zan haɗa kan "ya "yan Binna ne a wuri ɗaya shine yacemin baisan inda suke gaba ɗayansu ba , Sultana dai da tana nan amma wasu ke memanta saita bar wurinshi , Bayan an kwana biyu na sake komawa na tambaye shi ko masu neman nata sun sake dawowa ? Sai yacemin kullum sai sunzo yauma zasu zo ? Ban daɗe da zama ba muna fira da ƙarami sai gasu sun sake dawowa , drivern DK ne a da amma a halin yanzu sun rabu kuma bansan abinda ya rabasu ba , Bayan sun gama bincike² n su naje muka gaisa dashi Al ' Ameen nace masa lafiya kake neman Sultana ? Kai tsaye yace matar Dikko tasa a ɗauko ta kuma a halin yanzu sun gano tana zuwa erudite idan ta tashi tana zuwa islamiyya daga nan sai a nemeta a rasa , Tunda naji tana zuwa Erudite na ɗanawa wurin tarkon , tun safe nake zuwa ina zama a wurin bana ganinta washe gari dana koma sai naga DK ya kawota da kanshi a mota , daya sauketa ya tafi sainabi bayanshi naga ya koma goruba road mai gadin gidanshi shi ya tabbatar min da Sultana tana zama a gidan. Tashin hankali shine abinda Dady ya faɗa tare sa cewa wallahi bata taɓuwa a bayyane dole wurin boka zamu koma shine kaɗai ya isa ya kashe mana ita , domin barin yarinyar nan a raye barazane ga dukiyata domun ita kaɗai tasan sirrin komai idan har yarinyar nan bata mutu ba tabbas miliyan 45 na kuɗin gado zasu fito kuma daga cikin dukiyata zasu fito , manyan gonakai dake funtuwa da wanda suke a cikin gari gidajen zama da duk sauran ƙaddarori kai haka bama zai yuwu ba , Da kanshi ya ɗauko kayan Bello yace saka ka tashi mu tafi idan har ba haka ba dani dakai ƙaryarmu ya ƙare , zuciyar Bello cike da kudurirrika akan Dady domin dukan da yasa akayi mishi ya saka kayanshi suka fita daga cikin station suka nufi wurin boka... Bayan nayi wanka nayi sallah na kira Inna muka gaisa nace Inna yaushe zaki dawo ? Tacemin sai bayan wata biyu , tambayarta nayi cewa ina so nasan ya akayi kika auri Babana ? Basar da maganar tayi cewa Dikko ma ya kirani ɗazu da safe kashe wayar nayi na ƙyaleta ni bata bani ansar tambayata amma ita tana so tayi min nata maganar daya shafata ! Ina tsinke kiran Inna na kira wayar Dikko , yana zaune a palon mahaifiyar shi tana ta zageshi ɗaiɗaya akan wai bayayi ma Jiddah adalci baya cin abincin ta yace zai riƙa ci , kuma tayi maganar Mardiyya , yace taje ta riƙa kwana , wato ana sasanci dai tana ta farfaɗo matsaloli kuma akan Dikko , Dikko dai sai haƙuri yake bawa Momy ya ƙagara ya tashi yaje wurin An mata gashi harta fara kiranshi , hankalin shi yana kan wayarshi yaji Jiddah na faɗawa Momy wai tayi ma Dikko magana baya barinta baccin dare ita yana shiga haƙƙinta da yawa maganganun dai babu daɗin ji , kunya ma ta hana Dikko ya iya ɗago kai gaba ɗaya wutarshi ta ɗauke zufa yaji tana tsiraro mishi cikin jikinshi lallai yau ya saki da lamarin Jiddah miƙewa yayi zai fita itama Momy kamar saukar aradu haka taji maganar cikin karyewar murya tace Dikko jirata ku tafi , Momy ba gida zanje ba yana faɗin haka ya fice daga palon , A kunyance ya shiga mota kamar wani yana kallonshi a zuciyarshi yake cewa tashin kallabi amma kullu yaci amanar koko yanzu idan har Jiddah ta sameni da wannan matsalar ai zamuyi maslaha basai ta tonamin asiri ba , dakel ya ɗauki wayar Sultana cikin damuwa yace An mata da Allah yi haƙuri ganinan ina zuwa wurinki yanzu in Allah ya yadda, Karka zo gidanmu , me yasa ? Sunyi baƙi sosai kuma banajin daɗi ? Me ya sameki ne ? Inayin rashin lafiya , sannu bara dai inzo , a , a , nidai karka zo , wani abu ya faru ? Babu , gidan ne bana so kazo , ni kuma ina so in ganki bari inzo in ɗaukeki mu tafi goruba ? Nace tou , riƙe wayarshi yayi a hannu yana tuƙi a ranshi addu'a yakeyi Allah yasa An mata ita dai bata da wannan jakancin , Dikko yana fita Jiddah tace ni gaskiya Momy kin barshi ya tafi baki mishi magana ba , basarwa Momy tayi kamar bataji ba tace yanzu dai tunda nayi mishi faɗa saiki tattara Al ' Ameen ya maidaki. A hankali na fito daga ɗaki na shigo palo kuma har yanzu basu daina zagin Babana ba , shi kuma wanda suka zo su tara har yanzu bai iso ba , cikin sakin fuska na gaishe su babu wanda ya ansa inda Kaka take zaune na kalla tare da cewa zanje in dawo , Allah ya tsare hanya tayimin na fita dan Dikko yamin waya yazo. A ƙofar gida na sameshi tunda na fito yake kallona cikin yanayin damuwa har na shiga motar , zuciyoyin kowa na ɗauke da damuwa ni ina tunanin yadda zanyi in faɗawa Dikko abinda akayi min akan zagin Babana da aibatashi da akayi , shi kuma yana jinjina yadda zai faɗamin tashi damuwar , Saida muka tafi yace An mata babu gaisuwa ? Yayi maganar yana miƙomin hannunshi , kamar jira nake yayi magana na fashe da kuka , murmushin ƙarfin hali yayi cewa Allah ya baki haƙuri danshi a tunaninshi maganar da yayimin yasa nake kuka , ni kuma abun duniya ya dameni , Har mukaje goruba kuka nakeyi kuma Dikko bai bani haƙuri ba saida nayi kuka na gaji nayi shiru dan dama da yayi parking bamu fita a mota ba , saida na gama kukan yace An mata meke damunki....? Dakel nace masa damuwa ji nake dama in mutu kawai in huta , ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa kiyi haƙuri dukkan tsanani yana tare da sauƙi , ina tare dake kuma in Allah ya yadda damuwa ya ƙare , kuma kiyi haƙuri dan idan ina damuwa ko kinayin taki zan faɗa miki nawa ki koyi riƙe damuwa biyu a cikin zuciya ɗaya , kuma ki koyi farantamin koda kina cikin damuwarki kiyi ƙoƙari ni ki bani farin ciki. Yau idan zan faɗa miki abinda yake damuna ke kanki sai kin tayani jin babu daɗi , juyowa yayi sosai yana kallona yace An mata dan girman Allah ki daina tsokana na muna ɓatawa , ina da lalura ƙatuwa ki tausayimin ki riƙa kwantarmin da hankalina , ki kiyaye ɓatamin rai dan Allah , ki koyi riƙe damuwata kuma ki zama mai yayemin duk wani baƙin ciki idan kika ganin a yanayi mara daɗi , ni a rayuwata gaskiya ina san mace "yar gayu wayayya mai aji , wadda ta iya tarairayar namiji mace mai sirrinta sirrin ta da ɓoyemin nawa sirrin , macen da zata anshi buƙata ta kuma yi haƙuri ta biyamin ita cikin soyayya da kulawa ba tare data gajiya dani ba , ina san mace ma'aboci ƙamshi da tsabta danni gaskiya ban haɗa mace da komai ba ki zama mai kula da tsaftar jikinki domin ko wane lokaci zan iya buƙatarki kuma ina so duk lokacin dana zo ya zama na sameki a shirye dan natsuwa bata samu babu tsafta ba ƙamshi. Har yanzu ke yarinya ce kuma kina magana irin ta yara maganarki tanamin daɗi a haka amma yanayin kallon da kikemin baya ɗaukar hankalina kallon da kikema kowa bada irin kallon nake so ki riƙa kallona ba , dole sai kin zama jajirtacciya ki zama gogaggiya wurin iya sarrafawa da kuma ɗaukemin hankalina ga tunanin kowa saike , Kwantar da kujerar mota yayi ya kwanta saitin zuciyarshi ya taɓa yace kinga ni ba mahaukaci bane ba amma ke kina ganin inayin ɗabi'u irin na mahaukata , murmushi yayi yace ina da lalurar aljannu basu a jikina amma suna tare dani suna shafar jikina yayin da na shiga yanayin fushi , shi yasa idan raina ya ɓaci nakeyi abu kamar mahaukaci yadda kika faɗa , amma ana ta addu'a kuma nima inayi kema ki tayani kinji "Yar matana ? Nace to , ba tare daya kalleni ba yace bara inyi waya a kawo mana abinci muci kisha magani sai in madaiki gida... Wata irin ashariya boka ya babbaka tare dayin wani irin mazurai yana kallon su Bello...... 27/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 66 Daga Bello har Dady duk tsoro ya kamasu kowa a ƙagare yake yaji abinda boka zai faɗa bayan sun kora masa bayani cewa sudai duk yadda za'ayi ya kashe Sultana har yanzu basu samu yarinyar ba , kuma a halin yanzu babu wanda yasan inda take , Dariya boka yayi sosai sannan yace nace bazan iya kasheta ba , Dady yace me yasa ? Boka yace aljannun da nake tsafi dasu basa san mutum mai cika kamsus salawat dole sai yarinyar nan ta daina salloli biyar a rana kaɗai zasu iya kasheta , ba kuma zasu kasheta ba tana cikin jinin al'ada ba dole² sai ta daina sallah sannan kaɗai su iya kasheta. Dady yace zan baka miliyan ɗaya , girgiza kai boka yayi cewa bata ansuwa kuma bata ciwuwa kuje kawai kusan yadda zakuyi ku dakatar da ita daga sallolin dana faɗa idan ta daina ni kuma zansa aje a tsige mata wuya , cikin hayani ya ida maganar cewa ku tashi ku bani wuri...... Daga Dady har Bello da sauri² suka fito daga wurin boka bayan sun fito ne Dady ya kalli Bello yace duk yadda za'ayi ka samo mana yarinyar nan mu kasheta da kanmu idan har ka samota zan baka zunzurutun kuɗi har naira miliyan 20 , murmushi Bello yayi ya kalli Dady a ranshi yace haba ai kafin Sultana ta mutu kaine mutum na farko da zan fara kashewa , yadda ka wulaƙantani a ofishin "yan sanda kana tunanin ka wulaƙanta banza.....? Amma a fili sai yace zan iya Alhaji amma ba zanyi aiki bashi ba , Dady yace dama ka taɓamin aiki a bashi ne ? Bello yace har yanzu ina binka cikon kuɗin shiga rayuwar Binna da nayi tun muna matasa , ina binka kuɗin asirin da nayi masa ya shiga caca ya shiga harkar mata sannan kuma har yanzu kuɗin lalata rayuwar Sultana sisi ma baka bani ba , Dady yace to wannan zan baka dai , Bello yace tou idan ka haɗo kan kuɗaɗen saika kawomin ni kuma a ranar zan shafe lissafin sunan ta a cikin jerin sunayen masu lumfashi a duniya , Dady yace karka damu zuwa ƙarshen satin nan zan baka , haka dai suka shiga mota suna tattaunawa.... Auntyna ga wasu kayan mata na kawo miki suna da kyau sosai kuma zakiji daɗin amfani dasu masu kyau ne jarababbu ne , Mardiyya ce a gaban Jiddah take korata mata bayani akan kayan matan data haɗo take mata bayani cewa kinga wannan sunansa babu sauran kallo , wannan kuma rantse baki da kishiya , Jiddah tace ya rantse baki da kishiya.....? Murmushi Mardiyya tayi cikin kwantar dakai mai nuni da salon yaudara tace ai Aunty idan kikaje sayen maganin sai kinyi rantsuwa baki da kishiya ma sannan a siyar miki dashi , dan idan har kina da kishiya ba'a baki shi dan Yaya DK bazai sake zuwa wurin ta kullum yana tare dake manne kamar hanta da jini , dariya Jiddah tayi ta ɗauki maganin tace Mardiyya ina kika samominshi ne ? Mardiyya tace ni na samo miki shi a Banbaɗawa kuma Aunty da tsada na siyo shi fa , shi kuma babu sauran kallo Yaya baya sake kallon ko wace mace saike domin kece sarauniyar zuciyarshi , dariyar jin daɗi Jiddah tayi cewa kuma kamar kinsan aure zaiyi , wata irin faɗuwar gaba Mardiyya taji lokaci guda taji wutar ganinta ya ɗauke , Jiddah taci gaba da cewa ance ma Momy yana aiki gidanshi na goruba road wai acan zai ajiye matar , gidaje biyar ya siya ya haɗe yana tayi ma amarya gyara , amma Momy tace masa ko waye ya tsaya masa bazaiyi aure ba sai yace mata dama ai ba aure zaiyi ba , kuma da tace masa ance mata yana gyaran gida idan ba aure zaiyi ba me yasa yakeyi ? Shine yace mata masu gidajen ne kawai zasu siyar shine sukace da Allah ya siya shine fa ya siya.......! Amma ni wallahi inaji a jikina Yaya aure zaiyi , gyara zama Mardiyya tayi tare da cewa Aunty taya zaiyi aure bayan ya faɗawa Momy bazaiyi ba ? Murmushi mai ciwo Jiddah tayi sannan tace idan har Yaya yace zaiyi abu to wallahi duk duniya babu wanda ya isa ya dakatar dashi sai yayi , idan kuma yayi rantsuwa akan abu shima ko za'a mutu sai yayi , kaifi ɗaya ne shi kafin ya furta yake da wahala amma da zaran ya furta tofa ko kanshi baya saurara , Mardiyya tace amma me yasa baki faɗawa Momy auren nasa da gaske ne ba ? Jiddah tace Dady tayi ma magana akan ya dakatar da Dikko maganar aure ba zata yadda ayimin kishiya ba , sai Dady yace mata Babana zaiyi aure shine bai faɗamin ba yayi faɗa sosai sai Momy tace itama hasashe ne takeyi , sai Dady yace shirme kenan yama ɗauka gaske ne da yace me yayi ma Babansa aure haka babu shawara ? Cikin kwantar da murya da ladabin munafirci Mardiyya tace to aike ma Aunty ance ki samo sparm inshi kin gagara , Jiddah tace tunda bai bani ba wai ya zanyi ne ? Tayi maganar cikin hayani , ganin haka yasa Mardiyya ta sake kwantar da kanta tace akwai wani magani da zan samo miki a tea zaki zuba mishi ko a lemu amfanin maganin nan shine yana sa sha'awa na masifa kin gane ki bashi shi da safe zaiyi ta nemanki ya kwanta dake saiki ƙi yadda kiyi ta ja masa rai , zai kasa fita ke kuma kinayin abubuwa irin wanda zasu na tayar mishi da hankali kuma ba zaki kwanta dashi ba , zaiyi ta roƙonki idan kikaji nacin nasa yayi yawa sai kice zakiyi amma da sharaɗin zai baki.....? Zai ansa kai tsaye dan yana bisa matakin da bazai iya miki gaddama ba , haka dai sukaci gaba da tattaunawa taron wawayen... Ko da aka kawo abincin a mota mukaci saboda gidan akwai taron ma'aikata sosai sun wasu ta ko ina kowa yana aikin daya shafeshi , bayan mun gama cin abinci ya fita yacemin yana zuwa , nima ta cikin madubi na leƙa na gani an ɗaukeshi a mota sun fita daga gidan , ina ganin ya fita kuma ga mota nima na koma mazaunin matuƙi na fice daga gidan na nufi sabon layi , Lokacin danaje sabon layi ban fita daga cikin mota ba saboda banajin daɗin jikina , ina zauna na kira wata mata nake tambayar matar nan ko ta dawo ? Tacemin ta dawo amma yanzu bata nan taje Qerau , ni da kaina na buƙaci tayi min kwatance ina taje a Ƙerau tacemin gidan Kaka , nace wacece Kaka ? Tacemin baki san Kaka ba ? Nace ban santa ba , tacemin aiko kowa yasan Kaka garin nan , wayarta ta buɗe ta miƙomin bayan ta nunomin hoton Amisty tana cewa wannan itace Kaka , murmushi nayi tare dayi mata godiya na maida mata wayarta bayan na bata kuɗi na tunkari Qerau kai tsaye.... Ina tafiya ina tunanin Amisty har ta zama Kaka bama uwar karuwai ba Kakarsu fa ? Lallai Amity tana da sa'ar rayuwa , babu wani nisa tsakanin sabon layi da Qerau cikin ƙanƙanin lokaci na isa ƙofar gidan Amisty , taron karuwai da "yan daudu duk wata tsinana da bakin iyaye ya kama gata nan tana wurin karuwai burjik , hada wasu daga cikin "yan gidanmu suma dai duk anyi musu sign in karuwanci , Hamida na gani naga Fa'iza naga Farida naga Zainab ni da yake dai ban san sunansu ba amma duk fuskokin "yan gidanmu na gansu sunkai su goma sha wani abu ashsha... Inayin parking na sauke glass Hamida ta fara gani na ta rugo wurina cikin farin ciki tana Sultana kece ? Murmushi nayi kaɗan tare da cewa ya gda ? Lafiya qalau me kukeyi anan naga an taraku ? Kallon taron mutanen tayi sannan ta kalleni tace ƙuru'a akeyi , wace irin ƙuru'a ne ? Gasa za'a tafi ta wasan danbe ? Idona naji ya cika da hawaye na kalli Hamida sosai nace kema hada ke a zuwa gasar ne ? Dariya tayi mai nuni da nama raina ta , murmushin ƙarfin hali nayi cewa uhum ? Tace ai nima ina jagorantar team guda ne bayan anyi ƙuru'a idan mutum yaci sai ayi masa interview idan yaci sai ayi training. Ina ne zakuje gasar ? Na tambayeta , tacemin a gabi za'a gabatar da gasar , bin taron matan nayi da kallo na hango Safiyya yarinyar Baba Ƙarmi itama ta samu isowa Maman Affan da Maman Sadiq kallon Hamida nayi na tambayeta suma wa'ancan hadasu za'aje ne ? Tace suma suna da yaransu , amma ba matan aure bane ba ? Murmushi Hamida tayi cewa ai matan aure ma sunyi kowa yawa a ciki , to me yasa suka shiga harkar danbe bayan suna da mazajen su ? Hamida tace kowa da matsalar data kawoshi kedai bar kowa yayi rayuwarshi , jinjina kaina nayi a lokacin dana hango matar da nake nema dan haka nacema Hamida ta kiramin ita. Tafiya tayi dan kiramin ita yayin da ni kuma nabi taron dandazon mutanen ina kallo , hankalin duk wanda yake wurin akan motar da nake yake amma tunanin kowa dai Dikko ne shi yasa babu wanda yazo , turomin matar tayi ita bata dawo ba , bayan mun gaisa nace mata kin kuwa gane ni ? Murmushi tayi cewa ya kuwa za'ayi na manta Binna ? Nace yawwa , tou wai ya akayi ranar muna tsaye sai kawai kika ɓace abunki ? Cikin damuwa tacemin wallahi yaran Dikko ne suka ɗaukeni sukaje dani sukamin tambayoyi akan abinda na sani game da Binna da rayuwar ahalinshi , abinda yasa ya shiga harkar caca da kuma bincike akan mutuwarshi , yana da wasu abokan hamayya wanda suke takon saƙa nace musu babu , sundai bincike sosai kamar an bajewa uwar san banza dilar gwanjo. Kallonta nayi sosai sannan nace to me yasa baki dawo ba ? Riƙeni sukayi a wurinsu har sai da DK yazo da kanshi , da yazo , shi me yace miki ne ? Shima dai tambayoyi yaimin , a tambayar me ya tambayeki ? Hankalinta yana wurin taron su dan haka tacemin ki bari kawai zamuyi magana daga baya , nace a , a ki saurareni mana , dan Allah kiyi haƙuri ko kuma ki bani number wayarki idan na gama abinda nakeyi zan kiraki , wayata na miƙa mata tare da cewa kisa taki a ciki sai ki kira dan kiga nawa , haka tayi bayan ta gama ta miƙomin ta wuce , Fita nima nayi daga cikin motar ina tunani kafin Dikko ya gama yin bincikenshi insha Allah ni na gama da matsalata , domin ni nasan abokan takon saƙar Babana, babu wanda ya sani saini ɗaya kuma saina kwatarwa kaf ahalina kuɗin gadonsu sannan kuma da hannuna zan ɗauki fansar mutuwarshi , nayi maganar ina kallon tafukan hannaye na , Fitowata daga mota yasa wurin ya ɗauki ihu mutane sukayo wurina suna ta runguma ta , yayin da wasu ke tambayata inda na shige , Amisty Hafsa da duk wanda na sani babu wanda bai rumgumeni ba haka nayi ta gaisawa da mutane cikin riƙe aji da kamewa sosai yayin da wasu kuma suke tambayata inda nake zama , babu wanda naba ansa saidai nayi murmushi kaɗan , A wayance Amisty ta fara gabatarmin da sabbin karuwai da irin jajircewar su a harkar bariki , saidai in jinjina kai , su Nana da A ` i Karima da Saude har Asma'u babu wanda babu a wurin domin naga suma sun ƙwace da yawa , Amisty ta zama gogagga sosai a bariki ta anshi takaddun gaba da degree a wurin karuwanci taci bilicin an saka haƙorin makka ƙasa da sama , anyi hujen hanci duk dai inda kake neman karuwar data ansa sunanta a harkar karuwanci kana ganin Amisty ka tsaya , domin kallonta kanshi shima abin burgewa ne , tadai zama Kakar da gaske. Kallon Hafsa nayi nace ke kuma kinje wurin Dikkon ne ? A sakace tace ni naje wurin daga nan bansan yadda akayi ba , nace kamar ya ? Wasu suka saceni suka kaini wani gida sukayi danbe dani , keda baki san yadda akayi ba ya akayi kika san anyi dambe dake ? Na faɗi maganar ina dafa kafaɗarta muka fara tafiya muna fita daga cikin mutane ina mata tambayoyi kamar haka , su waye suka kamaki ? Ni bansu ba kawai napep yana sauki ni a fesra suka cakumeni , me yasa bakiyi ihu ba ? Nayi ihu dan a kawomin ɗauki daga baya sai suka toshemin bakina , me yasa baki ƙwaci kanki da karfi ba ? Bana iyawa saboda suna da yawa , da suka ɗaukeki ina suka kaiki ne ? A mota suka sakani suka tafi dani wani gida , da sukaje dake ko kinji suna cewa wani abu ? Eh bana iya tunawa dai amma naji mutumin dai yana ta maganganu kuma sunanki yake kira kawai dai na manta abinda yake cewa , Kiyi tunani mai kyau idan har kika tuno ni da kaina zan ɗaukeki a mota na kaiki wurin Dikko kuma tsaya ki gani , wayata na fiddo na fara kiran wayar Dikko , ashe Dikko harya koma gida ya samu bana nan , ƙin ɗaukar wayar yayi na sake kiranshi tuni Dikko ya gune yana jira in dawo ya saukemin rashin mutunci. Ganin Dikko bazai ɗauki wayar ba nace yawwa kin gane ki tuno idan har kikamin gamsashen bayani wallahi sai na kaiki wurin Dikko , murmushin jin daɗi Hafsa tayi cewa , bara in tuno muji , dafe kanta tayi tare da ƙurawa wuri ɗaya ido , tunda taji maganar zan haɗata da Dikko dole nasan zatace wani abu. Bayan wani lokaci tace yawwa , ni kuma nace dana kiraki kince min kina Qerau , nayi maganar niƙaf da hijabi nace Dikko yana jiranki a fesra ki fara tunani tun daga lokacin da kika hau napep. Hafsa tace bayan na sauka a napep na fiddo wayata na fara kiran wayar Dikko sai akacemin a kashe yake , ina tsaye a wurin ban tafi ba ina ta kiran wayar kawai naji an nannaɗeni ta baya , nace su waye haka ? Ina zakuje dani ? Sai wani ya mareni yace wurin ubanki zamu kaiki , na nemi a kawomin ɗauki sai suka shakeni da niƙaf suka sakani a mota , Sun kaini wani gida bansan ko ina ne ba , wani ne ya fara zuwa a kaina yana danbe dani , sunyi maganganu dai , tayi shiru , ƙara dafeta nayi sosai nace waccan motar kinsan ko ta waye ne ? Hafsa tace ta DK ce , nace tunda har nahau motarshi ai kinsan kusanci yakai ko ? Tacemin Eh tana kallona , nace tou duk cikar faɗin birnin katsina Dikko baida aminiyar daya wuce ni , idan nace yayi zaiyi idan nace ya daina zai daina ya yadda dani fiye da lissafinki , me kike so na roƙar miki a wurin Dikko ? Cike da zumuɗi tace ni ya aureni kawai , nace Dikko ya aureki ya gama idan har kika bani labarin komai baki ɓoyemin ba saina sadaki da Dikko faɗa ina saurarenki , saida ta sake tunani taci gaba da cewa ! Tabbas naji wani yace nine Bello aminin ubanki , kiji da kyau yadda kikamin video tsirara haka zanyi miki kema , ni na koyama ubanki iskanci amma ɗan iskan ya lashemin mata a daren farko , yace na ɗana masa tarko amma ɗan banzan ya tsallake , idan baki sani ba nine nayi asiri wa Babanki kuma nine na haɗashi yake tarayya da ahalinshi , Kuma yace nine nayi asiri wa Babanki ya sakaki a wasan caca nine na mayar dake kidahumar ƙarfi da yaji na sakaki kika antaya a ruɗun duniya , bayan ya gama magana yace ni Bello zanyi iskanci da "yar ka idan ka isa ka dawo daga duniyar mutuwa ka ƙwaci "yar ka a hannuna , Ya kira Binna daga baya kuma yadai yi maganganu sosai kuma Dadyna yana wurin , kuma mai maganar yace yayi asiri ahali ɗaya sunyi gauragauraya suna iskanci badai zan iya ganewa ba domin ina cikin wani hali a dai² wannan lokacin. Sakin Hafsa nayi tare da juyawa nace wane irin hali kike ciki ? Juyowa nayi na shaƙe wuyan Hafsa ina cewa wane irin hali kike ciki ? Wane irin haline wannan ? Me Dadyn naki yake faɗa......? Me yace ? Nayi maganar cikin hayani sosai tare da cewa na rantse da Allah idan dai harni ɗiyar Binna ce ɗaya daga cikinsu idan ya sakeyin rayuwa mai daɗi ni ba ɗiyar Babana bace , sakin Hafsa nayi tare da turata baya da ƙarfin bala'e ta kusa faɗuwa Amisty ta riƙeta tana lafiya Mother , idona cike da hawaye nace dake da Hafsa dani gaba ɗayanmu ahali ɗaya ne , Gaba ɗayansu babu wanda baiji faɗuwar gaba ba , cikin tashin hankali Amisty ta cire gilashin dake saman fuskarta tana kallona , saida na goge hawaye sannan nayi murmushi mai ciwo nace kunji wani iri ko ? To nima haka naji lokacin da aka faɗamin ku "yan uwana ne , nayi kuka kuma nayi baƙin ciki kasancewa ta a cikin gurɓataccen ahali , cikin ɗaga murya sosai nace tou ku sani ni ɗin ɗiyar Binna ce kuma nima jikar gidan su Hafsa ce dani da "yan uwana da kowa na nuna Hafsa cewa tou idan baki sani ba Kakarki itace silar roshe komai , duniya ya ruɗeta yasa ta kora "ya "yan kishiyarta saboda san duniya wanda basu ji basu gani ba , ni ɗaya tak nake a wurin uwata kuma soyayyata a zuciyar Babana ba ƙarama bace ba , fashewa nayi da kuka ina cewa amma shine suka kashe Babanan, me yayi musu ne ? Cikin musulmar murya na sake cewa me yayi muku ? Mu kuma me mukayi musu suka mayar damu marayun ƙarfi da yaji ? Inda taron "yan gidanmu suke na kalla tare da nunasu nace su kuma wa'ancan me sukayi muku ne ? Me suka tsare muku ? Shine kukayi silar maida ahalina karuwai........? Cikin ɗaga murya na cire gyalena na wurga saman mota ina cewa na rantse da Allah , na daki kaina , dai² zuciyata nakai ma duka cewa na rantse da soyayyar mahaifina idan nabar ubanki da kakarki sun huta Hafsa kice ni ba MARYAM ALIYU MUHAMMAD BINNA nake ba , ni ba ɗiyar BINNA bace ba. Cikin tashin hankali Hafsa ta rugo da gudu ta riƙeni tana cewa Uwar ɗaki me yayi zafi haka ? Ki goge ƙudirin ɗaukar fansa a zuciyarki , cikin hayagaga nace ke ji nan kije ki tambayi wannan ruɓaɓɓiyar tsohuwar meye dalilin da yasa ta kora Binna da ɗan uwanshi daga cikin gidan ubansu , murmushi nayi mai kyau ina kallon Hafsa cikin tsananin ɓacin rai nace to ki sani nice na shirya komai ta yadda aka saceki akaje akayi wasan danbe dake , nina shirya komai kaidina da sharrina yafi alkairi na yawa , idan har kina so na goge babanki daga siraɗin ɗaukar fansa na baki daga yanzu zuwa gobe da safe kije wurin kakarki ki tambayota dalilinta na kora iyayena daga cikisu kizo kuma ki faɗamin idan kuwa ba haka ba kema zaki zama marainiya kamar yadda mu "ya "yan Binna muka zama marayu , ina faɗin haka na wuce na shiga mota nabar wurin cikin ƙunar rai..... Daga Hafsa har Amisty sun gagara gane abinda Sultana ke nufi saboda toshewar tunani , Amisty tace taya ma zamu zama ahalinta ne wai ? Hafsa kuma tace kinji wata sabuwar barazana wai itace tasa aka saceni akayi danbe dani bayan babu abinda ta sani nice fa na bata labari yanzu bata san komai ba , tana ganin dan na bata labari zatayi amfani da wannan damar ta tayar min da hankali , can ita ta sani da ita dasu wannan ba damuwa na bane ba , Ina fita bakin titi wuri na samu nayi parking a gefen titi na fara kiran wayar Dady da wayar da Dikko ya bani ba tashi wacce ya bani ba , babu ɓata lokaci ya ɗauka , cikin wata murya daban nace bawan Allah sannu Allah ya ƙetare "yar ka daga hannun azzalimai , ai dama nace duk yadda za'ayi saina samu number ka na faɗa maka gadar zaren da ake gina maka na ƙarasa maganar ina fashewa da kuka , Dady yace wace ce ke ? Cikin kuka nace masoyiyar ka ce , wata ce take neman ganin bayan ka shine ni kuma zan tona mata asiri , dani da ita duk a bariki muka haɗu ƙawata ce kuma itama karuwa ce ana ce mata Sultana ko ka santa ? Murmushi Dady yayi yana cewa tana ina ne ? Tana ɓoye a halin yanzu domin tana nan tana nemanka ta kashe ka shine na sace numberka daga cikin wayarta dan in faɗa maka cewa ka ankare dai dan yarinya bata sanka da yawa , cikin rashin lissafi kawai Dady yace ai har yanzu Binna baida ɗiyar da zata ga bayana ke wace ce ? Nace zan bayyana amma sai ƙura ya lafa kuma karka faɗawa kowa domin da wani abokinka ta haɗa kai suke san ganin bayanka , Dady yace waye abokin nawa ? Nace bansan sunanshi ba saina siffanta masa kamanin Bello na ɗora da cewa wata rana kayi ma Sultana waya zaku haɗu a fesra hotel ita kuma ta kirashi ta faɗa mishi shine shi kuma ya bugama "yarka waya yace su haɗu a wurin dan yana jin haushinka sosai shine yasa yakai "yar ka sukayi danbe da ita kuma kaima yaso sai kayi danbe kaga "yar kace , wata irin ashariya Dady ya dandanƙara cikin jin haushi yace ni Bello zai cuta ? Amanata zaici ? Tabbas biri yayi kama da mutum domin idan ban manta ba ita Sultana tace min wai na ɗan ɓoye mota ta daga ciki dan wani ne zai sauketa , wato tayi haka ne dan kar Hafsa tazo taga mota ta ne , amma a cikinsu waye ya gayyato Hafsa , tsakanin Sultana da Bello........? Bello ne domin shine ya shirya komai yana jin haushinka fiye da yadda baka tunani , amma Alhaji ina ganin shawara ɗaya me zai hana kawai kasa a kashe Sultana kafin ita taga bayan ka , Dady yace haka muke ta ƙoƙari mun faɗawa bokanmu amma yace sai ta daina sallah kaɗai zata iya mutuwa , shin ko zaki iya dakatar mana ita daga sallah ? Wannan ba abu mai wahala bane kauda ita daga duniya ni kaina idan ka bani izini zan iya shafe maka labarinta daga duniya guba kawai zan zuba mata a abinci taci ta mutu amma sai ka farayin wani abu akan Bello , Dady yace bari in fita daga Office sai muyi magana , godiya nayi masa tare da kashe wayata , bayan na gama na cire layin da Dikko ya siyamin na ciro layin da Dady ya bani na saka a cikin wayar da Dikko ya bani na fara kiran wayar Bello da layin da Dady ya bani , wato number da ake kirana ana cewa za'a kasheni , dan ina so nayi recording ita wayar da Dady ya bani ƙarama ce. Tana shiga ya ɗauka sai yayi shiru dan abinda na fuskanta number da yake kiran nawa kila daban yasai layin , nace ka gudu daga inda kake ni ina san tseratar maka da rayuwar ka ne , cikin muryar shi dana sanshi da ita yace wace ce ke ? Sanin ko wace ce ni ba shine ba ina san tseratar da rayuwarka ne domin a halin yanzu suna san ganin bayanka , su waye ? Kamanun Dady na faɗa nace shine yake san cin amanarka , kun haɗa kai akan zaku kashe wata yarinya amma shine naji yana cewa sai ya kashe ka , dariya Bello yayi ni kuma na dannan record bayan nayi shiru shima cikin rashin lissafi yace wannan shine ƙudirna da ko wane wata da ko wane sati ko wane yini da ko wace awa kowace daƙiƙa saƙo da lungu rana da dare neman sa'ar mutuwarsa nake , saina kashe shi. Yana faɗin haka na tsine kiran tare da kashe wayar gaba ɗaya na nufi goruba road , zuciyar Dady tana ɗauke da gudirin ganin bayan Bello , danshi a ganinshi idan ya kashe Sultana sai ya kashe Bello sune damuwarshi kuma sune suka san komai , idan ya kashe su gaba ɗaya babu wata sauran barazana a dukiyarshi , yayin da Bello shima yake ƙudirin ganin bayan Dady zaisa Dady ya kawo kuɗin da zai kashe Sultana yana bashi kuɗin zai burma ma Dady wuƙa a ciki ya mutu shi kuma saiya ɗauki kuɗin yaje ya kashe Sultana shikenan ya rufe wannan matsala.... Tunda na shiga gidan wani irin kallo Dikko kemin fuskar nan a haɗe yana zaune saman bayan motar abokinshi , su Ashiru suna tsaye kusa dashi , jikina yana kyarma nayi parking na fito da sauri na nufi wurinshi , abokinshi na gaida sannan na matsa kusa dashi ina bashi makullin motar , bai ko kalli inda nake ba dan haka na ajiye makullin kusa dashi na koma gefe nima na tsaya kamar yadda naga kowa yayi , Hmmm yayi tare da ƙuramin idanuwa yana kallona cikin ɓacin rai , yakai kusan minti 3 yana kallona kuma ko ƙyabtawa bayayi dole na shiga taitayina jikina ya fara tsimama da ƙyarma tuni na sauke kaina ƙasa dan kallo ya firgitani , bayan wani lokaci na sake ɗagowa har yanzu ni yake kallo , da sauri na sake sauke kaina banma yi gigin sake kallon inda yake ba dan bana iya haɗa fuska dashi , tafiya na farayi dan komawa bayanshi ya daina ganina ta gabanshi saboda banajin daɗin kallon , Robar ruwa ya ɗauka a gefenshi da magani yace zo ki ansa , ban koma ta gabanshi ba na tsaya daga bayanshi na miƙa hannuna na ansa , robar ruwan ya bani maganin kuma ɓallomin yayi ya miƙamin , ansa nayi nasha bayan na gama na maida mishi robar da sauran ruwan dana rage , ansa yayi ya maida ita a inda ya ɗauka yace tafi Ashiru ya maidake gida , kwantar da kaina nayi saman motar nace ngode , baiyi magana ba Ashiru ya ɗauki makullin yace muje , Bin bayanshi nayi ya buɗemin gidan baya na zauna ya rufe ya zagaya ya shiga mazaunin matuƙi yaja muka fita daga gidan , tunda muka fita Ashiru kemin nasiha yana cewa wallahi yau Allah ya tsareki irin dukan da yaso yayi miki Allah kaɗai yayi iyaka dashi haƙuri mukayi ta bashi kafin ki dawo , dan Umar ya kirashi waya yace ya ganki Qerau , mai gida yace ya barki goruba saida ya turo mishi hotunanki sheda ya gani ya yadda kuma ya dawo bai sameki ba , lokacin da kike kiranshi waya tou lokacin ya hau muna ta ƙoƙoarin saukeshi , wai kema ranki ya daɗe dole sai kin fitar wai ? Murmushi nayi amma banyi magana ba , har muka iso gida nasiha Ashiru yakemin , fita nayi tare dayi masa godiya kawai na wuce ciki.... Wasu irin motoci ne parke a harabar gidanmu masu kyau da tsada , kila ɗan uwan Inna ne ya dawo , tunda na tunkaro hanyar da zai sadani da palon naji maganar shi yana cewa ƙaddara babu wanda ya gagara yahau , ni banga abin ƙin wannan yarinya ba , matar ɗazu take cewa wallahi nidai jinina idan dai ni na haifeshi bazai auri yarinyar nan ba , idan kuwa ba uwarshi bace ni tou yaje ya aureta nayi bare duniya dashi ko lahira kada Allah ya haɗani dashi , yarinya karuwa kowa yasan karuwace a garin nan gata ɓarauniya kuma daƙiƙiya kidahuma gata bata fito daga tsatso mai kyau ba , haba duk iyayen mutunci sun haɗa ɗiyansu aure da ita ? Ɗan uwan Inna yace tunda duk kowa ya hana ɗanshi ya aureta ni zan bada ita , cikin hassada tace ai kasan ɗan tsiya bai gaji arziƙi ba kana tunanin ka haɗa ta da ko driver n ka ko mai gadinka ai ƙarshe watsa maka ƙasa zatayi a ido tace bata sansa kaga kuwa ai ba haka kaso ba , ni ba cikin su zan bata ba , Sultan ɗana zan haɗasu aure a cikin satin biyu masu zuwa , Sultan kowa ya faɗa ɗanka mai mutunci da daraja shi zaka aurawa karuwa ? Gaba ɗaya palon ya gaurare da hayani har bakajin abinda wani yake cewa , Hawaye naji ya ɗigomin daga cikin idanuwa na , wayyo Allahna , kila sunyi tunanin zai haɗani da mai gadinshi ko driver ko wani dai mara galihu , ɓarauniya , karuwa , daƙiƙiya , kidahuma ban fito a tsatso mai kyau ba , yace yaji kuma ya gani ɗanshi zai aureni , ya zanyi da Dikko ? Idan har kuma ban amince da maganar ɗan uwan Inna ba ance dama zan watsa mishi ƙasa a idanuwa saboda ban gaji arziƙi ba ni ɗiyar tsiya ce , jinjina soyayyar Dikko nayi a zuciyata gaskiya Dikko yana min soyayya mai girma , a bayyane nace tabbas haƙuri zanyi dakai kodan in nunawa ɗan uwar Inna na fito daga ahalin masu mutunci zanyi haƙuri da soyayyar Dikko in anshi Sultan ko baimin ba , tou tayama zan iya rabuwa da Dikkon wai ? Tun ma farko kenan wayyo Allahna...... Ji nayi gidan yana juyamin yayin da zuciyata kece cewa *DIKKO KO SULTAN...?* cikinsu wa zan zaɓa......? 30/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 67 Biyu zuciyata ta kasu yayin da wani sashe yake cewa Sultana kada soyayya yasa ki manta da irin halakcin da Kawu yayi muku , kuna banzace a gidan Baba babu cin yau babu na gobe bare na anjima kaf ahalin Inna sun watsar daku basa shiga sabgarku amma Kawu ya shigo rayuwarku yana taimaka muku , Sultana ya sakaki makarantar boko da islamiyya , yana tare daku yana tsotse duk wata damuwarku yau rana tsaka kwatsam sai ya nemi alfar wurinki kice a , a ? Yaga kina tangaririya rayuwa tana ta wurgel dake ance miki karuwa ɓarauniya kidahuma jahila baki fito tsatson mutunci ba amma yace yaji ya gani a hakan yana so ma ɗansa ke , ga "yar uwar Innarki sai tada jijiyon kai takeyi nata bazai auri na banza ba haba Sultana ki so sa don Allah , Ajiyar zuciya na sauke yayin da wani sashe na zuciyata ya fara haskomin rashin mutuncin Dikko kai tsaye yake gargaɗina da ke Sultana ina hankalinki yake so ya tafi ? Dikkon me ? Mutumin da bai san komai ba sai rashin mutunci duka zafin kai , babu dariya bare fara'a kullum fuska a haɗe yanayin fushi da farin ciki iri ɗaya , ga matsalar aljannu yanzu ƙarshe ki zaɓi Dikko wani abu ya haɗaku yayi miki tsinannen duka yace ki bar masa gidansa ina zakije a lokacin ? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un sam Dikko bazaimin haka ba , taya ma wai zai fara korani ? Yama zauna dani babu aure kuma yayi haƙuri dani bai koreni ba sai da yake aurena zaice na tafi ? Zuciyata tace ai wancan zaman bana aure bane ba yasan zaki iya tafiya ko wane lokaci amma zaman aure daban ne haba Sultana yaufa da gobe ake magana , raba kanki da yau da gobe zama ne zakuyi daga nan har mutuwa , kifa tuno rashin mutuncin Dikko babu imani a rayuwarshi duk sissiye gidajenku da yayi har kin manta Sultana ? Babanki da kika fi so fiye da komai a duniya Dikko ya watse shi da ruwan dake kwance saman ƙasa , Babanki mai sanki ya mareki saboda Dikko ? Me ake da Dikko ...? Zuciyata ta kasa bani mafita , alkairin Dikko ɗaya ta kasa haskowa rashin mutuncin Dikko kawai take gani yayin da take harzuƙa ni tana tambayata ina maganar ɗaukar fansar budurcinki daya kece miki ? Kin fasa ramawa a shekara biyun ne ? Abinda ya faru dani dashi a ranar daya ɓanɓare min budurci ta ƙarfi da yaji ya dawomin kamar yanzu ne yakeyin abun dani , da sauri na rufe idanuwana naci gaba da kuka zuciyata tana ci gaba da huramin wutar ƙiyayyar Dikko , Da sauri na goge hawayena na shiga cikin palon da sallama , gaba ɗaya na gaishe su nayi ma Kawu sannu da zuwa na wuce , Maryam yaki , kawu ya kirani , gabanshi naje na durƙusa a saman ƙafafuwana cikin ɗa'a da ladabi , Maryam ai kin sanni ko ? Murmushi nayi ba tare dana kalleshi ba nace na sanka mana sosai , idan na baki guba zaki iya ci ? Cike da ƙwarin guiwa nace me kuwa zai hana Kawu ? Ai ba guba da zanci a abinci ko abun sha ba wuta idan ka hura kace na shiga sai nayi maka godiya zan shiga cikinta cikin aminci da salama Kawu , kallona yayi sosai cewa shin wani irin soyayya kike ma "yan uwan mahaifiyarki ? Goge hawaye nayi tare da cewa ina musu soyayyar da bana iya fasalta irinshi domin su ahalin uwa jigo ne mai girma ko soyayyarsu daban yake a zuciyata , tun kafin na sansu na gansu kullum mafarkina na gansu ina alfahari dasu kuma dana kasance a cikinsu inayin farin ciki bana fatan rabuwa dasu har abada dan su ɗin mutane ne masu mutunci da nuna soyayya akaina... Yayar Inna tace kunji makirci ko ? Tou mu bama sanki gidan uwar wa muka nuna miki so ? Ke nan "yar tatsiyar alhaki dake har kin iya makirci , bama sanki bakya sanmu amma tsabar ƙwarewa da bariki mu zaki ma bariki ? Tou uwarki ma kanta a gabana aka haifeta ki sani ni nasan kina nan kinaji kamar ki cakamin wuƙa na mutu , Murmushi nayi mai ciwo tare dayin magana a zuciyata nace tabbas hasashenki gaskiya ne , amma a fili nace haba Inna aiko da duniya tayi tirr da Allah wadai da dani , magana ce na faɗa mata ita da take cewa bata so na kuma a matsayinta na Yayar mahaifiyata.... Kallona Kawu yayi sosai tare da cewa shin zaki iya auren ɗaya daga cikin ahalin mahaifiyarki kuwa ? Kallonshi nayi tare da cewa me kuwa zai hana idan har ya ganni nayi masa...! Idan ya ganki kinyi masa shi kuma ke bai miki ba fa ? Karka damu Kawu nayi alƙawarin sadaukar maka da kaina duk abinda kake so zan aikata , duk uwa sunanta uwa yayar uwa da ƙannen uwa duk iyaye ne yunwa mai tsanani da kewar abinci ya kamani , tsananin yunwa bana iya tashi ko ƙwaƙwƙwaran motsi bana iyawa ina kwance ina jiran mutuwa tazo , sai ga "yar uwar mahaifiyata tazo da ƙwano riƙe a hannunta sai tace "yata na ganki kinajin yunwa sosai wannan ƙwanon yana ɗauke da abinci mai daɗi na taho dashi na baki sai kuma naji nima ina da buƙatarshi kiyi haƙuri ni naci ke kuma ki jira wani , ita tafi ni jin ƙwarin jiki tunda har tana iya tafiya ni kuma bana ko iya tashi tsaye saboda yunwa ga kuma ƙamshin abinci yana ta dakar min hanci amma sai ta hanani bayan taga ni nafita buƙata , ta san wannan abincin shine rayuwata idan ta hanani zan iya mutuwa a ko wane lokaci amma ina kallonta ta zauna ta cinye abincin nan kaf a gaban idona tayi min ƙwalele sai nayi haƙuri , Ina nan kwance na kusa mutuwa sai gata ta sake shigowa da wani kwanon abincin shima sai ƙamshi yake , sai ga ɗan uwa mahaifiyata shi kuma ya shigo da nashi abincin amma sai yace Sultana gashi kici amma kiyi haƙuri ya fara yami naji ance min kina nan yunwa zai kasheki shine naje na samo miki wannan kici dan ki rayuwa , saina ansa zanci sai wannan "yar uwar ta mahaifiyata ta ajiyemin nata kwanon tace kici wannan shine sabo bai lalace ba karki ci nashi zai lalata miki ciki , tou faɗamin wane zanci a ciki tsakanin mai kyau ko mai yami ? Wanda baiji tausayin karka mutu ba saiya tausaya maka saboda lalacewar ciki....? Gaba ɗayansu shiru sukayi suna kallona babu wanda ya bani amsa , kallon Kaka nayi nace Kaka wane zan ɗauka inci a ciki ? Cikin muryar tsufa tace ai wannan lalataccen shi kawai ya kamata kici , murmushi nayi na kalli Kawu nace abun mamaki shi ɗan uwan mahaifiyata yace abincin yayi yami amma ina dubawa sai naga ya fara tsutsa shin Kaka naci kona fasa ? Kaka tace ci kuwa , Kaka sai ita Yayar uwa ta buɗemin nata kwanon sai naga farfesun kaji ne da zafi ga ƙamshi tana kici wannan ki bar wancan ? Kaka tace kajin nan kuwa basa ciwuwa a gareki , dariya nayi na kalli Kawu nace ina fara cin abincin nan kawai sai ya koma min daddaɗa ina san duk wanda zaka bani ina san sa , ina sanka ina alfahari da kaf ahalin mamana fatan alkairi a gareku iyaye na gari , 🙏🏻 ina kaiwa nan na miƙe nabar palon. Ina shigewa Yayar Inna tace tou na gane wato habaici tayimin yarinyar can ? Nice na cinye abincin dan ki mutu tunda nace ɗana bazai aureki ba , shegiyar yarinyar makira munafika wannan idan ta auri ɗanka aisai ta rabaka dashi har abadan duniya , Kawu yace babu gudu babu ca da baya sati biyu masu zuwa zan ɗaura musu aure , ƙarshe dai saida rayuka ya ɓaci kowa ya tafi Kawu yana cewa zai turo Sultan idan Allah ya kaimu su gaisa..... Sai ƙarfe 2:19am na buɗe wayoyina kuma a dai² wannan lokacin nahau online na cire hoton Dikko dake a d p ina na saka hoton fulawa , layin Dady na kira yana shiga ya ɗauka yace baiwar Allah tun ɗazu nake kiranki wayarki a kashe , nace bari kaidai wurin yi maka record in maganar abokinka suka kusa kasheni shida Sultana shi yasa na rufe wayar na gudu dan tsira da rayuwata yanzu na samu wuri na tsaya haka nan na gwada sa'a har ina tunanin idan na kiraka a tsakar dare kamar nayi hauka ma , Dady yace ai ni tuni nayi bankwana da bacci matsaloli suna neman kunnomin kai , na yadda da Bello 100% tun yana matashi nake tare dashi amma yau rana tsaka zai tattara wannan mutuntakar ya zubar , Hmmm ai danma bakaji abinda yace maka ba , kuma ya buɗe kaff wasu ɓoyayyin surruka yana faɗawa ita Sultana , Dady yace wai me yake cewa ? Ina zuwa na faɗa tare da tsinke wayar , canja layikan nayi layin Dikko zuwa cikin wayar da Dady ya bani , layin Dady zuwa cikin wayar da Dikko ya bani , bayan na gama na kirashi ya ɗauka. Da babbar wayata na kunno mishi maganar Bello , yaji Bello yana cewa wannan shine ƙudirina da kowa wace daƙiƙa saƙo da lungu rana da dare neman sa'ar mutuwarsa nake saina kashe shi..... Dariya Dady yayi tare da cewa shirmen banza shirmen wofi akan kaina dukiyata da iyalina zan iya shafe labarin duk wani banza daga sahun masu lumfashi a duniya , speaker na saka wayar na kara babbar wayata na fara ɗauka , Dady yaci gaba da cewa ganin bayan Bello ba wani abu mai wahala bane a wurina na barshi ne ya rayu na wani lokaci dan kauda min rayuwar yarinyar dake adawa da dukiyata idan ya aika ta zuwa duniya matacci nima saina turashi zuwa can ni kuma inci gaba da rayuwata babu maƙiya sa ido da wata baraza akan komai dana mallaka a duniya domin na kauda matsala a rayuwata.... Ajiye recording in nayi a wayata sannan nace Alhaji Bello yana da hatsarin gaske bana tunanin zaka iya kauda matsala biyu a cikin kwana biyu na mutuwarka daya ibar maka , dariya Dady yayi tare da cewa ki bani zuwa jibi zakiji labari yasha banban yayin da za'a faɗa a gari cewa wani ɗan cacan ya sake , sai kuma yayi shiru ya canja maganar da cewa ngode zan kiraki zuwa safe idan Allah ya kaimu lafiya...! Godiya nayi masa mukayi sallama na tsinke kiranshi na kira Bello. Cikin maye ya ɗauka kuma daga jin yanayin wurin tabbas yana gidan caca , cikin muryar maye yace ke kika kirani ɗazu ? Ey nice na kiraka , na kiraki wayarki a rufe , Ey na bashi ansa , wai nine ma ɗan ƙaramin ƙwaron nan zai kashe ko ? Nace haka ya faɗa kuma haka yake shiryawa yace gobe²n nan iyalinka zasuyi kukan mutuwarka , amma wai me yasa yakejin zafinka haka da yawa ? Me kayi masa yake san ganin bayan ka ? Saurara kaji abinda yace maka. Kunno mishi record in nayi yaji Dady yana cewa , ganin bayan Bello ba wani abu bane mai wahala a wurina , na barshi ne ya rayu na wani lokaci dan kauda min rayuwar yarinyar dake adawa da dukiyata idan ya aika ta zuwa duniyar matacci nima saina turashi zuwa can ni kuma inci gaba da rayuwata babu maƙiya sa ido da duk wata baraza akan komai dana mallaka a duniya domin na kauda matsala a rayuwata. Cikin maye Bello yay dariya yace ni kuma a cikin daren nan zan sakashi a tarko naci gaba da farautar rayuwarshi zuwa ƙarfe 10 dai² na safiyar gobe zan kasheshi na kuma kashe Sultana saina kashe su wallahi , yana faɗin haka ya tsinke wayarshi. Wai me kike nufi ne ? Ni zakima gwala² ne ? Dikko ne kwance a saman gado yana jawo Jiddah jikinshi tana zuƙewa tanaja baya tasha wando jeans ta haɗa da belt , Mardiyya ta bata shawara ta daina bawa Dikko haƙƙinshi dan tana sakin jiki yana murjeta sosai shi yasa ya rainata ta kame abunta ta rufe a wando , saida ta bari wasa yayi nisa taga ya fara sakin layi ta ƙwace kanta , Dikko yace meye haka ne wai ? Cikin kwarkwasa da salo mai ɗaukar hankali tana yauƙi tace ai mantawa nayi da zakayi aure saboda ni bankai mace ba shi yasa zakayi min kishiya ? Tou kaje wurin waccen zaka aura sai ta baka maganin damuwar ka , murmushi Dikko yayi tare da ƙurawa Jiddah ido yace yanzu me kike so ne ? Saida ta sake girgizawa tace idan kana so ka kwanta dani sai ka sauka ƙasa ka bani haƙuri , ba tare da Dikko ya kalleta ba yace ai gara in mutu da in baki haƙuri danni mace bata ɗagamin hankali wannan abu fa duk taimakon kai da kaine , sauka yayi daga saman gadon yana cewa idan kinji kina muradi sai ki nema na baki danni bana hora mace da tauye mata haƙƙinta , Juyowa yayi ya kalli Jiddah yace duk macen data san kanta tasan mutuncin kanta bata tauye haƙƙin mijinta saboda wani tunanin banza nata , ni da mace neni na rantse da Allah duk mijin daya aureni sai yaga bariki na tashin hankali , ko inuwarshi na gani saina ɗage mishi zani na bashi natsuwa , amma ke har kinma samu an nemeki zaki rainawa mutane hankali waye yace miki horon hana namiji haƙƙinshi shine ke nemawa mace mutunci da martaba wurin namiji ? Idan har baki sani ba wannan abun babu abinda ya kaishi zubar da mutum mace wurin namiji , ƙimarki da darajarki sonki yana ƙara samun nakusa a zuciyata duk macen da tayi ma namiji horon hana haƙƙi taci baya a zuciyarshi. Misali kece kikayi tafiya a cikin tsananin rana ƙishirwa ya kamaki sosai kamar zaki mutu yayin da kikejin wannan ƙishirwar bakya tarar ruwan da zaki sha wurin kashe miki wannan ƙishirwa , kwatsam sai gashi kinga ruwa a gabanki jikinki yana kyarma kika duƙa da niyar sha sai wani ya hanaki shan wannan ruwan ya tareki , idan kina iyawa a dai² wannan lokacin me zakiyi ma wannan mutumin daya dakatar dake daga biyama kanki buƙatar ki.......? Jiddah tace sai inyi kokowa dashi in karɓa insha , girgiza kai Dikko yayi cewa ni bana iya gudu ina shan ruwa domin nasan baya kashe min kishirwata , haka kuma bana ci idan bana cikin natsuwa domin idan har naci abu ba'a natsuwa ba tabbas zaisa min tashin zuciya ko kuma inyi amai , ni bana danne mace da ƙarfi na kwanta da ita idan har na kwanta da mace ba'a cikin natsuwa ba bana samun natsuwar da nake so , ni a wahalce ita a wahalce me kayi kenan ? Abinda nake so ban samu ba , ni ba sakaran namiji bane da zaki tsuke da jeans da belt in kamaki da ƙarfi in cire miki na afka kanki kamar wani dabba ƙarshe inji miki ciwo kinga kaina nayi ma tunda gobe idan nazo na laɓe bayanki ina buƙata ya zanyi ? Ya ƙarasa maganar yanayi mata kallon ukku saura kwata , yaci gaba da cewa amma shawara ɗaya zan baki shine ki sake masu baki shawara su koya miki yadda ake tattalin miji wannan wacce ta koya miki haka ba ƙawa bace ba tunda har ta koya miki yadda zaki nakasa rayuwar mijinki , mai maimakon ta koya miki yadda ake tattalashi.... Tun asubar farko Mardiyya ce tsaye a cikin kicin ɗin Jiddah tasha wanka tasha jagira ta ranbaɗa powder da kwalli sai zuba ƙamshi takeyi kamar amaryar sarki , ta haɗu a cikin wani dakeken tsadajjen leshi baƙi tasha atacch ta zubo shi har tsakiyar bayanta , tayi kyau sosai , gaba ɗaya gidan ya karaɗe da ƙamshin girkin da takeyi Jiddah nacan kwance saman gado kamar asara dan Dikko tunda ya fita masallaci bai dawo ba gidansu ya wuce saboda takaicin Jiddah , Jiddah tana kwance Mardiyya ta dafo abinda zasu yi kalaci ta barbaɗe da asiri ta kawo mata , jakar ta sauko ta lashe , bayan Jiddah ta gama tace ta ajiye na Yaya a saman tebirin cin abinci bayan shima na Dikko an barbaɗe da magunguna... Misalin ƙarfe 11:40am ya fito daga wanka yana fitowa wayar shi ya ɗauka ya fara kiran An mata , lokacin da wayar shi ya shigo ina tsaye a jikin madubi dan fitowa na daga wanka kenan ina shiryawa Sultan zaizo misalin 12:20pm kamar yadda Kawu ya kira ya faɗawa Kaka ta sanar dani , a daddafe nakeyin komai dan har yanzu banajin daɗi jikina yadda ya kamata , Wayar yana shigowa na tsinke kiran , sake kira yayi na ƙara kashewa , kallon number yayi yana cewa haba An mata me kuma ya faru ? Bayan jiya ban dakeki ba ranar dana dokeki ma ai bakiyi fushi dani ba yi haƙuri ki ɗauki waya An matan Dikko ya ƙarasa maganar yana sake kiran wayar , wayar yana sake shigowa na ɗauka cikin ɓacin rai nace wai me ye ne......? Ke.... wa kike ma hayani ? Dakai nake , me yayi zafi ne to ? Haba An matana , yayi maganar cikin sanyin murya , natsuwa tazo jikina na nemi haushin Dikko na rasa kamar an tambayeni nace aure zanyi da ɗan Yaya mamana a cikin sati biyu mai zuwa , yanzu ma na fitowa wanka zaizo wurina mu gaisa , wane irin aure haka da rana tsakiya ? Ko dama kun jima kuna soyayya ne ? Cikin kuka nace a , a , ni banma taɓa ganinshi ba sunansa ma ban taɓaji ba sai jiya sunanshi Sultan , murmushin takaici Dikko yayi tare da cije leɓonshi na ƙasa yace to nima gani nan zanzo , a , a ka bari yazo ya tafi sai kazo , Dikko yace idan har nace zanyi babu wanda ya isa ya dakatar dani saina zo gani nan zuwa........ Yana faɗin haka ya kashe wayarshi. Cikin ruɗewa naci gaba da shiri kar Sultana yazo ya haɗu da Dikko tunda tun jiya Babanshi ya faɗa zaizo idan kuma ya koma yace Babansa yazo ya samu nayi baƙo ai abun babu daɗi , Yarinya Dikko zaki tonawa asiri ? Ni zaki faɗa ma aurenki nan da sati biyu ? Duk duniya naga mai aurenki idan ba ni ba , lallai An mata baki da hankali inma banda wawanci da rashin lissafi kai tsaye sai ace za'ayi miki aure da wani kawai kinma yadda kin hankaɗeni gefe ɗaya , naga jakin Sultan ɗin ina fama da matsalar Yazeedu zaki sake tattago wata , yana gama sa kaya kiran Inna ya shigo wayarshi... A zuƙuwa ya ɗauka , bayan sun gaisa Inna take faɗa masa mutuniyarshi ta faɗa mishi zatayi aure ? Cikin farin cikinta da jin daɗi take bawa Dikko labari cewa ai auren zuminchie ne dake a familynsu auren haɗi akeyi , cikin yanayin farin ciki Dikko yace to kun tambayi ita yarinya tana san yaron ne ? Duk abinda ya faru jiya kamar ansa Inna ta kwashe kaf ta rattabawa Dikko , dan ita bata san Dikko da Sultana soyayya akeyi ba kuma bata san waye Dikkon ba kawai dai tanayin waya dashi dan yayi tsayuwar arfa wurin ganota ya sadata da "yar ta shi yasa ta bashi wani matsayi na musamman a rayuwarta gashi kuma yana ƙoƙarin kiranta a waya yana gaisheta lokaci². Inna ta ƙara da cewa aiko bata sansa su babu ruwansu haka suke haɗawa a can gidan aure ake fahimtar junan , cikin ƙarfin hali Dikko yace Allah yasa alkairi Inna ta ansa da amin tace itama zata dawo kafin bikin , Dikko ya ansa da a dawo lafiya yana faɗin haka ya tsinke wayarshi. Ajiye wayar yayi yana cewa An mata da gaske bari zakiyi a rabaki dani ? Haba yarinya Dikko Yazeed Sultan gaba ɗayansu nine zakaran rukuminsu gani nan zuwa a dai² lokacin daya rataya kayan da zai saka a jikin wani ƙarfe ya rungume turare yana bugawa , wani irin turare ne na "yan gayu mai masifar ƙamshi da tsada wanda ni da naji kuɗinsa naji dama kuɗin ya bani na siyawa "yan gidanmu gidan zama , shi turaren ba kaya yana a jikinki kake shafawa ba , sargafe kayan akeyi saman wani abu sai a riƙe ta inda turaren ke fita cikin hannun haggu ana zungurashi da hannun dama turaren yana fitowa , tou idan wani yana wurin akayi feshin shi kanshi turaren saiya bi kayanshi da jikinshi , idan kuma aka sakashi a jikin kaya ko an wanke ƙamshin baya fita kuma haka ƙamshin zai kama jikin wanda ya saka kayan. Alhaji idan kuɗin nan sun haɗu ka kawomin dan zanba yaran da zasu tayani aiki wani abu a ciki yau nake so na kashe yarinyar nan gata nan na kamota , Bello ne kwance saman kujera ya ɗora ƙafa ɗaya saman ɗaya yana magana da Dady a waya , Dady yace kuɗi sun haɗu kana ina ne kaida yarinyar ? Bello yace ina sabon gidan bayan sabon gidan sarki ai ka gane gidana da nake gini ban gama ba ko ? Dady yace Eh Bello yace to ya taho da kuɗi ka ɗauki gawar Sultana , Dady yace gani nan zuwa ya tsinke wayarshi. Bello kallon yaranshi yayi yace yana zuwa sai ku rufeshi da duka harsai ya mutu mu kuma mu ɗauki kuɗin saimu gudu , Shi kuma Dady yana gama waya da Bello ya kira "yan sanda cewa a bashi jami'ai cikin kayan gida su biyoshi dan zuwa inda wani ya kashe wata yarinya , bayan ya gama waya da polisawa yace haba Bello tunda dai burinka ganin bayana nine nan zan ga bayanka a banza a wofi dani kake zance ko ka manta waye ni ? Muke da gwamnati mu'ahhukuma hannunka dumu² a kisan Sultana "yan sanda na kama sai su kashe ka , Sultana ta mutu Bello ya mutu damuwa ya ƙare..... Kukan motocin Dikko na jiyo suna shigowa wani irin kuka sukeyi suuuuuu ba ƙara sukeyi ba cikin laushi suke kuka suuuu ina lissafi a zuciyata saida mota biyar ta shigo , wani irin farin ciki naji a zuciyata a bayyane kuma nace barka da zuwa mutumina , a ƙagare na saka hijabi nayi waje cikin jin daɗi. A harabar gida su Ashiru sun wasu kuma sun hana shiga ko fita harsai mai gidansu ya gama abinda yakeyi ya tafi ikon mallaka kenan , wani ne ya buɗe min mota na shiga inda Dikko ke zaune yana ta soɓaro baki cikin sakata , ina shiga ya rufe murfin motar , kallon Dikko nayi cikin jin daɗi tattare da shauƙin so , ɗan kauda kanshi yayi gefe yayi kyau sosai a cikin ƙananan kaya amma idonshi ya faɗa ma'ana yaɗanyi rama , Murmushi nayi tare da cewa kayi kyau Dikko , ba tare daya kalleni ba yace ngode An matana ya ƙarasa maganar yana murmushi tare da ɗaga girarashin duka amma bai kalleni ba , sai yayi shiru , ni kuma na sake cewa baka da lafiya ne ? Lafiyana qalau yayi maganar yana duba wayarshi , to kayi shiru ina magana kana kallon waya , Ey amma kuma kallon wayana bai hana naji abinda kike cewa , Dikko na faɗa maka , kin faɗamin zakiyi aure kin cire hotona a d pn ki , na sani ai , kayi haƙuri haka Allah ya tsara , ajiye wayar yayi tsakanin ni dashi ya juyo yana kallona yace ku mata kullum tunanin ku ɗaya ne , daga aure sai ku haihu bakwa gina rayuwar zaman auren da soyayyar junanku , bata yuwu kawai magini ya fara gino katanga daga sama baza ta zauna ba saboda a saman iska yake ta ɗora buloluwanshi , ni kuma ta ƙasa na fara nawa nayi foundation mai kyau bayan na zuba masa siminti tsaƙƙuwa da yashi na bi a hankali na ɗora buloluwa na da ko wace daƙiƙa cikin salon iya gini , na bashi ruwa katanga ya zauna dai² da dai² cif da cif faɗamin taya wannan katangar za'a iya ɗauketa a sake mata wurin zama ne ? Sai a sauke bololuwan ai , bulo dubu ne Dikko ya jera taya zasu sauko duka ba tare da wani ya roshe ba ? Kallon shi nayi cewa aiko wasu sun roshe dole a samu rayayyu , bulo dubu ne aka cire kuma ana so a sakeyin irin katangar da ake so a sake ma wurin zama shin gini zai kai kamar waccan da wurin cire bulo wasu suka rushe ? Sai ayi dashi da fasassun , taya zasu zauna bayan babu dashi a cikin wacce aka rushe , sai a siyo sabo a ɗora , taya za'a haɗa sabon bulo da tsoho ? Ai gini dai ake buƙata abinda tsohon ya bada sabo zai bada irinshi , bolo ina 9incis ne sai akaje siye sai suka ce babu 9 sai 6 , sai insa su bugamin wani inci 9 idan aka samun banbancin siminti fa , wancan yaji suminti sabon kuma yashi yayi yawa...........? Sai ayi filester , ai bana buƙatar filester An mata wato kina tunanin zaki iya rusa soyayya ta ki gina ta Sultan akan tawa ko ? Ai idan kayi tunani da babu kai zuwa kayi , tabbas babu ni zuwa nayi kuma nazo kenan bana tafiya , Sultan zaizo yayi ta gininshi a saman iska ne domin nasan zuciyarki ta gama ginuwa da soyayyar Dikko rabaki dani a halin yanzu tamkar raba bawa da mutuwa ne , kinkuwa ga abinda baya yuwuwa ne duk wanda yazo saiya koma idan har kina ganin baki mutuwa to na yadda soyayyana zai goge a zuciyarki yarinyar kirki kawai kin shigemin zuciya yayi maganar yana sauke gilashin gefenshi saboda Ashiru yana magana , Mai gida wai wani daga ciki akace zai shigo yana ƙofar gida , Dikko yace a , a ya bawa Ashiru ansa yana ɗage glass in , nace kaji mulkin mallaka gidan ubanshi ne fa , ai ni kuma katsinar gaba ɗayanta a hannunmu take ko ina namu ne , banda nan dai ke yarinya shima nan ɗin nawa ne idan kuma kince a , a yanzu in nuna miki ki gani , Shiru nayi shi kuma yaci gaba da rattafo kalamai masu girma zuwa zuciyata kaina kwalwata da tunani na , yaci gaba da ginawa kamar yadda yace , karatunshi mai wahar gogewa ne , kalamanshi na da daɗi , soyayyarshi tana da girma , yaci uwar awa biyu yana ɗorani a inda bana iya saukowa , saida ya tabbatar na hawo sosai yace inje zaizo anjima idan Sultan ya tafi , saida na rungumeshi na fita , shidai baya san yana taɓani kona rungumshi zai ƙyaleni saina sauka a jikinshi da kaina , ɗan gayun namiji kenan ga kyau ga tsafta ga wanka ga ƙamshi saboda yawan wankanshi idan ka taɓa jikinshi sai kaji wani irin laushi kamar ka taɓa bayan zomo , ina nan tsaye har suka fita jikina sai ƙamshin shi yakeyi gaskiya Dikko na daban ne. Saida motocinsu suka ɓace daga wurin ko ɓushi²n ƙurarsu babu sannan motar Sultan ta shigo...... 31/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 68 Wuri ya samu yayi parking ya fito a nutse yana murmushi , hannu ya fara bawa mutane suna gaisawa duk wani ma'aikaci dake wurin saida Sultan ya miƙa mishi hannu suka gaisa cikin sakin fuska , shima dai wankakken matashi ne wanda shekarun shi bazai wuce kamar na Dikko ba , Wurina ya nufo yana murmushi , nima murmushin nayi masa cewa takwarana barka da zuwa , da yawwa ya ansa yayi gaba nabi bayanshi muka shiga ciki , a palo muka samu Kaka gaba ɗayanmu wuri muka samu muka zauna , bayan mun zaune Sultan ya gaishe ta , ta ansa cikin sakin fuska da ɗan barkwancin hakan nan dai. Fira sukaci gaba dayi da Kaka ni kuma na miƙe nayi ɗakina , ina zuwa alwallah nayi na gabatar da sallah azahar bayan na gama naci gaba sabgogin gabana a cikin ɗakina , kayan da Yazeed ya kawomin na buɗe ina gani , wanda sukafi burgeni suka tafi da tunani na fara zamewa gefe ɗaya zan kai ɗinki. Ina ta ciccire kayan ne Sultan ya shigo , kamar ya saba dani ya duƙa wurin kaya shima yana fiddowa yake tambayana me za'ayi dasu ne ? Ina murmushi nace ɗinki zankai na taɓa wanda zankai ɗinki da hannuna , ɗan murmushi yayi kaɗan ya fara ciro wasu daga cikin wanda na fitar zankai ɗinki yana cewa gaskiya wannan bama sanshi , tou wai har an kawo lefen ne ni ban sani ba .....? Dariya nayi nace bafa lefe bane ba , dani dashi gaba ɗayanmu kallon juna mukayi lokaci ɗaya , kyakkyawan murmushi yayi min yana cewa waye ya baki ? Wani ne ya kawomin , wayyo mun kuwa gode ya faɗi maganar yana komawa gefen gado ya zauna. Sultana ya kira suna na , ba tare dana juyo ba nace na'am , Abba yace nazo na ganki na kuma gaisheki ni Abubakar Sadiq nake suna kirana Sultan ne sunan Baban Mami na ne , ina da mata ɗaya yarana biyu , auren zumunci shine al'adar wannan ahali , amma ni aurena na farko banyi auren zumunchie ba saboda babu wacce zan aura a lokacin yaran duk basu girma ba ni kuma na tashi aure Abba yace inyi kawai daga baya idan yaran sun girma sai in kulle ta biyu da auren zumunchie , kin ganni na ganki ni kinmin a haka Allah yasa nayi miki.....? Ba tare dana juyo ba nace Ey mana kamin ina sanka , amma fa ni karuwa ce shin zaka aura karuwa ? Yi yayi kamar baiji abinda nace ba yaci gaba da cewa Mami ta bada shawara a ɗaura aure sati mai zuwa sati na gaba kuma sai ayi shagalin biki , nace tou Allah yasa alkairi ya bamu zaman lafiya fita da sharrin dake ciki ubangiji ya kauda shi ya tsinkule idanuwan maƙiya , am3n Sultan ya ansa tare da miƙewa idan kin gama haɗa kayan ki sameni a waje sai in kaiki , na ansa da tou shi kuma ya fice... Yana fita naci gaba da fiddawa bayan na gama haɗawa na zuba a lader na ɗauka na fita , a mota na samu Sultan na buɗe na shiga saida na zauna na rufe yace ina zamuje ne ? Nace masa goruba road , murmushi yayi tare da kallona yace kice dai amaryar tawa mai kuɗi ce goruba kike kai ɗinki ? Murmushi nayi ba tare da nayi magana ba , jinjina kai yayi bai sake magana ba ya taka mota muka fita daga gidan , muna fita wayarshi ta fara ringing ɗauka yayi banji abinda abokin wayar yace ba shidai yace zanje goruba ne , a , a kayi haƙuri don Allah jirani yanzu zan ajiyeta nazo don Allah , babu damuwa bara na fara zuwa tou yana faɗin haka ya ajiye waya , yana cewa yi haƙuri da Allah na anshi saƙo , babu damuwa na bashi ansa. Hajiya wai bayan su Dad inmu shi Malam kafin ya mutu yana da wasu "ya "yane don Allah ? Hafsa ce zaune a gaban Kakarta take tambayarta shin ko Dad inta yana da wasu "yan uwane bayan wanda ita ta aifa da cikinta ? Hajiya dake kwance tana gab da ramin mutuwarta tace Hassatu me yasa kikai min wannan tambayar ne ? Gyara zama Hafsa tayi cewa ba komai kawai dai ina so na sani ne , cikin yanayin wahaltuwa ta majiyyacci Hajiya tace yana da yara biyu amma basa tare damu a halin yanzu ? Hajiya suna ina ne haka ? Fashewa da kuka Hajiya tayi cikin kuka take cewa haƙiƙa ita rayuwa taƙaitacciya ce kuma ƙarewa takeyi ba tare da tayi shawara dakai ba , duniya da komai zaka ajiye kaje ga Allah , babu wanda yazo da arziƙi kuma babu wanda zai koma dashi , ruɗin duniya da shaiɗan yasa na tabka kuren da bashi da gyara kuma rayuwa ta riga ta ƙuremin , cikin kuka sosai taci gaba da cewa yau da zanga Aliyu da ɗan uwanshi dana roƙi gafararsu su yafemin , ni nake kwance ina ciwo amma duk lokacin dana kwanta da sunan bacci sai nayi mafarkin ina faɗawa cikin wani irin tsukakken rami kuma wuta yake ci a cikin sa , Hassatu duk arziƙin ka baka isa kayi ma wani arziƙi ba , haka kuma idan ubangiji ya arzurtaka kai bawa baka isa ka talauta wanda ubangiji ya azurta ba , kowa tsirara yazo babu wanda aka haifa da wando ko riga kowa haka ya faɗo kuma kowa haka zai koma daga shi sai likafanin shi , duk abinda kazo duniya ka tara kanaji kana kallo kana sanshi zaka tafi ka barshi magada suci gadonshi , ka bar musu dukiya sunajin daɗin duniya kwana kaɗan sun manta dakai sunci gaba da sharholiyar duniya sai ɗaiɗaiku a "ya "yan naka zasu riƙa tunawa dakai har ka samu suyi maka addu'a. Haka take ga mace , idan mijinta ya kwanta ya mutu kuka na wani lokaci zatayi daga inda aka raba gado aka bata shikenan ta mance da shafinka a rayuwarta , ga dukiya ka mutu ka bar mata gidanka taci gadonshi tanajin giyar kuɗi yana motsa ta taci abinda ranta yake so tasha wanda take so idan za'a nemi shawararta a misali za'a ce mata Hajiya ko a dawo da Alhaji daga duniyar mutuwa cewa zatayi a , a , a ƙara kwaɓa ƙasa a zuba a saitin kanshi , bayan wasu watanni tayi takaba ta gama tuni ta manta dakai namiji zata samu ta aura kana lahira wani yana kwana a gidanka... Idan kana da "ya "ya da ita kila idan tana da sauran imani ta kallesu ta tuna dakai , dan ba duka aka taru aka zama ɗaya ba , to ni ba auren nayi ba Hassatu dukiyar nake mawa wannan dalili yasa na fasa gidan na kora "ya "yan malam biyu suka shiga duniya yayin dana kashe uwarsu saboda san duniya kuma duk saboda "ya "yana nayi haka dan ina so suji daɗi kuma sufi na kowa , amma kaico duk wannan yaƙin da nayi Hassatu ubanki sai yayi ruf da ciki akan kaf wannan dukiya shi ya cinyeta duka ya hana "yan uwanshi komai nima mai yaƙin sisi bai bani ba duk abinda nace masa ina so , ko ya kawo abu ya ƙare sai yayi masifa sosai sannan ya ɗauko ya bani kamar zai dokeni. Ki gayamin ɗan da bai ma idonka ba bayan idonka zaiyi ne ? Hafsa tace a , a , murmushi mai ciwo Hajiya tayi sannan tace... Ina da abiyar zama kuma tana girmamani sosai a matsayina na Yayarta a wurin miji , tana bani girma na yadda ya kamata ko aiki taga zanyi bata barina nayi idan har kika ga ina aiki tou lallai Maryam bata lafiya ne , kuma ko tana ciwo saita daure cikin ƙarfin hali tazo ta kamanin dan dai ta bani girmana da mutuntuwa na ina gaba da ita a gidan aure. Tunda nake ban taɓa ganin ɓacin rain Maryam ba domin mace ce mai haƙuri kunya kawaici da kara , duk "ya "yana dana haifa bana musu wanka ko tsarkin kashi ko goyo duk Maryam take musu idan har kika ga ɗana a hannuna to wallahi nono yake sha kuma yana gamawa Maryam zata ɗaukeshi ta goye , wankina dana yarana duk itace take haɗawa tayi , Duk lokacin da Maryam ta samu ciki sai nayi yadda na lalata cikin nan ya zube nayi ta neman asiri karta aihu amma dake ubangiji yayi alƙawarin biyu sai sunzo duniya Allah ya bata Aliyu da Muhammadu , bana san yaran kwata² ina ta neman hanyar da zanyi na sabauta musu rayuwa dan bana san ace "ya "yana suna da "yan uba ba hangen wata irin ƙatuwar gona da Malam yake da ita tun a wancan lokacin an taya gonar naira dubu ɗari 3 da hamsin bana so ace an raba wannan kuɗi idan Malam ya mutu wasu su samu sai nawa kawai. Wannan gona duk duniya itace kaɗai Malam ya mallaka bayan ita bashi da komai a duniya kuma gonar itama ba gadonta yayi ba , domin talauci ne ya isheshi shine ta fara harkar tsibbunci kuma Allah ya dafa mishi kasuwa ya buɗe yayi ma wani attajiri aiki da buƙata ya biya shine ya baya da gonar yace ya riƙa noma dan ya cida iyalinshi. Haka Malam yaci gaba da aiki a ƙauye har manyan "yan siyasa suka ganoshi duk buƙatar da mutum yazo dashi insha Allah Malam yanayin aiki an dace , abinda ya maidomu garin Katsina wata yayi ma aiki tayi mishi kyautar gida muka tattaro muka dawo birni. Muna dawowa liƙafa yaci gaba sosai a taƙaice dai Malam ya tara manyan kuɗi da ƙaddarori manyan gonaye a garin funtuwa gidaje a cikin gari , ganin kullum Malam yana ƙara ginuwa shine na nemi hanyar da zan kora Maryam , bayan nayi shawara da wata aminiyata itace ta bani shawara mutuwar Maryam shine kawai mafita , idan ba mutuwa tayi ba ko sun rabu da Malam itama zata saka ran zataci wani abu a dukiyar gadon fitina za'ayi sosai shafeta daga duniya shine kawai abinda ya kamata muyi , to itace ta rakani wurin wani boka yayi asiri ya haɗa Maryam da aljannu aka tura mata yace idan ta firgita tayi ƙara aljannin zaiyi tsalle yahau saman harshenta take a wurin zai zuƙe jininta shikenan an rufe littafinta , idan kuma ta kira sunan Allah aljanni bazai iya zuwa wurinta ba , haka kuwa akayi Maryam dai ta tafi. Bayan mutuwar Maryam kuma nayi makircin da nasa Malam ya korasu Aliyu daga gidan nan , nayi tunanin idan suka tafi za'a sacesu dan nayi zaton kawai zasu halaka a duniya ne , da naji labarin basu ɓace ba shine nayi asirin da zasu manta da gida kwata² , kwatsam sai naji labari wani gida sun ɗaukesu suna zama dasu shine na faɗawa mahaifinki nace yasan yadda zaiyi da yaran nan dan a lokacin Malam ya rasu nace idan har hankin yaran nan ya dawo gida zasu buƙaci a basu gadonsu , Wannan dalili yasa Dady ya tura Bello ya shiga rayuwar Binna , saboda Bello baijin magana ko kaɗan iyayenshi ma kansu ji sukeyi dama basu haifi banzan ba , kuɗi Dady yake biyanshi kuma shine yace yana so Bello ya gurɓatawa Binna rayuwa yadda ko ya girma ya zama mara gulihu dan karya nemi kuɗi kuma yanaso Binna yayi wulaƙantacciyar rayuwa karya zama na gari dan baya so kwata² ya tuno da labarin gida , Bello da Dady sukayi ciniki Dady ya bashi rabin kuɗin aiki , shine Bello yayi asiri ya saka Binna ya fara caca shan giya neman mata da sauransu , wannan aikin duk na Dady ne Bello kuma ya biya mishi buƙatarshi , aikin Bello kuma shine ɗaukar fansa akan abinda Binna yayi mishi na ansar budurcin matarsa , Binna ya gudu shine Dady yace ba'a barin maƙiyi ya tafi ka dawo dashi wurinka yadda yayi maka kaima ka rama , shikenan Bello yaci gaba da jifar "ya "yan Binna da asiri... Duk nice na kawo wannan shawarar amma Ubanki ba "yan uwanshi ba ni kaina sisi ya hana a kuɗin gadon nan , girgiza kai Hafsa tayi tare da cewa har nawa ne kuɗin gadon ? Hajiya tace zunzurutun kuɗi Malam yabar naira miliyan 45 gonaye da kuma gidaje , miƙewa Hafsa tayi tana shafa wayarta tace tou ƙalu bale ga rayuwarku domin ɗiyar Binna ta tiso ƙeyarku gaba dake da Dady ƙaryarku ta ƙare ba abinda ya shafeni kinga tafiya.......tana kaiwa nan ta fice daga gidan. Da gudu Hafsa ta fita tana kuka innalillahi wa'inna ilaihir raji'un yanzu Baba Binna ƙanin Dady ne shine yayi iskanci dani......? Wani irin ihu tayi cewa na bani na lalace ni Hafsa ubana ya kwanta dani ya buɗemin jikinshi na gani , da sauri ta rufe idanuwanta ta dafe kanta , yauni na shiga 3 ni Hassatu na lalace Baba Binna Allah ya rufa maka asiri da baka raye yau da wane irin baƙin ciki zakaji idan har kasan ni ɗiyar ɗan uwanka ce ? Wayyo Allahna ƙanin ubana yayi iskanci dani kaico da wannan tsohuwa , tirr da halinki duk kece silar rushewar komai ni naga tsiraicin ƙanin ubana yaga na "yar sa Sultana kuma taga na Dady , itama ita da Dady kenan sunyi ? Tabbas sunyi shi yasa har ta ɗauko videon girmanshi ta turomin , kai mun shiga 3 mun lalace wani irin ihu ta kurmama tare da faɗuwa ƙasa somamiya..... Kai anshi ka irga kuɗin , Bello yakeyin magana bayan yasa wani matashi ya anso jaka daga hannun Dady , buɗe jakar sukayi amma da mamaki sai suka ga wayam , ce ma Bello sukayi ai babu komai a ciki , ɗago kai yayi da niyar yima Dady magana Dady ya gaggaɓe da dariya yace kana wasa dani kenan ko ? Ai kace idan na kawo kuɗi saika sokamin wuƙa na mutu Bello ka cika tsarabarka da yaji ƙaryarka tasha ƙarya yau nine ajalinka hukuma zata kashe ka da hannunta bayan ta kamaka da hannu dumu² a kisan Sultana , Bello yace ai hukuma bazata kashe ni ba ta dalilin kisan Sultana saida ta kamani ta dalilin kisan ka , idan baka sani ba bara na faɗa ma tun daga ranar da kasa akayimin duka a ofishin "yan sanda duk wani abinda ya faru tsakanin ni dakai tun daga ranar dana fara zuwa wurin Binna ya ɗaga wasu takaddu yace to ka sani yana rubuce anan ciki..... Wannan gurzajjin ne amma na gaskiyar ya tafi zuwa hannunshi , duk halakkacin da nayi maka lokaci ɗaya kasa ƙafa ka shure saboda kai kanaji kana da hukuma a hannunka kai ɗan siyasa tou ka sani nawa siyasar yafi naka , dani dakai yarinyar da muka haifa tayi wasa da hankullanmu lokaci guda wurin ganin ta haɗa mana fitina ta yadda zamu fara muna farautar junanmu , Na ganota ne domin kirana da tayi da layin da ita kaɗai na kirata dashi cewa saina kasheta , na yadda da hakan da tayimin maganar ka ta kuma yimin maganar Sultana , tana tsaye ne a saman ƙafafuwanta wurin ganin taga bayanmu dukanmu gaba ɗaya daga ni har kai , Shi yasa tayi amfani da wasu sirrika data sani wanda kwalwarta da tunaninta ya bata , sai tayi amfani da wannan sirrinka wurin kirana tace kace kaza² kaima saita kiraka wanda haka yasa yanzu kazo min da jaka babu kuɗi. Saboda ka yadda da cewa zan kashe ka ne yayin daka bani kuɗi domin tafiya da gawar Sultana , banzo da ita ba kuma ban kamota ba amma ina tare da duk wani motsi nata , ta fita daga gida bayan sallah azahar misalin 2:31 , wani ne ya ɗauketa a mota bayan Dikko yaje gidansu ya fita kuma yasa an tare hanyar fita da shiga harsai ya gama magana da ita ya tafi , Mota mai lambar kaduna ta daɗe a ƙofar gidan sakamon hanata shiga da akayi cikin gidan , bayan kimanin awowi biyu da wasu mintuna Dikko ya fita daga gidan mota mai lambar kaduna ta shiga , ta daɗe motar sosai sannan ta fito daga cikin gidan bayan mai tuƙa motar ya fito ɗauke da Sultana , Yaje kasuwa central market ya anshi saƙo , daga nan ya wuce goruba road , yanzu haka tana goruba road j ta fita daga cikin mota ta shiga shagon ɗinki a halin yanzu tana cikin farin ciki shin zaka bayar da kuɗi na basu damar kasheta ko kuwa.....? Dady yace takaddun da kake magana ka tura zuwa gareshi waye shi ? Bello yace Dikko ne nayi haka ne domin kuɓutar da tawa rayuwar shin zaka bada kuɗi nace su dawo dasu karsu isa wurinshi ? Har yanzu kana da sauran dama mutuwar Sultana ko kuma taka wace ce ka zaɓa.....? Dady yace amma me yasa ka tura shedar takkadu wa Dikko ? Saboda shine mijinta kuma ya zama dole yasan duk wasu sirrika da yake ta faman bincike babu dare ba rana , na yanke kawai na rubuta komai na tura mishi ta hanyar ɓoye sunana amma na bayyana naka , abinda yasa kuwa nayi haka dan kayi min kuri da hukuma shi yasa na miƙa kaina ga hukumar gaba ɗaya , Kai.... Dady ya faɗa tare da nufa wurin Bello ta haɗashi da bango yace kana da hankali ne ko kayi hauka ne ? Dariya Bello yayi tare da cewa lafiyata garass amma ka sani matar da Mami ta turo ta ɗauki kwalbarnan munyi dukawa matar sosai ta samu ta kubce bayan mun bita bamu samu ganinta ta ɓace mana a cikin asibiti , taje ta ɓoye tayi jinyar sirri a wani wuri daban bayan ta samu sauƙi ta dawo ta duƙufa neman Sultana bata samu ganinta ba amma a bincikenta ta gano Sultana tana tare da DK shi yasa ta tafi wurinshi domin buɗe mishi duk wani ɓoyayyen sirri kenan kaga faɗan yazo ƙarshe , na kashe ko a kashe ni wannan shine muradina domin ni nasan ƙaryana yazo karshe kuma banda sauran dubara ko mafita tunda case ya koma hannun Dikko......... Ka saki wuyana kawai kaje ka fara neman shedar da zaka kare kanka , 45miliyans sai aje ayi ÷ ÷ ɗinsu in to su Sultana........ Kowawa sukaci gaba dayi tsakanin Bello da Dady , dariya Bello keyi domin shi ƙarya yake ma Dady babu wani abinda ya rubuta akaima Dikko amma karuwarshi yaji labarin tana ta zuwa neman Dikko ba'a barinta ta ganshi , kuma yana ta farautar ta har yanzu basu haɗu ba , dan ƙawarta wacce ta bawa Sultana numberta tace zata kirata itace ta bata labarin yaran Dikko sun kamata sunyi mata tambayoyi kuma ɗiyar Binna tana nemanta , tace ta anshi number Sultana amma ta manta bata ajiyeta a wayarta ba , data tambayeta inda Sultana ke zama shine tace tana zaune wurin DK a goruba road... Shi kuma Bello ya girgiza Dady ne dan ya anshi kuɗi a hannunshi amma kamar yadda yace duk wani motsin Sultana yana hannunshi tabbas yana tare dashi... Saida suka gama cakuwa kowa ya saki kowa cikin wahala , saida Bello yayi nishin wahala yace kuma nine na tura yarinyar ka ta zama karuwar Binna , wani irin gumji Dady yayi da niyar riƙo Bello amma ya ruga da gudu ya hau mota ya nufi goruba road domin ganin bayan Sultana dan lokacin da boka ya ibar masa wa'adinsa ya cika , danshi baya iya auren uwarshi gara kawai ya kashe Sultana magana ce ta shari'a kawai ai tayi ana Sign daga ƙarshe ƙotu tacezaiyi gidan yari , Dady cikin ɓaci rai yace ma "yan sanda da yazo dasu suje zai sake nemansu , Hafsa kuwa mutane suka ɗauketa suka mayar da ita cikin gidan Hajiya , aka yayyafawa banza ruwa ta dawo , tana dawowa taci gaba da ihu tana na bani na lalace... Gaskiya Hajiya ke sheɗaniya ce ta bada labari a jarida ina ahalin mahaifiyar shi Ba Binna......? Wato mahafiyar ita Maryam kakar ba Binna kenan wacce ta haifi mahaifiyarshi ina suke...............? Ta tambayi Hajiya yayin data sake tafiya zuwa duniyar suma. Ina zaune a saman kujera shagon ɗinki ana nunamin style Sultan yacemin bari yaje ya dawo kafin in gama zaiga wani abokinshi a road na gaba , fatan dawowa lafiya nayi mishi ya tafi ni kuma naci gaba da dubawa saboda tun farko nace nidai suymin basai na duba ba amma suka tursasani wai indai duba... Bayan na gama zaɓa na miƙe ana auna ni juyowar da zanyi naji kaina ya sara sakamakon Bello dana gani tsaye ya raɓa ƙofa biyu yana kallona , wata irin mummunar faɗuwar gaba naji a dai² lokacin daya fara kwaikwayon muryata cewa kun haɗa kai akan zaku kashe wata yarinya amma shine naji yana cewa sai ya kashe ka , shigowa yayi cikin shagon yana cewa idan baki mata ba da kikayi wannan maganar ai dariya nayi miki , na baki ansa cewa ko wace daƙiƙa saƙo da lungu rana da dare neman sa'ar mutuwarsa nake saina kashe shi. Hihihihihihi yayi dariyarshi ta raini wayau yace zakiyi tunanin banda lissafi shi yasa nayi wannan maganar ? Tou saboda kece kaɗai na siya layin nan , nine nan na kiraki nace saina kashe ki , yasa anata gadinki ya hanaki fita saboda baya so ki mutu shin yanzu yana ina ? Ko ya isa ya tseratar dake daga mutuwa ? Kin taɓajin labarin zafi da radaɗin azabar fita rai ? Hihihihihi ya sake dariya yace ai na manta yarinyar malama ce ba mamaki an baki labari a islamiya yayi maganar dai cikin yanayi na jahilci. Saida ya sake dariya tare da tafa hannayenshi ya ɗora hannunshi a saman kunnenshi kamar yana waya da irin maganata zanzo fesra hotel sanye cikin hijabi da niƙaf napep zai saukeni idan ka isa ka kamani ka kasheni a wurin hihihihihihihihi ya ƙarasa maganar yanayin dariyarshi mai tada hankali sai kuma ya ɗaure lokaci guda yace a maimakon kizo sai kikayi wa Hafsa waya ke mai wayau kika rufzata a rami sai tazo saida ya sakeyin dariya ya fara matsowa inayin baya yaran shago kuwa rugawa sukayi suka fita daga cikin shagon lokacin da suka ga Bello ya fiddo wata irin shareriyar wuƙa daga cikin rigarshi yana cewa rana dubu na ɓarawo rana ɗaya cif shine na me kaya yau gani gaki bankwana da duniya , ya ɗaga wuƙarshi ya nufo dai² saitin zuciyata dashi........... Yana cewa ba kin kirani cikin dare ba ni kuma na faɗa miki cewa zan kashe shi misalin 10 dai² na safiyar yau , kina tunanin ina cikin maye ko ? Tou kwalba biyar na shanye a daren amma kaina baya manta komai , idan kin isa barzahu lafiya kicewa Binna zanzo na yayyafawa kabarinshi giya kwalba biyu ta tayashi murnar isowar uwar masu gida wurinshi.... 01/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 69 Hihihihihihi yayi wannan munafikar dariya da bana so , saitin wuyana ya ɗora wuƙar dai² maƙoshina lokaci guda na ɗauke numfashina zufa ta ketomin hawaye suka ci gaba da gangarowa nabi Bello da kallo , dariyar ya sakeyi tare da jan majina , yace kin tuna kika tuɓeni kika ɗaukeni video ? Ka turo da dubu ɗari biyar idan ba haka ba zan watsa su a yanar giza gizo , yayi irin magana na , dakel na haɗi yawun bakina cikin tsoro nace wai me kake so da rayuwata ne ? Bana buƙatar komai a halin yanzu sai mutuwarki , bara in faɗa miki abinda kika kasa sani nine nan na kashe Binna da hannuna , kuma nine na toshe miki kwalwa na maidake kidahumar ƙarfi da yaji nine na haɗa Binna da Hafsa da Amisty suka zama karuwanshi , haka yake jerasu a layi ya hau akan ɗaya ya sauka ya hau ɗaya , nine nan na shirya komai ta yadda ya faɗa wasan caca shine kawai zai fita a caca nayi na mayar dashi ya ƙiya saboda kawai yayi miki alƙawari ya daina yaso ya lalatamin tsarina ne ni kuma kawai na kashe banza , to me Babana yayi maka haka da zafi ? Ke matar da nake so ya maida ita zawara a ranar da nake farin ciki zan shiga daga ciki , da farko na barshi ta tafi Yayan Babanki ya zugani na dawo dashi ni kuma na hura wutar ɗaukar fansa a zuciya , zan gama da matsalar Binna dake na koma wurin ɗayan ɗan iskan saina ƙare kaf ahalinku dan bana buƙatar ganin jinin Binna a saman doron ƙasa , kauda kaina nayi gefe ɗaya ina wani irin gumji nace kaine ka kashemin min Babana......? Nine na kashe shi ko in nuna miki irin zamiyar da kikayi a jikin gawarshi ne ? Yadda nayi ya nunamin kina cewa wayyo Babana karka ka tafi ka barni tashi Babana baza ka mutu ba gani nazo , buɗe idonka kar kayi bacci uwar masu gida wayyo Babana yi murmushi hihihihihi yasha majina jeki....... Ya faɗa tare da so kamin wuƙa a kafaɗata wanda ba haka yaso ba zuciyata ya saita kuma a samanta yaso wuƙar ya shiga... Wani irin ihu nayi tare da haɗa hannayena wuri ɗaya 🙏🏻idona yana tsiyayyar da hawaye nace na roƙeka karka kasheni , wata "yar iskar rawa yayi da ƙugunshi yace ke kina tunanin zan barki ki rayu bayan nace miki nine na kashe Binna ? Cikin kuka nace ai banji ba , hihihihi yaja majina ƙazamin banza yace sai kin mutu...... Ci gaba yayi da yankata ina gocewa yanka 3 yayi min a kafaɗa wuyana da bayana , ta ƙasan sa na sulɓe nayi waje da gudu ina ihu , biyoni yayi da wuƙar tsabar toshewar basira yana saina hallakaki nine ajalinki wallahi baki wuce yau sai kin mutu , masu ɗinki da suka fito suma tuni sun tara taron jama'a dan a kawomin taimako , jini sai zuba yakeyi a jikina ina gudu Bello yana bina , da gudu na shigo titi zan tsallaka road in da gidan Dikko yake fitowarshi kenan zai fita , ina dafe wuyana na fara ɗaga hannu dan motocin suna san su wucemu ne , wani irin ihu nayi nace Dikkkkkkkkow na tun kari motocin da gudu kai tsaye , wani irin burki Ashiru ya taka ni kuma na juya dan jin maganar Sultan shine fa Bello ya samu damar sokamin wuƙa a ciki yana cewa saina kashe ki , wani irin yunƙurin amai nayi kamar raina zai fita na ɗagawa Sultan hannu dan bana iya magana.... Da gudu Dikko ya fito daga cikin mota ya zaro idanuwanshi kamar zasu faɗo ƙasa yace me zan gani haka ? Shima Sultan da gudu ya nufo wurin , wani irin gurnani Dikko yayi cikin wata irin murya yace An mata , tare suka iso wurina dashi da Sultan , Sultan yana ƙoƙarin riƙeni Dikko yayi mishi wani irin halbi ya koma can baya wurin motarshi ya faɗi ƙasa , rumgumeni yayi a jikinshi ya riƙe hannu Bello tare dayi mishi wani irin kallo cikin kuka yace An mata me yasa haka ? Bana iya magana kwata² saboda ina tafiya wata rayuwa daban , cikin rawar murya yace riƙeni An mata riƙe Dikkonki ina tare dake babu abinda zai sameki riƙeni mana , ko motsin kirki bana iyawa Dikko kuwa cewa yakeyi daina kuka an mata ba gani nazo ba , yayi maganar cikin sigar tausayi. Riƙon da Dikko yayi ma Bello tsabar firgita yasa shi ya suma , jinjina kai Dikko yayi tare da cewa Ashiru ku ɗaukeshi ku shigar min dashi ciki idan na dawo saina tillashi cikin ruwa kada ta cinye shi , ƙasa sukaja banza har zuwa ciki , Dikko kuma ya ɗauki Sultana yayi mota da ita a baya ya zauna yana rungume da ita hawaye yana fita daga cikin idanuwanshi , da gudu Ashiru ya fito daga ciki bayan ya rufe Bello a ɗaki yazo ya shiga mota yaja suka ɓace daga wurin kamar walƙiya. Sultan kuwa dakel ya tashi ya shiga mota a wahalce yayin da yake tunanin meya haɗa Sultana da Dikko ? Mutumin da baida mutunci ya raina mutane baisan darajar kowa ba , bai damu da halin ƙunci da wani zai shiga ba kanshi kaɗai ya sani bai san kowa ba , tare da cikin wanda Sultana ta kawo ɗinki shagonsu Sultan ya ɗauki ɗaya sukabi bayan motar Dikko amma iyakar kokontonsu motar ta ɓace babu wanda yasan ta inda tabi ta wuce , Tunda Bello ya tafi ya koma mota dakel zuciyarshi tana mishi wata irin babbakar babbaka kan ragon layya , yana tunanin maganar Bello { nine na tura yarinyar ka ta zama karuwar Binna } kai...... Yayi ihu tare da kaima sitiyari duka yace Allah ka rufamin asiri wannan labarin ya zama a bacci nakejin shi , na shiga 3 ƙanina ɗiyata ta zama karuwarshi wayyo Allahna tada motarshi yayi ya nufi gidanshi cikin tashin hankali , ko da yaje Hafsa bata nan daya tambaya mahaifiyarta tace tana ƙofar marusa gidansu. Cikin tsananin tashin hankali ya fito yaci taya ya nufi ƙofar marusa , a halin tashin hankali ya samu Hafsa data farfaɗo daga suma sai tace wayyo Allahna Ba Binna saita koma luww , ita Hajiya bata san suna Binna ba ita Aliyu ta sani , Dady kuma shi yasan Binna , Hafsa na sake dawowa Dady yace Hafsa me Binna yayi miki ne ? Dady me yasa ? Ya akayi kuka bari duniya ya ruɗa Hajiya ? Kun watsa kan gidanku kun gurɓata familynku ƙani yayi tarayya da ɗiyar Yayanshi , Yaya kuma yana neman ɗiyar ƙaninshi kaico da wannan ahali tirr daku , mutuwa kizo ki tafi da Hafsatu ina zamu kai wannan abun kunya , tashi tayi da gudu ta nufi rijiya tana cewa saina faɗa wallahi saina faɗa dakel aka riƙe Hafsa , tana ƙwacewa tayi kicin da gudu ta ɗauko galan ɗin kalanzir ta ɗagashi taci gaba da kwankwaɗa shima dakel Dady ya kwaceshi bayan tasha ta ƙoshi layi ta farayi tana mutuwa kizo taho na shirya taho ki tafi dani wurin Ba Binna ,.... Tun tana layi har ta faɗi ƙasa tana cewa kai waccan Hajiyar ƙarshenki bazaiyi miki kyau ba tsohuwar munafika "yar gadon san abun duniya mai kwaɗayin duniya kuma wallahi saikin mutu mutuwarki bazai miki kyau ba , tirr da hali irin naki azzalimar tsohuwa tari Hafsa ta farayi ƙuhul׳ sannan tace tsabar maitar duniya tou idan baki sani ba Aliyun da kike magana shine yayimin ciki kwanakin baya.... Wani irin juyi Dady yaji duniya tayi masa da gudu , cikin kuka Hafsa tayi dariya kamar mahaukaciya tace da nasan Ba Binna ƙaninka ne idan na bari an fitar da cikin nan Allah ya tsinemin albarka saina haifeshi idan namiji ne sunanka zan saka masa da mace ce sunan mayya Hajiya zan saka , wani irin ihu tayi tana cewa ni nafi san mutuwa dan Allah mutuwa kizo ina nan ƙofar marusa gidan Hajiya kizo ki tafi dani bana san rayuwar gaba , cikin kuka Dady yace ki daina kuka Hafsa bazaki mutu ba , girgiza kai tayi cewa mutuwa itace kaɗai natsuwa a gareni.... Murmushi tayi mai ciwo cewa Ba Binna ɗan gayu wayayye dashi ɗan boko kisan farko amma tsabar mugunta kuka molaƙe tare da tamiƙe mishi rayuwa , bazan manta ba nace masa Ba Binna ciki gareni fa , yayi murmushi yace Doughter ya akayi kika yi ciki ? Ko ƙauye fa an waye a binni sai kawai kikazo kika kwanta kika kwashi ciki , yana cemin Doughter saboda "yar sa ashe ɗiyarshi ce ta gaskiya...........? Nace masa Baba yanzu ya za'ayi nima bansan yadda za'ayi ba , na tursasa masa akan a fitar da cikin ya nuna shifa ba ruwanshi bana san ɓacin ransa dan idan ya juyawa abu baya ya gama dashi ni kuma bana san rabuwa dashi shi , ku kuma gida da kuka gane ina da ciki kukaje kuka zubar dashi , Allah duk mai sa hannu a kisan Ba Binna ubangiji ka tagayyara mishi rayuwa...... Tari ya ƙwace mata sosai mimmiƙewa tayi kamar wacce ake zare ma rai ta sake somewa , ɗaukarta akayi itama aka nufi asibiti da ita. Wata irin dariya sukeyi gaba ɗayansu suna cikin farin ciki tsakanin Jiddah da Mardiyya Al ' Ameen yake basu labari cewa yaufa an shafe labarinta a duniya , Mardiyya tace Uncle kana wurin ne ? Al ' Ameen yace bana nan Nabeela ta aikeni gidansu ƙawarta ina shiga goruba naga banzar ta fito guje kinji daɗin da naji ? Shi kuma ya biyota da wuƙa ina ta murna za'a kashe ta kawai sai naga mai gida ni kuma na ruga banma tsaya ba kar yace hadani , bayan na dawo daga inda zanje nake tambaya akacemin ai ta mutu... Cikin jin daɗi Jiddah tace damuwa ya ƙare , Mardiyya kuma tace Uncle mun goge ƙatuwar damuwa danni wannan matsalar ta gabana kallon ciki sati ɗaya nake mata , Jiddah bata san da ita ake ba ta rungume Mardiyya sukaci gaba da murna.. Misalin 9:00pm Sultana ce kwance saman gadon asibiti bayan likitoci sunyi mata duk wani abu daya kamata na bata kariya daga yanka²n da akayi mata , su 3 ne a ɗakin Sultana Ashiru yana tsaye gefen gadon Dikko kuma yana zaune saman kujera gaban gadon ya kwantar da kanshi saman gadon yana tunane² , Ashiru ne ya matso kusa dashi ya miƙa mishi wayarshi cewa mai gida maman Sultana ke kira , ansa Dikko yayi ya kara wayar a kunnenshi bayan ya ɗauka. Cikin kuka Inna tace Dikko me ya faru ne ? Sai kirana akeyi Sultana bata lafiya ance ɗan gwamna ya tafi da ita me tayi mishi ne ? Me tayi mishi ? yaro mara mutunci tun ina tare da mahaifinta ya addabi rayuwar Sultana yanzu kuma meya sake dawo dashi cikin rayuwarta ? Sassauta kukanta tayi cewa ina Sultana........? Murmushi Dikko yayi da gefen bakinshi yace Mama waye ɗan gwamna ? Ni ina zansan ɗan iska mara mutunci , kin taɓa ganinshi ne ? Kuma ya akayi kika san ya shiga rayuwar An mata ? Nima ban sani ba , ban sani ba tayi maganar tana sake fashewa da kuka , Dikko yace Mama me kike so ayima ɗan gwamna ne ? Ni ya fita daga rayuwar ɗiyata kawai , idan yace bazai iya ba ya zakiyi dashi ? Saima ya fita tunda ba tare aka haifesu ba dan ubanshi , jinjina kai Dikko yayi cewa to karki damu ina tare da ita a halin yanzu , kana ina ne ? Muna asibiti faɗa mata asibitin yayi tare da kashe wayarshi. Miƙewa Dikko yayi cewa Ashiru zanje gida zan dawo misalin 1:30am bana san kowa ya zauna duk wanda yazo yaga An mata kace ya tafi kawai asibiti bata buƙatar majinyata , jinjina kai Ashiru yayi alamar gamsuwa shi kuma Dikko ya fice daga ɗakin da sauri.... Ba'a wani ɗauki lokaci ba Sultan ya iso dashi da Kaka da Mami sai Abba su kaɗai suka zo , dan yayyen Inna cewa sukayi Allah ma yasa ta mutu uban kowa ya huta da jinin katafi² , gaba ɗayansu sun tausawa Sultana , sun daɗe a asibitin ganin Abba da Mami zasu tafi yasa Ashiru yace Hajiya ai kin ganeni ko ? Eh na gane ka kaine ka maido Maryam gida , Ashiru yace yawwa tou kuyi tafiyarku gida nan suna da malaman jinya , gaba ɗayansu suka tafi amma nayi imani da ɗiyar wani ce a cikinsu babu yadda za'ayi su tafi su barta da wannan darjejen ƙaton a ɗaki. Yaya kace idan ina da buƙatarka na sanar dakai , Jiddah ce tsaye a gaban Dikko dake saka kaya take mishi wannan maganar wani irin kallo Dikko yayi mata cewa yanzu kina da buƙata na ne ? Eh , idan mace tana san kasancewa da mijinta ai bada baki take faɗa ba tunda ba magana bace da zaki faɗa na baki ansa , matsawa yayi ya kamota jikinshi yana cewa waye yace da baki ake neman miji ? Murmushi Jiddah tayi shima murmushi yayi dan Allah ya sani dama a takure yake baya so ne ya shiga haƙƙinta shi yasa ya ƙyaleta harsai ta buƙata da kanta , yana riƙeta ya aika mata da takardar neman yarjejeni babu ɓata lokaci Jiddah ta amince gado suka koma Dikko yaci gaba dayi mata sign...... Bayan sati ɗaya ! Na samu sauƙi sai abinda ba'a rasa ba , kuma duk kwanaki bakwai ɗin nan Dikko yake kwana dani Ashiru kuma saiya tafi , idan safiya tayi Ashiru yake dawowa su yini da Kaka Dikko kuma sai dare yake dawowa ya kwana , Hafsa kuwa saida aka saka mata wata roba a gefen cibiyarta ake fitar da dattin kalanzir in data sha dan ta ɓanɓameshi da yawa , ita kuma Amisty ke jinyarta idan Amisty ta yini sai Mom inta ta kwana. Ga hidimar aurena kuma babu abinda aka fasa har an gurzo katinan ɗaurin aure nima na ansa na ajiyewa Dikko nashi idan yazo da daddare zan bashi dan idan Allah ya kaimu gobe lafiya akace za'ayi sallameni kuma Inna itama gobe zata dawo idan Allah ya kaimu muna cikin masu rayuwa. Bello kuwa yaci duka na bala'e a wurin Dikko saida ya lalata mishi ido ɗaya sannan ya tambaye shi abinda ya haɗashi da An mata ? Bello yace ba komai , Dikko yace jin daɗi kawai kakeji ka kasheta ? Bello yayi shiru Dikko yace tou ko ka faɗamin abinda ya haɗaku har ka yayyakata da wuƙa ko kuma na jefaka cikin ruwa kada ta haɗeye ka banza , Munafinci yayi ma Dikko yace wani Yayan Babanta yasa shi ya kasheta saboda tana ta tayar da hankali ta anshi gadon su shine ni kuma ya bani kuɗi yace na kasheta , waye Yayan Baban nata ? Inda Dady yake zama da number wayarshi Bello ya bada , Dikko yace aje a ɗaukoshi cikin mintuna biyar , motoci suka hau suka tafi ɗauko Dady dan tunda Bello ya suma daya farko yaga Dikko sai ya koma yauma abinda yasa bai suma ba Dikko yace kana sake somewa wallahi saina sa an rufe ka da ranka..... Bayan masu tafiya ɗauko Dady sun tafi Dikko ya kalli Bello yace dama kai ba wani ba inajin haushin ka dan ubanka yayi maganar yana yankawa Bello wani zaburarren mari harsai da haƙorinshi na ƙurya ya fita , Dikko yace ka ganeni ko ? Yayi maganar yana kai mishi wani irin halbi harsai daya fitar da jini daga bakinshi , duk kaine matsalata wai meme yasa bazan kashe ka ba.......? Da ido ɗaya ya kalli Dikko dan ɗayan ya daina gani kwata² cewa kayi haƙuri , Dikko yace ai dama ba yanzu zan kashe ka ba kana tunanin zaka mutu cikin sauƙi ka sokawa "Yar matana wuƙa ? Kayimin tabunna a jiki matata ? Ka san irin mutuwar da zakayi ? Bello yayi shiru , Dikko yace to kullum saina reɗi sokar jikinka ina ba karnuka harsai ka ƙare. A dai² lokacin da aka shigo da Dady , bayan an fiddoshi ne Dikko yaga mijin ƙawar Momy ne , ƙasa da sama ya kalleshi cikin kallon rainin wayau sannan yace ku tattarsu ku tafi dasu , jan Bello akayi aka sakashi a mota shima Dady mota ya koma suka tafi dasu daga gidan , shi kuma Dikko ya nufi asibiti.... A asibiti ya samu Sultan , fuskar nan a haɗe ba ɗan sakin fuska ni bana san wannan ɗabi'ar kullum ran mutum a haɗe kamar an aiko da saƙon mutuwa gareshi , wani irin ƙazantaccen kallo yayi ma Sultan dole tasashi ya tashi daga saman gadon ya nufi kujera zai zauna amma Dikko ya janye kujerar da ƙafa ya matso da ita kusa da gadon ya zauna yana cewa kinsha magani , Banza nayi dashi ban bashi ansa ba na kalli Sultan nace kazo ka zauna mana , murmushi yayi tare da cewa ai tafiya ma zanyi , nima murmushin nayi cewa karkaje yanzu ka tsaya , kallon agogon hannunshi yayi yana cewa dare yayi bara inje sai Allah ya kaimu Allah ya tsare hanya nayi masa yayi ma Ashiru saida safe ya fita , yana fita Dikko yace Ashiru saida safe , fita Ashirun yayi bayan yamin saida safe... Ashiru yana fita yaje ya rufe ƙofar da makulli ya dawo ya zauna kusa dani yace idan ina miki magana baki bani ansa saina ɓata miki rai "yar rainin hankali kawai , gyara zama nayi cewa ai dama saboda baƙar zuciyarka yasa bazan iya aurenka ba nayi maganar tare da ciro katin ɗaurin aurena daga ƙasan pilo na miƙa mishi cewa wallahi Dikko ina sanka amma bazan iya aurenka ba har abadan duniya , Ansar katin yayi yana murmushi , ni kuma naci gaba da cewa kai a rayuwarka babu abinda ka sani sai zafin kai , doke² , ɗaure fuska gaka mahaukaci ga aljannu kamar iccen tsamiya ni taurin kai , kai kuma zuciya talauci da arziƙi basa zama wuri ɗaya dole idan ɗaya yazo ɗaya ya tafi , idan arziƙi yana nan talauci zai tafi , idan talauci yana nan arziƙi yazo dole talauci zai kama gaban shi , naji shi wannan ɗin kina sansan ne ? Eh ina sansa , tou ai ba akomai An mata nima da kika ga na kafe kai da fata na aureki bawai dan ra'ayina bane ba a , a muradin zuciya ne itace ta tirsasa amma farin cikinta a kullum bai wuce ta ganki cikin farin ciki ba , duk yadda take sanki dole zata kulle ne idan taga kin samu inda zakije kiyi farin ciki , kin gane ko ? Kallona yayi da kallonshi mai tayar da tsikar jiki yace ina miki fatan alkairi ubangiji yasa alkairi ya baku zaman lafiya ai da kin faɗamin tun a gabanshi dana mishi Allah sa alkairi kuma saina riƙe hannunshi in jinjina masa cewa ina tayaka murna namiji mai sa'ar rayuwa. Faɗamin yanzu me kike so na baki gudumuwa a matsayina na babban abokin amarya ? Yayi maganar cikin ƙarfin hali damuwa kwance a idonshi , bana san komai domin babu abinda ba'ayimin ba a gidanmu , murmushi mai ciwo ya sakeyi cewa yi haƙuri ai badan sun gaza ba abokin amarya fa.....? Nace bana so , da hannunshi ya nune cewa to , to yi haƙuri ya canja maganar da cewa maganar wasu kuɗin gado da kike ta wahalar da kanki ba dare ba rana kiyi haƙuri ki daina maganar kuɗin ki faɗamin adadin miliyoyin da kike buƙata na baki ki bawa "yan gidanku a rufe matsalar , kallonshi nayi cikin idona nace ko naira ɗaya ne saina ansa domin wannan gadon shi zaisa na tabbatar cewa shima Babana yana da galihu , ganin na hasala da yawa ya miƙe yana warware kafet cewa bazance komai ba amarya tsautsayi gareta lallaɓa ta akeyi , a dai² lokacin daya dawo ɗaukar wayoyinshi na watsosu ƙasa ina kuka , baimin magana ba ya duƙa ya ɗauka ya koma saman kafet ya kwanata yana latse²nshi a waya. Da gudu na sauko daga saman gado na koma wurin Dikko ina kuka , juyamin baya yayi ya sargafa bluetooth a kunnenshi fuskar nan babu wasa a cikinta yaci gaba da abinda ya shafeshi , gabanshi na koma cikin kuka nace bana sanka , murmushi yayi da gefen bakinshi hawaye kwance a idonshi yana kallon wayarshi amma baiyimin magana ba , Gemunshi na fizga cikin ɓacin rai , wata "yar ƙara yayi kaɗan cikin salon ɗaukar hankali wani abu naji yanamin yawo a jiki , gyara gemun yayi yana cewa saina dakeki zakije kiyi bacci ko ? Cikin kuka nace ka dakeni da Allah dakeni Dikko na ƙarasa maganar ina shiga jikinshi , da sauri ya fizgi wani irin numfashi ya fitar dashi ta bakinshi tare da lumshe idanuwanshi ya sauke ajiyar zuciya a wahalce cikin murya mai sa mutum ya shiga yanayi yace An mata fita daga jikina don Allah , bazan fita ba , yi haƙuri An ma fita kinji "Yar matana yayi maganar cikin sigar lallashi ƙara riƙeshi nayi ina kuka da ƙarfin bala'e ya ɓanɓareni daga jikinshi ya mareni , da sauri na tashi na koma saman gado na kwanta ina kuka , tsoki yayi ya koma ya kwanta cikin ɓacin rai yana magana ƙasa². Kuka naci gaba dayi ni ba kukan marin nake ba kukan rabuwa da Dikko ne jibi kamar yanzu ina gidan Sultan , cikin kuka nace kuma ko rarrashin mace baka iya ba , ban iya ba kuma bazan iya ba , tunda kin samu wanda zai lallashe ki sai kije ya lallasheki , ai dan bayanan da kaga yadda ake tarairayar mace , waye yace namiji sai a gaban mace zai tarairayeta ki kirashi a waya yanzu ba kina da number shi ba ? Kirashi yasa ya miki natsuwa sakaran banza mai baƙuwar soyayya , bazan kira ba , sai Dikko da kika raina.......? Mtsw kimma ja ma kanki bara in sake jin ko tarinki kikaga yadda zanyi sukuwa samanki "yar yarinya kawai dake. Shiru nayi tare dajan bargo zan lulluɓe yace sauka ki kashe mana waccan fitilar da kika kunna ma mutane , murguɗa bakina nayi ban sake ko motsi ba har bacci ya ɗaukeni kuma ban kashe fitilar ba , shi baya san kwanciya da fitila yace idan fitalar ɗaki yana a kunne wai ƙwalwa bata daina aiki , idan aka akashe shine itama kwalwa zata huta , Dikko kuwa jin Sultana tayi shiru ya tabbatar mishi da tayi bacci tashi yayi cikin damuwa yazo gaban gadon ya ƙurawa An mata ido a zuciyarshi yace wannan "yar yarinya Allah yayi mata tsatstsagar masifa , Allah yasa mijin naki yayi haƙuri da yarintarki ubangiji yasa ya riƙeki da amana Allah ya wadata mishi zuciyarshi da tausayinki An mata , haka Allah ya hukunta bani ne nake da rabo akanki ba saboda rashin haƙuri na cinye nawa rabon tun bisa titi... Ina sanki ׳ Allah ka bani haƙuri da dangana akan rashin An mata , a bayyane yace haƙuri ma ai ya zama na dole haka Allah ya ƙaddara yadda da ƙaddara kuma imani ne , kashe fitilar yayi ya koma ya kwanta yana ta maimaita kalmar Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un , a wannan dare har garin Allah ya waye Dikko baiyi bacci ba yana cikin tashin hankali. Misalin 11:09am aka bamu sallama , Sultan yazo ya ɗaukeni Dikko yayi mishi fatan alkairi tare dayi mishi nasiha wai An mata yarinya ce ya lallaɓata idan kuma tayi mishi laifi yazo ya faɗa mishi shine kaɗai maganinta , murmushi Sultan yayi yace ai baza tayi ba , Dikko yace ina san haka kuma a kula ta riƙa shan magani akan lokaci Sultan yace insha Allah har zamu tafi Dikko ya dakatar da Sultan yace inzo fita nayi naje wurinshi gefe muka matsa wurin motarshi yace An mata nasan kina da rufin asiri kuma duk wanda ya rufawa wani asiri Allah zai rufa mishi duniya da lahira dan Allah karki sake kiba kowa labarin abinda nayi miki ki rufamin asiri don Allah kinji ? Fashewa nayi da kuka ina ƙoƙarin rungumeshi yaja baya yana cewa mijinki yana kallonki jeki Allah yasa alkairi ngode. Cikin kuka na koma mota Dikko ma ya shiga tashi yaja shine gaba mune baya , yana fita ya ɗauki hanya da tuƙinshi na ganganci kafin na ƙetfa ido tuni ya ɓace ko ƙurar motarshi babu , ci gaba nayi da zubar da hawaye yanayin Dikko yana burgewa komai nashi nidai yayimin Dikko yana da shiga rai sosai yana da farin jini amma matsalarshi zafin kai. Har muka isa gida kuka nakeyi , ina fita daga mota nacema Sultan ya bari inyi wanka in dawo yace to.... 02/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 70 *_Shafin nan gaba ɗayanshi sadaukar wane ga masoyan DIKKO a duk in da kuke a faɗin duniya , DIKKO na gaishe ku , ni kuma JAMILA MUSA nake muku fatan alkairi ku kasance a farin ciki , ina gaisuwa gareku domin ni kune maudu'una , farin cikina , gishirin rayuwar littafin KWARATA..._* 🤝🏻 *_na kuma miƙo gaisuwa gareku_* 👇🏻 *AMINA UMAR* _{ Ummieter }_ *HANEEY* _{ MRS KB }_ *HAWWA MUSA* *RABI MUSA* *AUNTY MUSA* *HAFSAT NASEER* *FADEELA LAMIƊO* *HAJIYA A' I QERAU* *SAFINA ALIYU KAROFI* *ASIYA ILU BARDE* { MMN SUDAIS } & *ZALIHA GAMBO RAƊƊA...* A rayuwarka babu abinda ka sani sai zafin kai , doke² , ɗaure fuska gaka mahaukaci ga aljannu kamar iccen tsamiya ni taurin kai , kai kuma zuciya talauci da arziƙi basa zama wuri ɗaya dole idan ɗaya yazo to ɗaya zai tafi , hawaye ne ya gangaro daga cikin idon Dikko bayan ya tuno maganganun da An mata ta jefeshi dasu , murmushi mai yagar zuciya yayi tare da kallon kanshi a madubi yana mai sakeyin murmushi wanda har saida kyawawan haƙoransa suka bayyana. Wai nine mahaukaci ? Duk dana faɗa miki lalurata amma shine kikemin gori wai aljannu kamar iccen tsamiya kwantar da fuskarshi yayi saman sitiyarin mota a bayyane yace bani ne na ɗorawa kaina ba ƙaddara ne kuma haka yazo rubuce a cikin ƙaddarar rayuwata , ɗago kanshi yayi yaci gaba da kallon gabanshi dan tuƙi yake kuma har yanzu baije inda zaije ba , yaci gaba da addu'a ya ubangiji ka bani lafiya ka yaye min wannan lalurar ka bani haƙurin rashin An mata , goge hawayen daya zobo mishi yayi yana ci gaba da cewa wai duk girmana ni nake kuka wa mace , macen ma An mata ashe dama bata so na , wani irin duka ya kaima sitiyari a hayaniyance yace ni kika yaudara ? Nidai kika yaudara bazan taɓa yafe miki ba An mata kuma Allah bazai barki ba saiya min sakkayya ya ƙarasa maganar hawaye na rigangato wurin fitowa daga cikin kwarin idanuwan shi. Har ya isa goruba ranshi a ɓace addu'arshi ɗaya Allah yasa kada wani ya hawoshi a dai² wannan lokacin da yake cikin ɓacin rai dan duk wanda yazo yana cikin wannan yanayi zafa a samu matsala , aljannu kamar iccen tsamiya ya maimaita a dai² lokacin da yayi parking , yanayin parking Yazeed ya fara gani , Fita yayi daga motar cikin tsananin ɓacin rai fuskar nan a haɗe , Yazeed yana ganin Dikko ya taso cikin girmamawa ya miƙawa Dikko hannu , bai anshi hannu ba yace ya akayi ? Cikin rawar murya Yazeed yace DK don Allah wani abokina ne aka kama wata ƙawarshi ta gayyaceshi zuwa gidanta sai mijin ya dawo ya ritsatsu dan Allah kayi magana yana sabon gari police station , Wani irin munafikin kallo Dikko yayi ma Yazeed , a hanzar ce Yazeed yaja baya yana kallon Dikko , tsoki Dikkon yayi ya fara tafiya Yazeed yabi bayanshi Dikko kuma yana magana cewe , baku da aiki kullum an kamaku wurin neman mata , nima yau an kamani na kasa fitowa , banyi maganin damuwa na bare inyi ma wani nashi , ina cikin ɓacin rai ka kama gabanka tun kafin in fara ƙwallo dakai.... DK ka duba lamarin nan don girman Allah kayi wani abu akai matsalar babbace , da sauri ya juyo yace kai........... Ka wuce fa , ganin idanuwan Dikko ba'a launin daya saba ganinsu ba yasashi juyowa da sauri ya dawo baya yana tunanin halin da abokinshi yake ciki. Matsala ce ta neman duniya shi abokin nashi yana da wata buƙata akan wasu harkokin shi nayau da kullum shine malaminshi yace sai ya samo maniyin matar aure kuma saiya nemi matar a gidan aurenta a saman gadon da mijinta yake kwanciya da ita , a jikin hankicif kawai ake so a gogo sperm in shikenan zance ya ƙare , amma zai dawo zuwa anjima idan Dikko ya sauko , zuciyarshi tace a , a kawai kaje wurin Sultana a gabanka zatayi masa waya a wuce da damuwar nan , kai tsaye Yazeed gidansu Sultana ya nufo ! A halin yanzu zuciyata ta cika fal da Dikko , muradina shine naga na haɗu dashi maganar gaskiya so nake na kasance dashi domin inajin Dikko kamar wata runduna ta tsagin rayuwata idan har na bari Dikko ya tafi na shiga3 na tawa ta ƙare , fashewa nayi da wani irin kuka a toilet nace ina sanka ׳ mutumina..... Sai ihu nakeyi a toilet babu mai jina saboda gidanmu cike yake da mutane "yan kawo lefe , kuma gashi gobe idan Allah ya kaimu ɗaurin aurena wanda za'a ɗaura 2:00pm idan Allah ya kaimu , saida nasha kukana har na gode Allah na fito daga toilet ko mai ban shafa ba na saka kayana , wayata na ɗauka na fara kiran wayar Dikko , Ɗauka yayi amma baiyi magana ba , cikin kuka nace Dikko gobe ne fa ɗaurin aurena , Ey ai kin faɗamin jiya da daddare ko kin manta , a , a ban manta ba ƙara tuna maka nayi fa , ina sane ban manta ba , to baza kayi wani abu ba ? Wani abu kamar me ? Shiru nayi ina kuka na kasa magana , Dikko yace Allah yasa alkairi ya baku zaman lafiya ina tayaki murna sosai yana faɗin haka ya tsinke wayarshi.... Wani irin ihu nayi wanda ya jawo hankalin duk wanda ke cikin gidan sukayo ɗaki wurina kowa yana tambayata lafiya ? Kamar baƙuwar mutane haka naci gaba da kallon mutane ɗaya bayan ɗaya cewa ya akayi ne ? Munji kina kuka ne , murmushin ƙarfin hali nayi cewa ba komai ni ba kuka nake ba wani abu ne ya faɗamin a ido , kowa Allah ya sawaƙe yayimin sannan suka fita. Hijabi na saka na fita wurin Sultan dana baro a mota yana zaman jirana , dakel na ƙaƙaro farin ciki na isa wurinshi amma yanzu ban shiga motar ba a waje na tsaya , ki shigo mana , a , a , haka yayimin , bawan Allah ko murmushi baya gajiya dashi yace kodai naje na barki ki huta ne ? Cike da zumuɗi nace Eh , tada motar yayi yana cewa zan anso miki kayanki kinsan jiya mukayi dasu , godiya nayi masa tare da mishi addu'a Allah ya tsare hanya dan na matsu ya tafi wurin Dikko nake so naje , ina tsaye a wuri harya fita daga gidan yana fita motar Yazeed yana shigowa .{{{}}} Inda Sultan ya ɗauke motarshi a wurin Yazeed ya ajiye nashi tare da sauke gilashin gefenshi An mata wurinki nazo , ai na sani tunda na ganka gidan nan dama nasan saboda nine kazo , to dan Allah ki shigo wani wuri zamuje muyi magana naga gidanku cike da mutane , babu wani jayayya ko tambayar ina zamuje na zagaya na buɗe mota na kame a gaba Yazeed yaja muka bar gidanmu! Iyalin Dady suna cikin tashin hankali da damuwa dan tun jiya suke neman Dady babu shi ba labarinshi kuma wayayonshi duk a kashe suke , saƙo da lungu nemanshi ake amma babu wanda yaji ko ɓirɓishin inda yake , cikin kuka Momy tace saika tafi ka saƙe duk ka tashi hankalinmu ? Ka tafi babu bankwana shin wai kana ina ne ? Wani irin gumji Dady keyi bayan an ɓanɓare Dikko dakel daga jikinshi yace baza ku faɗamin gaskiya ba ko ? Bello da wahala tasashi ya koma wata siffa daban tsakanin ranar daya yayyanki Sultana da wuƙa zuwa yau yace ranka ya daɗe wallahi shine yasa ni , yayin da shi kuma Dadyn yake cewa ƙarya Bello ke masa shine Dikko ranshi ya ɓaci yacicci ubansu yana cewa bazasu faɗa masa gaskiya ba suna masa wasa daa hankali ko ? Ya ƙarasa maganar yana ƙara kaiwa Bello halbi a baki. Cikin kuka Bello yace wallahi bani bane shine , Dady yace wallahi ƙarya yakemin shine tunda shi ka kama da wuƙa kuma shi idonka ya gani ya yayyaka mata a jiki ni misali idan ma har zanyi kisa zan faɗawa wani ne ? Koshi sakaraine baisan shari'a ba ? Me yasa da nace yaje ya kashe ta baije ya faɗawa hukuma ba ? Ko zan hura wuta nace masa ya shiga yaje ya faɗa ? Idan har ka duba wannan abun kasan duk ƙarya ne sharri kawai yake nemana dashi bansan abinda nayi masa ba ! Bello ganin Dikko yaɗan so karɓar uzirin Dady yasa yace to ranka ya daɗe tunda naga kanshi ya sani baisan nawa ba kuma naga yana ƙoƙarin fita ni ya barni a ruwa bara na buɗe maka gaskiyar abun yadda shike.... Labari tiryan² Bello ya zayyanawa Dikko kuma ya ƙara da cewa kuma kwalbar da ita matar taje ta ɗauko yanzu haka tana hannun shi , wani irin ihu Dikko yayi yace saina kashe ku.............. Wayyo , wai...... Wai , wai Allahna , kai........... Wai , saina kashe ku wallahi kaine ka mayar min da matata daƙiƙiya ko ? Zai fara duka su Ashiru suka danneshi ƙasa dakel saboda ai har yanzu akwai munafirci a maganarsu abinda su suka fahimta kenan , ya akayi kwalbar ta dawo hannun Bello bayan shi yace wata tazo ta ɗauki kwalbar kuma an bada ita wa wani malami ? Shi malamin ya akayi yasan Bello kuma ya bashi kwalba ? Dole bazasu bar akashe su Bello ba Sultana ya kamata a nemo kuma a nemo inda matar data ɗauko kwalba take , bayan ankai Dikko ƙasa Ashiru ya koma mota da gudu ya ɗauko magani har yanzu Dikko zubar da yaranshi yake duk girmansu duk ƙarfinsu tuni tsoro yasa Dady suma shiko Bello yayi fitsari baisan adadi ba , sunga bala'e da masifar daya girmi nasu , dakel aka sake kai Dikko ƙasa aka zuba mishi magani dole tasa ya ɗauke.... Fiddoshi sukayi suka kaishi mota aka sake kulle su Bello sai mai gida ya dawo , Bello kuma maimaita kalmar matata kawai yakeyi , har yaushe Dikko ya auri uwar masu gida ? Lallai akwai bala'e ɗiyar Binna zata zama matar ɗan gwamna ? Surukar gwamna ? Sam wallahi abinda bazai yuwu ba kenan an ɗaura auren ko kuwa ? Wannan ansar ita ya kamata na fara sani farko kenan , Kwance zariyar wandon shi yayi ya matsa kusa Dady yayi masa fitsari a fuska , nan take ya farko , ɗaure wando yayi yana cewa zaune fa bata ƙare ba matarka ba ƙawar matar gwamna bace ba ? Cikin jin haushi Dady ya tashi ya kama Bello da kokowa yana cewa ni zaka zubawa fitsari ? Bello yace kai da Allah dan ka farfarɗo akwai sauran rina a kaba fa , saida suka caku suka rabu da kansu , cikin wahaltuwa Bello yace kaji wani aikin kuma ko ? Tou idan baka sani ba ɗiyar Binna ta zama matar ɗan gwamna , Da sauri Dady yasa hannunwan shi biyu ya goge fuskarshi tare da yarfarwa , yace aure ? Ta auri Dikko ? Yayi maganar yana fiddo duk girman idanuwanshi , Bello yace ba kana can ka suma ba yace matata kuka mayar min daƙiƙiya yace duk saiya kashe mu , Dady yace sam ba'ayi aure ba , Bello yace idan ba'ayi ba kenan ai zaice budurwarshi , tunda kuma anyi sai yace matata , Dady yace idan anyi auren nan saina rabashi idan kuma ba'a ɗaurashi ba babu ubanda ya isa ya daurashi duk cikar faɗin birnin garin katsina.... An mata kin fito da wayarki ? Yazeed ne yake tambayar Sultana ko wayarta yana hannunta bayan ya samu ƙofar wani gida yayi parking , E na fito da wayata na bashi amsa , An mata dan Allah ki kira DK kice masa yayi waya a sakar min abokina , daga ina za'a sakeshi ne ? Yana sabon gari police station kamashi akayi , laifin me yayi aka kamashi ? Gonar wani ya aura kuma ya samu damar tattare kaf amfanin gona , to ya akayi harya tsaya aka kamashi ? Yankin ya shiga ba ita matar tazo nashi yankin , kaima Yazeed wannan ai ganganci ne , Eh An mata amma dan Allah kiyi ma DK magana yasa a sakeshi , murmushi nayi mai ciwo nace Yazeed zanyi masa amma me yasa wai suke san fasiƙanci da matan aure ne ? Mafi yawancin matan auren sune suke miƙa kansu wa mazajen waje ta hanyar ɓoye kawunansu su masu aure ne , kowa da irin matsalar dake shigar da ita bariki da aurenta , wasu rashi ne na talaucin abinda zasu ci ko sha , wasu kuma rashin basa samun gamsuwa ne wurin mazajensu , wata kuma tana da komai babu abinda ta nema ta rasa kawai ra'ayi ne , Tou su mazan me yake sa suna neman matan waje bayan ga nasu matayen a gida , gyara zama Yazeed yayi cewa mafi yawan mazan waje masu neman matan aure suna nemansu ne saboda matsalolin matansu na gida , wasu kuma suna neman matan aure ne saboda neman wani abu na samun duniya , me yasa dole sai a matan aure ake san samu ne ? Duba girman aure kuma ki tuno daraja wacce Allah yayi masa duk wanda ya ɓata matsayi da darajar aure ya halaka , nidai kira DK a fiddoshi , kayi haƙuri Yazeed gaskiya ni halin yanzu bana tare da Dikko , me yasa ? Haka nan na fita daga rayuwarshi ne dan ina so nima ya fita tawa rayuwar , wai miye tsakaninku ne ? Murmushi nayi a zuciyata nace anzo wurin , kallon Yazeed nayi cewa to kai a naka tunanin meye tsakaninmu ? Wata "yar munafikar dariya yayi yana cewa muje kawai na maida ke gida yanzu banda lokacin magana dan hankalina baya kwance amma zamuyi magana daga baya , yayi maganar yana taka motar muka tafi , saida muka isa gida sannan mukayi magana dukanmu , Yazeed yace zai kawomin wata ƙawarshi matar aure ce amma tana wasan danbe , kinsan miye danbe ? Ya tambayeni ? Nace masa a , a , Yazeed yace aiko yadda kike hakan nan kika shiga harkar danbe abin zai miki daɗi zaki taka matakai masu girma zaki fito duniya zata sanki kuma sai kinfi ƙarfi DK wallahi , Murmushi nayi tare da cewa in banda abinka taya zan iya raba fili inyi wasan danbe da ƙatti majiya ƙarfi ne ? Murmushi Yazeed yayi cewa ba irin waccan danben ba , kawai kidai kije zan turota tayi miki bayanin yadda danben yake , fita nayi daga motar ina cewa Allah yasa tazo lafiya , da amin ya ansa ya fita gidan da gudu lallai yana tare da damuwa , bin bayan motar Yazeed nayi da kallo nace ɗan raini kenan kamar yadda nake kallon kaina a madubi haka nake kallon inda ka nufa , murmushi nayi tare da tinkarar hanyar shiga cikin gida da sauri. Ina shiga palo Inna na fara gani ta kame saman kujera an wani waye an goge ta fito cikakkiyar hajiya ga haƙorin makka tasha kuma wallahi yayi mata kyau sosai , da gudu na ruga na rungumeta na fashe da kuka , cikin jin kunya take ƙoƙarin rabani da jikinta tana kallon idanuwan mutane ita a dole sai tayi alkunya irin tasu ta fulani , ke saukar min a jiki cikin kuka na sauka ina kamo hannunta cewa Inna zo kiji , da yanayin tausayi ta kalleni ta taso kuma ta biyoni , ɗakina muka shiga muna shiga na rufe ƙofa na sake ɓarkewa da kuka nace Inna nidai tsakani da Allah bana san auren nan..... Cikin tashin hankali ta kalleni tace Sultana ki rufamin asiri wannan maganar ma ki barta tun farko , ni gaskiya bazan barta kawai kice wani abu na rantse da Allah bana aurenshi nidai bana sansa kawai biyayya nayi ma Kawu nayi tunanin zaicemin ko ina da wani da nakeso amma sai bai tambayeni ba , Inna tace aiko dai ko zaki mutu wallahi auren nan babu fashi ni zaki tona ma asiri dan ubanki , kinsan bakya sansa uban wa yace tun farko kika amsa musu , bakisan halin mutanen ba kina wasa da sha'aninsu ko ? Cikin hayani nace nima kina wasa da nawa sha'anin bari in fita na faɗa musu bana san Sultan , Sultan in banza Sultan in wofi , wani irin wawan mari Inna tayimin , kamar zan hau bori nace wallahi bana auren Sultan saidai ki kasheni , to na yadda saidai ko ki mutun , aiko bana mutuwa zanje na faɗa musu bana san Sultan tunda ni ba tsoronsu nakeji ba na tunkari hanyar fita zan buɗe ƙofar ɗakin , fizgoni tayi ta maidani saman gado ita kuma cikin damuwa ta buɗe ɗakin ta fita ta kulle da makulli ta waje , da gudu na sauka daga gado naje jikin ƙofar naci gaba duka ina cewa bana so ׳ wallahi , Inna kuwa palo ta koma ta ɗauki wayarta ta kira Dikko , yana ɗauka ta fita waje bayan sun gaisa tace da Allah na dawo kazo ina san ganinka idan baka komai , lafiya dai Mama ? Ya tambayeta , gaskiya ba lafiya Sultana tana so ta sake tado min wata fitina da "yan uwana , bayan an tsayar da ranar aurenta duk kwanakin da suka wuce batace ta fasa ba saboda Allah saida taga gobe²n nan ɗaurin aurenta Dikko tace ta fasa ? Na rasa ya zanyi duniya Allah yayi ma Sultana taurin kai , murmushi Dikko yayi tare da cewa me ne ne matsalar ? Nidai kazo yanzu²n , zanzo idan anyi isha'e , a , a Dikko yanzu dai , gani nan zuwa........ Cikin ƙanƙanin lokaci Dikko ya iso Inna tayi masa jagora har ɗakina , Dikko yana da raini tsabar rainin shi duk mutanen dake palon ko ɗaya babu wadda Dikko ya gaishe da , haka ya wuto su yana musu kallon ƙyankyanmi fuskar nan haɗe kamar hadarin tsakar dare har ɗakina , ina kwance saman gado ina ta kuka dan na gaji da bugun ƙofa har na koma na kwanta. Bayan sun shigo ne naji Inna tace ina zuwa ta fita , shi kuma ya shigo cikin ɗakin har bakin gadona kuma bai cire takalmin ƙafarshi , kallo ɗaya nayi masa na juya mishi baya naci gaba da kuka , jawoni yayi daga saman gadon na fizge na koma na kwanta , cikin rarrashi yace zo inji waye ya taɓamin An matana ? Taho ya miƙo hannunshi , saukowa nayi daga saman gado naje kusa dashi na tsaya , kallona yayi sosai sannan ya kamo hannuna na dama ya ɗora saman kafaɗarshi ya riƙe tsakiyar bayana yace kallarni yayi maganar yana murmushi , kallonshi nayi ina kuka , wai me ne ne ? Dikko ya tambayeni , kwanciya nayi saman ƙirjinshi nace bana sansa , ke yar raini bana so kinaji na ? Kinga zaki tayar da hankalin Mama kiyi haƙuri kinji jaruma ta ? Dikko nidai bana sansa don Allah nayi maganar cikin kuka sosai ina mai ɗagowa na kalleshi , ƙarya kikeyi da bakinki kika faɗamin kina sansa kuma na tambayeki yayi miki kika ce min yayi sai yanzu kice kin fasa ? Baya yuwuwa wallahi duk wanda ya tsaya miki sai an ɗaura auren nan kuma babu gudu babu ja da baya , wallahi ko na tafi kika sake cewa bakiyin auren nan zanzo in tafi dake goruba jawoni yayi a jikinshi sosai sannan ya shafa bayana da lallausar hannushi yana cewa zakiji a jikinki , da sauri ya ɗagani jikinshi jin ana shigowa. A dai² lokacin da Inna ta shigo tana ta faɗa cewa ai dama nasan duk yadda akayi Sultana tana da maziga ashe wai wani tsinan yaro ne ɗan mara mutunci take tare dashi , kusa dani ta matso ta yayyanka min mari tana cewa meya haɗaki da Dikko ɗan iska yaron da baya ganin kowa da mutunci garin nan , ke banda kike jaka marar tunani duk wulaƙanci da tozarcin da Dikko yayi muku kin manta ? Tou idan kin manta ki tuna saida Dikko ya haramta muku mazaunin gida , gararin rayuwa wane ne bakuyi ba sanadin shi ? Ki rasa abokin tarayya sai mutumin da silarshi kika yanki tikitin shiga karuwanci , sassauta murya tayi cewa ban san Dikko na tsaneshi matsashi mai ɗagawa da baisan darajar kowa ba , yau da zanga Dikko dasai na ɗauki wuƙa na soka mishi a ciki ya mutu tsabar wutar ƙiyayyar shi dake ci a cikin zuciyata , Kin samu za'a rufa miki asiri wawiyar banza a aureki amma da yake ke jakace har kike tunanin zaki ce kin fasa idan banda ma Allah yasa Sultan ɗin mai imani ne an faɗa miki zai iya aurenki ne ? Tou Allah ya rufa miki asiri ma yaso ki a haka da duk katsina kin rasa mijin aure , wayata taje ta ɗauko ta kawo ma Dikko tace ka duba cikin wayar ka ganomin lambar ɗan gwamnan ka kirashi yanzu²n nan ka rabashi da Sultana... Daga ni har Dikko kallan kallo muke ma juna , cikin jarumta Dikko yace Mama ke baki san Dikko ba ? Ina fa zanso sanin lalataccen yaron nan , to amma waye yace miki yana tare da ya nuna ni , Sultan yake faɗamin yanzu yace ko rashin lafiyar da tayi Dikko shine yake kwana da ita kirawoshi.... Kallona Dikko yayi sannan ya kalli Inna yace ai ba buƙatar kiran shi , me yasa ne ? Inji Inna , saboda Dikko tuni yazo , yana ina ne ? Nine *DIKKO* kuma nine *DIKKOn* da kike nema........... Gani nazo! 04/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 71 *_Don Allah nidai ina roƙon alfarma wa mutanen da suke ɗaukar tsohon page ina suna saka mishi sabuwar number , abinda nake nufi misali sai a ɗauki page 1 a saka masa page 2 bayan ba labarin bane ba tou na roƙeki maimin haka dan darajar fiyayyen halitta S. A. W ki daina bana san haka idan Annabin ya isa dake ba danni ba._* *_Attention , labari mara daɗi daya riskeni kusan kwana biyu da suka wuce bana san yawan ƙorafe² a jikin pages ina amma yau dole tasa ni sai nayi magana , cikakken suna na shine JAMILA MUSA , kuma ni haifaffiyar KATSINA ce iyayena da komai nawa yana katsina masoyana ku saurara kuji , yake "yar uwa me amfani da suna na kina maula to kiji tsoron Allah domin ko ba komai ƙarya haramunne inji manzan Allah S. A. W bazan ja miki Allah ya isa ba amma dai kituna zaki mutu kuma nima zan mutu dani dake duk zamu haɗu gaban Allah SW , bani bace nake waya daku cewa ku turomin kuɗi zan siya data zan yi kaza² ni JAMILA MUSA bani bace ba ƙarya ne kuma ƙarya take da suna na tana ansar kuɗaɗe a hannunku dan haka kuyi karatun tanatsu domin da kuɗin nake buƙata a hannunku bazan roƙeku ba sadai na siyar da littafin amma ba komai nasan ƙauna ne yasa yasa kuke bayarwa amma daga yanzu duk wacce tace muku itace JAMILA MUSA ƙarya takeyi 07016--78 shine farkon da kuma ƙarshen number na ngode sosai masoyana ina muku fatan alkairi...._* Kaine Dikko ? Inna tayi maganar tana kallon idona ! Shima ni ya kalla yace ƙwarai nine Dikkon da kike magana , ai nasan kaima sunan ka Dikko bakai ba Dikkon gidan gwamna shi nake nufi , har yanzu idon Dikko a kaina yake ya ba Inna amsa cewa shine ai , kaine .....? Umm ya bata amsa , yanzu kaine ɗan iskan yaron nan daka raina mutane ? Murmushi Dikko yayi tare da cewa amma dai ai ke ban raina ki ba , wannan duk faɗar mutanen da basa so nane , na raina mutane bana ganin mutuncin kowa idan na taho bana kaucewa kaza² wannan duk labarin "yan uba ne Dikko ba haka yake ba kayane aka linke ta baibaya shi yasa ake ganin mununsu.... Kai da Allah rufe min baki ɗan iska mara mutunci na tsaneka duk duniya idan akwai wanda na tsana tou ka sani ba kowa bane kaine ...... , bana sanka yau ji nake kamar in yanke kunne na saboda ɓata lokacina da nayi ina waya dakai , har yanzu murmushi yake kuma bai daina kallona ba yace itama kamar yadda kikayi haka ta ɗauki zafi , nuna kanshi yayi cewa irin bakinmu ɗaya itama Momy wai bata san An mata kema baki san Dikko anyi anko kenan to amma ai dani da An mata kowa yana san kowa ke ko kin daina so nane ? Yayi maganar yana tambaya na da kanshi...... Nima murmushi nayi masa tare da bashi ansa ina sanka kuma saina aureka ko za'ayi ruwan bala'e da ƙanƙarar masifa a cikin familynsu wannan ni bai shafeni ba , duka zagi ko habaici baya gabana ko za'a mutu a dawo idan na kafe a hanya ɗaya tou wannan hanyar duk girman katsina babu wanda ya isa yasa na juya zuwa wata , nuna shi nayi sannan na nuna kaina Dikko ina sanka kuma saina aureka cikin amincin Allah da salama duk wanda baya maraba da auren nan tabbas canja maganar nayi cewa zai so ma... Cikin ɓacin rai Inna tace fita....... Dikko fitar min daga nan , a , a Mama cikin hayani Inna ta fara turance Dikko shima da yaren da tayi magana yayi mata nidai na zama "yar kallo dan banajin abinda suke cewa kuma bansan yadda sukayi ba Dikko ya fita cikin damuwa , kafin na sauko daga saman gado Dikko ya fita daga ɗakin da gudu na fita lokacin harya shiga motarshi ya tada , cike da fargaba na isa wurinshi nace Dikko ka tsaya dan Allah , tsayawa yayi yana kallon can gefen cikin tsananin ɓacin rai..... Kusa da motar na tsaya na dafa hannuna a saman glass ɗin daya rage bai ida saukewa duka ba , Dikko me Inna tace maka don Allah , dakel ya kalli gabanshi ya busar da iskar bakinshi a damuwance yace ba komai Sulthanah........ Dam׳ naji gabana ya faɗi sunan babu daɗi a bakin Dikko sai naji wani iri haka da ya kirani da Sultana tunda na haɗu da Dikko da rashin mutunci muka haɗu amma bai taɓa kamo tashar suna na ba sai yau lallai abun yaci tira karuwa ta tsira malam. Ci gaba yayi da cewa mu ɗau haƙuri mu sanya haka ɗin jarabtace , kuma kowa akwai nashi a rubuce , babu wanda ya isa ya musulta ita ƙaddara idan ka rasa karka manta da Allah , ubangiji keda iko mu bayi "yan kallo ne ! Idan kinyi imani da Allah kuma kin yadda akwai samu akwai rashi , kuma idan har kinyi imani ubangiji yake bayarwa kuma shine yake karɓewa yadda da ƙaddara ki tuna wannan shi ake kira da imani , zumuncin mu yana nan insha Allah kije kuma ki ba Mama haƙuri idan har kinyi imani da Allah ki karɓi auren Sultan kuma ki zama mai biyayya wurin mijinki , kije Allah ubangiji ya albarkaci rayuwarki na barki lafiya , yana faɗin haka ya sulala da motarshi a hankali ya fita , bin bayanshi nayi yana fita daga gidan ya tafi da tuƙin shi mai burgeni...... Kai tsaye g r a ya nufa dan ya samu ya sauke damuwarshi , yayin da hotunan abinda ya faru tsakaninshi da An mata ya fara wuce masa ta gaban idonshi , a ranshi kuwa kukan Sultana yaji a ranar da yayi mata babbar kajin ƙauri , tana roƙarshi cewa { kaji tsoron Allah karka ɓatamin rayuwa ka rufamin asiri dan girman Allah , } goge hawayen idonshi yayi tare dayin magana a bayyane amma dake banaji shine banyi haƙuri ba saida nayi kaicon ka Dikko me kaji ? Da nayi haƙuri na barta duk haka bai faru ba nima kaina da ina nan zamana lafiya haƙuri yana da matuƙar kyau a rayuwa kuma yana da wahala babu wanda zaiyi haƙuri yayi nadamar yinshi , amma idan kaƙi haƙuri kayi abinda zuciyarka tace tabbas sai kayi nadama da zaran ka gama aikatawa , wani irin wawan burki ya taka tare da juya kan sitiyari ya nufi inda su Bello suke yau saiya kashe Bello daya kawo mishi An mata wurinshi ! Saiya faɗa masa dalilin daya sa saishi aka zaɓa ya ɓatawa An mata rayuwa ƙalu bale gareka Bello..... Inna kiyi haƙuri don Allah zan auri Sultan , ko kiyi haƙuri ko kar kiyi babu gudu babu ja da baya aurenki da Sultan babu fashi wallahi , to Inna in Allah ya yadda , amma dan Allah Inna me kikace ma Dikko ? Ai na ɗauka da kika bishi ya faɗa miki na tsani Dikko sakarar banza ballagaza dake dama Sultan yacemin ko a asibiti tare kuke kwana idan har kika bari Sultan yace ya fasa aurenki ƙaryarki ta ƙare asirinki ya tonu. Haka ya kasance dani ɗan uwana ya fito yayi hidima da rayuwata munyi soyayya mai tsabta auren zuminci shine al'adar familynmu amma tunda ake haɗa aure ba'a taɓa samun maso san junansu ba sai mu domin mu ba haɗamu akayi ba mune muka haɗa kanmu , biki ko suna komai da kika sani duk inda zanje muna tare , munayi ma juna soyayyar da ta zama abin sha'awa ga duk wani wanda ke ahalinmu dan wannan soyayyar ta kafa tarihi mai girma , amma lokaci ɗaya Binna ya shigo rayuwata yayi min karatun yaudara zama ɗaya na ɗauka kuma na kifa kaina ƙasa nace na fasa auren Umar , duka zagi anyi amma na kafe sai Aliyu.... Abun ya zama abun tashin hankali da jimami a ahalinmu , yayin da wani ɓangaren ake kallon abun kamar anyi wani babban rashi , duk wani ɗan uwana ko "yar uwata suka juyamin baya wannan bai dameni ba tunda dai Aliyu yana tare dani , Umar yayi kuka kamar ranshi zai fita wasu kuma suna cewa ko na fasa a aura masani dole , amma nace idan har aka ɗauramin aure dashi wallahi saina daɓa mishi wuƙa ya mutu , kaf ahalina suka juyamin baya bayan an ɗaura min aure da Aliyu kinga dai yadda rayuwar gidan Babanki take kuma nayi haƙuri duk nayi ta tsotse dafin wahalar gidanshi amma kinga daga baya saiya sakeni waishi baya zuwa bikon mace , dakel aka anshe ni a gidan nan Umar kuma baiyi zuciya ba ya dawo yayi aure amma ba auren zuminci ba. Mazan basu da tabbas ko kace kana sansu daga ƙarshe sai sunyi maka tultular ruwan tsohon tulu suyi maka gori abu kaɗan kayi musu sai suce ka gagari iyayenka ka zaɓesu ka bar iyayenka , wanda ya gagari iyayenshi abun mamaki ne ya gagari mijinshi ? Ko a kuskure kayi abu sai sun goranta maka auno girma da rashin mutuncin Dikko Sultana , bani na faɗa ba duk garin nan kowa yasan halin Dikko ya gwane wurin rashin mutunci baya ganin ƙima ko darajar kowa koya aureki bazai riƙeki da amana ba , gashi yanzu ya faɗa cewa mahaifiyarshi bata sanki nima bana sansa , haka zakije ki fuskanci wulaƙanci da hantara a cikin zuri'arsu , kuma nayi imani wata rana saiya goranta miki yace miki karuwa kuma zai miki gori kinbar uwa kin zaɓi namiji , tazara mai nisa tako ina Dikko yayi miki asalinki da nashi ba iri ɗaya ba , tun ba'asan meye suna ba tunin duniya tasansu , mutane masu arziƙi da cikar asali sunyi kuɗi na tashin hankalin da kwalwarki bata ɗauka , sun nemi kuɗi kuma sun samu sun tarasu tun mutane na bacci , Dikko yafi ƙarfinki kuma yayi miki zarrar da baki kamoshi ki shafawa kanki ruwa ayi miki aski , Ke kina wasa da lamarin Dikko ko ? Hmmm dan girman Allah wata rana kije inda yake zama ki kalli mata masu siga da nagarta kamar ba mutane ba tsabar kyawunsu , Sultana har Dikko yana kallon dakakkin mata "yan gayun bala'e masu ilimi wanda suka goge masu aji zai saurareki ? Dan Allah kije wata rana kiga yadda mata kebinshi , ko yace zai aureki ƙarya yakeyi yaudararki kawai yakeyi dan nayi imani Dikko baya aurenki yafi ƙarfinki wallahi , kiyi haƙuri kiyi ma kanki karatun ta natsu ke ba ajinsa bace ƙarya yake ba sanki yake ba kaiki zaiyi kawai ya baroki , tunda dai abinda yake nema ya samu kuma tunda ya more kiyi haƙuri ki auri dai² ke shine zaman lafiyarki..... Inna wallahi Dikko yana so na , ke yarinya ce Sultana baki san Dikko ba baki da labarin halinshi ne ganinshi kikeyi filinshi kika sani baki san ɓoyenshi ba , duk yadda za'a faɗa miki iskanci Dikko ya wuce inda bakya tunani , hausawa na cewa idan ruwanka baya iskarka wanka sai kayi alwallah ka tashi..... Amma Inna Dikko baya neman mata kuma na zauna gidanshi har na gama zamana banga wata mace tazo ba , murmushi Inna tayi cewa ai kinji yarintar in banda abinki tunda kina nan taya zai bar wata macen tazo ? Ko an faɗa miki gidan da kika zauna nan ne kaɗai gidanshi ? Ai wayau sukeyi saboda siyasa basa neman mata a gida saidai su haura sauran jahohi su ƙwanƙwaɗi iskancinsu su dawo , shiko Dikko karuwanshi duk ba "yan nan bane ba zuwa sukeyi daga wasu ƙasashe kuma yana gama biyan buƙatarshi zai basu kuɗi su juya abunsu ba tare da wani yaji ko ya gani ba , kinga waye ya ganshi da mace anan bare yace shima manemin mata ne ? hmmm ke yarinya na kiyayeki da Dikko domin haɗarinshi yana girma. Nidai haƙuri nayi ta bawa Inna kuma na haƙura har a zuciyata na yadda da auren Sultan kuma na bawa Inna haƙuri sosai ta kuma gode tare da sanyamin albarka sannan tabar ɗakina , tana fita na rufe ƙofa na kwanta ni bansan me yasa ba idan har zanga Dikko ko naji muryarshi sai in nemi hankalina da tunanina duk na rasa ina ya tafi amma insha Allah koya kirani bana sake ɗauka na haƙura dashi Allah ya bani dangana..... Wata irin shaƙara Dikko yayi ma Bello cikin sanyinshi yace me nayi maka don Allah ? Me yasa ka haɗani da yarinyar da kukeyi rikicinku bayan ni bai shafeni ba ? Shiru Bello yayi baice komai ba , Dikko yace faɗamin ina saurarenka kadai lura ina cikin fushi ko ? Jinjina kanshi yayi cewa tou faɗamin kafin in ɓare maka biyu in kashe ka kuma na kashe banza sai ka zaɓa ga mutu ga kuma rayuwa...... Da sauri Bello ya dafa hannun Dikko , sakinshi yayi tare da cewa ina saurarenka , cikin kuka Bello ya faɗawa Dikko saboda yayi fyaɗe wa wata yarinya da suke gidan shine shima Binna ya rama akan matarshi , wannan dalili yasa ya kudiri shima saiya gurɓatawa Sultana rayuwa kasancewarta bugun zuciyar Binna , soyayyar da Binna yake mata yasa duk inda zata tafi yana tare da ita saboda baya so ta shiga cikin wata damuwa ko halaka , Binna baida tsoro kuma bashi da mutunci akan duk wanda ya taɓo masa Uwar masu gida saboda yana jinta kamar wata rayuwarshi , ni kuma ina nan haƙe dashi ina neman sa'a yadda zanyi na taɓo wannan rayuwarshi tashi dan huce raɗaɗin ciwon abinda yayi min , ƙwatsam sai Binna yazo min da labari cewa yau Uwar masu gida taso ta jawo masa fitina da kanta ta zagi ɗan gwamna yaro mara mutunci daya raina mutane dakel aka bashi haƙuri ya haƙura saina lura Binna yanayin maganarshi ya nuna yanajin tsoronka bayan shi kuma bayajin tsoro kowa. Ganin haka sai nayi amfani da wasu mutane daya ci bashinsu nace musu Binna yace bazai basu kuɗin nan ba yace ya cinyesu idan suna da wani isashshe yazo ya karɓar musu a hannunshi , nine na tunzurasu sukayi ƙararshi aka kamashi kuma ni dakaina na bada kuɗi wa "yan sanda sukayi mishi lullusar fitar hayyaci , kuma nine naje na biya kuɗi nayi belin shi , saina bashi shawara za'ayi caca yazo yayi ya shiga tunda yana da sa'ar caca bai taɓa faɗuwa a caca ba idan yaci kuɗin saiya biya bashin , nasan baida kuɗin da zai saka kafin alƙalamin caca shine nace masa kawai ya saka Sultana , da farko bai yadda ba duk da saida nayi masa asiri kuma bokana ya tabbatarmin da zai sakata a cacar ya kuma bani maganin da zan zuba mishi a abun sha wanda zaisa yayi wasi² , haka kuwa akayi bayan dai Binna ya yadda ya saka Sultana a wurin caca na zuba mishi maganin wanda yasa yayi wasi² ya faɗi a wasa. Ba wani abu kayi min ba na kawo ta wurinka ba saboda na lura Binna yanajin tsoronka kuma na tabbata ko tsafi yake kai kafi ƙarfinshi saboda kai ka zama dodon duniya kuma kai jan gwarzon maza ne dan kowa yasan ka gaji nagarta , duk wani ɗan ƙaramin tsafin shi bazai kamaka ba dan kai nari ne ko an jefe ka haka nan jifar zataje ta dawo kuma idan taƙamarshi yayi shari'a dakai kune gwamnati bai isa yaja dakai , Gwamnatin ubanka Dikko ya faɗa tare dakai mishi wani irin kyakkyawan halbi a baki saida yaci uban Bello da kyau ya kuma sake ɓare mishi haƙora sannan ya kashe Dady da mari yayi haukanshi sosai babu wanda ya bashi haƙuri dan babu mai riƙeshi sunci ubansu kuma suma yau sun ƙara saki da lamarin Dikko saida ya tabbatar sun tashi aiki ya nufi gidanshi cikin ɓacin rai ! Cikin farin ciki kowa ya wayi gari duk wanda ka gani a gidanan yau yanayin farin ciki , kowa sai hidimar gabanshi yakeyi yayin da ni kuma nasha wanka na tsuke cikin wani ƙaton leshi kalar launi mai kyau , nima dai duk da banajin daɗi hakan bai hanani nuna farin ciki ba amma na ciki yana ciki , Inna ma tana cikin farin ciki tana ta hidima da mutanen arziƙinta kai Inna gaskiya wayayyace "yar gayu kisan farko ga kyau ga hutu wallahi baka gajiya da kallonta. Misalin ƙarfe 2:00pm aka ɗaura auren da taron dubun mutane suka halatta , ina ɗaki kwance ina ta kuka na rasa abinda yakemin daɗi Inna ta shigo ɗakin cikin tsananin ɓacin rai tasha kuka har ta gode Allah , kayana ta fara tattarawa tana kuka idan ta zuba a akwati sai ƙawayenta su ɗauka sukai waje cikin mota su dawo , duk abinda ya shafeni saida Inna ta tattarashi kaf ta ware lefen da aka kawo jiya ta ajiyeshi a gefe wayata ta ɗauka tare da jawo hannuna tana fizgata cikin ɓacin rai haka muka keto cikin taron mutane kowa yana kallonmu , Kaka ta biyo Inna tana cewa Fatima wai kedai ban isa in faɗa miki ba ? Bata bata ansa ba har yanzu kuka Inna keyi , haka Kaka ta biyomu har harabar gidan amma sam Inna bata saurara mata ba ta buɗe bayan mota ta jefani ta kulle da kanta taja motar kamar zatabi ta kan Kawu ta wuce ta fita daga gidan , sauran mutanen da suka zo mata biki suka biyo bayanta. Har muka zo gidan Inna dake barhim estate Inna kuka takeyi , ƙaton gida ne da akayi mishi ginin zamani gidan "yan gayu an ƙawata shi da filawowi wanda suka ƙara martaba darajar gidan , tanayin parking ta fita nima fita nayi daga motar nabi bayanta ina kuka palo ta zauna tana goge hawayen idonta da tissue a haka taron ƙawayenta suka shigo suna ta bata haƙuri dukansu da turanci suke magana ni dai bansan abinda suke cewa ba saidai inaji lokaci² tana kamo sunan Dikko , haƙuri dai suke ta bata har wanda nake tunanin shine mijinta yazo kiranta yayi suka shiga ciki ƙawayenta suka ci gaba da tattaunawa akan abinda Yayar Inna tayi bata kyauta ba , Tayi ƙatuwar cin amana sukaci gaba da maganarsu da yaren da nake fahimta su kuma sun kasa gane saboda nine Inna take magana dasu da turanci tunda tasan ban iya ba , wai ashe ita Yayar Inna jiya itace ta faɗawa Sultan wai ni ina da cutar ƙanjamau lokacin da akayi min fyaɗe aka sakamin cutar shi yasa "yan gidanmu sukayi ta ƙyanƙyanmi na ko kofi na taɓa basa amfani dashi wannan dalilin yasa na shiga bariki kuma abinda yasa na amince da aurenshi wai ni nake faɗa zan yadda na aureshi ne dan na saka mishi cuta , kuma ni karuwar Dikko ce kuma kona aureshi wai ni na faɗa mata bazan daina bin maza ba , da Sultan ya faɗawa Kawu , Kawu yace ƙarya ne ka auri yarinyar nan zaka zauna lafiya amma sam mahaifiyar Sultan tace wallahi baya aurena , Kawu yayi faɗa cewa ya taro mutane daga wurare da dama zasu zo ɗaurin auren ɗansa saiya musu waya yace an fasa saboda wulaƙanci ? Shine Mami tace sai a ɗaura auren da ɗiyar ita Yayar Inna , yanzu da ita aka ɗaura auren duk Inna bata san wainar da ake toyawa ba saida aka ɗaura yau akayi ta mata habaici wai ta lulluɓo "yarta kura da fatar akuya taso ni na auri Sultan na goge masa cuta , sukayi ta faɗin maganganu marasa daɗi akaina shine Inna taji haushi kuma in banda munafirci jiya sune suka tunzurata ta nemo Dikko tayi mishi wulaƙanci , ashe su sunsan Dikkon shine Dikko ita kuma Inna bata sani ba tunda dai kawai shi wannan Dikkon ta ɗaukeshi matsayin ɗa yana girmamata ta gayyatoshi ne ya tayata tayi faɗawa wa Sultana sai kuma ya kira Dikkon gidan gwamna yayi masa concrete worning ya fita harkar Sultana , shine tayi rashin mutunci wa Dikko data gane shiɗin dai ne Dikkon da take nema tayi ma Dikko wulaƙanci a daren jiya sosai wanda kare baya ci , Ita ba rashin Dikko bazai auri Sultana ba dama tasan babu maganar Dikko ya auri Sultana gaskiya saboda ba irinshi bace ita , tanayin baƙin cikin zumincin data dagula tsakaninta dashi , sai kuma kukan abinda "yar uwarta ciki ɗaya tayi mata yanzu da bata raye haka rayuwar Sultana zatayi ta wurgegeniya babu mai taimakonta , ita kanta ta sani wato ta bada "yarta ita kuma Sultana ko oho ,....... Sai dare kowa ya tafi daga gidan shima mijin Inna tafiya yayi ba'anan zai kwana ba , Inna tana cikin damuwa sosai ɗakinta ta shige ta kulle , tou banda abin Inna ita kuma Kaka meya shafeta a cikin wannan matsalar ne ? Wata zuciyar tace baki sani ba kila itama tace wani abu , tou amma me yasa inna ta haɗa hada Kawu ? Oho zuciya tace sudai suka sani domin sunfi kusa...... Duk gargaɗin da Inna tayimin akan Dikko saida na kunna wayata na kirashi , kamar jira yake tana shiga ya ɗauka ya gaggaɓe da wata irin dariya yace amaryar Dikko ai nasan wallahi dudduniya babu maike saini , yaci gaba da dariya cikin dariya yake cewa abinda yasa bana aurenka baƙin rai baka dariya ba fara'a doke² gaka mahaukaci sai aljannu kamar iccen tsamiya hahahaha ashe rabon mahaukaci ce lallai zamuga wasan kura An mata matar Dikko , ke kafiya ni kuma aljannu kamar iccen tsamiya , hmmm inzo Barhim ɗin zaki fito wurina..............? Dan Allah kuyi haƙuri wallahi ina fama da matsalar rashin caji ne kuyi haƙuri da wannan ! 06/10/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA.....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 72 Bazan fito ba na bashi amsa , dariya ya sakeyi kaɗan cewa he ƙarya ne fa gani nan zuwa , kasan gidan ne ? Ko na sani ko ban sani ba damuwa na ne ina zuwa kuma ki faɗawa Mama ina gaisheta kice mata nine zanzo dan na kirata waya bata ɗauka ba , da sauri na miƙe ina tunanin yadda zan shirya kafin yazo naji yana cewa bafa sai inyi wanka ba ina zuwa nan da mintuna biyar yana faɗin haka ya tsinke wayarshi. Ɗakin da Inna ta shiga na nufa ina taɓa ƙofar najita a rufe , zan juya naji tace Sultana miye ? Inna Dikko ne yace zaizo , wane Dikkon ? Wanda kika sani , tou yanzu ya akayi ne ? Shigowa zanyi inyi wanka , duk kin san zaizo sai yanzu zakiyi wanka ? Nifa bansan zaizo ba Inna yanzu ya faɗamin yana zuwa , tou ki tafi ɗakinki mana , nidai Inna buɗemin don Allah , tsoki tayi tare da tasowa tazo ta buɗe ɗakin ta koma saman gado ta kwanta , bayanta nabi na shiga ciki har yanzu bata daina kuka ba ! Ban mata magana ba na cire kayana na shiga wanka , kafin in fito har Dikko ya iso sai kiran wayata yakeyi , Inna sai faɗa takeyi banda wawanci sai mutum yace zaizo na sirki wanka , ki fito ko baki gama ba , shiru nayi naci gaba da huɗɗar data shafeni , ita kuma Innar fita tayi taima mai gadi magana wai akwai baƙo a waje ya buɗe mishi ya shigo. Da mai gadi yayi ma Dikko magana cewa yayi ai nan ma yayi suna da yawa ne basai sun shigo ba , mai gadi ya koma ya faɗawa Inna bataji daɗin haka ba , shi kuma Dikko abinda ya hanashi shigowa kar Inna ta sake feƙa mishi rashin mutunci kuma An mata tana fitowa ɗaukar ta zaiyi su tafi idan sun gama ya dawo da ita kar Inna ta fito ta tona mishi asiri cikin bainan nasi..... Ina fitowa wanka na ɗauki kayana dana cire Inna tace ki ajiyesu dan ubanki ko su zaki maida ne ? Haba nifa ba su zan maida ba , da kika ɗaukesu ina zaki dasu ne ? Zanje in ajiyesu ne , da Allah aje ki wuce ga kaya can ta nuna inda ta ajiyemin kallonta nayi tare da cewa sannu ki daina kuka haka nan kar kanki yayi ciwo , idan yayi ina ruwanki naki ko nawa ? Allah ya baki haƙuri na nufi jikin madubi ina shafa mai sai powder tagumi Inna tayi ta bini da kallo har na saka kaya na shafa tutare kaɗan na ɗauki hijibin da Inna ta ajiyemin na saka na fita , Sultana tana fita Inna tayi magana a bayyane cewa wai Dikkon nan nawa ne don Allah ? Nifa na shiga rubibi dan har yanzu wallahi na kasa fahimta shin wai Dikko U DK shine yake zuwa wurin Sultana ko kuwa akwai wani Dikkon bayan shi Dikkon gidan gwamna ne ? Gaskiya ba DK bane tou ita Sultana ina ta samo wannan shi kuma .......? Cike da zumuɗi na fito na buɗe gaba zan shiga naga ya ajiye filet a saman kujerar da kabeji anyi mishi yanka mai kyau sai cokali mai yatsu babu mai ba magi komai babu a ciki kuma Dikkon waya yakeyi rufewa nayi na koma baya na shiga na zauna , ina zama ya tafi yau bada su Ashiru yazo ba abokanshi ne suke tare , yana gama wayar ya ɗauke filet in yana cewa dawo nan An mata , Daga baya na tsallaka na isa gaba na rumgume Dikko sunbatar gefen fuskata yayi zan kwanta jikinshi motar ta fara lilo da sauri ya figi sitirayi dan kaucewa motar gabanshin daya kusa haye mata , zaunar dani yayi saman kujerar daya ɗauke filet in yana cewa zauna An mata karmu faɗi , ƙin zama nayi zan sake tasowa ya danne ni da hannun damarshi ya riƙe sitiyari da hannun haggunshi ya miƙa hankalinshi da natsuwarshi wurin tuƙi yana cewa da nace kar kiyi wanka saida kikayi badai zaki daina raini ba ko ? Ni ? Waye yace maka nayi wanka ? Nayi wanka a ina ? Ko kana tunanin zanyi ne dan na burge ka ? Sauke hannunshi yayi daga riƙon da yayi min ya ɗauko filet in kabejin daga inda ya ajiyeshi ya ɗoro shi saman jikina yana gyara rigarshi yace ci , me zanci ne ? Koma miye idan kinci bakinki zai faɗa miki , wai kana nufin ni zanci kabeji kamar wata akuya ? Koma dai mece ce ke bai shafeni ba cewa nayi ki ci , haba Dikko ni gaskiya bana ci , cikin ɓacin rai ya kalleni yace ke..... Ɗauka kici , cikin sanyin murya nace haba kabeji ne fa har yanzu ni yake kallo yace kabejin ci ya ƙarasa maganar fuskarshi ba wasa. Ina gunguni na ɗauki cokali na fara ci , a dai² lokacin da muka iso goruba , amma yau ba gidanshi yaje ba wata kyakkyawar santa suka yanka suka haɗa majalissar su a saman titi sun kashe hanyar ta yadda wani baya wucewa dan duk a saman titin suka ajiye motocinsu su ishashshi duk wani abokin Dikko da nasan yana majalissa a gidanshi na ganshi har dai Yazeed na gani kuma naga irin "yan matan da Inna ta bani labarinsu daren jiya , kallon Dikko nayi da hankalinshi yake kan wayarshi naci gaba dacin kabejin ina yunƙurin amai bai kalleni ba yace idan kikaimin amai a mota saina zaneki , to ai na ƙoshi babu daɗi , ai a ba daɗin zaki cinyeshi kisha ruwa gashi nan a gefenki , Salaf ne fa , salaf ɗin An mata cinye shi da sauri , maganin mi to ? Ra'ayi nane kawai na tareki da kabeji kuma ki rufemin bakinki na fara gajiya da magana , Allah ya isa na faɗa ƙasa² naci gaba daci saida na cinye kabejin nan duka , ansar filet in yayi ya duƙo kusa dani yace to me ne ne ? Ngode na bashi ansa to yayi kyau sha ruwa ina zuwa ya ƙarasa maganar yana fita daga motar da filet in yana fita wani ɗan cika sheda ya ansa , shi kuma aka ɗaukeshi a mota suka tafi..... Kuma na kirashi a waya bai ɗauka ba , raina ya ɓaci kuma na ƙufula da yawa. Gaba ɗaya ɗakin yayi shiru kasancewar ƙarar saukar marin da Momy ta tsinkawa Dikko duk ƙannenshi dake wurin da gudu suka tashi , yayin da ita kuma Momy ke cewa saidai ka zaɓa ko yarinyar nan Dikko ko ni saboda ba so ɗaya ba biyu ba na rabaka da ita baka bari , kai da bala'e ma zaka rabu da ita dan duk duniyar nan idan zata taru bisa kaina bazaka auri karuwa ba sakaran banza da baka san inda duniya ta nufa ba yaushe ka koma sakarai ban sani ba ? Ina tantama anya ma kaine Dikkon dana haifa da ciki na ? Karuwa Dikko ? Me ka gani jikinta wanda harya gigita ka yasa kake neman ka zama wani zararre ? Mom..... Ƙara yanka mishi mari tayi tace idan ka sake min magana saina shaƙeka ka mutu na huta da baƙin ciki tashi ka fita ka bani wuri kuma kaci gaba da yawo da ita a garin nan ana bani labari , duk ranar dana sake jin labarin ka ɗauki yarinyar nan a motarka saina je har gidansu naci uwar uwarta na faɗa maka sakaran banza marar kishin kanshi tashi ka fita ta faɗa a tsawace , jiki a sanyaye Dikko ya miƙe ya fito daga palon , A waje ya samu Nabeela tana ganinshi zata ruga yace ke zo nan , cike da fargaba tazo ta tsaya gabanshi ta fara kuka , kallonta yayi na wani lokaci sannan yace waye yace ya ganni da An mata ? Cikin kuka tace wallahi Yaya bansan waye ba ina toilet ina alwalla naji ta tana magana a waya tana faɗa , bayan na fito ne na sameta tana tura maka text , Amma a tunaninki waye ya kirata ? Yaya wallahi ban sani ba , na baki nan da mintuna 5 ya nuna da hannunshi yana ci gaba da cewa ki ganomin ko waye idan kuma ba haka ba zaki shiga3n ki.... Yana faɗin haka ya nufi wurin mota ya shiga abokinshi yaja suka bar gidan! Lokacin da Dikko ya dawo har na fara bacci shigowarshi cikin mota ya farkar dani , ina tashi na ganshi nace sai in kiraka baza ka ɗauki waya ba ? An mata da Allah bazan ɗauka ba kiyi magani na mana , ai baka dai kyauta ba kuma haka rashin adalci ne ka barni a mota kamar sakara idan kuma na tafi kace na tafi saika shanyani ka kama huɗɗoɗin gaban ka ? Ke kalli idona , kallonshi nayi yace baki lura da yanayi ba ? Ai ni naga lura da yanayin yasa ka barni ni taya ma zan iya ganewa bayan duk yanayin iri ɗaya ne ? Rufe idanuwa yayi dan haka na kame bakina nayi shiru , Shi kuma idonshi a rufe yace na shanyaki sai zakiyi ya ya dani ne ? Shiru nayi ban sake magana ba dan yadda ya ɗauki zafin nan yana iya tsintsinka min mari , tafiya ya farayi da motar yana faɗa cewa ni bansan irin iskancinki gaba ɗaya na lura so kike ki mayar dani wani sa'ar wasanki wai me yasa ke kike san cin moriyar rauni na ne ? Kici gaba da haye man ƙaramar yarinya dake. Nidai ban sake mishi magana ba , Har muka iso ƙofar gidan Inna Dikko faɗa yake min yana cewa idan kinajin taurin kan ki sake magana kiga yadda zanyi parking nan in lalata miki fata , banza nayi dashi bance masa umm׳ ba , yanayin parking na fice da sauri bayan nayi mishi godiya kamar yadda yake so , har na kusa shiga gida ya kirani , dawowa nayi amma ban shiga motar ba , An mata kin yafemin ? Ya tambaye ni , da Eh na bashi amsa , tou zagayo nan kiji wata magana , zagayawa nayi saitin inda yake na tsaya ina kallon ƙasa..... Idan Allah ya kaimu gobe zanje kaduna , Allah ya tsare hanya na bashi ansa , to bazaki tambayeni me zanyi ba ? Da kamar ince masa ai bani na aike ka ba , amma sai nace ɗin me zakayo ? Murmushi yayi yace An mata baiwar Allah ba kai tsaye zaki riƙamin magana ba na faɗa miki ki riƙa lanƙwasa min harshe wai ke ni haka nake miki magana ba sanyi ? A shagwaɓe zakice zakaje kaduna ka abarni ne , shiru nayi na kasa magana , ina saurarenki , ni dan Allah bacci nakeji , ai kowa ma yanajin bacci sai kin faɗa zaki tafi idan kuwa ba haka ba zamu kwana a titi , sai kin faɗa da shagwaɓa sannan zaki tafi , nidai kunya ta hanani kallon Dikko bare na maimaita abinda yasa na faɗa , text ɗin da Nabeela ta turo mishi yake dubawa bayan ya ajiye wayar yace ina saurarenki. Ganin zamu dawwa a haka yasa na rufe fuskata na faɗa kamar yadda yace , buɗe fuskar ki , sauke hannuna nayi , matso nan , matsawa nayi kwantar da kanshi yayi samman murfin mota ya ƙara cewa matso , matsawa nayi da hannunshi ya nunamin nima na kwantar da kaina kamar yadda yayi , ɗaura kaina nayi ina kallon idonshi , shima kallon nawa idon yayi yace tou faɗamin ko baki so inji daɗi ? Ina so , kina so ko ? Eh , yimin magana a shagwaɓe yadda nace ki faɗa , dakel na iya faɗa cikin jin kunya bayan na rufe idona , buɗe idonki ba'a furta zancen so yayin da ido yake rufe ki faɗa a yayin da muke kallon idanuwan junanmu dan martaba soyayya , kallon idon abun soyayyarka yayin furta masa wata kalma da zaiji shauƙi yakan ƙara tabbatar da son mai magana a zuciyarshi , faɗa min kina kallon cikin idanuwana , dakel dai na faɗa , murmushi yayi tare da cewa jeki zanzo kafin in tafi badai haka yaso yaji ba , saida safe na faɗa tare da wucewa gida , saida na shiga gida Dikko ya tafi da tunanin wai me yasa yawancin mata basu iya magana mai tafiya da tunanin namiji ? Ba kallo mai burgewa magana mai laushi babu dai wani salo na tafiya da tunani wai a haka ma ita kunya ta takeji lallai yarinya kina da aiki kima tattara wannan kunyar gefe ɗaya ki ajiyeta saboda Dikko baya ma mace kawaici. Dakel Dady yaja jikinshi ya leƙo yana ma mai gadin dake faman tsaron su babu dare kuma ba rana magana cewa da Allah ɗan sammin aron wayarka , ba wani damuwa ko tunanin abinda zai faru ya miƙa mishi waya , lambar matarshi yasa ya kirata , saida ya tsinke ya sake kiranta ana biyun ta ɗauka , ko gaisawa basuyi ba yace mata ɗan ƙawarki yana nan yana cin mutunci mu akan wannan tsinanniyar yarinyar dana faɗa miki tana san ta anshi kuɗin gadon su dan haka ki faɗawa ƙawarki tasa Dikko ya sakemu dan wallahi idan na ƙara biyu awurin nan mutuwa zanyi , cike da damuwa tace Dikko bai sanka ba ? Ya sanni mana ɗan iskan saida yacemin ma albarkacinki naci cikin kuka Dady ya ida cewa amma duk aya sanni yake ta ganamin azaba ba dare ba rana ! Maman Hafsa tace amma dai Dikko baida mutunci , bara zan kira Maryam ɗin dan na tabbata duk iskancin da Dikko keyi garin nan bata da labari ɗan iska mara mutunci dako bakin duniya bai kamashi , Dady yace dama banda abinki ya za'ayi bakin duniya ya kama irinsu wanda basu fito ba saida suka shiryama duniyar , ki kirata an fara kashedi kuɗin zai ƙare ya tsinke wayar. Ina shiga gida a saman idon Inna na shiga kuma ta zageni sosai sannan ta shatamin layi karna sake bin Dikko fira idan ba'a ƙofar gida ba cikin palonta idan bayayi nan tou ya kama gabanshi , nace to na canja maganar da cewa kin daina kukan ne ? Dan bana so azo inda zata zagi Dikko , bata bani ansa ba dan haka nahau saman gado na kwanta kusa da ita ban daɗe da kwanciya ba bacci ya ɗaukeni da tunanin rigimar Dikko. Misalin ƙarfe 7:45am Momyn Hafsa ta kira Momyn DK tana ɗauka Momyn Hafsa tace tuba nake dai na tasheki bacci da safiyar nan dan Allah ina tare da damuwa ne nake ta Allah² gari ya waye , Momy tace ba komai , Mom Hafsa tace Hajjaju Dikko ne da mai gidana , Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un nan kuma ya dawo ? Eh , meya haɗa Dikko da mijinki Mariya ? Wata karuwars..... Ah ah Momy ta faɗa dan dakatar da Maman Hafsa tace Dikko bashi da karuwa ni kuma ban haifi mazinaci ba Allah ya tsaremin ɗana baya huɗɗar mata , me kuwa zai haɗashi da karuwa da har zaiyi riƙici da wani akanta ? Allah ya baki haƙuri ba haka nake nufi ba , Momy tace duk ma yadda kike nufi ki bari zan kira Dikko yanzu.... Kiyi haƙuri ki fahimci maganar tawa , Momy tace nafa fahimta kawai dai banji daɗi ba kike cewa wai karuwarshi kamar ba ɗanki ba ? Haba Mariya , haƙuri dai Mariya ta ƙara bawa Maryam sannan suka ajiye waya Momy bata bar Mariya ta gama maganarta ba , tsoki Momy tayi bayan ta tsinke wayarta , taci gaba da faɗa ita dai Dikko yana so ya kasheta ya hana mata zaman lafiya , idan ta rabashi da nan sai kuma ya koma nan Dikko ba ƙaramin yaro ba amma ya hana mata kwanciyar hankali , yanzu banda iskanci kuma meya haɗashi da mijin Mariya Jabeer , wayar Dikko ta fara kira tana faɗa amma sai Jiddah ta ɗauka tace mata tunda ya fita masallaci har yanzu bai dawo ba , Tun tsakar dare Bello ya fara tanɗar harshe kamar kwarton da yaga wawan zama , yana dariya ma Dady cewa saina tona maka asiri ׳ harararshi Dady yayi tare da cewa to ka tonamin dan wutsiyar gyatimin ka , dariya Bello yayi ta irin ya saki layi yana ci gaba da cewa saina tona maka asiri , a haka Dikko ya sami Bello yana ta abu kamar dai yaɗan zare haka.... Yana ganin Dikko yace Baba wannan Baban ne , Dikko rai babu haƙuri yayi ma Bello wani irin kallo yace nine Baban naka .....? Umm ya faɗa tare da gaggaɓewa da dariya yace ba kaine ka kamoni ba kayi man duka , kallonshi Dikko yayi tare da cewa ko kana so na ƙara maka ne ? A , a Baba na bari , tou me kayimin na dake ka ? Dan abinda shi Dikko ya fahimta kila kamar Bello ya tsorata da yawa yasa ya ruɗe , shi kuma Bello cewa yayi in faɗa maka gaskiya ? Da ƙarya ka faɗamin ? Inji Dikko , Bello yace wallahi nine nake so ta zama karuwa , Kuma nine na kashe Binna sa'ar caca na yana tafiya da rayuwar cacarsa dama boka yace zai haɗa sa'a tane a ta Binna danshi mai sa'a ne yacemin kuma idan har Binna ya daina caca shine komai zai lalace min bazan sake samun sa'ar caca ba kuma rayuwata zata zama kamar walƙiya idan har Binna ya daina caca , shine Binna ya fita a caca komai nawa yaja baya , Dana koma na faɗawa boka cewa komai ya taɓarɓare min kuma mutane suna gudu na , shine boka yace idan Binna bai dawo caca ba rigar da zan saka komai na rayuwa saina nema na rasa , dana ce Binna ya dawo caca ya ƙiya , shine na sake komawa na faɗawa boka shine ya tura aljannu suna bawa Binna tsoro a bacci ko zai dawo amma ya ƙiya. Mafita na ƙarshe shine boka yace mutuwar Binna itace tsira da kuma salama a rayuwata shine na kashe shi , Dikko yace ai bashi ka kashe ba kaine ka kashe kanka , labarin kwalba ya akayi yazo wurinka ? Malami karuwa da mawaƙi duk basu da amana , yayin da suka kama wani a lokacin suke watsi da duk wani mutunci dake tsakaninku , malamin da suka ba kwalbar ni malami na ne kuma nine na haɗashi da Mamy , da kwalbar tazo hannunshi shine ya kirani mukayi ciniki ita Mamy ta bashi naira dubu hamsin akan ya warware matsalar shine ya faɗamin ni kuma nace zan bashi naira dubu ɗari biyar ya bani kwalbar , shine nakai na anso , Aljannu goma ne a saman kwalbar suna gadinta daga nan har illah masha Allah , wannan sammu makarinsa ɗaya ne inji boka , saukar alƙur'ani mai girma tsawon wata ɗaya kullum sai an sauke alƙur'ani sau goma duk rana ɗaya a yanka raguna goma bayan an buɗe kwalbar kuma ba fasata za'ayi ba domin kwalbar itace matsayin ƙwalwar ita Sultana shi yasa akayi cushe² a cikinta an tosheta ta yadda iska baya shiga , buɗe kwalbar za'ayi a barta a buɗe daga ranar da aka san za'a fara sauka , sau goma za'a sauke fa kuma har tsawon kwana 30 za'a yanka raguna goma duk rana a raba ɗanyen naman sadaka..... Yanzu ina kwalbar take ne ? Tana ɓoye a wani wurin sirri nine kaɗai nasan wurin , na ɓoyeta tun bayan lokacin dana anso ta daga hannun malam , fita Dikko yayi ya nufi gidanshi , bayan yaje yace Ashiru yaje ya ɗauki Bello ya kaishi gidanshi ya ɗauko saƙo , Ashiru yace to , Dikko ya wuce ciki. Da wani irin ciwon kai yau Inna ta tashi ko motsin kirki bata iyawa tun jiya take kwarara amai kafin gari ya waye tayi laushi ko magana bata iyawa , ina zaune kusa da ita sai sannu nake mata bata min magana tadai bini da ido tana min kallo mai nuni da tanajin tausayin rayuwata , Mai gadi naji yana ta sallama daga waje dan haka na tashi na fita , nayi baƙi a waje shine abinda ya faɗamin , kai tsaye na nufi ƙofar gida wani mutum ne zaune a saman machine kusa dashi naje muka gaisa bayan mun gaisa ya ciro takadda daga aljihunshi yace gashi , nace ta miye ne ? Yace ki ansa ki kiranta mana , kaida ka kawota kaine zaka buɗe ka karanta , kallona yayi sannan yace sammaci ne ƙanin Babanki yana tuhumarki da sa hannunki a lalacewar tarbiyar "yar sa sai kuma maganar kuɗin gadonsu daya ji labari kin ansa kin handamesu....... Kallonshi nayi amma ban anshi takaddar ba nace ina zuwa , komawa nayi ciki na ɗauki wayata na kira Dikko , saida kiran ya kusa ƙarewa ya ɗauka , fita nayi waje babu ko gaisuwa na fara rattafa mishi damuwata , shima yana cikin damuwa domin bayan ya koma gida Jiddah ta faɗa mishi Momy tayi waya , bayan ya kira Momyn ne tace yaje tana kiranshi , da yaje tayi mishi zagin girgizar "ya "yan magarya tare da faɗa masa cewa kashedi na ƙarshe tayi masa akan Sultana idan ya kuskura ta sake kiranshi akan Sultana zata mishi wulaƙancin da katsina bazata iya ɗauka ba , yana cikin tashin hankalin zagi da tunanin taya zaiyi ya rabu da An mata ita kuma ta kirashi tana faɗa mishi tata matsalar kuma shine take so ya sama mata natsuwa , ashe shine ma ya kamata ya koyi aje damuwa 2 a zuciyarshi ba An mata ba , damuwar shi , damuwar An mata , ajiyar zuciya ya sauke sannan yace kina ina yanzu ? Ina Barhim , ina shi mutumin yake ? Yana waje , tou ki taho dashi mu haɗu daku wurin government house yanzu zan fito , ciki na koma na ɗauki hijabi na ko Inna ban faɗa mawa ba saboda na gani tana cikin damuwa bai kamata na ƙara mata wata damuwar ba amma nasan dole zan mata laifi tunda tace na daina bin Dikko kuma gashi zan bishi , kuɗin napep na ɗauka na fita waje , Ina zuwa wurin mutumin nace masa tou muje , ai ba yau ake nemanki ba sai sati mai zuwa zakije , Ey wurin Babana zamuje ka bashi kaga bai kamata ni na anshi sammaci a hannuna ba , kuma kaga daka zo bani ya kamata ka nema ba , iyayena zaka nema idan kuma ina da aure mijina , ina Baban naki ne ? Muje ai wurinshi zamuje yanzu , tada mashin inshi yayi yace in hau nace masa mu fita waje dai na samu napep. Ina gaba yana bayana saman machine har muka fito wajen estate in , na samu napep na shige ko a napep mune a gaba yana bin bayanmu da machine har muka isa daga nesa na hango motar Dikko dan haka na sauka a napep bayan na bashi kuɗinshi... Dikko yana hangoni ya matso inda muke tsaye , ta wurina ya tsaya tare da sauke gilashi , matsawa nayi kusa da motar ina cewa mutumin tou taho , ƙin tahowa yayi , ni kuma na sake cewa kazo ka kawo mishi yana jiranka ,tada machine ɗin shi ya farayi Dikko yace ya akayi ne ? Ya nuna kamar baima san abinda ya faru ba , wai kotu ake ƙarata wai ana tuhumata da lalata tarbiyar wata kuɗin gado duk ni ɗaya , a dai² lokacin da mutumin ya tashi machine ɗin shi Dikko yace kai zo nan , kashe machine ɗin yayi ya sauko dan yasa ko ya tafi zai bishi ne kuma idan ya bishi da damuwa. Daga ɗan can gefe ya tsaya ya gaishe da Dikko , bai ansa gaisuwar ba yace ya akayi ne ? E dama ranka ya daɗe wai ita ake nema a kotu dan ansa wasu "yan tambayoyi , wane irin "yan tambayoyi ? Wani ƙanin Babanta ne yake ƙararta , biro Dikko ya ɗauko gefenshi ya bani yace miƙa mishi ya goge sunanki yasa nawa , ai ranka ya daɗe ba kai ake nema ba , Dikko yace wanda ya kira uwa ya kira ɗanta ne , haka zalika duk wanda ya nemi mata mijinta ya nema rubuta suna na , Ƙin ansar biron yayi tare da cewa tuba nake ranka ya daɗe , miƙo hannu Dikko yayi cewa tou kawomin , miƙomin takaddar yayi Dikko yace kai zaka kawota da kanka , matsawa yayi ya miƙa mishi , duba takardar yayi bayan ya ansa yace to jeka zamu zo rana irin na yau ko ? Yace E ba damuwa kuɗi Dikko ya bashi masu yawa godiya yayi sannan ya tafi... Taho mu tafi , zagayawa nayi na shiga muka tafi gida , a hanya nake faɗa masa Inna bata da lafiya kuma tana ta amai tun jiya kuma na faɗa mishi kuka tayi sosai shi yasa bata lafiya , addu'ar neman samun lafiya yayi mata daga haka bai sake magana ba saini dana isheshi da surutu har muka iso gida , bayan munzo ne yake cemin ya fasa tafiya saboda wani uziri daya taso mishi , Sannan kuma ya tambayeni wai zan iya zama da Jiddah ? Ina zan zauna da ita ? G R A kinga ban gama aiki goruba ba kuma ni inaso muyi muyi aure , kallon gefe nayi nace idan munyi auren ka riƙa bani kabeji ? Murmushi yayi yace ke wallahi wannan kabejin nine nakecin shi a yadda kika jishi , babu daɗi ne ? Umm ba daɗi , zaki zaune da Jiddah ? Idan nayi maka laifi saika dakeni a gabanta ? A , a sai mun shiga ɗaki zan zaneki a saman gado kina so ko ? Tsoki nayi zan fita motar ya riƙoni yace An matana yi haƙuri kar kiyi fushi wasa nake miki fa , tafiya zanyi kar Inna ta tashi bana nan , naji zaki tafi amma kalloni , kallonshi nayi yace kin gode ? Ey , idan munyi aure ma idan kika zanu zaki gode ya ƙarasa maganar yanamin kallon tsakiyar fage..... Fizge hannuna nayi na fita , dariya Dikko yayi yana An mata zo , ban dawo ba yace ki gashemin Mama zan dawo anjima ki ajiyemin abun daɗi kinji ko......? Ban juyo ba kuma ban bashi ansa ba na shige gida , murmushi yayi ya rufe ƙofar da Sultana ta bari buɗe sannan ya wuce , yana tunanin anya bazai bari ya gama aikinshi ba ? Kamar idan ya haɗa An mata da Jiddah zata sha wahala kuma gashi shi ba mazauni ba , wata zuciyar tace kawai cakuɗesu tayi hankali ma........ Mutumin daya kawo ma Sultana sammaci gidan Baba ƙarami ya nufa , 08/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 73 Zaune suke ƙofar gida a saman dakali yana korawa Baba Ƙarami bayani cewa Dikko ne ya anshi sammacin daya kaiwa Sultana , gyara zama Baba ƙarami yayi tare da cewa ko shi gwamnan ne da kanshi ya ansa bai shafeshi ba shidai Sultana yake ƙara kuma koshi gwamnan ai yasan gaskiya in banda yarinyar nan ta gaji iskanci har tasan ta yadda zata haɗa wani da wata yayi iskanci ? Duk wannan bai isheta ba gidan da ni kaina ban sanshi ba amma ita taje ta ganoshi ta tattara kaf kuɗaɗen gado kuma tayi ruf da ciki dasu ! Amma kai waye yace maka ta anshi kuɗin gadon naku ne ? Jikar gidanmu ana ce mata Hafsa itace suka zo da wata yarinya ana ce mata Amisty , a saman wannan dakalin suka sameni cewa idan naga Sultana dan girman Allah inyi mata magana tasa a sako mata Dadynta , dana tambayeta abinda ya haɗa Babanta da Sultana sai ta koramin bayani ta kuma ƙara da cewa kuma ta anshi kuɗin amma har yanzu ba'a sako Dadyn ba shin saini in zura mata ido ta cinye duk wa'annan yawan kuɗin a cikinta ? Kuma iskancin Sultana bai tsaya nan ba saida tabi hanyar da aka lalatamin tarbiyar yarinya , ita kaɗai taji tana ra'ayin iskancinta taje tayi babu wanda ya hanata amma akan me zata gurɓatawa wata da bataji bata gani rayuwa ba ? Abokin firar nashi dai bai sake wata magana ba saidai sauƙi daya nema tare dayi ma Baba ƙarami sallama ya tashi , Baba ƙarami kuma yaci gaba da bunbunai shi ɗaya. A kwance na samu Inna tana waya da zani ɗaurin ƙirji da alama wanka tayi , gefenta na zauna ina tunanin rayuwar da zanyi a gidan Dikko idan har Allah ya ƙaddara na zama matarshi , zama dani da Jiddah ? Matar data zo har ƙofar gidan ubana suka ɗaukeni sukaje dani sukaci zarafi na ? Mahaifiyar Dikko ta tsaneni babu gaira babu dalili ga Al ' Ameen kuma tunda har mahaifiyar Dikko bata so na tou kuwa taya su "yan uwanshi zasu so ni ne ? Wace irin rayuwa zan fuskata ? Ya za'ayi idan har Jiddah tamin wani abu shin na iya ramawa ? Idan kuma na rama ta faɗawa Dikko ya goyi bayan matarshi ni ina zan saka tawa rayuwar ne ? Tunda dai nayi imani bazai goyi bayan ni bare ba ya yage bayan "yar uwarshi da sukayi auren zuminchie da mahaifiyar Jidda data Dikko uwa ɗaya uba ɗaya shin ya zanyi ne............? Maganar Inna naji tana cewa ina kikaje ? Nan baya na zagaya na bata amsa dan bana san ina tunanin Dikko ana min magana wallahi , Inna tace ai kin kyauta ni tashi akwai ƙullun koko a palo nima yanzun nan aka kawomin shi yau da maitar koko na tashi a rayuwata saida na samu ƙullun nan hankalina ya kwanta kije ki dama min shi. Inna ina zan dama miki wani koko ? Nan gidan mana , kinga karmu tsaya ba shari'a wahala ni ban iya ba Allah ya sani kuma Dikko yace yana gaisheki na faɗa mishi baki lafiya yace zai dawo anjima kuma a ajiye mishi abun daɗi..... Ya zo ne ? Eh , shine nace ina kikaje kika cemin kin zagaya baya ? Tayi maganar tana murmushi , nima murmushin nayi mata amma banyi magana ba. Tashi tayi ta saka kayanta aka ɗan matsa turare aka kashe ɗauri ta fita palo , tashi nayi nabi bayanta a saman kujera nasameta zaune tana waya da mijinta , bedroom in na koma na kwanta nasan dai kafin in tashi bacci tasan "yar dibarar da zatayi wanda zamu ci ma cikinmu ! Biye yake da bayan Bello saf da ƙafa har cikin tsakiyar filin tsakar gidanshi , dakel Bello yake tafiya kamar zai kife Ashiru na biye dashi har cikin ɗakinshi , gaban wani ƙato bedsite Bello ya durƙusa a gajiye sannan ya fara ƙoƙarin turashi gefe ɗaya , Ashiru yasa hannu ɗaya ya janyeshi gefe Ashiru na janyewa Bello ya ɗafe wani bargo sai ya janye wani katako wani zurmemen rami ya bayyana mai tsananin duhu da matsakaicin zurfi. Kwanciya Bello yayi ya zura hannunshi a cikin ramin ya jawo kwalbar kallo ɗaya Ashiru yayiwa kwalbar ya fara kakarin amai saboda yadda zuciyarshi ke tashi da tsikar jikinshi , bayan ya ɗauko ya miƙowa Ashiru yace kai kaci uwaka riƙeta muje , rungume kwalbar Bello yayi suka fita daga gidan..... Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un ta faɗa da wata irin ƙara mai tayar da hankali tare da tashi zaune saman tsakiyar gado tana sauke wani irin numfashin wahala , da gudu Inna ta shigo tana lafiya ? Wai , wai , wai tayi tare da goge zufar goshinta tana numfashi a wahalce , ke Sultana lafiya ? Har yanzu numfashin ta bai daidaita ba , Inna tace wai mene ne ? A tsora ce nace wani ne ya biyoni a bacci wai zai kasheni kuma idan inajin wasa idan na tashi naje Qerau yau zanga karuwa ɗaya ta mutu sanadin kwakwale mata idanuwa da yayi kamar yadda ya kwakwale idanuwan Mamy , cikin faɗa da ɗaga murya Inna tace ki koma baccin ki faɗa masa baki kasuwa kuma babu wanda ya isa ya kasheki , ta ƙarasa maganar tana kwantar dani ta lulluɓeni da bargo. Wayyo Allah Inna da Allah bana so wallahi banayin bacci , cikin hayani tace duk abinda ya cimmiki nasara a bacci a zahiri sai yayi nasara a kanki babu wani maiyi sai Allah haka babu mai rayawa da kashewa idan bashi ba ki faɗa masa baki mutuwa sai kwananki ya ƙare..........................! Saukowa nayi daga saman gadon jiki a sanyaye nace nidai banajin wani bacci , toilet na shiga na watso ruwa dan inɗanji ƙwarin jikina , ina fitowa ko mai ban shafa ba na zura kayana ina gama sakawa na wuce wurin Inna mukaci abinci tare... Duk wani mahaluƙin dake anguwar Qerau yau kam yana cikin tashin hankali abu ba'a magana anguwar ta cika faful sakamakon alhinin safkar idanuwan wata matar aure duk inda ka leƙa gida ko bisa santa labarin akeyi bayan an cire idanuwanta aka zo aka yadda ita a saman santa.... Tun asuba aka tsinceta mutanen da suka fito domin zuwa masallaci sallar asuba sune suka fara ganinta dan haka a hankali labari ya fara zagawa cikin anguwa kafin wani lokaci kuma gaba ɗaya gari ya ɗauka ba'a kaiga kaita asibiti ba tace ga garinku nan , Wannan tashin hankali ya zama baƙon al'amari ga mutanen wannan anguwa anyi mutuwa maimakon addu'a ga mamaciyar sai zaƙule²n abinda ya kaita ga afkawa bariki akeyi , ita dai mamaciyar tana da aure da yaranta biyu kuma tana zaman lafiya da mijinta , bakin abinda Allah ya rufa mishi asiri yana riƙe da gidanshi bakin iya gwargwadon karfinshi. Wannan matar aure dai ta samu damar antayawa a harkar bariki ne sakamakon gurɓatacciyar ƙawa data tsinta a saman yanar giza gizo , mamaciyar ta shiga harkar bariki ne a sakamakon ƙorafi wa ƙawar tata ta hanyar nuna gazawar mijinta a wurin riƙon gidanshi. Bayan ta tsinci wannan ƙawa a saman iska sun ƙulla alaƙa mai girma ta yadda kowa baya iya ɓoyewa kowa sirrinsa , wani zamani ne wanda Allah ya kawomu wai sai kaga mace a duniyar nan duk abinda taci ko tasha saita ɗaukeshi hoto ta turawa wata , duk ƙawar da kike tare da ita ta fara miki wannan tsire²n na ɗaukar abinci ta turo miki shi ta waya wannan ba ƙawa bace ba maza kija mata layi ba abokiyar tarayya bace ba idan har tanajin ita mai kirkice to ta zobo abinci a kwano ta bada a kawo miki bawai ta turo miki ta waya ki gani ba , kina gani miyanki ya fara tsinkewa saidai ki kalla ki ƙara kallo kina aimu ansha damu mukam mata muka rako wasu sun more duniya muko dai gamu nan rayuwa har yanzu bata canja ba. Abota ta ƙulle mai girma kowa yana ziyarta ɗan uwansa , yayin da suka shawartar junansu ta hanyar tura saƙo wa junansu ta whatsapp , ita dai mamaciyar tana tura ƙorafin mijinta ne idan yayi mata abu kaɗan , yake "yar uwata ki kwantar da hankalinki yatsun hannunki kawai kika kalla kinsan ba tsawonsu ɗaya ba wani yafi wani wani kuma bai kai wani ba , ita rayuwa bata yuwuwa ace kullum ke abinda kake so shi zaka samu dole , ita rayuwa juyawa takeyi wata rana asha zuma wata rana a lashi maɗaci haka rayuwar take tafiya duk wanda kika gani yana da tashi damuwar idan mai haƙuri ne ya ɓoye sirrin shi wa rayuwarshi da zuciyarshi ke kuma mai surutu jira kike a tara taron sabga biki ko suna duk inda kika zauna harshenki ake ji ke sarki matsalar gidan aure kullum an miki , kuɗin cefanenki bai kai ba , waya aikeki ? Waya sa ki ? Duk namijin da kika gani duniya babu namijin da yake so afi matarshi wanda duk baima iyalinshi ba baya da iko ne , idan ko maƙetacin namiji ne yana dashi ya ƙuntata miki barshi da Allah ja bakinki kiyi shiru ki lulluɓe aibin mijinki sai Allah ya lulluɓe miki naki.... Bayan ƙawance yayi girma ta waya sai aka fara ziyartar juna , mai mutuwa itace ta fara zuwa gidan rayayya tare da yaranta dan sada zuminci an tareta da shagali mai girma ta hanyar tara mata abubuwan motsa baki na zamani irin wanda bata taɓa ci ko sha a rayuwarta ba , an yini ana fira kowa yana faɗar irin rayuwar da yakeyi a gidan aure , yayin da ita wacce akaje gidanta take faɗo nata nasarorin rayuwar , mai mutuwa kuma ta hankaɗe zuciyarta taci gaba da tona asirin mijinta ta hanyar nuna gazawarshi wurin riƙon gida , bayan ta tashi tafiya ita wacce akaje gidanta ta shiga store ta ɗan tattaro mata kayan abinci ɗanye , irinsu shinkafa , taliya , makaroni , cuscus da dai sauransu ta haɗa mata da ɗan kuɗi bayan ta haɗa mata da kwancen kayan sawa.... Bayan an kwana biyu ƙawa tace itama zata zo , dan haka mai mutuwa ta hana ma kanta zaman lafiya ta faɗa maƙota neman rancen kuɗi wai ƙawarta zata zo bata so tazo ta raina mata , haka dai tayi ta faɗawa maƙota tana neman rance harta samo tazo itama ta haɗa irin tata ƙaryar , bayan ƙawa tazo ana fira ne tace mata amma yadda kike faɗar talaucin mijin naki kamar bai kai ba gashi komai na gani babu dai wata damuwa , hmmm "yar maular saita buɗe baki taci gaba da sana'ar nata tunda taga idan ta faɗi damuwarta kuɗi ake bata dan haka tace tou duk wannan da kika gani bashi na ciwo kuɗin a maƙota dan in fita kunyarki kindai san hausawa sunce abokin cin mushe ba'a nuna mishi wuƙa , taci gaba da ɗimi faɗi ba'a tambayeta ba , amma ni a gani na wasu matan sunayin "yar sana'a haka a gida dan su taimakawa mazajensu da abinda suka gagara yi musu. Da ƙawa ta tashi tafiya taba mamaciya kuɗin da suka gigita mata lissafi tace ta biya bashin da ake binta ita kuma tayi ta zabga , haka dai akaci gaba da abota rayayya tana taimakon matacciya sosai , ganin ana yi mata hauka da kuɗi yasa ta gaji ta tambayeta kodai tana kasuwanci ne ? Tace bata kasuwanci bata siyar da fari ko baƙi tana da abokai ne dai masu taimakonta a waje , ta nemi ƙarin bayani aka bata sirrin abun dan haka babu wani tunani ko hangen abinda zaije ya dawo itama ta yanki kati ta faɗa harkar bariki yanzu yau wa gari ya waya.........? Bello rungume yake da kwalba har suka iso inda aka ajiyesu ake basu horo , Ashiru kasa taɓa kwalbar yayi ya barta a hannun Bello yadai faɗawa mai gida sunje sun dawo , mai gida yace kawai yaje abunshi..... Bayan sati ɗaya Dikko yazo gidanmu a ranar da yace zai dawo kuma ciki ya shiga Inna da kanta ta lallaɓa ta nema masa abun daɗi kamar yadda ya faɗamin kuma yaci naji daɗi , daya zo kuma ya tanbayeni akan yadda akayi na saka Safiyya karuwanci nace ni babu ruwana kawai dai naji haushi ne sunamin gori na zama karuwa ranar da na rabu dashi a hanyarmu ta komawa makaranta mukayi faɗa na dawo gida ranar da suka ganni shine sukayi ta tura yaransu gida wai ga karuwa nan karna ɓata musu tarbiyar yara abin yamin ciwo shine na faɗawa Aunty Mamy daga nan bansan yadda akayi ba , Dikko yamin faɗa sosai kamar zai dakeni dan harsai da Inna ta kirani a waya dan a palo muke tana bedroom , ta tambayeni abinda ya haɗamu ban faɗa mata ba dan har Dikko yazo ya tafi Inna bata fito ba , A ranar ya sauke hidima wa Inna yayi jib da kwano na kuɗin da wallahi saida Inna ta ruɗe data gansu danni dama kyauta ta da Dikko biyu ce daga kuɗin daya bani a makaranta sai wanda ya sakomin a mota nasha mai da Umar ya kawomin wacce Al ' ameen ya ansa aka bawa Jiddah ita take hawa , sai kuɗin daya bani a ƙofar gidanmu ban ansa ba , ranar kam saida ya gigita Inna yasa mata mantuwar dole da manya kuɗaɗe a palo ya ɓaresu saman kujera ni kuma yayi fushi dani yai tafiyarshi saboda na haɗa Safiyya anyi iskanci da ita da baban Mardiyya duk da nace bani bace yace ba abinda ya dameshi bashi naci zamu bayan aure. A ɓangarensu Bello kuma bai saki Dady ba amma tunda Momy tayi magana yasa aka sassauta bala'en da ake musu , an canja musu wurin zama ana basu abinci mai kyau shi Dady kuɗi kawai zai bayar ya kama gabanshi amma yace yana jiran wasu kuɗaɗe ne suzo saiya bayar , Tun washe garin ranar da aka ɗauko kwalba Dikko yasa aka tara manyan malamai yayi musu bayanin abinda yake so na za'ayi masa saukar al'qur'ani sau goma a rana har tsawon kwanaki talatin , tou an buɗe kwalba kamar yadda Bello yace malamai kuma suka ci gaba da sauka kuma ragunann nan goma duk ranar duniya idan akayi sauka haka ake yankesu ana raba naman sadaka. Ranar da ya kama zuwa kotu banje ba lawyer Dikko ya tura bayan ya faɗa masa yadda kuɗi yake , idan kuma an gama shari'ar yana ƙarar baba ƙarami akan ƙazafin da yayi ma matarsa kuji wani neman rikici da rashin san zaman lafiya na Dikko kuma........! Maganar Bello daya faɗa shine ya kashe Binna da kanshi nayi amfani da wata magana daya faɗamin a police station cewa , inji tsoron Allah in babu nan akwai ranar hisabi duk wanda yaci zalin wani dai² da ƙwayar zarra ubangiji bazai barshi ba , ki daina ganin kin samu dama ta taƙin lokaci yasa ki manta da rayuwar gaba , karki biyewa zuciya ki kafa abinda zaisa kiyi nadama wata rana , tunda har yayi imani da ranar hisabi bazan bar akashe Bello ba zamu haɗu ranar hisabin dani dashi da *BA BINNA* wannan shari'ar Allah kaɗai zaiyi ta....... Hafsa kuwa tana tsaye wurin ganin ta gano inda kakar Ba Binna take kuma ta faɗawa Hajiya cewa idan harta ganosu saita faɗa musu itace silar mutuwar "yar su kuma tana roƙo Allah yasa masu zuciyane su kasheta kowa ya huta mai baƙin halin masifa kamar zuciyar fir'auna. Tunda nayi mafarkin an kashe wata matar aure a Qerau ban sake ganin mutumin a bacci ba kuma ban faɗawa Dikko ba , Dikko ya riƙo wuta sosai ya matse lamba wa Dady a tura gidansu An mata , Dady yace tou kadai ga yadda Mom inka take hawa da rana ɗaya bata sauko ba abun nata kullum gaba yakeyi akan bata yadda ka auri yarinyar nan ba , Dikko yace Dady nayi nisa fa za'a samu matsala Dady yace yanzu ya kake so ayi ? Ka tura "yan uwanka kawai su an somin auren ta babu wanda yaji babu wanda ya gani , Idan kuma bayan anyi auren matsala ta shigo fa ? Babu damuwa Dady ni zanji da duk wata matsala , shiru Dady yayi yana nazari sannan yace daga neman aure idan abun ya warware ba'a ɗaura ba fa ? Dikko yace babu maganar neman aure kawai ɗaura aure za'ayi daga nan sai ayi duk wadda za'ayi , tou ina zaka ajiyeta Babana ? G R A tare da Jiddah , Babana yarinyar nan bata iya zama da Jiddah gaskiya , Dady nidai tare zasu zauna Allah ya bada sa'a kawai zakace , murmushi Dady yayi tare da cewa Allah ya tabbatar da alkairi Dikko ya ansa da amin tare da faɗa masa ranar juma'a ne , Dady yace Allah ya kaimu zai tafi da Momy ta rakashi ganin likita kafin su dawo anyi komai an gama........... Dikko da kanshi yazo ya samu Inna sukayi magana yau duk laɓe²nta saida ya ganta kuma ya faɗa mata cewa ya tsaida ranar aurenshi da An mata ranar juma'a saura kwana 8 daga yau kenan , Inna tace ita gaskiya kwana 8 yayi mata kusa² tana da hidima sosai , Dikko yace shi baya buƙatar wuce wannan lokacin , kuma wane hidima gareta ta manta da yanzu An mata tayi aure da Sultan ? Ko sai nashi ne za'ace yazo da wuri ? Kodai har yanzu bata daina fushi dashi ba ? Shiru Inna tayi bata bashi ansa ba , saida ya ƙari maganarshi ya tashi yauma kuɗi ya safke mata na mamaki mai nuni da ko rashin kuɗi yasa kwana 8 yayi mata kusa² , baima saurareni ba kuma dana gaishi bai ansa ba. Bayan tafiyar Dikko Inna ta shige ɗaki ta kira ƙawarta suka tattauna dan ita Inna kallon ɗan duniya take ma Dikko shi yasa ta fara neman hanyar da zata gyara "yarta gani take wannan hanyar itace mafita.... Da mijinta yazo ta rattafa mishi auren Sultana yau saura kwana 8 aurenta , waishi ba'a kyauta mishi ba ya za'ayi masa haka abu babu notice tace yayi haƙuri , kuma daya tambayeta wanda Sultana zata aura aure haka kwatsam , cewa tayi sunanshi Muhammadu , waye ubanshi kuma sun bincika halinsa har zata ɗauki Sultana ga baƙon fuska ta bayar tayi mata aure haka kamar ta gaji da ita ? Inna tace sanin ubanshi halinshi da komai nashi sa fuskanci juna idan anyi auren , Inna ranar jinta takeyi kamar ba ita ba , tana cikin farin ciki mara musultuwa cikin ƙanƙanin lokaci gidanta ya cika da taron ƙawayenta ƙasaitattun mata masuji da kansu a gidan aure tou wai ita Inna ina ma ta samu wa'anan ƙwanƙwasashin mata ? Suke ta huɗɗinsu Inna ta faɗa musu Sultana Dikko zata aura , amma bansan abinda yasa ta ɓoyewa mijinta ba , Bayan kwana biyu yadda Dikko yasa aka haukata gidanshi yasa Jiddah ta gane aure zaiyi dan haka ta fara ɓarin kaya tana ta hauka tana zage² gaba ɗaya ta tashi hankalin duk wani wanda yake da dalilin sanin Dikko zai aure , tou ai babu mai iya tunkarar Dikko da zancen dakatar da aure sai Momy kuma bata nan Dady yajata sunyi tafiya dan Dikko yayi hidimarshi ya gama saida tazo ta samu amarya , Jiddah bata gama tabbatar da Dikko zaiyi aure ba saida taga katin ɗaurin aure kuma Umar ne ya kawo mata shi , Dikko yana kwance yana bacci ta shigo ɗakin da gudu bayan Mardiyya ta tunzurota ta shigo tana ta ɓarke²n zagi tana aibata shi san ranta bai mata magana ba yayi kamar bacci yake dan yasan zafin da raɗaɗin da mata keji yayin da za'a musu abiyar zama , ya gani yadda Yayarshi tayi da akayi mata abiyar zama aurenta kamar zai rabu dan Momy ɗaure mata ƙugu tayi ta dawo gida , ba abinda zaice ma Jiddah tayi duk haukanta kila haka zaisa ta samu natsuwa idan kuma tayi ƙoƙarin keta iyaka zai nuna mata nashi haukan sai yayi mata dukan da har ya gama auren tana saman gadon asibiti saboda shi abu ƙalilin ke ƙufular dashi.......! 10/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 74 Yaye bargon da yake lulluɓe tayi taci gaba kuka tana ɓarke²n zagi tana ma Dikko gori wai yaji kunya ya rasa wacce zai aura sai karuwa ɗiyar ɗan caca jahila matalautan da suka kasa siyen gidan zama saidai gidan haya ai duk talaucin da yasa mutum ya rasa gidan zama wannan talaucin ya kai abun a duba matsiyatan banza da wofi , Me yake nema a wurin yarinyar nan ? Bayan ita tafi ta komai kuma su masu kuɗi gidansu Sultana fa ? Duk abinda ake nema ga mace Sultana basu da , duk abinda ya cancanta ka aureta saboda shi babu ko ɗaya da take dashi , jahila daƙiƙiya mace babu ilimi ai kwankwon ashana ce domin shi ilimi tushe ne mai nuna dogon zango , kaga tun nan abinda kake nema baka samu ba , halin kwarai jari ne , bata dashi , su kuma kuɗi jigone masu nuna isashshen iko a cikin abunda na lissafo wane take dashi ? Ai ni ina da duk abinda kika lissafo ko ? Ai kaine kake dashi ba ita ba , to na bata ilimina na bata halina na bata duk komai nawa ke kinsan An mata kuwa ? Ki bari tun kafin raina ya ɓaci na fara maganganun da zakiji babu daɗi dan haka ki tattara mutuncinki ki barmin ɗakina ! Bana tafiya sai kayi maganganu akanta munafikin banza maci amana , murmushi Dikko yayi cewa nine munafiki Jiddah ? Maci amana ? Wace irin amana ne naci haka da har kikemin gori ? Ban sani ba baƙin munafiki , sauka yayi daga saman gado yana cewa Allah ya baki lafiya ya wuce toilet , ita kuma taci gaba da ɓaɓɓarka mishi zagi harya gama abinda yake ya fito Jiddah bata daina sokawa Dikko zagi ba. Inda take tsaye yaje ya riƙota cikin rarrashi yace ni ne ? Kwantar da fuskarta tayi saman ƙirjinshi tana kuka cikin shashshekar kuka tace Yaya dan Allah bana san auren nan , tou muje saman gado saiki faɗamin kinsan ban cika jin magana daga tsaye ba , ni bazan hau gado ba , tou tunda bazaki hau ba fitarmin daga ɗaki idan ba haka ba zan hau dake dole kuma jikinki zai baki labari , da sauri ta sauka daga jikinshi tayi waje da gudu tana kuka , murmushi Dikko yayi yace matsoraciya. Saman gado ta faɗa taci gaba da kuka a zuciyarta kuma jinjina irin muguntar Dikko takeyi macuci idan har yana jin haushin mace sai yayi mata ƙeta mamugunci nufinshi yashata basilla murmushin mugunta Jiddah tayi a zuciyarta tace badai Yaya bane ba ? Kije kin samu Sultana idan dai tsintuwar fatalwa riba ne..... Inna da kanta taje ta faɗawa Kaka Sultana zatayi aure Kaka tayi murna sosai kuma tayi ma Inna da Sultana fatan alkairi , ta kuma ƙara da cewa amma me yasa saida aure ya rage kwana 6 zata faɗa mata ? Inna tace mijin ne ya zaɓi haka , Yayarta dage zaune tana saurarensu tace badai girin² ba tai mai , Inna ta gane ta maso habaici maso faɗa wanda ya tanka shi yafi tou bata da lokacinta , Tunda Dikko yazo ya tsayar da ranar aurenmu dani dashi bai sake dawowa gidanmu ba kuma kona kirashi waya ya daina ɗauka ma , Inna kuwa kullum bata da aiki sai kwaɓe²n kayan mata tana bankamin saidai tsareni tana zagina wani lokaci hada mari wai bana gane wannan gata ne sai naje gidan aure , tun ina sha ina amai har cikina ya haƙura ya riƙa riƙeminshi dan idan zansha so goma na amayar Inna bata gajiya zata sake kwaɓa masifa ta bani na kwankwaɗar wa cikina. Labarin auren Dikko ya zaga kaf illahirin birnin garin katsina mutane sun fara canfashi ya cika aure² ya auri waccan ta mutu bai tsaya hutawa ba ya auro wannan duka yaushe yayi auren har yake tunanin sake auro wato ? Yayin da wasu kuma suke gani izzar kuɗi ce ke nuna ikonta shi yasa yana matashin shi zai aje mata biyu cikin shekara ɗaya.... Dikko kuwa babu abinda ya dameshi da labarin dake yawo a gari shidai zaiyi , tunda ya taho kuma yaga mai tareshi matsalar bai faɗa ba zaiyi amma da zaran ya yanke hukunci tou fa ko kanshi baya saurara , Duk "yan uwan Inna dasu ake hidima kuma hada yayarta kwansu da kwalkwata suna zuwa ba wanda aka rage tun bayan tsaida ranar auren da kwana biyu suka fara zuwa , kowa tambayar Inna yake tou ina maganar kayan ɗaki ? Saidai tace komai za'ayi , a kwana biyar za'ayi ? Inna tace Eh , Tou basu sani ba kayan ɗaki kansu da kayan kicin duk abinda iyaye kema "ya "yansu dan fitar dasu kunya Dikko yayi saboda tunda ya fara aikin gidanshi na goruba inda zai ajiyeni daga farko dama shine yake da burin zuba komai na gida tou kayan nan yasa aka sauke su a wani gidan mijin Inna sai idan za'aje jere Inna tasa aje a ɗauka a can yadda za'ace itace tayi. Komai dai na hidimar auren nan cikin munafurci akeyinshi , dan ko lefe Dikko ne ya kawoshi da kanshi da daddare misalin 2:54am dashi da yaranshi bansan sunzo ba haka kuma banji tafiyarsu ba , saida safe na tashi naga wasu irin lafiyayyin akwatina masu tsinannen tsada da kyau na tashin hankali , akwatina 24 da wasu irin ƙattin jikkuna biyar babu wanda ba'a takeshi da kaya ba , wannan shine faɗawa mai zuciya biki ba mai tarin dukiya ba tou Dikko komai ya haɗa , nidai ban buɗe ba amma da Inna da mijinta saida suka zindire lefen nan kaf suka ganshi gaskiya naira wurin lefen nan taci bugu harta gode Allah wallahi komai na cikin lefen abun burgewa ne babu abu na banza komai baka isa ka raina ba saidai hassada. Ƙawayen Inna "yan duniya lokacin da suka zo suka ga lefe sunyi ɓarin maganganu na isashshin mata wai Dikko dai ɗan gaye ne wayayye tebirin farko wallahi magana ya gayamin a lefe turaruka kamar suce wayyo Allah masu tsada abinda dai Dikko ke nufi yana san ƙamshi , wuraren daya kamata nayi amfani da turare suke faɗa duk abinda suka ɗaga a lefen sai sun faɗa fita nayi na bar musu ɗakin dan abinda na lura basu da kunya..... Washe garin da aka kawo lefe akaje ganin ɗaki Jiddah tayi wulaƙanci tayi hauka marar ɗaura zani tayi bala'en daya tada hankalin duk wanda yaje ganin ɗaki Jiddah tace babu wata mace data isa ta zauna mata gida , wallahi wannan gidan tane daga ita sai mijinta , Dikko nata ne ita ɗaya babu maishi sai ita gidanta ramin kura ne daga ita sai jama'arta sai kuma "ya "yanta babu wata banzar ɗiyar ɗan caca data isa ta zauna mata da mijinta amma idan har Sultana ta shirya mutuwa ta shigo gaba ɗaya ma auren mamarta akayi wallahi , amma idan har Caca ta shigo zata goga da ita a kishi tou tabbas tana musu albishir kwanaki bakwai cas ta bawa Caca a gidanta zata dawo babu jimawa idan tana da sauran shan ruwa gaba kenan idan kuma bata dashi su tarbata a rimin badawa , sunan wata maƙabarta ne........... Ta bubbugi ƙofofi ta rufesu ta hana ganin ɗaki tayi maganganu masu tsauri kuma kalamanta suna da kaushi ta fa barbaɗa rashin mutunci iyakar ƙarfinta guyawu a sace "yan ganin ɗaki suka dawo ba tare da sun samu damar ganin ɗaki ba , Inna da taji bayani kuwa cewa tayi to saidai ya raba musu gida , Inna ta yaba da masifar Jiddah baza ta yadda a haɗe Sultana da Jiddah ba dan cutar mata ɗiya za'ayi idan kuwa Dikko bazai raba musu gida ba ta yadda saidai a fasa auren nan, da ƙawayenta suka bata haƙuri cewa tayi har Sultana ma nawa take ? Ta gama haɗiye wani dafin zata fara kwankwaɗar na kishiya ? Masifa nawa zatasha ? Bazata laminta ba gara tasan abinyi tun kafin tabar nigeria idan zai yuwuwu ayi idan bayayi a barshi kowa ya samu natsuwa babu wanda zaisa ma "yarta ciwon zuciya........ Da daddare bayan kowa ya kama gabanshi Inna tayi ma Dikko waya tana san ganinshi , yace mata baya nan yaje kaduna amma yana shigowa katsina babu jimawa idan ya dawo zaizo insha Allah , fatan isowa lafiya tayi masa ta kashe wayarta , kallona tayi tace idan kin ga dama ki tashi kije kiyi wanka kin zauna bursunai² dake kamar an ƙwatoki bakin kura , ban kalleta ba nace ai ko ɗazu nayi wanka , dan ubanki yanzu ma sai kin ƙara wani , ai Dikko dai kike so ko ? Badai kin zaɓeshi ba ? Yanzu kika fara wanka tunda dai kina san Dikko kije kinsamu , Dikko da kike ganinshi ƙyalƙyal na rariya ne zamani ne da kanshi idan zaki iya ga fili ga mai doki , tun cikin mutunci nace ki rufawa kanki asiri ki auri Sultan kikaje kikayi ta hauka tun ina nida ke saida kika ɗaga murya aka jiyoki uwayen sharri suka kira ubanshi a waya suka faɗa mishi bakya san ɗansa sun nemi sharrin duniya sun ɗora miki hankalinsu bai kwanta ba saida suka ga an fasa auren nan , hmmm Dikko dai ko ? Bazan miki baki ba. Da kin auri ɗan uwanki asiri a rufe babu wanda yaji ya gani amma dake ke sakarya ce baki san wanda yake sanki ba kin biyewa ƙuruciya da san zuciya ga yadda ta kaiki Caca ma take kiranki tsabar ta maidake jaka ta ƙarshen benci iskanci da rashin kunya kuma duk garin nan ba na gaba da Dikko , "yar uwarshi ce can zaki musu iskanci su haɗe miki kai suci ubanki nidai bazan fasa tafiya ba , india ba fashi wallahi saina bi mijina zan baki makullin gida idan bai miki daɗi ba kizo ki buɗe ki shiga ko ki tafi wurin ahalin ubanki gidan Hajiya dai yai miki tsururu cikin hayani tace ki tashi daga gabana in daina ganinki , da sauri na miƙe zan fita tace baza kije kiyi wanka ba ? Jiki a sanyaye na dawo na wuce ciki danyin wanka ! Cike da damuwa Inna ta miƙe taje ta nemi wasu magunguna ta damesu da madara tana damawa tana mita Dikko ɗan duniya idan ba'ayi shirin tashin bama²i ba ai za'aji babu daɗi , Inna a ganinta wannan shine mafita ta mayar da cikin Sultana kamar wata tsohuwar rijiya duk abinda ta kwaso a cikinta take juyewa saboda wannan garinka da take bankawa "yarta abinci ma kwata² ya daina ciwowa gareta , wata "yar duniyar ƙawar Inna kuwa ke dafo wata munafikar kaza wacce ba'acinta ma sai an kashe fitila kamar kazar tsafi , Sultana tabi ta rame ta ƙanƙance saboda masifar Inna da magunguna idan ma tace bata sha haka zata rufe ta da masifa sai tasha a karkaɗe kofi , Ina fitowa daga wanka na hango Inna zaune gefen gado da ƙofinta riƙe a hannu , gabanta kuma kaskon garwashi ne , a takure nake tahowa dan ida bayyana a cikin ɗaki a tsawace tace min kiyi tafiya kamar kina da rai garwashin nan zai siƙe kuma kin sani sarai dakel aka samomin shi tunda gabanki nake ta nemansa tun safe , Inna shi kuma wannan ɗin na mene ne ? Na ubanki ne , tayi maganar tana kunce haɓar zaninta ta ciro wata "yar farar leda ta kwance tana ki wuto kizo ki duƙa nan , matsawa nayi kusa da ita nayi yadda ta nunamin ita kuma ta zazzage abinda yake cikin ledar duƙa tana cewa da kinsan ko nawa na siya saikin yaba ma ƙoƙarina , ko inda take ban kalla ba haka kuma ban bata amsa ba har ta uwarce ni dana tashi , tashi nayi ta miƙomin kofin ansa nayi nasha ta zuba ruwa na girgije na haɗiye , ɗaukar kwaskon tayi da kofin ta fita ni kuma na ɗauki kayana na saka na kwanta dan bacci nakeji bana wasa ba. Tana fita ɗakin mijinta ta wuce bayan ta ajiye kayan data fita dasu a kicin , ni kuma naci gaba da baccina , saida Dikko yayo mata waya yazo ta shigo dan taga ko na shirya ta ganni kwance ina bacci , cikin takaici ta tasheni bayan na tashi tace shine kinyi wanka ki iya ki shirya kika wani kwanta bacci ? Ƙara takurewa nayi da niyar komawa bacci tace ki tashi idan kin ga dama ki gyara jikinki kafin in gama magana dashi yana ƙofar gida , cike da farin ciki na sauko daga saman gado Inna kuma ta koma palo tana jiran shigowar Dikko.... Fuskata na wanke da bakina na fito , lokacin har Dikko ya shigo kuma Inna ta ratta mishi cewa saidai fa ya raba mana gida dan bazata yadda ba ɗiyarta tayi rayuwar takura , sundai yi maganarsu sun gama abinda dai naji Dikko yana bata haƙuri cewa shi babu macen data fi ƙarfinshi kuma gidanshi bai gagareshi yayi hukunci ba , inda yaso ya ajiye An mata bai gama aiki ba zaman na wani lokaci ne zasuyi kuma wani abu mara kyau bazai faru ba , Inna tace tou kai dole sai kayi auren ne yanzu ? Dikko yace ba dole bane ba lokaci ne yayi tunda ai ba yau naso muyi auren ba , Inna tace to gaskiya saidai ka bari idan ka gama aikin gidan sannan , mijinta ne yace ba'ayin haka idan bashi da ikon raba musu gidan ya zakiyi kenan ? Sai a fasa auren , ki daina haka ki musu fatan alkairi da addu'ar zaman lafiya , ba haka Inna taso ba dan na fahimci bata san gardama da mijinta , bayan sun gama ne suka shigo cikin bedroom in ita da mijinta , Inna tacemin kije ku gaisa farin ciki fal zuciyata na tun kari hanyar fita , zan fita daga cikin bedroom in naji mijin Inna yana cewa wai ba DK bane ba ? Inna tace waye kuma DK ? Bawan Allah cikin dai kokonto yace ba shi bane ba kamarsu dai tayi yawa wallahi shi wancan wanda nake magana bana tunanin ma zaizo nan , bata bashi ansa ba kuma sai suka rangaɗo suka biyo bayana suka fita daga ɗakin mijin Inna kuma yana ƙara kallon Dikko. Cike da farin ciki na isa wurin Dikko na rumgumeshi rabon da in ganshi ko inji muryarshi harna manta nayi faraicin lallausan jikinshi mai kama da bayan zomo , maimakon yaji daɗi ko yayi fara'a sai yace ke kullum sai kin hawomin jiki kamar wata mage ina dai lissafi kuma da guda² duk saina rama , gyara kwanciyata nayi saman jikinshi saida naja gemunshi sannan nace yanzu ma ka rama mana nayi maganar ina kallon cikin idonshi , murmushi duniyanci yayi cewa a , a ni na isa inzo har gidanku in rama abinda kikai min ? Zaki isko ni har gida saurin me kike ne ? Murmushi nayi ba tare da na sake magana ba , shi kuma yace meya sameki naji kin rage nauhi , da nayi niyar faɗa mishi abinda Inna takeyi amma sai wata zuciyar ta haneni kuma gaskiya dai idan ba'ayi hankali ba saina faɗa mishi abinda akemin ! Shi kuma a ranshi tunani yakeyi kila fa itama An mata anayi mata irin abinda ake ma "yan gidansu idan za'ayi musu aure , jinjina kanshi yayi tare da cewa Allah ya sawaƙe idan kuwa anyi mata cutar yarinyar nan zaiyi da yawa , An mata kawo kunnenki in tambayeki , matsawa nayi tare da miƙa kunne ne saitin bakinshi cikin raɗa yace naji kin rage nauhi meya sameki ne ? Wata irin kasala naji ta lulluɓemin jiki na ƙara kwanciya sosai a lallausan jikinshi ban bashi ansa ba Shi kuma yaci gaba da cewa Mama take baki wani abu ko ? Kaina na ɗaga mishi alamar Eh , ɗago fuskata yayi idanuwanmu suna kallon cikin idon juna yace ai na sani hada kaza ko ? Shiru nayi ban bashi ansa ba , yace ai mu na gidanmu ina kallonsu wallahi hada tattabaru ake basu mutum yazo ya kasa cin abinci nasan kema hada irinsu ake baki ai ni gaskiya wannan shigamin haƙƙin rayuwa akayi gaki an takura miki an ramar min dake babu gaira babu dalili saboda ɗaukar alhaki , ni babu wata kaza da nake ci , hmmm haba An mata aiko baki faɗa nasan komai miye baƙona a mata ? Ya fara lissafe²n kayan mata kamar wata tsohuwar karuwa bayan ya gama yace sune baƙin nawa duk abinda na faɗa nasan aikinshi idan baki sani ba , Allah dai ya sawaƙe ya kuma kyauta wahala saukar min daga jiki karki shanye daɗin ke ɗaya.... Murmushi nayi sannan na tashi na koma saman hannun kujerar da yake na zauna , mukaci gaba da firar duniya bana soyayya ba yana bani labarin abokin Yazeed da aka kama yace wallahi An mata fitinar zamanin nan yana bani al'ajabi saboda tsabar ƙazanta kina matar aure dan karnikanci kinabin mazan waje , ni na rantse da Allah da nine mijin idan nasa an kamashi Allah ya tsinemin , dariya yayi sannan yace dama ya sani yana riƙe banza yayi masa irin yadda akayi ma Saminu ya fashe idon dake ganin matan , nidai da nine ƙarya mishi wuya kawai zanyi ya mutu a rage annoba a ƙasa , dariya yayi yana kallona yace kiyi dariya mana , ƙinyin dariyar nayi kuma ban kalleshi ba , taɓoni yayi cewa An mata miye ? Ai kai dama baka iya komai ba daga duka sai kalmar kisa shikenan abinda ka iya faɗa , ke karfa ki raina min hankali , daga haka fira ya koma rigima wai wannan "yar maganar harya ɓatawa Dikko zuciya ni kuma bada wani manufa nayi maganar ba , tsoki yayi tare da miƙewa cikin ɓacin rai ya tunkari hanyar fita , Binshi nayi da ido harya fita daga palon , saida ya fita na tashi nabi bayanshi har ƙofar gida amma banyi mishi magana ba , ina fitowa duk su Ashiru suka gaisheni cikin girmamawa kaɗan na ansa gaisuwar nabi Dikko da aka buɗewa mota kafin a rufe na riƙe murfin motar nace kayi haƙuri idan kaji babu daɗi insha Allah bazan sake ba , ba tare daya kalleni ba yace na yafe miki , yawwa ngode na bashi ansa sannan na juyo da sauri na dawo cikin gida , murmushi Dikko yayi yace kura ta fara lafiya yau wace rana bata biye an tashi hankali ba , murmushi ya sakeyi tare da kwaikwayon maganar Sultana wai da haka zatace naje nace mahaukaci aljannu kamar iccen tsamiya ! Hmm jarumata kenan..... Ina komawa kwanciyata nayi naci gaba da baccina dan yau su Hajiya Inna ba'a ɗakin za'a kwana ba... Inna da mijinta kuwa bayan sun fita daga palo mijinta ya tabbatar da Dikko ne dan haka yace ma Inna wane gigi ya kaita ? Shidai babu ruwanshi tunda dama tun farko ta ɓoye mishi wanda Sultana zata aura Dikko dai ba kanwar lasa bane ba , amma yana musu addu'ar zaman lafiya kuma bazaiyi binciken inda Sultana da Dikko suka haɗu ba tunda dama ba'a so ya sani....... Duk iskancin da Jiddah ta zaƙula ma "yan ganin ɗaki bai isheta ba Mardiyya ta tirota tace idan ta saki ta tsaya sanya za'ayi babu ita ta tadawa Dikko hankali a daren nan ta hana mishi bacci , shi kuma a gajiye ya fito daga toilet ɗaure da rigar wanka a jikinshi dan baya buƙatar komai a halin yanzu sai bacci , da masifa Jiddah ta shigo ɗakin kallo ɗaya Dikko yayi mata ya ɗauke idonshi daga kanta ya matsa inda ya ajiye kayanshi na jersey ya ɗauka ya saka , Jikin socket ya matsa da niyar kashe fitila ta riƙe mishi hannu , kallon hannu yayi sannan ya kalli Jiddah na tsawon minti ɗaya yasa hannun haggunshi ya kashe fitilar ya koma saman gado ya kwanta , yana kwanciya ta kunna fitilar , jinjina kanshi yayi sannan ya sauko yazo ya kashe fitilar a karo na biyu , saida ta sake tabbatar daya kwanta ta sake kunna fitilar yanzu bai sauko ba yace kasheta , bazan kashe ba , ki kasheta nace , bazan kashe ba nace maka , rufe idanuwanshi yayi sannan yace ke........ Ki kashemin fitila nace , a ɗan tsorace Jidda tace bazan kashe ba , cikin wata irin murya Dikko yace na rantse da girman Allah idan har kika bari na sauko daga gadon nan wallahi saina takaita miki rayuwa zuwa ɗaya zan miki na tasheki aiki har abadan duniya , da sauri Jiddah ta kashe fitila tayi waje da gudu tana kuka.... Tsoki Dikko yayi tare da ɗaukar wayarshi ya fara kiran An mata , saida ya kirani so biyu ana 3n naji cikin faɗa yace wai ke An mata sai inta kiranki sai kin gama iskancinki zaki ɗauki waya , a sanyaye nace kayi haƙuri bacci nakeyi , nine baccin , kayi haƙuri bazanyi haƙurin ba duk kina nufin bakiji ina kiranki ba sai yanzu munafurci kawai , cikin ɓacin rai nace kai Dikko kaima munafurci , murmushi yayi sannan ya ɗaga idonshi dakel saboda baccin da yakeji yace nine munafurcin ko ? Haba kaima wallahi neman fitina gareka , tou yi haƙuri An matana raina ne ya ɓaci kuma bacci nakeji na fiso inyi bacci dake a raina kiyi haƙuri don Allah idan dake ne zanyi bacci idan bake bace wallahi bana iya bacci raina zaiyi ta ɓaci a banza kiyi haƙuri mu raba ɓacin ran kin yafemin ko ya ƙarasa maganar yana jan wani irin numfashi mai ɗauke tunani yace muyi bacci mai daɗi ki ga Dikko a baccinki jarumata , Shiru nayi banyi magana , a kasalance ya kira An mata cewa meye ? Dakel na haɗiye miyan bakina banyi magana ba har yanzu , An mata.... ? Na'am , Dikko ne ? Umm tou yi haƙuri kinji zanyi bacci na gaji saida safe ya kashe wayarshi , yana kashe wayarshi yaci gaba da baccinshi cikin natsuwa da kwanciyar hankali saɓanin Sultana da bacci ya gagari idonta , Dikko baida adalci gaskiya shi kanshi kawai ya sani , matarshi ta ɓata mishi rai akan me zai kira wata da bataji ta gani ba kuma bata san anyi ba ? Ita Jiddah me yasa bayacin ubanta yadda yake ma Sultana ? Danni nayi imani da Sultana ce ta kashe fitilar nan wallahi sai Dikko ya zaneta , amma ita Jiddah sai tayi kwance² ta ɗana iskancin ta amma Dikko baya zane mata jiki irin yadda yake ma Sultana me ne ne dalili ? Shin san Jiddah yafi ko kuwa .....? Ranar da akaje jere ma Jiddah ta ɓara iskanci wanda yafi wanda tayi ranar ganin ɗaki , ta tara ƙawayenta ƙosashshin "yan iska kuɗin mota ta turama ko wace har naira dubu ɗari wai suzo su tayata tarar kishiya sun cika gidan ba masaka tsinke sai iskancin suke zazzagawa wallahi zaman jere bai yuwu wurin mata ba maza ne kaɗai suka tsaya dan kayan na ɗaurawa ne kunga kenan ba aikin mata bane na maza ne , ko iri ɗan tukuicin nan da ake badawa na jere duk Jiddah ta murjeshi ta hana , dama na ganin ɗaki ma bata basu ba , kai Jiddah riƙaƙƙar "yar iska ce mai tikiti lallai Dikko ya ɗauki alhakin Sultana da zai haɗata zama da Jiddah....... Bayan tafiyar matan suka faɗa kicin ita da ƙawayenta wai wannan kulolin da duk wani abu da aka saka mata yafi ƙarfin sayen ɗan caca dan haka tasa suka kwashe duk abinda take so aka kai kicin inta , ita kuma Mardiyya an tsaida ita a kicin tana dafawa Dikko da baƙinshi abincin da zasu ci sai waya yakeyi a kawo , "yar kwalbarta ta jawo daga cikin breziya ta kakkaɓe maganin ta kaf a cikin abinci , hamdala tayi ga Allah bayan ta tabbatar ta gama zubawa..... Banda faɗuwa babu abinda gaban Inna keyi ganin taron mata sun dawo suma kansu sunji tsoron Jiddah ina ita Sultana ? Ƙaramar yarinya wacce shekarunta bai kai na Jiddah ba gaskiya zalinci yasa Dikko zai haɗa mata "ya zama da Jiddah , da tsausayi ta kalli inda Sultana take tana shiri Dikko ya turo Ashiru ya ɗaukota ya kawota wurinshi bayan yace masa wai kar yayi tuƙin ganganci kuma karya biyewa kowa yayin daya hau titi ya ɗauka duk wanda ke saman titi mahaukaci ne shi kaɗai ne mai hankali , hijabi Inna ta bani na saka bayan na gama shirina , saida ta rakoni har bakin get ta koma ni kuma na fita na shige mota muka tafi.... Kallon kaina nakeyi a zahirance wai in banda abin Inna taya zata sadani da hijabi ? Wannan ma idan wani ya ganni ai sai a rainani umm to ya zanyi ? Haƙuri kawai zakiyi Maryama.... Tun daga ƙofar gida har cikin gidan motoci ne , sai dawakai da aka tara a wajen gidan da ciki ƙosashshi "yan gayun dawakai masu tsada wata irin haniniya sukeyi sun karaɗe kaf illahirin wurin da kuka , ciki Ashiru ya shiga ya samu wuri yayi parking sannan ya turawa mai gida saƙo isowarmu , Shima rubuto masa yayi wai mu shigo yana ciki bayajin daɗi cikinshi ke ciwo , da Ashiru ya faɗamin cewa nayi bazan shiga ba idan baya fitowa ya bari , a , a ranki ya daɗe kiyi haƙuri mu ki shiga , wallahi bana shiga idan bazai zo ba ya bari yasa an ɗaukoni tun daga gidanmu nan ɗinma bazai iya zuwa ba ? Idan yana zuwa yazo idan baya zuwa can shi ta matse mawa.... Tura masa yayi cewa bazan shigo ba , yace gashi nan yana zuwa , fita Ashiru yayi daga motar yana cemin ki jirashi yana zuwa , ya daɗe sosai sannan ya fito mutanen da basu gaisa ba suke gaisawa bayan ya gama ya taho wurin motar , Gaba ya buɗe kujerar mai zaman banza ya ziro ƙugunshi ya zauna a gajiye ƙafafuwanshi a waje bai rufe motar ba , kwantar da kanshi yayi jikin kujerar yace wallahi bansan abinda ya sameni ba cikina kemin wani irin ciwo kamar zan mutu , ai idan ka mutu ka huta , Eh na huta ke kuma taki ta ƙare juyowa yayi ya kalleni sannan yaci gaba da cewa ai nasan idan na mutu ɗan ƙaramin hauka zakiyi sai kin riƙa kwacewa ana riƙoki , tou ka mutum ka gani idan zanyi haukan , hmmm yarinya kenan kina wasa da lamarina An mata , nima kana wasa da nawa lamarin kedai kika sani , kaima ka sani dakel yayi "yar gajeriyar dariya tare da duƙar da kanshi ya riƙe cikinshi yace wai Allahna..... Jikinshi yana wata irin kyarma ya kwantar da kujerar daya ke zaune kai yana cewa matsa daga nan ke , gefe na matsa yana cewa kin dai yafe ni ko ? Tou zan mutu in mutu ? Wata irin ƙara nayi cewa ban yafe ba Dikko dake duƙe ya riƙe ciki da sauri ya ɗago yace mene ne kuma ? Ajiyar zuciya na sauke na kalleshi murmushi yayi cikin ƙarfin hali idonshi ɗauke da hawaye kaɗan yace ya akayi ne wai ? Fashewa nayi da kuka nace mafarki nayi zaka mutu yanzu , murmushi ya sakeyi cikin jarumta yace ina nan zaune kikayi baccin ? ya ƙarasa maganar yana min wani irin kallo , tou amma na ganka ka kwanta kace zaka mutu , Dikko yace anan ɗin na kwanta ? Eh , ba kin ganni gani nan zaune ba ? Idan ba kaine ba waye ? To ni An mata ya za'ayi in sani ? Wallahi na ganka , hannunshi ya miƙomin na riƙe yace ke... wai mene ne ? Ko yunwa kike ji ne ? A , a , banajin yunwa kalli idona in ganki , kallonshi nayi shima ni yake kallo bayan wani lokaci yace ya isa haka fita muje ya fita........ Ƙin fita nayi ina tunani to wai idan ba Dikko bane ba waye ? A dai² lokacin daya buɗe murfin motar ya fiddoni yana cewa yunwa nakeji amma banajin zan iya cin abincin can gaskiya....... 12/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 75 *_Ga saƙon godiya Ummiee Zaria Jikar Lerawa Sultana tace a gaishe ki tana miki fatan alkairi..._* Nifa bazanje ba kaje kawai zan jiraka a mota , da Allah wuce mu tafi banasan yawan magana ji nake kamar zan faɗi , nidai kaje abinka dan Allah , zaki wuce muje ko saina baki kunya , ai kaima zakaji kunyar , ni banajin komai idan ban ɗaukeki ba kice ba Dikko nake ba kuma idan na ɗaukeki saina fita ƙofar gida a tsakiyar mutane zan ajiyeki in dawo , Kaɗan ne daga cikin aikinshi dan haka nace muje badan halinka ba , naji muje dan naki halinki kuma da bakije ba yau da kinga yadda ake saɓanin igiyar ruwa , tafiya nayi na barshi a baya biyo bayana yayi yana cewa "yar raini magana fa nake kuma nasan kinaji na... Kai aini yanzu na girma banda lokacin yarinta , dariya yayi yace ai nine zan baki girman kinga kina ƙasana har yau har gobe kullum ma kina ƙasa ina samanki yarinya kin gane abinda nake nufi yayi maganar tare da wucewa yayi gaba da ɗan gudu nima da sauri nabishi ina ƙarema gidan kallo gaskiya wannan gida ya haɗu masu kuɗi basu da aike sai bautawa ƙasar da bata da tabbas duk wannan ginin a kwana a tashi sai an tafi an barshi kuma ƙasar ce zata hiɗiye bata gajiya... Wata "yar munafikar ƙara yayi "yar ƙarama yace wayyo cikina kuma bai daina tafiya ba nima ban daina binshi ba , gangarewa yayi ƙasa da gudu nima da gudun na bishi muka sauka muna sauka naga mun fito waje irin na farkon gidan amma ba inda Ashiru yayi parking ba , tsayawa nayi ina kallon wurin da mamaki jin ban biyoshi ba yasa ya dawo da sauri kamar za'a kamashi ya jani ta baya ina kallon wurin shi kuma yana jana da sauri , jinjina kaina nayi tare da cewa "yan gayu , ai kune gayun An mata mu "ya "yanku ne....... Taho jirana akeyi , juyawa nayi na kalli gabana nace ina zamuje ? Can zamuje ai , ni gaskiya bazan je ba , ke da Allah wuce muje yanzun nan kika gama cemin kin girma ashe har yanzu An matance , nidai gaskiya bazanje ba , mi yasa ne ? Nifa tsoro nakeji , tsoron mi ? Da Allah wuce muje ke komai sai kinyi yarinta , ƙwacewa nayi nayo hanyar da muka fito da gudu , shima da gudu ya biyoni harna fara hawa matakal ya riƙoni yace wai me yasa kikemin haka ne ? Cikin kuka nace nidai bazanje ba , jawoni yayi kusa dashi yace tou in rungumeki sai muje ? Nidai bana so , yace um ummm Dikko ne fa ya faɗa tare dayimin kallon ƙauna , zo jikina kiji natsuwa An matana , a gajiye na sauka jikinshi cikin mutuwar jiki , yace tou ya kikaji akwai daɗi ko ? Eyy tou sauka muje babu wani abu da zai faru wallahi.... Ka tabbata na tabbata miki ya ƙarasa maganar yana duƙuwo dai² bakina na sumbaci gefen fuskarshi yace yawwa jarumata muje.... Yanzu bai riƙeni ba mukaci gaba da tafiya ta wata ƙofar gidan da ba'a rusa ba amma an fasa ƙofa ya shigo cikin gidan muka shiga shine a gaba ina baya kamar yadda yace nazo jikinshi zanji natsuwa na samu natsuwar banajin tsoro cikin dakewa nake binshi har muka shiga ciki... Wani irin yagegen palo ne kuma an ƙawatashi da wasu irin mahaukatan kujeru masu kyau palon yana da girma maisa kaji juwa ta kamaka anyi masa ado dai² da zamani , mutane ne cike a wurin maza da mata "yan gayu ibar farko sai ƙamshin gayu ke tashi , muna shiga Dikko yace tou ga An mata nan ku gaisa ina zuwa yana faɗin haka ya wuce , binshi nayi da ido harya shige ciki , Dawo da hankalina nayi wurin "yan cikin palo nace sannunku , yawwa ki zauna mana , a , a zan wuce ne kawai ina faɗin haka nabi Dikko inda naga ya shiga , suka ce kizo ki jirashi ya fito , ko saurarensu banyi ba na wuce ciki , a gefen gado na sameshi durƙushe rabin jikinshi a saman gado idonshi a rufe hawaye na zubowa daga cikin idonshi , da sauri na isa wurinshi nayi yadda naga yayi sannan nace masa Dikko wai miye ? Ba tare daya buɗe idonshi ba yace An mata cikina kamar zan mutu haka nakeji , kace kanajin yunwa kaci abinci to , bana iya cin abinci a yadda nakeji na , to kasha magani mana , zan sha jeki palo ki jirani kinji ko ? Cikin kuka na matsa kusa dashi nace nidai zan zauna nan , a , a karki zauna kinji jeki ina zuwa yanzu , nidai , cikin hayani yace da Allah malama fita ki bani wuri nace kije ki jirani ki tashi kusa dani bana san numfashinki yana sauka a jikina , matsawa nayi na zauna gefen gadon nace tou zan jiraka anan , Wani irin kallo yayi min tare dayin dariya , murmushi nayi nima nace meya baka dariya ne ? Ɗaure fuska yayi sannan yace ba dariya bace fusata ce , da gudu na tashi nabar ɗakin , tsoki Dikko yayi yace kin rufawa kanki asiri dana yi miki maganin kafiya , cire kayanshi yayi ya shiga wanka a daddafe.... A palo kuma sai caccakar abinci sukeyi yayin da wasu kuma ke tacin ɗamara cikin shiga irin ta mahaya doki sai naɗa rawani sukeyi , wuri na samu na zauna bana kallon kowa zuciyata ce ƙawar firana tana haskomin Dikko da ɗabi'unshi , murmushi nayi ƙasa² nayi magana nace mutumine kenan.... A hankali mutane suka fara ragewa dan har yanzu Dikko bai fito ba abinda dai na fuskanta ko wane yana tare da budurwarshi ne ko matarshi ne nidai shine ban gane ba dan banga sunyi kama da masu zaman "yan ci ba , ina wannan tunanin ne Ashiru ya shigo hannunshi riƙe da kofi inda nake zaune yazo ya bani da girmamawa yace wai mai gida yace in baki ki kai mishi , kai tsaye nace bazanje ba , murmushi Ashiru yayi tare da cewa yi haƙuri kije ki daina haka babu kyau kinfa san halinshi sarai haba ranki ya daɗe ki riƙa mishi uzuri , ni bazanyi uzirin ba a cikin ni dashi waye ya kamata yayi uziri wa wani ? Kiyi haƙuri duk wanda yayi haƙuri bai iske ba kaɗan yayi ki ƙara haƙuri wata rana zai zama tarihi , wane tarihi kullum abu ɗaya ni na gaji wallahi , yi haƙuri ki ansa kinga gashi yana kira , ƙin ansa nayi na gyara zamana , ɗaukar wayar yayi yace E mai gida , tou gashi nan zata kawo maka ya tsinke wayarshi , yace dan Allah ansa ki kai mishi , ansar kofin nayi na tafi ɗakin kai tsaye ! Bayan ƙofa ya laɓe ina shiga ya kulle ƙofar da makulli , a ɗan razane nace masa gashi cikin girmamawa , kalli can ya nuna min gado , kallo nayi sannan na kalli Dikko da yanayin tuhuma , yace haka kika ganshi ɗazu ? Girgiza kaina nayi alamar a , a yace ai kin rainani ko ? Tou yau so nake mu fidda raini dani dake , da sauri na kalli kofin na sake kallon gadon ya gyareshe tas , meye a kofin ne ? Ya tambayeni bansan ko miye ba , tou shanyeshi sai in buɗe miki ƙofa ki tafi idan ba haka ba kuma in ɗoraki saman gado kema in miki yadda kika ganshi , nidai ka ansa tafiya zanyi gida , ai ba wani gidan da zaki yau yayi maganar tare da matsawa jikin madubi yana kallon kanshi saida ya shafa gemunshi da bayan hannunshi na haggu sannan ya fara cewa one , bayan wani lokaci yace tow , three , four , five , da sauri nace me zanyi ? A harzuƙe ya kalleni yace shanyewa zakiyi sai kizo ki dafa ƙafata kice kin gode , idan kuma kika bari na irga goma saidai kiji Dikko a saman ruwan cikinki.... Six yaci gaba seven , eight , nine ..... Da sauri na ɗaga kofin na shanye na riƙe moƙoshi na tare dayin wata irin ƙara sannan na fashe da kuka na jefar da kofin kamar nasha guba har a zuciyata kamar an kwaremin ita ƙirjina zafi maƙoshina kamar an tsatstsargar minshi , dariya Dikko yayi yace services gobe ma ki sakemin kafiya zo ki gode , da sauri na isa gabanshi kaina yana juyawa na dafa ƙafarshi ina kyarma nace na gode , to jeki Ashiru ya maida ke gida sai mun haɗu a ɗakina gobe idan Allah ya kaimu , da sauri na miƙe yace kimin addu'ar saukowa doki lafiya , har yanzu wuyana kamar zai fita nace Allah ya tsare yasa ka sauko lafiya , daure fuskarshi yayi yace yawwa kije ngode , yayi maganar yana tillomin makullin ƙofar , da sauri na ɗauka na buɗe na fita ina kuka.... A inda nabar Ashiru a wurin na sameshi nayi gaba cikin ɓacin rai yace ta nan zamu bi , banza nayi dashi na wuce , maganar Dikko naji da tunda na fito ya biyo bayana naji yana cewa ina zakije nan bakiji ana miki magana bane zo nan , ba tare da nayi magana ba na dawo da hannu ya nunamin yace wuce ta nan kuje kuma karki daina kukan zanzo da daddare , Kallonshi nayi , cikin tsawa yace ki daina kallona ki wuce marece yanayi sai ina miki magana kita kikkifa ido kina kallona , bayan Ashiru nabi har yanzu ban daina kuka ba , komawa Dikko yayi yaci gaba da shirinshi wai zasu hau taka ango duk wani abokinshi na nesa dana kusa idan dai yana da rai da lafiya yazo , yasa an ɗauko An mata da ya ɗorata doki amma ta ɓata mishi , kayan daya ajiye mata ta saka ma badasu zaiyi tunda batajin magana... Abokanshi sunso ayi shagali amma Dikko yace a , a , sun tambayeshi dalili yace shi yasan dalili kawai bazaiyi ba , shine suka tsiro hawan doki dan tayashi murna kuma shima zai hau dan yana bawa hawan doki mutunci na musamman , Tunda muka taho kuka nake ina jinjina irin cuta da zalinci na Dikko , har yanzu wuyana bai daina maƙaƙi ba zafi yake daga ƙirjina har abinda ya sauko zuwa ramin zuciyata , goge hawayen da suka sake taruwa a idona nayi sannan na fara tunanin ya akayi Dikko ya kasu gida biyu ? To waye ya kwanta yace in matsa gefe ? Da nayi kuka kuma ya akayi naga banga na kwance ba naga Dikko ya ɗago ? Mafarki ne zuciyata ta tabbatar min da haka dan haka na manta da wani da na gani yana kwanciya a mota.... A ƙofar gida Ashiru ya saukeni ya wuce da gudu ni kuma na shiga cikin gida , duk sallamar da nakeyi babu wanda ya jini bare nasa ran za'a ansamin Inna da matan Baba ƙarami suke ta faɗa wai ni na koyawa Safiyya iskanci kuma naje na anshi gadon su Babana na lashe duk wannan bai isheni ba saida nasa Dikko ya ɗaure mijinsu sunga yadda za'ayi a ɗauramin aure , Inna tace aure anyi an gama ba fashi ko ƙarami ya ɗaura aure ko karya ɗaura sai an ɗaura auren Sultana idan Allah ya kaimu lafiya gobe kuma ko ni sai in fita in ɗaura mata aure tunda ba shegiya bace ba , shaggu ma an ɗaura aurensu bare Sultana , dama waye yake nemar a fasa aure ai jiki magayi dan hausawa kuwa cewa sukayi ko wattuna bara baiji daɗin bana ba , ai hangen duniya ne yasa kike harin bashi ɗiya ke haɗamammiya , Inna tace haɗama sai wanda ya isa yakeyi wani yayi yaga idan zai samu cusa kai babu ƙwarjini , matan Baba ƙarami sukace murnar mutuwa dai murnar banza yadda yayi ma mijinsu itama zai mata haka nan , banji abinda Inna tace ba na shiga ciki raina ɓace na fara kiran wayar Dikko.... Takalmi zanoty ne a ƙafarshi wando kamun ƙafa jawha milihi "yar gabas , babbar riga girken nufe yasha rawani mai bakin fara sai wuƙar hawan doki dake rataye jikinshi a jirge yadda dai masu hawan doki keyi , yasha kyau harya gode ma Allah sai hotuna ake ɗaukarsu a ɗan yamutse yake dan bayajin daɗi sosai komai cikin ƙarfin hali yakeyi... Bayan sun gama ɗaukar hotunan suka ɗunguma suka nufi inda aka ajiye dawakan duk wanda zai hau doki sunsha ado sosai , gaban dokinshi ya tsaya da yasha ado da sirdi tunbas ajikin sirdin anyi masa kwalliya da bishiri guda huɗu , kayan azurfa gaban fuskar doki ɗan wuya ɗan gaba , ƙasan sirdi aka sa labbati mai kyau ɗan gabas da sha hirji... Yana ƙoƙarin hawa tsadajjen dokin kiran Sultana ya shigo.... Ɗauka yayi ya kara a kunnenshi tare da cewa inajinki , wai kai da Allah Dikko mi yasa bakayin abu da lissafi ? Tafiya ya farayi dan komawa ciki saboda wurin yayi taron mutane da yawa Sultana kuma taci gaba da cewa in banda hauka ƙanin babana zakasa a ɗaure ? Ai kinsan ni mahaukacin ne kika faɗamin damuwarki me yasa ke mai hankali bakiyi maganin matsalarki ba sai kin sako mahaukaci a ciki to ? Dana faɗa maka cewa nayi kasa a kulleshi ? Wanda zai ɗauramin auren Dikko ? Tou ai sai a fito dashi ya ɗaura auren idan ya gama saiya koma , cikin hayani nace kai mahaukaci..... Kafin in faɗi maganar da zan faɗa yace ai kinsan inda kika barni kizo ki sameni in nuna miki girman haukata shi baya san ke ɗiyar ɗan uwanshi ce ba yayi ƙararki duk sansanci da aka kasayi a gida to inda ya kaiki a can zasu sasanta nine nakeyin shari'ar ne ? Ko nine nake ƙararshi ? Yarinya dake kuma kece mahaukaciya ni ina da hankalina dokin Dikko kawai dake in hau kuma inyi sukuwa......... Yana faɗin haka ya kashe wayarshi ! Cikin ɓacin rai ya fita ji yakeyi baima ɓatama An mata rai ba dama yace saiya zaneta iyakar raini duk girman duniyar nan baiga wanda ya rainashi ba kamar yadda An mata ta rainashi ba , ta kalli tsabar idonshi ta kirashi mahaukaci ta faffaɗa mishi duk maganar daya zo bakinta baida wata ƙima a idonta amma zataci ƙaniyarta , da ɓacin ran An mata ya hau saman doki ya zakuɗa yadda sukeyi idan zasu gyara , bayan ya gyara yayi ma dokin diddige kowa yahau nashi suka wuce cikin tsari da gogewa irin tasu ta mahaya doki ango a gaba abokanshi a baya suna taka ma ango wannan shine ake kira taka ango zasu ɗan zagane inda sukaga ya kamata abunsu dai na manya..... Dikko yana kashe wayarshi Inna tana shigowa , wuri ta samu ta zauna take tambayata abinda ya haɗani da Ba ƙarami , duk abinda ya faru dani bayan bata nan saida na zayyane matashi kaf amma ban faɗa mata zance Dikko yamin fyaɗe ba amma duk abinda nayi bayan na Dikko ban ɓoyewa Inna komai ba , bayan na gama tace yanzu inashi Baban Hafsa ? Bansan inda yake ba , shifa Bello ? Shima bansan yana ina ba , Hmmm Inna tayi cikin takaici sannan tace to dan uban ƙarami ya manta ni kenan ? Amma ina cikin gidan nan har aka kawo miki sammaci saboda Dikko ya fini mutunci kika saƙe a jikinki har kikaje kika kai mishi ina nan kwance Sultana ? Inna ranar baki lafiya bana so na tayar miki hankali , jinjina kai Inna tayi sannan tace naso ace ahalin babanki suka ɗaura miki aure amma nasan haka baza ta samu ba dan bana tunanin ƙarami zai iya ɗaura auren ki saidai "yan uwana su ɗaura miki aure...........! Ba tare dana kalli Inna ba nace ba naki ahalin ba na Babana , Baba ƙarami ne zai ɗaura aurena da kanshi gobe idan Allah ya kaimu a ƙofar marusa ƙofar gidan su Babana haka na faɗa ma Dikko kuma haka yasa aka rubuta a jikin i v kuma a gidan za'a ɗauki amarya Inna dangi uwa sunyi kuma suna nuna soyayya mai girma da fifiko wa nasu akan ahalin uba kowa dai da nashi wurin , amma su ahalin uba garkuwar rayuwa ne gaba ɗaya daga zaran baka dasu tou fa ka koma liƙe² , Inna tace a jikin i v masallacin G R A za'a ɗaura aure haka aka rubuta ana gama sallar juma'a , kuma ko ƙarami ya ɗaura ko bazai ɗaura ba mijina zai ɗaura aurenki idan mai kowa mai komai ya bamu aron rayuwa da lafiya anan gidan za'a ɗauki amarya duk wanda bazai zo ba yasha zamanshi a gida.... Tana kaiwa nan tace in fito za'amin ƙunshi mai ƙunshi tun ɗazu take jiranki , wai duk girman kwana takwas sai yau za'ayi ƙunshin biki idan Allah ya kaimu gobe naje saloon sai kace auren wasan yara danni ina kallon abun kamar a mafarki ne.... Daren yau duk inda ka shiga a gari maganar su Dikko akeyi labari ya barbazu duk inda ba'a tunani ya dangane , sunyi hawa mai kyau da burgewa abokanshi sunyi mishi kara sosai wasu ma basu taɓa zuwa katsina ba sai dalilin wannan aure , dan duk auren da yayi duka biyun ba'a a katsina akayi ba , sai yau mutane suka tabbatar suka kuma yadda da wannan aure , hotuna sai yawo suke a social media , duk abin nan sai yau Momy ta samu damar buɗe wayarta , shi kuma Dady ya kira Dikko yace ya rufe kaf wayoyinshi karya tsaya duk inda wani zai ganshi tunda yace shi damuwarshi a ɗaura auren idan an ɗaura zaiji da sauran matsalolin , Dikko yace E fatan alkairi Dady yayi masa sukayi sallama , Dikko yaso yaje wurin An mata bayan sun sauko daga hawa amma baya iya zuwa ga gajiyan doki ga kuma ciwon ciki dake neman hanashi ya miƙe tsaye koda suka dawo a daddafe yayi sallar magrib yayi isha'e sannan suka shiga gida a saman kafet ya kwanta a wahalce ya kifa fuskarshi saman pilow shi kaɗai yasan azabar da yakeji , abokanshi kuma sun daɗe suna fira bayan sunci abincin dare ne suka fara tafiya wasu zasu koma gidanjensu anan cikin gari , baƙi kuma suna tafiya masauki , Bayan kowa ya gama tafiya ne aka rage Dikko dashi dasu Ashiru , wayar wani ya ansa a yaranshi ya kira An mata amma duk kiran da yayi ba'a ɗauka ba saboda tabar wayar a ɗaki tana waje ana mata lalle , gajiya yayi da kira ba'a ɗauka ba ya mayar mishi da wayarshi , yace ma Ashiru ya samo mishi fura yaji ko zata shiga , fura dai itace ya samu yasha abinci dai ya gagareshi yau , abincin saidai aka fitar dashi dan ya lalace.... Bayan ta saka layinta Jiddah ta fara kira ko "ya "yanta bata nema ba sai Jiddah ta fara taɓowa ɗiyar zumuncin Allah Jiddah da ƙawayenta suna zaune a palon Sultana dan neman magana saboda bayan an gama jere an rufe da makulli amma sai ta kira aka ɓalle mata ƙofar wai wannan kujerun sunfi ƙarfin siyen ahalin caca mijinta ne ya siya dan haka babu wanda zai mata iyaka da dukiyar mijinta , komai na ɗakin amfani sukeyi dashi kuma cikin ƙeta da mugunta shi Dikko baisan abinda Jiddah take ciki ba dan ko ranar da Inna tace saidai ya rabawa Sultana gida bata faɗa masa cewa Jiddah tayi iskanci ba tace masa dai kawai ya rabawa Sultana gida da matarshi dan ta fahimci kawai da damuwa , shine Dikkon yace gidanshi bai gagareshi ba kuma shi babu macen data fi ƙarfinshi.... Jiddah tana ganin number waje ta san Momy ce dan haka tana ɗauka ta ɓarke da wani irin kuka mai tada hankali , na shiga3 na lalace ƙaryata ta ƙare kece garkuwata da bakya nan na zama abin tausayi duka na safe daban na rana daban har tsakar dare bai barni na huta ba saboda kawai zaiyi aure , wane irin aure kuma ? Momy wai baki sani ba ? Aure zaiyi har anyi jere yau duk inda kika shiga a garin katsina maganar hawan taka angonsu akeyi yace yayi hawan barin tarihi a katsina tunda ya auro muradinshi ni matar sadaka ce shi yasa baiyi ba a aurena dashi , Momy tace wai waye zaiyi auren ne ? Saida ta sake ɓarkewa da kuka cikin makirci irin ancucetan nan tace Yaya zaiyi aure har anyi jere gobe ɗaurin aure haka akazo jere jiya bakiji yadda sukemin habaici ba suna zazzagina nayi haƙuri na ƙyalesu Momy ina cikin matsala , wai wane Yayan zaiyi aure ? Inji Momy , Jiddah tace Ya DK , Momy tace wai Dikko nawa ? Ko wane Dikkon ? Jiddah tace shi , Dady dake zaune saman abin sallah yana lazimi ƙaddarawa yayi ma bata wurin , Momy tace wace ce zai aura ? Caca zai aura , Momy tace wace ce Caca ? Wannan karuwar , wata irin zufa ta ketowa Momy cikin tashin hankali tace Dikkon wai ? Jiddah tace Eh , kashe waya Momy tayi ta fara kiran wayar Dikko amma a kashe yake , Ashiru ta kira bayan ya ɗauka tace ya bata Dikko yasan da kwanan zance dan hakanyace mai gida yaje kaduna wurin wasan polo , haka Dikko yace duk wanda Momy ta kira a cikinsu baya nan yana kaduna tunda dama zaije polo saukar da akeyi ma Sultana shine ya hanashi zuwa , Momy tace shi da waye ya tafi kadunar ? Ashiru yace shida wani abokinshi , turomin number abokin nashi , har zata kashe waya taji bata iyawa tace ubanshi ne yahau doki yau zakacemin yaje kaduna ? Ashiru yace nidai ban sani ba hajiya nasan dai mai gida baya nan bara na turo miki number abokin nashi , ina jiranka ta tsinke wayarta , gyara kwanciya Dikko yayi bayan Ashiru ya gama waya da Momy dakel ya fara karanta tsohon layin Sultana dake hannunshi , bayan ya gama faɗa Ashiru ya tura mata , Tana gama waya da Ashiru ta kalli Dady tace kaji wai Dikko zaiyi aure , Allah yasa alkairi , Dady ya faɗa , Momy tace wai har Dikko nawa yake zaiyi mata biyu ? Dady yace yo shi ɗin na wasa ne ? Karuwa fa ? Karuwar aini daya faɗamin zaiyi auren nan da banyi tafiyar nan ba , kunga tun nan Dady ya zame kanshi , Momy tace kaima bai faɗa maka ba ? Dady yace um umm , haka Momy tayi ta gwada number da aka turo mata amma batayi , cikin daren ta kira "ya "yanta mata tace idan Allah ya kaimu gobe lafiya suje gidan Dikko daga amarya har danginta suyi musu terere .......! Hmmm tou waye ma zaije ya tashi rashin kunya har gidan Dikko duk girman mutum Dikko ya sauke mishi rashin mutunci , baka zo gidanshi ba kayi masa yaje ya isko ka har mazaunin ka ya gwagwaɗa maka rashin mutunci ina kuma ga ka hawo layinshi a cikin gidanshi................ ? Ranar ɗaurin aure ! Tunda safe Inna da kanta ta ɗaukeni a mota ta kaini gidan Kaka hmmm wai ni za'ama nasihar zaman aure , murmushi saida ta ƙari karatunta Inna ta ansa itama tayi har miyan bakinta ya kusa ƙarewa sannan tayi shiru kuma duk maganarta akan Dikko ne , daga gidan Kaka ta ajiyeni wurin wankin kai tace zataje ta dawo , Har aka gama abinda za'amin Inna bata dawo ba , ina nan zaune ina zaman jiranta kiran Yazeed ya shigo wayata , ɗauka nayi bayan mun gaisa yacemin An mata kanki ɗaya ? Nace meya faru ne ? Ki rasa wanda zaki aura sai DK haba An mata me zakiyi da DK ? Wallahi ba baki nayi miki ba ko kinje sai kin dawo kinsan iskancin DK kuwa ? Kuma wallahi ba sanki yakeyi ba yaudara ce kawai bakiga auren naku duk a munafurce akeyinshi ba ? Duk auren da yayi babu wanda baiyi hidima da shagali na tashin hankali ba , duk matan daya aura wallahi lefe akwatina 200 yayi kinga banbanci biyu ya fito ko ? Ji naki babu wani shagali tun nan kisan baya maraba da auren saboda baya sabgar mata yake so ya moreki ya koraki bayan ya gama hora miki zuciyarki da soyayyarshi , banbanci na gaba lefe akwati 24 yayi miki , kuma zai haɗaki gida ɗaya da matarshi cewa yayi wai bazai iya ajiyeki goruba ba gidan yafi ƙarfinki kinji yadda yake aibata ki ? Hmmm uwa uba kuma ga duka kwata² baisan darajarki ba mahaifiyarshi bata sanki ga masifar DK gana matarshi "yan uwanshi da mahaifiyarshi ina zaki saka kanki ? Ya ganki "yar yarinya shi yasa ya liƙe miki yayi ta cin zalinki Dikko mugune na bugawa a jarida kiyi karatun ta natsu kuma ki cire number na a wayarki nasan zai sake miki sabon layi ne ki kirani da sabon layin zan baki shawara , jiki a sanyaye nace tou , Ina kashe wayata Dikko ya riƙa zuwamin a zuciyata , kyawun fuskarshi maganarshi da yakeyi cikin sanyi sai kuma tsadajjen murmushin shi mai ɗaukar hankali kallonshi mai tayar da tsikar jiki rigimarshi idan ya kafe yana faɗa dani da gaskiyarshi jina yake kamar wata sa'arshi , murmushi nayi a zuciyata nace mutumi na Allah ya baka lafiya , amma fa maganar gaskiya Dikko yana da cuta a rayuwarshi , horn in Inna ya dawo dani daga tunanin dana lula , jakata na ɗauka nayi musu sallama na wuce.... Lokacin da muka dawo gida gidan ya fara ɗaukar taron jama'a ƙawayen Inna wankakkin matan da suka san abinda sukeyi , kuma matan Baba ƙarami sunzo dan rashin kunya da "yan uwan Inna , ɗakin mijinta ta wuce dan itama gobe zasu bar nigeria , ko walima bata tsayawa ayi da ita shi yasa bata da wani ishashshen lokaci kula da mutane tana ta shirinta , Ɗakin Inna na shiga ƙawayenta suka sa ni nayi wanka ina fitowa suka rubdigarmin suna min shiri na musamman nidai sai yanzu jikina ya fara sanyi da lamarin Dikko tsoranshi naji ya kamani da maganar da yayi min jiya a goruba wai muje saman gado mu fidda raini , sai wayar da mukayi dashi wai nice dokinshi zaiyi sukawa akaina , sai maganar Yazeed da yace Dikko ya ganni "yar yarinya shi yasa ya liƙemin zaiyi ta cuta na ne , fashewa nayi da wani irin kuka mai tada hankali nace nidai wallahi bana sansa , Inna data shigo yanzu cikin shiga ta wayayyin mata tace wane ne bakya so ? Dikko , dariya ƙawayenta sukayi gaba ɗayansu cikin shaƙiyanci suka kalleni cikin yanayin wayyo muna tausaya miki , Inna tace kin manta daren ɗaurin aurenki da Sultan abinda kikace akan Dikko ? Aimu saidai muce Allah ya baku zaman lafiya... Ƙara sheƙewa sukayi da dariya , kamar wata taɓaɓɓa haka nabisu da kallo ɗaya bayan ɗaya Inna tace ke da Allah ki rufe mana baki ko ki fita ki bamu wuri , wata ce tace a , a karta fita tazo nan ta zauna , saman gado na koma bayansu na zauna sukaci gaba da firarsu na tafiyar Inna...... ! Bayan sallah juma'a dubun mutane suka sheda ɗaurin auren *DIKKO U DK* da amaryarshi *MARYAM ALIYU MUHAMMAD BINNA...* akan sadaki naira dubu ɗari ɗaya lakadan ba ajalan ba , ɗaurin aure yayi albarka wanda manyan mutane da dama suka samu damar halakta daga jahohi da dama , Baba Ƙarami yaje amma yaƙi yadda ya ɗaura aure mijin Inna ya zama waliyin Sultana , ana gama ɗaurin aure Dikko ya buɗe wayoyinshi , yana buɗewa saƙon Momy ya shigo ! _Idan ka kuskura ka ɗauko "yar duniya ka watsa kanka ka watsa gidanka , kuma tunda bansan yarinyar nan ko ka aureta saika saketa.....!_ Murmushi Dikko yayi tare daci gaba da duba saƙonni , hada Yayarshi itama ta zazzageshi tass murmushi ya sakeyi sannan yace aike a cikin kayan miya ko matsayin ruwa baki kai ba sharar bakin kwata dake , na ɗayar Yayarshi ya duba itama dai abun babu kyan gani da daɗin ji , kanku akeji , saƙon Dady ya gani shi kaɗai ke masa fatan alkairi , bayan ya gama dubawa Ashiru yaba wayoyin yana gaisawa da mutane. Wallahi Uncle na zuba , Mardiyya ce tsaye a gaban Al ' Ameen yace haba Doughter da kin zuba maganin nan idan an ɗaura auren nan niba ɗan Babana bane , tayi masa rantsuwa cewa ta zuba saidai idan bashi ne yaci abincin ba ko kuma baici ba , dan abincin sa daban aka zuba mishi , jinjina kai Al ' Ameen yayi tare da cewa aiki ya kwana uban gayya ya mutu , muna fama da Jiddah Sultana ta shigo , dolensu kowa zata kama gabanta amma Jiddah ce farko sai Sultana tabi bayanta , Mardiyya tace Uncle tare zasu tafi gaskiya , Al ' Ameen yace tabbas ki faɗawa waccan jakar boka yace azo a anshi saƙo gobe , Mardiyya tace to ta wuce ciki , tana wucewa Al ' Ameen yace zaki bani motarki da manki da kuɗinki inje in biyawa kaina buƙata....... A wahalce Dady ya kalli Bello saida yayi nishin wahala sannan yace ɗan iskan yaron nan ma inajin ma ya mata damu ! Bello yace kaidai mu fita lafiya , Dady yace nidai jibi idan Allah ya kaimu za'a kawomin kuɗin nan na bashi na huta da wahala Dikko ɗan iskan yaro ne , dariya Bello yayi ta taɓaɓɓi yace mai naɗawa manya kashi.... Umar dai baya gajiya da gulma da kanshi yaje har gidan Amisty ya faɗa musu mai gida ya auri Sultana , Hafsa ita bata nan tana abuja wurin wata shaƙaƙƙiyar mata ta hawan kwakwa mai ranar bacci , Amisty tanajin labarin auren Sultana ta haɗa dabar karuwanta hada su wane yaro tace kowa ya shirya su tara gidan amarya amma kar a faɗawa Hafsa dan gudowa zatayi ta dawo kuma tayi zubin kuɗinta dan bata ɗaukar asara , Momy kuwa tana daga can ta tattara kan yaranta ta turasu gidan Dikko tace idan suka ragawa Sultana da duk masu rakota sai taci ubansu , dan haka suma suka taho ko wace kanta ɗure da iskanci suka iso gidan , Mardiyya kuma ta ɗora Jiddah saida ta tabbatar tafi jirgin sama tashi hankalinta ya kwanta , kuma faɗa mata Uncle zaije zaria boka yayi kira , Jiddah tace zasu haɗu da daddare. Yazeed kuwa sai ƙara kirana yake yana jaddadamin na cire numbershi karna manta ya sanni da mantuwa , raina ya ɓaci dan haka kallo biyu nayi ma numbobin suka zauna akaina gaba ɗayansu..... 13/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 76 Ina ƙoƙarin ajiye wayata kiran Dikko ya shigo , fashe wa nayi da kuka naƙi ɗaukar wayar harya tsinke wani kiran ya sake shigowa ban ɗauka ba sai kuka nake mai tada hankali , wayata na yada na tashi da gudu nabi Inna ɗakin mijinta dawowar shi kenan yana labarta mata yadda ɗaurin aure ya kasance , wai kuma ana gama la'asar za'a ɗauki amarya ! Ina zuwa na rungumeta tare da ƙara ɓarkewa da wani irin kuka mai kama zuciya , da tausayi ta ɗagoni daga jikinta itama hawayen ne kwance a idanuwanta amma bai zubo ba , da yanayin ko oho tace wai meye haka ? Bana san iskanci fa , shi kuma kukan na mene ne ? Inna na kirata tare da kallonta ina shashshekar kuka na kasa magana , murmushin ƙarfin hali Inna tayi ta jani muka fita ɗakin muka koma ɗakin ta , wata ƙawarta ce ta miƙomin wayata tace ana kiranki kuma har yanzu Dikko bai daina kirana ba , ina ansar wayar na kasheta gaba ɗaya...........! Inna da ƙawayenta kuwa nasiha sukemin wallahi hankalina baya wurinsu kwata² banajin su kuma bana iya tuna abinda suka faɗamin har suka ƙari surutunsu suka gama a , a ciki bana iya tunawa , bayan an gama nasiha na tashi nayi sallah la'asar kuma har nayi sallah na gama hawaye ke ratata daga cikin kwarin idanuwana , ina gama sallah aka fara shiryani dan kaini ɗakin mijina. Babu wani daga ɓangaren ango daya zo bikon amarya , duk maganar Inna batayi tsegumi ba ita burinta kawai akaini ta huta dan a ganinta aurena shine natsuwa a gareta dan tasan idan ta tafi ta barni yawo zanci gaba dayi tunda Allah ya kawo mai kwasheni sauka lafiya.... Babu abokin ango ko ɗaya duk motocin Dikko ne akayi amfani dasu wurin kai mutane gidan amarya , ni kuma a motar mijin Inna aka ɗaukeni dashi da ɗan uwan Inna sune suka kaini har gidan Dikko da kansu...... Da farin ciki masoyana suka shiga gidan tare da dabar su Amisty domin sun riga amarya isowa sai aka shiga a tare kowa dai da abinda yake faɗa irin dai abun nan namu na mata yadda mukeyi idan ankai amarya kun dai gane irin abun ai , Jiddah kuwa ta murza wani irin ƙaton wanka na tashin hankali kamar zata tashi duniya dan haɗuwa kai Jiddah "yar gayun bala'e ce kanta yana hayaƙin rashin kunya , wata irin guɗa ta rangaɗa ayyuri yuriiii........ Ƙawayenta suka ansa da barka da zuwa *CACA* ga caca ga tawagar karuwanta a baya fatan kunyo mana tsarabar kwalaben giya a cikin jikkunanku dan kunsan ba'a shiga kasuwa saida kuɗin siyayya amfani giya kenan sai ansha akejin muradin mace , giya mata caca sana'ar uban wata ƙawata ne , hehehe ram aka kashe kundai san iskancinmu na mata yadda yake..... Yayyen Dikko dai turawa ne sun huta tunda banajin abinda suke cewa kunsan ajiboters basu iya faɗa ba haka kuma basu iya hayani ba daga zaune dai suke ta watso nasu kalaman cikin harshen turanci , kuma su ƙawayen Inna babu wanda yayi musu magana , Mardiyya ce naji tana cewa gashi nan Aunty zai shigo , cikin yayun Dikko ne naji wata ta turance abinda yasa na fahimta naji Mardiyya tace Dikko ne , kila ta tambayi Mardiyya waye ne tace shine , kowa dake palon yayi tsitt , murmushi nayi a zuciyata tare da cewa sannu da zuwa jarumina , ban ganshi ba amma na hasko yadda zai fito daga mota , Zaiyi parking cikin ɓacin rai , sai ya fito daga mota da yanayin shagwaɓa zai tunkaro palon cikin jarumta zaiyi mazurai da kyawawan idanuwanshi idan ya shigo , daddaɗar muryarsa zata bayyana yanzu , sallamarshi naji yayin da ake ƙoƙarin shiga dani hanyar da zata sadamu da inda aka bani mazauni da "yan uwanshi ya fara gaisawa sannan ya kira Jiddah suka wuce ciki. Ƙarshen ɗaki aka kaini wato bedroom saman tsadajjen gadona aka ajiyeni a gefen gado , nasiha dai aka ƙara yimin an nunamin matsayin haƙuri biyayyar aure kauda ido akan ƙaramin abu danne zuciya yayin fushi , ba abun duniya baya duk girmanshi tsabta naga yadda abiyar zamana takeyi inyi ƙoƙari in wuceta a gayu , babu wanda ya zauna saboda yanayin hararar da ƙawayen Jiddah ke watsoma "yan kawo amarya abinda yasa ma basuyi yunƙurin yin wani abu ba dan Dikko yana nan , shima Umar ne ya faɗa masa za'a tashi bama²n masifa a gidanshi shi yasa ya taho , duk wani abu da za'ayi a wurin walima idan Allah ya kaimu gobe Inna ta ƙanƙare da dangin miji , tayi gara na fita kunya kuma duk Dikko ne yayi dan ya siyamin mutunci a wurin ahalinshi.... Amisty taso tayi magana dan na lura da bakinta amma ƙawayen Inna suka ce kowa yazo a tafi yanzu , amma tacemin akwai dawowa , inaji ina gani suka tafi suka barni , Oh saini ɗaya a ɗakina kamar mayya babu ƙawa ko ɗaya babu wasu "yan uwa da zasu kwana a gidana , jakata na jawo na fiddo wayata na kunna bayan ta gama kunnuwa na kira Inna , amma bata ɗauka ba , "Yan palo kuwa kowa cikinsa ɗure da iskanci a ƙagare suke Dikko ya fita su caccakeni san ransu amma yaƙi fita har aka kira magrib , suna tunanin zai tafi masallaci a gida yayi sallah , isha'e ma haka , Yayyen shi ganin bashi da niyar fita sukayi mishi sallama suka wuce , godiya yayi musu tare da cewa ku huta gajiya , amma sun ɗauki gudirin zasu dawo idan Dikko baya nan , Sultana ta samu ɗagin ƙafa na yau basa so suyi rashin mutunci Dikko yana nan idan ya birkice musu gano dai²nshi sai Allah. Misalin 9pm ya kira Jiddah ɗakinshi ya faɗa mata cewa idan Allah ya kaimu gobe rai da lafiya duk wata ƙawarta data san tazo gidan nan to ta tattara ta kama gabanta har Mardiyya baisan ganin kowa idan kuwa ba haka ba za'a samu matsala , amma sai Jiddah tace ƙawaye na zasu tafi amma fa Mardiyya babu inda zataje wallahi tunda tuni Momy ta gama magana idan kuma dan kayi aure zaka tona min asiri saika haɗa hada ni ka koremu gaba ɗaya.... Cikin ɓacin rai Dikko yace Mardiyya ta tafi daga gidana Jiddah , wallahi babu gidan ubanda zataje , Mardiyya ta barmin gidana gobe kafin raina ya ɓaci , wallahi ba zataje ko ina ba idan saboda kayi amarya ne sai haɗa hadani ka sakeni kuma kake maganar ta bar maka gida ai bani nace ta zauna ba Momy tace saboda haka ka bari sai ta dawo , tana faɗin haka tayi gaba abunta , shima tashi yayi ya nufi ɗakin amarya Sultana... Da ɓacin rai ya tunkari ɗakin Sultana yanajin tuƙuƙin maganar Jiddah da tace babu gidan ubanda Mardiyya zataje zaici uban yarinyar nan amma sai zuwa gaba dan yanzu duk idon jama'a akanshi yake yana iya mata wani abu ace daga yayi aure ya fara cusa mata damuwa , yana da cikin Jiddah duk ranar daya tashi haifeta zai wulaƙanta mata rayuwa yadda mai tunani baya zato, ina zaune a inda nayi sallah har yanzu ban tashi ba ina ta kiran wayar Inna ba'a ɗauka , babu ko sallama ya shigo ke An mata ni zakiƙi ɗaukar ma waya ne ? Dake kin ɗaukeni sakarai ma daga baya kika kashe wayar wai me kika maidani yana maganar yana shigowa cikin ɗakin , kai tsaye nace mahaukaci , kalmar hauka ya fita daga bakinki dan jiya ba yau bace doki , dokina ya ƙarasa maganar yana ɗaukata yaci gaba da cewa do ki , da iskanci yake faɗar do..... Sai yace ki , yana yin irin yadda akeyi idan an hau doki bari ki fara jin nauhi na sai ki fara kiyayata tun kafin mu fara wasan danbe , Dikko bana so , a , a ya maƙale ƙafaɗar shi irin yadda ƙananan yara keyin ƙiwya yayi maganar a shagwaɓe yana yin wani ɗan kukan shagwaɓa mai sa mutum yaji yana lilo tsakanin sama da ƙasa , cikina naji yana halbawa jikina yanamin wani yami² a dai² lokacin daya saukeni saman gado yana min wani irin munafiki kallo mai nuni da zakici gidanku sannan ya sake cewa do ki yayi min kyakkyawan murmushin shi mai fiddo mishi da ai nahin kyawun shi ƙuramin ido yayi sannan yace ai dokina ne ke ko An matana ? Rufe idona nayi cikin jin kunya nayi murmushi kaɗan! Ina sanki , idona a rufe nace Dikko dan Allah kada kaimin komai , ke meye nace ? Cewa kayi kana so na , ke kuma meye kike faɗa ? Cewa fa nayi kawai ina sanki , to idan na faɗa nima bazakamin wani abu ba ? Naga alama dai idan banyi wani abu ba bazakiji daɗi ba dan na lura kina tsammani wani abu daga gareni , buɗe idona nayi tare da cewa , a , a , ido ɗaya ya kashe tare da ɗagamin gira yace sumbata ɗaya tak , ai nasan bazai tsaya a ɗayan bane , durƙusawa yayi a saman guyawunshi ya dafa hannuwanshi gefe da gefe ina tsakiya kallona yayi sannan yace kamar ya ? Cewa nayi nasan bazai tsaya a ɗayan bane ba , murmushi yayi tare da kwanciya saman jikina a gajiye buɗe bakinsa yayi kaɗan da ajiyar zuciya mara sauti sannan yace Oh to kenan kin yadda da sumbatar ashe ? To amma nasan bazaka tsaya a ɗayan ba , da hannunwanshi biyu ya riƙe kaina cikin kwantattar murya ya ɗora bakinsa a saman leɓuna na yace ɗaya tak ya faɗa da wata irin murya mai tayar da tsikar jiki , cikin mutuwar jiki nace amma dai karya wuce ɗaya , murmushi Dikko yayi tare dayin wata irin sukuwa a kaina cikin sigar mugunta kamar yadda yace sannan ya ɗagani yana cewa tausayinki nakeyi An mata nasan baki iya ɗaukar Dikko wahala zan baki "yar yarinya ta bara dai inzo muyi bacci kinji ko , yana faɗin haka ya fita da tafiyarshi ta sakakkin "ya "ya , Ajiyar zuciya na sauke tare da lumshe idanuwana ba haka naso wasan ya ƙare ba , me ma Dikko yake nufi yana nufin ido zai sakamin saboda nayi ƙarama kai kuji mugu fa , hmmm lallai Dikko ba baƙon mace bane ba , amma maƙetacin mace ne , murmushi nayi cikin yanayin jin kunya kamar yana nan na rufe fuskata. Shiru² Dikko zai dawo babu shi ba labarinshi , tsoki nayi tare da gyara kwanciyata , tun ina tunanin Dikko zai dawo harna fitar da rai yana wurin Jiddah a can ya sauke damuwarshi yayi baccinshi ya manta dani , haka na haƙura nayi bacci da tunanin Dikko... Yauma nayi mafarki da mutumin nan kuma ya faɗamin ya ƙwaƙwale gobe saura ni tunda na shiga sahun ma'aurata , a firgice na farka tare da kwarara wani irin firgitaccen ihu wanda ya karaɗe kaf girman gidan gaba ɗaya duk mahaluƙin dake gidan babu wanda baiji ihuna ba , ina buɗe idona na nufo palo da gudu ban tsaya ko ina ba sai jikin firij na buɗe na ɗauka ruwa saboda wata irin ƙishirwa da nakeji kamar zan mutu , saida na shanye roba ɗaya ta ruwa , a wahalce na dawo da baya na zauna saman kujera ina goge zufa... Jiddah ce ta fito sanye cikin wasu irin kafirawan kayan bacci idonta da yanayin bacci tace uban waye nan yake mana kuka ? Kallo ɗaya nayi mata daga nesa na fahimci fitina ne ya fiddota kuma uwarta zanci yadda nake haƙe da ita saboda kirana da tayi da caca , ubanki ne yake kuka na bata ansa a dai² lokacin da Dikko ya dafa ƙarfen bene daga sama sboda mu dukanmu a yanzu muna ƙasa kowa ta sauko , ni abinda yasa na fito palon ƙasa nasan bazan samu ruwa a palo na ba shi yasa na gangaro na ƙasa nasan zan samu , ita kuma Jiddah masifa ya fito da ita ni kuma yau zan sauke mata duk wata tsutsar iskancin dake cizar mata kwalwa , An mata ya akayi ne ? Dikko ya tambaya , ruwa nasha na bashi ansa ba tare dana kalli inda yake ba , Jiddah kuma tace Caca ni kike zagi ? Sai in takaita miki rayuwa na illahta banza ba abinda za'ayi , Dikko ne yace kinsha ruwan ne ? Ey nasha , tashi kije ki kwanta tou , Babu gardama na miƙe zan tafi Jiddah ta riƙoni ta baya ta fara zagina tana cewa ke "yar marasa tarbiya babana bazai zagu a bakinki ba danni Babana bai sakani a caca ba , shi Babana yasan darajar matansa yasan na "ya "yansa kaf zuri'armu bamu da "yan iska banza ahalin kwarata , Dikko ne yace An mata wuce kije ki kwanta kinji , tou na bashi ansa tare da ƙwacewa Jiddah ta sake riƙoni taci gaba da cewa... Kuma ni babu wanda ya siye gidan hayarmu ya mayar da gidan kiwon dawakai karuwar banza karuwar wofi , murmushin takaici Dikko yayi tare da cewa An mata taho , ƙyale Jiddah nayi na tafi ita kuma taci gaba da cewa ƙaryar banza ƙaryar wofi ba ance ke wata shegiya bace ba da kin tsaya dana ciccire miki gashin kai , Dikko yace gashin kanta kike baƙin ciki dashi ? Dan a lokacin Sultana ta shiga ɗaki bata san wainar da suke toyawa ba , yaci gaba da cewa mace kenan An mata ta burgeta ina ga maza kuma kenan ? Wannan shine zaɓi na farko dana fara cankowa a rayuwata ƙatuwar banza da ƙanƙanuwar yarinya ta fiki tunani , yana faɗin haka yabi bayan Sultana.... Ai kaine ƙaton banza ko kunya bakaji kaje ka auro wannan "yar magen yarinyar idan ka isa kaje ka auromin min cikakkiyar mace wacce zata fito na fito itace kishiyata Dikko da zai shiga ɗakin Sultana yaba Jiddah ansa cewa wannan ma ta isheki yana faɗin haka ya shige , ita kuma taci gaba da cewa wannan yarinyar ni wallahi ba kishiyata bace ba "yar aiki ce ka kawomin kuma tayimin iskanci saina bata kashin bala'e , ƙawayenta suka fito suka jata suka koma ciki da ita suka ci gaba dayi mata huɗubar shaiɗan! An mata kukan me kike a tsakar daren nan ? Ba komai na faɗa cikin ɓacin rai , kusa dani ya zauna ya riƙoni na kwace kaina tare da matsawa daga kusa dashi dan haushin sa nakeji baizo ya kwana dani ba , kuma ko "yar kazar da ake bawa amare ni bai kawomin ba , ƙara matsowa Dikko yayi zai taɓani nace da Allah ka ƙyaleni , tou na ƙyaleki amma kiyi haƙuri dan ma an sakaki a caca to miye ? Shi a tunaninshi inayin fushi ne saboda maganganun Jiddah tou inajin ciwonsu amma nafi jin haushin shi a yanzu , Gyara bakina nayi banyi magana ba , cire takalmin ƙafarshi yayi suba silifas ba kuma ba soso bane ba amma dai zubin slifas garesu , kwanciya yayi saman gadon yace tou taho ki faɗamin , yi nayi kamar banji ba , bai sake magana ba ya gyara kwanciyar shi yaci gaba da baccinshi hannunshi a saman cikinshi inajin har yanzu cikinsa bai daina ciwo ba , can nesa dashi na kwanta ina kallonshi , Haba Jiddah ina wayewarki ? Ina barikinki ? Ina feƙewarki ? Maza fa idan sukayi sabon auren kansu rawa yakeyi ya kasa tsayawa wuri ɗaya ki fita sha'aninshi da matarshi ba jibi zai tafi ya barku ba ? Jiddah tace Eh to ki bari idan baya nan ki riƙa ci mata uwa la'ada waje idan gaban idonshi ne saiki riƙa tattalinta kina nuna mata soyayya ko ƙararki takai masa zaice bata san zaman lafiya , kibi sannu ki zuge mata rayuwar uwa kamar iccen zogala karki sake ki barta ta huta idan azaba tayi mata yawa ita da kanta zata gudu , salon mugunta sanka² suka koyawa Jiddah.... Kiran sallah asuba ya tashi Dikko daga bacci ni har lokkacin banyi bacci ba saboda tsoro , da sauri na juya mishi baya na daina kallonshi , sauka yayi daga saman gadon ba tare da yayi magana ba ya fita daga ɗakin.... Cike da tausayin Sultana ya koma ɗaki shidai yana tausayinta gata "yar ƙararrama shi tayi mishi yarinya ji yake idan yayi jijjiga akanta kamar zataji ciwo , domin shi dai buƙatarshi tana da girma An mata bata iyawa dashi wancan ma da yayi mata yana nadama kuma har yanzu bai daina ba , shidai kawai ya aureta ne dan ya natsar da ita wuri ɗaya tunda kullum yana tare da ita , na biyu kuma ya aureta ne dan girmanshi daya sake mata yasan duk lokacin data ganshi zata riƙa hango abunda ya shiga tsakaninsu , tou waishi tayama zai fara hayema An mata gata duk ta rame ta zama wata "yar ƙarama shidai an cuceshi wallahi wannan ai ɗaukar alhaki ne , ɗan gajeren tsoki yayi sannan yace in taɓota kuma ta taramin mutane ma a gidan nan dana fita kowa yasan abinda nayi , ummm abundai ba wani sirri.... Dikko na fita masallaci Jiddah da zugar ƙawayenta suka shigo ɗakina hada Mardiyya , a saman abin sallah suka sameni tsaye zan kabbara sallah , Jiddah ce ta kama hijabina daga wuya ta yageta har ƙasa ta wurgar da tsumman ta cire kallabin kaina tana taɓa gashina , bayan ta tabbatar ban jiƙashi ba tace Allah ya rufa miki asiri da na rantse da girman Allah yau saina safke miki gashin kai banza ɗiyar ɗan caca tayi baya , Mardiyya ta matso tace ni nan da kika ganni nafi haɗarin jirgin sama kyan gani , ni haɗarina girma ne dashi domin idan nabi ta rayuwar mutum na fita tou fa lallai ya gama rayuwa har abadan duniya , na shigo gidan nan da niyar tarwatsawa ai kin tuna labarin dana baki a mota ko ? Daga haka bata sake cewa komai ba , ƙawayen Jiddah suka ci gaba da zuwa gabana ɗaya bayan ɗaya wasu su shafa fuskata wasu kuma su shafa gashin kaina , wata ma cewa tayi wannan ƙugun duk ke ɗaya ? "Yar yarinya dake da wannan babbar halitta ina kuma ga ni'imar aure ta tsargaki lallai Jiddah sai kinyi da gaske idan kuwa ba haka ba saidai tashin zance , haka dai sukayi ta daƙuna ni yayin da wasu suka riƙe ƙuguna suna jinjinawa , wasu kuma suna kallon gaban rigata dole Dikko ke birkicewa koni na samu wannan ai na gama da ko wace irin mace , dariya sukayi gaba ɗayansu banda Jiddah da Mardiyya , A ƙawayen Jiddah mutum 3 ya rungumeni ta ƙarshen itace ta warware gashin kaina ta rungumeni ta baya ta umarci wata cewa tayi mana hoto , ɗaukar hoton akayi da ƙarfi ta juyo dani ta sake rungumeni tace a ɗauka , sake ɗauka sukayi ana gama hoton tace ina sanki , murmushi nayi tare da kallonta nace ai tun baki faɗa ba na sani , gaba ɗayanku zan iya fitar da fetir zan kuma iya fitar da kalanzir a cikinku , Ku baƙin mata ne kuma baƙine a harkar lesbian ƙananan "yan iska , ke Mardiyya ke zaki basu labarin Sultana duk wacce tasan ta rungumeni a cikinku saina ɗauko mata hoton uwarta tsirara , ita Mardiyya furtawa kawai tayi ni na cika mata kalmarta ta hanyar ɗauko ubanta a cikin yanayi mafi muni a rayuwa , ke Jiddah kike ko wace ce ? Ni nan da kika ganni iskanci ne ɗore a cikin cikina da zaran kin latso wurin ƙaryarki ya ƙare ki kiyayi haɗuwarki dani , me kike tunani ne ? Tou idan baki sani ba a daren jiya Dikko maimaicin dahuwar dambu yayi min ko an faɗa miki ni ƙazamiyar mace ce mai kwana da janaba a jikinta ? Anyi an kuma an ƙara an ƙara ƙarawa kuje waje ku jirani kafiran banza da bakwa kallon alƙibla , tsoki nayi tare da naɗe gashin kaina na nufi hanyar toilet , Dariya Jiddah tayi tare da cewa burgar banza yo me yayi dake a daren jiya bayan tare ya kwana dani ? Ihun ki yasa ya fito banza duk abinda ya shiga tsakaninta da Dikko a jiya da magiyar da yayi mata dan da farko bata yadda ba haka tayi ta tonawa Dikko asari abindai bai kamata ba , jin kukan motarshi yasa suka fita daga ɗakina Jiddah naci gaba da basu labari suna dariya , Jakunan banza duk saina ci uwarsu in Allah ya yadda wallahi naji ciwon yadda Jiddah ta buɗe sirrin Dikko abun baimin daɗi ba amma zai dawo ya sameni saiya faɗamin abinda yasa ya aureni , wayata naje na ɗauka na kira Inna yanzu ma bata ɗauka ba , Wannan tafiyar ma dubu ɗari biyar Jiddah ta bawa Al ' Ameen bayan ta cika masa mota taf da mai ya nufi zaria , zuciyarshi na saƙa ƙeta iri² , su kuma ƙawayen Jiddah shatar mota sukayi bayan sun tabbatar wa Jiddah zasu dawo sati na gaba...! Har yanzu ban daina kiran wayar Inna ba daga ƙarshe ma kashe wayarta tayi , tashi nayi na koma saman gado na kwanta ina kwanciya wayar Amisty tana shigowa , ɗauka nayi bayan mun gaisa take cemin Nana ta rasu , Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Amisty wace Nanar na tambaya idona cike hawaye , Amisty tace Nana wacce kika sani ? Me ya sameta ne ? Wallahi lafiyarta qalau tayi mana bankwana da dare ta fita asubar nan aka tsince gawarta an yadar da ita a bakin bola bayan an kwakwale mata idanuwa kuma an cire wasu sassa na jikinta babu nisa da wata maƙociyarmu itama haka aka cire idonta aka yadar da ita a saman bola bamu san abinda yake jawo hakan ba , wani irin ihu na kwarara tare da yada wayata ƙasa ina cewa na shiga 3 shi kenan sai ni yau zan mutu wayyo na bani na lalace shikenan ashe bazanyi tsawon kwana ba , A wannan yanayin Dikko ya shigo ya sameni , tambayana yayi abinda yake faruwa , kai tsaye na kwashe kaf na faɗa masa amma sai yacemin wai sheɗan ne yake zuwamin a bacci , haka ya lallasheni bayan ya faɗamin cewa shima da haka yakeyin irin nawa ko rashin lafiya ko wani zaiji damuwa duk abinda zai faru da wani a gidansu ko waye zai gani a bacci idan kuma ya tashi abin zai zama da gaske , wannan karki wani damu sheɗanu ne kuma zai daina , kallonshi nayi sosai sannan nace sheɗanu wane iri ? Aljannu mana , cikin tashin hankali nace wane irin aljannu kuma nayi maganar cikin mutuwar jiki na tsorata , cikin hayagaga yace ke da Allah ban sani ba , Nima cikin hayaniyar nace kar Allah yasa ka sani kuma ya toshe ilimin sanin naka , murmushi yayi tare da cewa tayi bakan damiyar nata saina kaiki goruba anjima naci ƙaniyarki "yar rashin kunya , sai kaje goruba zakaci me yasa anan baza kaci ba , anan ? A , a , ni bana taɓa ki a gidan nan ki ɓarewa mutane baki kiyi ta musu ihu saina kaiki can zan rufe ƙofa in baki wahala sannan na dawo dake , idan ka tashi karka dawo dani da raina ka kashe ni , babu wanda ya taɓa mutuwa kuma a kanki baza a fara ba amma zaki ci gidanku ƙaramar yarinya mai bakin tsiwa , badai kinci kaza ba ? Hmmm saina kulle bakin rashin kunya... Sai kazo ka kulle , hmmm bakina waye ya isa ya rufemin tunda ba mutum ya bani abuna ba , juyawa Dikko yayi ya fita daga ɗakin bai sake magana ba , wayata dana faɗar ƙasa na ɗauka tare da cewa Allah ya jiƙanki Nana ke kuma taki ƙarshen haka yazo Allah na roƙeka ka taimakemu muyi kyakkyawan ƙarshe , da yanayin mamaki nace tou shi Dikko da yaga nashi sheɗanun ko ance za'a kashe shi ? Wayata na ɗauka na fara kiranshi , ƙin ɗauka yayi a bayyane nace kai ta dama , yana ramawa ne dan ya kirani jiya ban ɗauka ba , tou saina kira so adadin yadda ya kira bai ɗauka ba sannan zai anshi kiran nawa... Da zullumin mutuwa a raina na koma bacci , wanda baiyi shawara dani zaizo ba , Dikko wanka yayi ya fice danshi Allah bai masa baccin safe ba , cikin bacci naji ni ina lilo saman ruwa da sauri na buɗe idona Jiddah na gani tsaye rungume da bokita a hamatar ta kaɗa kai tayi tare da nunamin inda agogo yake sannan tace an samu gado an wani mimmiƙe sauka kije kiyi aiki ko kina nufin nice zan girka miki abinda zaki ci , Kallon Jiddah nayi sannan na kalli inda ta jiƙa gadon sauran ruwan bai gama shiga cikin katifar ba nace ke zan dafa ma ko wa ? Ɗan ya tsina fuska tayi tare dayin wasa da bokitin hannunta cewa me kika iya wanda zaki girka ki bani naci ? Ai gidan ɗan caca babu cima , ƙanzo gari sai kuwa kwaɗon tuwo idan an samu kinga baki da ilimin dafamin abinda zanci , to me yasa kika tashe ni ne ina bacci ? Saboda baki isa kiyi bacci ba tashi zakiyi ki girkawa masu aiki abinci , saukowa nayi daga saman gadon nace aiko ubanda ya aifeki zanci , caca ubana yafi ƙarfinki mijina ma ya gagareki bare Babana ,ai saidai kici abinci ki miƙe a saman gado kafin Momy ta dawo taci uwarki ki koma inda kika fito , ni bana faɗa da kishiya saidai na kwace mijin ciwon zuciya ya kasheta , taya ma zan fara haɗa jiki dake in kwashi talauci ? Ai an daina faɗan kishi saidai ayi a ɗakin miji , ido fa yana kallo wallahi saidai ki gani ki haɗe yawu lafiyayyen namiji mai kuzari wanda babu irinshi a bariki , jarumi ɗaya mai naɗawa mata duka naushin shi da daɗin kalamansa wurin yabo nada daɗin saurare Yaya yafi ƙarfinki , mamayata aurenki yayi tunda kin shigo saidai kici abinci kisha ruwa amma Dikko yafi ƙarfinki , daren farko na a america nayi shi , naci kaza nasha lemu keko ko ruwan faro ba'a baki ba , mijina ya kwaremin kayan jikina idonshi yana kallon nawa cikin soyayya ya lallaɓeni yayin daya kwanta dani , Allah yayi miki albarka Jiddah shine abinda ya furta lokacin daya jini sabuwar mota ce kin kawo min budurcinki ya faɗa cikin jin daɗi , gyara riƙon bokitin tayi taci gaba da cewa , a jiya kuma riƙeni yayi a jikinshi saida yayi min kirari uwar gida sarautar mata farar mace alkebbar amarya ni waccan jakar ban ɗauketa mace ba shi yasa na baro ta nazo gareki ki bani maganin damuwata tou ina soyayyar ? Ai dama a saman gado ake nunata ɗakinshi yafi ƙarfinki bare har kisa ran hawa saman gadonshi wannan ni'imar Jiddah kaɗai zataji ƙwalelenki Caca , Ngode sosai da saƙon ta'aziyyarku a gareni , Alllah ya bada lada ubangiji muma ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo am3n , Kuyi haƙuri idan har kunga banyi typing ba wallahi ina da ƙaton dalilin daya hanani kuyi haƙuri ni bana mantawa daku kuna raina kamar yadda An mata take a ran Dikko , *RABI MUSA* katsina zance ko kaduna ? Mrs Usman Abdullahi yau nayi typing sai a sakarmin mara inyi fitsari , mu duk muna miki fatan alkairi ubangiji ya ƙara zaman lafiya da kwanciyar hankali "yar uwata , 17/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA ce....*💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 77 Murmushi nayi tare da shiga toilet na ciko boket da ruwa nazo na sheƙawa Jiddah bala'e Caca ni kika jiƙa ta fara anbaliyar aman zagi na "yan tasha ban bi takanta ba na koma toilet na sake cikowa nazo na zuba a gado sannan na mayar da bokitin na fito har yanzu bata daina zagi ba , bayan na fito na matsa gabanta nace sa idonki a nawa wace ce ke ? Waye Dikko ? Anshe goruba a hannun kuturu ba wuya yake ba , makaranta guda gareni da na tara taron mata nake basu ilimin zaman gidan aure nice malamar , ke har kin isa Dikko a nawa yake ? Bare kuma ke da baki da lissafi balbaɗaɗɗa mai tona asirin mijinta , ni bana kuri haka kuma bana cika baki a zahirance nake bayyanar da saƙona , maganar Dikko da ɗakinshi rashin cin kaza ko ya kwana a ɗakinki ba damuwa na ne ba , amma zan nuna miki yadda ɗakin miji ke zai gagareki shiga sakarar banza , kuma daga yau idan kika sake cemin Caca saina caccake miki idon uwa. Wani irin duka takaimin a fuska a wahalance na riƙe hannunta tare da cewa bani zaki daka ba ki koma wurin wacce ta faɗa miki saiki faɗa mata abinda nace idan ta baki ansar magana na kya dawo , kokowa ta kamani dashi ga sulbin tiyels da aka jiƙa kuma ai Jiddah tafi ƙarfina tunda shekarunmu ba ɗaya ba , bamu wani daɗe muna cakusawa ba Dikko ya shigo cikin ɓacin rai gaba ɗayanmu saida ya zazzabga mana mari sannan yace meya haɗamu ? Cikin fushi na juya mishi baya ina kuka ƙasa² , itama Jiddah kuka takeyi kunsan "yan gayu basa san wahala tasha mari ni kuma dama na saba , ni kuma yunwa ce ta saremin guyawuna da kuzarin jikina , cikin kuka take faɗawa Dikko abinda nayi mata da turanci , raina a ɓace nace idan ba munafurci ba a faɗa da yaran dana sani mana , Dikko yace ma Jiddah ta tafi , juyowa nayi tare da cewa ina zatace ? Ai babu inda zataje kayi gulma kace taje kuma ? Allah dai ya haɗani da munafikin miji., Nine munafiki An mata ? Eh idan ba munafurci ba kaje kacewa Jiddah ka ƙagara Mom inka ta dawo ta wulaƙantani baka so na ni jakace shi yasa baka siyomin kaza ba , ita kuma a daren farkon ta taci kaza tasha lemu ni ko ruwan faro baka bani ba , itace farar mace alkebbar amarya , bazanje ɗakinka na kwana ba shi yasa ta jiƙamin jikina da gadona wai a gidanmu ba'a hawan gado zan kwanta a ƙasa sanyi ya kamani ɗakin miji yafi ƙarfina bare na fara tunanin hawan saman gadonka , kuma jiya a ɗakinta ka kwana kana mata magiya , Dikko yace nine na kwana a ɗakinki ? Yayi maganar yana kallonta ? Yaci gaba da cewa nine nace miki ina jiran Momy ta dawo taci mutuncinta ? Ni nazo ɗakinki ??? Fuuu Jiddah ta fita daga ɗakin , kallona Dikko yayi sannan yace kebaki gane sharrin mata ? Na rantse da girma Allah bayan na fita daga ɗakin nan naje zanyi wanka in dawo kuma kema haka nace miki ina dawowa , toilet ina na samu Jiddah tanayin waya , nazo zan shiga toilet sai.... Tsoki Dikko yayi tare da cewa bama zan faɗa miki ba ni nasan abinda yasa ban dawo ba kiyi magani na , kawai kadaiji kunya an tirka ka. Kuma ni bazanyi maganin ka ba saidai ayita ta ƙare kawai ka bani tikitin saki nayi gaba abuna , danni bana iya zaman takura haka kuma bazanyi haƙuri da wulaƙancin dangin miji ba , wai ke ni zaki maida ƙaramin yaro , ina faɗa kina faɗa ni zaki maida kamar mace kina sakani a shirmenku nine aka turke? Tou ki buɗe kunnen ki da kyau ki saurareni idan har nasan zan sakeki a rayuwata da bazan ɓatawa kaina lokaci na auroki ba , da bana sanki ko kuma nasan zan auroki dan naci zarafinki dana barki a tare dani kawai na zamar dake karuwata , idan zanyi kawai zanyi ne idan banayi banayi kamar iska haka nake yayin dana taho babu wanda ya isa ya tareni sai nakai , ni bana lallashi kuma ban iya ba saidai idan kinmin yarinta zan zaneki ba abinda ya dameni ki dawo da hankalinki jikinki kuma kisan inda yake miki ciwo , Bawai zan zauna nayi ta kare miki faɗa ba dan idan yau ina nan gobe bana nan , ki koyi haɗiye damuwa da ba abun duniya baya dan ba komai kake nema ka samu ba a rayuwa , kuma bawai kullum zakiji daɗi ba abinda kike so bashi zaki samu ba , domin rayuwa juyawa takeyi kuma tana tafe da darussa da dama wata rana uwa zaki zama dole sai kin zama jaruma a gidan aurenki domin ta haka kaɗai zaki fuskanci rayuwa , idonki zaki buɗe sosai ki gano abinda yake tafiya a gidan nan kiyi maganin damuwa tun kafin ta dameki kiyi ƙoƙarin gusar da abin harin rayuwarki tun kafin ya gama farautar abun harinsa ya fara farautar taki rayuwa , duk wanda kika gani a gidan mijinshi yana da tashi matsalar , wata uwar miji , wata dangin miji , wata abiyar zama wata mijin ne gaba ɗaya , keda kina nufin kinzo zaki kwanta idan abin ya dameki ki ɗaga waya ki kira Dikko ya tare miki faɗa ? Ki gyara tunanin dan wallahi ko a gabana Jiddah ta faɗar dake sannu bazance miki ba , bana san zama faɗa da zage² tayar da fitina yana lalata arziƙin namiji kiyi haƙuri duk abinda tayi miki wata rana zai zama labari , baki yunwa baki ƙishirwa ba rashin sutura ko damuwar wurin zama , idan zaki kwantar da hankalinki ki zauna lafiya tou idan kuma kincemin yarinta ina da maganinki , Ita kuma Jiddah bata da lissafi tana tare da makashinta bata sani ba , nasan halinki sarai idan har na faɗa miki maganar nan kikayi gori wallahi idan naji saina zaneki da bulalar dukan doki , ni nace Mardiyya ta tafi Jiddah tace baza ta tafi ba , zagina fa tayi wai babu gidan ubanda zataje , tou idan baki sani ba Mardiyya ta turomin text , wai ga Aunty Jiddah can bata san zaman lafiya taje tana matsawa Aunty amarya , Aunty Jiddah bata san zaman lafiya ta cika tsatstsaga , amma zan faɗawa Jiddah dan tasan matsayin Mardiyya a wurinta dan ita tana ma Mardiyya kallon mai santa hmmm zata kaita ta barota domin duk ranar da haƙurina ya mutu zanyi ɓarna a gidan nan.... Ki fita harkar kowa kiyi rayuwarki tun kafin fushina ya shafeki , yanzu a ina zan kwana , cikin hayani yace ban sani ba , goge hawaye na nayi tare da matsawa can daga nesa shikenan kuma bazan ci kazar ba ? Fita yayi daga ɗakin bai sake magana ba , cire kayan jikina nayi na shiga wanka ina tunanin Mardiyya , tabbas a maganarta akwai lauje cikin naɗi , tana da wata manufa nata na daban , miye tsakaninta dani da har zata faɗawa Dikko ? Kuma har take goyon baya na ? Ba kece damuwarta ba zuciyata ta bani amsa , yayin da maganganun Mardiyya suka fara dawomin a cikin kaina , Ni nan da kika ganni nafi haɗarin jirgin sama kyan gani , ni haɗarina girma ne dashi domin idan nabi ta rayuwar mutum na fita tou fa lallai ya gama rayuwa har abadan duniya , na shigo gidan nan da niyar tarwatsawa ai kin tuna labarin dana baki a mota ko ? Lallai wani abu zai faru ko kuma yana faruwa , shi kuma Dikko yacemin idona zan buɗe sosai na gano abinda yake tafiya a gidan nan kiyi maganin damuwa tun kafin ta dameki kiyi ƙoƙarin gusar da abin harin rayuwarki tun kafin ya gama da abun harinsa ya fara farautar taki rayuwar , duk wanda kika gani a gidan mijinshi yana da tashi matsalar , ki gyara tunaninki dan wallahi ko a gabana Jiddah ta faɗar dake bazan miki sannu ba , wanka na naci gaba dayi ina tunanin duk amincin dake tsakanin Mardiyya da Jiddah shine take mata zagon ƙasa.......? Jiddah ki farka idan bacci kikeyi Mardiyya bata sanki dan zata kaiki ta baroki , zata kaini ta baronin kai takai ta baro ne ? Tunda an ƙunsa ka a ɗaki an faɗa maka ƙarya da munafurci ai dole zakace bata so na , um umm ita ta faɗamin kuna faɗa da An mata wayarshi ya miƙa mata cewa duba ki gani , ansa tayi ta gani Dikko ganin ranta ya ɓaci yasa yace kindai gani ko ? Tou ki dakatar da ita domin da zaran na yanke hukunci tou fa ko kaina bana saurara....... Cikin ɓacin rai ta fita daga ɗaki , Daren jiya An mata nasan baki iya ɗaukar Dikko wahala zan baki "yar yarinya ta bara dai inzo muyi bacci kinji ko ? Yana faɗin haka ya fita da tafiyarshi ta sakakkin " ya "ya. Wayoyinshi ya ɗauka daga palo ya shiga bedroom , a gefen gado ya ajiye ya tunkari ƙofar toilet kai tsaye , magana yaji ƙasa² a dai² lokacin daya dafa handle in da niyar murɗewa ya shiga muryar Jiddah yaji tana cewa Al ' Ameen Mardiyya tace kana kirana shiru , bayan wani lokaci tace taya zan fito bayan gidan yana cike da mutane idan an ganmu tare mutane zasu ɗauka wani abu a tsakaninmu tunda bakwa shiri yanzu , shiru , wane maganin ? Na zuba ai , ɗakinta , a , a idan ya gano da damuwa nan zai birkice kuma kaga damuwa za'a samu , ba komai mu haɗu ta ƙofar baya misalin 3:15 sai in baka , ba damuwa , idan kaje ka haɗani dashi zamuyi magana , yawwa sai anjima , fitowa tayi taga Dikko a tsaye a wayance yace ranki ya daɗe kema kinyi wankan ne ? A , a , ta bashi ansa , murmushi yayi tare da rumgumarta suka koma toilet in tare da tunanin me aka zuba a ina aka zuba ? Kardai itama An mata kamar na Sadiyya zai faru da ita ?, an zuba , kuma an kira ɗakin ta shine bai gane ba , bayan sun fito wanka ne ya kulle ƙofa yace ma Jiddah tare zasu kwana , A damuwance yaja ta zuwa saman gado bayan ya gama shirin kwanciya bacci , Sadiyya tazo mishi a zuciya ta tsaya mishi wayayya "yar gayu tanayin abu irin yanayin na An mata itama ma'aboci hawan jikinshi ce kafin suyi aure , A asibiti. Ranta ne ke ta kai kawo tsakanin maƙoshi da zuciyarta , hawaye yana zuba daga idonta tace ka yafemin kuma karka riƙeni a zuciyarka ka manta da abinda nazo maka dashi a daren da yafi ko wane dare farin ciki , amma sai ya zamar maka dare mafi muni a wurinka , na kasa sarrafawa bana iya danne sha'awata ka yafemin don girman Allah ta haɗa hannayenta biyu 🙏🏻tana kallon Dikko , Riƙe hannayen nata yayi tare da cewa na yafe miki nifa dama ban wani riƙe ba na faɗa miki na yafe miki² na yafe miki Sadiyya ya ƙarasa maganar yana kwantar da kanshi a gefen allon kafaɗarta yana ci gaba da cewa wai miye matsalar kukan nan ne haba Sadiyyata ki daina saka damuwa a ranki har abadan duniya wallahi na manta da wannan damuwar a raina , kayi min alƙawari ko bayan bana nan bazaka faɗawa kowa ba , nayi alƙawari bare ma kina nan bazaki je ko ina ba muna tare insha Allah , faɗamin meye ne ? Ya ƙarasa maganar yana ɗagowa ya ƙureta da kallo. Fashewa Sadiyya ta sakeyi da kuka Dikko ya riƙeta da riƙo mai nuni daya martabata yace bana san kuka fa nidai sauri ƙufula gareni faɗamin meye raina ya fara ɓaci zanyi fushi cikin mintuna biyu , cikin ɓacin rai yace me ne ? Murmushi Sadiyya tayi tare da cewa Allah zai baka lafiyar damuwarka idan na ganshi bana iya ganeshi amma idan naji muryarshi a yaranka zan gane maganar shi saboda bana ganinshi waya mukeyi yana bada saƙo ana kawomin kuma da sa hannunshi a lalurarka ya haɗa kai da matan Babanka an gurgunta maka rayuwa akan naira miliyan biyu , yayi amfani dakai ya kai min rayuwata ƙarshe bashi da imani duniyar kawai yake so shi akan kuɗin zai iya koma miye.... Waye ? Dikko ya tambayeta , sunan sa da sanin waye shi ban sani ba , ke me yayi miki ne ? Sama lumfashin Sadiyya ya ƙarayi cike da soyayya ta kalli Dikko sannan taci gaba da cewa. Na taso cikin soyayya da kulawa ta iyaye , iyayena shahararrin "yan boko ne suna da cikar arziƙi yahudawa ne sosai wanda basu damu da rayuwar yaransu ba , gani na a sake yasa nakeyin rayuwar data tari gabana bawai rayuwar iskanci ba rashin ji lanƙwasa gandar aiki bana aikuwa idan na shige ɗaki sai zanje makaranta nake fitowa , ɗakina babu mai zuwamin daga ni sai rayuwata sai kuma wanda naba izinin shiga. Rayuwata ta samu matsala ne a makarantar kwana { boarding }, bayan nayi jss3 a makarantar jeka ka dawo wato day aka kaini makarantar kwana , ni bana san boarding saboda wahalarta , amma fur Hajiya tace sai naje , na shiga damuwa Yayuna maza sukace dama da makarantar kwana na dace haka sukayi ta zugawa tun Dadynmu bashi da ra'ayin haka harya amince na tafi boarding. Ina shan wahalar makaranta yadda ya kamata domin dai ina bacci kamar a gida ina fita sch amakare kulle sai prefect sun zaneni , ni ban saba da wahala ba , kullum haka ake cimin uwa amma kullum saina makara kuma basa gajiya sai sun zaneni. Yauma gani durƙushe a gabansu S P inmu ce tace karku daketa ke zo nan , tashi nayi naje gabanta na durƙusa wasa tayi da bulala a jikina sannan tace me yasa bakyajin magana ke jakace kullum ayita dukanki bakyajin zafi ne ? Kiyi haƙuri bazan ƙara ba , kullum haka kike faɗa kin raina nasu ko ? A , a , hijabina ta cire ta zaneni saida ta tabbatar ta farfasamin jikina sannan ta wurgomin hijabin tace tashi kije. Yinin ranar kuka na yini yi , tun daga wannan ranar ta sakamin ido ko hostel bata bari na zauna lafiya nine ibo mata ruwa wankinta tsefe mata kai gyaran ɗakinta komai dai nice nakeyi mata banda lokacin kaina sai nata , wahala yasa na rame nayi baƙiƙƙirin , Tsugunne nake a ƙofar ɗakinta ina jiran fitowarta daga kwanar wata ƙawarta da gudu ta safko daga saman gado tana dariya tace ke ɗaukomun ruwan wanka nan , ɗauka nayi nabi bayanta har toilet , ajiye ruwan nayi zan fita ta riƙoni tare da cewa kwancemin towel ina , cikin jin kunya nace yi haƙuri Aunty , bazanyi ba kunce shi kafin ince ke zakimin wanka nan cire kar na sake miki magana , kiyi haƙuri don Allah , idan kika sake bani haƙuri saina ja miki sharri na hanaki zaman lafiya a makarantar nan kuma zan sakawa rayuwarki ido kuma saina miki fyaɗe zan lalata ki ne ba abinda ya dameni , zaro idanuwa nayi nace fyaɗe kuma ? Dama mace tana ma mace fyaɗa ? Dan Allah kiyi haƙuri , idan kika bari na sake magana zanci ubanki , rufe idona nayi tare da kai hannuna saitin da nake tunanin tana nan ashe baya taja , buɗe idona nayi dan ganin ko banyi saiti ba , daga can ciki na ganta ta sake wuri tana cewa ke nake jira , Cikin toilet in na shiga dan daga waje nake , shigo ki rufe ƙofa , dan girman Allah kiyi haƙuri, bana san haƙurin nan daga bakinki kullemin ƙofa nace , shiga nayi tare da cewa ai zan kunce basai na rufe ba , murmushi tayi tare da matsowa ta rufe ƙofa ta cire towel in jikinta babu kunyar Allah bare ni , ciremin hijabina tayi ta ɗora a saman inda ta ajiye towel inta tace kina so in daina dukanki ? Shiru nayi idona a rufe , bakyaji ina magana buɗe idonki mu fahimci juna , ƙin buɗewa nayi kuma banyi magana ba , Dariya tayi tare da ƙoƙarin fara ciremin rigata , riƙe jikina nayi da karfi ta yadda bazata iya cirewa ba , murya a sanyaye tace Sadiyya buɗe idonki mana , ƙin buɗewa nayi danni gaba ɗaya kunya ya kamani wannan ƙatuwar zata cire kayanta jikinta a gabana , hannuna ta kamo ta ɗora a saman ƙirjinta kamar wacce aka watsa ma ruwan zafi na janye hannuna , cikin rarrashi tace buɗe idonki mana bazan sake dukanki daga yau ba , kuma nayi miki alƙawarin wahala ya ƙare zanyi ta baki kulawa har na bar makarantar nan , zaki dawo ɗakina da zama zakiyi bacci kuma nice zan riƙa miki wanki komai da kike min ni zan miki natsuwa kawai zaki bani yanzu zan nuna miki yadda zakiyimin saki jikinki zan cire miki rigarki , Feƙaƙƙiyar "yar maɗigo ce tasan hannunta a harkar lesbian , tunda ta sameni ta tattara sabgar ko wace mace ta zubar saini , ta dawo dani zama ɗakinta bana wahalar komai kullum ina kwance tana nunamin soyayya fiye da yadda miji yake kula da matarshi ta iya tattalin mace kuma tana da karuwanta a met insu amma tunda ta sameni kawai ta zama mijina na zama matarta ko wanka bata bari na nayi da kaina kafin wani lokaci nima na goge a harka dan Yusra mayya ce akan mace , Karuwanta ganin ta zubar dasu hankalinta yana kaina yasa suka taso ma rayuwata ido , dan ta ɓata da kowa saini , duk inda zataje dani take tafiya a hostel lokaci guda nima na faso na zama gogaggiyar "yar lesbian ta ƙarshe , Yusra kishi gareta na tashin hankali wannan dalilin yasa take yawo dani lokaci guda suna na ya fara zagawa a makaranta dan Yusra azzalimar shugaba ce , taga dama yarinyar tayi mata laifi kafin ta sanni tace ta sameta ɗakinta da daddare yarinyar ta biya mata buƙatar ta korata , tunda ta sameni sai Allah ya fitar mata da san ko wace irin mace a duniya saini. Karuwanta kuwa neman sa'a na suke suci ubana , wasa² nima na fara halbawa neman mata , idan mace ta taho haka zan tsareta da ido ina kallon ƙirjinta ƙugunta yanayin zubinta da dirinta abun yana neman ya zamar min kamar wani bakin iyaye dan ko a sch na tuno da yadda muke rayuwa da Yusra idan ban ganta ta rumgemeni ta ɗan jagulani banajin daɗi , maganar karatu kuma na daina bana ganin kowa bana gane kowa sai Yusra , ko kora ta fita kafin ta dawo na fara kuka banda natsuwa sai tana nan , tun abun yana burgeta harna fara tada mata hankali domin yanzu na fita jaraba , wani lokaci sai munyi faɗa zan riƙeta a yunwance dana gaji nace mata nidai tunda kin gaji dani ki sakeni kawai zanje na sake wata tunda kin gaji dani , haƙuri ta bani wai ita bata gajiya dani kawai dai in fahimta bawai kullum akeyin abun ba sai an huta taya ƙarfinta bai gama dawowa ba zata iya bani wata natsuwar , ko abinci ne ka kwakwafe ma ɗaya saiya fitar maka a rai , haka nayi ta roƙon Yusra tou ta fitar min da lokaci na ni ɗaya idan ba haka ba gaskiya zan barta nayi gaba , Na rabu da Yusra ne a lokacin da asirinmu ya tonu , abokan harkarta suka sameni a ɗaki da safe ita kuma lokacin ta fita dan dubo yara dake shara , sukayi min duka har suka sumar dani , da Yusra ta dawo ta sameni hankalinta ya tashi bayan na dawo dani daga suma ta tambayeni abinda ya faru na faɗa mata , duk wanda ya dakeni saida Yusra ta buɗe masa kai da sukundireba , wannan ɗanyen aiki da tayi shine yaja mana zuwa wurin shugabar makaranta , anyi case mai girma domin kowa babanta attajiri ne kuma saida aka tattaro iyayenmu tonan asirin dai babu daɗi , haka aka zane Yusra bugun bala'e akayi mata bayan an ƙwace kallabinta aka koremu dukanmu daga makarantar , Nidai a gidanmu Yayuna maza sukamin bugun leƙa lahira ki dawo , bayan komai ya kwaranye e aka maidani makarantar jeka ka dawo , haka nayi ta farauto yara ina kawosu ɗakina in basu kuɗi , ganin ban fita harkar mata ba yasa aka cireni daga makaranta kwata² gashi bansan garin da Yusra take ba banda number wayarta na shiga tashin hankali harna rasa ina zan shiga , haka nan na haƙura na koma neman abokan Yayuna bana wani jin daɗinsu nidai Yusra ita kawai nake so , Ana cikin wannan badaƙalar ne Allah ya kawoka rayuwata , tunda na ganka natsuwa tazo min na fara mantawa da Yusra saboda tunanin ka nidai ban taɓa ganin namijin daya shigomin rayuwa ya tsareta ba kamar kai , ina sanka kuma naso na zama rayayya domin kai namijin duniya ne ina ma macen data samu gwarzon namiji kamar ka murna , duk kuwa wacce ta sameka a matsayin miji damuwa ya ƙare mata kuma ta zama abin a yaba mata , Bayan kazo gidanmu zuwan farko ka tafi aka fara kirana da wata number mai kiran nawa yana da wayau kuma bai shigo rayuwata ba saida ya gama bincike ni kaf , yasan matsalata neman mata da neman maza na , kiran farko yacemin shi wani almajiri ne dana bashi sadaka nace ni bana bada wata sadaka bana ma fita , sai yacemin ka bada ka tuna ai sai matsiyata ka bada ka manta wannan shine cikar arziƙi , ko kin tuna ko kin manta nidai zan taimakeki , a ina ka samu number na ne ? Musulmin aljani daga saudiyya ya turomin yace na taimaki Halimatus Sadiyya zaki tafi gidan miji bayan kin gama lalata mutuncinki a titi na baki taimako saboda halinki na ƙwarai , idan har kikayi aure namiji ya sameki ba a yadda yayi tunani ba da damuwa , zai wulaƙanta ki haka yay ta faɗomin rayuwata kamar yana karatun littafi , banyi tunanin haka zamuje ba , a dai² wannan lokacin ne Momyn Hafsa ta shigo. Sadiyya taci gaba da cewa shine ya aikomin da wasu layu yace nayi ƙoƙarin sakasu a ƙasan katifa kafin ka kusanceni , idan ka kwanta dani kaji ni a yadda kaji inyi kuka ince ka rufamin asiri , hmmm ya cuceni ashe ba'ayin kuka wanda ya bashi tsibbun yace idan har nayi kuka tou zanyi ta kuka har ranar da za'ayi kukan rashi na , bayan ya tabbatar da hakan shine ya sake kirana ya faɗamin zan mutu kuma a ranar aka cire layina daga wayata kwata² bansan waye ya cire ba , saida ta goge hawaye tace kuma yace zan tafi tafiyar da babu dawowa duk macen da tayi yunƙurin shigar Dikko haka zaiyi ta aikasu ƙiyama babu sassauci , kuma shine yake da sa hannu a damuwarka da taimakon matar uba , shiru Sadiyya tayi daga nan maganar ta ya ƙare , jijjigata Dikko yayi amma shiru domin yana da tarin tambayoyi da zaiyi mata , wannan dalilin ne yasa Hafsa tace yayi kuka kamar rashin zai fita , a cikin ku waye ne ...? Karku kashe An matana , tou ko kune take gani a bacci...... ? Wannan dalili ya hana Dikko komawa ɗakin Sultana yaji an anbaci magani kuma ance ɗakinta tun a daren bai bacci ba har lokacin da Sultana tayi kuka a dai² lokacin da Jiddah ke dawowa daga wurin Al ' Ameen kuma ya fita ta kicin amma basuyi magana ba kuɗi kawai ta bashi ta dawo , shi yasa bai fito da sauri yaje wurin Sultana ba , ita tana hawowa ta ƙasa shi kuma daga sama yake saurarensu saitin ƙofar baya kamar yadda tace , haka yasa su biyun suka kasance a ƙasa shi a sama Jiddah da Sultana a ƙasa , kuma idonshi biyu Al ' Ameen ya kira wayarta kamar dai² lokacin da tace su haɗu , ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa yarana , to waye a cikin ku ? waye kai me kake so ne da rayuwata ? Al ' Ameen ne gurfane a gaban bokanshi yace shi Jiddah ba damuwarshi bace ba yanzu Sultana itace matsalarshi boka yayi waje road da ita Mardiyya zataji da Jiddah. Da kokowa Jiddah ta kama Mardiyya tana dan ubanki ni zaki ma munafurci yau sai kin bar gidan nan tunda ba gidan babanki bane ba , ni zaki kashewa aure Allah ya tona miki asiri kaza² , Mardiyya tace Aunty wai me akayi ne ? Kinje kin turawa Yaya text kince muna faɗa ke baƙar munafuka , cikin kwantar da murya Mardiyya tace Allah sarki Aunty ina tsaye ina tayaki kishi na ƙwaƙwafe a wurin ganin na ƙwatar miki "yan cinki amma bazaki gode ba , iyayena sai cewa suke na dawo gida amma ban tafi ba saboda ina so naga bayan Sultana daga gidan nan ta ƙarasa maganar tana fashewa da kukan makirci , tou a haka zakiyi ? Me yasa zaki tura text wa Yaya ? Cike da ladabi tace Aunty dan ya yadda dani ya haɗani da kula da rayuwar Sultana ta haka zan shiga jikinta nasan sirrinta kafin ta ankara mai gamawa ta gama , amma kiyi haƙuri bansan abun zai miki babu daɗi ba , jakar bata gane komai ba sai tace tou kiyi haƙuri Mardiyya ai bansan haka kike nufi ba , wuri ta samu ta zauna Mardiyya taci gaba da kaita tana dawowa. Lokacin dana fito wanka har an canja sabuwar katifa an goge ɗakin tas an sa masa turaren ƙamshi mai daɗi a gefe kuma wasu irin ƙatunan food flarks ne masu kyau a ajiye , wurin naje na buɗe dariya nayi tare da lashe bakina nace kajin ne ko me ne ne ? Koma dai miye zanci shagalina na gama na kwanta yarinya ta sake dawomin ɗakin ko tacemin caca saina kware mata fatar fuska. Dikko kuwa daga wurin Jiddah wurin su Bello ya nufa , gaba ɗayansu sun zama abun tsoro sun saɓa kamannunsu abun dai sai Allah ya basu lafiya , Dady yaji uwar bari yasa an kawo kuɗi da takardun gonaye filaye da gidajen daya haɗa yayi handama da babakere , saida ya ƙara cin ubansu ya diddira musu yace ko a mafarki An mata ta sake ganin wani a cikinsu wallahi saiya takashi da mota yaja da'ira ya raba kowa da ita mai ƙararren kwana yazo , sunci uwasu har babansu sannan aka sakesu sai sun haɗu a wurin rabon gado , suka wuce shi kuma yayo gida. Qerau cike take taf da mutane an zubar da gawar Nana a ƙofar gida ta zama abun kallo masu wayoyi sai ɗauka hoto sukeyi , abunda babu kyan gani mijinta kuwa mutuwarta ko jikinshi amma su Amisty sunji ta sosai , Hafsa kuma har yanzu bata dawo ba , yau zaman makoki da jimami a Qerau kuka da baƙin ciki yana wurin dangin gawa. Saida naci na ƙoshi zuciyata ta fara tashi duk abinda naci dan na kwantar da tanzomar tashin zuciyar baya tsayawa kamar zanyi amai amma baya zuwa , toilet na shiga na wanke bakina na jawo amai amma yaƙi zuwa kam aiko sai kazo wallahi dan duk abinda naci ya tashi zuciyata fitarshi daga jikina shine natsuwa , saida na sheƙa amai hankalina ya kwanta , ina gamawa na gyara wurin na fita , hijabina na saka na fita dan samun abinda zanci dan gaskiya yunwa nakeji na tashin hankali. Cikin yanayin gajiya na sauko na shigo palon da farin ciki , sai yanzu naji hayani , Aunty Suwaiba na gani zaune a saman keken guragunta a ɓangare ɗaya kuma ana riƙe Dikko yana saiya kasheta , yau kwata² baya riƙuwa duk wanda yaje kusa da Suwaiba dan ɗauketa sai Dikko yace kaima saina kashe ka , sai raba ido takeyi kamar karuwa ta tsare uztaz a ɗaki , ta sharara wani irin fitsari yafi liter goma ta ruwa , kallonta nayi sannan na kalli inda ake riƙe Dikko suna ta ƙoƙarin kaishi ƙasa amma yau sun kasa kwantar dashi , to me ya haɗa Dikko da Suwaiba kuma ? Kai.......... duk saina kashe ku...... dukanku...... yayi wata irin girgirza tare da zazzage su Ashiru ya ɓarar dasu ƙasa , ya nufi wurin Suwaiba idan har yaje mata a yanayin nan zai maida ita kamar damejin milcose , Ashiru ne ya riƙe ƙafar shi daga kwance wani irin ihu Dikko yayi mai tada hankali yace kai zan kashe kaina.............. Zan mutu saina kashe kaina..................... 18/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 78 Duk wanda ke gidan nan ihu Dikko ya tada mishi hankali wata irin zabura yakeyi Ashiru ya riƙe ƙafarshi dakel haka yaba sauran dake ƙasa kwance damar tashi suka nufo Dikko suna kamashi , duka ya farayi duka ɗaya tak yakeyi mutum ya tafi baccin wahala , cike da tausayi nabi Dikko da kallo to wai miye matsalar ne ? Cikin wata irin murya yace wai bana ce bana so ana riƙeni ba , saina mutu... Jan keken da Suwaiba take zaune suka farayi dan fita daga palon , kai............. Wai , wai Allahna wayyo......... Kai....... Idan ta tafi saina kashe kowa a gidan nan duk saina kashe ku...... Riƙe keken nayi nace babu inda zakuje da ita sai Dikko ya bada izinin fitarta wallahi , Mardiyya tace gaskiya ki bari a fita da ita gudun matsala. Kallon Mardiyya nayi sannan nace nabi matsalar da gudu , babu gidan ubanda zakuje da ita baƙaƙen munafukai duk sai Allah ya tona muku asiri ɗaya bayan ɗaya , Suwaiba hankalinta baya wurina kwata² jikinta ko sai kyarma yake idonta kuwa ya zubar da hawayen firgita bata san adadi ba , a dai² wannan lokacin aka kai Dikko ƙasa dakel bawan Allah har yanzu bai daina kuka ba idonshi yana ratata da hawaye hannunshi ya ɗago yana kallon inda Suwaiba take zaune aka zuba mishi magani ya ɗauke. Ɗakinshi suka kaishi a ƙasa suka kwantar dashi saman kafet , bayan sun fito Ashiru ne yaja Suwaiba zai fita nace idan har ka bari aka gudu da ita wallahi saina faɗa masa , cikin damuwa ya kalleni ba tare da yayi magana ba ya fita da ita sai Dikko ya dawo daga hutun taƙin lokaci za'a zazzage sauran tashin hankali , yau wata zataci gidansu mudai ba ruwanmu , nidai kicin na wuce nayi abinda ya shafeni , ina tausayin kaina amma gaskiya ina tausayin rayuwar Dikko. Kafin wani lokaci gidan ya anshi taron "yan uwanshi wanda suke uwa ɗaya uba ɗaya duk wacce tazo ɗakinshi take wucewa fuskokinsu babu daɗi , ina gama abinda nake ɗakina na wuce banbi takan kowa ba. Da sauri na shiga bedroom dan kukan wayana da nake jiyowa , Yazeed na faɗa a bayyane tare da ansa kiran da sallama , gaisawa mukayi bayan gaisuwa yace bai canja miki layi ba har yanzu ? Eh zan kiraki anjima , ba damuwa na tsinke wayar. Har yanzu Jiddah bata daina doke²n waya ba har Momy saida ta faɗawa ta tashi hankalinsu dan haka zasu tattara suma su dawo a cikin kwana biyu masu zuwa. Al ' Ameen bai haɗa Jiddah da boka sunyi waya ba , yadai tattaro bala'enshi ya nufo katsina cikin ƙwarin guiwa , Tunda Dikko ya tafi wurin 2 na rana sai gab da magrib ya dawo kuma har yanzu "yan uwanshi suna nan basu tafi ba suna ta tattalinshi , kallo yabi su dashi bayan ya buɗe idonshi da salati , murmushi yayi wanda bai fito a saman fuskarshi ba , ƙanwarshi yasa ta miƙo mishi wayoyin shi , saida wayoyin suka zo hannunshi sannan ya tashi zaune ya jingina da gado ajiye wayoyin yayi a gefenshi ya tsare babbar ɗakinsu da ido. Sannu tayi mishi , gyara bakinshi yayi cikin damuwa ya ɗan shafa gemunshi tare da dafe kanshi cikin ɓacin rai , gaba ɗayansu kowa sannu yake masa amma har yanzu ɓacin rai ya hanashi yayi magana , miƙewa yayi ya nufi toilet su kuma suka koma palo gaba ɗayansu , wanka yayi tare da ɗauro alwalla ya fito , yana fitowa ya ɗauki wayarshi ya kira Sultana , babu daɗewa ta ɗauka. Ke ban lafiya kinfi ƙarfin kizo ko ? Magana tayi yace kizo ina kiranki , bayan tayi magana yace babu komai kiyi haƙuri , tou ya kashe wayarshi , Nabeela ya kira ƙanwarshi , ta ansa da na'am jeki kizo da An mata , yana faɗin haka ya saka kayanshi ya fara gabatar da sallar la'asar data wuceshi. Itace da Jiddah suka ɗaukoni har gidanmu , kallo ɗaya nayi mata na ɗauke kaina , banda suke tsoron Dikko nasan da babu abinda zai hanata ɗuɗɗura ma uwata zagi dan yanayin fuskarta ya nuna tanajin haushi na kamar ta dakeni , shegiya ni kawai akace ta kira amma saida taje ta fara tura Jiddah sannan tazo ta kirani , banyi mata magana ba nabi bayanta har ƙaton palon da nake tunanin nan ne na Dikko. Sallama nayi amma gaba ɗayansu babu wanda ya ansamin sallamar kowa ranshi a haɗe kamar yace kinci uwarki , ban sake magana ba nayi murmushi tare da murza ƙuguna na wuce inda nake tunanin nan ne hanyar da zata sadani da bedroom in na wuce ina musu tafiya mai nuni naci uwarku nasha ruwan kanwa maganin kwarnafin ciki. Tsaye na sameshi a gefen gado yana ɗora hula saman kanshi ɗayan hannunshi wayoyinshi ya matsa jikin madubi yana kallon kanshi , da ɗan gudu na isa wurinshi na rumgumeshi , murmushi yayi amma bai taɓani ba yayi magana da fulantaci cewa , { dusudu kairu woni sudu ya nuna da hannunshi yaci gaba da cewa leso an min minwoni Dikko kuma inmin ɓilatama edow misudduma e guda miwaddanma fijo danbe ayidi koh ? Ya tamabayeni , } abinda yace wannan shine ɗakina nunawa yayi da hannunshi yana cewa gadona ni nine Dikko kuma nine zan ɗoraki a sama in lulluɓeki da bargo in miki wasan dambe ai kina so ko ? Rufe fuskata nayi a ƙirjinshi , murmushi yayi tare da ajiye wayoyin a saman madubi yace anshi. Ɗagowa nayi na kalleshi , kallona yayi da salo mai tsuma zuciya wasa yayi da harshenshi tare da cewa bisimillah yana duƙowa dai² yadda zai kawoshi wurin bakina , riƙe wuyanshi tare buɗe bakina ya saka nashi a ciki , da hannu ɗaya ya riƙemin ƙuguna yana wasa da harshenshi a bakina , kyarma jikina ya farayi tunda uwar data kawoni duniya idan ba Alhaji mai gidan "yanci ba babu wanda ya taɓa shiga bakina sai Dikko , nashi kuma ba irin na Dikko bane ba dan salon na Dikko daban ne , me ye kike kyarma ? Ba tare daya cire bakinshi ba ya tambayeni ? Kaina na girgiza alamar babu , dafo kaina yayi ina kallon idonshi cewa bakya so ne ? Ina so na bashi ansa , cire bakinshi yayi tare da rumguneni saida ya ajiye ajiyar zuciya yace ba kin rainani ba , ni mahaukaci ko ? Zaki ga haukana a saman gado yarinya , Hmmm zan ɗoraki gadona badai kina so ki hau ba ? Shiru nayi ba magana , yaci gaba da cewa zaki hau yarinya kuma zakiji abinda kowa yakeji daga gareni , sakina yayi daga jikinshi yace ɗauko wancan makullin ki sanyo hijabi ki sameni waje , inda ya nuna makullin na ɗauka a lokacin harya fita palo yana gaisawa da "yan uwanshi , cikin farin ciki na fita ina mai jin daɗin yadda Dikko ya haɗamin bakinshi da nawa , hakan soyayya ne mai girma , wata munafukar ƙara nayi da murna na shiga ɗakina nima na zama mace naje ɗakin Dikko kuma ya rumgumeni da kanshi kuma ya sumbaci bakina wannan ranace mai daraja a gareni , saida nayi "yar rawa nace godiya nake mutumina....... Bayan sun gama gaisawa yace ma Jiddah taje , Yayarshi tace ka ƙyaleta mana , miƙewa yayi tare da cewa ku gaida gida na gode sosai , yana faɗin haka ya fice abunshi , shi yana so yayi magana dasu dake su bahohi ne basa gane karatun kurma tou ya bar muku ita ku zauna tare ku dangi na kusa. Dikko na fita suka fara zagin Sultana wai waccan "yar ɓeranyar yarinyar su take ma yanga ita mai ɗakin miji zataci ubanta , kan Jiddah suka juya haya² suke bata shawarar korar Sultana daga gidan Dikko , wai banda karuwanci kamar Sultana har ta iya yanga dan zata shiga ɗakin miji , Jiddah tace karuwa fa , Yayar Dikko ta ƙara ɗora Jiddah akan ta zage ɗamtse karta kuskusara tabar yarinyar nan ta huta har ta gaji ta bar gidan babu shiri , jakarta dake gefenta ta zage ta fito da wani magani na mata ta bawa Jiddah tace ki gwada wannan daga chaina nazo dashi bana ce miki komai ba labari sai naji ki a waya , haka suka ɗan ci gaba da ba Jiddah haske ga kuma ƙannensu da basu yi aure ba zaune suna ta sakin maganganu su haka suke tou ko Dikko yana nan haka zasuyi firarsu yana jinsu idan anyi abun dariya yaji yana iyawa yayi idan baya iyawa ya girgiza kai , ko kuma yace mata bakwajin magana.... Cike da zumuɗi na fita waje inajin farin ciki a zuciyata , rai a haɗe ya fito fuskar nan babu wasa , saida yazo inda nake tsaye yace muje yayi gaba nabi bayanshi ina rawar kai , kallona yayi tare dayin murmushin mugunta , yace shiga muje ya buɗe gefe ya shiga ni kuma na shiga mazaunin tuƙi naja motar da ƙwarin guiwa na fita daga gidan. Ajiyar zuciya ya sauke tare da kwantar da kanshi jikin kujera a sakace yace goruba ya ƙarasa maganar yana lumshe idanuwan shi , cikin jin daɗi nace tou mai gida nayi yadda su Ashiru keyi , murmushi yayi tare da buɗe idonshi yayi min kallon gefen ido , murmushi nayi tare da ɗaga mishi gira , dariya yayi a ranshi cewa zaki natsu... Saida na ibi hanya ya gyara zamanshi yace An mata na rasa abinda yakemin daɗi duniyar nan kamar zan mutu haka nakeji an dawomin da zuciya a bakin maƙoshi ya nuna saitin wuyanshi yana ci gaba da cewa an hanani na zauna lafiya kowa sai jifata yake kamar wani wanda yayi ridda , duk wanda ya raɓoni yasu² ma asiri suke ma junansu kowa so yake ya yafi ɗayan uwanshi a wurina , abun ya tashi ya koma jefe² mutane suna cewa wai duk wanda zai zauna dani sai yayi ɗamara da neman taimako idan ba haka ba yanzu akai mutum ƙiyama a dawo , ashe ma ba iya su suka tsaya ba nima ɗin so suke su kashe ni gaba ɗaya na zama kamar wani sakarai na zama wani ɓawon ayaba kamar bani ba haka nakeji na wallahi da raina ya ɓaci sai in zama wani zararre meke damuwana ? Dafa kanshi yayi yana hawaye yace ni kaina sai yanzu nake ganewa na zama mahaukaci na gaban feji wai wannan wane irin masifa ne ? Na rasa ina zansa rayuwata naji natsuwa , shiru nayi banyi magana ba , dan na lura yana cikin ɓacin rai na barshi ya sauke damuwarshi ko zaiji salama a zuciyarshi , ci gaba yayi da cewa abun bai tsaya a ni ba yana neman ƙetara iyaka , nafa gaji na gaji................. An mata wai meke damuwa na don Allah , Horn nayi aka buɗe get na shiga jikina a sanyaye , jiki a sanyaye ya jawoni jikinshi bayan nayi parking ya fashe da kuka yana riƙe kanshi da hannun haggunshi yace { surbajo waikowanna tayan gin Allah , a andi yaw an dunda in an huddi anduki min minajado , idume² gadaimi dun najabe gin Allah , ahn............ade'iti , to mirugga hugondube le ahan daga kuwanaibeyan e direba'en Ashiru en bedillai komoi rakkilayan mihoshsheta midillida emada midalai katsina misomi e masifa } abinda yake cewa An mata wai mike damuna don Allah , kinsan ciwo na tunda kece kika fara gane ni mahaukaci ne dame² nake yi na mahaukata don Allah ke.......... Kinyi shiru , tou zan kori duk wani wanda yake tare dani daga masu aiki direbobi su Ashiru kowa zai tafi ya bani wuri zan ɗaukeki nidai zan bar katsina gaskiya na gaji da masifa.... A tausaye na kalleshi nace kayi haƙuri Dikko ba'a kora maƙiyi kuma a cikinsu baka san waye yakeyi ba karka kora kuma karkayi nisa dasu , nasan wannan saboda Bello da Babana ka san mutane suke koya maka darasin rayuwa , ko maƙiyi ya tafi dawowa akeyi dashi karka bari maƙiyi yayi nisa da rayuwarka barshi kusa dakai kana karatunshi ta haka ne kaɗai zaka iya ganinsa sannan kuma kasan inda ya dosa , taya zan karantashi tunda na zama mahaukaci kuma ai kece kika ce ni mahaukaci ne , kayi haƙuri bazan sake ba insha Allah , meya haɗaka da Suwaiba ? Da yanayin damuwa Dikko yace fita ki shiga ciki ina dawowa bai bani amsar tambayar da nayi masa ba , fita nayi , daga inda yake zaune ya koma kujerar dana sauka yaja motar kamar walƙiya ya ɓace daga gidan , ajiyar zuciya na sauke tare da juyawa na shiga ciki , ta inda yabi dani daren ɗaurin aure nabi na wuce har na isa ɗakin daya kulleni yasa nasha wani abu a kofi daya kira shi da service , a gefen gado na zauna nayi tagumi Dikko da fulatanci kuma shi naga Mamanshi buzuwa ce dan bata da hausa mai kyau shi yasa yakeyin wata irin magana shima hausar dai duk bata riƙe musu baki ba , Babanshi shine irin yarenmu amma baƙaƙen fulani ne sune na daji kenan amma bana tunani ya iya yare gaskiya tou a ina Dikko ya iyo yarenmu.............??? Zuwan Suwaiba.... Da gudu ya shigo gidanshi a dai² lokacin da aka fito da Suwaiba daga mota aka zaunar da ita saman keken guragunta , ita taji labarin auren Sultana ance mata ta auri wani matashi mai "ya "yan banki ta taho cin arziƙi bata san Dikko take aure ba , tou ita dai zata faɗa abinda ya kawota , bayan yayi parking ya fita da sauri dan hankalinshi baya wurinsu ciki zai shiga da ƙarfinshi saboda yasa abi mishi Al ' Ameen amma wanda yabi Al ' Ameen in yayi haɗari shine aka kira Dikko dan number Dikko ya bayar , Yana gaf shiga Suwaiba tace wayyo Allah na shiga3 ku maidani mota da sauri karku bari ya ganni kashe ni zaiyi , Dikko daya shiga da ɗan gudu ya dawo baya da sauri jin muryar ta , bayan idanuwanshi sun tabbatar mishi itace ya juya gaba ɗayanshi yace saina kashe ki............. Kalmar kisa daya anbata tasa su Ashiru fitowa da gudu , dan baya faɗar kisan da wasa cikin yanayi mai tada hankali dasa tsoro yake furta kalmar , da gudu ya nufi wurinta yana saina kashe ki , wallahi saina kasheki...... Yau bazaki sake guduwarmin ba , kafin yaje wurinta suka riƙeshi kuma shi baya so suna riƙeshi yana fassara riƙon da an maidashi wani sakarai tou da an riƙeshi shine yake ida firgicewa yayi ta fizge² yana zabura yana faɗar saina kashe..... Ina yake.......... Zaki faɗamin ko saina kashe ki , riƙe suke dashi sosai irin riƙon da sukayi mishi ya bashi damar yin tsalle daga jikinsu ya kai mata wani irin ɗimautaccen halbi tun a wurin tayi fitsari na farko , ƙara riƙeshi sukayi ya birkice , palo aka taho da ita , shi yasa da Sultana tace idan ka bari ta gudu saina faɗa masa , tou shi Ashiru shine ya kawota palon dan ayita ta ƙare.... G R A ya koma yana jiran isowar Al ' Ameen , amma har 12 na dare babu Al ' Ameen ba labarinshi domin Mardiyya ta mishi waya cewa Suwaiba tazo gidan karya dawo , kuma itace ta fita taje ta anso saƙo ta dawo shi kuma ya ɓace cikin gari abunshi da motar Jiddah , Dikko ganin Al ' Ameen bazai dawo ba yasa ya haƙura ya bar gidan kuma gashi zaiyi tafi idan Allah ya kaimu gobe amma idan harya kama Al ' Ameen na lahira saiya fishi jin daɗi , ita kuma Suwaiba a gabanta ya faɗa cewa idan har ta ƙi faɗar sunan mutumin nan injishi a ƙware mata fatar jikinta babu sauƙi , shi kuma yaron shi da yayi haɗari a wurin rijiya mai suminti an dawo dashi katsina yana asibiti , kuma Dikko yaje ya duba shi , saida ya gama abinda zaiyi a cikin gari ya nufi goruba....... Da ɓacin rai sosai ya dawo goruba , tuni Sultana ta manta da tayi bacci , ajiye ledojin daya shigo dasu yayi sannan ya cire kayan jikinshi daga shi sai short nicker ya matsa ya fara tashin Sultana daga bacci , baccinta yayi nisa dan haka ta sake gyara kwanciya ta rufe idonta , jawota yayi bakin gado , buɗe idona nayi cikin yanayin bacci , Dikko na gani tsaye daga shi sai gajeren wando , da sauri na rufe idona na sake buɗewa , ɗan buɗe bakinshi yayi kaɗan yaja iska da wani irin yanayi yace tashi na dawo yayi maganar cikin raɗa. Tare da matsawa wurin wayarshi da ake kiranshi , kai amma Dikko baida kunya in banda iskanci basai ya ɗaura zani ba sai kawai yazo ya tsaya haka ƙarere a gabana ko kunya bayaji , tsoki nayi tare da kauda kaina gefe ina kallonshi da wutsiyar idona , kunga bashi da ƙiba ko amma daya hunce yana da ƙirar ƙarfi irin nasu na masu ɗaga abun ƙarfi wanda suke motsa jikinsu , juyowa yayi ya zauna saman dressing mirrow inda ake jera kayan shafa yaci gaba da waya da turanci yana min wani irin kallo. Ta saman idona na kalleshi shima yaci gaba da kallona da yanayin ido zai raina fata , yanayin kallon da yayi min yasa naji zuciyata ta karaya tsoro ya kamani lokaci guda jikina ya fara kyarma da sauri na sauko daga saman gado a tsorace nazo kusa dashi nace na bari , riƙoni yayi da ɗayan hannushi wanda baya waya dashi ya nunamin irin kofin ranar nan da idonshi , kallonshi nayi yayi min irin murmushin da nayi mishi a mota shima ya ɗagamin gira kamar yadda nayi masa , Zanyi magana ya rufemin baki da hannushi yaci gaba da magana a waya da idonshi ya nuna karkimin kuka , cire hannunshi nayi na koma saman gado na kwanta , har na samu damar komawa bacci bai gama wayar ba , bayan ya gama wayar ya kashe wayoyinshi gaba ɗaya ya nufi inda take kwance ya sake tashinta yana cewa ai yau bacci bai ganki ba , bake mara kunya ba , an turke ka mahaukaci munafikin miji sai kuma wata kalma data daɗe tana zugar min zuciya da kika faɗa ma Umar wai ni Dikko nine zaki gauraya dani ? Tou ki tashi mu gauraya dani dake duk wanda ya raga ma wani shi ba ɗan Babanshi bane ba , badai kin rainani ba , tou na auroki mun zama ɗaya bana so ki tausayin min kuma idan kin ragamin baki haɗu ba ƙaramar yarinya dake tashi ga kazar nan ga komai nan na kawo miki ki anshi daren farko da ƙoshi a wurina , Abinda ya wuce bai kamata ana dawowa dashi baya ba , ni nawa ɗabi'ar kenan dawo da anjima yanzu inajin farin ciki yayin dana ke zalintar wanda nafi ƙarfi nakanyi murmushi ko dariya yayin da wani yakeyin kuka ko yake cikin halin tashin hankali , nidai nasan aka share miki fili dani nafi ƙarfinki a saman gadon ma nine oga hannunshi ya kawo yana ƙoƙarin cire min kayan jikina yaci gaba da cewa ki tashi ki gyara gadon nan kamar yadda kika ga nayi a daren aurenmu idan kin gyara kuma kije ki rufe ƙofa zanyi wanka na shirya nahau saman gado na jiraki kizo ɗaukar fansar shekaru biyun da kike jiran zuwansu yau ga abun ɗaukar fansar a gabanki ba tare da shekarun sunzo ba , kinga kin rufe ɗaki babu wanda zaiji kuka na ba bare in saka ran mai kwaceni a hannunki sai kinji tausayina kin kyaleni. Ai ni na yafe maka , maƙale kafaɗarshi yayi cikin shagwaɓa yace ni ban yafe ba saifa an fitar da rainin nan yau hankalina zan kwanta zanyi tafiya ne shi yasa nake so ko a waya naji muryar gabana zai faɗi , kinga idan bana nan duk inda nake idan kika cemin Dikko kar kayi zan kiyaye saboda karki sake kulle ƙofa , a dai² lokacin daya buɗe ziff in rigata ya cireta daga jikina tare da saukoni daga saman gadon , na ƙwace da gudu na koma ina kuka , ke.......... Bana san wani kukan munafurci ba kinsan zaki gauraya dani ba kece ai kika faɗa da bakinki ba nine na matse bakin kika fada ba , nidai dan Allah bana san haka , cikin ɓacin rai yace sauko , Dikko dan girman Allah kayi haƙuri , na rantse da girman Allah bazanyi haƙuri ba yau sai kin gauraya dani , da nayi niyar ƙyaleki amma ɗazu da kikacemin munafukin miji shi yasa zakici kaza ki bada tukuici idan ba haka ba ni zan gauraya dake , ƙara fashewa nayi da kuka wurgomin makullin ɗakin yayi yace sauka ki kullo ƙofar , cikin kuka na sauka tare da ɗaukar hijabina , ki cireta tun kafin in sa ki sauke duk kayan jikinki , ajiyewa nayi zanja zani na sama yace ke........ Karfa ki bari na ɓaci. Juyawa nayi na kalleshi ya ɗauke kanshi gefe yana murmushi hannunshi a saman kofin , kulle ƙofar naje nayi na kawo mishi makullin yace kije ki ɓoye abunki inda bana iya ɗaukowa kar inji wahala in gudu , banyi magana ba na ajiye a gefenshi na gyara gadon , bayan na gama yace zo ki sha , cikin ɓacin rai naje na ɗauka na shanye yau ma kamar na ranar ne cikin kuka na riƙe Dikko nace ngode , cikin iskanci yace a , a yau ba'a nan zaki gode ba bari sai kinji yadda nake a wasan danbe. Juyani yayi na bashi baya ya kwantar da haɓarshi a saman kafaɗata yana sauke wani irin numfashi mai saukar da kasala ganin yadda na riƙe jikina yasa yayi wasa da gashin gemunshi a wuyana lokaci guda tsikar jikina ta mimmiƙe jikina yaci gaba da kyarma , cikin wata irin marainiyar murya yace ke kuma kazar auren naki da kuka zaki ci ? Banyi magana ba dan ina cikin yanayin damuwa ganin Dikko nake kamar bashi ba wallahi , ni duk abun a baƙunce yazo min ina hasko baya data wuce shi yasa nake kallon daren yau kamar a mafarki , duk ya zaneni da bulala mari halbi kuma yau zai kwanta dani. Shima bai sake magana ba ya jani zuwa toilet , tare mukayi wanka kuma har akayi wanka aka gama idona a rufe yake dan Dikko bashi da kunya ko na misali , saida yayi alwallah ya fita ya barni a toilet in nima nayi na fito, Nima dai kamar yadda yayi a daren farkon Sadiyya da Jiddah haka yayi a nawa , bayan mun gama ya miƙe tare da zare jallabiyar daya saka ya matsa jikin gadon yana cewa zoki nunamin yadda kike so na kasance , bara na baki satar ansa , mu ƙaddara wannan shine filin danbe an saka kuɗi masu yawa , dani dake mune "yan wasan kuma kowa yana jiran kowa sai aka haɗamu a wasa , da farko kafin ki shiga filin ki nemi albarka gado , sai ki hawo da ƙwarin guiwar ki , yadda ake wasan zaki riƙe kaina goshinki hanci zasuyi dai² da nawa , zakiyi magana da salon yarinta sai ki kalleni kallo ɗaya zakimin saiki rufe idonki ki fara tunano duk irin muguntar da kika iya ta yadda zakiyi nasara a kan abokin wasan naki , karki yadda ki faɗi idan kika bari na buga miki game over ta wannan hanyar zan riƙa horaki duk lokacin da kikayimin laifi , banza nayi banyi masa magana ba , yaci gaba da cewa daga lokacin na tashi daga Dikko zan koma ubangidanki a fagen jarumta , harararshi nayi cikin kuka ban masa magana ba har yanzu. Murmushi yayi cewa ba damuwa , ƙudi yayi kaɗan mu ƙaddara abun da kowa yana jiran kowa ni dake , nine nayi miki irin raini da kikayi min aka haɗamu a wasan wane irin duka zakimin idan kika kamani , har yanzu banyi magana ba kuka nakeyi cike da soyayya ya kalleni yace karki damu nine ɗan wasan ai , ba damuwa bara in sakoki a filin Allah yaba mai rabo sa'a ya ƙarasa maganar yana dawowa inda ya barni ya ɗaukeni ya ɗorani a saman filin wasa........ 20/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 79 Kifa kaina nayi saman katifa bayan ya saukeni a gado saboda kunya a raina kuwa ina jinjina girma da rashin kunyar Dikko , maganganun Yazeed ya fara dawomin sai kuma Inna da tace Dikko tantiri ne tunda kina so kin sama ga fili ga mai doki , wannan shine filin ni nice dokin kenan , zuciyata tace Allah sarki Sultana wallahi Dikko mugu ne.....! Birkitoni yayi yana kallona yace yau zakiji idan ni Dikkon banza ne , kece zaki ba kanki labari idan niɗin na wofi ne ? Kuma yau zaki sheda niɗin ɗan Babana ne domin da bakinki zaki sa musu albarka da suka haifoni suka baki ni kyauta yau zaki tabbatar da na haifu kuma ni ɗin ɗane hada gyara , ya ƙarasa maganar yanamin kallon da bana so........ Kayi haƙuri , albarkoki wallahi "yar mata , dan Allah 🙏🏻, sai inyi haƙuri in zama munafukin miji ? Umm ummm wallahi sai an fitar da raini kowa yasan matsayinshi , kayi haƙuri fa , wai in ƙyaleki ? Nama zama sakarai kenan , duk haɗashi da Allahn da nayi fur Dikko yace bayajin yaren da nake magana dashi , cikin ɓacin rai nace tou kar Allah ya baka haƙuri kayi duk zalincin dan na baka haƙuri sai kake ganin kamar inajin tsoron ka ne ? Dariya yayi tare da cewa ai nasan wannan bakin tsiwar bazaiyi shiru ba , tsorona kuma daga yanzu zai fara ziyartar zuciyarki ko a waya kikaji muryata sai kinyi ladabi bare kuma ki ganni kamar haka , ya ƙarasa maganar yana tuɓe zanin dake jikina , da sauri na dafe ƙirkijina na matse cinyoyina , yanzu baya ko murmushi yayi min wani irin kallo tare da cewa taso , Cikin ɓacin rai na tashi tare da rufe idona na matsa inda yake durƙushe , riƙe fuskata yayi yace buɗe idonki , fashewa nayi da kuka nace Dikko na bari don Allah , rungumeni yayi a jikinshi cikin wahalalliyar murya yace ba abinda kikayi min An mata da farko dai ina baki haƙuri kiyi ƙoƙarin ɗaukata kinji jarumata , ina da masifa jarabata bansan irinta ba , ni ban haɗa mace da komai ba bana neman mata kuma bana sabgarsu ban taɓa zina ba saida ƙaddara ya ratsa min a kanki hankalina bai kwanta ba saida na auroki na samu natsuwa , kiyi haƙuri akanki nasan daɗin mace dake na fara kuma akanki na iya , ni bana kallon iskance² amma duk wani logo na mata a tafin hannuna yake bana da sauƙi , mace kuma ni kaina tausayi take bani idan na riƙeta a gado bana ma mace kawaici haka kuma bana lallaɓata zanyi ƙoƙari na murje shekaruna kafin su sauka dan wata rana inaji ina kallon mace bana iya mata komai , yanzu ko inajin ƙuruciyata ina da lafiya babu inda yakemin ciwo a jikina jini babu inda baya halbawa yaudai ina miki sannu da jiki ɗaukar fansa ko soyayya ? Shiru nayi naci gaba da kuka , bana san kuka bana san yagushi sannan bana san magiya duk idan kikayi zan ida warwarewa gaba ɗayana , kalli agogo , ƙin kalla nayi naci gaba da kuka , yace tou yanzu 1 saura kwata kinga dare ne karkiyi kuka da ƙarfi kindai san kin kulle ƙofa da makulli ya ƙarasa maganar yana latse gefe da gefen kumatuna da yatsunshi na buɗe bakina da sauri saboda zafi. Dariya yayi tare da yin irin maganata yace Dikko mugu ya ƙarasa maganar yana haɗe bakina da nashi daga durƙushen ya fara hawa jikina yana sakin ƙarfinshi , a hankali nake tafiya ina sauka yana ƙara sakin nauhinshi har na kwanta saman gadon ya kwanta saman jikina sosai yana fitar da wani irin numfashi daga hancinshi mai sa jiki ya zama matacce , bakinshi a nawa yace ke buɗe idonki idan bana kalloki taya zan samu natsuwa , Buɗe idona nayi ganin Dikko a wani irin yanayi yasa na firgice , murmushi yayi tare da cewa idan kika sake rufe idon nan ke zaki nemeni wallahi kinji dai na rantse ya ƙarasa maganar yana ɗaure fuska yaci gaba da cewa ki kalleni da kyau kema ki koya , ƙara tura bakinshi yayi sosai a bakina yadda ko maƙoshina bana iya haɗawa nunfashina ya fara sama , ɗagamin gira yayi tare da dafe kaina cikin wani irin salo yaci gaba da sumbatata yana lumshe idanuwa , duk inda yasan idan ya shafo a jikina zai firgitani saida ya bashi haƙƙinshi cikin salo mai wahalar gogewa a zuciya motsin kirki na kasayi nakai matakin da nake buƙatar a fara buga wasan , haka Dikko yaita ranfa dani kamar mage ta kamo ɓeran daya bata wahala , kunsan sai ta gama wasa dashi ta bashi wahala ya suma ya dawo sannan take cinye abunta.... Saida ya gama ɗimautani sosai ya murgina ƙasa na koma samanshi yana sauke wani irin numfashi kamar wanda yasha gudu ya gaji , hannu na ya kamo nasan inda zai kaishi dan haka da sauri na rufeshi , dakel yayi dariya kaɗan yace misali idan nace bazanyi danbe ba a wannan yanayi ya zakiji ne ? Gabana naji ya faɗi a zuciyata nace daka ɗauki alhakina , jijjigani yayi ke bakiji na ne ? Idan kina so nayi sai kince don Allah kayi idan bakayi danbe ba zan mutu a shagwaɓe nake so da irin wannan kallon ya nunamin , idan ba haka ba yanzun nan zan saukeki daga saman gadon nan inyi bacci , yana faɗin haka ya juyamin baya ya lulluɓe da bargo tare da rufe idanuwan shi, Fashewa nayi da kuka nace Dikko wai miye haka don Allah , ba tare daya juyo ba yace ba kuka zakiyi ba sai kin faɗa zanyi idan ba haka ba yau saida kiyi kwanan haƙuri dan na gaji ya ƙarasa maganar yana yaye bargon ya ajiye a gefe ɗaya yace kallarni fa , da sauri na kauda kaina gefe ɗaya ni kaɗai nasan abinda na gani , to kin huta yayi maganar tare da sake jan bargon zai rufe jikinshi , riƙe bargon nayi kallon raini hankali yayi min yace kina so ne ? A kunyance na ɗaga kaina , to zo ki rumgumeni sai ki faɗamin , kwanciya nayi a saman jikinshi jikina yana kyarma na nace don kayi haƙuri idan bakayi danbe ba zan mutu na faɗa a shagwaɓe kamar yadda ya nunamin da irin kallon daya gwadamin nayi mishi , riƙeni yayi a jikinshi yace fa'idar neman miji mutunci ne , ke kina ƙarawa kanki daraja da martaba a zuciyarshi , babu girman kai ko nuna kafi wani yayin da kake kwance da iyalinka , kuɗi mulki ko saurata duk basa aiki a dai² irin wannan lokacin kar kiyi tunanin nine zan riƙa nemanki daga yau kinajina ko ? Eh , kuma kullum idan ina nan banaso ki ragwantamin ko alwallah nayi ki bada himma ki warwareta naji zan canja wata , ina sanki ne so adadin yadda bazaki iya ganewa ba bana so wata mace ta fiki martaba a zuciyata ta fanni iya karemin haƙƙina a nan ida har tafi ki nan tasha dake , ki riƙe akalata sosai idan kuma kika kasa zan ƙara aure ne kawai tunda na lura duk lusaran mata natattara a gdan , ke ɗinma da nake tunani gara ke tun ban taɓaki ba kin ɓare baki kina mani kuka da wata ƙyarmar banza , tsoki yayi tare da nunamin yadda zanyi masa nidai baƙuwar maza ce iskanci nawa a baki yake , har yanzu jikina bai daina kyarma ba gaba ɗaya kunya ta dameni na ƙagara aje filin yaƙi dan inji irin tashi jarumtar. Ya gane abunda nake nufi sarai amma dake ɗan iska ne sai ya basar yaci gaba da wani luguidani , kai wallahi Dikko kwallon ɗan iska ne , lokaci² yakanyi murmushi sai kuma ya ɗaure fuska yayi min kallonshi mai tsayawa a rai , can ya gaji yace tunda a haka za'a tsaya sauka ki ɗaukomin kayana , girgiza kaina nayi alamar a , a , tou ai naga karatun yaƙi gaba An mata , a , a ɗagoni yayi daga gefenshi da nake kwance sama ya ɗagani daga kwance har saitin cikinshi , da ƙafa ɗaya ya buɗe ƙafa ɗaya tawa bayan yayi addu'a ya sakoni a saman alƙalaminshi da ƙarfi ya shigar dani , wani irin ihu nayi shi komai nasa sai yayi cuta , jifa yadda ya shigar dani da ƙarfin tsiya babu imani ba zaibi sannu ba kuma yanaji ana dakatar dashi , ke rufemin baki ba kece kikace inyi miki ba muje , cikin kuka nace wai miye haka ? Ni bance miye ba saike dan baki da kunya ci gaba da nushi lokacin ki ya fara.... Ƙasa motsi nayi sai kuka nakeyi dan azaba ji nake kamar zan mutu wallahi , idonshi yana kan agogo ni kuma ina kwance a ƙirjinshi ina kuka , shafa bayana yayi yace karfa ki manta a filin wasa ake yayi maganar yana ƙoƙarin ɗagani na ƙara komawa na kwanta kamar wata doluwa , da hannunshi yasa dan ɗagani na ƙara komawa na kwanta yace munafukin miji fa , iyakar turkewar kenan ? Murmushi yayi tare da cewa lokacin ka ya fara Dikko. Birkicewa yayi tare da jawo ƙafafuwana ya ɗora saman kafaɗarshi yayi min runfa da ƙirjinshi hannunwan shi ya ajiye gefe da gefe na sannan ya kalleni yace , nasan zakiyi ji mamaki ina magana da yarenki ko ? Tou ni bana sauƙaƙawa gaba duk ƙarantar ta haka kuma bana san raini duk wanda ya rainani saina sa ya raina kansa , Tun ranar da kika faɗamin zaki ɗauki fansa shekaru biyu hankalina bai kwanta ba saida na tabbatar duk wani logo na fulani na kamo tasharshi , ba'a fini iya mugunta ba amma ina da yafiya , nakan manta da ɓacin rai na fuskanci rayuwar gaba kuma haka na faɗa miki a ke a dole shekara biyu zaki ɗauki fansa ga abin ɗaukar fansar kin gagara ramawa , kinyi maganganu akaina marasa daɗi amma kamar yadda kikace abinda ya wuce bashi da kyau dawo dashi baya na barshi amma sai nayi hukunci hada marin da kikayi min wallahi. Daga haka yaci gaba dakai nushi kaɗan² , har yanzu ban dainajin azabar saukar dani da yayi a alƙalamin da ƙeta ba , cikin kuka nace Dikko da zafi fa , Ey amma ai nushin yana da daɗi ki ɓoye hawayenki kila zasuyi miki amfani anjima yanzu sharar bage aka fara gyara kwanciya ki anshi hukunci , a wannan rana na raina kaina nayi ihu nayi kuka har muryata ta shaƙe nayi yagi Allah ya isa ban yafe ba na faɗa bansan adadi ba , a zuciyata kuwa ina tunani Alhaji mai gidan "yan ci baimin irin wannan muguntar ba , Dikko yace duk Allah ya isa ɗaya saina ƙara mata muntuna 20 akan duk awa ɗayar da zanyi , kuma idan kika sake yagushina saina rama baki fini haƙora ba bara ki sake cizo na kiga yadda zanyi dake saboda ba'a cizo ba'a yagushi a danbe ki bada himma kiyi nasara lokaci yana tafiya miki idan nayi nasara akan ki ƙaryarki ta ƙare.... Dole na haƙura na ƙyaleshi , a hankali yake tafiya yana ƙara murza totir lokaci yana tafiya yana ƙara yawan gudunshi a haka har ya warware gaba ɗayanshi , ya manta da ƙarantar da yake tausayi ya neman hanyar da zai sama ma kanshi natsuwa ya ƙanƙameni , wani irin kukan kissa yakeyi Dikko mai daɗin sauti da ratsa zuciya mai wahalar mantuwa a rayuwa , a hankali yake fitar da sautin kukan cikin sagwaɓa Dikko baijin magana wallahi jarumin namiji ne a fagen daga da iya jan linzamin mace a filin wasan danbe , lumshe idona nayi cikin wahala a raina nace tabbas babu mai irin jarumtarshi a mazan bariki Jiddah , ɗaya kawai na ɗana nasu wato Alhaji bansan yadda suke ba amma sai sun haɗa da "yan dabaru , duk namijin da baya iya sauke haƙƙin iyalinshi ya zama lusarin miji a wurin mace kuma ta samu kafar rainashi idan ba'ayi dan mai gona ba anyi da mai gayya , idan bata raga maka ta wani wurin ba tabbas zata martabaka da ƙoƙarin kare martabarta da kayi a fannin kare haƙƙin aure , ɓanɓare Dikko na farayi yi dan na kusa ɗaukewa , da sauri ya ƙara riƙeni a shagwaɓe yace wayyo ya faɗa tare da ƙarayi min kyakkyawan riƙo wai , wai Allahna a , a An matana ƙyaleni , ki ƙyaleni....... Ya zalinceni iya zalinci ya cuceni ya nuna fin karfi yadda yayi min alƙawarin saiya sumar dani dan na kiyayeshi na gane shi ba sa'ar wasa na bane ya turani suma naje na dawo kuma tabbas tsoranshi ya shiga zuciyata kamar yadda yayi alƙawai , nayi kuka na bashi haƙuri amma saida ya tabbatar yayimin lullusar kece raini ya barni bayan yasa nayi masa godiya da addu'a Allah ya ƙara mishi lafiya a fagen filin wasa yayi ta nasara a wasan danbe , Yayi amfani da ƙarfinshi ya bani wahala ya zagaya a wasan farko kuma an faɗar dani , na biyu ma shine yayi nasara a na 3 akayimin game over 3/0 wasa ya ƙare kuma Dikko ya rainani daga yau kuma har zuwa wannan lokacin ban daina kuka ba dan ƙetar da yayi min , bai sake bi takaina ba yaci gaba sabgar gabanshi ko kallo na ba sakeyi ba , bayan ya tsarkake jikinshi ya saka jallabiyarshi ya ɗauki wayoyinshi da makullin mota ya tun kari hanyar fita , Ina zakaje ? Na tambayeshi , bai kalleni ba ya juya yace Al ' Ameen nake nema nasan yanzu ya gama iskancin guje²nshi ya dawo , nifa tsoro nakeji gaskiya , cikin masifa yace kije kiyi ta jin tsoron ke baki da kunya ma ni zaki faɗa ma tsoro ya ƙarasa maganar yana min wata irin harara gabana naji ya faɗi , da sauri na komar da kaina na kwanta , tsoki yayi tare da buɗe ɗakiya fice cikin ɓacin rai. Saida na tabbatar ya fita na sauka gado a gajiye ina gunguni cewa ɗan masifa tsakar daren ma ba'a hutawa da fitina Allah ya baka lafiya , Ina shiga toilet in na tunkari inda naga ya tara ruwa tare da tara hannuna ruwan zafi ne tsoki nayi tare da tsugunawa dan toilet in bashi da kwamin wanka kuma ba cikin ainahin gidanshi bane inda ya siya ne wurin ne kaɗai ba'a rusa ba gidan maƙota kenan. Cikin ƙanƙanin lokaci ya isa G R A ko tsoron dare bayayi tunda ya tafi ranshi yake ɓace harya isa da wani irin tuƙuƙin fushin ci ma Al ' Ameen mutunci ya isa har yanzu bashi gidan motar daya fita da ita itama bai dawo da ita ba , ɗakin Jiddah ya nufa gaba ɗayansu daga ita har Mardiyya suna bacci saida ya gama kallesu tsaf sannan ya kashe hasken fitilar yaja ƙofa ya nufi ɗakin Sultana... Sauke katifar gadon yayi tare da buɗe plow bed in duk abinda yake san gani babu , tsoki yayi tare da maida katifar ya nufi wadrof duk saida ya zubar da kayan ciki akwatinan lefenta ma haka ya zazzagesu ƙasa yaita janye²n kaya babu wani damuwa , palo ya koma nan ma babu wani sheda duk kayan daya zubar bai maida ba , Allah ya sawaƙe wahala ya faɗa tare da fita daga ɗakin. Koda na fito daga toilet a gaban gado na durƙusa rabin jikina a saman gado naci gaba da baccin wahala , bacci yana ɗaukata na ganshi a gabana yana saina kwakwale idonki , a tsora ce nace wai mene ne damuwar ? Ka fita hanyata meye nasaba na dakai kullum ka kwakwale , me Nana tayi maka ka kwakwale idonta ? Me Aunty Mamy tayi maka ka kwakwale ? Kuma me yasa daka cire ake mutuwa ? Ansa zan baki ko kina so na fita rayuwarki ? Eh ka fita hanyata , tou ina wayar da kikayi min record , Dikko ya cire m card , idan har Dikko ya baki record in nan nayi miki alƙawari zan nuna miki inda aka binne asirin da akayi mishi , wani mutum ne yazo ya kamashi da kokowa yace idan ka faɗa saina kashe ka , kai ku riƙota karku bari ta gudu , wayyo na kwarara ihu tare da miƙewa a firgice a dai² lokacin da Dikko ya shigo , dakamin tsawa yayi wai wannan koken banzar ni ya fara isata , wuce kije ki kwanta , zanyi magana yace ki wuce nace bana san iskanci da Allah , fashewa nayi da kuka , yace mizanate , wai zai zaneni , ƙyaleshi nayi naje na kwanta ban daɗe da kwanciya ba na tafi bacci dan duk jikina wani irin ciwo yakemin. Dikko kuwa gefen gado ya zauna yana latse² a waya , bayan wani lokaci kuma ya juya ya tsare An mata da kallo tana sauke ajiyar zuciya lokaci² ta kuka , murmushi yayi kaɗan yace An mata rigima ubangiji ya zaunar damu lafiya ya kare mana fitina Allah ya ƙara ninka miki soyayya ta fiye da wadda nake miki kunji irin san kan nashi fa. Yau ko bacci ɗaya Dikko baiyi ba yana zaune duk abun duniya ya dameshe har lokacin sallah asuba yayi , da zai fita masallaci ya tashi Sultana ya wuce , ina gama sallah na kwanta a wurin na ci gaba da bacci , 6:33am ya dawo kuma a lokacin muka bar goruba , a mota nake tambayarshi memory yace baisan ina yake ba , zan sake magana yace nayi masa shiru yanajin ɓacin rai , shiru nayi ban sake magana ba , shi kuma yaci gaba da lissafin tafiyarshi a zuciyarshi. Zasuyi hannun riga da Momy zai fita katsina a daren yau su kuma zasu bayyana a gobe idan Allah ya kaimu har suka isa gida da abinda Dikko yake saƙawa kuma yake warwarewa , har ɗaki Dikko ya rakani kuma har yanzu Jiddah basu ma san gari ya waye ba amma gaba ɗaya duk wani ma'aikaci dake gidan maza da mata kowa ya tashi ya kama hidimar gabanshi , gidan cike kamar ana wata hidima saboda babu wanda ba'a gidan yake zama ba idan dai har a gidan yake aiki , ƙaton gida ne sosai saboda yafi gidan goruba girma bama a haɗawa kowa da ɗakinshi palo bedroom da toilet akwai masu dafa abinci a saman icce can bayan gidan a manya tukwane a cidasu kuma a basu albashi , ko ɗan uwa gareka ka kawoshi shidai Dikko babu abinda ya dameshi amma saboda fitinar Jiddah wai nice zan tashi nayi musu girki , suna fa cin daɗi domin abinci da nama baka isa ka raina ba gaskiya Dikko yana da cikar arziƙi ubangiji ya ƙara rufa asiri. A harmitse na samu ɗakina kallo ɗaya nayi masa na nufi gado , Dikko yace a haka zaki kwanta kina ganin ɗaki a haukace , ban masa magana ba na haye gado saida na kwanta nace wanda ya ɓata zaizo ya gyara , da fushi ya nufoni na sauka gado da sauri kafin iso na nufi inda kayan suke na fara tattarawa ina kuka , dama kin bari na sameki a kwance......... Yana faɗin haka ya fita yana faɗa , ɗakinshi ya nufa danyin wanka , saida na gyara ɗakin nan tas na shareshi na goge sannan na kwanta naci gaba da bacci. Tunda ya fita sai bayan la'asar ya dawo tare da Nabeela , nima tuni nasha baccina na tashi nayi wanka na kame mutuncina cikin riga da zani na atamfa , yau Jiddah ita kuma fitina take ji tunda na fita take sunkuyawa iyayena zagi amma ban tanka mata ba sai Dikko baya nan zanci uwarta kafin ya dawo , tou ashe bani ɗaya ba har Dikko bata raga mishi kina jiyo hayaniyarta tana masa rashin kunya , ran Nabeela idan yayi dubu ya ɓaci kamar Yaya DK Jiddah kema rashin kunya wallahi ta sire mata kamar fitar tusar safe. A palon ƙasa yabar Nabeela yazo ɗakina cikin sauri² yace zo ki gani , tashi nayi naje wurinshi nima na ɗaure fuska kamar yadda naga yayi , murmushi yayi ba tare daya kalleni ba hankalinshi a kan takaddar yace yau an raba an fitar da haƙƙin kowa , an bawa shi mijin ƙawar Momy na ɗakinsu domin alƙalin haka yayi rabo ɗaki² , na ɗakin su Baba aka bada shi wa wannan mutumin da yayi ƙararki , nasa an rabasu aka fitar dana gidanku kuma za'a ciccira su a fitar da kowa kema An mata da Allah ki yafe musu kuɗin nan yayi maganar yana kallona da damuwa kalli kiga ya nuna takaddar yana gwadamin yadda rabon gadon ya kasance , An fitar dana Kakarsu Hafsa ita da tayi takaba aka sake kasawa aka fitar dana ɗakinsu Dady saina ɗakin su Baba , an raba aka fitar wa da Baba ƙarami nashi gidanku yara 61 da mata 3 ni tafiya zanyi idan sun gama kasanfinsu sa ajiye miki naki ya ƙarasa maganar yana jawoni jikinshi , riƙe kafaɗarshi nayi da hannun dama na tare da kwantar da kaina a jikinshi. Ni zan tafi ga Nabeela nan na taho miki da ita ta tayaki zama kema ki samu mai ebe miki kewa , bana san faɗa karki kuskura ki biyewa Jiddah kuyi faɗa kinji ko ? Nace tou , zan baki makullin mota kuma bana san yawo mara amfani na yaddar miki da izinina ki fita duk lokacin da buƙatar fitar yazo , shiru nayi banyi magana ba , ɗagoni yayi daga jikinshi yace a wl'a a yetti , tou baki ce kin gode ba , cike da damuwa nace miyyetti. Shima da yanayin damuwa yace , midillidai e maraicimada , tomi tunitake emada minanai beldun wala miwonda e mada miwadai katunanimada kullum , jemmare keya idewdi mahimmanci sosai to a han idan tunitida jemmare keyah e dume ittata kewamada ? Abinda yace wai zan tafi da maraicinki , idan na tunaki zanji babu daɗi bama tare zanyi ta tunaninki kullum , daren jiya yana da muhimmanci sosai a wurina idan kika tuna daren jiya da me zaki ibe kewa ? Fashe wa nayi da kuka tare da sake komawa jikinshi na kwanta ina hawaye , dariya yayi sosai tare da saukeni daga jikinshi yace inzo muje ɗakinshi yayi gaba nabi bayanshi ina kuka. Jiddah kuwa sai babbaka uwar ashariya takeyi bansan abinda akayi mata ba , Nabeela kuwa ɗakina tasa aka sauke mata kayanta bayan Dikko ya woner ta cewa idan ta kuskura An mata tace tayi mata wani abu ko taji wahalar zama da ita ko tayi baƙin ciki uwa uba tayi kuka zai kasheta ne ba ruwanshi , gabanta sai faɗuwa yakeyi ya wannan zaman zai kaya ne......... ? Muna shiga ɗakin ya bani makulli wai in kulle ƙofa , zan ruga ya riƙoni cike da damuwa yace haba An mata , na Allah kiyaye fa zaki bani yi haƙuri don Allah yanayin maganar cikin nuna haɗama da zaƙuwa , zanyi magana yace yi haƙuri haba An matana Dikkonki fa cikin lallashi yakeyin maganar idonshi ya canja launi zuwa kalar jaraba , nidai don Allah ka ƙyaleni , cikin ɓacin rai yace bana san yawan magana zaki yi da arziƙi ko in danneki in kwata ta ƙarfi da yaji ne , a , a me yakai ta ƙarfi , to anshi , makullin ya bani yace rufe ƙofa cikin kuka naje na kulle ƙofar na dawo , bargo ya shimfaɗa a ƙasa yace jirani ina zuwa , wurin firij ya matsa ya fiddo wani ɗan madaidaicin galan ya zubo wani abu a kofi ya taho gabana ya durƙusa tare da zaunar dani yace tou sha , yana kai min kofin a bakina , wannan miye ? Da Allah sha malama kina ɓatamin lokaci , nidai kullum saina sha fa , Eyyy yauɗin ma zakisha idan ba haka ba zan ɗura mikishi ne ta hanci bata baki ba , one , two , three , tsaya zan sha , tou sha , ansar kofin nayi daga hannunshi nakai bakina miƙewa yayi ya fara kwance belt inshi....... Shegiya butulu tsinanniya butulal cin amana kamar karuwar data zauna a garin legos aka zazzabga mata bulala , dariya Suwaiba tayi tare da cewa ko zaku kasheni bazan faɗa ba , ni har kun nunamin iskanci nida naci tsaye a gefen hanya nake miƙewa a bani tukuici ba'a katsina ba saida na tsalleke jahohi da dama naje iskanci daga ƙarshe na tare a ƙarƙashin gada can legos kaga kuwa rashin kunya ta tafi duk yadda kuke tunani , Ashiru yace ku barta mai gida zanje in ɗauko yanzu yana faɗin haka ya juya Suwaiba tace Ashiru kar muyi haka dakai zan faɗa ko saurarenta baiyi ba ya fice , Suwaiba ta darkaka wani irin ihu mai tada hankali tasan Dikko hankali wala..... Daƙel na dawo ɗakina da bargon da Dikko ya kwanta dani a samanshi , ya bani makullin ɗakin goruba wai idan na samu lokaci inje in gyara ɗakin sai makullin mota da kuɗi , Nabeela na gani zaune a palona sallama nayi na wuce ciki ina kuka , tasowa tayi ta biyoni matar Yaya me akayi miki ne , banyi mata magana ba na hau saman gado na kwanta tare da tura fuskata a bargon naci gaba da kuka , gefena ta zauna wai inyi haƙuri idan naji babu daɗi kuma me akayi min nake kuka , maganar Dikko naji a palona dashi da Jiddah yana cewa bari in anso in baki ni An mata bazata biye miki ba , kuma idan tayi miki wani abu wanda bai miki daɗi ba ki faɗamin zan rama miki , ni nafi ƙarfin in faɗawa miji ya kare min faɗa saidai inci uwar yarinya , tou ni kuma kika taɓata zakiji da ɗaci. A tare suka shigo yace An mata ina makullin motar dana baki , ba tare da nayi magana ba ko na ɗago na miƙa mishi , ansa yayi yace gashi na kashe fitina , ke An mata anshi na mota ta , wallahi bazata hau motarka ba saida ta anshi ta hannun Al ' Ameen dole , Dikko yace na rantse da girma Allah baza ta hau motar nan ba yadda tayi gwanjonta wa ke ta gama da ita har abadan duniya bata maimaici da mota tunda tana da ni , ai itace take hawan ta tun farko ka mayar mata kayarta , bazan mayar ba kuma yanzu bata hawanta , tou saidai ta fasa fita sai ta zauna harsai ka dawo , sai ta fasa uzirinta saboda bana nan ? Sai ta fita inda ranta yake so idan ke kike aurenta sai in gani , ba abinda ya dameni wata mota ce dai bata isa ta hau gidan nan ba saita hannun Al ' Ameen danma ta samu an bata motar a gidan ubanta ai a nepep take zuwa duk inda take zuwa , gidan mijinta ne yadda na saka sadaki na auroki haka na biya na aurota , nan ba gidan Babanta bane gidan Dikko ne kuma Dikko bazai bar matarshi tayi yawo a nepep ba wasu ma sunyi rawa bare ɗan makaɗi hannuna ya riƙe tare da cewa kiyi amfani da wannan motar kafin in dawo idan kuma kika bari ta anshi makullin ta baki motar Al ' Ameen zasu kaiki su baroki. Yana faɗin haka ya fice , Nabeela da Jiddah suka bi bayanshi dan rakiya nidai banje ba , Jiddah bansan abinda ya firgita ta ba , saida suka dawo daga rakiya Nabeela ta wuto ɗakina , Jiddah kuma sai ɓaɓɓarka zagi takeyi saita kamu sunan Dikko ta luƙaƙa mishi zagi , wai gidan Dikko shine auren ƙaddara tana da saurayinta wanda yafi Dikko komai akaje aka cuci rayuwarta ana "yar murya da yanzu tana can ƙasar waje tana rayuwarta mai daɗi , sai ta kashe auren Dikko marar zuciya nace ya sakeni ɗan jaraba mayen mata yaƙi ya sakeni , Nabeela ta fita da gudu tace ke jaka har kin isa ki kira auren Yaya ƙaddara sakarar banza jaka dake , wace ce ke ? Ƙazamar banza bakisan halinshi ba ne amma idan kika sake zaginshi uwarki zanci ɗanyaɗanyarta bazan gasa ba , masifa ta cakuɗe tsakanin Nabeela da Jiddah sukayi ta masanyar kalamai nidai ban fita ba saboda sunfi kusa tunda da Maman Dikko da Maman Jiddah uwarsu ɗaya ubansu ɗaya ni ina ruwana ? Duk wannan faɗan Mardiyya saida tayi musu video ta turawa Dikko , Nabeela ta dawo ɗaki tana ta zage² ni lokacin ma har na fito wanka ko inda take ban kalla ba dan abinda na lura yarinyar bata da kunya ko na misali , kayana na saka na fita dan sama ma cikina abinda zanci. Bayan sati 3 Gaba ɗaya yanzu Sultana ta kwanta ta samu wata irin natsuwa ta musamman ta rage rawar kai domin an kammala saukar da akayi mata dan warware sihirin da Bello yayi akanta , yanzu zuciyarta ta natsuwa ta daina bata umarni akan muguwar ɗabi'a sai shakkun Dikko da takeji ko waya ya kirata a ɗaɗɗare takeyin waya dashi bata sakin jiki kamar can baya duk bayajin daɗin hakan. Momy ta dawo , a ranar data dawo ranar tazo gidanmu ta yalyaɗa ruwan rashin mutunci ta zageni tai mani gori ta mareni tai mani ƙwanya kuma tace tana nan tana jiran dawowar Dikko ko zai mutu saiya sakeni ai dan yasan zata dawo shi yasa yabar ƙasar , tafa zuba ruwan rashin mutunci na wuce misali haka Jiddah kuma tasa an ƙwace makullin motar Dikko an bani na wanda Al ' Ameen ke hawa , Umar kuma ya buga ya faɗa mishi ya kirani yace kar in sake in hau motar nan idan zanje wani wuri in faɗa masa zai turo akaini , A ɓangaren Inna har yanzu bata nemeni ba , kuma ni bansan number da take amfani dashi ba a can india , ƙawayenta dai sukan zagayoni lokaci² kuma suma wai basu da number Inna , Zama na da Nabeela banajin wata damuwa zata dai shata surutunta iya iyawarta banda lokacinta danni bana fira da yarinya gudun raini ta raina mutane "yar iska ce ta gaban jarida , bata da kunya yarinyar kwata² danni ko wuri ɗaya bana kwanciya da ita dan nasan tana zaune dani kuma tana karatun rayuwata ne shi yasa nake kiyayewa dan nasan banda haƙuri. Yazeed ya kirani kuma yace min yana san gani na wai zamuyi magana mai muhimmanci duk abinda nake nayi ƙoƙari mu haɗu gobe , nace masa zan duba, A ɓangaren Bello yana so yayi wani abu amma bashi da wadatacciyar lafiya dan tunda suka fita daga hannun Dikko gaba ɗayansu basajin daɗi ta lafiyarsu sukeyi a halin yanzu bana gabansu ! Hmmmm a daren yau ƙawayen Jiddah suka bayyana a gidan..... Dan sunso zuwa tuni Jiddah ta dakatar dasu wai sai Dikko baya nan , to sunji ya tafi sun zo kuma kowa ta ɗuro iskanci cike da kanta sun taho.......... 22/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 80 *_TASHAR TSAKAR GIDA , AN GAISHE DA MADUGUN SHIRI UMAR MAI SANYI..._* Wata irin shewa sukeyi tasu ta matan tasha , gaba ɗaya sun haukata gidan da hayani suna ta nuna yadda sukayi maraicin junansu , bayan sun gama murnar haɗuwarsu kuma suka runguɗa sukayo kicin ɗina cike da gadara da nuna isa kamar irin gidan baban nan nasu. Ina tsaye ina ɓare magi suka shigo dan na daina cin abincin gidan kwata² saboda duk idan na ci sai naji tashin zuciya sai nayi amai hankalina yake natsuwa shi yasa na zage nake girkawa da taimakon Nabeela. Ko inda suke ban kallah ba naci gaba da abinda ya shafeni tunda nasan iskanci ne ya kawo su dan bama kicin ɗaya da Jiddah kowa da nashi , Nabeela tana zaune gefe saman kujera tana waya da ƙawarta suka faɗo tare da fara buɗe² , ke Mardiyya ƙara ruwa ki ƙara yawan magi ki zuba shinkafa bama cin kuskus naci uwar kuskus naci uwar mai dafa kuskus ɗin yarinya tayi magana in shaƙe mata wuyan uwa , duk inji Jiddah fa, Hahaha suka gaggaɓe da dariya gaba ɗayansu tare da kashewa aka rangaɗa guda cikin iskanci , wacce tayi hoto dani tace yarinya kuma tace uhum taga yadda zamu naɗa mata shegen duka a gidan nan idan kin isa ki kalleni koda motsin kirki kiga yadda zamu ci uwar ɗiyar ɗan wasan caca , suka sake sheƙewa da dariya a dai² lokacin da Mardiyya zata zuba ruwa a tukunya , Jiddah kuma ta kwashe magin gabana tana cewa babu fa a gidan ubanta amma dan wani kilbibi hada wani zuba magi sai kace an saba ci a gida , wacce tayi hoto dani tace tsoho harya karci ƙasa baya gane testing in magi baya gane gishiri , Mardiyya tace taya kuwa zai gane bayan baki ya mutu da giya anzo nan za'a nuna mana ƙaryar rashin kunya dama ɗan talaka bai iya samun wuri ba , kashe waya Nabeela tayi tace ke ya zaki ƙara mana ruwa bayan kinga muna sauri shi yasa muke dafa abu mai sauƙi , kallona tayi sannan taci gaba da cewa matar Yaya ya kina kallonsu bazakiyi wani abu ba ? Kinfa san inajin yunwa a gabanki zaki bari a dawo mana aiki baya..... Ke karki zuba ruwan nan , Jiddah tace zuba , Nabeela tace idan ko kika zuba su za'a samu matsala , ansar ruwan Jiddah tayi tare da zubawa tace ni na zuba "yar gadon rashin kunya marasa ragowa , ni bana neman suna haka kuma bana neman gindin zama tare da Dikko bare a kaɗamin ganye , masu so asan dasu kuma suke so su zauna su haƙuri ya duba dan gudun kar a korasu a koma cin ƙanzo da garin kwali danni a gidan Babana ban rasa komai ba , hehehehe bafa garin kwali ba garin kwaki , Oh 🤦🏻‍♀kinsan abinda baka sani ba danni bansan da labarin gari ba saida na haɗu da Caca Yarinya tayi iskanci ta koma gidansu aje can aci gaba da cin abinda aka fi wayau dashi , Mardiyya tace sai Aliyu ya sake sakata a caca , Jiddah tace ni kuma zan siye gidan in ajiye karnuka tunda shi dawakai ya ajiye , cikin ɓacin rai Nabeela ta taso daga inda take itama dai "yar babbar bala'e ce ni kuma fita nayi daga cikin kicin ɗin cikin ɓacin rai , wani irin mari Nabeela ta zabga ma Jiddah tare da ɓaro ruwan daga saman gas cikin masifa tace shin ba nace karki zuba mana ba ? To zan sake zuba wasu idan akwai wata "yar ƙaramar mara kunya ta sake taɓawa taga idan ban ƙona mata fuska ba banzaye ƙazaman banza duk kun cika mana wuri da tsamin dauɗa. Jiddah tace ni kika mara ? Nabeela tace an mareki dan ita Nabeela ba Sultana ta shigar ma faɗa ba cikinta take ma yaƙi sake ɗora tukunyar tayi saman gas ta zuba wasu ruwan , itama Jiddah ta sake ebowa ta ƙara zubawa akan wanda Nabeela ta ɗora sannan ta yanka mata mari wai ta rama marinta , sake ɓare ruwan Nabeela tayi suka sake tashar magana zuwa harshen turanci kowa yana faɗawa ɗan uwanshi kalamai masu zafi daga baya kuma suka fara bige². Kokowa ta rikice tsakanin Jiddah da Nabeela tun a kicin har suka fito waje , Jiddah na cewa ke har kin isa kice muna tsamin dauɗa , Nabeela tace nafa sanki tun baki san abinda kike ba duk ƙaryar shafa turaren da saka suturar waye ya koya miki in ba ni ba ? Wato yanzu kin waye iskancin ki zai sauka a kaina ko ? Mutuncin da duk wani feleƙe ma nice na siya miki rigar mutunci a gidan auren idan na zare hannuna daga kanki kashin ki ya bushe dusar gero dake... Mardiyya kuwa komawa tayi daga gefe taci gaba da video , duk yadda akayi a raba faɗan ƙin rabuwa sukayi domin Nabeela tsatstsaga gareta itama kafiya kamar na Dikko kuma ƙarfi gareta dan duk ƙawayen Jiddah shigar mata sukayi , faɗa yayi nisa kuma Nabeela taƙi ta haƙura gashi sunyi mata taron dangi dole saida aka kira Babbar ɗakinsu Dikko wacce ke zaulayarshi tana cewa saida tayi aure aka haifeshi , itace tazo kuma ko ita Jiddah bata ragamawa ba saida ta zagate tasss ta uwa ta uba. Da mamaki ta kalli Jiddah tace ni kike zagi ? Na zageki dangi masifa ahalin rashin mutunci , bana tsoron uban kowa a cikinku duk wacce tayimin sai inci uwarta , haƙuri taba Jiddah tare da cewa ita Nabeela tazo su tafi , Nabeela tace bazata ko ina ba tunda bata jin tsoron kowa kuma idan ta sake ganin yarinya a kicin ɗin sai ta kunna mata wuta , tayi tsoki ta nufi kicin tana gunguni , Ina kwance ɗaki ta shigo taita zagina wai nice munafuka nazo da asiri dan na firgita Jiddah na hanata zaman lafiya da mijinta , saida ta zageni tas itama tayimin mari da ƙwanya ta tsitstsinen min albarka tayimin gori sannan ta tafi. Daga gidan Dikko G H ta wuce taje ta faɗawa Momy sai an miƙe tsaye da addu'a akan Jiddah yau taga aikin asiri dan tunda take da Jiddah tun kafin asan zata auri Dikko tana ganin mutuncinta kuma tana darata ta amma yau saboda aikin asiri ita Jiddah ta zaga wai mune dangi masifa ahalin rashin mutunci bata tsoron uban kowa a cikinmu duk wacce tayi mata sai taci uwar yarinya , Momy ki duba lamarin nan fa duk da dai niɗin ina da zaulaya ina shiga sabgar yara amma ko Dikko da nake masa hawan ƙawara ina masa abinda bayajin daɗi duk rashin mutunci sa yana ɗagamin ƙafa ni Jiddah ta zaga ? Gaskiya Momy kija linzamin abun tun wuri idan har kika bari Dikko yasan halin da ake ciki zaije yayi abinda bai kamata ba idan ya dakar musu "ya ko ya saketa zuminchie zai lalace , ya saki wannan karuwar tun abun nan ana iya dakatar dashi kafin yakai fagen da bakya iya tsawatawa , Momy tace taje zatayi magana da Dikko kuma zatayi magana da Jiddah. Mardiyya ta turama Dikko video n faɗa ya gani amma baiyi magana ba kuma bai kira Nabeela ba nima daya kirani ban ɗauka ba , ya kira har ya gaji ya daina kira dan kanshi. Mardiyya ita ta dafa abinci wa su Jiddah kuma haka ta barbaɗe shi tas da asiri takai ma kidahumar ta lashe , ni kam kafin Nabeela ta gama ta dawo har nayi bacci tsabar ɓacin rai...... Haka dai nake dogara rayuwar gidan Dikko babu daɗi tsakanina da "yan uwanshi sai kyara sai hantara ga gori basa so na ko kaɗan , Momy kuwa sai bawa Jiddah shawara takeyi tana ɗorata a hanya yadda zata zauna lafiya amma tana nan shawarar ke amfani da zaran ta tafi Mardiyya zata warwareta kaf ! Ƙawayenta ma haka suke wulaƙanta ni san ransu yanzu kwata² ma na daina fita ko palo kullum ina ɗaki sai sun gama iskancinsu sun tashi nake fita da sauri naje nayi abinda zanyi na dawo ɗaki bawai dan ina tsoronsu ba saidai dan gudun rayuwar da zanyi dan a halin yanzu idan nabar gidan Dikko bansan ina zanje ba , gidan Kaka yafi ƙarfina saboda gidan ɗan uwan Inna ne kuma ban auri ɗansa Sultan ba an buɗa , gidan Baba ƙarami bazaije gareni ba Dikko yasa an ɗaureshi saboda ni , Inna bata nan kuma har yanzu ban samu wayarta ba kuma babu wanda yace min yana waya da ita , idan na tashi hankali nayi faɗa da Jidda tabbas Momy zata iya korata idan an koreni nikam ina zanje ? Dan haka zaman gidan Dikko shine mafita zanyi haƙuri idan ma na tayar da hankalina Dikko ya sakeni bansan ina zan nufa da rayuwata ba , Ga Bello ga Dady suma duk ni suke jira , shin rayuwar bariki zanje inyi ? Shin zan dawwa a harkar bariki kenan ? Haƙuri shine maslaha kuma na haƙura , ina tare da damuwa sosai na rasa wa zan faɗawa inji sanyi dan haka kawai zan faɗawa Yazeed , dan yace mu haɗu a washe garin waccan ranar banje ba amma ina jira idan ya sake kirana zan fita idan har ya yadda zai bani mafita kuma zai zamar min garkuwa kawai zan fita daga gidan Dikko inje in auri dai² ni sai in zauna lafiya.... Kwance nake a gado ina nazari yadda rayuwata zata kasance idan na fita daga wurin Dikko , tsikar jikina ta tashi a dai² lokacin dana tuno ranar da zai tafi , yadda lokacin ya kasance yazo a zuciyata ya tsayamin kukan da yakeyi nakeji a raina sautin kukanshi cikin shagwaɓa Dikko baijin magana dana tuna sai inji hankalina ya tashi tsigar jikina duk ta mimmiƙe bana tunanin komai sai san kasancewa dashi , Dikko jarumin namiji ne a fagen daga ya iya jan linzamin mace a filin wasan danbe cikakken namiji ne mai zanawa mace natsuwa mara gogewa a rayuwa taya zan iya rabuwa dakai ne.....................? Muna waya da Yazeed kuma har yanzu nace masa zamu haɗu amma banje ba banma fita ba gaba ɗaya , har Dikko yayi wata 3 da sati3 da tafiya kuma har yanzu ƙawayen Jiddah suna nan kuma suna hantara sbd sun nemeni da les naƙi , sun nunamin duk wani karuwanci naƙi yadda , da sukaji haushi sai suke tira Jiddah ta riƙa jamin sharri a wurin Momy , haka zata turo "yan uwan Dikko su wulaƙantani wani lokaci su mammareni , kawayen Jiddah kuma sunyi alƙawarin zasu jamin sharri wanda bana iya fitar dakaina a wurin Dikko wai ya sakeni in koma inda nafi wayau lokacin nice zan nemesu idan na nemi na abinci da wurin zama na rasa , gashi banda lafiya ni bansan abinda yake damuna ba sam bana san hayani kuma bana san yawan magana , Mardiyya kuwa tuni ta cire hoton da ƙawayen Jiddah suka ɗaukeni a wayarsu wanda suka ɗaukeni washe garin da aka kawoni ta turama Dikko bansan iyakar sharrin data faɗa ba ko na kirashi waya baya ɗauka rabon da nayi waya dashi tun ranar data tura mishi hoton ya turamin kuma ya kirani yace shi bazai sakeni ba duk abinda naji ina iyawa inje inyi kaina nayi ma, ba bugu ba zagi amma idan na kasheshi na huta , gashi shi baya tsayawa ya fahimceke idan dai ya sauke nashi shikenan , Na rasa wanda zanyi shawara dashi , da na fara tunanin su Amisty sai zuciyata ta gargaɗeni da na fita hanyarsu gara dai na faɗawa Yazeed tunda tun farko shine ya faɗamin cewa idan ina da damuwa na faɗa masa zai bani shawara , wayata na ɗauka na kirashi bayan mun gaisa nace yau zan fito ina zan sameka ne ? Wai yana jibiya , zanzo jibiyar wurin ina kake ne ? Ba'a kai jibiya ba kinsan me mujiya ? Ina ne haka ? Hirji matattara tantirai , yaushe zaka dawo ne ? Sai DK ya dawo , yaushe zai dawo ne ? Gobe idan Allah ya kaimu , zanzo hirjin , sai kinzo yana faɗin haka ya tsinke wayarshi. Dakel nayi wanka na shirya cikin riga da siket na material cikin kayan da Yazeed ya kawomin wanda wurin kai ɗinkinsu ne Bello ya sossoka min wuƙa , kwalli kaɗai na shafa sai viseline dana shafama bakina kaɗa bayan na shafa mai da powder a fuskata , Nabeela tace nayi kyau kuma saida tayimin hoto , komawa nayi gefen gado na zauna bayan ta gama ɗaukana hoton ina neman sa'ar fita , wato inaji Dikko bai faɗa zai dawo ba kawai zaiyi mamaye ne dan da Jiddah tasan zai dawo ƙawayenta zasu bar gidan kuma dole zatayi gyara na musamman dan taci burin dawowarshi duk kuwa data kira aurenta dashi na ƙaddara ne. Nabeela tana shiga toilet wanka na ɗauki jakata gyale na da makullin goruba na fice abuna , a bakin get na samu Umar muka gaisa yace Hajiya ina zakije ne ? Goruba na faɗa kai tsaye , yo ke baki san mai gida ya dawo ba ? Yana ina ne ? Yana abuja ai shi yasa ƙawayen hajiya zasu tafi nine na samo musu mota tasha baki ga har an fara fitowa da kayansu ba , waye ya faɗa musu ya dawo ne ? Ni na faɗa musu nima abinda yasa na sani Ashiru yacemin na gyara masa ɗakinshi kila shigowar dare zasuyi gobe idan Allah ya kaimu , daga cewa kayi shara sai kazo kayi ta surutu kai bakinka me yasa baya shiru ? Dariya yayi tare da cewa tubani neke ranki ya daɗe , murmushi nayi cewa tou bani aron motarka na dawo , bani yayi na wuce na shiga naja nabar gidan cike da damuwa , naso ace Dikko ya samu ƙawayen Jiddah yaci ubansu , amma nasan ba saboda su yayi shiru da dawowarshi ba nasan dan Al ' Ameen ne , saida na fara zuwa goruba na gyara ɗakin na kama hanyar jibiya. Wata irin zuba Al ' Ameen ya goge da boka ya kirashi a waya ya sanar dashi cewa Sultana tana da ciki , tashin hankali gashi Dikko zai dawo gobe kuma yanzu Zaria bata zuwa gareshi kuma boka ya tabbatar ma Al ' Ameen ita kanta Sultana bata san tana da cikin ba , idan kuma har Dikko ya dawo cikin bazai zubdu ba duk irin baƙin asiri da za'ayi shawara ɗaya yasan yadda za'ayi a zubar da cikin dan wallahi ɗa namiji ne zata aifa , Cike da tashin hankali Al ' Ameen ya kashe wayar ya kira Jiddah ya faɗa mata cewa idan har ta kuskura aka haifi cikin nan wallahi ƙaryarta ta ƙare duk yadda za'ayi a zuba mata abinda zata ci cikin ya zube , cikin rashin fahimta Jiddah tace wake da ciki ne ? Al' Ameen yace Sultana mana Jiddah tace yaushe ta samu cikin kuma waye yayi mata cikin ? Al ' Ameen yace mai aurenta mana , Jiddah tace ƙarya ne ai Yaya bai kwana da ita ba , Al ' Ameen yace tou tana dai da ciki kuma ɗa namiji zata haifa idan ko ta haifi ɗan nan na rantse da girman Allah ƙaryarki ta ƙare kisan yadda zakiyi da cikin nan ko maganin zubar da ciki ne ki bata a abinci ko abun shanta , saida Jiddah ta sunsunkuya zagi ta luƙaƙashi sannan tace ta daina cin duk abinci da ba itace ta dafa ba a gidan nan dan uban uwarta , shawara dai Al ' Ameen ya bata akan ta kira Yayyen mai gida ta sanar dasu ya faɗa mata abinda zata faɗa musu , godiya Jiddah tayi tare sa kashe wayarta tana neman mafita , kam ya zata yadda ita bata aihu ba sai wata data zo ɗazu da safen nan.........? Bazai yuwu ba koda duka sai sun fitar da cikin nan. Da tambaya har na isa inda Yazeed yake tunda ni bansan wuri ba mutane ne sukayi ta ɗorani a hanya har naje , bayan na isa na sanar da Yazeed nazo na faɗa masa inda nake yace yana zuwa , an daɗe sosai sannan yazo ta wata munafukar santa ya fito da mota , gaba yayi nabi bayanshi munyi tafiya mai nisan gaske wanda har na fara tunanin na kawo kaina , wato abun ba'a cikin inda za'a gansu sukeyi ba sunyi nisa da mutane , daga inda yace na sameshi zuwa inda ake wasan tafiya ce mai nisan gaske inajin su kaɗai ne suka san wurin. Muna isa na samu wuri nayi parking dandazon mata ne kamar ƙasa karuwai da suka ansa sunansu , murzajjin "yan iska da suka sha iskanci har sukayi gyatsa saboda lalacewa , wai ana gabatar da shirin wasan danbe babu jimawa , dan haka maganata Yazeed ya hana na faɗa wai in jira inga yadda ake wasan danbe sai muyi magana daga baya , haka mukayi ta ratsa mutane muna wucewa da yawa a wurin na sansu , Safiyya ɗiyar Baba ƙarami tana gani na ta taho da gudu tana zage² wai nice nasa aka kulle babansu , Yazeed ya dakatar da ita wai ta kiyayi kanta idan ba haka ba zai goge sunanta dama Kaka ta matsa masa yaa saka sunanta , laƙwas ta koma bata sake magana ba , gabana sai faɗuwa yakeyi nake bin bayan Yazeed , wato abinda na lura karuwan kila akwai manya akwai ƙanana domin an kasasu wuri daban² haka muka wuce har muka isa wani ƙaton wuri , tsakar fili ne na gida amma an zagaye wani wuri daban an ɗaga wurin da ciko yayi sama yadda duk inda kake zaka iya hange kamar dai yadda akeyin na restyling daga saman wurin kuma an ƙawatashi da wasu irin manyan katifai da pilaluwa an shinfiɗe da zanin gado , Wurin wasu lafiyayin maza ya kaini duk gajeren wando ne a jikinsu wai in gaisa dasu sune mazan da zasuyi wasa , murmushi nayi kaɗan na anshi karka rasa fuskata ɗauke da damuwa , bayan mun gaisa yace musu matar DK ce , DK 😳 suka zazzaro ido da mamaki sannan suka bini da kallo har naji babu daɗi , bayan sun gama kalleni tsaf sukace tou su babu ruwansu suka ci gaba da lissafin kuɗinsu , Yazeed yace taho nan ki kyalesu matsoratan banza , A , a , ni tafiya zanyi kawai mayi waya ai bansan haka wurin yake ba , Yazeed yace da Allah ki jira kiga danben dana baki labari kwanaki baki sani ba , a , a basai na kalla ba , wayarshi ya ciro a aljihu yana cewa tsaya ki gani mana kafin na ankara ya ɗaga wayarshi ya kwaso mu hoto solfie , zan masa magana akan me yasa ya ɗaukeni hoto Amisty ta shigo da gudu ta rungumeni cikin farin ciki da sauri na juya amma Yazeed ya ɓacemin , wata irin zuba ta ketomin yayin da zuciyata tace bakiyi zufa ba tukun ƙaryarki ta ƙare...... Amisty tace ai ana cemin kinzo kinji daɗin da naji , cikin tashin hankali na saki Amisty nabi hanyar da zan nemo Yazeed iya dubawa ta ban ganshi ba , tou me yake nufi ko ya ɗauka ne dan ya riƙa hansar kuɗaɗe a wurina kamar yadda na riƙayi a baya ? Kwawalwata tace ya ɗaukeni dan ya turawa Dikko idan ya gani zai sakeki shi kuma saiya ɗaukeki ya sakaki a danbe yana kasuwanci dake dan dama haka ya faɗa a baya....... Dariya Yazeed yayi a dai² wannan lokacin cewa alhamdulillah nasara tazo haba ina zan bar DK da wannan babbar ƙaddarar ? Yarinya kyakkyawa mai kyan diri da siga mai ɗaukar hankalin duk wani lafiyayen namiji , kai ko mara lafiyar ya ganta dan ubanshi saita burgeshi munafiki ya samu "yar yarinya yana hutawa abunshi ai ba taka bace ba wannan nagartacciyar surar , tunda dai ban aura ba gara kowa ya rasa , ka tsere ma kaf abokanmu a naira riga mota matar ma sai kafi kowa ? Idan mun yadda kenan kai mana wayau , yadda nake ƙarƙashin ka gara na samu ko da macen na tsira , kai sarkin dabara kawai kaje ka ɗauko ɗanyen jini dan ka bamu wahala haka zamuje muna ganinta hankalinmu yana tashi to ni burina kawai ka saketa hankalina ya kwanta dan nan gaba yarinyar nan ta goge bata riƙuwa ga kuɗi ga hutu ga gayu dan yadda DK yake ɗan gaye dole komai nasa ya zama ɗan gayu , gara ni in kwasheta idan kuma bata aureni ba sai kawai in barta a wasan danbe nasan duk lokacin dana buƙace ta zan ɗan rage zafi uwa uba kuma zan linka arziƙi dan duk katsina banga irin mazan da zanba ita ba. Na nemi Yazeed har na gaji ban ganshi ba , kuma na kirashi bai ɗauki waya ba , dan haka na haƙura na fito daga inda nake dubashi na sake dawowa wurin da ake taron danben a lokacin wurin ya cika taf tsit kake ji babu wata hayani ana kiran sunaye.... Hamida Aliyu Muhammed Binna , shine sunan da naji an kira tsagal² ta tashi ta shiga saman filin aka ɗauki ihu da tafi yayin da wasu ke busa usir , idan mutun ya shiga filin saiya tsaya ya kalli mutane sannan ya tuɓe kayanshi ya tafi da kwarkwasa ya hau saman katifa , sai a sake kiran wata itama haka zatayi duk sai an gama kiran sunayen matan sun hau katifa sai a kira mazajen da zasuyi wasan su jera layi sai aci gaba dakai naushi. Banda lokacinsu domin ina tare da tashin hankalin daya fi wanda naga Hamida a ciki tunda ita tayi kuma kowa yasan tayi fita nayi daga wurin ina kuka , nifa ? Ina hotona zaije ? Kai nidai jakace....... Aunty kusan abinyi fa dan Caca ciki gareta kuma wallahi ko ranar da aka kawota Yaya dani ya kwana a ɗakinshi kuma washe gari ya tafi amma tana da ciki , idan har ya dawo ya samu cikin nan zai yadda yace nasa ne saboda ta gama dashi za'a ɓata muku ahali shege ya fito a cikinku , idan kuma aka saketa ta fita da cikin nan shima idan ta haife cikin shima shine zaice nasa ne , gobe zai dawo meye mafita ? Zan shigo idan Allah ya kaimu suka ajiye waya , bata faɗawa Momy ba kawai ta yanke hukunci a kanta.... Sai bayan isha'e na dawo gida a gajiye a waje na bada makullin motar Umar a ajiye mishi idan ya dawo , Nabeela tana gani na tace ke kinji kunya kika shigo da cikin shege a gidan aurenki , kin ɗirka dabkekiyar asara ai Yayan zai dawo zaki faɗa masa a gidan uban waye kikayi ciki... Wata irin mummunar faɗuwar gaba naji na wuce ciki ban nuna damuwa ba , ikon Allah ashe ciki gareni ? Allahu akbar sai yanzu ma na tuna da yaushe rabon da inyi jinin al'ada , daɗi naji sosai a zuciyata addu'ata ta farko Allah yasa in haifi mai kama da Dikko komai da komai , tunani na biyu ya akayi suka san ina da ciki bayan ni ban gane ba ? Can su suka sani dai , kuma Dikko zaizo ya faɗa musu shine yayi cikin ba cikin shege bane ba , da farin ciki nayi bacci tare da tunanin Dikko. Da asuba bayan nayi sallah bacci na koma , ban daɗe da kwanciya ba na tafi bacci yauma ya bayyana a mafarki na , kinga inda ya ajiye ne ko kuwa ? Ya tambaye ni , ban gani ba kuma na tambayeshi yace baya san surutu , tou albishiri na kwakwale amma yau ba'a mutu ba kina da ciki kuma zasu zubar da ciki kiyi ƙoƙari ki samoshi idan ba haka ba haɗuwa ta gaba tafiya ce babu fashi , waye zai zubar dashi , ta inda mutumin nan ya fito a ranar da nayi mafarki a goruba yauma ta wurin ya fito ya kamashi da kokowa , yana cewa waye yace ka faɗa ne ? Kokowa sukeyi sosai har mai cewa ya kwakwale ido ya samu damar cire abunda mutumin ya rufe fuskarshi , Al ' Ameen na faɗa lokacin da aka cire abun daya rufe fuskarshi a dai² wannan lokaci naji saukar bulali a jikina...... A firgice na farka daga bacci Jiddah da Yayar Dikko suke ta dukana babu ji babu gani , da sauri na sauko daga saman gado ina cewa me nayi muku ne ? Jiddah tace dole ki tambaya abinda kikayi tunda kinje kin samu an ɗuro miki ciki ke zakici dukiya tou Allah ya warware miki asiri tun ba'ayi nisa ba , riƙeni Yayarshi tayi Jiddah tayi ta kaimin duka a ciki da bokitin ƙarfe wani irin ihu nayi nunfashina ya tafi sama na kasa kwacewa , saida ta gaji sannan suka danneni ƙasa Yayar Dikko tayi min allura suka fita daga ɗakin bansan inda kaina yake ba. Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Dikko ya faɗa tare da cewa Ashiru An mata wani abu ya sameta , Ashiru yace me kuwa zai sameta mai gida , Dikko yace tabbas wani abu ya faru wallahi dan naji a jikina wanda rabon da inji haka har na mata kiramin ita , duk kiran da akayi ma Sultana bata ɗauka ba , cikin tashin hankali yace kiramin Nabeela itama bata ɗauka ba , Jiddah yace a kira , itama bata ɗauka ba dan tabar wayarta a ɗaki tana ɗakin Dikko ita Mardiyya wai suna gyarawa , Mardiyya yasa aka kira tana ganin wayar Dikko ta fita daga wurin Jiddah sannan ta ɗauka , bayan ta gaishe da Ashiru yace mai gida yace kina gida ne ? Eh , tou meya faru a gidan ? Saida tayi dube² tace nidai naji ana cewa an zubar da cikin Aunty Amarya.... Kallon Dikko Ashiru yayi tare da cewa mai gida wai bata gida bayan ya kashe wayar , tsoki Dikko yayi cewa tafiya katsina ya kamani yanzu , Ashiru yace ka bari sai anjimar mana , umm umm muje yanzu , kallon agogo yayi yace la'asar tayimin a katsina. Mardiyya kuma komawa tayi suka ci gaba da aikinsu , Nabeela kuwa bata nan bata san abinda akeyi ba dan tana makarata , su kuma hidimarsu sukaci gaba dayi mai kwalliya ta musamman Jiddah ta gayyato danni taci gayu yadda zata yaƙi zuciyar Dikko , Mardiyya ta tsareta da kallo mai tattare da maganganu. Sai bayan la'asar Nabeela ta dawo har yanzu ina kwance a wurin da akamin allura na suma har na dawo da kaina na kasa ko motsin kirki wani irin ciwo cikina kammar raina zai fita , cike da fargaba Nabeela ta durƙusa gabana tace waye yace miki ana zubar da cikin shege a gida ? Daga na faɗa miki sai ki kashe kanki tou ni tafiya zanyi wallahi bakija min sharri , tana faɗin haka ta miƙe ta fara tattara kayanta , bata gama haɗawa ba Dikko ya bayyana a ɗakina misalin ƙarfe 4:29pm. A tsorace Nabeela ta gaishe shi ta fita daga bedroom in , bai ansa gaisuwar ba ya nufo inda nake , hararata yayi cewa wani kuma sabon rashin mutunci ne kwanciya a ƙasa ? Yayi maganar yana ɗan tauna cingom bakinshi a rufe , kifa kaina nayi ƙasa dakel nace banda lafiya , me ya sameki ya tambaya cikin sigar lallashi.... Shiru nayi , da damuwa fa , banda lafiya ga naje wurin Yazeed kuma ban san laifin da nayi ma Dikko ya daina ɗaukar wayata ba , idan kuwa ya gano ni yau idan ya fara dukana waye zai ƙwaceni gashi ban iya tashi.........? 24/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA.....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 81 Me ya sameki ne ? Ya sake tambaya a karo na biyu , nayi ɓari ne , kallon ɗakin yayi sannan ya dawo da kallonshi wurina yace wane ɓari ? Yayi tambayar a cikin rashin fahimta , ina da ciki ne shine ya lalace , ɓacin rai kwance a idonshi ya gyara zaman hular saman kanshi ya duƙo inda nake kwance sai yanzu ya lura da jinin dake kwance a wurin , shi bai gani ba amma Nabeela tun shigowarta ta fahimta , cikin tsananin ɓacin rai yace ban gane ba fa.... Ban sake magana ba daga haka dan maganar ta isheni kuma a wahalce nakeyinta , Nabeela........... Ya ƙwala mata kira da sanyayayyar muryarshi , da gudu ta shigo jikinta yana kyarma ta tsaya daga can gefe cewa Yaya gani , bai kalleta ba yace me ya faru ? Cikin rawar murya tace Yaya wallahi , tare ta yayi da cewa karki cemin wallahi² me ya sameta ? Yaya ina makaranta , karki faɗamin kina makaranta me ya faru.............. ? Idan na sake magana zan kashe ki...... , cikin kuka tace matar Yaya ki faɗa masa abinda ya faru bayan bana nan , ke karki ɗaukeni sakarai ai na ganta na kiraki , nunawa yayi da hannunshi ya fara one , two , three , four cikin rawar murya tace Jiddah........ Ba damuwa na Jiddah ba abinda ya sami An mata nake tambayarki , ƙara fashewa tayi da kuka ta sake kallona tana cewa matar Yaya kiyi magana , tashi yayi yaje gabanta ya yanka mata wani irin mari harsai da ta duƙe yace idan kika sake mata magana saina karya miki maƙoshi me ya faru........? Yaya wallahi bana nan naje makaranta yanzu na dawo lokacin da zan tafi na barta tana bacci , a ina take baccin ne ? Saman gado , ya akayi ta sauko ƙasa to ? Kila ta tashi ne ta faɗi , jeki palo ki jirani zan fito idan kuma kika kuskura kika bar gidan nan na rantse da Allah saina baki wahala , cikin kuka tace tou sannan ta fita. Dawowa yayi kusa dani , ya kalleni yanayin shi ya nuna yana nazari ne , bayan wani lokaci yace tashi , a tsorace na fara ƙoƙarin miƙewa amma na kasa , da Allah tashi bana san iskanci , tou na faɗa tare da tashi durƙushe dakel , tsugunawa yayi gabana yace ya akayi ciki ya lalace ? Yayi tambayar da harshe mai tada hankali , fashewa nayi da kuka nace Dikko , An mata ya akayi ciki ya lalace ya tsareni da idanuwanshi masu tada hankali idan yana fushi , kayi haƙuri na faɗa cikin rawar murya , bansan shi ba yaci gaba da cewa wato banda iskancin hotunan da kikayi har ma kike tunanin zan barki ciki ya zube ? Ba zubewar ciki ba yau ko naƙuda kikeyi saina zaneki , tashi kije ki gyara jikinki yana faɗin haka ya fita daga ɗakin. Gaba ɗaya ji nayi kamar an tsintsinkemin lakar jikina , idan kuma Dikko yasan naje wurin Yazeed wace matsalar zan fuskanta ? Ya zanyi ? Ni ba lalacewar cikin ne damuwana ba rayuwar da zan fuskanta idan ya gano cewa na fita naje wurin Yazeed , dakel na shiga toilet dan wanka , Cikin tsananin ɓacin rai yaje ɗakinshi , gefen gado ya zauna ya dafe kanshi , zuciyarshi tana mishi babu daɗi miƙewa yayi ya matsa jikin window ya zuge labile yana kallon yadda rayuwar gidanshi ke tafiya , kowa sabgar gabanshi yakeyi ɗora fuskar shi yayi jikin window ya dafa hannunshi a sama yana kallon waje , a zuciyarshi yake zance cewa An mata baki da lissafi ko kaɗan na rayuwa , ina baki dama ta rayuwa amma baki gane abinda nake nufi dake sai idan bana nan duniyar zaki san ni ɗin na gina miki rayuwa , baki da Baba mahaifiyarki ba take , take ba tana can ta kama sabgar gabanta tana gina sabuwar rayuwarta , baku da ahali mai kyau kwata² , Jiddah ce ta shigo ɗakin da sallama. Ansawa yayi tare da juyowa ya kalleta so ɗaya ya koma yadda yake yaci gaba da zance zuci "yar rashin kunya da kinsan ina tausayinki iskancin da zaki zazzaga a gidan nan ba ɗan ƙarami bane ba mu zuba dani dake duk wanda ya fasa yaji kunya , tashi yayi a wurin ya nufi hanyar toilet yaga Jiddah zaune a gefen gado , ya akayi ne ? Ya tambayeta cikin kwarkwasa tace ba komai ta ƙarasa maganar tana kakkaɓa ido dan ibar mishi hankali , tou yayi jeki zanyi wanka , tashi tayi tana mummurza tafiya da salo mai ɗaukar hankali ta nufi wurinshi. Murmushi yayi ya bita da kallo harta iso wurinshi ta shige jikinshi , ajiyar zuciya ya sauke tare da riƙeta sosai yana kallon fuskarta da tasha ado da kwalliya , ɗan shanye idon dama tayi tare da cewa nayi ne ? Sassauta ganinshi yayi tare da ɗauke idonshi baiyi magana ba , gyara tsayuwarta tayi ta fara rattafa bayani kamar yadda Mardiyya ta turota cewa. Bayan Jiddah da Yayar Dikko sun gama dukan Sultana Jiddah ta kwakwkwaɗa mata bokitin ƙarfe a ciki suka danneta suka ɗura mata allura , suna gamawa suka fita a ɗakin , bata samu Mardiyya a ɗakinta ba data koma tana wurin Al ' Ameen , dan itama Mardiyyar tana gama ɗaukar video ganin zasu fito yasa ta fice da sauri ta ɓoye ƙasan bene , suna wucewa tayi wurin uncle. Uncle gabana faɗuwa yakeyi fa , da Allah can matsoraciyar banza badai kinyi video ba ? Eh kwantar da hankali yau duk bala'e ni na faɗa miki gaba ɗaya gidan nan zai watse , tabbas idan mai gida yaji labarin ɓarewar ciki ranshi zai ɓaci , da zaran yayi fushi baya iya saita kanshi dan haka zai fara duka babu ji babu gani kuma bazai saurari kowa ba , abinda za'ayi yanzu ki faɗawa Jiddah idan mai gida ya dawo taje ta faɗa masa , murmushi yayi tare daci gaba da cewa zai sakesu gaba ɗaya , ita Sultana zai saketa saboda hoton nan , ita kuma Jiddah zai saketa ne idan ya daketa zatace bana auren duka sai ka sakeni dama mun rufeta da wannan asirin duk wanda yazo zatace bazata zauna ba sai an saketa tabbas saiya saketa , Yayarshi kuma bayanin hukuncinta yana wurin Jiddah dama itace ƙatuwar munafukar kinga sun rabu kawai sai kuyi aurenku ya faɗa yana murmushi , kina shiga sai ki haihu idan namiji ne sai mu kashe shi mu cinye dukiyarshi , idan mace ce sai a bari sai an ƙara , dariya sukayi tare da tafawa.... Bara inyi wanka in fito Dikko ya faɗa tare da fitar da Jiddah daga jikinshi , gefen gado ta koma ta zauna tana jiran fitowarshi shi kuma ya shiga toilet.... Lokacin dana fito daga wanka Nabeela ta gyara wurin dana ɓata tass kuma har yanzu bata daina kuka ba , ina fitowa toilet ta shiga da kanta ta wanke kayan dana cire ta wanke toilet in , bayan ta fito tace matar Yaya tsakaninki da Allah ni ina nan wani abu ya faru dake ? Ko inda take ban kalla ba na fara saka kayana. Har Dikko ya fito daga wanka Jiddah tana nan , saida ya gama shiryawa yana saka kaya tace Yaya gaskiya abinda Aunty Rabiya takeyi bata kyautawa , Yayarshi kenan , ba tare daya kalleta ba yace me tayi miki ne ? A dai² lokacin da yake ɗaura belt a ƙugunshi , kaga dai ko ni kishirya Caca bana iya yimata irin abinda ita Aunty tayi , a dai² lokacin da yake saka riga , yace kiyi maganarki kai tsaye mana yana kallon kanshi a madubi tare da gyara zaman rigarshi , Caca ce take da ciki shine tace sai ta zubar dashi dan ita ƙawayenta sunce babu aihuwa a tsarin rayuwarsu , tsayawa cak Dikko yayi tare da daina ɓalle botiran rigarshi ya kalli Jiddah ta cikin madubi , data faɗamin zata zubar da cikinta dan ita zatayi gaba , shine na bata haƙuri tace bata yadda sai ta fitar ita ba zata zauna wani rainon ciki da "ya "ya ba taje ta tsufe ta lalata ƙuruciyarta , ni kuma sai nayi ma Aunty Rabiya waya a matsayinta na babba tazo tayi ma Caca magana dan karta zubar da cikin , shine tace ita ai bata so ka haihu dama shine fa tazo tayi mata allurar zubar da ciki.... Shiru Dikko yayi yana addu'a a zuciyarshi dan ya saita kanshi amma ya kasa sarrafawa , yayi ya riƙe yaƙi riƙuwa , a zuciye ya fita daga ɗakin zuciyarshi tana tafarfasa da wurin Momy zaije amma yana kawowa ƙofar ɗakin Sultana yaji baya iya wucewa , shiga yayi Nabeela tana ganinshi ta durƙushe irin gani na miƙo kaina , bai kalleta ba ya kalleni yace nidai ko An mata...... ? Dikko dai ko ? Ya tsareni da ido , kayi haƙuri , kamar jira yake inyi magana yace ke............. Saina kashe ki ya fara wani irin gurnani mai tada hankali , da gudu Nabeela ta fita tana neman ɗauki dan ita a tunaninta itace Dikko ya faɗa zai kashe , cikin sanyi nace ba komai kashe ni na faɗa hawaye na gangarowa daga cikin idona , dan bana iya tashi , nunani yayi cewa rufe min bakin munafuka jaka dake da bakisan inda duniya ta nufa ba na tsaneki....... Bana sanki haka kuma bana san ganin ki ya faɗa tare da kaimin wani irin halbi yana ci gaba da cewa ai baki burgeni ba da baki haɗa hada kanki kika mutu ba , bani kika cuta ba rayuwarki ce , zanje in dawo yau mai kwatarki a wurina sai Allah banza ƙazama..... Fuuuu ya fita daga ɗakin , a palon ƙasa ya haɗu dasu Ashiru ko inda suke bai kalla ba ya wuce ya fita da sauri ji yayi G H tayi masa nisa wani irin ihu ya kurmama mai tsananin tada hankali ya durƙushe a wurin wai....... Wai , wai Allahna , wayyo , kai.........saina kashe kaina ya riƙe wuyanshi da ƙarfin bala'e , duk yadda akayi a ɓanɓare hannun Dikko daga wuyanshi yaƙi fita , kuma daga durƙushen an kasa kwantar dashi tashin hankalin ya girmi tunanin duk mai tunani , a ruɗe Nabeela ta fara kiran wayar Momy amma bata ɗauka ba , Yayarsu ta kira ta faɗa mata sannan ta turawa Dady text kuma har yanzu Dikko bai kwanta ba kuma bai cire hannunshi daga wuyashi ba har yaji ma kanshi ciwo jini yana fita daga wuyanshi. A wannan halin Dady ya samu Dikko idan hankalinshi yayi dubu ya tashi , itama Yayarshi haka tazo ta sameshi duk wani mai san rayuwar Dikko haka suka zo suka sameshi har Momy kuma zuwa wannan lokacin ya daina lumfashi gaba ɗayanshi ya ɗauke , Ashiru Dady ya kalla yace me yayi zafi haka ? Cike da damuwa Ashiru yace muna Abuja yacemin yaji gabanshi yana faɗuwa tabbas wani abu ya faru da Hajiya amarya shine yace in kirata dama sun kwana biyu basa waya ni bansan abinda ya haɗasu ba , Momy tace shegiya ɗiyar matsiyata idan wani abu ya samu ɗana itama sai an ratayeta. Hannu Dady ya ɗaga mata ya dakatar da ita sannan yace ma Ashiru ina jin ka , sai na kirata bata ɗauka ba , yace na kira Nabeela itama bata ɗauka ba itama Hajiya Jiddah shine yace na kira Mardiyya bayan na kirata na tambayeta tana gida tace min Ey nace me ya faru a gidan ne ? Shine tacemin ita dai taji ana cewa an zubar da cikin Aunty amarya ne , bayan na gama wayar nace masa Mardiyya bata gida gudun karya shiga damuwa shine ya matsa muka taho katsina , ni daga haka bansan komai ba. Dady yasa aka kira Mardiyya bayan tazo ya tambayeta abinda ya faru , tace Aunty Rabiya ce tazo tayi ma Aunty Amarya allurar zubar da ciki , Rabiya zatayi magana Dady yace ta rufe mishi baki , shiru tayi tana kallon Jiddah , Dady yasa aka ɗauki Dikko gaba ɗaya kowa da kowa aka nufi ɗakinshi dashi , a ƙasa Dady yasa aka kwantar dashi sannan ya umarci kowa ya fita har Momy , fita sukayi gaba ɗayansu , magani ya fiddo a cikin wata kwalba ya zuba mishi a kunne dan tun lokacin daya bi Dady ranar da gaya hotunan Sultana zata sha giya idan baku manta ba ai a ranar ya fara faɗa zai kashe kanshi , daga nan Dady yace zasuje saudiyya sai aje da Dikko wurin magani , salati yayi tare da buɗe idonshi , Dady yace Babana ka rufa man asiri ka barni na zauna lafiya..... Kai......... Saina kashe Rabiya..... Riƙeshi Dady yayi idonshi ɗauke da hawaye yace yi haƙuri Babana , a , a , saina kasheta......... Kuma saina ɗaure mijinta daya barta take fita har tanayin iskanci a gidana birkicewa yayi daga hannun Dady yayo waje da gudu , Rabiya na ganinshi ta sauka ƙasa da sauri amma kafin ta ida gangarawa ya rigata sauka saboda shi ta sama ya sauko , yana ƙoƙarin riƙeta tace Jiddah ce...... Jiddah tana gani kowa yana rugawa amma sai ta tsaya , sokewa yayi saman guyawunshi zuwa ɗaya yayi mata ta faɗi ƙasa somammiya miƙewa yayi da gudu yabi Rabiya Dady yace ku riƙeshi mana , kai......... Karku taɓani idan kuka taɓani saina kashe kaina , daf da zata fita daga cikin palon yayi mata wani irin halbi ta fice somammiya , itama An mata saina kashe ta........... Dady yace wai bazaku kwantar dashi ba , wata irin zabura Dikko yayi bana kwanciya ya nufi hanyar ɗakin Sultana , da gudu su Ashiru suka bishi , kai...... Karku taɓani , wai har so nawa zan faɗa bana so ana riƙeni ne............. ? Ya juya tare da sauke ma Ashiru hannu a ciki ya koma baya ya faɗi ƙasa yana ihu , wurina ya nufo yana zabura cewa saina kashe ki......... Da sauri na jawo lokar bedsite na ɗauko abuna yana matsowa na feshe mishi fuska ya faɗo saman gado ruf da ciki saida ya kalleni sannan ya rufe idonshi a hankali ya tafi hutun taƙin lokaci , haka kawai zan zauna ne aljanu su lahanani ? Sun tsaya bayan fage suna ta iskanci an kasa maganinsu tou ni nice maganin su Allah dai ya bani lafiya. Dady bai shigo ɗakina ba Momy ce ta shigo saida ta zageni tas tace kuma Dikkon zai dawo daga duniyar suma zata faɗa masa nice na zubar da cikin zaici ubana kuma zai sakeni , a raina nace wane dare ne jemage bai gani ba ? Aini halin Dikko da duk haukarshi saidai in ba wani labari dan nayi imani nice mutum na farko dana fara ganowa shi mahaukaci ne , Dani da Rabiya da Jiddah aka tattara aka nufi asibiti damu umarnin Dady bayan an tafi dasu Sultana Dady yasa aka fiddo Dikko daga ɗakin Sultana aka maidashi ɗakinshi , Washe gari , duk wani taimako daya kamata anyi mana dukanmu nidai saida akayi min wankin ciki domin likita ya tabbatar da cikin ya lalace saboda allurar ta daɗe a jikina babu wani abu da zasu iyayi , Rabiya kuwa tunda ta dawo batayi ma kowa magana ba , Jiddah kuwa kuka take bata zama da Dikko saiya saketa tana ta ɓaɓɓarka zagi ita ba jaka bace ko a gidansu ba'a taɓa dukanta ba sai wani can ƙaton banza , gaba ɗayanmu dai sallamarmu akayi dukanmu kwananmu ɗaya a asibiti , Yayar Dikko mijinta ya ɗauketa Jiddah Al ' Ameen ni kuma Ashiru muka nufi gida , Jiddah kuma wurin Momy ta tafi sai an saketa..... A ƙofar shiga ciki naci karo dashi , shi zai fita ni zan shiga ran nan nashi a haɗe yana waya ko inda nake bai kalla ba , gaishe shi nayi ƙaddarawa yayi baiji ba ya wuce , jiki a sanyaye na shiga ciki , Nabeela ta gyara ɗakin ta gogeshi ta sakar mishi ƙamshi mai daɗin shaƙa , sannu da jiki tayimin , kaɗan na ansa na wuce bedroom na kwanta. Yana shiga mota kiran Yazeed ya shigo a wayarshi , kallo ɗaya yayi ma wayar ya ajiyeta a gefe yana ƙoƙarin tashin motar wani kiran ya sake shigowa , bai ɗauka ba ya fita daga gidan da tuƙin rashin sanin darajar rayuwarshi , ya kusa isa inda zaije text ya shigo , ɗauka yayi ya duba Yazeed ne mai turo saƙon , hannunshi ɗaya riƙe da sitiyari ɗayan riƙe da waya , dubawa yayi , _DK An mata ta fita hanyata , kaga dai har yanzu bata daina bibiyata ba sai bina takeyi ka duba a whatsapp na ajiye maka saƙo danni gaskiya bana san mayata...._ Da hannu ɗayan daya riƙe wayar ya tura masa..... _Wace ce An mata kuma.....?_ _Matar ka.....!_ _Wace.....?_ _Sultana ɗiyar ɗan caca_ _Oh wai An matana......?_ _Eh_ _Me tayi maka ne ?_ _Tana biyoni duk inda naje..._ _Tou yi haƙuri ina driving , amma kana ina yanzu sai inzo in sameka muyi magana....._ Yazeed bai sake turo saƙo ba , ajiye wayar Dikko yayi yana cewa zakaci ubanka idan na riƙe ka , mtsww ko saƙon meye ya ajiye Koma dai miye saina gama zan duba , itama An mata saina sa ta rana kanta tunda bata da wayau bazan sake mata murmushi ba sai tayi nadamar sani na , banda Dady ya bashi haƙuri yace mishi babu mai laifin sai Rabiya tunda taje tayi abinda batayi shawara ba , dan yadda Mardiyya ta faɗa masa ya yadda da hakan shi yasa ya faɗawa Dikko aka ɗorawa Rabiya laifi gaba ɗaga banda haka da saiya tada Sultana aiki yadda ko bata tare dashi ta zama condem bata sake amfanin komai sakara ƙarar yarinya da ita..... Bayan ya isa inda zaije yayi parking , bai fita a mota ba tunanin jiya ya farayi , duk abinda yayi ya dawo mishi a kanshi , Allah ka yayemin wahala , lallai An mata ni zata ma haka ko ? Wato ni zata feshe ma fuska ? Lallai yarinyar nan duk yadda akayi har yanzu tana da wani kuɗiri akaina , wata zuciyar tace ba haka bane ba , wani sashe na zuciyar shi yace kaima kawai ka yada ƙwallon mangwaro ka huta da ƙuda , murmushi yayi a bayyane yace An mata bata yaduwa kuma ita ba ƙwallon mangwaro bane ba idan na yadar da ita ina zataje ? Wane hali zata shiga ? Idan har na rabata dani banyi mata adalci ba gaskiya zama da ita dole saidai zan bata wahala a daren yau saina zane mata jikinta tasss , zan zauna lafiya na kwana biyu idan kuma zafin ya huce zan ƙara mata tunda ita ta zama doki sai an daketa zata tafi , bayan kwana biyu kuma zamu haɗu a saman bargo Allah ya baki lafiya jarumata..... Fita yayi daga motar ya wuce ranshi a ɗan sauƙaƙen damuwa , kafin ya isa inda ya dosa su Ashiru har sun bayyana a wurin , a hankali mutane suka fara kawo hankalinsu wurin saboda zuwan su Ashiru , DK ya faɗa tare da riƙo hannun Dikko suka taɓa murmushi Dikko yayi kaɗan , abokin nashi ya cire hannunshi tare da nunawa da hannunshi ranka shi daɗe ya kake ya kyau ya zati ya ƙwarjini ya iko ? Murmushi Dikko ya sakeyi yace hali dai na nan Saminu me kazo yi nan ne.....? Ya tambaye shi yana wucewa abunshi , Bin bayan Dikko yayi yana cewa Allah ya kawoni kai ka fito ta can ni kuma na hudo ta nan kaga yauni lafiya lau kenan gani ga mai girma DK , Dikko bai sake magana ba ya wuce ciki saida ya gama dube²nshi yace da yaranshi dake binshi ku shiga ku dubomin shi , sun duba sosai basu ga Al ' Ameen ba , jinjina kanshi yayi yace ku wuce muje , yayi gaba suka rufa mishi baya , abokin nashi ne yace DK sallamarni mana nima in sheda , Dikko yace ni kuɗina basu zuwa wasan danbe , dan girman Allah ni yaushe rabona da danbe ai na bar ma su Yazeed , Dikko yace tunda aka fashe idon ka zakace ya faɗa yana dariya , nidai dan girman Allah DK bani , kai ba abinda zan baka , har wurin mota yabi Dikko yana haɗashi da Allah , Dikko kuwa mamakin yadda Saminu ya lalata ma kanshi rayuwa harya dawo ya fara maula abun bai mishi daɗi ba kuma baiso mishi haka ba , saida sukaje mota ya bashi kuɗin da babbban dumtsiya , cah.... Mutane suka rufo wurin suna maula. Nidai Momy saiya sakeni , Momy tace ke sakarar banza karki kuskura Dikko ya sakeki ba dan ni na haifeshi ba Dikko miji ne ki riƙeshi wannan lalurar nashi zai zamar mishi tarihi Jiddah ki kwantar da hankalinki ki maido natsuwarki a jikin ki karki kuskura ki bari ya rubuta ko ya furta kalmar saki Dikko da kike ganinshi baida mutunci , haka kuma baida haƙuri kamar amai amma ida kikayi haƙuri komai zai zama dai² amma maganar saki ya fita harshenki , Nidai gaskiya bana sansa , cikin rarrashi Momy tace keda ɗan uwanki idan baki so sa dan komai ba kiso sa dan zumunci mana haba Jiddah ina wayanki ina lissafinki ina tunaninki ? Karki ma kuskura kiyi wannan rashin wayan a gaban Dikko dan nayi imani da Allah ko da wasa kikayi masa maganar saki saiya sakeki duk kuwa yadda yake sanki ko zai mutu saiya rabu dake , Nifa gaskiya na gaji ko za'ayi tashin hankalin da ba'a ƙara maimaita kamarshi saiya sakeni , Momy tace ji Jiddah karki yi abinda zai baki damuwa daga baya fa , idan ya sakeni duk ranar dana zo nace kisa ya maidani ki tunomin wannan ranar , Momy tace ai bana fata ma yanzu tashi kije kiyi wanka kici abinci ki huta zuciyarki tayi sanyi , ni babu ranar da zuciyata zata huta sai ya sakeni , Momy tace yi haƙuri Jiddah idan kina gidan Dikko waye ya isa ya shiga ya katantane ? Bare idan "yan uwanshi sunje a watsar dasu a palo , idan kina gidan dake da duk wani ɗan dana haifa da "yan uwana gidan bazaku zama a raɓe ba , kuma idan ma dan wannan karuwar sakinta zaiyi kinga daga ke baza sake aure ba , nidai ko ya saketa bana zama , Jiddah kalmar saki ya fita daga bakinki bakisan hakin Dikko ba , tashi kije kiyi wanka kiyi bacci , tashi tayi tana ko za'ayi tashin hankali sai Dikko ya saketa. Al ' Ameen dake rakuɓe yace Hajiya ki bari yayi mata ɗaya kila ta huce , Momy tace da Allah rufemin baki ɗan iska fita ka bani wuri , Allah ya taimakeki ya faɗa tare da fita , cikin farin ciki yace a gaban mai gida zata faɗa na gama da wannan wasan sauran Sultana..... Lokacin mu ya kusa farawa ! Suwaiba kalleni , Dikko ne zaune saman kujera ya kashe zamanshi da ƙafa ɗaya saman ɗaya , duƙar da kanta ƙasa tayi tana kuka , tunda nake faɗin kisa ban taɓa kashe wa ba amma zanyi rantsuwa kuma kinsan halina na faɗa ma na cika bare kuma na rantse idan har kika kuskura nayi rantsuwa zan kashe ki saina kashe ki , in kashe ki kuma na kashe banza dake da ɓeran gidana babu banbanci yadda zan kashe shi ba'a tuhumata abinda yasa na kashe shi haka zan ɓatar dake cikin mintuna biyar zan shafe labarinki a garin katsina , Waye....... ? Na rantse girman Allah ga sunanshi a zuciyata amma bana iya faɗa , Dikko yace duk halakacin da nayi miki dake za'a haɗa hannu na zama lusarin namiji ? Me nayi miki haka don Allah..... ? Ki faɗamin shi kawai sai insa a maida ke gidanki cikin mutunci da mutuntawa , wallahi ranka ya daɗe ga sunan shi a zuciyata amma bana iya faɗa , cikin ɓacin rai Dikko yace ku fiddomin zuciyar ta , ta ni idan na duba zan gane ko waye...... 25/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 82 Suwaiba najin haka ta saki wani irin fitsari tare da jan jiki ta matsa kusa da Dikko tana ƙoƙarin riƙe ƙafarshi ya kai mata wani irin halbi saida ta koma baya suuuuuu , ke ni ba'a taɓani duk duniya abinda na tsana kenan wani ya riƙemin jiki shi yasa ko ina cikin yanayin fushi aka taɓani nake ƙara firgicewa , ku fiddomin zuciyarta nace................... ! Cikin kuka tace dan darajar Annabin rahma S. A. W kayi haƙuri ka ƙaramin zuwa gobe dan soyayyar da kake ma fiyayyen halitta idan har ban faɗa ba kayi min duk abinda kaga dama , sannan kuma ka tattaromin kaf yaranka duk wanda kasan ya taɓa zama ƙasanka lokacin da kayi rashin lafiya ko baya tare dakai to a nemoshi a taho dashi tunda na kasa faɗar sunansa idan naga fuska zan gane.... Miƙewa Dikko yayi baiyi magana ba ya fice daga wurin , Ashiru ya kalleta yace an daiji ɓitir shegiya munafuka Allah ya ƙara tona muku asiri gobe iwar haka lahira most go dan mai gida zai kashe ki....... Ya nuna yadda Dikko yake faɗa cewa zan kashe ki........ Sai bayan la'asar Dikko ya dawo , gidan yau shiru ba Jiddah ba Mardiyya Nabeela ma bata nan tunda ta fita bayan na dawo daga asibiti har yanzu bata dawo ba , da sallama ya shigo ɗakina ko inda yake ban kalla ba na ansa naci gaba da kallon wayata da nake ta kiran layin Inna. Kusa dani ya zauna ya riƙoni jikinshi yana wannan numfashin nashi mai tayar da hankali , kyarma jikina ya farayi nace sakeni , anƙi a sakekinki , cikin hayani nace da Allah ka ƙyaleni ke muguwa daɗi kikeji na taɓaki ga jikinki nan ya nuna , da hayani na ce sakar.... Mmmmmm na ƙarasa saboda haɗuwar bakunanmu wuri ɗaya. Shiru nayi tare da ƙara riƙeshi , girgiza kaina yayi da yanayin na kalleshi , jiki a mace na saka idona a nashi naci gaba da ansar saƙonshi , saida ya gama luguiguita ni ya cire bakinshi yana cewa me ya haɗaki da ƙawayen Jiddah ? An mata bakijin magana dai ko ? Kwanciya nayi a jikinshi da yanayin kasala nace Ey banajin maganar , ke yarinya zaneki zanyi ki gama ƙaryar rashin kunyar ina dawowa anjima ya ƙarasa maganar yana tashi bayan ya saukeni daga jikinshi , nima sauka nayi daga gadon nabi bayanshi har ɗakinshi. Juyowa yayi ya kalleni tare da cewa zaki rufe ƙofa ne ? Girgiza kai nayi alamar a, a , tou me ne ne ? Ba komai na faɗa ina ƙoƙarin zama gefen gado , ke ׳ karki zauna koma can ya nunamin gefen madubi , babu wani damuwa na koma na zauna , kayanshi ya fara cirewa yana bani labari wai Suwaiba idan ta bari ya fara ranfa da ita saiya ɓoye halittar ta , wallahi An mata da tausayin matar nan nake amma yanzu na tsaneta ko ganin ta bana san yi shegiya ƙazama... Zama yayi saman bedsite wai inzo in cire masa takalminshi in samu lada , kallonshi nayi ban tashi ba , taso mana shi yasa matan yare suka more ma matar malam bahaushe da ni mijin bayaraba ne ba'a bari na in cire riga dakai na , za'a ciremin da soyayya ana faɗamin kalamai masu daɗi ana kulawa dani harsai naji kaina ya min girma , ya ƙarasa maganar yana zame takalmin shi ya cire safarshi miƙewa nayi ganin yana kwance belt a tsorace , a , a koma ki zauna ai ba yanzu zan dakeki ba sai anjima , yi zamanki ni wanka zanyi. Cikin kuka nace kayi haƙuri dan Allah , saida yazo kusa dani ya sumbaci gefen fuskata ya latsa cikina saida na zabura da irin maganata yace aradu bazan haƙura ba me kuka ci ne ? Ya ƙarasa maganar yana tambayata , ni abinci naci , ai nasan abinci kika ci idan akwai saura kawomin yunwa nakeji , Miƙewa nayi na fita , bayan Sultana Dikko yabi da kallo a ranshi yace Allah yasa "ya "yana suyi kama da An mata , amma kar suyi rashin jinta , ubangiji ka sake azurtamu da wani rabon mai albarka ka bawa An mata lafiya ni kuma ka bani haƙuri da dangana , ina can ina yawo ni banga irin abin nan da masu ciki keyi ba , ko me tayi ta kwaɗayi data samu cikin Oho , tou amma me yasa Jiddah tace wai An mata tace baza ta aihu dani ba ? Ya taɓa saitin zuciyarshi , murmushi yayi tare da faɗa a bayyane yace ƙarya ne "Yar mata tana san Dikko kuma dole zata so ta haihu dani kodan soyayyar da muke ma junanmu , rigima kenan naga Sultana da baby da farin ciki ya shiga toilet danyin wanka. Ɗakinshi na dawo da abincin kuma har yanzu bai fito ba , ajiyewa nayi na fice a ɗakin , gaf zan shiga ɗakina ƙanwarshi mai bi mishi ta tareni tayo zugar ƙawayenta saida kowa ya zageni fes a cikinsu sannan ƙanwar tashi ta ansa tare da fara sokamin zagi waini har na isa saboda ni ɗin banza Yaya DK ya daki Aunty Rabiya waye ni bare ubana ɗan caca karuwa da aka saka a wasan caca su waye familynki ? Karuwan banza gaba ɗaya wace ce ke bare kuma ubanki duk cikar faɗin birnin katsina ? Waye ya tsaya miki ya ɗauremiki ƙugu kike iskanci , Dikko dake fitowa yace ni nine na tsaya mata dan hayaniyar su ta fiddoshi daga ɗakinshi jallabiya ce a jikinshi har yanzu jikinshi da sauran lema kuma itama kanta batayi tunanin zata sameshi gida ba , kuma Ashiru yaa fita da motarshi shi yasa ta ɗauka baya nan yaci gaba da cewa kuma itace tasa na daketa kuma kema saina baki kashin bala'e zaki fita gidan nan , ke har kin isa kizo har gidana kiyi ma matata takakkiya ? Kin taɓa ganinta taje cikinku ne ? Matata zaki zaga....... Dan baki da kunya ? Ashe nima zaki iya zagina idan kika samu dama ko ? Ya fara fita yanayinshi yana An mata zaki ga wanda ya tsaya mata ? Tou ni nine na tsaya mata ya nuna kanshi cewa to gani kin ganni ya akayi ne..... ? Kyarma jikinta ya farayi tace Yaya ..... Daka mata tsawa yayi kafin ta faɗi maganarta yace zanci ubanki kika sake kiran suna na , kayi haƙuri , tou daga yau naji labari ko na sake ganinki gidana saina zaneki bata haƙuri , kallona tayi tare da cewa yi haƙuri cikin ladabi , kallon Dikko nayi ya ɗagamin gira , ba komai na bata ansa , hanya ya nuna musu tare da cewa kuje , da sauri suka gangare babu wanda ya sake magana ko waiwayenmu har suka fita , zo muje ya faɗa tare da wucewa gaba nabi bayanshi. Har ya gama cin abincin baiyi magana ba bayan ya gama ya ɗauki wayarshi ya fara dube² tare da ɓalle botir in gaban rigarshi ya shafa kanshi da yanayin damuwa kallona yayi sannan ya sake kallon wayar yace da ina da ina kikaje da bana nan ? Dam׳ naji gabana ya faɗi kafin inyi magana harya ƙufule yace bakiji ina miki magana , daburcewa nayi nace naje goruba , daga nan sai ina ya faɗa yana tsareni da ido , ƙyarma muryata ta farayi nace sai ina naje tou ? Ina tambayarki kina tambayata ? Kayi haƙuri , miƙewa yayi yace inyi haƙuri.....? Tou kinma san abinda kika yi kike cewa inyi haƙuri kenan ? Nima miƙewa nayi na fara kuka , koma ki zauna idan kika fita ɗakin nan saina kasheki............ Karka kasheni Dikko , ke......... Rufemin baki wato saboda kin ɗaukeni mahaukaci shi yasa kikaje wurin Yazeed kai............ Saina kashe ki........... Da gudu na fita ya biyoni yana ihu ni zaki tona ma asiri saina kashe ki........ Na kusa shiga ɗakina naga kafin in shiga in rufe ya riƙeni da gudu na hau ƙarfen bene na sulala ƙasa suuuuuu kai............... Saina kashe ki......... Maimakon ta fita waje a taimaketa sai tayi tunanin a dole nan ciki zata sama ma kanta mafaka wata irin kururuwa yakeyi mai tada hankali yana maimaita saina kasheki.............. Yana wata irin zabura , da gudu ta sake komawa sama ya sake binta har yanzu bai kamata ba saina kashe ki........ Kawai yake faɗa , irin na ɗazu ta sakeyi amma sai sautsayi ya gitta...... Wani irin ihu Dikko yayi ke....... Karfa ki faɗa ki mutu , na fasa bazan kashe ki ba , An mata ya nufi inda take tafiya zuwa ƙasa dan riƙeta amma kafin ya riƙota takai ƙasa.......... Kai............... Saina kashe kaina zai faɗa ƙasa aka riƙeshi , riƙe kanshi yayi da duka hannayenshi biyu yace kai......... Wai , wai , wai Allahna wayyo................... Saina kashe kaina.......... Wasu suka riƙe Dikko dake wani irin ihu wasu suka tafi wurin Sultana da ko motsi batayi , An mata........................ Ya faɗa tare da faɗuwa ƙasa somamme. Nabeela Mardiyya da Jiddah da suka shigo yanzu gaba ɗayansu wurin Dikko suka nufa suna kuka , ita kuma Sultana masu aiki mata ne akanta maza na tsaye kowa yana tunanin abinda yayi zafi har Dikko ya jefota daga saman bene ya kasheta , cikin ƙanƙanin lokaci gidan ya cika da "yan uwansu Dikko wannan karon har wanda suke Baba ɗaya ba'a bari ba kowa yazo tunda sharri ne ya samu dan duk wanda aka faɗa mishi cewa akeyi Dikko ya jefo matarshi daga saman bene ta mutu , abiyar zaman Momy kuwa cewa takeyi tunda ya kashe shima sai an kashe shi hukuncin wanda ya kashe shima kisa ne , yaro ne yana iskanci ba'a iya hanashi ya zama ɗan ido kar akayi masa magana ya ragu , tou wallahi yadda ya kashe ɗiyar mutane shima sai an kashe shi Allah yasa mun gani da idonmu kuma saina tsaya ma iyayen yarinyar nan shari'a daga nan har a tashi duniya sai na tsaya akan kafafuwana an kashe Dikko tunda ɗa baifi ɗa ba. "Ya " Yanta mata tace su ɗauko Sultana , Momy ta kalli Rabiya tace karku bari ta fita da yarinyar can tunda babu wanda yake da tabbacin mutuwarta dan ko bata mutu ba zata iya kashe ta yadda ta shirya lafiyayen sharrinta , gaba ɗaya wurin ya gauraye da hayani har bakajin maganar wani yayin da matar Dady ke cewa sai an tafi da Sultana , Rabiya tace ita a suwa ? Dan taga Dikko yana sume har ta samu bakin magana ai zai dawo , jin zance Rabiya yasa ta kira Dady ta faɗa masa Dikko ya jefo matarshi daga sama ta mutu , Salati Dady yayi cikin tashin hankali , babu daɗewa shima ya bayyana a gidan , ga Dikko kwance a dai² inda yaso ya riƙo Sultana aka riƙeshi ya suma , ga Sultana a ƙasa kwance kuma har yanzu ba'a taɓata ba daga yadda ta faɗa haka aka barta , Dady bai fara zuwa wurin Dikko ba wurin Sultana ya tsaya ya kalleta cikin tausayi sannan ya kalli "yan ɗayan ɗakin yace su ɗaukota su Ashiru kuma suka ɗauko Dikko suka fita daga palon aka bar Momy da " ya "yanta mata "yan rashin kunya masu irin baƙin haƙin halinta...... Fita Momy tayi tana cewa ina za'aje mata da ɗa ? Cikin ɓacin rai Dady yace ashe kina sansa ? Tio Babana ba ɗanki bane ba nawa ne , ga "ya "yanki nan na ɗauki nawa na bar miki naki wa'anda kike so ni ina sansa kuma bana san abinda zai sameshi insha Allah bazai mutu ya barni ba saina mutu na barshi duniya daga haka bai sake magana ba aka sakasu a mota suka fice daga gidan..... Wannan ranar ta tuno ma Momy da zuwan Suwaiba gidansu , Dikko yana da rigima haka kawai yaje ya ɗauko musu wannan "yar iskar ya tausaya mata amma ita ta saka masa da sakayya mafi muni a rayuwa ta gudu ta barshi da masifa dake neman kaishi ƙiyama babu gaira babu dalili , ya taimaketa amma ta zama silar warwarewar rayuwashi gaba ɗaya kuma ta gudu ta barshi da hauka shi ba mahaukaci ba , jiki a sanyaye ta dawo palo wuri ta samu ta zauna ta zabgaga uban tagumi tana matse hawaye. Suwaiba kuwa bayan tafiyar Dikko kuka tasha harta gode Allah , bakin gaskiyarta ta kasa faɗin sunan wanda Dikko yake so ta faɗa masa to ya akayi ta kasa faɗa shine tambayar da take ma kanta bayan a zuciyarta tasan sunan , tana wannan tunanin ne Al ' Ameen ya bayyana , tana ganinshi ta fara kaine kuma saina faɗa masa , dariya Al ' Ameen yayi tare da cewa haba "yar gurgus na kulle zuciyarki bakinki baya iya faɗar Al ' Ameen , kuma idan baki sani ba nine na harbeki kika zama gurguwa , abinda ya kawoni wurinki shine fatan sauka lafiya ayi rayuwar lahira lafiya ina nan saina ga bayan mai gida saina kashe shi na kwashe kaf dukiyarshi sai nayi rayuwar duniya mai daɗi nahau manyan motoci in ƙaro mata 3 masu zafi naje duk sauran ƙasashen da bai kaini ba , Waye yace maka ina nan ne ? Ni na sani da kaina dan nasan dama bazaki wuce nan ba , ya baki daga nan zuwa gobe mahaukacin banza yana can yana nema na a gari kamar wani lusari baisan ina tare dashi ba , daga wurin mahaifiyarshi nake na sauke zango na a wurinki , naira miliyan biyu aka bani naje na haɗo sammu nine na bashi a banci kuma a lokacin ni ɗaya nake tare dashi a ƙasar London , kuma nine na kashe matarshi har lahira , ni nayi komai kuma nine zan kulle bakin furta zan kashe ki................... Zan kashe ka.................. Saina kashe ku............... Saina kashe kaina............ Haba mai gida kayi haƙuri zaka mutu saurin me kake ? Mutuwar fa yana gaf da kai da zaran na haɗa auren nan aka samu haihuwa sai mu kashe ka kaga mun hutar da kai faɗar zaka kashe kanka Al ' Ameen zai aika ka zuwa duniyar mutuwa , Hajiya Suwaiba na wuce sauka lafiya zuwa lahira , murmushi yayi tare da ci gaba da cewa zai dawo yana zuwa zaice saina kashe ki.......... Haka zai faɗa Al ' Ameen baya faɗuwa dan haka sai ya kashe ki kinga na ture wata matsalar aiki ya ragemin yana faɗin haka yayi tafiyarshi yana dariya. Fashewa da kuka ta ƙarayi cewa Allah zai tona maka asiri babu daɗewa azzalimi maci amana , murmushi Al ' Ameen yayi bai juyo ba ya ɗaga kafaɗunshi 🤷🏻‍♂ ya fice da sauri , kifewa Suwaiba tayi a wurin kuma sunan Al ' Ameen yaƙi zuwa a bakinta , Tunanin irin halackin da Dikko yayi mata ya dawo kanta , wurin da take taji yana juyawa yayin da zuciyarta tace ta yanka kanta ta rubuta *AL ' AMEEN* a jikin bango idan Dikko yazo zai gani , wayyo Allahna , ta goge hawaye tare da komawa ta kwanta a wahalce ta fara tunanin rayuwar baya................ !!! Kuyi haƙuri da wannan don Allah , na farko dai banda caji , na biyunsu kuma ina da hidima wanda ba lallai ne gobe zuwa jibi kuji ni ba , amma idan na samu yadda nake so zanyi ko kaɗanne fatan zaku gafarceni....... 27/11/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 83 Da farko dai Dikko mutumin kirki ne a wurinta , nagartaccen namiji mai zama , tsayayyen namiji mai lafiya da cikar zati da kwarjini , jarumin namiji ba lusari ba , idan akace mutum bashi da mutunci ko rashin ragowa idan dai baiyi maka ba tou kai mutumin kirki ne a wurinka , duk halin mutum na kirki dana banza idan dai bai nuna a kanka ba tou bazaka sheda mugayen halayenshi ba , Dikko yana da mutunci amma shi baya shiga sabgar kowa , ko a baya data sanshi da lafiyarshi tasan baida haƙuri haka kuma bai ɗaukar sakarci da shirme , kayi ta magana yana jinka saidai yayi kunnen uwar shegu dakai , yana da tausayi sosai amma yafi tausayin mata a rayuwarshi. Baya dariya baya murmushi idan kuma ka cika shi da surutu zai tsare ka da dara²n idanuwanshi har sai kaji tsoro kai da kanka zaka lallaɓa ka tashi ka kama gabanka , baya sabgar mata baida budurwa ko ɗaya amma yana da dawakai masu lafiya da ƙoshi , babu hoton mace a wayarshi amma zaka iya samun hoton doki babu adaɗi a wayarshi , ya yadda da doki sosai kuma bayajin wahalar sayenshi baida magana sai ta doki dan ko yana zaune da abokanshi idan suna fira masu zancen "yan mata sukeyi , masu mata suka labarta nasu shi zaice dokinshi kaza² , sai zancen kayan doki maganar polo kalamanshi dai suna tsayawa akan doki ne kawai da abinda ya shafi dokin , idan ance masa shi baya budurwa zaice shi baya san raini dan yaji yadda su kansu suke magana akan matan , kuma yana ganin yadda matan gidansu ke ranfa da maza , gashi kuma suna faɗar irin halayen da matan ke musu , kanaji da girmanka da shekarunka ƙaramar yarinyar daka haifa tayi maka rashin kunya shi duk sabgar da zata zo da raini ko rashin kunya baya ciki shi yasa bai shiga sabgar kowa saita doki , dan doki idan ya sanka kaine kake cidashi kake shadashi akwai ragowa tsakaninka dashi amma idan ya tashi aure zai auri cikakkiyar mace data san kanta mai shekaru da yawa shi gaskiya bazai auri "yar ƙaramar yarinya ba dan idan ya auri yarinya shi kanshi saiya raina kanshi ƙaramar yarinya mai ƙananan shekaru bata dace da rayuwarshi ba... Murmushin ƙarfin hali Suwaiba tayi tare da goge hawayen dake kwance a saman fuskarta , a bayyane tace ashe dai da rabon sai ka auri ƙaramar yarinya , yarinyar ma ta ƙasan² shekaru , yaushe kuka haɗu kukayi soyayya har aka kai matakin aure .....? Hmmm koma dai miye Suwaiba ba damuwarta bane ba , Marin birich a jahar Lagos , madakata ce ta mutanen da basajin magana ko kuma nace wanda suka gagara , madakata ce ta mutanen da suka fi ƙarfin gida ko suka aikata ɓarna saisu gudu daga jahohinsu sai suyi ma kansu masauki a wurin domin tsira da rayuwarsu , mazauna wurin gafurtacci ne kuma gagararri wanda suka ansa sunansu wurin rashin jin magana ko iskanci. Duk irin matsalar da kaje da ita a wurin sai kaga wanda ya shafe taka ya burjeta murus , idan kuma zancen iskanci ne da duk wata ƙaramar rashin kunyarka tou fa daga wurin dai an rufe littafi , idan ko ke karuwa ce a iskanci har kika je Lagos kikayi rayuwa a ƙarƙashin gada tou lallai iskanci daga kanki an kashe boss , duk namijin da yaje wurin shima dai abin kwatance ne tou ina ga mace kuma....? Matsalar iyaye itace ta kaini garin Lagos kuma nayi rayuwa a wurin dana faɗi sunanshi daga sama , auren soyayya nayi dani da mijina wanda ni dai Allah ya sani dama bawai wani cancan nake jinshi a raina ba , na aureshi ne saboda girman dukiyarshi wanda mu a zuri'armu attajiri ne sosai dan talaucin mu , ni bana sansa kwata² amma ina nuna masa soyayya saboda kuɗinshi shi yasa yayi tunanin ina sansa har a zuciyata , Tou mundaiyi auren na soyayya kamar yadda mutane suke kallo a zahirance amma a baɗinance ni a wurina kuɗinsa na aura , tunda aka ɗauramin aure dashi iyayena sukayi min huɗuba cewa nadai gansu a gidan haye suke zama tou inyi ƙoƙari na ƙulla musu mazauni kafin mijina ya sakeni dan masu kuɗi basu cika zama da aure ba nayi ƙoƙari na gina kaina kafin yayi min wurgin kashi a shara , a nawa ganin nidai ina kallon anyi ma masu kuɗi fahimta ce mara kyau domin auri saki hali ne , kamar jini haka yake gudana a cikin zuciyar mai irin ɗabi'ar danshi auri saki babu ruwanshi da mai kuɗi babu ruwanshi da matalauci haline ne kuma yana ƙarkashin zuciyar maishi. Tunda aka kaini gidan mijina duk ƙarshen sati sai an aiko ƙanina daga gidanmu wai in bada kuɗin zubin adashe , akan me zance babu ? Dan ko shi ƙanin nawa idan yazo sai ankai ruwa rana nake haɗa masa kuɗin motar komawa dan mijin dana aura mannanu ne bashi da alkairi ko kaɗan dan ko kuɗin cefane ya bada idan ya dawo sai anyi lissafi saiya ƙwaƙwale canjin shi tass ya barni zero ɗina. Mahaifiyata data ga kullum ƙanina yana zuwa yana dawowa babu kuɗi satin gaba yana zuwa ta tattaro ta taho da kanta , nasha zagi sosai tace ina nan na shige cikin a c na manta da ita , ina nan kullum sai naci nama nasha ruwan lemu , da safe naci shayi da burodi na barta a daura tana can kullum safiya tana karo da zazafen tuwo , taɓarya zata kasheta saboda daka da wahalar rayuwa , ina shafa ruwan sabulu mai ƙamshi idan zanyi wanka tanayin wanka da garin omo sai Allah ya tsenemin tunda na barta take shan wahalar rayuwar. Na nuna mata cewa kuɗin bafa a hannuna yake ba nima a ƙarƙashin wani nake sai abinda aka bani , kuma bani nake da alhakin kula da ita ba taje tayi haƙuri taci abinda Allah ya hore mata tace bata yadda ba dole irin abinda naci irinshi zata ci , kuma saina shiga adashen nan duk abokan aure na babu wacce bata mallaki ƙaddarar dabbobi ba dan haka nayi ƙoƙari na samu. Duk yadda naso na nusar da ita ƙin yadda tayi wai a dole saina samo idan ya shiga wanka in riƙa lalube masa aljihunsa dan wallahi ta aiko satin gaba bata samu kuɗin nan ba kashe wannan auren zatayi dan bata ga amfanin aure babu ci gaba ba , nace tou , data tashi tafiya saida ta tunbiji kayan abinci shinkafa taliya makaroni kuskus ta ɗauke sauran madararmu duk abinda ta gani gidan saida tayi gaba dashi buhu guda ta cika na shinkafa da abinda ta tattara daga gidana. Bayan mijina ya dawo ya shiga store ya fara dube² dama wannan shine al'adarshi duk daren duniya idan ya dawo saiya duba kayan abinci , idan kuɗi ya bani saiya anshi canji , idan naman abinci ya kawo saiya irgashi , tun daga store ya fara faɗa wai yau yaga abinci yayi ƙasa bayan yabarshi da yawa kafin ya fita , ina na kai mishi abinci ? Nace ina kuwa za'a kai abinci inda ya wuce cikin ciki........? Karfa na raina masa hankali haka yai ta zazzaga ruwan wulaƙanci karshen film in dai yace min dangi ɓarayi sata kamar ɓere zai maida abincin ɗakinshi duk safiya zai auno min gwangwani ɗaya tunda na zama ɓarauniya ba ruwanshi da baƙo kuma idan taliya ya bani ita zanci daga rana har dare , in shinkafa ne itama haka , ya kwasa rashin mutuncin shi daga baya ya kwashe komai zuwa ɗakinshi , binshi nayi ina bashi haƙuri ya basar ya shige toilet , yana shiga naci gaba da bashi haƙuri ina ɗaga kayan daya cire , kayi haƙuri don Allah , a dai² lokacin dana ƙwale² aljihunshi tas , bazan ƙara ba , a dai² lokacin dana ajiye wando na ɗauki rigarshi , na bari don Allah na kwashe kaf kuɗin masu yawan gaske na fita daga ɗakin , ban nufi ɗakina ba na nufi bayan gidan na tona rami na rufe su na maida busashshiyar ƙasa na rufe nayi ma wurin alama da tsinken tsintsiyar kwakwa..... Ɗakina na koma naci gaba da kuka ban ƙarawa , a haka ya sameni yana ina kuma kika kaimin kuɗin na , rigima ya kaure tsakaninmu tashin hankali na kada Allah maimaita mana anyi shi , kuma tun daga wannan ranar ban ragawa aljihun mijina ba , ba aljihu kaɗai ba ko wanka ya shiga haka zan bincike kaf ma'adanar kuɗinshi , kafin wani lokaci na ƙware da wurin iya sata , kuɗi kuwa duk satin duniya sai anzo an ansa a gidanmu. Mijina kuwa sai ya daina shigowa da kuɗi gida ya riƙa barinsu a mota , dana duba naga babu komin dare saina lallaɓa na cire makullin naje na buɗe na kwashe kaf kuɗinshi , koda ya kai ƙarata gidanmu iyayena cewa suke aljannu ne dansu "yar su ba ɓarasuwa suka haifa ba , suka ɗauremin ƙugu naci gaba da tsula tsiyata.... Daga dai ƙarshe mijina ya samu kwanciyar arziƙi dan haka mahaifiyata ta murje idonta tas ta kashe auren nan mijina yayi kuka ya shiga tashin hankalin rabuwa dani ni dama can bana wani sansa , bayan mutuwar aure na gama iddah na sake auren wani amma baikai mijin dana baro rufin asiri ba , shima haka na taso tattalin arziƙinshi saidai na ƙareshi kaf nayi gaba abuna , kuma har zuwa wannan lokaci iyayena basu sayi gida ba , aure na gaba mijin wayayye ne domin shi a banki yake ajiye kuɗinshi ban wani daɗe ba na kashe auren dan zuwa wannan lokacin nima na goge da idan babu malasa gaba nakeyi abuna , bayan wani lokaci na sake aure na auri wani manomi bagidaje ne dan haka shi amfanin gonar na riƙa siyarwa , shima ya gaji ya sakeni daga haka ban sake aure ba dan duk wanda yazo ce masa akeyi ni ɓarauniya ce , wannan dalili yasa ban sake auruwa ba , A gida zaman dai babu daɗi dan banda aure kuma banda inda zan samo kuɗi aka fara hantara ta a gidanmu , dan haka na fara sata da maƙota cikin ƙanƙanin lokaci na zama mashahuriyar ɓarauniya a cikin anguwarmu , ko shaguna naje sayayya danaga ba'a kallona sai inyi sata in gudu.... Duk wannan ƙoƙarin da nakeyi a haka banyi ma iyayena ba dan haka na haɗa dai da "yar bariki ta , ina karuwanci ina sata kuma har yanzu basu sayi gidan zama ba , ganin haka yasa idan na sato na daina basu naci gaba da sata ina ɓoye abuna , wulaƙanci a gidanmu kuwa na dare daban na safe daban , a wurin iskancina na haɗu da wani babban attajiri shine ya ɗauki hayata ya tafi dani Lagos , a ranar daya kwana dani a ranar na ɗauke jakar kuɗinshi na gudu , Ban bar Lagos ba na nemi matattarar "yan iska wanda suka gagara shine aka bani tayin marin birich ranar da naje da ƙarfin bala'e aka ƙwace kuɗina , naga iskanci da ƙaryar rashin kunya , naga dabar data girmi irin wacce nake gani a garin Daura , naga karuwancin daya girmi nawa naga salon sata wanda ya girmi tawa , wurin yamin nayi zamana da safe zan fita cikin gari nayo iskanci na dawo , wata na biyar a wurin mai hali baya barin halinshi nayi sata naci bugun rabani da yaro kuma sunce sai sun kasheni haka suka ɗaureni a jikin ƙarfe suka watsamin fetir suka cinnamin ashana dan sunfi ƙarfina ina ji ina gani zan mutu kuma gani ɗaure , a dai² wannan lokacin ne Allah ya kawo Dikko , dashi da abokinshi shima kuma kanshi baisan haka wurin yake ba yayi rakiye kawai ni bansan abinda yakai su shi abokin nashi ba. Dikko yasha dariya sosai sannan ya ɗauki ruwan wani gahurtaccen ɗan daba daya zuba a bokiti zaiyi amfani ya sheƙamin a jiki wutar ta mutu , tun bai gama zuba ruwan ba ɗan daban yasa yaranshi suyi ma Dikko gunduwa² wanda ya kunna min wuta kuma yasa yaranshi su sake tashin wata wutar amma akan Dikko , saboda wurin gungu² ne na sansasanin "yan iska , kowa da zugarshi kuma kowa yana da yaranshi mutanen dai sun kasu kashi daban². Wanda Dikko ya rako ya ruga da gudu ya duƙa gabansu yace su rufa mishi asiri Babanshi yake neman gwamna karsu kashe shi , ashe ma basu zama gwamnan ba ? To ko ɗan shugaban ƙasa ne sai sun kunna mishi wuta , su kuma dabar wanda aka ɗaukar ma ruwa suka ce ko gwamnan ne sai sun fyeɗeshi harya isa ya shigo da'irarsu ya haresu ? Shi kuma Dikko yana kwunce Suwaiba daga ɗaurin da akayi mata kuma har yanzu bai daina dariya ba..... Kawai dai anyi tashin hankali mara kyau dakel aka samu aka fitar da Dikko daga wurin da taimakon wanda abokin Dikko yazo wurinshi , kuma duk tashin hankalin nan da Suwaiba ya tafi , tun a mota Dikko ke kuka wai yanajin tausayin sauran matan da aka baro shi wannan wane irin rayuwa ne ? Me yasa mata zasuyi iskanci wai.......? Ya bani shidai baya so yaga mace tanayin abu da bai kamata ba shi dai zai koma ko zai mutu saiya fitar da duk wata mace a wurin , abokinshi yace tou ka rufawa kanka asiri dan ka sake ka koma wurin nan saidai wani ba kai ba , Dikko da kafiya cewa yayi saiya koma su kashe shi , duk haƙurin da aka ba Dikko ya kafe kai cewa saiya koma a kashe shi..... Nice na bashi haƙuri nace kar ya koma dan na fahimci shi ma'abocin tausayin mata ne amma yana da kafiya idan ya duƙe akan abu sai yayi , nace kayi ka haƙuri ka ƙyalesu duk wacce ka gani itace taje da kanta take zama , kuma idan ka koma zasu nemeni su kasheni , daga haka yayi shiru dai bai sake magana ba , ni bansan abinda abokinshi yaje yi ba , kuma bansan dalilin da yasa shi Dikko yayi rakiya ba , dalilina na bashi haƙuri nasan idan har tsautsayi ya maidashi sai sun kashe shi har lahira.... A cikin jirgi muka zo kano daga Lagos jikina yana ta raɗaɗin wutar data ci jikina sama² , a kano aka ɗaukemu a cikin wasu irin zafafan motoci har katsina , saida ya kaini asibiti aka dubani. A gidansu Dikko kuwa mahaifiyarshi tayi tashin hankali akan bazan zauna ba , ta zage shi so babu adadi tunda yace kiyi haƙuri Momy zata zauna bai sake magana ba yaci gaba da sabgar gabanshi , ita irin mutanen nan ne masu ƙyanƙyamin mutane , ankai ruwa rana Dady yace tunda Babanshi yace saina zauna babu wanda ya isa ya hanani zama. Tunda nake zaune a gidan banda wata damuwa domin Dikko yace duk abinda nake so na faɗa masa , shike ɗauke da duk wata ragama tawa duk abinda nake so zan rubuta a rubuce na bada akai mishi , baida hankali wurin kyautar kuɗi hannunsa a sake yake yana da alkairi sosai amma bashshi da mutunci idan aka taɓoshi duk gidan sai kowa yaji masifarshi yana iya sati yana masifa akan abu ɗaya bai gaji ba dan bai gajiya da fitina gashi da kafiyar bala'e idan ya duƙe kai akan abu babu gudu ba ja da baya.... Tabbas Dikko yamin gata yamin halakci fiye da tunanin yadda mai tunani zaiyi zato , ko tafiya yayi ya dawo haka zai jibgomin tsaraba ta sutura saboda duk yadda zan faɗi gayun shi bama zan iya musultawa ba , yanda yake ɗan gaye saida ya tabbatar ya maidani "yar gayu ta gaban jarida , kuma nayi masa koken rashin mazaunin iyayena shi ya tsayar dani akan ƙafafuwana lokaci guda nasha gaban duk wani mai tayarmin da ƙura ya kulleni da motar hawa ta abun kwatance a idon duniya..... Amma sai na ƙulla aminci da abiyar zaman mahaifiyarshi , ita tana jawoni a jikinta saɓanin mahaifiyar Dikko dan haka aka shiga neman kai ƙarshen rayuwar Dikko dani , itace take aikena nemo mata asiri tana san ganin ƙarshen Dikko tace yadda itama bata da namiji babu wacce ta isa tayi namiji a gidan , tun da aka haifi Dikko take neman sa'arshi bata samu ba kuma baza ta daina ba haka kuma bazata gajiya ba har sai ranar da Dikko ya daina numfashi. Ina cikin ƙulun bitar bin malamai da bokaye Al ' Ameen ya saƙo cikin aiki ta hanyar bina da yayi ban sani ba har inda zanje , bayan ya tabbatar da komai yazo ya zayyana min hankalina ya tashi kuma na firgita amma sai yacemin na haɗashi da matar Dady na faɗa mata cewa shima yana san ganin bayan mai gida ne kuma yana shirye akan zai bata taimako ko wane iri take so. Tayi na'am da haka itace ta bada kuɗi Al ' Ameen yaje ya samo asiri aka haɗa manyan masifa aka binne a wani daji sai iskokai suke gadi ana biyansu da jini duk karshen sati , wanda kuma ake so yaci a abinci shine idan yaci zai riƙa haukacewa duk lokacin da yayi fushi yana maganar kisa , iskokai kuma sune zasu riƙa shafarshi , Al ' Ameen yace zai iya bashi , tou shine maganin daya bashi a London , dan rigimarshi shine suka juya abun da faɗanshi shi yasa duk lokacin da yayi fushi sai ya riƙa cewa saina kashe ka................ Farkon asirin rashin lafiya ya farayi kaɗan² Dady yasa aka dawo dashi nigeria baida lokacin tafiya ya tsaya yana ta siyasa , Dikko yayi ciwo na tashin hankali babu wanda ya bashi tashi a duniya , saida aka saka mishi robar hanci kowa ya haƙura dashi , shine Dady yaita rashin lafiya sakamakon ciwon Dikko har ya samu ciwon zuciya saboda tunani , aminin shi Dady shine ya gano ciwon Dikko asiri ne ya kuma faɗawa Dady ciwon Dikko bana asibiti bane ba dan wasu Allah ya basu lilimin gane sihiri , kuma ya miƙe tsaye ya gano cewa Dikko ana so ne ya mutu ta ko wane hali idan bai mutu da kanshi ba yayi kisa sai a yanke mishi hukuncin kisa kuma shi ya samo duk wannan magungun nan da ake mashi amfani dasu , Abinda yasa Dikko yasan ina da sa hannu a rashin lafiyarshi , mai aikin Momy taji muna magana da Al ' Ameen a palo ni kwata² bansan tana nan ba kuma bansan ta shigo ba , Al ' Ameen yana magana ƙasa² yake faɗamin boka yace abokin Dady ya miƙe tsaye akan saiya gano duk wani mai sa hannu a rashin lafiyan mai gida shine boka ya bada wasu layu yace aje a tsakiyar gidan nan a rufe ana rufesu an rufe zancen , zaici gaba da magana aka kirashi a waya ya fita bayanshi na bi muka bar ɗakin gaba ɗayanmu , tou itace taje ta faɗawa Dikko iyakar abinda taji amma bata san da waye nake maganar ba , shine yazo yace min ni bazaimin komai ba amma in faɗa masa ko waye yake da saka hannu kuma waye zai binne layu a cikin gidansu , kafin inyi magana shine ya nufi wurin Mom inshi wai tazo taji da kunnenta an haɗa kai da Suwaiba an cuci rayuwarshi sai idan yayi magana ace bashi da haƙuri ya cika masifa , sanin halin Dikko yasa kafin ya dawo na gudu dan nasan duk da yace bazaimin komai ba nasan sai yayi idan har ya riƙeni mai kwatata a hannunshi sai Allah shine na gudu Dikko baisan daga inda nazo ba kuma baisan ina zan koma ba tsintoni yayi kuma na gudu abuna , ashe Al ' Ameen shine yayi sanadin zamana gurguwa , ya bini ya kasheni gudun karna tona musu asiri , shine ya ɗiɗɗirka min alburusai a ƙafa , wanda na faɗi bansan ina kaina yake ba saidai na gannin da yankakkin ƙafafuwa. Bansan Sultana ba ina jinya aka ajiyemin kwalba da waya , na kira Malamin na bashi shi kuma malamin ya kira Bello ya bashi bayan sunyi ciniki ya ƙara masa akan farashin da ita matar data bani ya maida ma Bello kwalba , bansan Sultana tana auren Dikko ba , abinda yasa kuwa na koreta daga wurin nace mata bana san matsala ta sake shigowa rayuwata dan bansan ita kuma abinda rayuwarta ta dosa ba.......... Lahaula wala kquwwata illah billahil 'aliyyul azeem Dikko ya furta suna fita daga cikin gidanshi ya dawo daga sumar da yayi , a ɗiymuwance yace ina ne nan ina kuma zamuje ? Kallon kanshi yayi sannan ya kalli inda aka kwantar da kujerar gaban mota Sultana kwance , laluba aljihunanshi yayi sannan yace ina wayoyina ? Ya tambayi Ashiru , ban ɗauko ba , to koma , da rubos Ashiru ya koma har ƙofar get in gidan , yana tsayawa Dikko ya fita da sauri yaje ya ɗauko wayoyin ya dawo , yana shiga mota ya kira waya , bayan an ɗauki waya yake sanar da M D in asibitin yana da maralafiya suna zuwa babu jimawa dan a shirya ma zuwan nasu , ya kuma faɗa masa abinda ya faru , na cikin wayar yayi magana shi kuma bai sake magana ba ya tsinke kiran , kallon Sultana yayi yaga tana ciccire² ko fizge² kawai dai { Convulsion } salati yayi tare da cewa kai bi tacan , da sauri Ashiru ya juya sitiyari yana cewa Dady yace mu haɗu dashi gida , Dikko yace ba gida ba takamin motar nan da gudu kayi ta can yana nuna mishi hanyar da zaibi da hannunshi idonshi yana kan Sultana , gudu Ashiru yake falfalawa amma Dikko cewa yakeyi kaje ׳................ Ƙannenshi "yan ɗayan ɗakin dake binsu suna ganin Ashiru ya canja hanya suma suka bi bayanshi da gudu kamar yadda suka ga Ashirun nayi. Dikko yana tsinke kiran M D ya kira doctors team on call su tanaji ɗaki a amenity DK yana zuwa da mara lafiya kuma su shirya ma zuwan mara lafiyar da zai kawo. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iya asibitin ƙashi kuma har yanzu Sultana bata daina fiffizgewa ba , tuni an shirya ma zuwansu a saman ɗan gadon da ake ɗaukar marasa lafiya aka ɗorata aka shiga da ita cikin accident and emergency , Taimako na farko da aka fara bata allura akayi mata diazepam dan dakatar da wannan fiffizgewar da takeyi , cikin mintuna 3 gaba ɗayan jikinta ya saki ta daina ciccire² a mintuna biyu da suka sake bugawa ta ɗauke gaba ɗayanta wato ta tafi bacci..... Daga A & E aka wuce da ita amenity nan aka bata ɗaki , cike da tausayi Dikko yabi Sultana dake kwance a saman gado da kallo mai nuna da yana tausayinta sannan ya juyo ya kalli Ashiru dake bashi waya Dady yana kiranshi , ansar wayar yayi sannan yace ma "yan uwanshi suje waje , tashi sukayi suka fita har Ashiru , magana yayi da mahaifinshi bayan ya gama ya zauna a gefen gado ya riƙo hannun Sultana yana shafa fuskarshi dashi , da hannunshi na haggu kuma yana shafa gefen fuskarta ya tsareta da kallo yana mai addu'a ubangiji ya taƙaita wahala yasa An mata karta samu damuwa , likitoci suma kuma suna jiran farkowarta su ɗauki BP { Blood Pressure } nata sai ansan abinyi........ A hankali ya mayar da hannun nata ya ajiye tare da cewa wannan fa shine wauta bugun mace da mangariba , wayarshi ya ɗauka yana ƙara kallon hoton da Yazeed ya turo mishi shida An mata , yayi rantsuwa kuma ya ɗauki alƙawari da zuciyarshi Al ' Ameen Yazeed da Suwaiba idan ya barsu sun huta bai yafewa kanshi ba , Allah dai ya bawa An mata lafiya............ 01/12/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 84 Kiran Ashiru ne ya shigo a wayarshi saida ya sake shafo fuskar Sultana ya ɗauki wayar tare da cewa ku shigo na gama , shigowa sukayi tayi dan duk wani yaron Dikko ya samu damar isowa a asibitin ɗakin baya anshe su , kallon Sultana Dikko yayi sannan ya kallesu yana cewa ku ɗan rage ina fitowa babu jimawa ya ƙarasa maganar yana kallon ƙannenshi yace ku kuma ku tafi gida kunji ngode , Yaya ai zamu kwana a nan ne inji Dady munyi waya dashi , murmushi Dikko yayi kaɗan tare da tsareta da ido irin kallon nan na rage gulof yace Dadyn yace ku kwana ? Ah Yaya ta daburce , ɗaure fuska yayi tare da cewa ku wuce ku tafi zanzo gidan anjima kunji ya ƙarasa maganar cikin sanyi. Tou Yaya kuzo mu tafi tana jan "yan uwanta cikin rashin jin daɗi , har zasu fita Dikko yaga kamar babu daɗi yace Ni'ima zo ita ya kira dan itace babba a cikinsu , dawowa tayi ta tsaya gabanshi tana cewa gani kanta yana kallon ƙasa , me ne ne ? Kinji kamar ban kyauta ba ko ? A , a , Yaya , kun tabbata ? Ya ƙarasa yana kallon inda sauran suke tsaye , gaba ɗayansu suka ansa mun tabbata Yaya , yawwa to ngode ku huta gajiya , yawwa suka faɗa suna Allah ya bata lafiya..... Momy kuwa bayan Dikko ya ɗauki wayoyinshi ya fita itama bin bayanshi tayi ita da zugar ɗiyanta wai tunda har akan Dikko Dady ya faɗa mata magana ta bar mishi shi kuma kada wanda ya buga mishi waya ya jajanta mishi yayi rashin lafiya sai Dikko ya gane bashi da wayau su mata ne kuma suna da yawa su haɗe mishi kai idan har suka bari ya rinjayesu zasu sha wahalarshi karsu sake zuwa gidanshi kowa yaje yayi rayuwarshi , idan yaji ya takura zai kira Dady ya faɗa mishi a lokacin ita kuma zata faɗawa Dady magana , Yazeed kuwa tunda ya tura hoto bugun zuciyar yaci gaba da halbawa ga abokinshi da aka kama wanda yayi ma Dikko magana ya fito dashi zasu shiga kotu , kuma ya daɗe da tura hoto baya goguwa kuma Dikko kaɗai ya isa ya tsaya mishi , matsala ta taho lallai haɗuwarshi da Dikko ba daɗi amma addu'arshi ɗaya Allah yasa Dikko ya saki Sultana..... Matar Dady kuwa ta shiga ta tsaya tsaff a cikin yinin ranar yau tasa Al ' Ameen ya samo mata lambar wayar Maman Sultana har gidan Kaka yaje ya samota da kanshi , bayan ya kawo mata ta rangaɗa mata kira babu daɗewa Inna ta ɗauka suka gaisa ta gabatar da kanta da cewa ita matar gwamnan katsina ce , Inna tace sai akayi ya kuma ? Dan ita a tunaninta Maman DK ce , ita kuma taci gaba da rattafa mata cewa Dikko ya jefo mata "ya daga saman benen kanta ya daki ƙasa saboda shi ya riga gangar jikinta zuwa ƙasa ta daku sosai idan ta yadda ta ɗauke "yarta kafin ya kashe ta dama tana ta shan wahalar dangin miji tsangwamar kishiya masifar miji ga duka ga zagi ga gori abundai ba kyan gani , bayan ta gama faɗar duk buƙatunta Inna tace tou ngode sosai amma ni bana tare ma Sultana faɗa a gidan aure kuma duk abinda mijinta zai mata ni bai shafeni ba ai ina sane da ita tunda nasan na haifeta , na barta ta gurzu da rayuwa dan dani da ita ba'a san gawar farko ba ta koyi rayuwa ta koyi riƙe damuwa haƙuri da rayuwa dan idan nice yau bani ce gobe ba dan nima kin ganni nan nima nabi mijina dan shine gatana kuma marufar asiri na , Sultana yanzu tabar ƙarƙashin iyayenta ta koma ƙarƙashin aure banda iko da ita kuma ita ba yarinya bace idan taji ta matsu tana da ƙafafuwa ta gudu , Allah ya bata lafiya....... Tana faɗin haka ta tsinke kiranta.... Hmmmm Inna kenan manyan duniya... Bayan awanni biyu da wasu "yan mintuna Sultana ta dawo , kamar mahaukaciya haka ta riƙa kallo tana motsa kanta kaɗan² tana kallo wurare , Ashiru yace sannu Hajiya , binshi tayi da ido ta kwalalo su sosai , Dikko dake zaune saman abin sallah ya tashi yaje wurinta An mata sannu , shima kallo tabishi dashi duk kamar dai mutane baƙi ne a wurinta sai kace wata sakara , Murmushi Dikko yayi tare da duƙawa kusa da ita yace sannu An mata , bata iya magana kwata² ta riƙe wuri ɗaya da ido tana kallo , ke me ne ne ? Baki ganni ba ? Ashiru yace mai gida ai sai a hankali zata ganeka , ƙarya ne ta ganeni mana ke ba kin gane ni ba ? Yayi maganar yana juyo kanta ta yadda kallonta zai dawo wurinshi , Kallo ɗaya tayi ma Dikko ta juyar da kanta gefe hawaye yana fita daga idonta , murmushi Dikko ya sakeyi tare da cewa bana faɗa maka ta gane ni ba , ɗan taɓe baki yayi yana cewa haushi na akeji baiwar Allah An mata ai koni saina baki shawara kiji haushin Dikko nima kaina haushin kaina nakeji , Ashiru jeka waje , Allah ya taimaki mai gida ya faɗa tare da fita daga ɗakin , Gefen gadon ya zauna yace An mata kiyi haƙuri don Allah na bari bazan ƙaraba ki gafarceni na yadda ni mahaukaci ne ya ƙarasa maganar hawaye yana fita daga idonshi , girgiza kai tayi dan bata iya magana , kinyi haƙuri ko ? Da kanta ta nuna a , a , haba An matana nasan kinyi haƙuri kuma bakiji fushi ba ke mai yafiya ce a gareni ki ƙara yafemin kinji An matana..... Ya ƙarasa magannar cikin yanayin neman gafara.... A , a , ta sake nunawa , hannunshi yasa saman idonta ya shafa ta rufe idon yace haba ƙaramar yarinya yau kuma Dikkon ake ma haka ? Abokin faɗan naki ? Kinyi min adalci kenan An mata ? Kiyi haƙuri mana nayi miki alƙawari bazan sake ba dan Allah ya riƙo hannun ta ɗaya ya soka "yan yatsunshi a ciki ya juyar da bayan hannun nata ya ɗora dai² saitin zuciyarshi ya danne da ɗayan hannun nashi yace kinji yadda zuciyata ke halbawa itama haƙuri take baki kiyi haƙuri An mata badan halin Dikko ba dan Allah ki rufamin asiri ki yafemin , karki yadda wani ya gano kinajin haushi na a gaban idon mutane ki nuna babu wani damuwa na yadda idan mun koma gida duk abinda kika ga dama kiyimin na yadda amma dan girman Allah idan kinga mutane ki riƙa sakin ranki karki wani haɗe rai kinji ko........ ? Shiru tayi batayi magana , kalli ya nuna mata idonshi jifa Dikko yana kuka ke bakyajin ƙunya ina miki kuka "yar yarinya ya ƙarasa yana murmushin ƙarfin hali , kallonshi takeyi har yanzu ba magana , hannunta yasa ya shafa gemunshi tare da ɗaga mata gira yace na bari matar Dikko ya faɗa da wani irin yanayi , duba wayarshi yayi da saƙo ya shigo , ɗaure fuska yayi ya goge hawayen tare da kama kanshi wai likitoci zasu shigo inji Ashiru ya turo mishi a waya , shima ya maida da to.... Hada Ashiru suka shigo , gaisawa sukayi da Dikko suna mishi yamai jiki , alhamdulillah daga haka bai sake magana saidai idan sunyi magana Ashiru yayi magana , bayan sun gama ɗaukar BP { blood pressure } nomal kamar yadda sukace aka wuce da ita C T Scan { Computered Tumography }. Dikko dai baije ba sai Ashiru da sauran tawagar suka bi bayan a can sun gama abinda sukeyi suka buƙaci sa hannun Dikko ya sa ya tafi ansa kiran Dady bayan ya gama sa musu hannun zai dawo kafin su gama abinda sukeyi. Dady yayi ma Dikko faɗa sosai akan me yasa ya jefo ɗiyar mutane daga sama ko yayi hauka ne ? Waye yace masa ana dukan mace ma tun farko kenan ? Shi me yasa yakeyin abu kamar ƙaramin yaro wai ? Haƙuri yaba Dady shi bafa shine ya jefota ba faɗa yayi mata kawai saita firgita , Dady yace tou waye yace ana firgita mace ? Me na faɗa maka akan mace tun auren ka da Sadiyya ? Tunda baka san ta ka sawaƙe mata ta kama gabanta kafin ka jawomin tashin hankali , Dady ba haka bane , tare shi Dady yayi cewa ka rufe min baki ya faɗa cikin faɗa yana ci gaba da cewa ka saki yarinyar nan , haba Da.... , cikin hayani Dady yace bana san maganarka ka bani takaddar sakinta har sai yaushe zan huta da halinka Babana.......? Hawaye ya zubo daga idon Dikko yace Dady ni banayin saki , sai kayishi Babana sai ka saki yarinyar nan bazan bari ka kashe yarinyar mutane ba , yanzu da , da tsautsayi shi kenan maganar nan bazai rufe ba yana can yana zagawa a gari ka kashe matarka , dama na Sadiyya har yanzu surutu bai tsaya ba akan ka tsafe yarinyar mutane banda hauka kuma zakaje da gangan ka jefo yarinyar mutane kai sarkin zuciya itama ta mutu ka zama matsafin kenan ko................? Shiru Dikko yayi kanshi yana kallon ƙasa lokaci bayan lokaci yana buɗe bakinshi kaɗan yana jan iska cikin ɓacin rai , Dady kuma ganin Dikko yana kuka yasa ya sassauta maganarshi yana cewa ni ne kaɗai na isa na faɗa maka gaskiya komin rashin daɗinta bana san abinda kake yi kaji ? Ya ƙarasa maganar cikin sigar lallashi , kallon Dady Dikko yayi sannan yace kaima mahaukaci kake cemin ko Dady ? Baban naka ne mahaukaci ko ? Ya faɗa yana ɗora kanshi a kafaɗar Dady yana kuka , tunda kacemin mahaukaci kowa ma zaice ni mahauka ci ne. Bakajin magana Babana nace bana san halin nan bazaka bari ba ya kake so inyi ? Kayi haƙuri Dady na bari bazan sake firgita ta ba , idan na sake ji kuma fa ? Sai kayi min faɗa ya ƙarasa yana kallon idon mahaifinshi cikin soyayya , murmushi Dady yayi shima Dikkon murmushi yayi tare da rumgume Dady yana dariya........ Aka daina zancen saki. Daga wurin Dady wurin Momy ya wuce duk sallamar da yayi bata ansa ba daga ita har "yan uwanshi kuma babu wanda ya kalleshi , Rabiya sai haɗe rai takeyi tana hararar bango , cikin rashin jin daɗi Dikko yace Momy meya faru ? Fuuuu ta tashi tayi ciki suma suka tashi suka bi bayanta , cikin yanayin damuwa Dikko yabi bayanta tana zaune a gefen gado sai ɓata rai take , wurinta yaje ya duƙa gabanta ya riƙe hannunta cikin lallashi yace baki lafiya ? Cikin faɗa tace lafiyata qalau , tou me yayi zafi haka ? Ya faɗa yana tsareta da ido , ban sani ba tunda kaje ka haɗani da ubanka kai ɗan zinari , me nace masa Momy ? Kace masa ni bana sanka , Rabiya tace Momy ji har kin manta kina masa magana shi yasa yake iskancin daya ga dama , cikin ɓacin rai ya leƙa ta gefen Momy inda Rabiya take zaune yace ki fita hanyata kafin in kwantar dake , Momy tace kwantar da ita Iliya ɗan mai ƙarfi , ƙannenshi ya kalla tare da cewa da Allah ku fita kuba mutane wuri , tashi sukayi suka fita wurin ya rage daga Dikko sai Momy sai yayyenshi , Rabiya tace to ka kwantar dani mara kunya , bai kalleta ba yace Momy me nayi miki ? Dikkon ne mai laifi a wurinki ? Haba Mamana waye zai haɗani dake ? Cikin sansanyar murya tace Dadynku ne yayi min wulaƙanci a gaban kishiya abin baimin daɗi ba , Rabiya tace ki kyale shi Momy ai duk shine munafukin , dunƙule hannunshi yayi tare dakai zamiya taja baya da sauri yace zan...... Riƙeshi Momy tayi tace ya isa ta faɗa tare da miƙewa taja hannunshi suka fita waje , Wurin motarshi suka tsaya tana masa magana wai yanzu ya daina santa a gaban idonshi ake mata iskanci a gidan nan yana kallo bayayin komai , yace Momy tou yanzu kuma me akayi miki wanda nayi shiru ? Ɗan ɓata rai tayi cikin rashin san zaman lafiya tace yanzu ba a gabanshi Bilki taje take faffaɗa mata maganganu marasa daɗi ba shine yayi shiru { abiyar zamanta } Dikko yace Momy dan girman Allah kiyi haƙuri babu yadda za'ayi ta faɗa miki maganganu kedai ki bari a zauna lafiya , sai kice anyi miki laifi kullum inyi ta hauka har an fara cemin mahaukaci , tou Dikko ƙarya nakeyi ta juya zata koma ciki da ɓacin rai tana gunguni , da sauri yasha gabanta yace shikenan zan mata magana , dariya tayi irin ta ƙasaitaccin mata , duƙawa Dikko yayi ta dafa kanshi tana cewa Allah yayi maka albarka , amin ya faɗa ta koma cikin ɗaki , A gajiye ya koma mota ya kifa fuskarshi a saman sitiyari shidai baisan abinda yasa gidansu akeyin bahaggon zama ba , sai zafin kishi da nuna "yan ubanci "yan wancan ɗakin basa san "yan wancan ɗakin , kowa ɗan ɗakinsu ya sani kuma shi yake so , sai kuma wani babban shirme idan ana faɗan kishi sai kowa ya shigar ma mahaifiyarshi wai me yasa mata sukeyin haka ? Shifa a tunaninshi matar uba uwa ce , ita kuma "ya "yan mijinta kamar itace ta haifa , gaskiya gaba ɗaya babu kyautawa su kuma wanda iyayensu basa gidan an ɗauki masifar duniya an ɗora akansu ga masifar aiki ga aike² kamar ba "ya "yan Dady ba sunayin wata irin rayuwa kamar "yan aiki kuma a hanasu ganin Dady saidai shi idan yana nan yake musu jagoranci zuwa wurin Dadyn , kuma shima Dadyn ya kamata idan baya nan ya dawo yaga kowa suma ya nemesu tunda ai yasan ya haife su , haka ya siyama kowa sabuwar mota amma duk wanda babu uwarshi a gidan babu rabonta , dole shine ya siya musu motocin da suke hawa Momy kuwa tace ina wuta ta jefa Dikko tayi tashin hankali saida aka kai ruwa rana suke hawan motoci , su Momy basa tunanin idan Dady ya sakesu ko suka mutu suka bar nasu "ya "ya wace irin rayuwa zasuyi ? Ya kamata a riƙa adalci a rayuwar "ya "yan da basa tare da iyayensu a gidan miji dan babu wanda yasan abinda gobe zatayi haka kuma babu wanda yasan maci tuwo sai miya ta ƙare , shi kuma yayi bakin ƙoƙarinshi wurin ganin Momy ta jawo yaran jikinta tana basu kulawa tarbiyya da tsaro kamar yadda take ba nata "ya "yan amma tace sam bata ƙaunar ɗan kishiya , tsoki yayi a dai² lokacin da text in Umar ya shigo Al ' Ameen ya shiga gidan gwamnati yanzu , dan yadda yasa aka sakawa duk wani motsin Sultana ido a baya haka yasa a sakawa Al ' Ameen..... Yana tashin mota wani text in ya shigo amma yanzu ba Umar bane Al ' Ameen ya shigo yana ɗakin Aunty , kai tsaye wurin Dikko ya nufa da gudun tashin hankali ɓacin rai yana hawa , tunda motarshi ta tsaya gaba ɗayansu sukayo waje hada Al ' Ameen da matar Dady ita tana cewa wannan wane irin iskancin tuƙi ne zaka zo ka tashi hankalin mutane , wani irin kallo Dikko yayi mata sannan ya kalli Al ' Ameen yace me kazo yi nan ne ? Shiru yayi baiyi magana ba , fitowa yayi daga cikin motar ya taka ƙafarshi ta baya ya dafa murfin motar da hannun damarshi na haggun kuma riƙe a ƙugunshi yace da kai nake me kazo yi nan ne ? Aike na tayi , zuwa ina ? A daburce yace ca ca can..... Ya nuna da hannunshi , har yaushe aka fara aiken ni ban sani ba ? Yanzu ne mai gida , tou ya akayi ka shiga ɗakinta ? Kai Dikko bana san iskanci ni zan aiki yaro kazo kana mishi tambayoyi , hannun daya dafa murfin mota ya ɗaga mata ba tare daya kalleta ba yace hajiya ba dake nake ba yanayin fushi yana gaf ki kama gabanki ko kimin shiru , sakin murfin yayi ya matsa kusa da ita ya riƙe ƙugu yace ai nima a cikin matan na tashi kuma duk wani makirci na iya kuma duk a wurinku na koya ki bari kafin in gigita miki tunani , wurin Al ' Ameen ya koma ya riƙe wuyanshi amma bai matse ba yace tunda kake ka taɓa ganin wani mai aikinta yaje ɗakin Momy ? Kafin Al ' Ameen yayi magana ta ɗaga murya tana salati cikin kuka wai ita Dikko ya daka ? Ta shiga 3 ta lalace , Dikko yace tou tunda sharrin kike so bari ki tara man mutane idan Dady yazo zance Al ' Ameen na kama ɗakinki , ta ɗage baki bata ƙara ihun ba kuma bata rufe bakinta cikin tashin hankali ta kalli Dikko tace ummmmmm , murmushi Dikko da gefen bakinshi yace ummmm a dai² lokacin da yayi ma kan Al ' Ameen kyakkyawan riƙo da duka hannayenshi ya buga shi da bango yayi mishi fashin kwakwa , amma ba fashewa yayi biyu ba , take a wurin Al ' Ameen ya ɗauke , dariya Dikko yayi ya kalli matar Dady har yanzu bata rufe bakinta ba , but ya buɗe ya jefe Al ' Ameen ya rufe yaja motar da gudu ya barɓaɗeta da hayaƙi bata matsa ba tana tsaye wurin , Goruba yakai Al ' Ameen ya cire wayar jikinshi ya nufi asibiti dan dare yayi. Satina 3 a asibiti bayan nasha doguwar wahala dan bayan an haska ƙwalwata likitoci sun tabbatar da jini ya shiga brain ina saida akayi min borrhole surgery kuma kullum Dikko ne yake jinyata komai shi yakeyi min yana bani haƙuri akan abinda ya faru bazai ƙara ba , amma na daka kaina ƙasa bazan komai zama dashi ba. Inna kuwa Dikko ya kirata ya faɗa mata banda lafiya tace Allah ya sawaƙe itama tasha fama da rashin lafiyar wai tayi ɓarin ciki , da yace mata gani cewa tayi tana gaisheni itama zata dawo kwanan nan , Dikko kuwa ya ƙufule akan duk wanda baizo ganin Sultana ba shima saiya rama , zama dai cikin mata yasa shima ya iya tsegumi da irin halinsu , Bayan an gama kai magunguna a mota da dai abinda ya kamata yace muje , fashewa nayi da kuka ni bazan zauna ba , haba An mata wai meye kikeyi haka don Allah ? Nifa gaskiya bana sanka saika sakeni da , da ƙarar kwana dana mutu an fara kiran marigayi Sultana , yi haƙuri bazan ƙara ba , nidai bazan zauna dakai ba mahaukaci , ba komai idan ma kince mahaukacin ne ai banji wani damuwa ba na yadda ni mahaukaci ne kiyi haƙuri dan girman Allah An mata , nifa bana zama dakai saika sakeni , daka min tsawa yayi tare da cewa anƙi a sakekin kuma tunda ke yarinya ce ta tashi mu tafi bara ki sake magana kiga yadda zanyi dake dan kiga ina lallaɓaki kike tunanin na warke ? Tou ina nan yadda kika sanni tun farko ban canja ba sai abinda yayi gaba ya ƙarasa maganar yana min kallon da bana so. Naji tsoro amma saina kalli ƙasa na sake cewa saika sakeni , zama yayi kusa dani yace An mata kalli ya nunamin cikin ƙwayar idonshi da kallonshi mai ɓatar da damuwa yace yanzu ko dan albarkacin wannan bazanci ba ? Haba ƙaramar yarinyar Dikko cikin sigar lallashi ya ƙarasa maganar yana murmushi tare da rungumoni jikinshi , A wahalce na sauke ajiyar zuciya cikin shashshekar kuka , dafe ƙeyata yayi da hannunshi yace ai na sani kiji natsuwa daga jikina An mata yayi maganar yana jawo numfashi daga cikin cikinshi saiya ɗan riƙeshi a ƙirjinshi kamar shashsheka haka da ɗan sauri² mai tayar da tsikar jiki cikin salo mai tada hankali , shiru nayi ban sake ko motsi ba na ƙara lafewa a jikinshi , murmushi yayi a zuciyarshi yace haba An mata ina zaki tafi kibar mahaukaci ? Ai muna tare harsai hauka ya ƙare. Saida ya tabbatar ya ladabtar da jikina ya fara ƙoƙarin sakina , ƙara riƙeshi nayi ina kuka , me ne ne kuma ? Ba komai na bashi ansa , tou sakeni , anƙi a sakenka na faɗa da irin ansar daya bani aa farko ina ƙara lafewa a jikinshi kamar ƙadangare ya lafe jikin bango idan yaga mage , murmushi Dikko yayi cewa tou tashi muje gida sai ki rufe ƙofa ga makullinma tun yanzu ya bani a dai² lokacin daya ɗagoni yana kallona yace kinga sai muci karenmu ba babbaka ko......? Ya ƙarasa yana ɓata fuska a sakace , Murmushi nayi banyi magana ba ina kallonshi , yace yawwa jarumata muje ya ƙarasa maganar yana saukoni daga saman gadon.... Ashiru ne ya ɗaukemu , dani da Dikko muna baya kuma tunda muka baro ɗakin har yanzu bai sake magana ba sai haɗe rai yakeyi kamar bai sanni ba , ko magana nayi mishi saidai yayi min wani irin gittaccen kallo , ni na kasa gane inda ya dosa wani irin birkitaccen hali yake dashi yanzu mutum anjima ba mutum ba , tsoki nayi ban sake magana har muka isa goruba road , ajiyemu Ashiru yayi ya tafi da motar ledar magungunan ya bani wai inje ciki yana zuwa kuma inyi wanka.... Banyi magana ba na shige , na daɗe sosai har nayi wanka na fito bai shigo ba , jikin madubi na matsa ina duƙar da kaina inda akayi min aiki , taƙaitaccen murmushi nayi tare da komawa da baya na zauna saman gado ina kallon kaina a madubi nace ina Amisty ? Kizo kiga ranar da nake faɗa tazo , Nace miki naji a jikina zan rasa wani babban abu mai muhinmanci a rayuwata , ni kuma zan shiga wani babban tashin hankali wanda bansan ranar zuwanshi ba , ashe abinda zan rasa ba komai bane sai Babana , tashin hankali kuma ashe shine wannan na taɓa kaina yau itace ranar wayyo gani anyi min aiki cikin kai niba mahaukaciya , fashewa nayi da kuka gaskiya rayuwata ta cika tsalle² a dai² lokacin nan ya shigo yana cewa kin fara ko ? Kedai kika sani An mata kiyi duk abinda kikaji kina iyawa , da gudu na tashi naje na rungume Dikko cikin kuka nace wai me yasa rayuwa take tsanantawa ne ? Ba tare daya riƙeni ba yace An mata duk yadda rayuwa ta baki kawai ki ansa , ya ƙarasa maganar yana jana zuwa gaban gado ya zaunar dani , wayata ya ciro daga aljihunshi Hafsa ke kirana , shine ya ɗauki wayar yace ya akayi ne ? Bayan wani lokaci yace lafiya , kila gaisheshi tayi nadaiji yace lafiya , ........, tana bacci , ........ Wane wuri ne ? ........ Tou bata da lafiya idan ta samu sauƙi zan kaita yana faɗin haka ya tsinke kiran ! Ajiye wayar yayi da nashi ya ɗauki kofi zai fita , tun kafin ya fita cikin kuka nace bazan sha ba , baiyi magana ba ya dawo ya ajiye kofin a inda yake ya nufi toilet , kuka naci gaba da yi ina maimaita bana sha kuma bazan sake sha ba mugunta kawai , har ya fito wanka ban dai tsegumi ba , ko inda nake bai kalla ba yaci gaba da huɗɗar gabanshi , ganin zai saka kaya nace nayi wankan na faɗa a tsiwace , tou ina ruwana da wankanki , ai kaine kace nayi wanka , rigarshi yake ƙoƙarin sakawa yana cewa tou ki kwanta kiyi bacci idan kuma kina zuwa tashi mu tafi G R A zanje Jiddah bata da lafiya , banyi magana ba na tafi inda ya ajiye kofin na ɗauka nace zansha , ai babu ya ƙare ki saka kayanki kawai mu tafi , yi haƙuri , a , a , dan Allah Dikko ai nace babu ya ƙarasa maganar yana kallona , na bari , zaki sha ne ? Ey tou jeki ibo ya faɗa yana cire rigar daya saka tare da cewa dandai baki lafiya amma yau dasai nayi miki rowa ƙaramar yarinya dake , murmushi nayi tare da juyawa na murza ƙuguna cikin salon jan hankali da neman faɗa , murmushi yayi ya biyo bayana yace bakijin magana ko An mata ? Nima yadda naga yana ɗaga gira nayi nace kai ka koyamin rashin jin ai... Ah ni ƙarya kikemin , tare dashi mukaje wurin firij ni na riƙe kofin ya zuba yana kallona yace An mata nan gaba kodai nine zan riƙa riƙe makulli , hmmm idan ya ƙare bana sake siyowa inba haka idan kika kamani a ɗaki saina ci ƙaniyata yayi maganar yana riƙoni jikinshi bayan ya maida "yar jarkar a firij , ɗaga hannuna nayi da niyar shafa gemunshi amma saina ɗorashi a goshinshi , dan shima haka yakeyi baya yadda mace ta gane abinda yake tada mishi hankali a jikinta kuma ko yana kwance da mace yana warwarewa yana saiti baya surutu shiru yakeyi sai wani munafikin kukan kissa mai tsayawa a rai da tada hankali idan ka tunoshi , kome nake abun yana yawan zuwamin a rai , idan na tuno abun sai hankalina ya tashi sai naji maganar Dikko ko na ganshi ko naji ni a jikinshi nake samun natsuwa , Hmmm Dikko duniya , amma ban sani ba ko ni ɗaya yake ma haka ......? Saifa na taɓo dan haka na ɗan basar na taho da hannu ina kawowa saitin bakinshi ya sumbaci hannun muah yana sauke wani irin nishi , tsikar jikina ta tashi yarrrrr da sauri na shanye maganin nace ngode , murmushi yayi ya jani zuwa ɗaki..... An danbace cikin tsari da sabon salo ba irin wancan ba... Sai bayan isha'e muka isa G R A kuma an sauke bene anyi ma palo gyara na bada mamaki idan baka san wurin ba zaka rantse bene bai taɓa zama a wurin ba a cikin sati 3 , binshi nayi har ɗakin Jiddah ina ƙara kallon palon , ɗakin cike yake da mutane da "yan uwan Jiddah da mahaifiyar Dikko da danginshi , sai wata mai kama da maman Dikkon kila itace maman Jiddah , wani irin kallon tsana Momy ta bini dashi har naji babu daɗi jikina ya fara ƙyarma , kusa da Dikko na zauna idona ya cika da hawaye kuma har yanzu jikina bai daina ƙyarma ba dan ni a halin yanzu bana so nayi wani abu da zaisa nayi nisa da Dikko wallahi bana iya rabuwa dashi , cikin rawar murya nace Momy ina yini ɗauke kanta tayi bata ansa ba , kallona Dikko yayi yace me ne ne kike kuka ? Dakel na haɗiye yawun bakina nace ba komai , kallon Momy yayi sannan ya sake kallona , tana ganin Dikko ya kalloni ta nunamin saita kasheni , da sauri na ɗauke idona na gaishe da Maman Jiddah , itama ɗayan mara wayan ɗauke kanta tayi in banda rashin wayau abiyar zaman ɗiyarta aida da wayau ko ba daɗi tayi ta "yan bariki tace lafiya lau Sultana badai wayau "yan mata sunma makaɗi tusa..... Duk basar dani sukayi sukaci gaba da firarsu ita Maman Jiddah babu ɗan kawaicin nan irin na sarakuta da Dikko ta saki baki sai ɓarin maganganu takeyi na rashin lissafi a gaban Dikko abinda na fahimta wurinta Jiddah ta gado surutun tsiya kamar akku , ita kuma Maman Dikko bata da yawan magana kuma bata cika dariya ba tana da natsuwa sosai tanayin magana cikin aji da kamun kai amma bata da mutunci "yar masifa ce wato mafaɗaciya su kuma su Dikko a wurin uwarsu suka gaji rashin mutunci , suna da sakin layi idan mutum ya shiga jikinsu dole zai raina su dan basu da sirri ga Mardiyya amma sai sakin layi suke suna maganganu....... Dikko kuwa bayan ya gaisa dasu Momy wurin Jiddah ya koma yana ta jera mata sannu haushi abin ya bani kuma na ƙufule har a wuya ji munafurci ɗazun nan yake nuna ba wata bayan ni amma yanzu yaga Jiddah harya manta da Sultanar banza , kallon Jiddah nayi sai wani kwarkwasa takeyi tana kashe mishi ido shi kuma yabita da kallo , komi ya sameta ? Oho ma banza , miƙewa nayi na fita dan abune nasu na "yan uwa ni kuma a cikinsu bare ce ba "yar uwa ba dan haka na tattaro mutunci na nabar ɗakin , Palo na dawo na zauna , shiru² ba Dikko ba inuwarshi har 9:13pm gajiya nayi na kirashi a waya , ya akayi ? Ya tambayeni bayan ya ɗauka , bacci nakeji , kashe wayar yayi ya fito saida yazo inda nake zaune yace ai na ɗauka kin tafi kin kwanta , jeki ki kwanta fita zanyi yayi maganar yana miƙomin wayoyinshi , cikin ɓacin rai nace ai dama dole zakace naje na kwanta tunda kaje ka kasa ka tsare kai tattabara sarkin aure , yarinya kenan idan kinga dama tashi muje , nifa bana kwana gidan nan a ina ma zan kwana tunda an rushe ɗakin na ? Bai bani ansa ba yace tou naji baki kwana tashi kije Ashiru ya maida ki goruba , ai ni tsoro nakeji saidai mu tafi tare idan nayi bacci kaje inda zaka je , duk in fasa abinda zanyi sai kinyi bacci kammar sakaran namiji ? Ke zaki koyamin yadda zanyi rayuwa ma kenan ko ? Idan kinga dama ki bishi ni kinga tafiyata kuma karki zubar min da wayoyi yayi gaba abunshi............ 02/12/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 85 Da sauri nabi bayanshi har an buɗe mishi mota ya shiga , yana shiga nima na shiga kafin a rufe , kallona yayi baiyi magana ba sai tsoki tare da matsawa daga kusa dani yana hararata , murmushi nayi kamar sakarai ina yaƙe haƙora , yadda nayi abun na bashi dariya yace hmmm Yarinya , tafiya aka farayi da motar ni kuma na miƙa mishi wayoyinshi yace in riƙe mishi zasu ajiyeni gida shi Kano zaije , cikin rashin jin daɗi nace haba Dikko Kano kuma yanzu na ƙarasa maganar kamar zanyi kuka , yi haƙuri An mata zan dawo ai ba kwana zanyi ba yayi maganar yana jawoni jikinshi , kwace jikina nayi ina cewa ai saika kaje kayi ta tafiya , yi haƙuri , ban sake magana ba har muka iso gida , Anayin parking na fita cikin ɓacin rai , kirana yayi nai banza dashi kamar banji ba , cikin fushi yace kije kiyi ta zuciyar ƙaramar yarinya dake , ban juyo ba na shige ciki da gudu ina kuka nidai bana so ya tafi da daren nan shine zai tafi ya barni , har sun fita daga gidan Dikko yaji kamar babu daɗi suka dawo , palo ya sameni kwance saman kujera ina kuka , cikin rarrashi yace An mata zo nan , dan bai shigo ba daga bakin ƙofa ya tsaya , ina tashi nayi bedroom , da sauri ya biyoni na kusa shiga ya riƙeni cikin disashshiyar murya yace haba An matana meye na fushi tou ? Yi haƙuri bazan daɗe ba maganina zan anso kinsan banajin daɗin tafiya da rana kafin ma kiyi bacci zan dawo insha Allah kinji An matan DK ya ƙarasa maganar yana rungumeni , banyi magana ba , ina shashshekar kuka , kinyi haƙuri ko ? Ey , hannunshi yasa a aljihunshi ya ciro cingom saida ya saka a bakinshi yace kallar ni , tashi nayi daga jikinshi ina kallonshi , murmushi yayi da kallo mai kwantar da hankali tauna cingom in yayi sannan yace idan miji zaiyi tafiya ba'a mishi haka kinji ko ? Tom , ba'a yin abinda zaisa ya tafi da fushi kinji ? Tom , idan miji zaiyi tafiya addu'a ake mishi sai a rabu cikin soyayya da nuna kowa zai shiga taitaiyin shi idan abokin rayuwarshi baya kusa ki nunamin girman yadda zakiyi maraicina idan bama tare , zan tafi da soyayyarki kuma zanyi kewayarki zan dawo gareki ina mai farin ciki darajar waccan kulawar , kinga na baki wayoyina nace kije Ashiru ya maidake gida ni zanje na dawo ko ba daɗi sai kimin fatan alkairi , Kalli idona ki gani , kallonshi nayi cikin yanayin jin kunya , da nace zanje in dawo sai ki kalleni da irin wannan kallon ya nunamin cikin wata irin murya da shagwaɓa ina zakaje haka ne ? Kin gane ? Zanji wani iri a zuciyata kinyi min magana da salon da dole saina kalla , sai ya saki muryarshi yadda yake magana yace sai ince hajiya kano zanje , sake shagwaɓewa yayi ya nuna yadda zanyi idan zan bashi ansa , amma sai kiyi ta abu da Allah na yarinta ba lallashi komai maganarki a tsaye baki lanƙwasamin harshe nace miki bana san yadda kikemin magana saiki tayi min kallon da bana so , daga nace zan tafi kano ba addu'a ba komai fuuuuu ke ƙaramar Yarinya , kinsan Allah idan kikayi wasa saina ƙara aure , Tou kaje ka ƙara mana na hanaka ? Kinji yarintar ko ? Ji abinda kikeyi kina magana da miji kina ɗaga mishi murya , ba abinda kika iya sai kwanciya jikina shine kaɗai aikinki saina raba wurin kwanciya dake tunda ke Yarinya ce , kaje ka raba , murmushi yayi yace nasan ciwonki , yadda nayi maganar ya nuna dole zakace naje na kwanta tunda kaje ka kasa ka tsare kai tattabara sarkin aure , murmushi yayi tare dayin wasa da idonshi yana ci gaba cewa yes haka kishi ne , kishi kuma so ne , da hannunshi ya rungume kanshi yace wayyo An mata na kishi na ci gaba sabo , Da wata irin tafiya mai taɓa zuciya ya fita yana cewa ko bakimin addu'a a gabana ba nasan zakiyi a zuciyarki kuma saina yo miki tsaraba tunda kikaji kishina a zuciyarki saina sa kinyi farin ciki mage zan samo miki , ya fice , murmushi nayi da farin ciki na shige ɗaki da gudu na hau gado ina tsalle Allah ya tsare hanya mutumina. Bayan na kwanta na ɗauki wayata na kira Amisty , babu wani daɗewa ta ɗauka bayan gaisuwa nace Amisty don Allah rubuto min An mata ki turomin , kamar ya ? An mata haka zaki rubuto min , tou ta faɗa tare da ajiye waya , burum ta rubuto ta turomin , gyara kwanciya nayi na rubuta An mata , wayar Dikko ta buɗe , Allah sarki Dikko ashe da gaske yake da sunan da yake kirana ya kulle wayarshi , ba wani ruwana da saƙonni wayarshi dan bana ganewa , ma'adanar hotuna na shiga ina kallon Dikko da "yan uwanshi , haka dai nayi ta zaliƙe² a wayarshi har na shiga inda nakejin maganata da tashi duk wayar da nakeyi dashi yana record kenan , Allah sarki Dikko , saida nayi filla² da duk inda nake iya shiga a wayar amma banga hotuna na ba , tou ina suke ai yacemin wayarshi bata san kowa ba daga An mata sai Doki , tou naga dukuna babu iyaka a wayar amma ina An mata tou........ ? Tashi nayi zaune na ciji ɗan tsayana cikin yanayin mamaki to dama masu gemu sunayin ƙarya ? Tsoki nayi tare da ajiye wayar , ina ajiyewa kira ya shigo , kamar ansa ni na ɗauka tare da cewa waye ? Caca , Oh Jiddah ce kenan ko ? Zuciyata ta fara turani inyi abinda zan ɓata mata rai amma sai wani sashi na zuciyata yace bari suja miki sharri Dikko ya sakeki , da sauri na kama kaina nace yana wanka , uban waye yasa kika ɗaukar mishi waya tou ? Ina da ansar bata amma nidai bana so naje nayi abinda zai jawomin tashin hankali har Dikko yayi fushi dani , tsinke kiran nayi , haka kiran yaita shigowa amma ban ɗauka ba , tunda kiran Jiddah ya shigo kira yaci gaba da shigowa , ita kuma ɗayar wayar naga hoton jirgi daga sama ita kira baya shigowa kenan ? Da naji kiran yayi yawa zasu hanani bacci kawai na kashe wayar , nayi kwanciyata naci gaba da bacci abuna.... Yau kwanan Al ' Ameen 22 babu wanda yasan inda yake , duk wanda yasan yana da haɗin guiwa da Al ' Ameen akan "yan tsirkulle² hankalinshi a tashe yake danjin Dikko ya tafi dashi tun daga ranar da Dikko ya tafi dashi har zuwa yau basu da nutsuwa , su basu san ba'a kan matsalarsu Dikko ya riƙe Al ' Ameen ba shi Dikkon ya ɗauki Al ' Ameen dan yasan abinda ke tsakaninshi da Jiddah ne , wanda har ba'a magana sai tsakar dare , shi bai wani san akwai wani abu tsakaninshi da matar Dady ba..... Zaune take ta wani kame abunta a saman kujera ta ɗauke kanta gefe gudu ba kajin wani lafiyayyen motsi sai ƙarar cingom in ita ƙasa×⁴ , kallonta Dady yayi yace wai meke damunki ne ? Duk kinbi kin tashin hankalinki akan wani dalili naki na daban , akan me fushin wani ni zai shafe ni ne ? Saida ta ƙara ƙaras² sannan tace haba mai girma gwamna ya za'ayi ace duk inda Dikko yake ajiye mutane ace an kasa samo Al ' Ameen ? Kafa san halin Dikko kila ma yaje ya kasheshi ya jefar dashi ruwa , tou ni gaskiya bazan daina fushi da tashin hankali ba sai an samomin Al ' Ameen a daren nan..... Dady bai sake magana ba ya fara kiran wayar Dikko , gaba ɗaya wayoyin a kashe suke , Ashiru ya kira kuma ba tare dashi Dikko ya tafi ba saboda shine yace ya maida Sultana Goruba shi zaije ya dawo sai bata bi Ashiru ba tabi Dikko , cike da girmamawa Ashiru ya ɗauki wayar Dady ya gaishe shi , bayan gaisuwa Dady yace ina Babana ya kai Al ' Ameen ? Har ga Allah Ashiru bai tunanin komai ba yace yana Goruba road , Dady yace ka kawoshi yanzu² , Ashiru yace insha Allah suka ajiye waya , Bayan Dady ya gama waya da Ashiru ya kalli Bilki yace tou kinma ji yana Goruba Ashiru zaizo dashi yanzu , murmushin jin daɗi tayi ba tare data kalli Dady ba tayi godiya kusa da ita ya zauna................. !!! | cikin "yan mintuna da basu wuce 15 ba Ashiru yakai Al ' Ameen , kuma lafiyarshi garas dan Dikko bai dakeshi ba tunda ya buga mishi kai a bango ya suma bai sakeyi mishi wani abu yana mishi tambayoyi ne kafin ya gama yaci mutuncin shi , Momy kuwa tana can sake da baki tana bacci bata san wainar da ake toyawa ba , dan ita ba ma'abociya sa ido bace da sanin halin da wani yake ciki ba , barta dai da zafin kishi taƙalo fitinar da bata garai bata da dalili dan mafaɗaciya ce ta farkon shafi kuma bata san zaman lafiya ko kaɗan , ko shiru taji gidan kwana 2 ba'ayi faɗa ba haka nan zatace ta fita ana mata kallon hadarin kaji haka zata saka Dikko gaba tace anyi mata an matsa mata ita zata kashe auren nan tayi tafiyarta bata zama hawan jini ya kamata idan kuka bari na mutu kun shiga3 kaza² duk dan dai ayi hayaniya , haka zata haukatoshi ya fito yaita cancara ruwan rashin mutunci dan duk yafi kaf "yan uwanshi fitina bai gajiya da faɗa kuma baida haƙuri kamar amai idan ya fara babu kyau , tou bata tsayar da kanta wuri ɗaya ba bare ta gane inda duniya ta dosa..... Da inda ya ajiye Al ' Ameen ya fara bayan ya dawo daga kano babu shi babu dalilinshi , agogon hannunshi ya kalla 2:15am jinjina kai yayi ya nufi ciki , wayoyinshi ya ɗauka duk ya fitar dasu a jirgi , kai tsaye Umar ya fara kira , cikin yanayin bacci ya ɗauka , bayan ya ɗauka Dikko yace ina Al ' Ameen ? Kallon Al ' Ameen dake kwance kusa dashi yana bacci yayi sannan yace har kin farka kenan ? Dikko yace kai nine ta farka gidan su wa ? Ai na gane ki ranki ya daɗe Baki daɗe da kwanciya ba a kusa dani kikayi mafarki ? Shiru Dikko yayi yana sauraren Umar daya maidashi mace , Umar kuma yaci gaba da cewa ....... A ina kika ga ɗakin ne ? ....... Tou Allah ya ƙarawa mai girma gwamna lafiya da nisan kwana muyi ta zarce muci gaba da zama a gidan gwamnati kuma kema zan kawoki har sai kin kwana kamar yadda nake kwance dani da mai gidana Al ' Ameen a ɗaki ɗaya yana bacci , kashe waya Dikko yayi tou waye ya tafi da Al ' Ameen wato yana can ma yana bacci yasan zan nemeshi shi yasa bai tafi G R A ba ya tafi wurin Umar , tashin Sultana ya farayi , da sauri na buɗe idona a firgice dan mafarki nakeyi da mutumin nan , An mata tashi na dawo lafiya kuma na samo miki magen kamoni yayi yana sauko dani yake cewa muje ki anso fita zanyi , banyi magana ba kafin in saka takalmina har ya fita daga ɗakin ina fitowa harya fice daga palon da sauri , kafin na gangare daga sama har ya sauka , cikin mota na sameshi kwalin da magen take ciki ya miƙomin tare da cewa jeki saina dawo , ajiye kwalin nayi ƙasa zan riƙeshi a kasalance yace yi haƙuri An mata idan kika taɓani yanzu zaki jawo rigima , nidai dan Allah , tou taho ya faɗa yana kamo hannuna ɗan jirgewa nayi na zauna a jikinshi na kwantar da kaina a ƙirjinshi baimin magana kuma bai taɓani ba shi kaɗai yasan ɓacin raan da yakeji a zuciyarshi saida na gaji na tashi da kaina ya ɗauki kwalin ya miƙamin na wuce ciki shi kuma ya fita...... Yau yazo da wani irin ɓacin ran da babu wanda ya taɓa ganinshi a yanayin , yayi ihu yayi hauka yace ana shiga mishi haƙƙi ya daki kanshi da saitin zuciyrashi yace shi ba mahaukaci bane ba , shi Dikko yasan abinda yakeyi ya rantse da girman Allah a tsautsayi wani ya kuskura yazo kusa dashi saiya kashe shi da gaske yake kisa zaiyi zai kashe ko waye ya kuskura yazo inda yake idan kuma mutum ya taɓashi to tabbas ko gawarshi bazatayi kyan gani ba saidai shima ya mutu ya yadda da wannan , idan da wanda ya gaji da rayuwar duniya yazo yau shine zai kashe ko waye idan baiyi kisa yau a gidan nan ba tou wallahi ya yadda shi ba ɗan Babanshi bane ba ina Al ' Ameen ina wanda yaje ya taho dashi waye yasa aka fito dashi ne............ Ya ƙarasa maganar yana buga kafarshi ƙasa da ƙarfi tare dayin wani irin ihu mai tada hankali da gigita , dake dare ne ihun Dikko da hayaniyarshi ya karaɗe kaf ilahirin girman gidan gwamnati ihunshi na yau yafi na kullum tashin hankali dasa ɗimuwa , duk mai imani saida ya tausaya ma Dikko kuma kowa yasan wannan abu badai mutum ba , kowa yayo waje inda yake tsaye yana hayaniya sun zagayeshi amma an rasa waye zai shiga wurinshi , sunan Al ' Ameen ya kira da wata irin murya yace ba duka ba zagi ba harara bare magana mara daɗi ka fito da kafafuwan ka kazo ka shiga mota kafin in irga 10 idan kuma ka bari na fito dakai da kaina saidai uwarka ta sake haifo wani ba kai ba dan zaka shiga 3n ka kuma zaka bani ka lalace , rufe idanuwa yayi cikin rashin mutunci ya fara kiran numbobi One , Two , Three , Four , Five , Six , Ser..... Da gudu Al ' Ameen yazo gabanshi , Momy tace me yayi maka ? Babu ruwanki kuma nayi rantsuwa duk wanda yazo kusa dani saina kashe shi.............. Waye yaje ya ɗauko ka ne ? Ashiru ne Al ' Ameen ya bashi ansa , bai sake magana ba yayi gaba Al ' Ameen yabi bayanshi wurin yayi tsit kamar babu kowa yana fara tafiya suka riƙa darewa suna buɗe hanya har ya wuce , saida Dikko ya fita da Al ' Ameen hayaniya taci gaba tashi kowa yana tausayin rayuwar da ta samu Dikko gashi mahaifiyarshi bata da ragowa bare a fahimtar da ita yadda lalurar ɗanta take bata ajiye komai ba sai girman kai wulaƙanci rashin mutunci da masifa dama marar mutunci haka ake masa ana ganin kuskure babu mai gyara masa saidai a barshi yaje can yaji da halinshi..... Uwar Jiddah kuwa data biyo Momy cewa tayi Maryam ashe ɗanki mahaukaci ne shi yasa kika maƙale saiya auri Hauwa'u ? { Jiddah } da yanzu tana can ƙasar waje tana aure yanzu haka ma takarar gwamna zai tsaya Dikkon ma har nawa yake ? Aure babu wani ci gaba ita ba ciki ba sai haƙuri irin wannan haukan yayi ya riƙemin ɗiya yaita bugu ita ba ƙato ba ? Kai ׳ gaskiya abun baiyi tsari ba kila ma bugun da yayi mata ne yasa take rashin lafiya gaskiya an shiga haƙƙina kinci amanata wallahi saida Hauwa'u tacemin bata zama kwanaki daya bigeta tace saiya saketa kika shiga kika fita ta haƙura ta zauna ashe zalinta ake ci , Momy tace aini ban iya neman asiri ba ita tayi ma kanta karatun ta natsu ta koma nidai shawara na bata kuma ta ɗauka , Maman Jiddah tace tou wallahi bana lamunta ni ban yadda da auren bugu ba waye ma Dikkon ? Waye shi........ ? Murmushi Momy tayi mai ciwo a zuciyarta tace Dikko kuwa kowa ne dan ba sakarai bane ba yasan damarshi , bata sake magana ba ta kwanta , Maman Jiddah kuma wayarta ta ɗauka ta fara kiran Jiddah tana ci gaba da cewa aure babu wani ci gaba har yanzu ko ciki babu ina ma amfanin rayuwar Dikko ɗan iska kawai daya raina mutane. Bayan Jiddah ta ɗauka tace Hauwa'u ashe Dikko hauka yake mara ɗaura zani ? Magana Jiddah tayi , mahaifiyarta taci gaba da cewa wallahi nasan ba komai bane sai hassadar ganin zaki ci gaba shi yasa Maryam tasa kika auri Dikko da yanzu kina can ƙasar waje kina huta .......... Eh da kema zaki zama matar gwamna ........ Wallahi hassada ce kawai tunda taga ita "ya "yanta basu auri gwamnoni ba shi yasa tayi zalinci ta haɗa aurenki da mahaukacin ɗanta , haka dai taita maganganu Momy kuma bata ce ummm ummmm ba...... Inda yakai Suwaiba yaje yakai Al ' Ameen , kuma wuri ɗaya ya haɗasu babu abinda ya dameshi Suwaiba kuwa sai bacci takeyi kamar jakar data kwana tana wahala , saida Dikko yayi ma Al ' Ameen lullusar fitar hayyaci ya ɗora da cewa idan wani ya sake zuwa ya bishi yaga yadda zaibi ta kanshi da mota kuma ya kashe banza , a wahalce Al ' Ameen yace nasan idan ka kashe ni ko bayan bana raye zaka tuno da maganganu na.... 3 ta wuce ya koma gida kuma bai sake tashin Sultana ba haka kuma baiyi bacci ba yana zaune a gefen gadon yana nazarin wasu maganganun da sukayi da Al ' Ameen , Al ' Ameen miya haɗaka da Jiddah ne ? Wallahi mai gida ba abinda ya haɗani da ita kawai dai tana aike na ne na samo mata asiri tana san ganin bayanka , kamar ya zata ga bayana ? Saboda makirci da sharri irin nashi saiya kawo mishi zanje can baya wanda shi Dikko daga shi sai Allah sai Jiddah suka san wannan sirri na zance sperm , ya akayi maganar yaje wajen Al ' Ameen da wasu zantuka na rayuwar shi da ita a fanni auratayya ? Me yasa Jiddah ta tona mishi asiri ? Me yasa ta faɗeshi a yanayin da duk duniya ko iyayenshi baya fatar su san yana shiga irin wannan yanayin me yasa ׳............... Kai wannan wace irin mace ce ........... ? Hayaniyar shi ta farkar dani daga bacci , takalmin ƙafarshi ya fara cirewa ranshi a matuƙar ɓace kanshi yaji ya yamutsa daya tuno har kwanciyar da yayi a jikin Jiddah da bai sauka ba sai bayan mintuna 20 duk hadashi ta faɗawa Al ' Ameen wani irin ihu Dikko yayi mai tada hankali , da gudu na sauka daga saman gado jikina yana kyarma dan na firgita kuma ban taɓajin irin ihun ba , fashewa nayi da kuka , ke zo ki kwanta mana , maganar shi ta ƙara gigitani dan haka da gudu na fita daga ɗakin ya biyoni yana cewa karki hau bene An mata ki rufamin asiri , tsayawa nayi nace tou me nayi maka ? Da hannunshi biyu yake nunawa na yanayin lallashi bake bace ba yi haƙuri taho , A tsoroce naje wurinshi na riƙe hannunshi ina kallon idonshi , murmushin ƙarfin hali yayi tare da cewa wuce muje ciki idan ina ihu ki daina fita da gudu kinji ? Ni bana san ihun tsoro nakeji , kiyi haƙuri na bari bazan ƙara ba An mata , tou ina kakai m card in nan ? Cikin murya mai kwantar da hankali yace me zakiyi dashi ne ? Wata ɗauka da nayi zan goge , dalili ? Nidai ka bani , ni wallahi bansan inda na ajiyeshi ba , wani abu ya faru ne ? Ey , tou meye ne ? Muje ɗaki , hannu na yaja muka koma ciki gaba ɗayanmu toilet muka shiga ni na wanke fuskata da bakina na fito , duk daren nan saida Dikko yayi wanka shi bansan abinda yasa ya mada rayuwarshi ta dare ba yanayin abu da dare kamar rana , bayan ya fito ya saka kayan jersey ya ɗauki wayarshi ya shiga duniya yace ina saurarenki..... Gefen gado na zauna shi kuma yana zaune gefen madubi , da farko dai ina baka haƙuri akan maganar da zanyi , baimin magana ba hankalinshi yana kan wayarshi , naci gaba da cewa can² baya na haɗu da wani mutumi muka shiga har ƙallar rayuwa dashi amma babu wani abu daya shiga tsakani , yadda abun ya faru na faɗa masa kaf da zancen maganar recording da nayi masamasa , Ranar dana fara ganinshi a bacci da zancen ƙwaƙwale ido da yakeyi kuma yake faɗamin kuma ya zama gaske , ganin Al ' Ameen a baccina ranar dana ga Dikko ya rabu biyu daren ɗaurin aurenmu kenan , yace shine ya turomin tsafinsu a auna nauhin idona saboda naci kuɗin su ban biya da idanuwa na ba za'a ɗauramin aure gobe sai su cire idona , a tsarin tsafinsu basa cin idon wacce babu igiyar aure akanta zanyi aure sai aka zo dubani , shine nayi kuka kake tambayata abinda ya faru , ranar da aka kawoni gidanka a ranar nayi mafarki dashi yacemin ya cire ido saura nawa tunda nayi aure.... Abinda yasa har yanzu basu cire idona ba saboda wannan record in da nayi mashi yana so ya tabbatar babu wata sauran hujja a wurina suna so na basu su goge shi , shin idan na goge ko sun goge zasu fita harkata ko kuwa zasu kaini nima kamar yadda suka kai sauran matar aure ne ? Tsoki Dikko yayi ba tare da kalleni ba ya gyara zaman shi yana cewa ƙarya ne , wannan labari tatsuniya ne , a , a Dikko da gaske ne wallahi , An mata banda ƙaryar bacci to me ya kawo Al ' Ameen a mafarkinki ? Yacemin Al ' Ameen ya munafurce shi kuma wallahi zai tona masa asiri Al ' Ameen shine jagorar matsalar rayuwarka , duk haukan da kakeyi shine , ni banasan wannan maganar karki sakemin irinta , Dikko wallahi har inda aka binne asirin ya nunamin , cikin hayaniya yace da Allah bana san iskanci in banda iskanci ya za'ayi Al ' Ameen ni yayi min wani abu ? Zan sake magana ya dakamin tsawa yana cewa kwanta kiyi bacci idan na sake jin surutunki saina zaneki , Dik..... Ki rufemin baki karki ɓatamin rai a daren nan............. Ya ƙarasa yana rufe idanuwanshi. A hankali na koma na kwanta tare da fashewa da kuka nace na rantse da Allah da gaske ne , kuma a ido biyu zan iya gane wurin , ka tsaya na faɗa maka abinda yace Al ' Ameen ɗin yayi masa mana , ke.................. Ki rufemin baki....... Idan kika sake magana saina kashe ki...... Shiru nayi ban sake ko tari ba nabi shi da kallo , dakamin tsawa yayi cewa daina kallona ki juya can ki kalli bango , banyi magana ba na juya naci gaba kallon bango kamar yadda yace , har aka kira sallah asuba ban sake magana ba kuma ban koma bacci ba saishi dake ta ansa kiran waya , ana kiran sallah asuba kuma ya maida wayar jirgi ya sauya kayan jikinshi zuwa jallabiya ya fita masallaci. Abinda ya faru a baccina kamar yadda na saba mafarki dashi lokaci bayan lokaci , ina ganinsa a wasu kwanaki na baccina wanda bana iya ganewa ko tuna lokacin da yake zuwa a baccin saboda ba kullum yake zuwa ba kuma ranakun zuwan nashi daban ne , Ranar da naga sunayin kokowa da Al ' Ameen , wata ranar kuma da yazo a baccina kamar yadda ya saba yace mi yasa ban goge ba ? Nace masa Dikko bai bani ba , shine yacemin inyi alƙawari na samo mishi record Al ' Ameen yaci amanarshi ya yadda dashi amma ya zalinci rayuwarshi , ga yadda ya faɗamin dai , kuma yace abinda yasa zai tonawa Al ' Ameen asiri yana so Dikko ya ƙoreshi daga ƙasanshi shima saiya tagayyara kamar yadda shi mai ƙwaƙwale idon ya tagayyara....... Dani da Al ' Ameen dukanmu iyayenmu ne sukayi aiki a gidansu Dikko , mahaifinshi Dikko mutumin kirki ne mutum mai mutunci da mutunta kowa kuma yana da alkairi da san kyautatawa wanda bashi da hali haka kuma bashi da ƙyanƙyamin talakawa , lokacin da iyayenmu suke aiki a gidansu shi mahaifin Dikko lokacin yana da mata 4 cas mahaifiyar Dikko itace babba amma yayi aure² dan samun ɗa namiji , Dan ya tashi hankalin rashin samun namiji tun kafin haihuwa tayi nisa , haihuwar Maryam 3 a wancan lokacin kullum mata take haihuwa dan haka kawai Dady yaci gaba da aure saida ya tara huɗu gaba ɗaya , ganin haka yasa ita kuma ta dakata da haihuwa kwata² saboda baƙin ciki da kishi , ta tashi hankalin miji ta hanashi zaman lafiya da kwanciyar hankali dan duk yadda zan kwatanta fitinarta ta zarce wurin , ga rashin san zaman lafiya ga wulaƙanci idan ta fara fitina babu wanda ya iya yasa tayi shiru , dan haka itace ta ɓata kaf gidan ya haukace aka shiga sahun kishi da jefe²n juna , a lokacin da take ita ɗaya bata san "yan uwan Dady dan ita Allah yayi mata tsantsani da ƙyanƙyami idan dai ku masu kuɗi ne ko "yan gayu tou kune abokan tafiyarta dan ita "yar gayu ce ajin farko da ƙarshe bata tarayya da mutumin data fi wayewa cewa takeyi zai kidahumar da ita , tasan hannunta kuma tasan abinda take dan duk matan da Dady ya auro babu kamar ta , ga kyau ga gayu ga aji idan ta raina ka ko ƙofar ɗakinta baka taka mata bata da mutunci yadda baki tunani , idan tana sanka kawai tana sanka idan bata sanka bata sanka........ Itace babba kuma itace ta ɓata gidan , ita bata iya neman asiri ba amma tasan logo da kissa na duƙunƙune kan namiji shi yasa Dady ya fifita ta akan kowa sai suke ganin kamar asiri take masa dan haka suka tisota gaba jifa , nan fa gasar haihu ya tashi dan haka akaci gaba da watso ma Dady "ya "ya mata , ganin buƙatarshi bata biya ba ya fara tarawa da ebewa , amma ita Maryam duk rashin kunyarta ba'a taɓa jaraba mata bulalar saki ba. Ganin ana haihuwa yasa itama taci gaba da haihuwa , tana komawa haihuwa Allah ya bata Dikko , tunda ta haifi Dikko su kuma suka tasashi gaba yadda basu haifa ba babu wacce ta isa itama tayi namiji sun yadda su kashe shi a tashi a tutar babu... A kanshi aka samu namiji kuma har yau ba'a sake samu ba , bayan Dikko ya girma kuma aka riƙa harin rayuwarshi a waje idan ya fita shine dalilin da yasa aka haɗashi dasu Ashiru , shi kuma Al ' Ameen da ƙarfin bala'e ya shiga ya fita yake tuƙa Dikko kuma bansan abinda ya rabasu ba a halin yanzu amma dai nasan basu tare ya koma tafiya da zugar yaranshi. Abinda yayi min shine , dani dashi gaba ɗayanmu munyi aure wurin zama da duk hidimar da kika sani anayi a aure Dikko ne yayi mana gaba ɗayanmu , tunda nayi aure na fita daga ƙarƙashin shi domin a lokacin Al ' Ameen ya zuƙeni daga jikin mai gida , amma duk da haka na yadda da Al ' Ameen sosai ganin iyayena da nashi sun tashi wurin aiki ɗaya kuma gaba ɗayanmu a gidan muke zaune , na yadda da Al ' Ameen jinsa nake kamar a ciki ɗaya muka fita , ashe ni mugunta ta yakeyi mugune azzalimi ne ya yaudareni anan inda nake tsaye a nan aka binne sihirin da akayi ma mai gida , abinda yayi min shine zaici gaba da faɗamin ne Dikko ya tasheni yacemin wai in tashi ya dawo , tabbas zan gane wurin amma ta ina zanbi inje wurin ? Ina Dikko ya ajiye m card in nan wai ? Har ya dawo daga masallaci ban tashi ba a yadda ya barni ba , kuma banyi sallah ba , cire jallabiyar shi yayi ya maida kayan daya cire ya kwanta. Shin wai wannan mafarkin da gaske ne ko kuwa tatsuniya ne kamar yadda Dikko yace , tashi nayi naje nayi alwallah nazo na kabbara sallah , shi kuma Dikko bayan ya kwanta yana tunanin maganar Sultana da zancen Sadiyya sai kuma maganar Suwaiba da tace masa ya tattaro kaf yaranshi duk wanda yasan ya taɓa zama a ƙasanshi ko basa tare yazo dashi , ita kuma Sadiyya tace masa a cikin yaranshi wanda ya kasheta yake , An mata kuma tace masa Al ' Ameen , shin wai me ye gaskiyar lamarin nan , Gaishe shi nayi bayan na gama sallah , bai ansa gaisuwar ba kuma bai kalleni ba , nima ban sake gaishe shi ba nayi kwanciyata a wurin , bayan wani lokaci yayi tsoki tare da saukowa daga saman gadon , canja kaya yayi ya ɗauki makulin mota ya fita , tashi nayi na koma saman gadon ina cewa aikin banza adashen tusa..... Kai tsaye wurin da ya ajiye Suwaiba da Al ' Ameen ya nufa......... 04/12/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 86 Ya za'ayi Al ' Ameen ni yayi min wani abu ? Tou me mutumin ya faɗa mata ? Ina yasan Al ' Ameen ? Me yasa ni kuma Al ' Ameen zai zama jagorar matsalata ne bayan dashi ake nemamin magani , mi yasa dole sa a mafarki zai bawa An mata labari ? Ƙarar wayarshi ya dakatar dashi daga tunanin daya tafi , Momy ya faɗa tare da ɗaukar wayar suka gaisa , Dikko kana ina ne ? Ina nan bisa titi , ina zakaje a safiyar nan ne ? Zanje gida , wane gidan ? G R A , daga ina kake ne ? Goruba , daina tambayar tayi cewa Dikko kazo ina neman ka yanzu²n nan , cike da damuwa yace me kuma akayi miki ne ? Dikko nidai tafiyata zanyi na gaji da zaman haƙuri , kuma fa bata iya tafiya ko ina ta bar Dady , Momy kiyi haƙuri dan Allah, Ni bazanyi ba , tunda ka tafi da Al ' Ameen jiya Bilki ta hana gidan nan zaman lafiya ta turo "ya "yanta sai rashin kunya sukemin dan taga ba kowa cikin yara duk su Nabeela suna wurin Jiddah ko nice zan fita inyi faɗa da Yara ne ? Nidai nasan nafi ƙarfin Bilki daga ciki har waje wani iskanci saida tasa yara suyishi , cike da damuwa Dikko yace Momy dan girman Allah kiyi haƙuri , wallahi bazanyi ba saidai idan Bilki ta koma uwarka sai in ƙaleka dama kwanaki dana faɗa maka ta zageni kace zakayi mata magana bakayi mata ba sakaran banza mara kishin uwarshi tana faɗin haka ta tsinke kiran. Innalillahi wa'inna ilahir raji'un ya faɗa tare da samun gefen titi yayi parking , wayar Ashiru ya fara kira , Ashiru kuwa yanaji yana gani yaƙi ɗauka dan Umar ya bashi labarin abinda mai gida yayi a jiya kuma dama yasan tunda ya ɗauko Al ' Ameen saiya fuskanci matsala tou shi ya za'ayi ma yace ma Dady baisan inda Al ' Ameen yake ba taya zaice kuma bazai ɗauko shi ba ? Yana ajiye wayar zai tashi motar text in Ashiru ya shigo , kayi haƙuri mai gida Dady yasa na ɗaukoshi kuma na kira wayarka a kashe ka gafarceni nasan ban kyauta ba , tsoki Dikko yayi tare da ajiye wayar saida ya fara tafiya ya fara kiran wayar Dady. Cike da fargaba ya ɗauki wayar yace Babana lafiya ? Dan shi a tunanin Dady ba lafiya shi yasa Dikko ya kirashi a safiyar nan , Dady wai me nayi maka ne ? Babana ba komai , tou me yasa za'a hanani na zauna lafiya ne ? Da sauri Dady ya tashi daga kwanciyar da yake yace me akayi maka ne ? Horn Dikko ya danne ɓiyyyyy , Dady yace a , a Babana , Dady kawai zan mutu na huta , yi haƙuri Babana² dan Allah tashi tsaye Dady yayi cikin tashin hankali yace wai ina damuwar take ne ? Me yasa kasa aka taho da Al ' Ameen ne ? Yadda sukayi da Bilki ya faɗa masa , kashe waya Dikko yayo bai sake magana ba ya ajiye a gefe , me ne ne tsakanin Al ' Ameen da matar uba wai ? Ko dan yace zaice ya kama Al ' Ameen a ɗakinta ne ? Tou kodai ? Karka yi zargi zuciyarshi ta faɗa masa , to me ya shafeta da lamarin Al ' Ameen haka da yawa ? Dama kwanaki daya dokeshi itace tayi video ta turawa Dady , yanzu kuma shine tasa akaje aka taho dashi ko ? Maganar Sadiyya ta dawo mishi a zuciyarshi an haɗa kai dashi da matan uba an maidakai lusarin namiji , ni kuma yayi nasara akaina yakai min rayuwata ƙarshe , ka tattaro kaf yaranka har wanda suka daina maka aiki ka kawosu idan na ganshi zan ganeshi { Suwaiba } , wallahi mai gida ba abinda ya haɗani da ita kawai dai tana aike na ne na samo mata asiri tana san ganin bayanka , { Al ' Ameen } , a , a Dikko da gaske ne wallahi , { An mata } , banda ƙaryar bacci to me ya kawo Al ' Ameen a mafarkinki ? Dady kuwa sai kiran wayar Dikko yakeyi amma yaƙi ɗauka dan haka ya kira Momy yace mata yasan itace ta ɓatawa Babanshi rai har so nawa yace su daina saka "ya "ya a damuwarsu basa bari , me yasa suke san ɓata mishi gida ? Kullum yana ƙoƙarin haɗawa su kuma suna rusawa ? Wai me yasa sukeyin abu na rashin tunani haka ? Tou wallahi tayi kuka da kanta dan zai mata rashin mutunci idan wani abu ya sami Babanshi. Da wani irin ihu ya shiga inda ƙannen shi suke kaf dan duk irin wannan lokacin basa bacci zasu zauna sai bayan 6:45 su tashi idan da makaranta kenan haka wannan tsarin yake ko bakya sallah duk idan akayi sallah kaf "yan gidan sai sun haɗu a wurin amma "ya "ya ƙananansu da manyansu idan dai ɗan da Dady ya haifa ne harshi Dikkon , kuma ko aure kikayi idan dai kika zo gida sai kinyi wannan zaman tunin duniya haka suke haɗuwa kuma ba addu'a akeyi ba , ba karatu akeyi ba zasu haɗu dai kawai su zauna a wurin suyi fira ne , idan kuma ranar da babu makaranta sai 7 suke tashi , saida ya zane kowa a cikinsu duka bana wasa ba amma ƙannenshi bai daki yayyenshi ba kuma babu wanda baiji ma ciwo a cikinsu ba ya ɗora da cewa daga yau idan wata ta sake shiga cikin faɗan iyaye saiyabi ta kanta da mota ya wuce "yan iska marasa kunya , dakel aka fito dashi daga wurin yana cewa suma su Nabeelar duk saiya ci mutuncinsu wallahi ba babba ba yaro duk wani ɗan daya sake shigar ma uwarshi faɗa a gidan nan shine zan kawo ƙarshen rayuwarshi............ Sai kuka sukeyi , shi kuma ƙwacewa yayi ya nufi ɗakinsu , a falo ya samu Momy ta kashe saman kujera ta murza wani irin ɗaurin kallabi mai burgewa dan fita zatayi zuwa wurin Dady parking in da Dikko yayi yasa ta koma ta zauna tana ta gunewa , kusa da ita ya zauna ya riƙe duka hannayenta yace Momy dan Allah ki daina damuwa , nuna kanshi yayi da hannu ɗaya ɗayan kuma yana riƙe da hannuwanta yaci gaba da cewa idan ina nunfashi babu wanda zai isa yasa miki damuwa kuma babu inda zakije mu muna tare dake nima ina tare dake Mamana Dady nawa ne shima yana tare da duk abinda nake so kiyi haƙuri baza a sake miki abinda zaisa kiji damuwa ba , cikin sanyin murya tace Dikko ya za'ayi yara su riƙamin rashin kunya idan nayi magana sai ace banda haƙuri , ba tun jiya na faɗawa Dadyn naku ba yace wai bana san zaman lafiya , yi haƙuri Momy fushi yasa ya faɗi haka , me yasa baiyi fushi ya faɗawa Bilki ba saini mareniyar wayanshi ɓacin rai yasa Momy taita maganganu Dikko dai tsareta yayi da ido bai sake magana ba , wato ita dai mace duk shekarunta idan tayi wani abun saidai ace Allah ya sawaƙe , A mota ya ɗauketa suka tafi wurin Dady , shima ranshi yayi mishi zafi sai faɗa yakeyi yana kuma ƙara ɗora laifin a wurin Momy itace ta fara koyawa yaranta rashin mutunci kuma ai itace ta fara nuna rashin san zaman lafiya a matsayinta na babba , murmushin ƙasaita tayi tace ma Dikko yaje ya jirata falonta tana zuwa , saida ya gaisa da ya fita , Dady kuwa yabi Dikko da kallon soyayya harya fita , ×××××××. Tunda Dikko ya fita Hafsa ke kiran wayata naƙi ɗauka ta dameni sosai dan haka na ɗauka bayan mun gaisa tacemin wai na fasa zuwa ne ? Ina ne na fasa zuwa ? DK bai faɗa miki rasuwa ba ? Waye ya rasu ne ? Kakar Babanku duk "yan gidanku suna can yau ake addu'ar 3 muma yau zamuje , wace ce kuma Kakar Babanmu ? Wacce ta haifi Maman Babanku , ke ina kika santa ne ? Kaka Sahura ta faɗa man inda take ni naje na gano wurin nakai "yan gidanku , ranar da mukaje na dawo na barosu can a ranar ta rasu , dan lokacin da zamu tafi na kiraki DK ya ɗauka yace baki lafiya sai muka tafi data rasu kuma na kirashi yace idan kin samu sauƙi zai kawoki , tou Allah ya jiƙanta na faɗa a tsiwace , dan Allah kiyi ƙoƙari kuje yau kuma duk "yan uwa sun haɗu kiga dangi kema , shi yasan wurin ne ? Ey nayi masa kwatance ranar dana kirashi na faɗa masa rasuwar , { wato ranar da aka sallamoni daga asibiti kenan } tou me yasa bai faɗamin ba , zan gani ina faɗin haka na tsinke kiran , Gaskiya fa ya kamata naje ko dan nuna soyayya wa kabarin Babana , Allah ya jiƙanka Babana yasa ka huta nayi rashin ka a duniyar nan shi kenan ka tafi inda bazan sake ganinka ba har abadan duniya , ka tafi tafiyar da babu dawowa shikenan ka tafi ka barni........, dole naje wurin ahalinka ko dan jaddada soyayya a gareka Baba na gari , kai sarkin fushi zakaje ko bazaka ba ne ni naje ? A dai² lokacin dana fara kiranshi , saida ta tsinke bai ɗauka ba , sake kiranshi nayi itama saida ta kusa tsinkewa ya ɗauka da abinda bana so wai ya akayi ne ? Dikko koma ya akayi ai zakaji yanzu , dan yadda akayin ne yasa na kiraka , ke karki min rashin kunya kinji , ba wannan ba ni zakaje ko ka fasa zuwa ne ? Ina ? Ba Hafsa ta faɗa maka rasuwa ba shine sai kace saina samu sauƙi bayan ni lafiyata qalau , ni bazanje ba sai kin dawo , tou babu damuwa ngode , ina faɗin haka na tsinke kiran , wayar Inna na kira , cikin hukuncin ubangiji kuma ta shiga amma bata ɗauka ba , ci gaba nayi da kira taƙi ɗauka , Dikko na sake kira , bayan ya ɗauka yace ya akayi ne ? Dikko na kira Inna kuma ta shiga amma bata ɗauka ba , da kyau , daga haka bai sake cewa wani abu ba , kaji , naji , tou kace wani abu mana , ai shine nace nace hakan da kyau , nidai baka so na , baka damuwa da abinda yake damuna , ni bansan abinda yasa kake min haka ba na faɗa cikin hayaniya ina kuka , duk saida na safke mai isata sannan yace tou yi haƙuri An mata gani nan zuwa zan miki abinda kike so , tou me yasa ni kake min haka ko ka daina so na ne ? Ina sanki mana tayama zaki fara wannan tunanin ? Bana fata kuma bana tunanin akwai ranar da zanji sanki ya ragu a zuciyata , kiyi haƙuri ki bini da addu'a har ubangiji ya yaye min damuwata dana tuno da abinda yake damuna sai inji raina yana ɓaci shi yasa a ko wane lokaci nake miki magana hayaniya² , kana ina yanzu ? Ina nan inajiran Momy data sallameni zanzo wurinki ai haka yayi miki ko ? Ey , to baki ce kin gode ba , murmushi nayi tare da cewa godiya nake mutumina , yawwa jarumata ngode yana faɗin haka ya tsinke kiran , bin wayarshi yayi da kallo yace mata kenan , ita ba abinda ya dameta shin ina lafiya ? Ko ina cikin yanayin fushi me ya sameni bayan na fito babu ya hanya ba komai itadai burinta ayi mata dai² , zan faɗa mata ba'a kiran miji kai tsaye a faɗa masa damuwa sai an tabbatar da yana cikin natsuwa. Momy ta daɗe bata dawo ba , har Ashiru ya iso gidan danshi zai maida Maman Jiddah tunda Al ' Ameen bashi nan kuma tsarin nan Momy ce ta tsarashi shi kwata² Ashiru baisan Dikko yana nan ba , ita kuma Maman Jiddah tana gama shirinta ta fito falo dan Momy tayi mata waya cewa wanda zai kaita ya iso itama tana zuwa yanzu , shine tayo parking ta bayyana a falon , cikin girmamawa da mutuntawa Dikko ya gaishe da surukarshi.... Ba yabo ba fallasa ta ansa tana ta riƙe fuska , ko inda take bai sake kallo ba , ita kuma taci gaba da cunkusawa cikinta abinda ta samu an ajiye mata dan karin safe tunda zata ibi hanya ko kunyar sarakuta babu , Dikko kuma fita yayi ya koma mota yana jiran Momy , yana zama yaga Ashiru yasha ta baya da gudu , tsoki yayi tare da kallon agogon jikin waya 8:39am kuma har yanzu Momy bata fito ba shawara ya yanke kawai ya fara ganin Jiddah kuma suma su Nabeela ya zanesu kamar yadda ya zane "yan uwansu zaije ya dawo kafin ta gama ta fito , tashin mota yayi ya nufi gidanshi.... Yana fita Momy ta iso taga babu Dikko kawai ya wani ɓace abunshi , Momy kuwa tana shiga wuri ta samu ta zauna tana ma "yar uwarta magana , amma ke dake gidanki idan kin tanka tou Maman Jiddah tayi magana sai wani cika take tana batsewa , Momy taji ba daɗi amma ta haƙura ta kanne dan abu na "yan uwan taka dole sai an haɗa da haƙuri da kuma kai zuciya nesa , data tashi tafiya duk abinda Momy ta bata cewa tayi ita ba baƙuwar arziƙi bace ba tafi ƙarfin ita ta bata wani abu ta ansa ta riƙe kila zasuyi mata amfani wurin nemawa Dikko rubutun danga na , Momy tace wane irin rubutun dangana kuma ? Maryam gaskiya ni na kashe wannan auren , cikin tashin hankali Momy tace Yaya don girman Allah kiyi haƙuri wai miye matsalar ne ? Kuɗi , banbancin kuɗi ne ke naki ɗan gwamna ne ni kuma gwamnan zata aura gaba ɗaya , zaɓe yana tunkarowa bana tunanin ku zaku sake zarcewa siyasa zata wurgar daku a can tsohon gidanku gidan gwamnati kuwa zai zama na masu rabo , Momy tace mu kenan masu rabo ni inaji a jikina munci kuma sai mun sake wannan zaman darajar manzan Allah S. A. W gidan gwamnati sai mun maimaitashi , maganar kuɗi kuma ba damuwar Dikko bane ba saboda shi basu ne gaban shi ba yana dasu yadda tunaninki da ƙwalwarki basu ɗaukar misali dan dayabi izzar kuɗi da mulki wallahi Jiddah bata kai mace ba a wurinshi , Maman Jiddah tace aiko ke kinsan Jiddah mace ce hada gyara gwamna da kanshi yake santa gwamna fa ? Shin ke kin raina gwamnati ko ? Ban raina gwamnati ba amma nima na san nawan tunda ya fara saiya taka matakin da bakya tunani , da haukan zai taka matakin da har ni bana tunani ? Momy tace ba mahaukaci kuma ba hauka Dikko duniya , zamani ɗaya tak a ƙarni matashi mai sa'ar rayuwa , yaro da kuɗi abokin tafiyar manya , mahaukaci da kuɗi kuma mai maihankali babu , gwamnan da kike tunanin kashe auren Jiddah saboda shi tun kafin na ganshi nasan waye shi na tabbata duk kuɗinshi shi 30 baya Dikko ɗaya , yadda baki tunani Dikko ya kafu shi kanshi ubanshi alfahari yakeyi dashi yace yasan ko bayan baya raye zai tallafi "yan uwanshi shi yasa ya dage saida ya tabbatar ya gina Dikko sosai , amma duk da haka shi kuɗi basu ne gabanshi ba shi yasa yake rabar dasu kamar hauka , abinda yasa na kafe sai Dikko ya auri Jiddah dan naga wasu sunci ma bare nawa bana san ya baku² shi yasa na haɗa auren Jiddah dashi , dan nasan Dikko bashi da mutunci idan nice yau gobe bana nan na gina ku ne ku "yan uwana ko bayan bana raye arziƙin Dikko bazai muku wahalar ci ba saboda akwai Jiddah , amma idan har kika kashe auren nan kuka bar bare kuka hana zuminci wallahi gidan Dikko raɓe zaku zama , kuna iya zuwa ma tace muku baya nan kuma yana nan ta hanaku ganinshi , kallon banza ko magana mara daɗi kukayi ma matarshi tabbas nasan saiya ya taka muku burki ko kuma ya ɗauki matakin hanaku zuwa gidanshi ba abu bane mai wahala a wurinshi , ni bana miki hassada kuma bana miki baƙin ciki dan "yarki zata zama matar gwamna shawara na baki dai dan kece ya kamata tun yanzu ki daina tunanin kashe auren , a sanyaye tace kuma kece zaki anshi kuɗin nan ki fara nemawa "yarki rubutun dangana tun yanzu , ɗa ɗaya tak ragamar mata idan dai harya kafa soyayyarshi a zuciyar Jiddah tou sorryn ku ina jajanta muku domin ni kaina bansan a ina Dikko ya gaji zuciya ba , da zaran ya yanke hukunci tou fa ko kanshi baya saurara , karki raba domin yadda mukayi zaman nan zamu sake maimaitashi idan har kika tafi da Jiddah wallahi kuma Dikko yasan dalili tou fa tabbas yadda kika ga kiyi sabon rubutu a saman allo bai bushe ba ki tsomashi ruwa ba tare da kin murza ba rubutun zai sauka to haka Jiddah zata wanke a cikin zuciyarshi ko matalwa batayi , shawara ya rage naki neman rubutun dangana da mafita yana wurinki..... Tana faɗin haka ta wuce ciki abunta , Maman Jiddah kuwa fita tayi dan Ashiru ya fitar da duk wani abu nata , haka ta fita waje taita tata ruwan rashin mutunci wai Maryam tana mata hassada mai takarar gwamna yana san "yarta take jin zafi , kurar Momy ta riga tayi kuka shi yasa kowa yake ganin Momy bata kyauta ba abu har ga "yan uwanta ashe ba'a kishi ba har "yan uwanta bata raga musu ba , saida ta gaji da tonon sililinta tayi ta tona musu asiri dan wasu basu iya riƙe ɓacin rai ba idan suna fushi sai su manta da abinda gaba zaiyi su kulle idanuwa suyi ta wulaƙanci na rashin lissafi , ko a mota haka ta ci gaba wulaƙanci su "yan gadon rashin mutunci , duk yadda Ashiru yaso ya nuna mata waye Dikko idonta ya rufe ita mai takarar gwamna kawai kuma saita kashe auren , da ɓacin rai suka isa G R A lokacin Dikko harya zane su Nabeela suma ya farfasa musu jiki ya wuce wurinsu Al ' Ameen. Haka ta tisa ƙeyar Jiddah hada Mardiyya suka kama hanyar Kaduna , Dikko baisan wainar da ake toyawa ba , Momy kuwa tayi kukan baƙin ciki bata nunanin idan bata raye wannan karuwar zata bar Dikko yayi zuminci da "yan uwanshi , dole a sake nema ma Dikko wani auren a cikin familyn Dadynshi...... Lokacin da Dikko ya isa Al ' Ameen ya dawo kuma ya shaƙe Suwaiba tana ta halbe²n mutuwa , halbi ɗaya Dikko yayi mishi a haƙarƙari ya sake somewa , dakel Suwaiba ta nuna Al ' Ameen tace shine , idan baka yadda ba kuma ka tambayi Mustapha zai maka bayanin komai , wane Mustapha ? Mustaphan daka sani kuma saida ya zalinceshi ya munafurce shi yaci zalinshi sos.... Daga haka ta ɗauke Dikko yasa aka tafi da ita asibiti kuma a tsareta , Al ' Ameen kuma bazai dakeshi ba saiya dawo..... Saida ya sake komawa ta gidansu ya tafi da abinda zasuyi kalaci kuma baije wurin Momy ba , sai 10:15am ya isa gida , lokacin harna shirya , bafa inda zakije yarinya , haba ? Ummm , to me yasa ? Bai sake magana ya zauna a gefen gado sannan yace An mata wai me mutumin cikin bacci yake ce miki ne ? Nima bana san wannan tatsuniyar , to wane iri ne ? Na manta , ke.............. Bana san iskanci ni zaki faɗamin kin manta................. Cikin ɗaga murya da hayaniya ya faɗa , a tsorace nace kamarshi biyu ce duk na faɗa masa sifofinshi dana sani , tashi yayi tare da kwantar dani saman gado yace me yace miki Al ' Ameen yayi mishi ne ? Bai faɗamin ba ka tashe ni daga bacci , danne ni yayi ta ƙarfi yace koma bacci ki tambayoshi abinda Al ' Ameen yayi mishi.................. , kyarma jikina ya farayi cikin kuka nace ai bazaizo ba ranakun zuwanshi daban ne a sati sau biyu yake zuwamin kuma ni bansan wace rana da wace rana bace ba , ke............... Kiyi bacci ko in kashe ki........ Fashewa nayi da kuka nace Dikko ka ƙyaleni don Allah , zaro ido yayi cikin ɓacin rai yace bazan ƙyaleki ba aradu sai kinyi bacci. Dikko dan Allah , An mata dan Allah , mintuna 30 na baki kiyi bacci kizomin da duk wannan ansoshin , me yasa baya zuwa sai a bacci ? Me yasa baizo wurina ba sai wurinki ? Me Al ' Ameen yayi mishi zai tona masa asiri ? Me yasa yake san ki goge recording ? Me yasa yake kwakwale ido ? Me yasa basu cire naki ba ya kuma nuna miki hanya ta yadda zaki gane zuwa inda kika ce sun binne tsafinsu , me ne ne tsakanin Al ' Ameen da Aunty a cikin mintuna 30 idan kuma kika tashi babu wani bayani zan kashe ki kema kin zama munafukata kenan gawarki zan jefar da ita a cikin ruwa kadojina su cinyeki banza kawai dake , kafin in irga 10 kinyi bacci kafin na irga 200 kin tashi kuma zaki bani ansar duk wannan tambayoyin dana aikeki a wurinshi ki samomin...... Fara kiran nombobi ya farayi tuni har na saki fitsari dan nasan wallahi bazai zo ba , wani irin firgitaccen mari ya yankamin har kin isa kiyimin fitsari a saman gado ? Ni zaki ɓatawa ɗaki ? Da duka hannayena na riƙe kumatuna na runtse idona dan bana san kallon Dikko a irin wannan yanayin , shaƙemin wuya yayi yace me yasa kikayi min fitsari a saman gado ? Saina kashe ki na gano ki kema munafuka ta ce ashe , dama kince min saikin ɗauki fansa akaina shine kika zubar da ciki dama ko ? Duk yana cikin ɗaukar fansa , zuwa wurin Yazeed shima ɗaukar fansa ne , yanzu kuma kin ɗaukeni mahaukaci dake za'a haɗa kai ayi min asiri shine zaki rainamin wayau wai a cikin bacci kike gani dan kin ɗaukeni kidahumi ko ? Tou saina kashe ki.............. Ihu na farayi amma ya riƙemin maƙoshi na fara kakari ina halbe² Dikko yana cewa saina kashe ki tunda kema munafuka ce na tsaneki Sultanar banza Sultanar wofi , faɗowa nayi daga saman gado ni na rigashi zuwa ƙasa daga saman gadon ya ziro hannunshi ya riƙeni Allah ya bani sa'a na tashi da gudu nayi waje ya biyoni yana ihu mai tada hankali , sulɓewa nayi a ƙofar fita falo , wata irin zamiya ya kawo ya riƙeni na tashi da gudu , wuƙa ya ɗauka a saman firij ya jefeni da ita saida ta caki bayana ta sauka ƙasa , hannuna na miƙa ta baya na riƙe wurin , da gudu na gangare falon ƙasa kamar biri ya sauko ta sama ya rigani bayyana a cikin palon , sai ihu yakeyi yana faɗin saina kashe ki........... Da gudu na koma sama ya sake biyoni yana cewa bana sanki na tsaneki kuma saina kashe ki , tunanin yadda zanyi na fita na rufeshi nakeyi dan idan harna fita waje haka zai bini yana ihu , tausayin Dikko ya kamani sosai kuma na rasa yadda zanyi na fita dan ta ko ina ya riƙe hanya , tsayawa nayi tare da durƙusawa na duƙar da kaina ƙasa na rufe idona cikin kuka nace tou gani na tsaya idan dai har mutuwata zaisa kayi farin ciki na baka fansar raina ka kashe ni , Wani irin halbi yakai min saida nayi baya suuuuuu nayi ƙundunbala ina birkitowa na tashi da gudu ashe dai da gasken kashe ni zaiyi , saman benen na koma nace zan faɗa in mutu , ai nine zan jefaki da kaina , da gudu na sauka nayi waje kafin yazo naja ƙofar kai............. Saina kashe kaina , nidai bansan yadda akayi ba daga haka........ Fashewa Sultana tayi da wani irin kuka mai tada hankali da gudu mahaifiyarta ta shigo tace kin fara ibadar taki ko ? Cikin kuka tace har abadan duniya bazan daina kukan rashin Dikko ba , ina sanshi ׳ ina ƙaunarka mutumina , saida tasha ihunta harta gode Allah sannan tace Dikko zamani mai zaman kanshi inji Inna , ɗan gayun namiji wayayye ajin farko , mai buɗewar ido da gogewar rayuwa , bazan gaji ba kuma baxan daina kukan rabuwa dakai ba har abadan duniya , saida ta samu natsuwa nace tou ina Jiddah take......... ? Ina Al ' Ameen ? Ina Bello ina Dady ina su Amisty ina labarin sahura , kinyi karatun boko ko kuwa a , a , kin haihu da Dikko ko ah ah ? Dan naji a labarin naki baki min zancen karatu da haihu ba , da kika gudu kika zo gidanku "yan gidan su Dikko sunzo ko kuwa........? Ina Suwaiba ? Ina matar da Mami ta haɗaki da ita wacce ta bawa Suwaiba kwalba ? Ina Mardiyya ? Ina Alajinki ? Ina mutumin dake ƙwaƙwale ido ? An cire asirin ko a , a , Goge hawaye Sultana tayi sannan taci gaba da cewa........ *JAMILA MUSA...* Mai karatu ina fatan dai ka gane ? Domin farkon labarin zaku kamoshi idan kuka duba ai kunga labari ne bani ce nake faɗa muku ba Sultana ce take bada labarin rayuwatar da Dikko ne , Allah dai yasa kun gane....... *SULTANA....* Maman Jiddah suna isa Kaduna da asibiti suka fara saida aka wanke cikin Jiddah tas dan tana ɗauke da ƙaramin cikin Dikko wata3 , Maman Jiddah kuwa bayan ta tabbatar da ciki ya fita ta buga waya ta faɗawa Momy ta zubar da cikin dake jikin Jiddah , hankalin Momy idan yayi dubu ya tashi tayi kuka kamar zatayi hauka taso ace ko cikin ta bari dan idan ka haihu da namiji duk matsayin da yakai da matakin daya taka idan dai kuna da zuri'a ka more mishi , dan duk ranar da aka wayi gari idan Dikko ya ida kicimewa tace ta auri Dikko saima an bata kashin bala'e dan tace tanaji a jikinta Dikko wani babban sa'a ne kuma shi ɗin hatimin nasara ne , idan ta bar cikin ta haihu itace haihuwar zatayi ma rana ba Dikko ba , amma abinda ya faru ya riga da ya faru , Dikko kuwa data faɗa masa bai jahilci lamarin ba cewa yayi Allah yasa hakan da tayi shine alkairi a rayuwarshi , kuma ta faɗa masa Maman Jiddah ta tafi da ita akan zata kashe auren shi ta aura mata mai takarar gwamna yace ai wannan ba komai bane ba , idan ita rabonshi ce dasu sake zama idan kuma babu rabo shikenan kawai. Bayan wani lokaci kuma Maman Jiddah tazo tayi wulaƙancin na ƙarshe saida ta zazzage auren Jiddah hankalinta ya kwanta , da Momy ta kira Dikko akan ya saki Jiddah cewa yayi ai itace ta auro Jiddah , sai kuma ya saketa tazo daga baya idan wani abu ya haɗota da "yan uwanta tace shine yaje ya saketa , ya yadda zai saki Jiddah amma rubutunta ya zama a sama zai saka hannunshi daga ƙasa.... Momy itace ta rubuta saki3 kai tsaye ba tare da tunanin komai ba , ta kuma ɗora da cewa saboda Maman Jiddah ta buƙaci sakin Jiddaah dan zata aura mata mai takarar gwamna , bayan ta gama ta miƙawa Dikko ya saka hannu tare da rubutawa. _Ni Dikko Umar Dikko na saki matata Jiddah saki 3 , ina mata addu'a Allah ya bata miji na gari wanda yafi ni...._ Tunda Jiddah taga takaddar saki tayi kuka , kamar ranta zai fita dan ita kwata² bata san haka za'ayi ba , uwarta ke cin kuɗin mai takara kuma itace ta tabbatar mishi da zata kaso auren Jiddah ta bashi ita , ita dai Jiddah tasan tana sanshi a da amma tunda aka zo da zance Dikko ta jingineshi a site , bayan auren Jiddah da Dikko ita kuma Maman Jiddah taci gaba da cin kuɗinshi akan zata bashi auren Jiddah ta ci gaba da aske mishi aljihu ta kuma tabbatar mishi da saita kaso auren Jiddah ta bashi ita , shi kuma yaji baƙin cikin kasashi Jiddah da akayi dan haka ya buɗe bakin A T M ya riƙa yayyafa mata ruwan kuɗin , saida aka kaso auren yace baya aurenta shima idan ta ga wani haka zata kashe nashi ta bashi aurenta , kuma ya ƙara da cewa shi babu wata takarar gwamna daya fito yayi haka ne kawai saboda yaga ita mayyar duniya ce , Ita kuwa Jiddah haka tayi ta guduwa tana zuwa wurin Dikko kuma haka take tarashi a Abuja , shine ya taka mata burki yace ta daina binshi karta ja mishi sharri , taƙiji taci gaba da binshi yace tou duk ranar daya sake ganinta wurinshi zai kashe ta ne kawai kuma ya kashe banza...... Mardiyya kuwa tana tare da Jiddah amma ba'a gidansu ba itama ta koma gidansu da zama amma suna ƙulle dai tunda ana gari ɗaya , Mardiyya itace take raka Jiddah wurin boka ana ci gaba da neman asiri akan Dikko ya shiga tashin hankali yaji idan baiga Jiddah ba yaji kamar zai mutuwa , idan ta haɗo tsibbunta haka zata zo wurin Momy idan taji Dikko yana gari aita barbaɗe² , Momy kuwa bataji wani komai ba dan ita Allah yasa tana san "yan uwanta , Dikko kuwa ko a ƙwalar rigarshi , itama dai Mardiyya tana ta ƙara gyara nata ƙaimun , amma har yanzu kamar suna tura agwagwa ruwa ne dan Dikko bayajinsu wannan jagwalgwalon sihirin nasu bai zo ba , Banda labarin Al ' Ameen haka kuma banda labarin Suwaiba kowa banda labarinshi dan a gidanmu nayi haihuwar farko , na haifi namiji kuma "yan gidansu Dikko sunajin labarin haihuwa suka zo suka ƙwace ɗan wai bazaisha nonon karuwa ba , sunan Dady suka sa mishi { UMAR FARUK } suna kiranshi da Papi , haka Umar ya faɗamin , kuma shine ya bani labarin saukar da Dikko yasa akayimin , ina zuwa makaranta yanzu nayi JSCE kuma tunda naje ban ɗauki position sama da 5 ba , dake kafin na koma saida Inna tayi tsayuwar arfa wurin bani taimako da karatu na musamman a gida , ina js2 nayi jarabawa da "yan js3 , Inna ta siyamin mota nake zuwa makaranta da ita , Sahura ta rasu , kuma dani da Inna munje gaisuwa , kuma naje wurin ahalin Babana a can ƙauye dani da Inna , kuɗin gado basu bani ba sun haɗa gaba ɗaya sun cinye , Dady dai shima rayuwar sai a hankali , Bello kuwa yana can yana fama da rashin lafiya ni banje ba kuma bansan abinda yake damunshi ba , Tou yanzu ina Dikko ya mutu ko yana raye................? Wani irin ihu Sultana ta darkaka daga haka ta ɗauke ashe ba'a tambayarta Dikko ni kuma na tambayeta.......!!! 06/12/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 87 *_Wallahi idan kunji haushi na da gangan , inaji dai kun manta yadda labarin nan yake tun farko , masu cewa na gaji na yanke labari kuma dai matsalarku , kamar yadda na faɗa yadda ta tsara abunta dole haka zanyi idan ya miki a haka kibi idan bai miki ba ki barshi babu lallai fa ba dole dan anyi ciwo an warke ai ba'a ba mutuwa haushi ba , nabi tsakar dare nabi rana nayi safiya nayi marece , naji daɗi ko ba daɗi nabi dai ina muku dan kuyi farin ciki amma jiya kawai dan rashin adalci ni hada masu gayamin kalami mara daɗi hmmm aiko idan har kukaimin haka ni baku kyauta min ba kuma ƙullu yaci amanar koko...._* Inna ce ta shigo cikin ɗakin da sauri inda Sultana take taje ta riƙeta tana shafa mata ruwa take min magana cewa Jamila da Allah kiyi haƙuri da labarin nan haka nan ki tafi sai wani lokaci , Inna ki gafarceni don girman Allah ki barni takai min ƙarshe , Inna tace a , a kije kawai , zan sake magana ta dakatar dani ta hanyar ɗagamin hannu , jiki a sanyaye na fara ƙoƙarin sauka daga saman gadon a dai² lokacin da Sultana ta buɗe idonta dan dawowa daga sumar da tayi wanda ta dawo ta dalilin ruwan da Inna ta shafa mata , cikin kuka tace Inna barta na faɗa mata , Inna tace to karki sakemin wani koke² na faɗa miki , insha Allah Inna , fita Innar tayi ni kuma na koma na zauna ita kuma taci gaba...... Dikko bai mutu ba kuma bai sakeni ba , da na barshi rufe a palo ni bansan abinda ya faru dashi ba tunda ni banyi waya dashi ba kuma ban ganshi ido² ba. Dikko na kira Inna kuma ta shiga amma bata ɗauka ba , da kyau , daga haka bai sake cewa wani abu ba , kaji , naji , tou kace wani abu mana , ai shine nace hakan da kyau , nidai baka so na , baka damuwa da abinda yake damuna , ni bansan abinda yasa kake min haka ba na faɗa cikin hayaniya ina kuka , duk saida na safke mai isata sannan yace tou yi haƙuri An mata gani nan zuwa zan miki abinda kike so , Abinda na fahimta ni a nawa tunanin shine , tunda yana da matsalar fushi da saurin hasala , idan yana fushi kuma baya iya murza kanshi , ban sani ba tunda bai faɗamin dalilinshi naƙin saurere na ba , kila shi zuciyarshi ta tabbatar mishi da cewa lallai ni munafukarshi ce kamar yadda ya faɗa , dole da mamaki ya za'ayi ace sai a mafarki zanga Mustapha , me yasa tunda yasan Dikko baije wurinshi kai tsaye ya faɗa masa damuwarshi ba sai yazo wurina kuma sai a yanayin bacci ? Miye nasabata ko alaƙa ta dashi ? Shi yasa ya warware gaba ɗayanshi ya kasa saita kanshi sai lalurarshi tayi mishi tasiri a dai² wannan lokaci ya alaƙanta abun akan ni dama na zubar da cikinshi dan ina so na ɗauki fansa , kuma na faɗa masa cewa zan ɗauki fansa komin daren daɗewa zansa masa baƙin ciki da damuwa mara gogewa , saiya kira zuwa na wurinYazeed shima yana cikin ɗaukar fansa wato kuma sai yake gani da ni aka haɗa kai akayi masa asiri tunda har nasan Mustapha kenan har yanzu ƙudirin fansa bai goge min daga rai ba , maganar gaskiya ne kenan tunda itama Suwaiba ta kira Mustapha kuma Sultana tasanshi amma sabon rainin hankali wai a mafarki , a ganinshi ina tare da Al ' Ameen bayan shi kuma ya rabu dashi ne saboda ni dan yakai gulmata a wurin Dadynsu Dikko tun lokacin dana zauna gidan Dikko na farko , shine dalilin daya haɗashi da Al ' Ameen ya rabu dashi ya dawo da Ashiru , wanda lokacin da zan koma makaranta a karo na biyu mukayi faɗa da Mardiyya a motar Dikko na dawo katsina su kuma suka wuce Abuja. Zan faɗa in mutu , ai nine zan jefaki da kaina , da gudu na sauka nayi waje kafin yazo naja ƙofar , kai.............. Saina kashe kaina , da gudu na fita daga gidan jikina yana ƙyarma kuma har yanzu ban daina fitsari ba , gaba ɗaya na ruɗe na rasa abinda yake min daɗi , ina gudu ina waiwaye ko ya biyo ni ne ? Nabar wayata a gida kuma ban riƙe number Inna ba amma tunda har nake kiran wayar a da bana samu yau kuma na kira na samu tabbas zan samu Inna hakan ya tabbatarmin tana nan , kuma lokacin ban lafiya ai ta faɗawa Dikko itama zata dawo babu jimawa , ta dawo kenan shi yasa na samu kiran ya shiga , napep na tare na nufi barhim estate.... Kamar yadda nayi tunani kuwa haka ya tabbata , a buɗe na samu gidan na faɗa da gudu nabar mai napep a ƙofar gida , bedroom na samu Inna kwance tana baccin gajiya da gudu na hau saman gadon na riƙeta ina waiwayen bayana , a firgice ta farka tace ke lafiya ? Me ya faru ne ? Gaba ɗaya bana iya magana dan na firgice yadda tunani baya tunani , bayana na buɗe mata inda ya jefeni da wuƙa sai kuma wasu wurare danaji ciwo wurin guje² , sai gefen kafaɗa ta dake min ciwo saboda halbin da yayi min nayi ƙundunbala , mai napep kuwa mai gadi ya sallameshi ya kama gabanshi. Meya faru dake ne ? Inna take tambayata , bana iya magana sai kuka , dan haka ta sauka ta ɗauki wayarta ta fara kiran wayar Dikko , amma duk kiran da tayi masa bai ɗauka ba , itace ta taimakamin nayi wanka ta bani kaya na saka , fita tayi ta samamin abinda zanci kamar baƙuwar abinci haka naci gaba da cin abincin a zalamance ina tsare Inna da kallo , kuma har zuwa wannan lokacin kiran Dikko takeyi , ina gama cin abinci na kwanta naci gaba da bacci wahlala. Inna kuwa kiran Dikko da tayi bai ɗauka ba shine yasa ta fusata ta fara wallahi׳ wannan auren saina kashe shi ni har ya isa in kirashi bazai ɗaukamin waya ba , shiɗin banza shin ɗin wofi me akayi² shi ne ? Ɗan iskan yaro mara kunya daya raina mutane , nan fa ta fara kiraye²n ƙawayenta Dikko ya daki Sultana ya caccaka mata wuƙa yaji mata ciwo , yarinyarta ta lalace kunga yadda Sultana ta koma ? Aure sai kace auren bauta ? Waye Dikko ? Saboda tsabar ma shi ɗan iska ne ya zanemin ɗiya kuma nake kiranshi baya ɗaukar waya , to ni nafi shi kangara da taurin rai naga yadda za'ayi ta koma. Bayan ta gama kiraye²n waya ta tasheni a bacci ina tashi na ganta da wata irin zuƙeƙiyar wuƙa , cikin magana mai kama da raɗa tacemin idan wani yace miki kina san Dikko dan ubanki kika ce kina sansa saina kashe ki idan mutane suka tafi , idona cike da hawaye na ɗaga mata kai , idan kuma kika kira Dikko ko ya kiraki ni kika ɗauka saina kasheki dan ubanki babu wanda yaji babu wanda ya gani , kaina na girgiza alamar to , sakarar banza Dikko baya sanki ya raina uwarki na kirashi ma bai ɗauki wayata ba , dama matar Babanshi ta faɗamin kullum dukanki yakeyi ga tsangwama ga gori ga masifar kishiya ki zubar da ɗan iska kwandon shara ki fuskanci sabuwar rayuwa , sake kaɗa mata kai nayi , Inna tace sai kin samu wanda yafi shi tunda ubangiji ya halicceki nagartacciyar mace , hawaye ne ya gangaromin daga cikin idanuwa nidai nasan wallahi ƙarya ne babu wani inda zan samu wanda yakai Dikko bare kuma wanda yafi shi..... Inna kuma taci gaba da cewa idan kuma kika kuskura kika sake zaɓarshi kika koma zama dashi wulaƙancin da yayi miki a baya sai yafi wannan kina komawa gidanshi na cire hannuna a lamarinki , kuma duk ranar daya sake dukanki idan kika je wurin "yan uwana ko ahalin Babanki ko nan gidan da wannan wuƙar zan kashe ki in huta , yanzu ma da kai na bata ansa , saida ta ƙare duk mai isarta sannan ta ɗaukeni a mota muka tafi asibiti. Tunda muka fita duk idan naga ɓakar mota ta wuce da gudu sai inji kamar Dikko ne a cikinta , tunanin Dikko kawai nakeyi ko yana a wane hali ? Ko ya zaiji idan ya tashi bana nan ? Me yasa nazo gida dama na tsaya a wurinshi gashi yanzu Inna ta ɗauka da zafi harta fara cewa wai ya sossokamin wuƙa , sossakawa fa , jifana yayi fa kawai , yanzu ya zanyi idan na tuna dashi a halin da nake yawan tunaninshi ina gidanshi , wace irin rayuwa zan fuskanta , dandai babu kyau zunubi mai girma ne tsallake maganar Iyaye da kawai saina koma amma ina iya komawa matsallar data fi wannan ta taso ina zanje a lokacin kuma.......? Waye zai ƙwaceni ? Allah sarki mutumina ko kana a wane hali , kana raye ko kuwa ka kashe kan naka kamar yadda ka faɗa......... ? Har mukaje asibiti muka dawo tunanin Dikko nake , ya wani zo ya tsayamin a rai , ji nakeyi dama kawai zan buɗe idona naga mafarki nakeyi ina buɗe idona sai in ganni a gaban Dikko da nayi farin ciki , koda muka dawo gida bedroom na shiga naci gaba da tunanin da bashi da gaira bare dalili , shashshekar kukan Dikko nakeji a zuciyata yadda yakeyi idan yana kwance dani , yadda yakeyin wata ƙyarma yana wannan kukan nashi , bawai ɓare baki yakeyi yana ihu ba , a , a wani iri dai yakeyi mai riƙe zuciya dasa mutum tunaninshi a ko wane lokaci , nashi daban ne dan Alhaji mai gidan "yanci ba irin na Dikko yakeyi ba , kai na Dikko daban ne salon nashi ma yasha banban , uwa uba ya iya sumbatar mace cikin salon da bashi tafiya har abadan duniya , ko ina kike ko ina kikaje sai kinyi tunaninshi dole , Haka nake zaune a gidan Inna tunanin Dikko yasa gaba ɗaya na fita hayyaci na , na ƙara ramewa haske na ya rage ga rashin lafiya ta kunno min kai sai jarabar shan kankana idan na riƙe ƙwallo saina cinyeshi dukanshi , da safe ina tashi dashi zan fara , da rana haka idan zan kwanta bacci , Inna kuma dan na rage yawan tunani yasa ta samanin malami mai bani karatu na musamman a gidan , ina dai tunani sosai amma hakan bai hanani gane abinda ake koyamin ba , itace ta sakani a makaranta kuma ta siyamin motar da nake hawa , ina cikin wannan hali na shigar ƙaramin ciki Inna tabi mijinta sukayi tafiyarsu ta barni a gida dani da wata tsohuwa dan ina tunanin kila mijinta ya sake matarshi dan tafiya da Inna yayi yawa duk lokacin da zaje da Inna yake tafiya , A makarantar da nake zuwa a nan na haɗu da Umar bansan abinda yakai shi ba , naji daɗin ganinshi sosai wallahi sai naga kamar zanga Dikko ko zaicemin gashi mai gida zaiyi waya dani , bayan mun gaisa nace masa ko yana koyarwa ne anan ? Yace min a , a wurin wani yazo , ina taso yayi min maganar Dikko ya ƙiya , nace tou ko yanzu ka daina zama Qerau ne ? Nayi haka nidai dan inji an kamo tashar Dikko amma ya ƙiya , tou ina mai gidan naku ne ? Abinda kin guji mai gida sai kuma kice wani ina mai gida? Kamar ya na guje shi ? Ey ai haka kikayi ma Momy rashin kunya dan tazo tafiya dake , Dady yace aje a taho dake kije kiyi jinyar mijinki shine kika ce bakya san mahaukaci sai an sake ki , ai kinsan da rashin lafiyar nashi kika gudu kika barshi , tou haka akayi ? Na faɗa a zuciyata , Umar kuma yaci gaba da cewa mai gida yasha wahala kema Hajiya baki kyauta ba da kika faɗawa mahaifiyarshi baki san mahaukaci , yanzu yana ina ne ? Waye ma yasan a ina yake ? Yana can Dady ya tafi dashi itama kanta uwarshi bata san inda yake ba , a nan yake faɗamin mai gida Dikko yamin halakci da bai kamata koma miye na baɗa masa ƙasa a ido , shine ya faɗamin Dikko yasa anmin sauka da ragunan da aka yayyanka ya ƙara da cewa wallahi da nasan matsayina da yadda mai gida yake so na yake ƙoƙarin kyautatamin da ban saka mishi da muguwar sakayya ba , nasan mutum nawa Dikko ya rabu dashi saboda kawai nayi farin ciki ? Me yasa na tsananta ? Me yayi zafi haka ? Miye dalilin saka sharri akan alkairi , naji dai babu daɗi amma koma dai miye nasan Dikko zai dawo kuma tabbas zaizo , nice na faɗawa Umar inda nake na kuma yi masa kwatancen gidanmu.... Mai ƙwaƙwale ido kuwa na sake mafarki dashi , abinda Al ' Ameen yayi min ni na yadda dashi 100% shi yasa a gidana banyi mishi shamaki dashi ba , ko ina nan ko bana nan zai shiga gidana kamar gidanshi , tunda na fara neman matar da zan aura na faɗa mata cewa Al ' Ameen Yayana ne , tana ganin girmanshi kuma tana girmamashi a matsayin shi na Yayana , idan bana gari ko wani abu matata ke so Al ' Ameen nake turawa yaje yayi mata , Hmmm , da Al ' Ameen ya samu sake nidai banda wani ƙarfi kuma iyayena basu dashi tunda na faɗa miki daga ni har iyayena duk a ƙasan baban Dikko muka tashi , Al ' Ameen kuma a wancan lokacin shi yayi ƙutu² ya fitar damu a gidan yaje ya haɗo bala'en dashi kaɗai yasan iyakar irin makircin daya shirya akayi mana rashin mutunci a lokacin Dikko baya nan ya raka Dady ganin likita , amma a cikin rashin mutunci babu Momy a ciki dan ita bata cika surutu ba kawai dai idan tana sanka tana sanka idan batayinka ko sabgar ka bata shiga , matan Dady sune sukayi wulaƙancinsu suka koramu kafin dawowar Dady kinga bamu san abinda mukayi ba kuma Al ' Ameen bai nuna mana komai ba duk dashi muka sha jimamin abun har kuka yayi tare da cewa shima zai bar aikin gidan , Babana ne ya bashi haƙuri yace kada abinda akayi mana ya shafeshi a taƙaice dai ya bawa Al ' Ameen baki akan zai haƙura yaci gaba da aiki. Fitarmu a gidan yasa muka fuskanci sabuwar rayuwar babu , talauci ya tiso ƙeyarmu gaba , na kira wayar Dikko bayayi danni a lokacin bansan akwai number ƙasar waje ba , kawai na ɗauka duk ɗaya ce , na kira Dikko har na gode Allah wayarshi bata tafiya dan nayi imani da Allah ko kisan kai nayi idan na zaunar dashi nayi mishi kuka zaiji tausayi kuma ko za'a mutu idan yace mu zauna gidan wallahi koshi Dadyn bazai koremu ba dan idan har Dikko yace masa kaza za'ayi tou sai anyi shi , idan Dikko baya san abu Dady duk yadda yake sanshi saiya fita sabgarshi , Dady yana ma Dikko soyayyar da tunda nake ni ban taɓa ganin irin soyayyar ba , amma saboda sharri da makircin Al ' Ameen saida yasa Dady yayi ma Dikko faɗa karon farko a rayuwarshi zuwanki a rayuwarshi kenan..... Ba'a zagin Dikko ba'a daka mishi tsawa ba'a mishi kallon banza , amma yadda duk baki tunani Dikko yana da tarbiyya dan duk wannan soyayyar baisa ya zama sakaran namiji ba yasa abinda yake kuma Dikko ba ɗan iska bane yana da tausayi amma bashi da mutinci duk yadda baki tunani dan shima ya gaji baƙin hali wurin uwarshi kaifi ɗaya ne idan zaiyi² kawai , idan bayayi babu gudu babu ja da baya bazaiyi ba , yana da halin ko oho kuma yana da mantawa da duk abinda zai ɓata mishi lokaci yana da kafiya ko zai mutu saidai ya mutu ya yadda wani irin hali dai shi kaɗai yasan irin abunshi. Ban wani ɓoyewa mata ta halin da muke ciki ba , ta tausaya min sosai , Al ' Ameen kuwa shine ya samamin uban gida aka bani mota na riƙa aikin mota ina ɗaukar fasinja zuwa jahohi daban² , da nace bana so yacemin na riƙe motar kafin mai gida Dikko ya dawo sai asan abunyi , haka na haƙura na anshi motar idan na tafi sai inyi wata ɗaya bana nan , idan iyalita tana san wani abu zan aiko direbobi masu yo wa katsina sai a bawa Al ' Ameen yakai ma matata..... Ina can su suna nan bansan wane irin ɗan wanke suke jefawa ba , matata mace ce mai mutunci mai biyayya mai kawaici da kauda ido akan abun duniya , amma kinsan yawancin mata suna "yar ciwa²r nan tasu ta idan aka baka kuɗin cefane ka ɗan maƙale wani abu , tou haka matata take idan na aiko mata da kuɗi zata ɓoye batayin abinda ya kamata kuma bata cin abinci mai mahimmanci saita maƙale haka kuma ko ruwan da zatayi amfani dashi bata siya saidai idan an dawo da fanfo taje tabi layin ruwa acan ƙofar gidan wani tsohon attajiri da yake fito da tiyo waje mata suke ibar ruwa. Al ' Ameen kuwa gani yakeyi kamar nine kasashshe wurin kula da iyalita , saiya fara wanketa da ruwan naira dan idan dai kana tare da Dikko tabbas kaima zaka samu bakin gwargwado kayi hidima da rayuwarka cikin rufin asiri kamar dai kaima mai halin ne , haka yake cikamin gida da abokanshi ni ban sani ba yakai cefane yakai abinda za'a dafa tayi girki suci a zauna min a gida har dare ana fira da matata , idan zan dawo gari ya sani dan ina faɗa masa bana ɓoye masa komai , matata kuma bata taɓa faɗamin Al ' Ameen yana zuwa shida abokanshi ba tunda dai na faɗa mata Yayana ne ta yadda a hakan kawai. Bansan yadda akayi ba ya ɓatamin mata ba idan ina nan nine miji idan kuma bana nan Al ' Ameen shine mai gida , haka maƙota sukayi ta bugomin waya suna faɗamin abokina fa yana zagayawa idan bana nan , da farko ban yadda ba sai naga tou idan sharri ne me yasa mutane da yawa zasu faɗa ? Ashe neman da yake mata akwai gejin da zai kai yana amfani da ita an bashi kuɗi ana neman idon matar aure amma sai anyi fasiƙanci da ita so adadin kwanakin da suka faɗa mishi sai a zuba mata maganin a idonta ana zubawa shi kuma tsafin zai cire idonta , ni kuma ranar da zan dawo katsina sai ban faɗawa kowa zan dawo ba , da farin ciki na shiga cikin gidana amma saina samu matata ba ido tana ta kakarin mutuwa , dana tambayeta sai tacemin Yayana ne yake nemanta shine ya cire idonta , daga haka ta mutu. Nasan banda wani Yaya wanda ya wuce Al ' Ameen kai tsaye nayi ƙararshi amma sai ya samu ɗaurin ƙugu wurin manyan da yayi musu aiki sukaje suka baza kuɗi aka kori shari'ar kuma har lokacin Dikko bai dawo ba , haka na ƙara ɗage ƙara duk inda mukaje kuɗi ne suke magana , maimakon inyi haƙuri saina biye sharrin zuciya nima na nemi hanyar tsafi dan nayi alƙawari sainayi kuɗi da gasken gaske , zuciya ta ingizani nima na faɗa sana'ar ƙwaƙwale idanuwa , wanda Al ' Ameen ya haɗani dashi ya bani mota shine aka kaiwa idon matata , dan haka na koma wurinshi nima na shiga ƙungiya kuma da idon nashi matar na fara , na lashi takobin duk matar auren da ta zama makwaɗaiciya saina ƙwaƙwale idonta kamar yadda aka ƙwaƙwale na matata , Ƙungiyar ashe tana da wani tsari wanda ni ban sani ba , su zasu baka magani kayi amfani dashi ido kawai zai fita kai zaka zuba magani su kuma zasu turo tsafunsu ya zama maciji kana zuba maganin a idon mace macijin zai tsotse idon ya kuma shanye jinin jikin mace , idan yasha jinin saiya zuba wani a cikin ƙwarin idon daya cire kafin tsafin ya gama tsafinshi shine jini zai riƙa ɗiga a idon mutum da zaran an gama shikenan mutum ya tafi kai kuma sai a baka kuɗinka , tsarinsu shine shekara 3 sai kaima su tafi dakai , Mu mune ƙanana su kuma sune manya , mu zasu tura muje mu nemo musu matan aure muyi iskanci dasu sai mu zuba magani , kashe duk yaransu sukeyi bayan shekaru 3 sai suyi sabbin zubi , bansan da wannan tsari ba na faɗa ƙungiya kai tsaye saboda wani muradi nawa , ba wurin gudu babu wurin tsira mutuwa tazo min kuma shima Al ' Ameen zai mutu idan dai kayi musu aiki saika tafi saidai a wayi gari ba'asan abinda ya kashe ka ba , to me yasa sai matan aure suke so ne ? Wannan tsarin tsafinsu ne shi ya faɗa musu irin wanda yake so bashi ya basu kuɗi , wasu zasu ce "yan mata , wasu matan aure , wasu zawarawa wasu mahaukata wasu jarirai wani tsafin kuma zaice mace mai ciki yake so , wasu makafi wasu guragu ko "yan maɗigo ko mazina ci , mai wasa da sallah ko wacce ta raina iyayenta , tou su nasu wacce ta raina aure suke buƙata , kinga ke ni ban kwanta dake ba amma kinci kuɗi dana tabbatar ke ba matar aure bace ba suka sa na koraki , amma sun matsa akan mutuwarki dan record in da kikayi sun takura sosai akan ki mutu , amma basu samu galaba dake tsafi yace kinyi kusanci da sallah yawan karatun al ƙur'ani da addu'a lokacin kwanciya bacci , cire hular saman kanshi yayi ya duƙar da kanshi gabana yace kin gani bani da sumar kai bansan ranar da aka cireta ba sun bugamin lamba , shima kuma tabbas nayi imani sun bugawa Al ' Ameen irinta gaba ɗayanmu zakiji labarin mutuwarmu. Tou ta ina ne zanbi nazo inda aka binne tsafin da akayi ma Dikko ne ? Labarin tsafinshi ya goge idan ya dawo zai baki labarin komai banda sauran lokaci wanda aka bani ya ƙare , hankalina kuma ya kwanta tunda shima Al ' Ameen zai mutu , yana faɗin haka ya zama maciji suuuuuu ya gudu da wuce , da tashin hankali na farka kuma tun daga wannan ranar ban sake ganinshi a bacci na ba har yau , Inna ta daɗe a tafiya lokacin data dawo cikina ya shiga wata 7 bata sake komawa ba har na haihu , dana aihu ni na faɗawa Umar na haihu ita kuma Momy tazo har asibitin da muke ta anshe jariri wai ba zaisha nonon karuwa ba yazo shima ya zama karuwi , ta tata rashin mutunci dai² iyawarta tayi gori tace kuma tunda bata san zamana da Dikko duk wanda ya tsayamin a garin nan zata ga wanda ya isa yasa na sake zama da Dikko , zai dawo saki 3 zai bani babu sauƙi , idan kuma ina tunani Dadynsu zai tsayamin kamar na aurenmu da Dikko yaƙiji ya aureni Dady ya goya mishi baya yanzu haka bazai goyu ba , shi da kanshi zaisa Dikko ya sakeni , ban santa ba labarinta na keji , nayi kuka nasha hauka bansan iyaka ba , kuma da suka tafi da jaririn Umar yazo ya faɗamin wai Momy tace ma Dady nice nayi waya wai azo a ɗauki jaririn nan yadda bana san Dikko haka bana san jaririn kuma duk jinin da Dikko ya haɗo dashi bana sanshi , idan basuje sun ɗauki yaron nan ba komai zai iya faruwa tunda tun cikin naso na zubar bai fita ba zan kashe yaron , ta dai haɗa da ɗan makircita. Abinda yasa nake kuka har na tafi shine , Umar yacemin Dady yake faɗa da yana tausayina kuma yana so na tunda Babanshi yana so na , ashe bani da mutunci har na danganta mishi ɗa da mahaukaci kuma nice zan kashe mishi jika daga wurin Babanshi dama na zubar da ciki a farko tunda nice nasa Rabiya tayimin allura , Allah yaba Babanshi lafiya ya dawo saiya sakeni......... Dana tuna zan rabu da Dikko sai inji dama mutuwa nayi kawai na huta da baƙin cikin rayuwa..............!!! Ga Dikko yace baya zuwa bikon mace , iyayenshi sun ɗauki zafi , nima Inna ta gune akan rashin ɗaukar wayar da Dikko baiyi ba kuma har yanzu bai kirata ba , kuma tace idan har na koma gidan Dikko babu ita babu ni har abadan duniya saidai idan Dikko zai zama uwata , tasa kullum ina kiran wayar Dikko akan ya bani takaddar sakina naje nayi aure , wayoyinshi gaba ɗaya basa zuwa , shin yana ina ? Yana nigeria ? Ko yana ina ? Me Dikko zaice idan ya dawo ? Wane hukunci zai ɗauka ? Ya zaiji idan iyayenshi suka ce nice na maida musu ɗanshi nace bana riƙewa saboda bana sanhi , shin zai sakeni ko kuwa zai zauna dani ? Ya zanyi ׳.................. ??? Yadda zanyi da mafita da rabuwa , gaba ɗaya na tattara lamarina wurin ubangiji duk abinda ya zartar a kaina dama haka yazo a rubuce kuma bawa bai isa ya goge ƙaddara shi ba , 07/12/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA....* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 88 *_Godiya mara iyaka zuwa gareku ,_* 👇🏻 *_HADIZA MATAWALLE..._* *_RUKY " " " " " "_* *_FATY " " " " " "_* *_ZEE " " " " "_* Ngode sosai ku huta gajiya Allah ya daɗa zuminchie... *_Gaisuwa marar iyaka zuwa gareki ZAINAB AHMAD KADUNA { Sheke } ina miki fatan alkairi tare da NA'IMA ABU KANKIYA..._* Tabbas wannan zance haka yake , Allah ya bawa Dikko lafiya ya ƙara soyayya a tsakaninku ya kuma ƙaro irinsu Papi hada Junior Dikko muzo musha suna , murmushi Sultana tayi amma batayi magana ba , saukowa nayi daga saman gadon ina ɗan gyarawa cewa ni zan wuce zan tara ƙarshen labarin a takardar labarin rayuwarki , godiya tayi min sosai mukayi sallama cikin mutunci da mutuntawa , itama Inna munyi sallama cikin mutuntawa na barsu lafiya nima zan tara muga ƙarshen labarin tare daku masoyan Sultana & Dikko , Bayan Jamila ta tafi wanka na farayi tare da ɗoro alwallah dan magrib ya gabato , ina fitowa kayana na saka na shafa mai sama² da powder naci gaba da tattara kayan da Inna keyin parking zatayi tafiya zuwa Abuja ita da mijinta. Inna ce ta shigo ɗakin tana cewa wai ga wani Abbakar can yana miki sallama a waje , ba tare dana kalleta ba nace wane Abbakar kuma ? Abokin ɗan iskan yaron nan mana , murmushin jin daɗi nayi a zuciyata a fili kuma na ɗan basar cewa Hajiya Inna kenan waye ɗan iskan yaro kuma ? Dikko , Inna wai me yasa kikejin zafin Dikko da yawa ? Bana san yaron ne kwata² gaba ɗaya ya siremin kamar tusar safe.... Saura kaɗan na fita na zageshi dan dai kar ace na haukace , ai bana nan ma dan ni bazanje ba , aiko sai kinje kodan ya ganki baki lalace ba ci gaba aka samu ba ci baya ba yaje ya bawa Dikko labari , nidai Inna gaskiya bazan wani je ba , aiko sai kinje kuma kin barbaɗa masa rashin mutunci yadda Dikko da uwarshi suka tozartaki kema sai kin tozartasu kuma sai ya baki sakinki tunda basu da mutunci.... Inna kenan na faɗa a raina , a zahiri kuma na bita da kallo , kin wani tasani kina kallo kamar niɗin baƙuwarki ce ki wuce kije ki dawo , banyi magana ba na ɗauki hijabi na fice , a harabar gidan naga wata irin lutsetsiyar mota ɓaka sai sheƙin sabinta take tunda na taho nake ganin kaina a jikinta bana iya ganin na cikin motar shima a gilashin kaina nake gani saboda yana da duhu , jikina ya bani ba Dikko bane a ciki amma ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba duk inda wannan motar ta fito tashi ce kuma ban taɓa ganinta a cikin motocinshi ba , A jikin motar na tsaya na ciki ya sauke gilashin motar tare da cewa sannu , yawwa na faɗa rai a ɗan haɗe , ya gida ? Lfy , kin gane ni ? Ey a Bakori daka kawo katifa a motar ka ko ? Murmushi yayi tare da cewa ashe baki da mantuwa , ya akayi ne ? Gefenshi ya kalla ya ɗauko wata "yar leda bansan ko miye a ciki ba ya miƙomin ba tare dana ansa ba nace meye a ciki ne ? Ki ansa koma miye zaki gani , hannuna ɗaya a ƙugu ɗayan nake nunashi amma bada ɗan yasa ba kawai ka faɗa danni bazan karɓa ba , ki ansa An mata , ban sake magana ba na juya na wuce dan kar in ɓata lokaci Inna ta biyoni ta yabamin , sallah na samu Inna tanayi nima abin sallah na shimfiɗa na kabbara sallah. Kai Ashiru ɗauki yaron nan ka maidashi gida fita zanyi , riƙe Dikko yaron yayi yana kuka cikin gwaranci yace bajan je ba tare da maƙale ƙafaɗarshi , Ashiru yace mai gida bazai zo ba , kai da Allah ɗaukarshi basai zaije ba ku tafi zanzo nima , ƙara riƙe Dikko Papi yayi yana kuka , kafin Dikko ya sake magana Abbakar ya shigo inda Dikko yake tsaye yayi parking tare da sauke glass yace DK bata ansa ba , ko tace maka wani abu ne ? Yadda sukayi da Sultana ya faɗa masa , babu damuwa An mata tana da matsala , ni bansa abinda ya faru ba tunda bana nan bazan iya ƙarda komai ba , kawai anje an kwaɓa abu duk sun jagwalgwale min komai , taya kai tsaye zan tunkari inda take bayan Momy taje ta ɗauko yaro ta taho dashi dole kowa zaiji babu daɗi , Momy Dady duk su ba'ayi musu dai² ba , itama Mamar kanta yayi zafi , kallon Ashiru yayi tare da cewa kiramin Umar yazo yanzu²n nan ya ƙarasa maganar yana kallon Papi daya duƙunƙune shi , isowarshi kenan su Nabeela suka zo dashi yi ma Dikko sannu da hanya da kuma dubashi da jiki , shi kuma sai wani bin Dikko yakeyi kamar yasanshi dan ko su Nabeela gajiya sukayi suka tafi suka barshi yaƙi binsu , iyakarshi gidanshi baije gidansu ba , Kai ka sanni ne ? Ya tambayi Papi fuska a haɗe , yadda yayi abun yasa Papi yayi dariya danshi a tunaninshi Dikko wasa yakeyi mishi , kai kasanni ne nace ? Ƙara ƙyalƙyalewa da dariya yayi yana kallon Dikko , tsoki yayi tare da buɗe mota ya sakashi a baya ya rufe yace ma Ashiru idan Umar yazo kace masa nace yaje wurin An mata haka kawai zakace masa , Ashiru yace to , zagayawa yayi ya shiga gaba suka fita da Abbakar , A palon Momy ya samu Jiddah tasha wanka na ɗaukar hankali da firgita tunani , Dikko ne a gaba Abbakar yana ɗauke da Papi da yayi bacci , suna shiga Momy ta ansheshi tana cewa Nabeela taje ta kwantar dashi , ansar shi tayi ta shiga ciki dashi su kuma suka samu wuri suka zauna , Yaya DK sannu da zuwa ya ƙarfin jiki ? Ko inda take bai kalla ba bare ta sa ran zaice yawwa , gaishe da Abbakar tayi shidai ya ansa saida ta rufe bakinta sannan Dikko ya gaishe da Momy , ta ansa cikin jin daɗi tana nuna yanayin farin ciki ɗanta ya dawo lafiya kana kallonta dai kasan tanajin daɗi ne a daren nan , labari marar ma'ana taita bashi akan Papi shidai shiru yayi baiyi magana ba kuma ko murmushi baiyi ba hankalinshi da kaf tunaninshi yana can wurin tunanin yadda zai taro matsalar da suka haifa da kansu , amma An mata ta bashi mamaki yayi tunanin ko bashi ne da ita suka haifi Papi ba zata iya riƙe mishi ɗanshi ko bayan baya nunfashi amma shine ta bada yaro da baiji bai gani ba da yana da ƙarar kwana daya mutu shikenan ya sake tashi a zero..... Momy ce ta dawo dashi daga tunanin da yakeyi taci gaba da fanfo da ƙaga abinda bai faru ba kuma ba'ayi ba akan Sultana tayi mata rashin kunya ita da uwarta , yadda ta faɗawa Dady haka ta faɗawa Dikko ta kuma ƙara da cewa tuntuni suke aiken rashin mutunci akan ka sakar mata "yar ta , hankalin Dikko akan waya yace wa suka aiko ? Wata maƙociyarsu ce can Barhim , sai kuma kai tsaye aka barta ta shigo saboda an aikota daga gidansu An mata ? Ya ƙarasa maganar yana tsare Momy da ido , tou ƙarya nake Dikko , ah yi haƙuri ba nufi na kenan ba , daga haka bai sake magana ba sai ita taci gaba da farfaɗo maganganu marasa daɗi da ɓatanci , a ranshi kuma yace da na saki yarinyar nan gara na dawo da ita muci gaba da cakuɗawa daga inda aka tsaya har tayi hankali danshi kullum kallon Yarinya yake ma Sultana bai san ta ƙara girma ba , saida Momy ta tsiyaye mai isar ta tana faɗa tana kunnuwa ta tata rashin mutunci iyakar iyawarta , har tayi ta gama Dikko bai sake magana ba , ita ta gaji da kanta tace ya tashi ya bata wuri sakaran da baisan inda duniya ta nufa ba , miƙewa yayi ya fice Abbakar ya biyo bayanshi amma Jiddah Momy tana fara faɗa ta tashi.... Bai fita ba saida ya haɗu da sauran "yan uwanshi suka gaisa suna mishi sannu da addu'ar Allah ya tsare gaba ya bashi lafiya mai ɗorewa , suma dai sunyi mishi labarin Papi wai ya tambayi Papi ina Mamanshi yaji me yake cewa , murmushi kaɗan Dikko yayi wanda iyakarshi kawai a saman fuskarshi ya tsaya baizo baki ba , bai wani daɗe ba ya wuce saboda Dady baya nan , Abinda yasa ya tura Abbakar wurin Sultana waya ce ya bada yakai mata zasuyi magana dan tabar wayarta a goruba road ta gudu tou yaso ta ansa wayar suyi magana yaji ita kuma Mama ko tayi fushi ? Wai me yasa wasu iyayen miji suke tsanantawa akan matan "ya "yansu ne ? Suke nuna ƙiyayya tsana da kuma hantara ne ? Matar ɗa abun so ce kuma itama ɗiyarki ce inda mutunci , abin tausayi ce ta wuce wulaƙanci , baki san yadda take zaune da ɗanki ba , tanajin daɗin sa ne ? Ko kuwa wahalarshi take sha ? Idan kinsan ɗanki yana da kyawawan hali kila ita matarshi munana yake mata , idan ke yana da haƙuri a wurinki kila ita rashin haƙuri yake mata Koma dai wane irin baƙin hali ɗanki yake da tadai yi haƙuri ta zauna dashi , waye yasan ni ina dukan An mata ne ? Duk wanda ya ganta idan dai mai hankali ne da ilimin karantar rayuwar ɗan adam yasan An mata bata da kwanciyar hankali , na doketa na zageta mari rashin haƙuri akanta gashi kuma sam² baya mata uzuri akan komai ƙanƙantar laifi idan tayi mishi , gaskiya iyayen miji ku daina tsanantawa wa matan "ya "yanku a gidan aure dan baku san yadda su matan suke haƙuri da "ya "yan naku ba , An mata tayi haƙuri da halinshi tuni ba tun yau ba kuma a hakan dai tana sonshi bata daina ba , ko a yaddar mishi ko kar a yaddar mishi , ko aji daɗi ko kishirya hakan shidai ba yaro bane yasan abinda yake shine yake auren matarshi dalilin wani bazaisa ya sake aurenshi ba , dan haka babu wani abinda ya dameshi dasai an yadda ya dawo da ita kawai zaije ya taho da matarshi , Umar ne zaune a palon Inna yaci abinci yasha lemu ya wani mimmiƙe yana kallo , dan ita Inna bata san Umar ko daga ta ina ya fito ba kawai dai tana gani na dashi data tambayeni waye shi nace mata a can gidan Babana lokacin bata nan ne yake min mutunci tou shine take cewa ya shigo idan yazo , A zahiri kallo yakeyi amma a baɗinance wallahi rahotanni kawai yake iba , danshi Allah yasa mishi bakinshi bashi da saiti akan magana duk abinda ya gani ko yaji kamar mai aljanun surutu saiya faɗa , ya daɗe sosai daya tashi tafiya Inna ta bashi kuɗi wai yasha mai , Ƙarfe 8:21pm yabar gidanmu misalin 8:41pm Dikko ya bayyana a gidan , kuma kai tsaye ya shigo har palo ba tare daya bari an bashi izinin ya shigo ba , da sallama ya shigo daga ni har Inna muna ciki ina tayata tattara kayanta , jin muryar Dikko yasa na sauko daga saman gado da gudu Inna tana cewa ina zakije ne ? Banyi mata magana ba na bayyana a cikin palon a dai² lokacin da itama Inna ta fito , gefe na koma ina maida numfashi Inna da Dikko suna fuskantar juna kan Dikko a ƙasa ni kuma duk su nake kallo saina kalli wannan na kalli wancan , Mama barka da yi..... Fizgoni Inna tayi muka koma ciki gefen gado ta zaunar dani ta durƙusa gabana ta riƙe hannayena , cikin lallashi tace karki manta da yadda kikayi kuka Dikko ya turo aka ɓanɓare miki yaro daga aihuwarshi yace a anso mishi ɗanshi baya so yasha nonon karuwa , kinaji kina kallo suka anshe ɗan suka tafi dashi , a gaban idonki nayi ta kiranshi a waya yaƙi ya ɗauka daga baya ma ya rufe wayoyinshi gaba ɗaya kuma har zuwa yau bai kirani ba , wannan shine ya dace ya zama siriki na ? Mijin da bashi mutunta mahaifiyarki ? Mijin da baya so ɗan sa yasha nononki yace miki karuwa ? Kar ɗansa yasha nononki shima ya zama karuwi ? Wannan shine mijin daya dace ya zama siriki a gareni ? A , a , tou sakinki zai baki maza nawa kika sani suna jiranki ? Me zakiyi da Dikko daya fara tsofewa ? Nan zai tsofe ya barki ki shiga tararrabin rayuwa , sakinki kawai nake so ki anso zakiga mijin da zaki aura yafi Dikko duk abinda kike tunani kiyi ƙoƙari ki more rayuwarki tun kafin duniyarki ta ƙare. Inna waye zan aura ? Wayarta ta ɗauko ta nunomin hoton wasu matasa har 4 wai idan bana san wannan ga wannan kuma duk shekarunsu kamar na Dikko ne , bayan na gama gani nace umm umm suma dai duk sun tsofen tunda naga zasu kai shekarun Dikko , amma aisu basu ciccika fuska da gashi ba , gemu take nufi da ƙasimba , taci gaba da cewa ya sakeki ki auri zaɓina ko kuma dani dake kowa yaja tashi da'irar danni gaskiya bana san Dikko a matsayin siriki , me yasa Inna ? Saboda yaron baida kunya ko kaɗan , to me yasa kika yaddarmin na aure shi tun farin fari ne ? Wancan karon ra'ayi ne yanzu kuma muradi ne shin Dikko kika ɗauka ko ni.............??? Haba harma sai an tambaya ? Ai ke na zaɓa Inna , idan ni kika zaɓa ta faɗa tana bani biro da takarda a hannuna anan ciki zaki dawomin da ansar , ansa nayi na fito jiki a sanyaye ban samu Dikko a palo ba , dan haka na fito harabar gidan , a mota na sameshi zaune yana waya , tsayuwa nayi ina jira ya gama , buɗe murfin motar yayi ya fito da duka ƙafafuwanshi waje sannan ya kirani da hannunshi ɗaya wanda bai riƙe waya dashi ba , matsawa nayi ya riƙeni jikinshi ni kuma na dafa kafaɗarshi ina wasa da gemunshi da ɗayan hannuna , murmushi yayi ya kalleni amma bai daina magana a waya ba ni kuma baiyi min magana ba yadai tsareni da ido yana kallona. Ɗauke idona nayi gefe ɗaya na janye hannuna daga gemunshi , kamo hannun yayi ya maidashi a dai² lokacin daya ajiye waya , riƙo ƙuguna yayi da duka hannayenshi ya jinjina shi tare da ɗan girgiza jikina sannan ya ansa biron hannuna da takaddar ya ajiye a gefe , jawoni yayi jikinshi yace me ne ne zakiyi da ? Ya nuna inda ya ajiye , Inna tace ka sakeni , wane irin saki haka babu daɗin ji ? Shiru nayi banyi magana ba , yana nan dai da halinshi na faɗa , yace ina miki magana kinmin shiru kuma kinaji , yanzun ma banyi magana ba , turani yayi baya daga jikinshi yana cewa wuce ki bani wuri , da sauri na sake komawa , dakamin tsawa yayi karki sake ki taɓani ya ƙarasa maganar yana gyara zamanshi zai rufe mota , Ƙara matsawa nayi da sauri na riƙe murfin motar cikin rawar murya nace yi haƙuri na bari , cikin fushi yace ni duk abinda kika min banji fushi a kanki ba saike mai Mama zaki wani cemin wai tace miki na sakeki ? Me nayi miki ? Ƙiyayyar harya kai fagen saki ? To me yayi zafi haka ne ? Ke ko kunya ma bakij.... Nima irin abinda ya taɓayi min can² baya nayi mishi nima na kulle bakunan mu wuri ɗaya , da sauri ya sauke ajiyar zuciya ya riƙeni jikinshi sosai yanayin lunfashi da yanayin gajiya , riƙe fuskarshi nayi da duka hannayena gefe da gefen fuskarshi na lumshe idanuwa na nima inayin irin yadda yakeyi idan yana kwance dani , murmushi yayi mai sauti amma bai raba bakunanmu ba kuma ba magana yayi ba yana dai ci gaba da fitar da numfashin kamar wanda yakeyin mura , miƙa yayi a kasalance da niyar ƙara jawoni jikinshi najiyo muryar Inna tana ta kwararamin kira cikin ɓacin rai , ƙoƙarin raba jikina da nashi na farayi amma ya wani riƙeni sosai , ƙyarma jikina ya farayi har yanzu bai saki bakina ba , nace Dikko Inna ke kirana kar tayi faɗa fa , fita yayi daga bakina yace shigo , Inna kuma ƙara kira takeyi Sultana........ Ƙoƙarin kwace hannuna na farayi daga riƙon da yayi min dan tafiya wurin Inna , shi kuma yacemin shigo , Inna fa ke kirana , Innar , shigo nace , ah ni gaskiya bazan shiga ba , shigo nace , haba Dikko wai meye haka ne ? Nima bansan koma miye ba , Sultana.......... Na rantse da Allah idan nazo wurin nan saina zaneki , Inna ta ƙara² faɗa , cikin kwantacciyar murya yace karki tafi ki barni , ko kina so inyi rashin lafiya ne ? Ya ƙarasa maganar yana yimin yaudararren kallonshi fuskarshi ɗauke da kyakkyawan murmushin shi mai ɗaukar hankali , girgiza kaina nayi alamar a , a , tou zo muje kinji jarumata yayi maganar cikin sigar lallashi , ita kuma Inna zuwa wannan lokacin ta ƙufule ta daina kirana , ni kuma Dikko ya ɗaukeni a mota muka bar gidan....... Shin Inna laɓewa tayi ta gani abinda mukeyi ? Me yasa ta kirani , Allah kaɗai ya sani. Saida muka fita daga barhim na matsa na riƙe Dikko , murmushi yayi cikin izza sannan ya riƙeni da ɗayan hannunshi ɗayan kuma ya riƙe sitiyari amma baiyi magana ba , kwantar da kaina nayi a jikinshi fuskata tana kallon kyakkyawar fuskarshi saida naja gemunshi nace ina kaje ne ? Ba da fuskarshi ya kalleni ba da idonshi ya kalloni kaɗan sannan yace nima bansan ina naje ba , ba kin gudu kin barni ba ? Baki san ɗana ko An mata ? Hmmm ba komai ni ina sanki a haka , Sauka nayi daga jikinshi cikin hayaniya nace bana san² , ai basai kin faɗa da yanayin fushi ba nasan yadda abun yake , ai nima na sani , karki min rashin kunya ƙaramar yarinya , Dikko nayi , ai baki da lissafi mai gotacciyar kwalwa dake kuma saina ƙara aure tunda har yanzu baki da lissafi , kaje ka ƙara mana ba kaji abinda Inna tace ba , shiru yayi bai sake magana ba saini nayi ta rattafa ɗimi kamar wacce ta lashi wuta , kafin muje G R A harna ratto mishi yadda Momy tazo ta ƙwacemin ɗa , har yanzu bai sake magana ba , bayan yayi parking bai fita ba kashe motar yayi ya ɗauki wayarshi yana latse² , ni kuma har zuwa wannan lokacin abin faɗawa Dikko bai ƙare a wurina ba , saida na gaji na ɗauke da kaina , cire makullin motar yayi tare da cewa muje yayi maganar ne a dai² lokacin daya fita daga motar , nima fita nayi nabi bayanshi ina cewa kuma ai ni banajin tsoron kishiyar ko an faɗa maka ni ɗin lusarar mace ce mai ma auren miji kuka , jinjina kai yayi cikin ɓacin rai , saida muka raba palon 2 ya juyo yace nidai kika raina ko ? Yadda yayi maganar cikin ɗaure fuska yasa na koma baya ina kallonshi , jinjina kai yayi cewa muje yayi gaba nabi bayanshi har ɗakinshi.... Yau da kanshi ya rufe ƙofa , kuma bai wani bani wannan maganin nashi da yake bani idan zai kwanta dani ba , na yau wani iri ne daban saida nasha akaje wasa , kamar dai na daren farkonmu yauma saida ya tabbatar ya gama gigitani yace tunda na raina shi saida in tashi in tafi gida , kamar sakara haka naita kuka ina bashi haƙuri amma sam Dikko ya kifa kanshi wai bayajin yaren da nake mishi magana dashi , nayi kuka kamar raina zai fita ina cewa bana san hakan wai kai me yasa mugu ne da Allah ? Ba kin rainani ba ? Tou yi haƙuri , cewa zakiyi kin bari bazaki ƙara ba , na bari bazan ƙara ba , ɗan gajeren tsoki yayi cewa kawai kije idan kinyi hankali sai kizo inyi wasan danbe , riƙeshi nayi ina kuka yace min na fita jikinshi karya kasheni , ƙin fita nayi naci gaba da kuka ina kallonshi , dariyar mugunta yayi min sosai yana min video , kuma ban daina mishi magiya ba , haka yaita gwalgwala ni , yana dariya wai saina faɗa yadda ake cewa wasan danbe da indianci idan ba haka ba shi bayaji da hausa , cikin ɓacin rai nace ban iya ba buɗemin ƙofar na tafi , anƙi a buɗe ba makullin a hannuna yake ba ? Idan kece kika kulle ai sai kinga dama kike buɗewa , sai kin faɗa , kuma ko kin faɗa sai Dikko yaga dama zai danbace ƙaramar yarinya ya ƙarasa yanamin gwalo , da nazo nayi shiru sai inji bana iyawa , kamar wata zararra haka ya haukatani a ɗaki naita hauka yana min dariya , saida ya gaji da ranfa ni sannan ya kwanta dani da wani irin baƙon salo , daga farko naji daɗin yadda yayi min daga ƙarshe saida yayi ɗabi'ar tashi dan idan baiyi mugunta ba ji yake bai haɗu ba , da naji azaba nayi magana sai ya nunamin vidion yace kefa kika roƙa , saida ya tabbatar ya wahalar dani sosai sannan yace gobe ma ki sake raina ni kindai ga amfani na... Tare mukayi wanka , kuma kayan da nazo dasu sune na maida , saida na gode masa kamar yadda ya koyamin , shine da kanshi ya maidani gida , bayan yayi parking yace kin yafemin ? Saida nayi shashshekar kuka nace na yafe maka , rumgumeni yayi a jikinshi yace Allah yayi miki albarka , nace amin , kuma wasa nakeyi miki bazanyi wani aure ba , ai babu mai iya haƙuri da halina saike , ina sanki sosai "yar matana Allah ya ƙara miki haƙuri da halina , banyi magana ba ina kallonshi dai , murmushi yayi tare da sumbatar saman bakina , yace yi haƙuri don Allah , banyi magana ba har yanzu , da , da ne nake masa wannan kallon daya zazzaromin ido yace daina kallo , kinyi haƙuri ko ? Ey , tou jeki , kuma ki huta gajiya ngode , yawwa nima ngode na faɗa a dai² lokacin dana fita na rufe ƙofar bam , Ajiyar zuciya ya sauke bayan Sultana ta shige , vidion da yayi mata ya kalla sannan ya ƙyalƙyale da dariya yace baiwar Allah An mata , cike da tausayin Sultana da soyayyarta mai girma ya ɗaga mota yabar gidan. Har yanzu Inna batayi bacci ba , a palo na sameta zaune tayi takurarren zama , Inna har yanzu bakiyi bacci ba ? Na tambayeta , ummmm ta bani amsa ba tare data kalleni ba , kuma cikin yanayin jin kunya dai ta bani ansar , zan wuce ciki ta kirani har yanzu bani take kallo ba ta kasa haɗa ido dani kwata² , ɗazu bakiji ina kiranki ba ? Yi haƙuri Inna banji ba , dama taya zakiji tunda kina so kibi Dikko , shiru nayi ban sake magana ba , tou tsaya kiji ina tsaye wurin ganin na nemo miki mutuncin ki da martabarki harni zan kiraki kiyi kunnen uwar shegu dani kibi namiji a gaban idona ke mara kunya ko ? Yanzun ma shiru nayi mata , idan wani abu ya faru ke kin isa kice Dikko ne ? Munafikin Allah ya saɗaɗo ya biyo dare ya ɗaukeki to ina kukaje ? Kaina na kallon ƙasa nace kiyi haƙuri don Allah , Wallahi bazanyi haƙuri ba saidai ki tattara kayanki ki koma wurin Dikko danni babu mai jamin dogon zance da karkata kai ina wallahi² , tunda kina san Dikko kawai kije ki koma amma ki sani idan har shi yayi miki wani abu ko "yan uwanshi karma ki sake kizo min gida na faɗa miki , tunda kika zaɓi Dikko wallahi na bar mishi ke duka , dama ai nace miki idan kika zaɓi Dikko a kaina saidai dani dake kowa yaja tashi da'irar , kin bishi kuma kin dawomin babu takaddar sakin ki , zanyi magana ta dakatar dani ta hanyar dakamin tsawa tana ci gaba da cewa jaka ya ɗaukeki sakarar banza da baki da kyakkyawan tunani , tunda kin bari ya rainaki ya ɗauke matattara sauke buƙatunshi , yazo yayi miki daɗin baki kin kwashi jiki kin bishi amfaninki kawai ya samu natsuwa dake ya samu kuma ya maidoki hoto kawai dake , to sai kije idan wahala ta kasheki kece kika huta idan sun barki kin zauna ɗangin nashi kiyi ta haihuwa suna ɓanɓare "ya "yan ta ƙarfi da yaji , shi kenan kin zama jaka saidai kullum kisha wahalar ɗaukan ciki ki haihu a barki da shan ruwan zafi , In , ki rufemin baki ko inci mutuncinki a daren nan , kuma sai kin barmin gida tunda kin zaɓi Dikko akaina , I , ki rufemin baki wallahi kika sake kamo suna na saina wulaƙantaki , simi² na wuce ciki ita kuma tana cewa ki tattara kayanki yazo ya tafi dake , tunda kinƙi ya sakeki ki aure wanda nake so a cikin maza 4n dana nuna miki......... Da safe Inna haka ta barbaɗomin kayana a tsakar gida ta rufe ɗakunanta , duk haƙurin dana bata² saurareni ba bayan ta cemin kar na sake naje inda duk wani ɗan uwanta yake , duk saboda ta kirani Dikko yace nazo muje akan me zan bishi ? Kuma itama ai tasan kiran wanda yake gaba tsakanin miji da uwa , kawai dai tana so ta kashe min aure ta auranmin wanda ranta yake so , a cikin mazan da tace na zaɓa su tana da tabbacin daga su har iyayen nasu dashi kanshi wanda zan aurar bazasu wulaƙantani ba ? Dikko baice baya so na ba , bai wulaƙanta ni ba , tou wai me ma yayi min ne ? Ko sai in kashe auren nawa inzo in zama na Jiddah nima in tashi biyu babu , idan kuma nabi irin nata ra'ayin ita Inna kenan itama ba wannan mijin aka ce ta aura tun farkon farko taƙi aurensa taje ta auri Babana , saini zance Dikko ya sakeni inje inma kashe auren Allah ya jarabeni da fitinar duniya , zawarci ai shima ɗaure yake da ƙugunshi , Saida nayi musu rakiya har wurin mota duk addu'ar sauka lafiya da nayi mijinta kaɗai ya ansa ita kuma ko kallona batayi ba , addu'a ta dai su sauka lafiya kuma su dawo lafiya. Haka na yini a filin gidan Inna har kicin inta ta rufe abinta , ina zaune a ƙofar ɗakinta data rufe kamar asara duk abinda zanyi a bayin tsakar gida nake huɗɗoɗina amma har dare babu abinda naci saboda banda ko si² a hannuna. A ranar yau Dikko bai zo ba , kuma a maƙotan gidan Inna na kwana ganin zan kwana da mai gadi , a gidan ne suka bani abinci naci , Washe garin tafiyar Inna ma Dikko baizo ba , kuma ranar ma a maƙota na kwana , saida akayi sati biyu da tafiyar Inna Dikko yazo , ina maƙota mai gadin gidan Inna ya kirani , yauma babu driver ba ɗan rakiya a mota na sameshi zaune daga shi sai wani ɗan kyakkyawan yaro anci mishi gayu cikin wata irin zuƙeƙiyar shadda { getzner } hutu ya zauna a jikinshi sosai , kallo ɗaya zakayi ma yaron kasan gidan kuɗi ya fito daga shiyar manyan mata gogaggi wanda suka san darajar wanka da gayu sai kuka yakeyi , Yaya mu cafi jida ya cire hular da aka ɗora mishi a kai ya riƙe a hannu sam ya hana Dikko yayi min magana , Kai ni bazan tafi ba waye yace ka biyoni ? Ni a nan zan kwana , ƙara fashewa yayi da kuka yana ta maimaita suje jida , kashe motar yayi yana cewa muje ciki , taya zan iya faɗa masa Inna ta kulle ko ina ne ? Ah kawai mu zauna a mota shi kuma harya fito da yaron daya zo dashi yasa na ɗaukeshi sai yagushin fuskata yakeyi yana kuka baya co , ƙafarshi ɗaya a waje ɗayar a ciki yake miƙomin wayoyinshi da hular da yaron ya jefar , daka mishi tsawa Dikko yayi yana cewa kai bana san iskanci kaji , shiru yayi yana kallon Dikko yana kuka kaɗan² , saukeshi ya tafi da ƙafafuwanshi , da sauri na sauke shi nima ina kallon Dikko kamar yadda yaron keyi tare da cewa wurin fa a rufe yake.... Tou kije ki buɗe yayi maganar hankalinshi nakan wata leda da yake dubawa , shiru nayi na rasa abin cewa , da faɗa ya juyo kunzo kunmin tsaye nace kuje ciki zanzo , babu makulli a hannuna , sai a hannuna nake da ? A , a ina nufin bana nan Inna ta fita bata dawo ba , daga Abujar ? Kai tsaye nace masa Ey , da ɗan yanayin damuwa yace shikenan ku shigo mu tafi ba tare daya kalleni ba yayi maganar yana gyara zamanshi ya rufe , Zagayawa nayi zan shiga motar yaron nan ya fara kuka bana shiga musu mota , Dikko yace kai zan zaneka wallahi , fashewa yayi da kuka yana turani baya , juyawa Dikko yayi bayanshi ya ɗauko dorina yace masa gafara daga nan , cikin kuka yace bata ciga ya matsa baya ya riƙemin hijabi wai basu zuwa dani , da bulalar ya kawo duka yaron ya matsa yana kuka bai sameshi ba sai cewa yakeyi bacu zuwa dani , Dikko yace An mata shigo muje mu barshi a nan , ɗaukarshi nayi na sakashi ciki nima na shiga na rufe , tunda muka ibi hanya Dikko yake faɗamin Mama ta kirashi ta tozartashi iyakar iyawarta , abun bai mishi daɗi ba dan saida tasashi ya sameta har Abuja ta wulaƙantashi hmmmm , cika idonshi yayi da hawaye yace ta faɗi maganganu masu muni a kaina marasa daɗin ji , nayi mata uzirin ɓacin rai nasan duk fushin abinda ya faru ne ta tattara ta sauke a kaina da bansan abinda ya faru ba , ina can ina jinya banma san ina nake ba , ina nan zan barki kizo ki zauna gida har banzo ba ? Da nasan inda kaina yake ko a waya ai zan kiraki tunda gashi ranar dana dawo ai ranar nazo wurinki , kuma ita Mamar da tace ta kirani ban ɗauka ba idan naga kiranta zan basar ne ? Haka nan ma nake kiranta na gaisheta babu ranar da bana kiranta na gaisheta tunda na aureki , tou idan baki saki ba ranar da kika kulleni a ɗaki kika gudu kinsan yadda na kasance a wannan ranar ? Ba abinda ya dameni da yadda ka kasance har ni kake cema kayi ma Inna uziri idan bakayi uzirin ba me zakayi ? Ko itama haukar zakayi mata ne ? Cikin ɓacin rai yace aike yarinya ce uzirin ne hauka ? Ni nasan darajar duk wanda ya haifi ɗiya ya bani , bawai rashin kunya ko rashin ɗa'a yasa nace nayi mata uziri ba , ina nufin nasan taji fushi da ɓacin rai akan abinda akayi miki na ɗauke Papi ya nuna yaron yana ci gaba da cewa shi yasa kirkina dubu wannan dalilin ya gogeshi na dawo mara mutunci a idonta , to kici gaba da kiran hauka zamu haɗu anjima , shiru nayi ban sake magana ba har muka iso G R A , haka na taho ba abinda na ɗauko daga gidan Inna , kuma bansa yadda sukayi ita da Dikko ba amma tabbas nasan zai faɗamin yadda sukayi da ita har yaje ya taho dani , da yadda ya kasance bayan na kulleshi na gudu , da yadda suka ƙare da Yazeed da Aunty Suwaiba Al ' Ameen da kuma labarin Mardiyya. Saida Parpy yayi bacci Dikko yasa Ashiru ya maidashi , kuma yau da ya bani maganinshi ban ma yadda nasha ba dan abinda na fahimta ta cikin maganin nan yake haukatamin lissafi , yayi lallashi nace bafa zansha ba , haba An matana dan Allah kisha , Allah bazan sha ba , kar Allah yasa kisha "yar rainin hankali , oho maka dai...... A ranar wasan ba magani akayi shi , kuma ran Dikko ya ɓaci , tunda naƙishan maganin banzarshi , har gari ya waye bai min magana ba sai fushi yakeyi , daya tashi fita ma nayi masa a dawo lafiya bai ansa ba , daya dawo ma sannu da zuwa na ma bai karɓa ba. Haka dai mukaci gaba da dafa rayuwar , Momy tayi ruwan wulaƙanci da taji labarin na dawo kuma tazo ta zabgaga rashin mutuncin ta iya ƙarfinta , kuma Dikko yaji babu daɗi sosai ya bani haƙuri kuma nayi , Dady kuwa Dikko ya zauna ya warware masa komai kuma Dady yayi ma Momy faɗa yace bataji dai daɗin halinta ba , ɗiyar ɗanta da girmanta ta zauna tana mata ƙarya bata kyauta ba , kuma ya ƙara maimaita mata batayi hali mai kyau ba data raba uwa da ɗanta ta guji ranar da sakayya ta waiwayota , shi dama bai wani ɗauki zafi da Sultana ba Momy ce takaishi ta baroshi kuma yanzu ya gane gaskiya dan haka ya dawo daga rakiyarta. Gaba ɗaya Dikko ya tsameni daga sabgar "yan uwanshi , biki suna jaje ko mutuwa bana zuwa , yace tunda basa so na kawai inyi rayuwata na manta da sabgar duk wanda baya sabga na , hankalina kwance banda wata damuwa dan Dikko ya hana duk wannan gayyar "yan gidansu zuwa gidanshi , kuma makaranta ɗaya muke da sauran ƙannenshi amma ba wanda suke ɗaki ɗaya ba , ban koma SS a tsohuwar makarantar da Inna ta kaini ba , Ashiru ke kaini yana ɗaukoni , idan kuma Dikko yana gari shine yake kaini yana dawo dani , Muna cikin haka ne babbar ɗiyar Rabiya ta kwanta ta mutu , kuma banje gaisuwa ba , mutuwar ta tashi rankatakaf hankalin ahalinsu Dikko , saboda babu wata jinya da tayi lafiyarta lumi tana cin abinci maka'ikan mutuwa ya zare ranta , koda akaje asibiti likitoci sunce tuni ta mutu saima a wurin wankan gawa aka kwakwale sauran abincin daya maƙale a bakinta. Rashin shigata cikinsu yana musu ciwo Dikko kuwa ya zuƙeni daga cikinsu kwata² , tou rashin zuwa gaisuwar ne ya ƙara basu mamaki , abin ya damesu , koda Momy tace ma Dikko meya hana matar ka zuwa gidan gaisuwa ? Cewa yayi shine ya hanani , dalili Momy ta tambaya......... Kuyi haƙuri wallahi wayar lumshewa takeyi bata doguwar tafiya yau dasai na ƙarƙare labarin nan amma ku bari mu ƙara ko feji biyu ne , 18/12/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 89 *_YAHANASU YUSUF A Y RAƊƊA , {{ Mrs TANIMU MUSA QERAU }} yau gaisuwar taki ce ke ɗaya matar Yayana , ina miƙo saƙon dubun gaisuwa ta zuwa gareki tare da addu'ar fatan alkairi , kiyi farin ciki , cikin farin ciki kuma kyakkyawa..._* Shiru Dikko yayi ya gagara cewa ummm ummm idonshi yana kallon ƙasa ya kwantar da gefen kanshi a gefen kujera kusa da inda Momy take zaune , ita tana sama kenan shi yana zaune a ƙasa , cikin sigar lallashi tace Dikko mace ta fini mutunci a idon ka ko ? Yanzun ma shiru yayi babu amsa , idona biyu ban mutu ba kenan , idan kuma na mutu ka gama da "yan uwanka har abadan duniya haka kayimin adalci kenan ? Yanzun ma a ɗauke yake baiyi magana ba , me yasa daga kai har matarka bakuje wurin zaman ta'aziyya ba...... ??? Ba tare daya ɗago ba yace ai ni naje , sau ɗaya tak kaje fa , ko kana tunanin ban sani ba ko bana ganewa iye..... ? Duk yaran gidan nan tunda akayi rasuwar nan suna gidan Rabiya suna tayata jimamin rashin ɗiyarta , duk wacce ke aure kuma mazansu duk dasu ake zaman ta'aziyya , sai kai zaka kawomin wata sabuwar aƙida a cikin zuri'ata ka warwaremin zaman lafiya ka jefa ƙiyayya a cikin kai da kuma "yan uwanka ? In banda kake ɗan iska yarinyarta ta kwanta ta mutu ba ciwon kai bare na jiki , kuma ba yarinya ba budurwa Dikko kace kaine ka hana matarka zuwa gidan ta'aziyya kuna cikin "yan uban suna nan suna kallonku kuma suna karantarku idan har kuka kuskusara suka ga wata ɓaraka ta fita a cikinku sai sun hanaku zaman lafiya , Zaiyi magana ta daka mishi tsawa tace rufemin baki mara kunya , baka san dama ƙufule nake dakai ba ? Ni bana san "yar iskar yarinyar nan bana santa ׳ ko zan mutu bazan so yarinyar nan ba , ƙaton banza ƙaramar yarinya ta maida kai susutancen namiji , har nawa take da zata juyaka sakaran banza marar tunani , tou ita ɗin da kake gani kana iya rabuwa damu saboda ita muɗin dai daka ɗauka ba'a bakin komai ba mune na gaskiyar , ita kana iya rabuwa da ita kuma wata zaka auro , mace ana canja ita amma ni da "yan uwanka baka iya canja mu har abadan duniya , ka saki gaibu ka kama zahiri idan ba haka ba sai kayi dana sani wata rana , da sauri ya ɗago ya kalli Momy cikin damuwa yace kar kiyi min baki Momy , ba baki nayi maka ba , gaskiya na faɗa maka , bani na faɗa ba kaima ka sani kuma kowa ya sani , karuwa har amana ne da ita ? Karuwa bata zaman aure , sai ka gama gina rayuwarta zata zazzage ka tayi gaba abunta , badai yarinya ka auro ba ? Yarinyar ma karuwa , karuwar ma da bata fito daga tsatson mutunci ba ko ? Hmm addu'a ɗaya ma zakayi karta kashe ka , dan wannan yarinya daga ganin idonta babu Allah a lamarinta kana can ana barbaɗa maka kana tanɗewa , Allah kaɗai yasan iya ƙazantar da take baka kake ci a abinci , layu kuma baka san ta ina kake takasu ba , ka kwanta akansu ka tashi akansu gaba ɗaya ta ɗimauta ka , ka dawo wani sakarai , banajin daɗin ganin wannan ranar Dikko ka cuci rayuwata daka auri karuwa , ka rusa gidanka ka rusa rayuwarka da bayanka , dama mutuwa nayi banga zuwan wannan ranar ba , ta ƙarasa maganar kamar zatayi kuka. Parpy dake tsaye bayan Momy saman kujera yana wasa da makullin motar Dikko yace , Culcana , shi Dikko ba wai duka yaren Papi yake ganewa ba dan hausarshi bata fita yana tsamin baki , Momy taci gaba da cewa , ina gudar maka irin abinda ya faru da mijin Safiya Ya'u ne , haka mijinta yaje ya auro karuwa , Papi ya juyo ya anshi labarin yana zaro ido cikin tsoro cine Culcana ta yankaci , ya ƙarasa maganar duk idonshi a waje yana nuna yankawa da hannunshi dai² wuyanshi , maimakon Momy tayi ma Papi faɗa tunda ita tana gane abinda yake cewa sai tace Ey mana haka zata yanke Yaya ya mutu shima , dariya Papi yayi yana kallon Dikko , ita kuma taci gaba da cewa hankalinta da natsuwarta bazata zauna lafiya ba harsai taga ya saki yarinyar nan , zata natsu. Jiddah ce ta shigo palon da sallama gaba ɗaya palon ya disashe duk wani ƙamshin turare da wani turaren wuta gaba ɗaya turarenta ne kaɗai ke tasiri , tafa wanku yadda hankali baya iya hasasowa dan Jiddah "yar gayu ce sosai , murmushi tayi tare da taɓo Perpy tana cewa dan Yaya yazo baza kamin Oyoyo ba ? Da sauri yayi baya yana goge inda ta taɓa mishi fuska , Momy ji abinda Perpy yakemin , Momy tace ai kun saba , Perpy kuma cewa yayi kuma baciyi cau ba , Jiddah tace kam lallai ma yaron nan aiko na haɗu kuma nayi kyau ka tambayi Yaya kaji , daga bayan Momy ya leƙo Dikko yace Yaya aije batayi cau ba , shiru Dikko yayi bai kalli Perpy ba kuma bai ɗago daga yadda yayi zamanshin tun farko ba , a yangance Jiddah tace Yaya barka da yini , yawwa ya faɗa tare da fiddo wayarshi daga aljihu yace Momy zan tafi , da sauri Papi ya sauko yayi gaba kar Dikko ya tafi ya barshi , Jiddah kuma ciki ta wuce tana wata irin tafiya mai ɗaukar hankali , da wutsiyar ido Dikko yabi bayanta da kallo , a ranshi yace hmm mata kenan.......... Momy kuwa taci gaba da cewa , ashe karuwar nan badan Allah ta auri mijin Safiya ba kuɗi aka bata akan ta kaso shi , shi yasa gabana yake faɗuwa kar haka ta kasance dakai , shima kamar kaine dai , da iyayenshi sun hanashi aurenta amma yayi kunnen uwar shegu dasu yaje ya aurota , ashe bai sani ba ajalinshi ya ɗauko , daya aureta dangi suka taso ta gaba saiya tsameta daga cikinsu dama tunda taje gidan bata ma wani yadda tayi ciki ba tunda tasan aiki ne ya kaita , Dikko ni nake faɗa maka wannan labarin dare tabi ta yankeshi ya mutu har lahira , da wuƙa nake faɗa maka , Allah ya jiƙanshi , saida Momy ta ƙara zage Dikko sosai tana farfaɗa mishi manyan illoli game da auren karuwa da kuma haɗarinta , sannan tace ya tashi ya bata wuri sakaran banza da mace ta gama dashi , Jiki a sanyaye tattare da damuwa Dikko ya fito daga palon , makullinshi ya ansa a hannun Papi ya faffalla mishi mari yace ya wuce ya bashi wuri idan ya sake biyoshi saiya ci ubanshi , riƙe Dikko yayi ya fashe da wani irin kuka mai tada hankali , danshi Dikko idan dai ranshi ya ɓaci tou saiya rarrabashi kowa ya samu , cikin hayaniya yace sakeni yayi maganar yana zazzaro mishi ido , kallon Dikko yakeyi kuma bai daina kukan ba yaƙi sakinshi , jin ihun Papi ne yasa Momy fitowa tace me yayi maka ne ? Ni babu inda zanje dashi , Momy tace sai kaje dashi , cikin ɓacin rai yace haka zan ɗauki yaro inta yawo dashi a gari kamar wani sakarai , ai sakaranne , shima ya san kai sakarai ne shi yasa yake ganin ka kamar wani abokinshi. Ni gaskiya babu inda zanje dashi , Momy tace wallahi sai ka tafi dashi , Papi kallon Momy yayi yana shashshekar kuka bai saki Dikko ba , Momy tace sai yaje dakai daina kuka kaji ko.....? Har yanzu ita yake kallo sai kuma ya kalli Dikko bayan wani lokaci , Dikko baiyi magana ba ya buɗe mota ya shigar dashi suka tafi.... Momy kuwa palo ta koma cike da ɓacin rai , irin wannan ranar ce take gudun zuwanta kuma gata nan tazo , wannan dalilin yasa taso Yaya tayi haƙuri karta kashe auren Jiddah , gashi tun ba'ayi nisa ba Dikko ya hana kowa zuwa mishi gida , ya tsame matarshi tsam daga cikinsu bare in tazo su riƙa muzanta mata , gaba ɗaya Dikko ya canja hali kuma ya rage masifa ya zama wani ruwan sanyi saboda mace , ita dai Allah ya sani bata san Sultana kuma idan dai tana rayuwa saita raba Dikko da yarinyar nan , dan ta faɗawa wata ƙawarta abinda yake faruwa kuma tana nema ma Dikko auren "yarta amma tace matarshi ta katantane ko ina ta hana wata shiga , ɗiyar Yayarta ma da yake aure itace tayi mata asiri ta tashi hankali saida dai akayi saki Jiddah ta samu natsuwa , kuma saki 3 ne babu damar a koma , ita bata iya wannan ɓatar ba ta neman asiri amma idan zata iya ta fitsare ƙafafuwanta ta fitar da Sultana ita kuma zata sa Dikko ya auri ɗiyarta. Da ɓacin rai ya dawo gidan , tunda naga yanayinshi banma shiga sabgar shi ba daga sannu da zuwa ban sake mishi magana ba , kuma bai ansa ba , tunda ya shiga ɗaki bai sake fitowa ba , da Papi yayi bacci text ya turomin inje in ɗaukoshi daga ɗakinshi , ko da naje ɗaukarshi faɗa yayi tamin wanda shi kanshi baisan dalilin faɗan ba , waishi yafi ƙarfin mace ta raina shi , haka kuma babu wata banzar macen da zata iya juyashi ko wacece ita , nidai ban masa magana ba na ɗauki Papi zan fita yace idan naje na kaishi inzo , a ɗan tsorace nace ina zan kaishi ne ? Saman kaina zaki kaishi , Allah ya baka haƙuri , na ɗauka zan kaishi wurin Ashiru ne ya maidashi , duk yadda kike so haka zakiyi , yadda dai kake so Dikko , to da kinsan wurin Ashirun zaki kaishi zaki tsaya kina tambayata saboda raini......? Tou ki sani jiya ba yau bane ba idan kuma kika ce zaki min yarinta yanzu zakiga yadda zan ruɗa miki rayuwa. Ajiye mishi ɗanshi nayi zan fita , An mata zo nan , yi nayi kamar banajin shi , wallahi idan kika fita saina zaneki , zo nace , tsayawa nayi ban dawo ba , karki bari na sake miki magana , ɗaure fuska nayi na koma wurin shi , cikin ɓacin rai yace ke har kin isa ni zaki ma baƙin rai ? Wace ce ke ? Ɗaukarshi , ban sake magana ba na ɗauke shi na fita , Ina kaishi na dawo , ci gaba yayi da faɗa yana rufe idanuwanshi cikin rashin mutunci , waishi ya gaji da cin zarafin da ake masa akaina , ko aure kanshi farau saidai insan inda zanje danshi ya gaji , da wane rayuwa zaiji da Allah , gani nima mara kunya na raina shi harna faɗa masa , tou ya gaji wallahi saidai in tafi gidanmu , ƙyarma jikina ya farayi gaban ya faɗi , a raina nace na shiga3 Inna ta koreni kaima ka koreni ? Abinda Inna tace tunda na zaɓi Dikko ko zai kasheni karna zo mata gida ta yafe mishi ni duniya da lahaira , cikin rawar murya nace Dikko me kuma nayi maka yanzu....... ? Ba abinda ya dameni ki barmin gidana ni na gaji bana iyawa , kayi haƙuri idan nayi maka wani abu insha Allah bazan sake ba , cikin ɓacin rai ya juyo tare da nunani yace ke............ Ki barmin gida nace , Fashewa nayi da kuka nace kayi haƙuri don Allah , bazanyi ba.......... Sai kin tafi daga gidan nan , yau akanki zagi nawa Momy tayi min ? Tacemin sakarai har take cemin Perpy ma yasan ni sakarai ne , ance kin shanyeni tou yau sai kin barmin gidana dan kowa yasan ni ba shanyeyyen namiji bane ba , ya ƙarasa maganar yana ciro bero daga gaban aljihun rigarshi.... Cikin kuka nace haba Dikko me kakeyi haka don Allah ? Ke ni ba mahaukaci bane ba nasan abinda nakeyi ya nuna saman ƙoƙon kanshi , ita Mamar taki kinsan me tacemin akanki ? Ta muzantani ta tozartani me nayi mata ne ? Kayi haƙuri Dikko , naƙi inyi haƙuri tunda kika shigo rayuwata farin ciki yayi bankwana da zuciyata , matsalar yau daban ta gobe daban in fita waje a ɓatamin rai in dawo gida dan na samu natsuwa kimin rashin kunya , ba tattalin miji kwata² baki san darajata ba , kina ƙasa na amma kina nuna ke wata isashshiya ce , wace ce ke ? Wanda kinsan ko a gado nine a samanki duk ta inda aka juya , na bari , hararata yayi cikin fushi yaci gaba da cewa , wane fi'ili zakimin duk wani feleƙenki a tafin hannu a yake , me ma kika iya ? Me kika sani akan namijin....... ? Shiru nayi ina kallon ƙasa , yaci gaba , kullum ɗaurin zanin ki iri ɗaya ne , tafiyar ma tun wacce na sani , kullum kina nan dunkume ba ranar da zaki buɗe idonki kisan wace irin rayuwa akeyi , babu ilimin zama da miji sai rashin kunya shi kaɗai kika iya mutum ya taɓaki ki ɓare baki kiyi ta wani kukan munafinci , { idan yana kwanciya dani } me kika nema kika rasa ne ? Ni wallahi bana san kidahumar mace , bana san jakar mace bana san ƙazamar mace , idan na faɗa miki yadda nake so kiyi rayuwa dani sai kicemin ina miki cin fuska , me Jiddah tafi ki ne ? Babu abinda takai ki a cikin mata dubu baki kasuwa ba'a fini mata ba amma an fiki sanin zamani , cikin ɓacin rai nace niba kidahuma bace ba , kuma kai kanka kasan ni ba ƙazamiya bace ba , dan kaga ina baka haƙuri kake ganin kamar inajin tsoron rabuwa dakai ne ? Banda ilimin zaman mijin kuma bazan koya ba , idan ka rabani da kanka zan mutu ne ? Ai saika rubutu abinda zaka rubuta ga biron nan a hannunka , ni ba abinda zan rubuta da biro ajiyeta zanyi saidai in zaneki kikaimin rashin kunya , murus zan kasheki babu wanda yaji babu wanda ya gani , amma yau sai kin tafi gidanku na faɗa miki , bazan tafi gidanmun ba , wallahi babu inda zanje , cire kayanshi yayi ya nufi toilet yana cewa shi yasa duk namijin da yasan abinda yakeyi wallahi bai auren yarinya , kullum kaida mace faɗa cikin gida , ai kasan inda ake auro manyan mata kaje ka auro mana , shigewa yayi bai sake magana ba , ni kuma naci gaba , banyi shiru ba har yayi wanka ya fito. Yana fitowa yaci gaba , ina ma amfanin mace ba soyayya , kije cikin matan gidanmu su koya miki yadda ake tattalin miji , ki koyo yadda ake rainon miji , a koya miki kissa su koya miki wanka da saka sutura tunda ni kin raina ni , Nabeela zata koya miki yadda ake tafiya a gaban miji je kiga yadda suka wayar da Jiddah suka buɗe mata ido baki ajiye komai ba sai girman kai , da raina miji , kin ɗauki miji kamar wani sa'arki ina magana kina ɗaga min murya sama sai kace kece kike aure na. A daren yau saida ya tabbatar ya ɓatamin rai harsai da nayi kuka ya jagulamin lissafi tas , sannan yayi shirinshi yana gama shiryawa ya wurgamin kuɗi a saman gado shi ya tafi Abuja kuma kar in sake zuwa makaranta saiya dawo , binshi nayi ina kuka , kila tausayi na bashi ya tsaya ya rungumeni yace An mata bakijin magana wallahi , cikin kuka nace Dikko dan Allah na bari , na faɗa ina kallon idonshi , riƙeni yayi sosai a jikinshi , a hankali ya duƙo saitin fuskata cikin magana mai saukar da kasala yace yi shiru , ya ƙarasa maganar yana tsareni da kyawawan idanuwanshi , rufe bakina nayi ina kallonshi , buɗe bakinshi yayi , yayi wani iri da harshenshi kaɗan yana wasa dashi sannan ya kirani da harshen nashi , Saida na sauke ajiyar zuciya cikin shashshekar kuka na riƙe jikinshi tare da shiga bakinshi da nawa , kullum idan zaimin wani abu yakan canja min sabon salo ne , nayau daban , na gobe ma zaizo da baƙon salo , ya ɗauki wasu "yan ƙalilan mintuna sannan ya sakeni daga jikinshi , ƙara riƙeshi nayi ina kuka nace dan Allah karka tafi , ba tare daya kalleni ba yace ki bari sai kin iyo riƙe namiji a gida sai ki riƙeni in zauna , inaji ina gani yayi tafiyarshi.... Ɗakinshi na koma na faɗa saman gado ina kuka , nidai Allah ya sani banda wannan idon tsakiyar kai irin na gogaggin mata , ko a can baya dana riƙa iskancin nan ba'a hayaccina nayi ba , ina naje ina aka sanni ne ? Wa na gani waya ganni ? Ban taɓa haura Katsina ba daga Daura sai Katsina iyakata nan , kenan tunda akayi min sauka aka sauke duk wani sheɗanci dake saman kaina , tou me Jiddah tayi wanda yasa Dikko yake faɗamin ita a magana harso 2 ? Duk yadda akayi kila yaga Jiddah ta burgeshi ne , shidai Dikko yana san gogaggiyar mace , mai tafiya da zamani , wacce ta waye sosai idonta ya buɗe da duniyanci amma a gidan aure , ƙwanƙwasashshiyar mace a fagen tarairayar miji , "yar duniya da tasan logon maza , wacce ta shahara ta kuma ƙware a wurin iya wasan danbe , Tou ba Dikko kaɗai ba duk mazan zamani mata haka suke , gadai Jiddah an saketa amma tunda tasan yadda yake san mace ta kasance ta kasa sanya , kullum a riƙe take , irin su Jiddah ne matan da idan namiji ya sakesu zasu kashe shi da bariki shi kuma yaci gaba da zagayawa kina gida kwance kamar asara ana can ana hidimar duniya babu ke , yanzu zamanin nan duk inda kika nufa mazan sun zama iri ɗaya ko wane baya san afi matarshi kuma basasan baƙauya ko ƙazamiya , wallahi duk kyanki duk tsarinki duk iya haɗuwarki duk irin sigarki da nagarta da kike da , idan dai baki da gayu baki da wayewa baki iya girki ba tsafta da ilimin zaman aure ke hoto ce , hoton ma elajiment da zaran an liƙaki a bango an gama dake , tou haka macen da bata san damarta ba take wurin mazan zamani , baki da wani amfani saidai ki share gida kici abinci , idan kuma kikayi sa'a da ɗan duniyan namiji kina nan sake da baki kina ta rashin wayanki yana can shi kuma yana miƙa kuɗinshi ana sashi a ɗaki , duk hidimar da miji yake miki zata ragu tunda masu ci sun ƙaru , gaki ke matar gida ga matan bariki , yake "yar uwata me akafi ? Wane duhun kai kika tsaya ? Tou rayuwa ta canja , zamani ya juya keda mijinki kina ji kina kallo makwaɗaitan matan bariki zasu ɓanɓare miki miji ta ƙarfi da yaji , Dan wallahi wasu mazan basu iya ba koya musu akeyi , wasu kuma dama can jarabar a jininsu take , wasu abokai ne suke kaisu su barosu , wasu kuma matan nasu ne da kansu suke yanka musu tikitin shiga bariki, idan kikayi masa magana ya daina kwanciya dake in kinci sa'a ya faɗa miki illolinki idan kina da rabo saiki gyara , idan kuma kin samu namiji mai zafi ya buɗe miki ita tsaye yace ake ƙazamiya ce ba wanka ba gayu ba shafa turare haka zai dosoki kina ƙarnin hayaƙi ko zufa ko zarni fitsarin yara , ke kuma sai kiji haushi an faɗa miki gaskiya ki masa rashin kunya , idan akaci sa'a da irinsu Dikko su zaneki a barki da kunburaren jiki , ke kuma fuuu kinyi yaji daga nan matsala ta samu hanyar shigowa , mata mace ƙwalisa ce ita , fulawa ce bata rayuwa saida gyara , zamanin ga ya lalace idan kuma kika kwanta tou fa lallai kinji a salansa , bawai ina nufin ki tashi ki nemi asiri ba , a , a ki tashi ki gyara domin zamanin yazo da sabon salo. Tunda Dikko suka ibi hanya saidai yayi tsoki , Sultana fa ga mace har mace komai yaji , ga kyau , ga siga , nagartacciyar mace gata tayi dai ko ta ina baka isa ka kusheta ba inba hassada ba , ga ƙugu An mata , ƙaramar yarinya da ita amma Allah yayi mata zubin bodi irin na manya mata , saidai ɗanyen kai ya hanata ta fuskanci damuwarshi , wace ce Jiddah ? Wace ce ita idan An mata tana nan ? Gaskiya An mata kyakkyawa ce , mace ce ta tsara , fitacciyar mace mai kyakkyawar halitta , bakinta mai kyau , tana da tsarin haƙora masu burgewa kuma tsaftatacci , tayi sosai gaskiya saidai matsalarta yarinta , zuciyarshi ce ta bashi haƙuri cewa shekarun Jiddah da Sultana ba ɗaya ba , inda Jiddah taje Sultana bata je ba , ƙawayen da Jiddah keda su ba irinsu An mata take da , ba wani , yaran ƙauye ai basu kai An mata ba ake musu aure kuma lumi suka riƙe miji babu mai ji , saishi ko kwanciya zaiyi da ita saida "yan dabaru , zuciyarshi dai haƙuri take ta bashi akan cewa idan Sultana ta goge wallahi shi kanshi saiya zama swry ya kwantar da hankalinshi da sannu za,azo wurin...... Wayarshi ya ɗauka tare da tura mata text , taje makaranta , sai kuma adireshin { address } in gidan Rabiya taje mata ta'aziyya , sai izinin hawa mota da inda zata ɗauki makullin saboda Ashiru bashi nan , hada lambar { number } Momy ta kirata tayi mata gaisuwa , kuma daga makaranta gidan Rabiya karta je ko ina...... Saida safe naga saƙon Dikko bayan nayi sallah asubahi zan koma bacci na gani dana ɗauki wayar , ban ce masa na gani ba kuma ban kirashi ba nima na basar da lamarinshi , da ya tafi saida yayi wata ɗaya da sati biyu kuma har yaje ya dawo banyi waya dashi ba , koya kirani ma bana ɗauka kuma banje gaisuwar ba , kuma kuɗinshi a inda ya wurgasu a gado ban taɓasu ba banma ko kalli inda suke ba , yadda yabar ɗakin haka ya dawo ya sameshi , ya cancara ruwan rashin mutunci a daren nan saida yasa ni na gyara ɗakin na goge ko ina da ina yace kuma tunda banda wayau kar in sake zuwa mishi ɗaki , ni kuma abinda ya ɓatamin rai dashi da yace wai me Jiddah tafi ni ne ? Ashe ma kallonta yakeyi , sai kuma abun ci baya waini zanje Nabeela ta koyamin yadda ake tafiya a gaban miji , inje inga yadda suka wayar da Jiddah suka buɗe mata ido , wato ni ban iya komai ba ? Shine abinda ya ƙonamin rai nake zuciya tunda ya tafi har ya dawo kuma ban huce ba. Fita nayi daga ɗakin ya biyoni yana cewa ko zaki mutu saina faɗa miki gaskiya duk duniya baki da wanda ya isa ya faɗa miki iskan nan mai kaɗawa saini , ko yayi miki daɗi ko yai miki zafi saina faɗa , ke ni har zaki nunamin fushi ? In banda iskanci ni zaki barma ɗaki har inje in dawo yadda na barshi haka zanzo in sameshi , nace kije ma Rabiya gaisuwa shine baki je ba kuma bazaki ba inyi duk abinda zanyi , zama nayi a gefen gadona nidai na rasa abinda yakemin daɗin duk an jagulamin lissafi , wayata na ɗauka ya fizge wayar ya bugata a bango duk ta tarwatse yace ina miki magana zaki latsa waya , nace kije ki koyo zamantakewar aure idan kinji fushi ki koyo saiki zauna lafiya. Ke in kina da hankali ma har ni zakiyi gaba dani ? Nine nake aurenki ko kece ? Ni zan kiraki a waya ke a dole kinyi fushi , tou ƙarya na faɗa ne ? Ba komai cikin wannan sakaran kan sai wauta da yarinta , idan kinga dama ki shirya zamu fita , yana faɗin haka ya fita abunshi. Goge hawaye nayi cikin ɓacin rai , duk duniya babu wanda ya cuceni sai Inna , ko waya na kirata ta daina ɗauka , gata a raye Dikko yake iƙirari shine kaɗai zai faɗamin gaskiya , tabbas shine zai faɗamin , zanji fushin na iya zamantakewar zama dashi dan mu zauna lafiyar..... Ya daɗe sosai sannan ya dawo ɗakina , yasha gayu cikin sigarsu ta "yan gayu , nima nayi wanka na shirya amma daya shigo saida ya gyaramin diresin , yana cewa saura in munje ki saki baki kita surutu ko yawan murmushi , daga ina yini Allah ya jiƙanta kika sake ko kallon wani muka dawo zan kulleki a ɗaki. Shine a gaba ni nake bayanshi bayan ya gyaramin tafiyata muka fita , 9:32pm a palon Rabiya tayi mana , kafin ta fito saida tasa aka fara tara mana "yan abubuwan taɓawa , Dikko ya nunamin ko ruwa nasha muka koma gida saiya ɓatamin rai , yana tsaye wurin ganin ya siyomin mutunci amma ni bahaguwar kwanya gareni , Bayan wani lokaci ta dosa , ƙarar takalminta kakeji a saman tayils ƙwas׳ , ƙamshi yayo gaba ta bayyana a palon sai isa takeyi mijinta na biye da ita , saman kujera mai zaman mutu 3 { 3sieter } suka zauna , mu kuma muna saman 2sieter , gaisawa aka farayi nima na gaisheta tare dayi mata ta'aziyya , ta amsa dai cikin sakin fuska , daga haka ban sake magana ba , sukaci gaba da firarsu , bamu wani daɗe ba muka tafi , kuma Rabiya tace ko ruwa musha Dikko yace an gode , tace tana zuwa kila wani abu zata bayar yace ai zamu dawo , A mota ne yake cewa kaje wuri ana marmarinka ka tafi kafin ka fita ran mutane , kin gani dai ko ? Dare ne muka je amma kallarta shirye , tsakanin palo da bedroom sai an saka takalmi masu kyau , kana doso miji yasan ka taho , amma ke duk babu wannan takalmin ma "yan maraɗi kike yawo dasu babu wani notice saidai kawai mutum ya ganki , har muka isa gidan gwamnati Dikko faɗa yakemin , kuma saura idan munje canma inyi surutu ko inci wani abu Jiddah tana nan idan ta barbaɗeni ba abinda ya dameshi , Daga gidan Rabiya har gidansu babu abinda na kalla kar yacemin na cika ƙauyanci , a kame nake dan nima ba sakara bace ba , amma a raina inajin daɗi , tunda Dikko yayi parking su Nabeela suka yo waje har Papi shima baiyi bacci , duk sannu sukayi mana , Papi kuma ya tafi wurin Dikko yana oyoyo , hannunshi ya kama sukayi gaba Papi yana bashi labari shidai baya gane yarenshi. Wata irin mummunar faɗuwar gaba naji lokacin da idona ya sauka akan Momy , kai uwar Dikko "yar gayu ce , ta haɗu ׳ , Allah yayi mata kyau sai kuma ya haɗu da hutu uwa uba kuma gayu , kamar yadda Dikko yayi nima a ƙasa na zauna jiki a sanyaye sai mulki Momy ke zubawa , kai Momy tayi wallahi ta haɗu "yar gaye ce first class kuma ko a ajin ma itace ta gaban benci , bayan sun gama gaisawa da Dikko nima na gaisheta , saida ta mula tasha iska bayan ta gama kalleni tas sannan tace lafiya qalau , ƙannenshi suka shigo wanda muke karatu dasu makaranta ɗaya , wai me yasa kwana biyu banje sch ba ? Saida na kalli Dikko sannan nace musu ba komai , su jina suke kamar wata ƙawarsu dan haka sukace inzo muje ɗakinsu suma , Momy tace bazata je ku koya mata kilbibi ba , Dikko yace Momy ki barta suje , kasan yaran gidan nan munafukai ne basu aje komai ba sai kilbibi da gulma idan suka ɓata maka mata da tsigudidi ka huta , Nabeela tace matar Yaya zo kiji , ta leƙo daga ciki tana kirana , kallon Dikko nayi , da girarshi ya nunamin inje wurin Nabeela , tare da sauran masu cewa naje ɗakinsu duk muka runguɗa ciki , muna shiga suka ciremin kallabi suna ganin gashina , Nabeela ta ɗauko abin taje kai ta fara tsigarmin kai , wai ince ma Yaya zan kwana , nidai banyi magana ba , sune sukayi ta surutu nima ina so ince wani abu amma Dikko ya hanani magana dole nayi shiru , Jiddah kuwa yanzu ta shigo ta fara masifa wai anzo ana ciccira musu datti a gado , ganin babu wanda yabi ta kanta ta koma palo ta faɗawa Momy amma sai Momy tace idan mun gama an gyara , Nan Dikko ya barni yace zaije ya dawo , Momy ma ciki ta dawo bayan fitar Dikko , kuma bata wani ji ƙanƙamina ba , ganin Dikko ya tafi yasa ta kora duk wanda ba itace ta haifesu ba , tana satar kallona lokaci² irin kallon nan na gefen ido , itace ma tayi ma Nabeela faɗa ta rufemin kaina saboda dare , shine Nabeelar tace muje ɗakinta , Momy tace bazanje ba , Har 11:46pm Dikko bai dawo ba , ni kuma na gaji ni bana san irin kallon da Momy kemin kila kuma karatu na takeyi , kallon Nabeela nayi tare da riƙe hannunta nace nidai muje ɗakinki , Momy tace muyi zamanmu , sai kuma take tambayata bayan gidan Rabiya sai ina Dikko ya kaini , nace sai nan , zai kaini gidan Yayarshi wacce yake bi itama inje in mata ta'aziyya nace to , wai kuma duk abinda akayi in riƙa zuwa idan ba haka ba babu wanda zai sanni nace tou , Sai 1 saura Dikko ya dawo kuma Nabeela tace masa in kwana yace a , a , itace ta anshi Papi ni kuma muka wuce gida , tun daga wannan ranar ina zuwa gidansu Dikko amma tare dashi , idan kuma anyi wani abu biki ko suna Nabeela take zuwa ta tafi dani ko Dikko baya gari , basa dai min wani gani² ko habaici , amma Jiddah idan muka haɗu sai tacemin ga irin asiri wai na mallake dangi miji , bana tanka mata tunda dai Dikko ya gargaɗeni da baya san inje in zama ɗaya dasu na riƙa kama kaina banda yawan surutu banda yawan dariya , ba ruwana da sabgar kowa , kuma kar in kuskura na riƙa shiga sabgar Jiddah. Shigata cikin familynsu Dikko yasa na gane banbanci tsakanin "yan geto area da boti sayit , na gane matsayin wanka kuma na gane shima kanshi wankan iri² ne , na gane matsayin gayu kuma nasan nawa gayun an daina yayin irinshi , na zubar da gayun rayuwar baya dan na ɗauki sabon darasin wanka a wurin wayayyin mata , lokaci guda kaina ya fara hayaƙi nima na fara fizge² , idona ya fara wayewa , akwai banbanci tsakanin wayewar talauci arziƙi da kuma rayuwar lingu , ko a karuwanci ashe iri² ne nawa da nayi a baya wahalallen karuwanci ne , Nabeela tana taimako na tana shiga dani wuraren da tunda nake ma bansan akwai su a cikin garin Katsina ba sai su masu kuɗi , kai talaka ya rayuwar haƙuri ? Talaka bawa alere dangin jakki ka mutu gobe a sake sabo , da nasan zanzo irin wannan rayuwa da ban ɓatawa kaina lokaci ba wurin shirmen da nayi a baya , wanda bai haifa min komai ba sai ɓacin suna , karuwancin wahala ya bugamin tambari mara goguwa , kai kuɗi na inda suke gayu wayewa da buɗewar ido na gidan gwamnati , idan taƙamarki wanka sai kin gama wankuwa har kin gaji , idan kika tunkari ahalin Dikko sai kin raina kanki , Nidai ban sani ba , shin Dikko yayi magana da "yan gidansu dan su ɗago rayuwata ko kuwa sune suka ga ya kamata su wayar dani oho musu , nidai dama can gaskiya bawai wata kidahuma bace ba saidai kunsan wayewar kuɗi da talauci ba iri ɗaya bane ba , kawai dai ciwona rashin ganewa a boko shine ciwo na tou yanzu ina ganewa kuma na iya , rabon da muyi faɗa da Dikko harna manta , shidai burinshi ya samu natsuwa cikin kulawa da soyayya kuma kullum nazo masa da baƙon salo , na jiya ba irin na yau ba , na yanzu daban na anjima ma yazo a baƙo , kuma karna gajiya da sauri shine dalilin yasa yake bani magunguna dan na ɗauki buƙatarshi har ya samu gamsuwa ba tare dana gaji ba , na zama jajirtacciya mai juriya a fagen tsakiyar filin wasan danbe , sai kuma biyayya shi mutum ne mai san ka bashi girma , yana san girma sosai kuma yana so ka girmamashi , saboda san girmanshi yasa Rabiya ke zaulayarshi cewa saida tayi aure ma yazo duniya , kuma shi mutum ne mai san godiya , yana san godiya akan duk abinda yayi maka , sannu da zuwa idan ya dawo cikin soyayya rakiya idan zai fita da addu'ar Allah ya dafa mishi akan duk abinda yasa gaba na alkairi , yawan damuwa da rayuwarshi ta hanyar yi masa waya idan baya nan , sai kuma idan yana gari bana zuwa ko ina sai makaranta shikenan matsalarshi. Inna kuwa har yanzu babu ruwanta dani , ko gidanta mukaje dani da Dikko haka zata watsar damu sai mun gaji da zama mu tafi , dan dama Dikko shi komai rayuwarshi na dare ne yakeyi kamar mara gaskiya , shi yasa ko gidan Innar sai dare muke zuwa. Ita dai yanzu Momy bata da sauran ja tunda tayi karatu na kuma ta fahimci rayuwata , kawai dai tayi ma Dikko addu'ar mu zauna lafiya , ɗiyar ƙawarta kuma da taso ta aurawa Dikko ashe itace karuwar bata sani ba , can wata ƙawarta ta faɗa mata yarinyar nan da take nemawa Dikko fa batajin magana har ciki aka zubar mata kwanan nan , sai ta zauna tayi karatun ta natsu tare dayi ma Dikko addu'ar su zauna lafiya da Sultana , sai kuma tayi hangen idan Sultana ta tafi bata san wace surukar zatayi ba , shine suke lallaɓa Sultana a jone , a taƙaice dai kawai ta gane idan bata share masallaci ba aradu kasuwa zata share hada mofin , Amma duk da haka nan dai yana nunamin nesa² dai , danshi yasan "yan gidansu yanzu sukeyin ka anjima su sauke ka ƙasa , Dikko dai yana tsaye kullum yana ta kwatanci yana ɗorani hanya , idan yaga na lauye nan zai ɗagoni ba faɗa ba ɗaga murya , zaice wannan da kikayi ba haka akeyi ba , haka zakiyi , zama dai nayau da gobe idan kuma yayi min wani abu nayi fushi , zaicemin ba'ayin fushi da miji kuma ko nayi miki abu ya ɓata miki rai ki riƙa haƙuri ba komai ne zakiyi fushi akanshi ba , rayuwa juyawa takeyi ba kullum akeyin farin ciki ba , kuma shima kanshi ba kullum zan sameshi yanajin haƙuri ba idan na hawoshi yana ɓacin rai ba abinda ya dameshi kawai zai zaneni ne kuma inyi masa godiya idan ya gama , wannan shine ake cema yau da gobe... Ina shiga ahalin Inna sosai , duk abinda akayi ina zuwa , idan Dikko yana nan Ashiru ke kaini , idan basa nan ni zanje da kaina , idan yana Katsina da abokinshi Abbakar suke fita ni kuma a barni da Ashiru , idan kuma zai bar gari tare suke tafiya gaba ɗayansu , masu gadi da sauran masu hidimar gida ake bari , dan yanzu Dikko baida lokacin kaini wani wuri kuma ko yana gari nima kaina wahalar gani yakemin suna can wurin siyasarsu zaɓe yazo sunƙi haƙura su fita wasu su shiga , itama Momy bata zama suna can basa nan basa can hada Jiddah ake zuwa , niko banma ga fuska ba bare ince ko so ɗaya naje naga yadda akeyi , hmmmm Dikko ? ׳ halinshi saishi. Gidan Sultan ma duk abinda akayi ina zuwa , amma ni Dikko baya bari na zama wuri , mintuna 15 shine nawa idan na fita , idan yaji dani 25 ne , makaranta kaɗai nake zuwa na daɗe , nidai bansan dalilinshi na wannan tsarin ba , ko gidan Inna idan naje shima haka ne , ni idan tana gari ina zuwa dan wallahi shi yanzu ya daina zuwa gidan kwata² , haka zamuje yaita gaisheta tanaji tana kallonmu tai mana banza , shi kuma tsakani da Allah ya bita² harya gaji idan kuma zamu tafi taita zagin Dikko tana aibatashi , shi yasa ya daina zuwa , tun kana da mutunci a idon siriki yana jin nauhinka har kazo kayi abinda zaka fita ranshi haba ina ma amfani da Allah..............? Sati biyu rabon da nasashi idona sai yau a asibiti , yazo ganin Kaka nima Ashiru ya kawoni muka haɗe , kuma shine ya iskeni , yana shigowa nasa takalmina nayi gaba ina jirashi waje , koda ya gama abinda yakeyi bansan ta ina aka ɗaukeshi ba kawai ya ɓacemin saida na ga an hau motoci babu shi , na koma ko an barshi ban ganshi ba , nima sallama nayi musu na wuce gida raina ɓace , kuma shi ba waya yakeyi ba saida ya turo text. Duk yadda na kasa na tsare a ranar ban ganshi a gida ba , washe garin ranar ma baya nan , wata washe garin sai naji shi kawai ya halba Abuja bansan abinda yajeyi ba , kwanashi biyu ya dawo , ina makaranta ya dawo kafin in dawo harya bar gidan , naji babu daɗi dan haka na zauna na zuƙa mishi zuƙeƙen text nace kana can kana yawon kamfen ka manta da yankin iyalinka , waini waye ya faɗamin shi yawon kamfen yakeyi ? To nidai koma me kakeyi ina san ganinka , gani nan zuwa......... ! 22/12/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 90 Bayan na gama dubawa ajiye wayar nayi na nufi madafar abinci dan samawa cikina abinda zan bashi , ko uniform ina ban cire ba yunwa nakeji sosai kamar zan faɗi , Dikko kuwa bai wani daɗe ba yazo , kicin ya sameni wai gashi yazo ta ina zai fara kamfen in a yankin iyalin tashi , yayi maganar yana murmushi , dariya nayi sannan nace kaima sai kawai ka kama kayi wani tafiyar ka abunka , gaba ɗaya ka wani manta dani na ƙarasa maganar ina shiga jikinshi , Dariya yayi cikin izza ya riƙe ƙuguna yace yi haƙuri An mata , naƙi inyi haƙurin , nine zahiri bakiyi ba tunda har kin faɗamin magana , wai na manta da yankin iyalina banyi kamfen ba , dariya kika bani nace tou ? 🤔 bari in rugo kar aƙi bani ƙuri'a ranar zaɓe , wannan "yar yarinya har tayi ƙorafi gaskiya Dikko bai kyauta ba. Ey mana inata jin babu daɗi na zama kamar wata marainiya dubeni da Allah duk na wani zama abin tausayi , na ƙarasa maganar a shagwaɓe ina kallon idonshi da yanayin kallon da yake so , murmushi yayi tare da lumshe idanuwanshi yace An mata......... Ya ƙarasa maganar yana sumbatar bakina. Fita nayi daga jikinshi na juya da niyar tafiya inda na ɗora girki , riƙo ƙuguna yayi ta baya yana jawoni jikinshi , ai ƙarya kikeyi bayan nazo kamfen , da Allah ka ƙyaleni yunwa nakeji , taɓe baki yayi tare da ɗaga gira yace , tou ? Ya faɗa cikin yanayin mamaki sannan yace , idan nayi tafiyata karki sake kirana kice inzo kamfen , tou ka tafi mana sai me.... ? Juyawa yayi yaɗanyi tafiya , inajin ƙarar takalmin shi , na juyo a dabarance naga shin da gaske tafiyar zaiyi , ina juyowa muka haɗa ido , dariya yayi tare da cewa yes 💪🏻 , da baki juyo ba dana tsaya amma kinga tafiyata , da za'aimin yanga a wani latsani sai Allah ya kamaki nima saina rama , yana faɗin haka ya fita daga kicin in da sauri , kashe gas in nayi na bishi nima da sauri , ɗakinshi ya wuce yana dariyar mugunta. Lokacin dana shiga harya cire agogon hannunshi , da farin ciki ya rumgumeni wai oyoyo An mata , ya faɗa yana tsuke bakinshi tare da lumshe idanuwanshi yana ɗan kaɗa kanshi cikin yanayin shauƙin so , ya riƙeni sosai a jikinshi , murmushi yayi mai sauti ya sake maimaita wai kana can kana yawon kamfen ka manta da yankin iyalinka , kai An mata , tou ya akeyin kamfen a yankin iyali ya ƙarasa maganar yana haɗa idanuwanmu wuri ɗaya kowa yana kallon kowa , bayan wani lokaci yace caf aiko lallai nan ne ya kamata inyi kamfen muje a gama abincin inci nima in ƙara tsatsubo ƙarfina. Bayan mun koma ya zauna a saman matakalar da zaka shiga kicin yana yanka albarsa , da yaji azabar yaji yace kai ban iyawa anshi harna yanke , kawo dai in miki wani abun wannan wahala ji naji ciwo yana nunamin inda ya yanke tare da goge idonshi yace wai wahala , nidai albasar zaka yankamin , ke ban iyawa kinji , nima ban iyawa saidai a dafa abincin ba albarsa , ai yama fi daɗi yi sauri ki gama. Ciki ya shiga yana wanke hannunshi wayashi ta fara ringing , ni yasa na ciro mishi ita daga aljihu , dana faɗa masa Momy ce da sauri ya anshi wayar tare dayin sallama , bansan abinda Momy tace masa ba saidai yanayin idonshi ya canza zuwa launin ja , ya tsareni da kallo har naji tsoro ya kamani , gani nan zuwa ya faɗa tare da fita daga kicin in cikin tsananin ɓacin rai , ajiyar zuciya na sauke tare da cewa Allah ya tsare hanya , bai ansa ba ni kuma naci gaba da abinda ya shafeni. Hankalin kaf "yan ɗakinsu Dikko idan yayi dubu ya tashi har Momy gaba ɗayansu sun hallara a bedroom inta sai koke² sukeyi , wai Jiddah ta bawa Perpy fiya² a lemu , Dikko yayi tashin hankali shi ba kanshi yakeji ba An mata yake tausayi , yasan zata shiga damuwa duk da tana nuna kawaici da kara akan yaron amma ai tana san ɗanta kodan bata fito ta faɗa ba ? Yarinya mai kunya da kawaici waye ma zaiyi irin haƙurin da An mata tayi ? Idan da wata mara kunya ce aka ɗauki ɗanta ba uwar miji ba ko uwar waye sai anyi tashin hankali , Allah kaɗai yasan ciwon da takeji akan rashin Papi baya kusa da ita , amma bata taɓa faɗa ba bata kuma taɓa nunawa ba , koshi bata taɓa nuna mishi ba daɗi ba akan rashin Papi , ta daiyi haƙuri tabar ma ranta , kuma babu wanda yasan ina ma Jiddahr tayi , Dikko kuwa cewa yayi shi baiga ma duk dalilin wannan fitinar da tashin hankalin da yasa aka ɗauko Papi ba , mema yasa tun farko aka ɗauko yaron daga wurin An mata , shi ina zaisa ranshi ? Wane hali rayuwar Sultana zata shiga ? Gaskiya fa ba'ayi ma rayuwarta adalci ba , me yasa ׳.............. ? Wallahi idan har Papi ya mutu saiya kashe Jiddah , sannan shima ya kashe kanshi dan wallahi yana jin kunyar An mata. Shima Dady cikin tashin hankali ya iso , ganin Dikko yana kuka yasa Dady shiga wani irin mawuyanci hali , yace Babana yi haƙuri ka daina kuka , a shagwaɓe Dikko yace kuka Dady ? Ai yanzu ma na fara , yi haƙuri Babana zai samu sauƙi bazai mutu ba , ya faɗa yana kallon idon Dikko cikin yanayin shi Dikko ya tausaya mishi , Dikko yace haba Dady misali nine a irin wannan yanayi nayi imani kai da suma zakayi , yadda kakejin ni nine zuciyarka ya nuna kanshi , sannan yaci gaba da cewa nima uwarshi itace zuciyata , idan har yaron nan ya mutu , An mata ɗan ƙaramin hauka zatayi , wane irin hali kake tunanin zan shiga idan ta shiga wani hali ? Idan na shiga wani hali kaima shiga zakayi , kana shiga Momy ta shiga , Momy na shiga kaf "ya "yanta sun shiga , na rantse da girman Allah idan yaron nan ya mutu tou tabbas nima mutuwa zanyi dan bazan yadda inga tashin hankalin da An mata zata shiga ba , saina hau saman bene zanyo ƙundubala kuma nima saina sha fiya²n in faɗo matacce........ Yana faɗin haka ya fita yabar ɗakin. Cikin damuwa Dady yake kiran Dikko , Babana² , amma Dikko yai tafiyarshi , hankalinshi kuma ya tafi wurin Sultana da tace masa yana can yana yawon kamfen ya manta da yankin iyalinshi , dole yaje ya bata natsuwa duk haƙurin ta saida ta cire kunyarta ta nemi haƙƙinta wurinshi , itama Jiddah sai yaci uwarta idan ya riƙeta babu wanda ya isa ya tashi hankalin An mata idan dai yana numfashi , ƙaramar yarinya mai haƙuri , ai haƙurin An mata yayi haƙuri ko sai an kasheta ne wai............? Cikin wani irin ɓacin rai mai tsananin ɓaci ya dawo , ni bana san ganinshi a yanayin fushi tsoro yake bani wallahi , tunda na gama abincin banci ba naje nayi wanka ina zaune ina zaman jiran dawowarshi , sannu da zuwa nayi mishi bai amsa ba , saida yazo dai² inda nake zaune yaja hannu na har zuwa ɗakinshi kuma baiyi magana ba. Dakel ya rufe ƙofa sannan yazo inda nake tsaye ya fara cire kayan jikina , kallonshi nayi cikin damuwa nace baka da lafiya ne ? Baimin magana ba yaci gaba , saida ya saukeni duka sannan ya jani zuwa bakin gado , da hannu ya turani na faɗa sama ina kallonshi , bargo na ɗauka na rufe jikina tare da saukowa ina matsawa inda kayana suke nace masa ka barshi kawai ngode , yaye bargon yayi tare da maidani saman gadon , ban sake saukowa ba , a damuwance shima ya hau gadon , har yayi abinda zaiyi ya gama baiyi magana ba kuma bai wani nuna yanajin shauƙi ko farin cikin kasancewa dani ba , kuma duk fushin da yakeyi bai hanashi maidai nushi ba , ya maida duka sosai , saida ya tabbatar na samu natsuwa kuma ya bani natsuwar da farin ciki da ƙoƙari ba wani lalaci , saida ya tabbatar nakai sosai sannan ya barni , ya rigani yin wanka , yana fitowa ya shirya , godiya nayi masa tare da masa addu'ar Allah ya ƙara mishi lafiya kuma ya bashi wata lafiyar a fagen wasan danbe , yayi nisan kwana mai albarka , baiyi magana ba ya shirya ya fita daga ɗakin amma duk wayoyinshi a nan ya barsu kila ba fita zaiyi ba. Bayan ya fita nima na gyara jikina na fito , palon ɗakinshi na sameshi zaune saman kujera ya kwantar da kanshi saman hannun kujera , ina fitowa ya fara faɗa wai ba ya hanani wannan ƙazantar ba ? Kodai in rabo kayana ɗakinshi da nawa , yana nufin in ibo wasu in ajiye a ɗakinshi , ko kuma duk lokacin da zanzo in riƙa tahowa da wasu kayan , daga yau bazai sake min magana akan idan na cire kaya na daina maidasu ba saidai zai zanemin jiki tunda kunnen ƙashi nake da , murmushi nayi ba tare da nace masa komai ba , nasan kila wani ya ɓata mishi rai yana neman hanyar da zai dakeni ne danya huce shi yasa yake nemen ya tsakuloni faɗa tunda banda haƙuri in masa rashin kunya ya zaneni yai tafiyarshi , dole kimin dariya tunda kin raina ni , haba niɗin banza ? Ni na isa in raina ka tunda nasan amfaninka ina faɗin haka nayi waje..... Cike da tausayi yabi bayan Sultana da kallo , wata zuciyar tace masa kodai ya faɗawa An mata abinda ya faru , yayin da wata zuciyar ta gargaɗeshi akan ya barta kawai tayi farin ciki , idan kuwa ba haka ba yau bata iya bacci kuka zatai tayi mishi kuma yace zai daketa , ya ƙyaleta Allah dai ya bawa Papi lafiya kawai ya ɗauko mata ɗanta , ashe shi yana ta hasashen Jiddah zata barbaɗe An mata ashe tunaninta ya karkata ne akan ɗanta , hmmm Allah ya kauda ɓacin rana , dan ya ɗaukar ma kanshi idan har Perpy ya mutu wallahi saiya kashe Jiddah , Dady kuwa ya kira Dikko baisan adadi ba amma Dikko yayi fushi bai ɗauki wayar ba , Momy ma ta kirashi itama har ta gode Allah amma sam Dikko yanaji kuma yana gani amma ya basar da kiransu , Dady kuwa yayi ma Momy fata² yace bata da lissafi kwata² in banda hauka da rashin tunani irin na mata , yace yarinyar da uwarta ta kashe auren "yarta da ɗanta akan wani dalili banza can nasu na mata , kuma "yar ta fita da ciki taje ta zubar da cikin kuma ta kirata ta faɗa mata dan taga iyakarta , duk abinda sukayi hakan baisa ta gane inda duniya ta nufa ba taje ta sake jajibo Jiddah ta kawo cikin zuri'arta , dama ita Momyn Jiddah ta zubawa fiya²r ta mutu kowa ya huta , ya ƙara da cewa kuma idan har Papi wani abu ya sameshi ba abinda ya dameshi da yadda zuminchin su yake saiya ɗaure Jiddah daga ita har uwarta. Momy zatayi magana Dady yace ta rufe mishi baki , ba abinda zata faɗa mishi , batayi ma Mom Papi adalci ba , ko albarkacin yadda Babanshi ya jefo yarinyar mutane daga sama kuma ta dawo daga duniyar ƙanwar mutuwa a hakan bata rabu da Babanshi ba ta haƙura ta zauna dashi , idan bata sani ba Babanshi dukan yarinyar nan yakeyi wahalarshi takesha kamar tashin hankali amma ahakan tayi haƙuri ta zauna dashi bata taɓa guduwa ta barshi ba , Cike da nadama Momy tace taya zai daketa ne ? Dady yace da kanshi ya faɗamin ko nasan sunyi ne ? Yaje ya ɗauko amanar yarinyar mutane yazo ya kulle yarinya a gida yana ta gana mata azaba , nayi imani da Jiddahr ce tuni saita faɗa kuma sai anyi tashin hankali , ita kuwa ya doketa ya zageta duk haukarshi idan ya tasoshi akanta yake sauke masifarshi , ko wani ya ɓata mishi rai saiya je ya juye akanta ko ita jakace ne ? Ita iyayenta basa santa ? Ko ita ba haifarta akayi ba ? Amma duk wannan baiyi ba da masifa saida sukaje suka fitar mata da ciki tun farko ya nuna Rabiya , yace duk da haka tayi haƙuri kullum tana liƙe dashi haba baki da adalci , da kece akayi ma wani daga cikin "ya "yan naki ko aka taɓoki a gidan nan haka zaki ƙurmusashi a ɗaki ki haukatoshi ya fita yaita hauka yana saiya kashe² , baƙin halinki yasa aka birkita miki tunanin ɗa , baya auren karuwa , ita karuwa ce ki kiyayi kanki da duniya , da hannunshi ya nuna yace duk sirrin dake rufe ki kiyayi buɗeshi idan kuwa ba haka ba wata rana sai kunya ya hanaki fita , mtswww ya fita daga ɗakin..... Dikko nidai banajin daɗi , ba tare daya kalleni ba yace An mata me ya sameki ne ? Ya tambaya a sakatance , kallonshi nayi tare da cewa cikina ne ke ciwo na faɗa ina kwanciya jikinshi , yana burgeni idan yayi magana da shagwaɓe ko sakata irin nasu na "ya "yan "yan gayu , sannan yayi murmushi dakel yace to ko sai na ƙara kamfen in ne ? Yayi maganar yana riƙeni da riƙon da nake so , ƙara lafewa nayi sosai a jikinshi , gyara kwanciyarshi yayi tare da ɗagoni daga saman gadon ya ɗora rabin jikina a jikinshi yace ta ina kikejin ciwon ne ? Ya ƙarasa maganar yana laluba cikina da lallausan hannunshi , agogo ya kalla da sauri ya saukeni daga jikinshi yace Dady yayi maganar yana sauka daga saman gadon jikinshi yana ƙyarma , lafiya yazo gidan nan ? Yayi maganar cikin tashin hankali , a zuciyarshi yace na shiga3 kardai Papi ya mutu Dady ya taho , da sauri yasa talkaminshi ya fita , Sauka nayi daga saman gadon na fita palonshi ta jikin window na tsaya tare da yaye labulaye , a dai² lokacin da naga Dikko ya isa wurin Dady da gudu ya riƙeshi yana magana , wurin da nisa sosai banajin abinda yake ce masa , amma shi Dikko yanayin maganar da yanayin fushi yana nuna kanshi sai kuma ya nuno bayanshi , da hannu Dadyn ya nuna mishi yayi haƙuri yana shafa kanshi , girgije hannun Dady yayi daga saman kanshin da yake taɓawa ya juyo cikin fushi , riƙoshi Dady yayi ya rumgumeshi yana magana cikin yanayin lallashi , shima Dikkon riƙe Dady yayi ya rufe idanuwanshi yana ci gaba da magana , bansan yadda akayi ba naga Dikko da Dady sun shiga mota sun fita daga gidan , Ashiru da Abbakar kuma sun fita a motar Dikko sunbi bayansu , tsoki nayi tare da cewa wannan siyasar banza Allah ya raba Dikko da ita...... Yau bai kwana gida ba , kuma washe gari bai dawo ba sai 11:30 na dare , ko makaranta yau ni naje da kaina ba Ashiru ya kaini ba , kuma daya dawo gidan baifi mintuna 5 ba ya fita , dan naji shigowarshi amma kafin in fito harya fita ban samu haɗuwa dashi ba , saida yayi kwana biyar baya gida kuma yana Katsina , ranar daya dawo , dashi da Papi dasu Nabeela suka sauka gidan , palo na samesu su dukansu "yan uwanshi manyansu da yaransu , Papi sai kuka yakeyi yana kiran Momy , Dikko kuma yana kwance saman kujera 3siater da yanayin damuwa , Rabiya tana zaune saman hannun kujera sai cewa takeyi yayi haƙuri , kai gaskiya bazan gaji da faɗa ba , "yan uwan Dikko wayayyin matana ne , "yan gayun billahillazi , ibar ƙarshen ƙarni , gogaggi masu ilimi da buɗewar ido , duk iya gogewarki idan kika tun karesu wallahi sai kin kama kanki dakarun mata ne da zamani kebinsu , sannu nayi musu nima na samu wuri kusa da Nabeela na zauna ina kallon Dikko , kaɗan ya buɗe bakinshi yaja iska ta ciki da yanayin da idan muna cikin wani yanayi dani dashi , murmushi nayi tare da sauke kaina ƙasa , shima murmushin yayi tare da cewa An mata ga ɗakinki nan yana kiranki , da gudu Papi yayi wurin Rabiya yana ci gaba da kiran Momy ya maƙale ƙafaɗarshi ya riƙeta ya juyo yana kallona. Jawoshi Dikko yayi gabanshi yace kai sa idonka nan , kallonshi Papi yayi yana kuka , nan ne gidanku ɗan ƙwaƙwar tsiya kana can kana ƙwaƙwa za'a kashe ka bari inji ka sakemin kuka kaga yadda zanci maka , dariya akayi gaba ɗaya , duk suna kallon Dikko da Papi , ƙara ɓata fuska da baki Papi yayi saida yayi ajiyar zuciya yace Momy , Dikko yace ga Momy can ya nunoni tare da cewa kai fashin iyaye kakeyi ne ? Ajiyar zuciya ya sake saukewa a karo na biyu yana kallon Dikko , murmushi Dikko yayi cewa zaka hau doki ? Ya ƙarasa tambayar da girarshi , kai ya ɗaga alamar zai hau , waya Dikko ya ɗauka ya fara kiran Umar , bayan ya ɗauka yace a kawo doki Papi ya dawo gida , yana faɗin haka ya tsinke kiran yace je ka wurin Momy itace zata ɗoraka a doki , wurina ya taho yana ajiyar zuciya , amma da yazo saiya tsaya wurin Nabeela yana kallona , Dikko yace kace mata ka daina kuka zaka hau doki , cikin shaƙaƙƙiyar murya ya faɗa yana kallon cikin idanuwana , dan kauda kaina nayi cikin yanayin jin kunya , dariya Dikko yayi tare da cewa Papi riƙeta idan baka riƙeta ba bazata ɗoraka ba tace , da sauri na tashi , dariya Dikko yayi sosai yace ku kalli fulani da kawaici , yau ni ga ɗan farko gaban An mata , kam aiko yau saina ɓanɓare miki kunya tashi yayi ya ɗauki Papi suka biyoni ɗaki , A kona ya sani ya sauke Papi ya riƙe hannunshi yana daga ta bayanshi , cikin kwantacciyar murya yace riƙeni ya faɗa yana min kallon ƙauna , riƙeshi nayi cike da soyayya , yace sumbaceni ya nunamin saman bakinshi da ɗan yatsa kuma bai daina kallona ba , matsawa nayi na sumbaci bakinshi , da hannun ya riƙo ƙeyata ya haɗe bakuna wuri ɗaya yana sauke ajiyar zuciya cikin ƙaramin sauti mai tada hankali , bakinshi a cikin bakina yace ke Papin ne baki ɗauka ? Ni bana san wannan kunyar gaskiya so kikeyi yazo bai saba dake ba kullum yana kiran Momy ? Haba An mata nidai bamu iya irin wannan abun ba kinji ? Kija ɗakin a jiki idan Umar yazo da doki ki ɗorashi da kanki , yana san doki sosai , kuma zan bar muku doki ɗaya anan zaki ga ya liƙema gidan nan bazai wani sake tunanin gidanmu ba , kiyi wasa da ɗanki kija shi jikinki idan kina wannan kunyar haka zasuyi ta ibe miki "ya "ya suna tafiya dasu su kuma zasu saba da can ke kuma ko oho , idan kika bar "ya "yanki sake haka za'ayita labbatarki ana kakkashe miki su , ki koya ma "ya "yanki tsoron mutane , banda Allah yasa Papi yana da sauran rayuwa yanzu da an kashe miki ɗa , kuma ai nasan zakiyi kuka ko ? Ya ƙarasa maganar yana ci gaba da tsotsar bakina cikin wani irin bahaggon yanayi , mutsurniya na fara ya girgaza kanshi alamar in bari , kuma in bashi harshe na , riƙe harshen yayi tare dayin murmushi mai sauti yana kallon idona cike da tsantsar ƙauna , gaba ɗaya jikina mutuwa yayi na kasa wani ƙwaƙwƙwaran motsi , da ɗayan hannunshi ya kamo hannuna ya ɗoramin inda yake so na riƙe mishi kanshi , nice na ajiye ɗayan da irin yadda yake so ya kasance , dan nima zuwa wannan lokacin na fara zama "yar hannu , ina riƙeshi kukan Papi ya fara fitowa , sakeni yayi tare da jana ya kwantar dani gefen gado dan yasan bazan iya tsayuwa ba , dan cewa yayi wai da an taɓani sai kawai in wani mutu murus , shi wannan abun yana mishi baƙin ciki ragguwa da ni , fita yayi daga ɗakin dashi da Papi..... Har dare duk basu tafi ba , nima ban sake fita ba , koda Umar yazo da doki shine ya ɗora Papi , abinci ma Momy ce ta bada aka kawo musu , bayan abinci yazo Nabeela tazo ta kirani muci abinci , gaba ɗayansu sun hallara a saman tebirin cin abinci nima kujera naja na zauna , mai bin Rabiya take ba Dikko labarin yadda suka ƙare da mijinta da zaiyi aure , bansan farkon labarin ba , amma tunda naga Dikko yana gaggaɓa dariya nasan cuta akayi , jakarta ta buɗe ta fiddo irin maganin da Dikko ke bani , ƙara ƙyalƙalewa yayi dariya yace nafa yadda basai na gani ba , mata ? Mata ? Hmmm , Rabiya tace ai raina ta ma yayi ni tayama namiji zai fara hasashen ƙara aure bare ya fara tunkarar matan , dariya Dikko yayi tare da riƙe kanshi da hannun haggunshi yaci gaba da cin abinci kanshi yana kallon filet in da yake cin abinci , Nabeela tace ai wallahi ba wanda ya isa ya auramin tsoho tayi maganar tana fashewa da kuka , Rabiya tace banza karki ma kanki baƙin baki wannan jakar matar tashi ba a bakin komai take ba wurinshi , koma komai ce ke a wurinki mayinos ce , cikin kuka tace ni sai kace nice kaɗai ɗiya a gidan ? Dikko yace tou auren tsoho miye kuma ? Yayi maganar yana ɗaure fuska , yace ko dan anyi magana a gabanki zaki mana rashin kunya , cikin kuka tace Yaya amma waye aka haɗa da tsoho ? Saini ? Rabiya tace ai tsohon yafi saukin shigarwar lungu , ga matarshi wata tutar ƙasa ce , ke har akwai macen da zata tayar miki da hankali ? Dikko yace ƙyale sakara , Nabeela tace nifa banajin matarshi kawai dai yamin tsufa ne , Dikko yace to zani ne shi da zaki ce ya miki tsufa wurin ɗaurashi ? Ko zani ne shi ai abun iyawa ne ma , idan ya miki tsufa ai kinsan irin wanka ke da zaki ɗauka iya wankuwarki iya adadin yadda tsufan zai ɓoye a jikin tsuhuwar sitirar da kika saka , kinga tunda ya haɗu dake basai ki rage mishi tsufan ba ? Nuna Rabiya yayi tare da cewa ai kamar Hajjaju ce da atamfar data ɗaura tun ina rakiyar zance take da atamfar nan har yanzu kullum kyau take mata duk tsufarta , dariya akayi gaba ɗaya amma banda ni , Rabiya tace lallai Baban Dady amma wallahi ka rainani da yawa , kai lokacin da nayi zance ma ina kazo duniya ? Ɗaure fuska yayi , gaba ɗaya suka sake ɗaukar dariya , maibin Rabiya tace bar ɗan iska saboda yaga ya ajiye wannan gemun yake raina mutane sai munbi dare mu askeshi , dariya yayi tare da cewa da kuwa kun asko masifa , mai bin Nabeela ta canja firar da cewa mukam dai sai baba gomna muma muna bayan Dady , Nabeela tace idan ya faɗi zaɓen fa ? Kike wani kiran gwamna , mai bin Rabiya tace bama zai faɗi ba sai yaje insha Allah , ah munga su Nabeela as matar gwamna , kwarkwasa kenan , Dikko kuwa cewa yayi oh , An mata kin daiji ko ? Wai ita matar ta gidan itace tutar ƙasa , bata miƙe ba kenan tana kwance , jinjina kanshi yayi tare da cewa lallai matan ciki sai sun dage , ai ya kama ace idan mijinki zaiyi aure ita wacce zata shigo ya zamana gabanta na halbawa saboda shakkunki da tsoron kishi dake , amma sai ya zama ita mai shigowar wai itace zata halba zuciyar ta ciki , kina aikin me mace ? Haba mata ? Idan ke tutar ƙasarce kamar yadda kuka faɗar saita shigo gidan dake da mijinki da "ya "yanki tazo ta gigita miki miji , kina can kina haukar banza zakiji karatun yasha banban , idan kuma mara adalci ne saidai ya yarfeki tunda shi ya samu lallausar rayuwa , nidai idan zan ƙara aure nasan amaryar sai taji tsoron An mata , Rabiya tace ƙwarai kuwa ita bama zata yadda ta fara shigowa ba ko Sultana ? Tayi maganar tana kallona , Dikko kuwa cewa yayi ai zanyi auren da wuri ne , Gyara zamanshi yayi tare da cewa bara in baku labari , a london na haɗu da wata "yar tasha , tunda ta shigo jirgi kawai tayo wurina ta zauna kusa dani , ɗan yamutsa fuska yayi tare da nuna yadda mata keyi , da irin maganar mata , yaci gaba da cewa aka wani cemin sannu ko ? Ya nuna yadda tayi maganar da yadda ta zauna , yadda yayi abun ne ya ba kowa dariya gaba ɗaya harni saida nayi dariya ina kallon Dikko , wallahi Dikko baijin magana ko kaɗan , shi kuma baiyi dariya ba yaci gaba da cewa da wutsiyar idona na kalli sakarai a zuciyata nace suna can na baro gidanmu , nidai ban mata magana ba , riƙe take yarinya tana da aji sosai gaskiya "yar gayu ce kuma ta iya wanka tana fama da wani irin girman kai , amma duk girman kanta da tazo wurina saida ta saukeshi , nidai banyi mata magana ba kuma ban kalli inda take ba , can bayan wani lokaci sai ga Abbakar yazo , yana zuwa yace DK ya haka kuma ? Shima Abbakar ya kwaikwayi maganarshi , yaci gaba cewa keda ke Katsina idan kin gansu ko kinji maganarsu tou Dikko yasan suna nan daga ita har Abbakar in , Abbakar yace malama da Allah tashi , batayi ma Abbakar magana ba ta juyo wurina tace suna na Yusra , haka nan naji zuciyata ta tashi kamar zanyi amai wallahi , da sauri naci cingom , Abbakar kuwa yaci gaba da cewa bara ki tashi a wurin ba ? Wurin zamanta ta nuna mishi da hannu tare da cewa ni ba'amin magana a saman kai , danni maza basa burgeni , saboda hauka irin na Abbakar ƙiƙi² ya kamata da kokowa , yana bara ki tashi a wurin ba ? Naso in musu dariya amma sai nace ya barta , bayan ya saketa ni saina tashi nace shi ya zauna , ina tashi ta taso da yanga sai ƙwarƙwasa take tana yauƙi tafiya cikin tsari da ɗaukar hankali irin tafiyarki Hajjaju ya nuna Rabiya , yace cikin kissa tace haba Yayana ya nuna da salo mai burgewa yana ci gaba da cewa tace yi haƙuri idan na ɓata maka rai , tana maganar tana wani kakkafe ido , ya nuna yadda takeyi , gaba ɗaya aka sakeyin dariya amma yanzu banda ni , Dikko yayi wata irin dariya , yace kamar wani sakarai haka na kalleta , kallona yayi tare da cewa tafa burge , kunga kenan ya ɓadda labarin akan yadda ya ɗaukoshi , ai farkon labarin cewa yayi duk girman kanta da tazo wurinshi saida ta sauke , kuma yace data faɗi sunanta yaji zuciyarshi ta tashi , amma da yaga naji kishi saiya juya labarin kunga kenan ya fasa faɗar yadda labarin yake kenan , bai ci gaba da labarin ba , duk yadda akayi kila Yusra ƙawar Sadiyya matarshi data mutu , irin tafiyar Rabiya da ya faɗa kenan yana so ni na koya kenan. Cikin fushi na tashi , amma kafin in miƙe ya zaunar dani da ƙarfarshi yana kallona , Rabiya kuma tace , tou ya kukayi ? An mata najin kishi mubar maganar , Rabiya tace haba Sultana ai laifin kine ma fuska kika bashi har yazo gabanki ya samu ikon maganar mace , Dikko yace ai ban shanyu ba shi yasa zanyi ma Perpy wata Momyn. Canza labarinsu sukayi akan kishiryar Nabeela wai ƙazama ce ba gogewar rayuwa , bata iya komai ba saidai taci ta jibge a wurin , Dikko dai bai sake magana ba ni yake kallo , yanajin yadda ake ta aibata sakarkarin mata , sai ƙara yi ma Nabeela ɗamara ake ana ƙara ɗorata a hanya , bayan wani lokaci kuma sai suka koma labarin kayan mata , tashi Dikko yayi dan har yanzu Umar bai dawo da Papi ba , Nima tashi nayi na barsu , ina shiga ɗaki wanka na shiga , lokacin dana fito har sun tafi , sai Nabeela da Papi kaɗai , ina fitowa suka shiga danyi mishi wanka , kafin ta fito na ɗauki kayana nayi ɗakin Dikko , sannu da zuwa yayi min tare da ansar kayan cikin ladabi , yace Allah ya taimakeni kenan ? Ai ina nan nace tou kai Dikko me ya kaika ? Ila marin mace da mangariba , 🤔 ai na ɗauka yau dahuwar kan rago zakimin ? Nayi tunani kila a saman wuta zan kwana dan nayi wannan maganar , nace Dikko yau zakaci ubanka An mata tayi fushi kuma ga Nabeela , Allah dai ya rufamin asiri ashe ina da rabon zanyi farin ciki a daren nan yayi maganar yana zaunar dani gefen gado , yaci gaba da cewa ai ban sani ba "Yar matan nawa ta girma ba. Kusa dani ya zauna ya rungumoni , sannan ya shiga rattaɓamin kaf abinda ya faru da Papi , naji babu daɗi sosai amma shi saina nuna mishi ai ba komai , yace munafuka ce Jiddar nan , yace lokacin da nayi rashin lafiya , wanda na tafi na barshi kenan , yace tazo ta zauna tayi ta haɗa masifa , kuma itace ta kai Momy ta barota suka ɗauko Papi kila tun lokacin take so ta kashe shi.... Bayan kin tafi kin barni........... Kai.................... Saina kashe kaina , wallahi saina mutu tunda baki so na mutuwa zanyi , Yazeed kike so ko ? To ni zan mutu in bar mishi ke , buɗe ƙofa nayi na fito , na biyo bayanki amma ban ganki ba , komawa nayi ina ihu , na ɗauki wayar wuta da aka sauke ƙasa na koma ciki , ina shiga na hau sama ina ihu saina kashe kaina , mai gadi ya fara kiransu Ashiru , nasan na ɗaura waya a wuyana bayan na ɗaure ƙarshen a jikin ƙarfen bene nayo ƙasa , Daga haka ban sake sanin abinda ya faru ba , Ashiru yacemin da mai gadi yai mishi waya gaba ɗayansu suka zo , hankalin kowa ya tashi gani na zube a ƙasa , kila wayar bai ɗauru ba , ko kuma nayi ma ɗaurin nauhi shi yasa ban tsaya a saman iska na mutu ba , a haka suka sameni , da suka tambayi mai gadi abinda ya faru , yace bai sani ba amma ya ganki kin fita da gudu ni kuma ina kiran Yazeed , Dady suka kira kai tsaye suka sanar dashi cewa Mai gida ya mutu , Dady yana jin haka ya maƙale wurin ya daina aiki kwata² , sune suka sanar da kowa Dikko ya mutu , Dady kuwa daya dawo saidai yace Babana , haka yaita ɗaukewa kamar "yan nepa suna wasa da wuta , tafiyar ƙarshe ce da yayi saida aka kaini government house Dady ya dawo , yayi kuka wanda bana san ina faɗa , saida aka taru Dikko ya mutu , An mata da anyi gaggawa rufeni da an binneni da raina. Bayan an tabbatar ban mutu ba wanda shima Dady ne ya kafe ban mutu ba , irin sabbatun nan na wanda zafin rashi ya ɗimauta , haka Dady yasa akaita kirayen² likitoci , a ido ni na mutu amma a baɗinance Dikko yana nan , murmushi yayi tare da cewa wai aljannu sun shanye numfashi na , haka aka fita dani waje akayi ta magani daban ciwo daban , jinyar nan da Dady akayita bawan Allah.... Abinda yasa dana samu sauƙi ban wani ji damuwa akanki ba , nasan ina da fushi sosai kuma haka nike da riƙo kuma ina da halin ko oho , duk abinda na bashi baya na gama dashi har abadan duniya wallahi , bansan abinda yasa ni bana iya fushi dake ba , ko nace zanyi zuciya dake bana iyawa , tunda nake a rayuwata ban taɓa gardama wa iyayena saida kika zo rayuwata , Labarin mafarkin da kikeyi kaf abinda kika faɗamin saida Mustapa ya faɗawa Ashiru , kuma shine yace wai anyi ma Al ' Ameen lamba su duba kanshi zasu ga aski da lambar mutuwarshi , ni bansan Al ' Ameen yana tsafi ba kwata² , tou tayama zan fara mishi wannan mummunan zaton bayan rayuwar kowa a rufe take , babu wanda yasan sirrin wani sai wanda ya faɗa , Mustapha yasa aka fitar da Al ' Ameen yace wallahi mutuwa zaiyi kuma idan ya mutu hannuna zan tabbata matsafin kamar yadda mutane duniya ke kallona. Naso naga Al ' Ameen dan naso zanyi magana dashi amma hakan bai yuwu ba , shi Mustaphan yayi ma Ashiru jagoranci zuwa inda sukayi tsafe²nsu , komai Ashiru yayi saida suka gama komai lumfashi na ya dawo , tunda nake ban tabajin irin wannan tashin hankali ba wai an shanyemin nufashi kiji wani masifa , hmmmm , Yazeed kuwa Ashiru yaci ubanshi kuma shine ya maido Abbakar company duk bansan anyi ba , Waye shiɗin ? Kawai abokina ne amma abotar ba wani can² ba ya faɗa yana yatsina fuska , tou shi me yasa Ashiru ya ɗaukoshi ne ? Munyi maganar shi da Ashiru anyi ma wata "yar uwarshi fyaɗe harta mutu , da na shiga cikin lamarin Ashiru ya fitar dani , amma ni Mustapha yacemin wai matan Babanku dasa hannunsu a damuwarka , kwanciya yayi tare da kwanto dani jikinshi yace can damuwarsu duk abinda mutum yayi kanshi , idan nayi maganarta nayi imani Dady saiya saketa ni kuma bazanji daɗin haka ba , saboda duk Momy za'a ɗorawa laifi , familyn su Dady haushinta sukeji sosai danma suna shakkun su Rabiya ai da yanzu sunyi waje da ita , ya faɗa yana nunawa da hannunshi , yaci gaba da cewa "yan uwan Dady basujin magana yadda baki tunani amma zaki gani tunda zaki shiga cikinsu , suma dai wayayyi ne amma Momy ta raina ma wayewarsu shi yasa "ya "yanta suka fita daban , tsarinsu ya fita daban idan kun shiga zakiga yadda su Rabiya ke bada haske a taro , gasu da rainin wayau , idan su Rabiya suka raina miki ƙura tom hmmm ya jinjina kanshi , amma duk wani banzar wayewar familyn Dady idan "ya "yan Momy sunzo to kin zama "yar kallo da koyon gyara inda aka tsere miki a wanka , zamani yazo anan zaki gani ki koya ki kuma yi gyara , ni dama bana wani shiga sabgar kowa , tunda bana binsu biki ko suna , iyakata dasu gida , idan basa nan zanji babu daɗi gidan yamin ba daɗi kuma Momy bata da magana , ni kuma faɗan da mukeyi dasu ne nakejin kewarsu idan basa nan , ko wuri zasu zasuce munafiki yau idan muka tafi bazamu dawo da wuri ba , kuma kowa baya rayuwa da "yan wasu ɗakin sai "yan ɗakinsu , haka zan gaji da zama in fita cikin gida bana nan bana can kamar wani maraya tunda ni bana fita waje iyakata gida Dady baya bari naje wani wuri saidai in saci hanya idan baya nan , idan suka dawo zanyi farin ciki , kuma zasu bani labarin duk abinda ya faru idan sunje wuri sun dawo , ni ba abinda ya dameni da rayuwar wani tawa nakeyi , sai "yan uwana mata sune kaɗai abokaina muyi faɗa mu shirya , suma "yan uwan Dady ni babu wani ruwana dasu dan Momy ta koyamin tsoronsu tun ina ƙarami , su kuma suna so na saboda yadda Dady yake ƙaunata dan soyayyar Dady a kaina bai ɓoye ba , amma iyakata da mutum sannu daga nan kawai zan zama kurma , kenan bayaji bare ya bada amsa , idan kuma ba'aci sa'a ba ko kayimin magana sai in maka shiru bazan ma ce maka sannun ba sai in tsare ka da ido ya faɗa yana murmushi , yace sai kiga simi² mutum ya kama gabanshi , kuma ba ƙarya ya faɗa ba , ashe yana sane da duk iskancin da yakeyi , dan aradu idan Dikko ya riƙeka da ido sai kaji babu daɗi har ka kama kanka , tou gashi baida yawan murmushi kuma shi dariya ma sam² da bayayi sai yaji mugunta zakiji shi ƙa׳ yana dariya , kuma dariya ba ƙaramin kyau take mishi ba , Allah sarki mai uwa baya san laifinta , amma gaskiya Momy gaba ɗayanta batayi ba bata da mutunci ko kaɗan , gata da raini , rankatakaf ta ɓata "ya "yanta da baƙin hali basu san mutunci kowa ba saina mazajensu shi yasa mazan nasu kamar sun masu asiri biye mazajensu suke dasu , kuma ita bata iya neman asiri ba saidai bariki da duniyanci wurin iya nannaɗe zuciyar namiji , shi yasa Momy ta share kowa a wurin Dady dan yanaji da ita sosai , amma basa san ace Momynsu tana da miyagun halaye , kai , amma gaskiya "yan uwan Dikko da suke ɗaki ɗaya zamani ne su , makaranta ce mai zaman kanta , sunyi׳ , sun haɗu׳ wayayyi ajin farko , kuma sunfi "yan ko wane ɗaki yawa a gidan , ga kuma Mai gida DK nasu..... Satin Papi 3 a wurina amma har yanzu bai daina kukan Momy ba , kuma Nabeela tana nan ta dawo gidan kwata² da zama , ga Dikko baya zama , ni kuma banda lafiya , dana ce masa ko akai Papi wurin Momy cewa yayi kar a sake akai mishi ɗa wani wuri yaje yaita kukan idan ya gaji zai daina , Nabeela kuwa ta faɗawa Momy Papi yana ta kuka shidai Momy , tazo da kanta itama dai tayi kewar Papi , cike da soyayya Papi ya riƙe Momy su tafi wurin Dady , har ranar da suka dawo dasu Rabiya saida yaba Momy labari amma wasu ya manta sai ya tambayi Nabeela , murmushi Momy tayi irin na ƙasaitaccin mata da irin yanayin kallon Dikko , dai² gani sukeyin kallon amma idan kasa ido sosai zakaga kallon nasu yanayin ƙasa kuma basa motsa idon , baka ganin lokacin da idon yake tafiya idan suna rageshi , idan kuma suka gyara kallon nasu sai kallon ya bada wani iri mai burgewa , da irin kallon ta tsare Papi tana cewa ni duk naga ka zama wani baƙauye ta faɗa tana murmushi da gefen bakinta tana ci gaba da cewa Nabeela anya zanyi auren nan ? Kafin Nabeela tayi magana Papi yace ni nayi cau ya faɗa yana harar Momy. Dariya tayi tare da cewa ni bakaimin wani kyau ba , iyayenka basu iya raino ba kuma bazanje dakai ba , kuka ya farayi yace ina juwa , dama da yawo ta kama Papi , duk wankan da akayi Papi saida Momy tasa Nabeela ta sake wankeshi aka gayeshi tace Nabeela taje anjima ta dawo dashi , gaba ɗayanmu mukayi mata rakiya ta tafi. Dikko kuwa ya kirani yayi faɗa sosai yace an ce masa wai anga Papi gidansu , meya faɗa min ne ? Zanyi magana yace in mishi shiru ni dama na raina mutane , ya ƙara da cewa ya rantse da Allah idan wani abu ya sameshi ni idan nayi mishi kuka saiya zaneni , itama Nabeela zai haɗu da ita shima Papin zaici ubanshi bari ya dawo , yana faɗin aka ya tsinke wayarshi. Ashiru ya bashi haƙuri , Dikko yace shi bawai yana hana Papi zama wurin Momy ba , fiya² fa aka bashi sai kace wani ƙwaro , idan suka kashe mata ɗa ni ba abinda ya dameni kuka ne dai bata isa tayi min ba , gidan nan munafinki gida ne kuma na faɗa mata , mu kanmu "yan gidan ya muka ƙare bare kuma wani jika , kadai san halin Momy haka take zama ta tisa Papi taita habaice² , tana irin wannan maganganun nasu na mata. Haƙuri Ashiru yai ta bashi ƙarshe dai Dikko yayi shiru ya ƙyale Ashiru. Nabeela kuwa kila shi ya kirata yaci mata mutunci , bansan yadda akayi ba taje ta taho da Papi , yana ta kuka , ta waya Dikko ya zageshi yace kuma bari yaji ance masa ya sake kiran Momy saiya turo Jiddah ta kashe shi aje can a jefar dashi , bazai sake ganin Momy ba kuma bazai sake cin abinci ba , Na faɗawa Inna banda lafiya , kuma na faɗa mata ciki nake da , na ɗauka zatayi farin ciki ta kirani tunda saƙo na tura mata , cewa tayi can ni ya dama , kuma bata faɗamin duk abinda ya shafeni da Dikko kar na sake faɗa mata ba ? Dole na haƙura naci gaba da rayuwata daga ni sai Dikko da "yan uwanshi mata. Rabona da Inna kenan , saida ta kirani ta faɗamin rasuwar ɗan uwanta baban Sultan , yayi haɗarin mota , a nan gidan Kaka ake zaman ta'aziyya , za'ayi jana'izarshi da bayan azahar , dani da Nabeela da Papi muka tafi , kuma kaf "yan uwan Dikko sunje min a ranar da akayi rasuwar suna nan akayi jana'iza bayan an dawo sukayi gaisuwa wa Inna Kaka da matan mamacin sukayi tafiyarsu , amma muna tare da Nabeela , Dikko kuwa bai zo ba dama baya gari , yadai turomin text in tafi gida haka nan bawai nan zanje in jibge ba harsai an raina ni ba , dana nuna masa ya bari zuwa anjima cemin yayi ya gama magana , dana faɗa ma Inna zan tafi taji damuwa tace in bari sai anjima nace mata shi yace in tafi , taji ba daɗi dan kowa da "ya "yanshi a kusa dashi haka na tafi tanaji kuma tana gani bataji daɗi ba , gashi ba dama ta kira Dikko. Tun daga ranar ban sake zuwa ba sai ranar addu'ar 3 , Momy ma taje min a ranar kuma su Inna anji daɗi matar gwamna tazo , haka taita tattaro mutane tana cewa ga surukar Sultana suje tayi musu ta'aziyya Momy kuwa riƙenta take tana wannan rainin nata , da ta tashi tafiya ta bada kuɗi masu yawan gaske sadaka , shima Dikko ranar addu'ar 3 yazo , kuma yana zuwa yayi gaisuwa yai tafiyarshi bayan shima ya haukatasu da kuɗi sadaka , ranar mu kuma sai dare muka koma gida dani da Nabeela bayan nima na bada tawa sadakar dan nima yanzu inaji na dai² nake da duk wani mai jin shi yana da hatimin nasarar shi , dan duk wata damuwa ko takaici Dikko ya shanyemin shi , baya bari inyi tagumi shi yasa ya sakarmin ragamar girman kuɗi , buɗa min fili kawai yakeyi ina yadda naga dama da rayuwata.... Yana nan bazai sake tafiya ba sai an gama zaɓe , itama Nabeela bayan zaɓe za'asa ranar aurenta , addu'arta Allah ya maida Dady a mulki sai kuma wanda zata aura shima ya haye , shima Dikko addu'arshi kenan Dady ya koma mulki , nima ina mishi fatan komawa bana so su faɗi....... 24/12/2019 👇🏻 *JAMILA MUSA...* 💅🏻 ⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊 _-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_ *KWARATA* _{{Kalu bale gareku matan aure}}_ *JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_ _Sadaukar wa gareku,_ 👇🏻 *ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_ & *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* 🅿 ------ 91 _Alhamdulillah_ _Alhamdulillah_ _Alhamdulillah_ *_Assalamu Alaikum masoyana , suna na Jamila Musa wacce kuka fi sani da Meelat Musa , ina muku fatan alkairi maudu'in rayuwata 😊 , zanyi matuƙar kewarku sosai , inajin wani iri a raina , jiki yai sanyi , idona shima zaiyi kewarku , yana muku bankwana da hawaye 😭 , gaskiya ina matuƙar sanku yadda bazaku iya ganewa ba , hmmm , tou ina dai muku fatan alkairi a duk inda kuke a faɗin duniyar nan alfaharina , zan tafi׳ , sai kuma Allah ya sake haɗamu idan muna rabon sake haɗuwa a cikin sabon littafina mai taken ƁOYAYYAR SOYAYYA , KWARATA yazo , kuma zai tafi , Dikko da An mata suna muku fatan alkairi , ni kuma Jamila nake neman yafiyar duk wanda na mishi babu daɗi , wani ban ganshi ba , amma rubutu na yaje gareku , ina alfahari daku , kuma ina muku fatan alkairi , ina matuƙar ƙaunarku sosai da sosai , masoyana da mukeyin waya daku , wasu kuma cht da wanda Allah yasa na gansu ido² duk ta dalilin Dikko da An mata ina matuƙar ƙaunarku , Allah ya sadamu da alkairi gaba ɗayanmu , ngode ׳ da yadda kuka nunamin ƙauna , na barku lafiya......_* 👏🏻 Yaya janje , a , a , da gudu Papi yabi bayan Dikko yana kuka , kai nifa babu inda zanje dakai , ƙara faɗar janje yayi yana bin bayan Dikko da sauri dan taƙaita gudun saboda ya isko shi , a , a Dikko ya sake maimaitawa , bin bayan shi Papi yakeyi yana ci gaba da kuka , dariya Dikko yayi sosai yace tou zo muje , yayi maganar yana kama hannun shi , juyowa Papi yayi tare dayi ma Nabeela gwalo da tace Allah yasa kar a tafi dashi , murmushi Dikko yayi ba tare daya sake magana ba suka fita , yayi kyau sosai a cikin ƙananan kaya , riga jinin kare baƙin wando rufaffun takalmi suma baƙi sai baƙin agogo , Papi kuma manyan kaya ne jikinshi..... Dariya nayi tare da kallon Nabeela nace zakisha mamaki , tunda yayi waccan dariya lallai sai yayi ma Papi wani abu na mugunta , kuma zaki sha al'ajabi bara su dawo , dariya Nabeela tayi tare da cewa kuma nima in rama gwalon da yayi min da zai fita..... Gaban mota Dikko yasa Papi yana cewa ai dai zakaje ko ? Ya ƙara tambayar Papi , goge hawayen shi yayi tare da cewa Janje Yaya , yayi maganar yana kallon idon Dikko , tou zauna , zama yayi a dai² lokacin daya tashi mota ya fara tafiya , Ashiru dake tsaye daga gefe yace Mai gida ai ban san fita zakayi ba , ba tare da Dikko ya tsaya ba yace ai ba nisa zanyi ba , ya ƙarasa maganar yana ɗage gilashin gefenshi da ya sauke danyin magana da Ashiru ya fice daga gidan da gudu..... Suna fita muma muka zagaya can bayan gida ina taya Nabeela aiki zatayi baƙi , gidan ne gaba ɗaya aka firgita , yasa ana ta rosheshi , nidai a ganina asara ce kawai dan wallahi gidan ya haɗu iyakar haɗewa , kuma banga abinda yayi ba , duk komai na gidan da aka fitar tsohon namu kenan , yaranshi ne suka kwashe su , ni ɗakinshi ma nafi tausayi dan Allah ya sani an daddaƙe ma kuɗi rai a ɗakin Dikko , anyi masa haɗuwa ta haɗaɗɗin haɗewar masu haɗuwa , can baya ma da akayi gidan anyi surutunshi sosai kuma har yanzu ba'a gama surutun ba , yanzu kuma wane irin gini za'ayi...... ? Aikin baizo wurinmu ba shi yasa bamu tashi ba , amma dai duk an fitar da komai na gidan su Ashiru sun kwashewa "yan uwansu , ba komai a gidan muma goruba road zamu tafi a daren yau sai an gama aiki zamu dawo , aikin da nake taya Nabeela baida wani yawa , amma kunsan yadda jiki yake , shi jiki sabo ne dashi , idan an horashi da wahala da ita zai horu kuma idan harma bakayi abun wahalar ba bakajin daɗi , idan ya saba da hutu tabbas baya iya ɗaukar wahala , shi yasa "yan gayu ashe muke ganinsu kamar sun raina mana hankali , to ba haka abun yake ba , saida na shiga fagen na gane haka , nima dai yanzu bana iya sakin jiki inyi aikin nan kamar jakkar ci rani , idan kuwa nayi aiki mai yawa sai nayi jinyar gajiya..... Bare dama akwai masu aiki maza da mata , kuma duk wani ma'aikaci , daga direbobi , masu shara , masu girkin abincin da ma'aikatan gidan ke ci , masu gadi , masu ban ruwa wa fulawowi har masuyi musu aski su gyarasu idan sun zame daga tsarin da ake sansu , gaba ɗaya a gidan suke zaune , suna da wurinsu daban , kuma a gidan ake basu abinci kuma albashi ake basu duk ƙarshen wata , amma shi Dikko bayacin abincin gandu , namu mukeyi daban ina da mai aiki ta daban amma baya san abinci masu aiki sai ni zanyi idan yana gari , kuma masu aiki basa gyara masa ɗaki , ko yanzu da bana lafiya shi yake gyarawa ya goge komai fes kamar mace , ya iya gyaran gado idan har yayi miki gyaran gado zakisha mamaki , baya san ƙazanta ko kaɗan , da nace masa Nabeela cewa yayi a , a , dan iyakarta palonshi bata taɓa shiga bedroom inshi ba , nidai da nazo amma ban sani ba ko a zamanin Jiddah tana shiga ba , saida muka gama abinda mukeyi Nabeela tasa aka kwashe komai aka kai a motar ta , sannan muka taho dan komawa ciki. Da gudu ya shigo gidan a dai² lokacin da mu kuma muka bayyana gaban fuskar gidan , tun kafin motar ta ida tsayawa cak ya kashe motar ya fito , tunda nake da Dikko ni ban taɓa jin waƙa a motarshi ba sai yau , ya wani ƙuro volume , buɗe hannuwan shi yayi ya nufo inda muke tahowa yana wata "yar munafukar rawa , daga ni har Nabeela dariya mukayi , rumgumeni yayi tare da ƙyalƙyalewa da dariya ya raɗamin wai Papi ya girma , cikin rashin fahimta na leƙa ta gefenshi naga Papi ya fito daga mota yana cewa ban nuna muku , dariya Dikko ya sakeyi sannan ya sakeni yana cewa yanzu zai cire wando ya fara kuka , ya faɗa yana nuna ma Papi yayi rawa , tsalle Papi ya farayi yanayin yadda Dikko keyi , murmushi Dikko yayi tare da kallon Papi ayyo ah² wayyo yana murmushi , sakin jiki Papi yayi yana ta rawa , saida Dikko yaga ya shagala yana rawa , ya koma mota yai tafiyarshi. Nidai ban gane girman da Papi yayi ba , kuma ni kwata² raina bai kawomin kaciya Dikko yayo ma Papi ba , saida muka shiga ciki yaci gaba da cewa ban nuna muku abinda Yaya yayi min , ya faɗa yana rumgumer bango , duk babu wanda yayi ma Papi magana , bayan Nabeela ta fito wanka yace mata , yayinya joki in nuna miki , cire wando Papi yayi , Nabeela tana zuwa , yayi dariya tare da maida wandonshi yace baci gani ya faɗa yana mata gwalo , kowa fita harkarshi yayi muka ci gaba da abinda ya shafemu , shi kuma sai murna yakeyi , saida ya fara shan azaba ya cire wando , muma bamu sake shiga sabgar shi ba kuma bamu sake kallonshi ba , allura tana fita Papi ya fara ihu.... Yana taɓa kaciya , Nabeela ta fara dariya tana ɗaukarshi a waya , tana cewa da nace karka je ba sai da kaje ba ? Yanzun nan zan tura Momy ta gani , nima abun dariya ya bani sosai , iskancin Dikko saishi , kullum abunshi gaba yakeyi babu alamar sauƙi , Nabeela daina video tayi ganin Papi yana halbe² a ƙasa yana cewa nama ɓata da Yayan nan , rumgume Papi tayi suka ci gaba da kuka tare , Duk daɗewar da Dikko yayi waje harya dawo daga Papi har Nabeela basu daina kuka ba , da nace masa me yasa yayi haka baiga Papi ƙarami bane ba ? Kallon Papi yayi tare da cewa gobe ma idan ka biyoni ƙaro maka zanyi , cikin kuka Papi yace kuma na fata dakai , ai nine na ɓata dakai shi yasa naje na kaika akayi maka , miƙa hannunshi yayi tare da cewa zo muje , maƙale kafaɗa Papi yayi yana harararshi cewa kuma saiya faɗawa Dady , murmushi Dikko yayi tare da cewa tou jeka fa faɗa masa , yayi maganar yana fito da wayarshi yace bara kaji ma in kira Dadyn ya ƙarasa maganar yana kara wayar a kunnenshi. Bayan wani lokaci ya fara magana a waya , Dady ga Papi zai kawo ƙarata yayi maganar yana ba Papi waya , cikin disashshiyar murya Papi yake faɗawa Dady abinda Dikko yayi mishi , bansan abinda Dadyn yace masa ba , ajiyar zuciya Papi ya sauke sannan yace to , shiru yayi , bayan wani lokaci Papi ya sake sauke ajiyar zuciya yace to , ajiyar zuciya ya ƙara saukewa ya faɗi Nabeela , ɓata fuska yayi ya taɓe baki yana ajiyar zuciya , bayan wani lokaci kuma yaba Nabeela waya , bayan ta gama tabani waya nima na gaishe shi , yamin sannu da mai jiki , bayan mun gama gaisawa nima nayi masa addu'a kamar yadda naji Nabeela tayi , sannan nabawa Dikko waya , fita yayi daga ɗakin yana magana a waya. A gaggauce muka shirya muka bar gidan , saida muka biya ta wurin Momy , tayi faɗa sosai da abinda Dikko yakai Papi akayi mishi , ta kuma yi addu'a Allah yasa a fita lafiya , anjima zata aiko Ashiru wurin Papi , bamu wani daɗe ba muka wuce goruba mu dukanmu , shi gidan an gama aikinshi , kuma babu abinda ba'a saka ba , komai na gidan sabo ne katakal , har kicin ma anyi mishi tsari mai kyau babu abinda babu. Abundai , sai Allah sabunanni...... Satinmu biyu a goruba road , gaba ɗayanmu bamu da wata damuwa , rayuwar mukeyi cikin farin ciki , amma tunda wannan satin ya kama Nabeela da Papi basa tare dani saboda asabar ta gaba ake zaɓe suna can gidansu , mijin da zata aura kuma an tsayar da ranar aurensu ne idan yaci zaɓe za'a haɗa da murnar cin mulki da kuma shagalin ɗaurin aure , idan akayi rantsuwa kuma amarya zata tare a gidan gwamnati kenan...... Ni yanzu gaba ɗaya na daina gane kan Dikko , ya burke bansan abinda yake damunshi ba , saidai idan na buƙaci ganinshi zaizo ne ya bani haƙƙina da zaran kuma ya gama zai kama gabanshi , da nace masa wai ina yake zuwa yanzu sai yacemin shi bazai zauna gida ba tunda ba mace bane shi , Abun ya dameni sosai , dan haka na kira Rabiya na faɗa mata kai tsaye , haƙuri ta bani tare da cemin in bari idan aka gama zaɓe zata zo , Inna dana kirata nace mata shawara na kirata muyi cemin tayi idan dai ya shafi Dikko karma na fara faɗa mata. Har akayi zaɓe aka gama ni bansa Dikko a ido ba , kuma Allah ya basu sa'a sun sake ɗagewa sama , wanda Nabeela zata aura shima yaci , duk shagalin da akayi banje ba Dikko ya hanani zuwa , Nabeela bataji daɗi ba kwata² , Momy ma taji babu daɗi da tace azo a taho dani cewa yayi idan dai shine yake aurena ya hanani zuwa idan kuma aurena ba a hannunshi yake ba tou inje , Momy da kanta ta haɗani da Dady a waya nayi mishi murna , Shagalin sake komawa a mulki banje ba , amma na ranar da aka ɗaura auren Nabeela naje , kuma tun safiyar ranar ina wurin Momy , kayan da zan saka Momy ce da kanta tayi minsu , duk abinda ya kamata itace tasa akayimin nima dai na fito kamar sahun "ya "yanta tunda ina da kyau na mai burgewa da baka gajiya da kallona , kuma banda irin wannan duhun kan na ƙauyanci , suna ta nunamin ƙauna da soyayya daga ni har Papi , Hmmmm , anyi wani irin shagali daya zo ma al'ummar jahar Katsina baƙo , ɗiyar gwamna ta auri gwamna , manyan mutane daga jahohi da dama sun samu damar halattar wannan gagurumin ɗaurin aure , wanda aka tara dubun² mutane , ni ina nan zaune a bedroom in Momy saman gado zaune kusa da Rabiya , abun duniya duk ya dameni , dan yanzu ko wayata Dikko ya daina ɗauka idan na kirashi saidai ya turo min text , wai idan wani abu nake so daga gareshi in mishi a rubuce basai na wani dameshi kira ba , kenan idan bani na buƙaceshi ba shi baya buƙatata ? Me hakan yake nufi tou......? Lokacin da za'a tafi wurin shagalin party , yanzun ma Momy ce ta bani kayan da zan saka da mai kwalliya ta kuma tsaida Rabiya wurina dan ita tana fama da jama'a , idan dai mutum ya gitto wurin ya gani zaice masha Allah , wasu daga ahalinsu Dikko basu sanni ba , idan akace wacece Rabiya zatace matar Dikko ce , ko abokan wasa daa suka fara jana da wasa Rabiya cemin tayi kar in koya musu , basu da mutunci. Duk yadda dangin miji zasu soki idan dai baki da power wurin miji kin zama katin ɗaurin aure , Jiddah tana cikin tawagar "yan gidansu , kuma hada Mardiyya Hafsa da Mom inta suna tare da Asma'u amma banga Amisty ba , nidai duk jina nake a takure , Papi kuwa yana liƙe da Nabeela tana fama da hidima amma yaƙi tafiya wurin kowa sai wurinta , duk yadda Momy taso su Ashiru su fita dashi Dikko cewa kar wanda ya ɗauko shi wai su barmin ɗa na can , nidai bansan abinda ya faru ba tsakanin ni da kuma Dikko , amma kuma na fahimci kamar Momy da Dikko akwai abinda yake faruwa. *_Uhum baya da ƙura kenan_* Anyi shagali na wuce ni na rubutashi , kowa ta ƙiyasta yadda hankalinta da tunaninta zai iya ɗauka , ɗiyar gwamna ta auri gwamna , ga gidansu amarya da kuɗi ko ba mulki su dama attajirai ne wanda kullum kuɗin nasu kamar aiko musu su akeyi , caf lallai , neman suna ba banza ba , ga wani ya tafi nema amma ya rasa ranshi bai samo ba , su Dikko tun ba a waye da sanin amfanin a sanka ba sukayi suna kuma aka sansu , sun nemi kuɗi kuma sun samu tun ba'asan amfanin kuɗi ba , rabon da naga Dikko harna manta sai yau a wurin party , yayi wani irin wanka na tashin hankali , yasa wata irin sheɗaniyar shadda akayi mata ɗinki "yar ciki wando da babbar riga , gemun nan yasha gyara sai ɗaukar hankali yake , yana tauna cingom a hankali cikin salo mai ɗaukar hankalin duk wanda ya kalleshi , yayi׳ , ya haɗu iya haɗewa , ya burge , yayi kyau harya gode Allah , wallahi an tara duk irin mutanen da baku tunani wurin shagalin nan , amma na rantse muku da girman Allah babu kamar Dikko a wurin , ya haɗu iya haɗuwa yaci taro , yaba maza azaba kuma yaƙi barinsu su huta , duk wani mai kucakin gayu a wurin ya kama kanshi , yana gaba su Ashiru na biye a bayanshi , yana tafe yana jin kanshi kamar zai tashi duniya.... Su Ashiru na biye dashi ɗauke da wasu irin ƙattin jakukkuna biyu , tunda ya doso wurin yake ɓata rai , mutane sukaci gaba da darewa suna buɗe mishi hanya yana wucewa , daya wuce sai abi bayanshi da kallo. Rabiya dake tsaye kusa dani tajani muka tunkaro hanyar fitowa , wai dan kar in gani , hmmmm , hankalin kowa ya koma wurin Dikko tunda ya shiga inda ake rawa , ya kafe kanshi yaci gaba da ɓara mata kuɗi , makaɗa suka ruɗe , duk wani mawaƙi da aka tara wurin nan ya daina waƙa sunan Dikko kawai yake kira ana mishi kirari , da kuɗin hannunshi ya ƙare sai a miƙa mishi , DK kawai suke kira , dakel aka fiddoshi daga wurin dan bashi da hankali akan ɓarar da kuɗi , idan zai kwana a haka baya gaji kuma bazai daina ba , zaiyi ta zubawa ne baya gajiyawa , haka kuma idan zai bayar yake kyauta maisa ɗimuwa. Wace ce ita.....................??? Nace muku banda labarin Bello ko Dady ko ? Babu ruwansu dani , dan tunda Dikko ya gwagwaɗa musu layi akaina , yace musu ko ciwon kai nayi ko naji an kira sunansu bacci a bacci yayi musu rantsu kashe su zaiyi , tou wannan dalili yasa suka fita sabgata.... Mardiyya Jiddah Amisty Hafsa Saude A ` e Tawagar gidanmu , su tuni na siya musu gida kuma har yanzu basu daina harkar bariki ba , danbe da duk wata harkar iskanci..... Ummu Affan , ita mijinta a saketa , Abbu Afsar wato { Alaji } wanda da Dikko ya tafi dani Babana ya ƙafe ? Wanda ya siya min rigar birthday ? Ya kula da Baba ? Tou har yau ni banda labarinshi , kuma ba abinda ya dameni da sanin halin da yake ciki. Yazeed Wace ce Dikko yayi ma liƙe a wurin party...... ? Mu koma baya...... Gyara zamanshi yayi tare da cewa bara na baku labari , a london na haɗu da wata "yar tasha , tunda ta shigo jirgi kawai tayo wurina ta zauna...... Dikko yace ai ban shanyu ba shi yasa zanyi ma Perpy wata Momyn , Ashe ni ina tunanin Yusra ƙawar Sadiya matarshi data rasu ne , abinda yasa tace ita maza basa burgeta bata samu irin tsarin da take so ba , shi kuma yace kamar wani sakarai haka ya kalleta , Ya ɓoye labarin , haukata ya hana na barshi naji yadda labarin yake na tsaya wani kishin banza da wofi , duk yadda Dikko yake tsaye akaina ? Kuma "yar uwarshi ke tsaye kaina , soyayyar mu da Dikko zakuyi tunanin akwai wata bayan An mata........? Wane sakaci nayi ne ? Me na rageshi dashi ? Meye yarinyar daya kakkaɓe idonshi ya mata liƙe take masa , Dikko baya zina ya akayi wata macen ke riƙeshi waje har yakai 3 dare bai dawomin gida ba ? Jamila Musa gareki....... Jama'a duk wanda ya kalli labarin nan yasan tuni na yankeshi , naso kuyi haƙuri kubi labarin yadda yazo min , ba labarin zamu kalla ba darasin ciki zamu ɗauka , amma sai kuka firgitani , idan kunyi nazari shi labarin rayuwarka yasha banban da labarin shaka tafi , ba ƙirƙira bane ba da zan rubuta muku yadda kuke so ba , kowa da yadda Allah ya rubuto mishi jarabtarshi , kuma babu wanda ya isa ya goge ƙaddar rayuwarshi a yadda tazo , Maganar lalurarshi , yace Ashiru yaji da komai , kuma duk Dady baisan anayi ba , bai faɗa masa ba saboda baya so Dady ya saki matarshi dan kar Momy tayi baƙin jini , meya faru bayan Mustapha yakai Ashiru wurin daya ce nan ne asirin yake ? Ya aka ƙare ne ? Ina Al ' Ameen ? Ya mutu ko yana raye ne ? An dai buga mishi lamba haka Dikko ya faɗa tunda bashi nan baisan abinda ya faru ba , Al ' Ameen daya fita daga inda Dikko ya tsareshi ina ya tafi ? Me yayi bayan ya fita ? Meya faru ? Koma dai miye idan ta amince zakuji ya warke ko yana tare da matsalar ne.............? Duk mai imani yasan akwai jarabta , ni naso na rubuta muku yadda duk zamu ƙaru gaba ɗayanmu , naso kuji yadda Sultana tayi rayuwarta a gidan Dikko dole ta nan zamu warwaro matsalolinmu , mu fahimta inda muke da gyara kuma mu gyara , amma sai kuke cewa bana san Sultana ina bata wahala , bayan bani bace na ɗora mata ba , wasu kuma sai suke zagin Dikko , wasu Sultana , wasu kuma niɗin suke zagi babu gyara babu dalili , daga gyara kayanka ai bai zama sauke mu raba.....? Nidai ina san insan yadda kissa da kisisina da kuma kwarkwasa take , tafiya magana kallo da dai sauransu , mi ke kawo yawan mace²n aure ? Tou idan mai labarin ta yadda zaku jini , salon labarin zai dawo muku da wannan tambarin..... 👇🏻 *KWARATA RETURN...* _{Ƙalu bale gareku matan aure....}_ *SAINA AURI DK* Labarin zaizo muku a kyauta ne kamar dai yadda wannan yazo , bana siyarwa bane ba , Ga dai . *JIDDAH* *MARDIYYA* *HAFSA* *YUSRA* Kowa a cikinsu saita auri Dikko , su suna waje An mata a cikin gida , gadai Yusra tana riƙe Dikko yana kai 3 na dare yana waje , shi baya zina tou dame take riƙeshi wanda har yake tafiya wurinta yabar matarshi ? Me ta iya wanda Sultana ta raga mishi ? Sultana zata yadda kuwa wata ta shigo ? Koma dai miye idan ta amince zaizo a cikin sabon labari mai taken. *KWARATA RETURN* Alhamdulillah jama'a , Jamila tana godiya sosai , sai Allah ya haɗamu a sabon littafina in Allah ya yadda 👇🏻 *ƁOYAYYAR SOYAYYA...* Gasuwa ta musamman gareka *IBRAHIM MUSA QERAU* { Alhajeje } ngode sosai da ƙoƙarin da kayi mana , muna godiya sosai daga kai har mutuminka Mai gida DK , ngode׳ sosai. Godiya gareku "yan uwana , ngode sosai da irin taimakon da kukemin , wurin ganin kun tayani yaɗa wannan labari , ngode sosai da ƙauna Allah ya daɗa zuminci. 👇🏻 *SA'ADATU* {{ AUNTY MUSA }} *HAWWA MUSA* {{ F JIDDAH }} *RABI MUSA* {{ MRS USMAN }}} BISSALAM. MASOYANA 😊 na barku lafiya , ina matuƙar kewarku cike da maraicinku....... *RUƘAYYA MATAWALLE* , ina godiya da kyautar rake...... 😘 26/12/2019 👇🏻 Daga alƙalamin *JAMILA MUSA QERAU...* ngode ׳ Allah ya sake haɗamu da alkairi.