Complete Hausa Novels

A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel

Reading file: A Jininsa Yake Part 3 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 2 of 7

Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100

Ajininsa yake 3-02
Posted by ANaM Dorayi on 08:53 PM, 20-Nov-15
Under: Ajininsa yake
_______ NA ZULAIHAT SANI KAGARA_______<br />
<br />
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....<br />
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473<br />
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
To shi kenan ya wuce." Ya kamo ha6ar ta, yi
dariya,"Yi dariya 'yar gidan Abba!<br />
Ta fado kirjinsa, tana murmushi.<br />
Ya rungume ta, ya runtse ido, wasu kwalla suka
yi masa caa, fadi yake a ransa, "Son ki ya kama
ni Nusaiba, ki yafe min don Allah.". (Hhhhhhh,
Anzo gurin, ammafaaaa...uhm! Maji ma gani)
<br />
<br />
Bai ko san ta kici-kicin tashi ba, sai da ya ji tana
kira,"Abba!<br />
Ka shake ni!<br />
Ya hanzarta sakin ta, yana goge kwallah. Ta bi shi
da kallo,"Wash!<br />
Ka wani matse ni Abba, ai sai in mutu."Ya tashi
ya bata wuri, ya shige bayi ba tare da ya ce
komai ba.<br />
Jim kadan ya fito, ya wanke fuskarsa, kwance ya
same ta, ya matsa gabanta ya ce,"Hirar ta isa
haka, ki yi barci ki huta." Ta amsa da ka, ya
duk'o ya sumbace ta, ya ja mata mayafi. Ya ja
kujera ya zauna, ya sauke numfashi,"Allah ka ga
iya kokarin da na ke yi. Allah ka taimake ni
yarinyar nan ta sami lafiya.<br />
Ta ce,"Ka kwanta mana Abba." Ya ce,"Zan
kwanta, ke dai yi barcin ki." Ta rufe ido.<br />
Tare da gyara kwanciya.<br />
Da asuba ya fito bayi da alwalar sa, ya shimfida
sallaya, yayi sallah. Ya jima yana addu'o'i kafin
ya jiyo motsin ta.<br />
Ya waigo yana kallon ta, ta tashi zaune, tayi mika
tana salati. Ta kalli can, ta kalli nan, bai ce da ita
k'ala ba.<br />
Ta k'ura wa Bebin da ke barci cikin (Net)
ido.<br />
Ta dago kai ta dube shi, suka yi ido 4.<br />
Yayi murmushi, ya ce,"Kin ta shi?<br />
Fashewa tayi da kuka, ya taso da sauri ya zauna
gefen ta."<br />
Nusaiba, ke Nusaiba, za ki fara koke-koken nan
ko?<br />
Tayi shiru tana tunaniin Antin ta.<br />
Hawaye na ta ambaliya.<br />
Ya rik'o ta, ta kwace jikin ta, kuka take tana
k'arawa.<br />
Ya ce a ran sa,"Na shiga 3, yau kuma da kukan ta
tashi." Ya matso, ta matsa. Ya ce,"Ni Nusaiba, ni
ki ke gudu? Bata kalle shi ba, balle ta ce wani
abu. Ya sake matsowa, ta matsa. Ya ce,"Shi
kenan, bari in yi tafiya ta, in tafi ko? Ta amsa eh,
da kai. Ya ce,"Tabd'i! Da magana yau,"Cikin
ransa.Ya rasa yadda zai yi, dole ya sa mata ido,
tayi ta kuka. Can kuma ta tashi ta fito koridon ta
zauna, bisa kujera. Shi ma ya biyo ta nan ya
zauna, yana gadin ta.<br />
Jim kada ya ji kukan Ameer.<br />
Ya mike ya ce da ita,"Ga Ameer can ya tashi, in
kawo shi ya sha? Ta kyale, bai ma ishe ta kallo
ba, ya shige ciki ya dauko shi, ya tsugunna
gabanta,"Yauwa, 'yar gidan Abbanta kenan, dubi
Bebin mu kuka yake yana jin yunwa, dan ba shi
ya sha." Ta dauke kai, tamkar bada ita yake
magana ba.<br />
Abu fa ya gagara, dole ya dauko wa Ameer fida
ya tura masa, yayi ta tsotson ruwa da
glucose.<br />
Kullum karfe 7 nan take masu. Alh.Basheer suna
nan zaune kuwa, sai ga su.<br />
Naseer ne ya fara hango su, ya mike ya nufo
su.<br />
Su ma tsayawa suka yi cak, ganin Nusaiba a
zaune wajen.<br />
"Yaya dai? Alh.Basheer ya tambaye shi, yayin da
Ummi ta kar6i Ameer a hannun sa.<br />
Ya ce,"Ai yau ko Ameer ta k'i ba shi nono.<br />
Kuka kawai take yi,"Ya ce,"Likita ya zo?<br />
Ya ce,"Ka tsaya nan, kai kuma koma gun ta, bari
in nemo Likitan." Ya koma wajen ta.<br />
Alhj ya zaga ya wuce, ita kuwa Ummi ta
lafe.<br />
Jimawa kadan suka dawo da Likita. Abin ya ba
Naseer mamaki daya ga Lkita ya zo, ya tsaya
gabanta bata zage shi ba.<br />
Ya ce,"Nusaiba, tashi mu shiga ciki, mu yi wata
magana." Kai tsaye ta mike ta wuce. Naseer ya
saki baki, shi ma ya taso ya biyo su. Ta zauna
bakin gado, ya jawo kujera ya zauna ya
ce,"Kukan me ki ke yi?<br />
Ta ce,"Antina ta mutu ko?Ya ce,"An gaya miki
bata mutu ba, Antin ki na gida." Ta runtse ido
wasu hawayen suka tsunke mata, ta sa hannu ta
share. Ya ce,"An ce kin ki ba Bebin ki nono,
saboda me? Haka za muyi da ke saboda Allah?
Ta dube shi da kyau ta ce,"Doctor ka yi min wani
taimako don Allah, lambar Abba na zan ba, ka
kira min shi." Idanuwan Naseer suka k'ara yo
waje, ya koma da baya da baya ya fito waje. Shi
kuwa Likita k'ara tsura mata ido, ya ce,"Abban
ki? Ta ce, eh. Ya ce,"Ina zuwa." Ya leka yayi kiran
Alhj da hannu. Ya taso daga inda yake zaune ya
zo. Likita ya kamo hannun sa, ya shigo da shi a
hankali. Kan ta na duke ya ce,"Wannan Abban
naki ki ke nema? Tana yo ido hudu da shi, ta
mike hawayenta suka yawaita, ta ce,"Abba! Wani
tsananin farin ciki ya kama Alhj, dole kwalla suka
cika idon sa, ya ce,"Bebin Abba! Ta rugo da gudu
ta rungume shi. Tuni Ummi ta fado dakin ta hade
su ta rungume, kuka suke saboda murna. Haka
Naseer ke sharar kwalla. Amma ya rasa abinda
zuciyar sa ke sakawa game da wannan al'amari.
Tabbas Nusaiba ta warke, to me zai biyo baya?
Da alamun zai shiga magana, yanayin da ta
nuna. Yayi ta maza ya shigo. Alhj Basheer ya
rungume shi, suna wa juna barka. Likita ya fita,
ya bar su cikin farin ciki da murna maras
misaltuwa.Bayan sun natsa. Ummi ta dubeta,
duk ta rame ta ce,"Sannu Nusaiba, Ubangiji Allah
ya k'ara karewa." Ta ce,"Amin. Ta miko mata
Bebi ta ce,"Kin ga Bebin da aka ciro miki? Ta dan
dube shi, tayi murmushi , ta dauke ido,"Na gan
shi Ummi ta. Kwalla suka taru fal a idonta, ta
kasa shanye su, sai da suka zubo. Abban ya
rungomu kafadunta, ya ce,"Yi hakuri daina kuka,
komai ya wuce Insha-Allah." Ya ce,"Allah ya
yarda Abba. Bari in yi sallah." Ta mike ta wuce
bayi ta jima bisa sallaya, tana yi wa Allah godiya
daya dawo mata da rayuwarta dai-dai. Ta dawo
gefen gado ta zauna kusa da Abban ta. Ya jawo
ta jikin sa, ta dan numfasa ta ce,"Abba lokaci yayi
da zan gaya maka wata magana, ina fatan za ka
gafarce ni." Naseer na jin haka, ya mike ya bar
dakin. Abba ya ce,"Babu komai Bebina, gaya min,
me ke da mun ki? Ummi ta sa masu ido tana
kallo. Ta k'ara gyara zama ta ce,"Na san za ka yi
mamaki, idan na gaya maka cewa tun aure na da
Naseer, babu kwanciyar hankali tsakani na da
shi. Ai kuwa Alh ya sha mamaki, ba shi da kadai
ba har Ummi da take zaune. Ya kara dubanta,
baki sake, ya tambaya, "Saboda me? Ta
ce,"Abinda na fahinta,"Abba, shine ya kar6i aure
na ne kawai don ka cika masa ido, ba zai iya ce
maka a'a ba. Amma a hakakin gaskiya Naseer
baya so na, kuma ya nuna min kiyayya, ba don
Antyna na tsaye ba, ina ganin wuyar da zan sha,
ba 'yar k'arama bace.<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....<br />
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473<br />
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi<br />
<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Shi yasa na ke son ta, domin tayi min komai,
kuma tayi iyakar kokarinta wajen jawo hankalinsa
zuwa gare ni, sai dai haka bata samu ba, saboda
babu sona a zuciyar sa." Ransa ya 6aci kwarai, ya
ce,"Me yasa tuntuni ba ki gaya min ba? Ta
ce,"Saboda kai ne Abba. Ba na son wani tashin
hankali ya shiga tsakanin ku. Kuma ina ganin ai
ya girmama ka ne, tunda ya kasa fitowa fili ya
nuna maka baya so na. Shi yasa na yi ta kokarin
zama da shi shekara daya da rabi, sai da Allah ya
kawo rabon wannan Yaron, sannan ya shiga daki
na. Daga baya na yi tunanin bai kamata mu
zauna muna cutar da juna ba, shi yana jin haushi
na, ni ma ina jin na shi. Sai na same shi a daran
da wannan abin zai faru, na yi masa magana.
Abba cewa yayi idan na k'ure shi, zai 6atacciya,
dole in koma gidan mu, har d'an baya so, ya bar
mana...................!!! Tana shiru. Ummi ta
cafe,"Ina, inda kuma yayi karya kenan. Ai ba mu
kai masa ke da Da ba." Alh.Basheer yayi shiru,
zuciyar sa na tafasa, abin kamar a mafarki yake
ganin sa, domin ko alama bai ta6a mafarkin
Naseer zai ci amanar sa haka ba. Ya dubi Ummi
ya ce,"Har hada mata kayan ta mu tafi." Ta mike
tana fadin,"Ashe ga damuwar da ta kusan hallaka
rayuwarki Nusaiba, kenan. Yayi wa kan sa. Kuma
sai Allah yayi miki sakayya." Nusaiba ta kada
kai,"Ba haka bane Ummi ta, ba laifin sa bane,
kar ki manta soyayya, gamon jini ce, laifin sa 1,
shine daya danki amanar da ba zai iya rikewa
ba."Alhj ya ce,"Duk laifin iyayen sa............ Tayi
saurin katse shi."A'a Abba, iyayen Naseer ba su
da laifi kuma ina mai tabbatar maku yadda ya
yaudare ku, haka ya yaudare su. Ba su san komai
ba a game da zaman mu. Sun rike ni tamkar 'yar
cikin su. Idan na ce ga abinda su kai min, na yi
masu karya, sai Allah ya tambaye ni. Abba, rokon
da zan maka daya ne, don Allah, don son Annabi
kar ka k'ullaci kowa akan maganar nan, ni ce
baya so, to ka dauki 'yar ka. Ai shikenan, an
gama magana." Ya ce,"Haka ne Nusaiba, ki yi
hkr, ni ma na gane kuskure na, ni na jawo miki
duk abinda ya same ki." Ta ce,"Ban ta6a ba ka
laifi ba Abba, ba kuma zan ta6a ba ka ba. Ai kai
alheri ka k'ulla, sai dai ka san a wannan zamanin
ba kowa yake son ayi masa za6in abinda ya
kamace shi a ruywar sa ba. Ya fi son abinda
ra'ayinsa ya ba shi. Ka ga kuskuren da aka samu.
Ina alfari da kai Abba na, kuma ko a yanzu ka
sake za6a min miji. Wallahi zan aure shi. Bai san
lkcn da ya rungume ta, ya fara kwalla ba. Haka
Ummi ke ta share hawaye, tana sawa Nusaiba
albarka. Ta mike ta shiga hada kaya. Hayaniyar
hama'a suka jiwo gaba daya jama'ar Naseer ne.
Zarah ma kayan barci ne ajikin ta, ta dora zani ta
sa hijabi. Suka doro cikin dakin. Zarah na
fadin,"Amarya!Ta zaburo da gudu, "Antina! Suka
rungume juna, sun sha kuka, sai da Umma ta
raba su ita ma, ta rungume ta. Daga nan ta
matsa ta gaida kowa. Su Malam Balarabe, Malam
Umar. Ya gaisa da Sageer da amayar sa. Bayan
an gama gaishe-gaishe. Malam Balarabe yasa aka
yi addu'a, kowa ya shafa. Aanan suka lura babu
Naseer tun shigowar su. Inna ta fara
magana,"Jama'a wai ina dan Inna ne? Malam
Umar ya ce,"Kai wai dama babu Naseer a wajen
nan? Sageer ya amsa,"Ai kuwa baya wajen nan,
tunda muka zo? Malam Balarabe ya ce,"Ah to ina
ya je? Ya fadi, yana kallon Alh.Basheer. Ya
ce,"Gaskiya ban san inda ya je ba. Kuma dama
ina son ganin ka, idan ba za ka damu ba." Ya
ce,"Bismillah Alhj, ba damuwa." Suka fito waje,
yayin da Zarah da Nusaiba ke like da juna suna
maida yadda abubuwa suka faru. Alh.Basheer ya
kebe da M.Balarabe, ya kwashe bayanin da
Nusaiba tayi masa kaf, ya gaya masa. Tun da ya
soma magana, gaba daya jijiyoyin jikin Malam
Balarane suka tsinke, jiri ya fara dibar sa. Allah
yasa a zaune suke, da babu abinda zai hana shi
faduwa. Tabbas ya san Naseer baya son auran
nan, aka yi shi, amma ko alama bai ta6a sanin
rashin mutunci da wulakancin da ya rinka
aikatawa ba. Ya jima kafin ya ce,"Alhj wannan
magana ta ban kunya, kuma Wallahi tallahi ban
san komai a game da zancan ba. Nusaiba bata
nuna mana ba, balle ta furta da bakin ta. Don
girman Allah ka yi hakuri Alhj. Ya ce,"Ai magana
ta k'are, tunda baya son ta, ni ina son abata
kuma zan tafi da ita, ba tare da 6ata lkc ba.
Amma D'a, ban sako mata shi cikin gara ba, sbd
haka nan za ta aje shi ko ya kashe ko ya bar shi
da rai, duk ya rage nasa. A karshe, ka gaya masa
na gode. Allah ya saka da alkhairi. Kan
M.Balarane yayi gingirinn! Kunya kamar ya nutse
kasa. Idanuwan sa suka cika da kwalla, ya rasa
me zai ce wa Alhj? Kawai sai ya juya ya dawo
dakin, gaban kowa ya daga murya ya
ce,"Nusaiba, don me za ki min haka???Akan me
za ki zauna sama da shekaru 2 cikin wulakanci da
bak'in ciki, amma muna tare, ki kasa gaya min?
Ba ki min adalci ba Nusaiba, domin da kin gaya
min da tuni na yanke hukunci, sai dai ya nemi
wani uban, ba ni ba! Kowa yayi tsuru-tsuru.
Nusaiba kuwa tuni ta fara kuka. Ya matsa gadabn
Ummi ya tsugunna." Hajiya ki yi wa girman Allah,
ki yi hakuri. D'a ne ka haife shi ba ka haifi halin
sa ba. Ko alama ban san halin da suke ciki da
matar sa ba. Ga mahaifiyar sa nan a zaune, ko
ita da ke zama tare da su munafikin Yaron nan
bai ta6a barin ta gane wani abu ba, balle ni da
ban zama cikin gida. Maganar tafiya da Nusaiba
kuwa kun yi dai-dai, domin ko ni ne hakan zan
yi. Saboda haka kowa yayi shaida. Ni Balarabe na
tsame hannu na akan komai daya shafi Naseer,
duk abinda ya ga dama yayi rayuwa
ce................ Ya fashe da kuka, jikin kowa yayi
sanyi, matan da ke wajen ma tuni suka soma
taya shi, musamman Umma da ta ji abin kamar
saukar aradu. Sageer ma waje yayi kirjin sa na
bugawa, ga ranar da yake jin tsoron zuwanta,
kullum yana gaya wa Naseer. Amma kunnuwansa
iskar duniya ta dode masa su. M.Umar da Alhj
suka riko M.Balarabe,"Ka yi shiru haka,"Malam
Balarabe, kar zuciya ya kwashe ka, ka yi masa
baki." Ya dube su ya ce,"Ni Naseer yayi wa tijara
haka, Babu komai, rayuwa ce!Ya dubi Umma ya
ce gaba,"Ke dauko masa D'ansa mu tafi, ki kai
masa kayansa, idan ya ga dama ya jefa shi bola!
Malam Umar ya ce,"A' ba'a yi haka bane, duk ku
zauna a sasanta magana. Ai in rai ya 6aci, hankali
ke nemo shi. Alhj ka yi hakuri, mu zauna da
Naseer mu ji ta bakin sa, don girman Allah kar ku
yanke hukunci kai tsaye haka." Alhj ya kada
kai,"Ban k'i taka ba. Amma Naseer ya riga ya
k'are magana, sai dai hukuncin daya yanke ne
ban yarda da shi ba, d'a kan ba na mu bane, na
shi ne. Don haka anan za'a bar shi. Iya magana
kenan." Malam Balarabe ya ce,"Magana tayi dai-
dai Alhj, ku bar masa shi, ya san uwar da za ta
shayar masa D'an shi. Ki dauko shi mu tafi, na
gaya miki, idan kuma ki na nan, ni na wuce! Yayi
waje. Malam Umar ya bi shi. Umma ta dubi
Ummi, ta ce,"Don girman Allah Hajiya kar ku yi
wa Yaron nan haka, shi bai san komai ba, ku
tausaya masa." Tayi shiru, ta rasa me za ta ce?
Yadda Alhj ya fusato, babu mai sa shi dukan
D'an nan. Haka Zarah ta rike Nusaiba,"Amarya
kar ki ta fi, don Allah ki taimake ni. Idan ki ka
tafi da wa zan zauna? Suka k'ara fashewa da
kuka. Ita dai Fa'iza ba baki, sai ido. Bata fahimce
komai ba, take ta faman kuka. Alhj ya fice ya bar
su nan, suna ta faman magiya. Jim kadan ya
dawo tare da Likita. Shi dai ya ga ana ta koke-
koke, a zaton sa duk na murna ne, yayi abbuwan
da zai yi, ya gama ya ba su sallama tare da
takardar magunguna da za ta ci gaba da sha na
tsawon kwana 7.Alhj da kansa ya rink'a dibar
kaya yana kaiwa cikin mota, har ya kwashe su
duka. Ya kamo hannun Nusaiba, ya wuce da ita.
Ummi ta biyo bayan su, suka bar Umma da jariri
bisa gado, yana ta faman barci. Ta k'ara fasa
kuka. Inna ta kamota tana rarrashi. Haka Zarah
ke durk'ushe, hannu 2 bisa kai. <br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....<br />
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473<br />
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi<br />
<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Daga inda Naseer ke 6oye, yana hango su Alhj
suka zo suka wuce a moTa. Yasa hannu ya goge
hawayen da ke kuncinsa. Jimawa kadan ya hangi
su Umma. Inna na dauke da Ameer, suka shiga
motar da ta kawo su. Direba ya ja suka bar
asibitin. Wasu hawayen suka sake zubo masa,
yayi kamar ya hadiyi zuciya ya mutu. Ya nufi inda
ya aje motar sa, ya shiga haka ya dawo gida,
baya gani wuri sosai. Ya rasa inda zai je, sai yayi
fakin kofar shago, ya shiga ya sallami su Abbas
ya ce duk su tafi gida. Ya kulle kansa ciki, ya rasa
abinda ke masa dadi a duniya. Cikin gidansu
kuwa kamar anyi mutuwa, shiru ba ka jin motsin
kowa. Jim kadan Zarah ta fito da jakar kayan ta,
ta lallabo zuwa sasan su Umma. Ta leko a
hankali, ta ga babu kowa, ta cire takalmanta ta
wuce sadaf-sadaf kamar 6arauniya. Tayi waje kan
ta tsaye tayi gidan su. Inna ta zura mata ido,
kafin ta ce,"Ke kuma fa? Ta shige uwar daki da
gudu. Inna ta biyota,"Na ce ke kuma fa? Kin
shige da gudu. Menene na ce? Ta ce,"Allah Inna
ni ma ba zan zauna ba. Haba ai wulakancin yayi
yawa, ko alama yayana baya jin magana. Ta
balbaleta da fada,"Laifin waye? Ai duk ku na
sane, aka rasa wacce za ta gaya wa manya, don
ayi maganin abin, sai yanzu da zance ya lalace,
za ki ce Naseer ne baya jin magana? Maza dauko
jakar nan, ki koma inda ki ka fito, tun kafin
Babanki ya k'araso gidan nan, ya sameki." Ta
6arke da kuka, tana fadin,"Ba inda za ni Inna,
idan har na koma gidan nan, to yayana ya dawo
da Nusaiba. Kuma ku matsa min ku gani. Wallahi
tafiya ta zan yi." Inna tasa mata ido tallafe da
baki. "Ki ka ce me? Lallai wuyanki ya isa yanka,
to zan ji idan kke ki ka haife mu." Ta yi zamanta
bakin gado, har Inna ta gama babatun ta, ta
fice." Na rantse da Allah ba zan koma ba, ya je
ya ci kan sa a gidan, tunda shi ba'a gaya masa
ya ji." Koda Malam Umar ya dawo, babu yadda
ya iya yi da ita, ya gama fadansa da barazanarsa
ko gezau zuciyar Zarah bata yi ba, kuma ta
rantse ta maya, muddin suka bari ta bar nan, ba
za su sake ganin ta ba. Shi yasa da ta dauko jaka
ta fito. Inna ta dauko muciya ta kora ta daki, ta
ce,"Koma daki marasa kunya, idan Naseer din ya
zo ya dauke ki! Ta maida jaka ta yi zamanta cikin
dacin rai da takaici tare da tausayin Nusaiba da
karamin goyonta.<br />
Sageer ma da ke zaune a dakinsa, babu abinda
ya fi damun sa irin dan karamin yaron da aka
aje. Alhalin bai san komai ba. Fa'iza ta
ce,"Yakamata ku taimaka wa yaron nan a maida
shi wajen Maman shi,"Wallahi shi ne abin
tausayi, ba ka ji yadda na ke ji ba, kamar inyi
tsuntsu kai shi wajen ta." Ya ce,"Shirun nan da ki
ka ga nayi. Ameer kawai na ke tunani." Yayi
hucin zafi, ya dauko waya daga aljihu ya nemo
lambar Naseer. Ta dan jima tana bugawa kafin ya
dauka, ya ce,"Ka na ina ne? Murya dishe ya
amsa,"Shago." "To ina zuwa." Ya kashe waya, ya
dubi Fa'iza,"Wai yana shago, bari in je in same
shi." Ta ce,"To ba za ka dan ci komai ba? Ya kada
kai, bari dai in je in dawo. Ya fice, tana fadin a
dawo lafiya. Ya kwankwasa kofar shagon, ya zo
ya bude, suka koma ciki tare. Daga kallon Naseer
kawai. Sageer ya gane yayi nadama, gaba daya
ya jeme ya fita hayya cin sa. Ya dube shi a
sanyaye ya ce,"Ka ga irin abubuwan da na ke
gaya maka ko? Yanzu ina ribar wannan abu?
Kullum ina gaya maka yi wa iyaye biyayya ibada
ce, duk kuma mai yin sa ba zai ta6a ganin 6acin
rai ba. Amma Naseer na ka ji, ni ban san abinda
ke damun ka ba. Dan yaro jariri an ajiye maka
shi, ina amfanin sa? Iyayen ka na ta kuka saboda
kai, wacce irin masifa ce wannan? Ka farka daga
bacci Naseer, kai ba yaro ba ne."Ya dube shi
kwalla suka zubo ya ce,"Ban san abinda zan ce
ba Sageer, domin ni kaina na san mai laifi ne,
saboda haka duk hukuncin da aka yanke min,
yayi dai-dai. Sai dai babu wanda ya san cewa na
dade da yin nadama, sannan in na ce ba son
Nusaiba yanzu, na yiwa raina karya. Shi ya sa na
dage ba dare ba rana wajen kula da ita tare da
rokon Allah ya bata lafiya, don in samu in nemi
gafarar ta, na kuma nuna mata iya so da kaunar
da na ke mata yanzu. Allah da ikonsa sai ta sami
sauki, hankalinta ya dawo jikin ta, a lokacin da
iyayen ta ke wajen, sannan bata 6ata lokaci ba,
ta zayyane masu komai. Ka yarda da ni Sageer?
Ka taimake ni, domin ni yanzu ban san yadda zan
yi ba." Sageer yayi shiru, yana kada kai<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....<br />
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473<br />
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi<br />
<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Tabbas ya yarda da maganganun Naseer, saboda
yana daya cikin masu mmkin yadda Naseer ya
rinka kula tare da ririta Nusaiba, sai dai a lokacin
ya dauka saboda halin da ta shiga ne, kuma bata
son kowa ya kusance ta, sai shi. Ya nisa kafin ya
ce,"Yanzu tinkarar Abban, tashin hankali ne ba
karami ba, kuma dole ne aje a same shi, tunda
shine jigon komai. Abin yi shine, ka taso mu je
wajen sa, ayi ta ta kare ko kashe mu zai yi." Ya
kada kai,"Gaskiya Sageer ba zan iya ba.ka je kai
kadai tukuna, ni na fi kowa sanin halin Abba." Ya
ce,"Shi ke nan. Za ka jira ni a anan din ne? Je ka
dawo ina jira. Ungo key din mota don ka yi sauri.
Ya kar6a ya fito a sukwane, ya fada mota, yayi
gidan su Naseer. Yayi sallama falon Abba, a
lokacin Umma tana goya Ameer ta fito ta siyo
masa madarar jarirai, bayan ta nemi Zarah ta
rasa a cikin gidan, don bar mata ajiyar yaron
kafin ta dawo. Shi yasa zuciyan Abba ke kara
tafarfasa, ya sani babu makawa ita ma tafiyar ta
ta yi. Da kyar ya amsa sallamar Sageer. Ya shigo
a darare, ya nemi gefe ya makure, ya ce,"Sannu
Abba." Ya ce,"Me aka yi Sageer? Ya ce,"Abba
Naseer ne................Ya dakatar da shi da
hannun sa kafin ya ce,"Tashi ka tafi! Sannan idan
ka je, ka gaya masa ita ma wacce yake son ta tafi
abinta, saboda haka ya zo ya kwashe kayan sa,
ta bar min gidana in huta." Ya tashi ya durk'usa
Abba................Ya runtse idanuwansa,"Sageer ina
ganin mutuncinka, don Allah, don son Annabi ka
tashi ka tafi. In dai akan maganar abokinka ne,
na riga na datse magana, na yi rantsuwa Naseer
ba zai sake sani kaffara ba. Saboda haka ka je ka
gaya masa, shi 'yantacce ne, kar ya dami kan sa.
Tashi, kanzil ban ka kara fadi ba, idan har ni ina
isa in gaya maka. Idan kuma ban isa ba, to
kacigaba da zama. Sageer ya shiga 3, Abba ya
daddaure shi, ga magana bakin sa babu damar
fadi, yana ji, yana gani, ya tashi ya fice. Yayi
tsaye jikin mota ya rasa tudun dafawa. Ga wata
sabuwa, kuma ita ma Zarah ta yi gaba. Duk da
dai yana ganin na ta mai sauke ni, amma ba
dadi ace ita ma tana gidan su.Ya fi minti 5r a
tsaye, sannan ya bude mota zai shiga. Ya hango
Umma tafe. Ya tar6e yana mata sannu da Zuwa.
Ta amsa za ta wuce cikin gida, ya ce,"Umma ku
taimaki ni Naseer na cikin wani hali, komai za iya
faruwa da shi. Ta ce,"Shine me? Sai aka ce
karshen Umma ya zo? Ya ce,"Ba haka ba ne
Umma. Wallahi Naseer yayi nadama, tun ranar
da ta sami kan ta cikin wannan yanayin, kuma ba
shi da wani buri daya wuce idan ta ji sauki, ya
bata hkr akan abinda yayi mata. Sai kuma aka
sami akasi, komai ya yamutse. Ta yi dan
murmushin takaici ta ce,"Yaro man kaza. To
yanzu da ka zo nan ka na ta dogon bayani, akwai
Nusaiba a nan ne? Tana fa Kaduna, a gaban Ka
Babanta ya dauke ta. Ba sai ya je can ba, ya roke
ta. Menene abin zafi? Ya durk'usa bisa guiwa, ya
ce,"Ku yi wa girman Allah Umma ku yafe masa,
ke ma kin san duk abinda ki ka fadi, ba zai yuwa
ba. Sai da goyon bayan ku." Yana sa aya Abba na
tsayawa kofar zauran, bai ce wa Umma komai
ba, ta wuce cikin gida. Shi ma ya bi bayan ta.
Sageer ya sauke numfashi, ya tashi ya fito ya
tafi. <br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....<br />
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473<br />
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi<br />
<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Yana shiga shagon zama kawai yayi, ganin haka
Naseer din ma yayi shiru, ya san babu nasara.
Sun dau minti goma a haka, kafin Sageer ya
ce,"Wai Zara ma ta tafi gidan su."Ya dube shi da
sauri." Me na yimata ita kuma? Kashe ni suke so
su yi ko? Shi kenan." Ya goge kwalla. Wayar sa ta
hau bugawa, da kyar ya dauka. Yakubu ne ke
kiran sa. Ya rasa ta yadda zai yi ya dauka. Ya
dubi Sageer, ya ce,"Zo mu je gidan Yakubu." Ya
tashi suka tafi. Ya maida masa bayanin komai.
Yakubu yayi masa fada kamar zai ari baki, shi
kansa ba karamar kunya ya ji ba lokacin da Alhj
ya kira wayarsa, yana gaya masa Naseer ya ci
amanarsa. Duk da haka yayi masa alkawarin
shiga maganar, sai inda karfin sa ya kare. Shi
kuwa Naseer B ana maganar, yana kallon kowa a
dage, zuciyar sa gwanin haske, har yana addu'ar
kada Allah yasa su shirya. Amma bisa fuskar sa,
ya fi kowa nuna damuwa kamar yayi kuka. Daga
gidan Yakubu, wajen Zarah suka iso, misalin
karfe 1 na rana. Sun shigo gidan. Inna na kwashe
abinci cikin kula. Ta daga ido ta dube su, tana
amsa sallamar su. Gaban ta ya yanke ya fadi,
ganin yadda Naseer yayi wanu duhu lokaci guda.
Ta ce,"Dan Inna! An gaishe ka da aiki. Ku shiga
gani nan zuwa." Ya wuce simi-simi. Sageer ya bi
bayan sa, suna zaune. Inna ta gama abinda take
yi a kicin, ta bi su dakin. Zarah ta leko daga bayi
ta ga Inna, ta shige sai ta sadado ta aje buta, ta
suri hijabin Inna dake shanye bisa igiya ta yi waje
ta bar unguwar. "Sannu dan Inna, ka sha aiki
Wallahi, ya gajiya? , Ya sunkuyar da kai Sageer ya
ce,"Inna kuskure ne, kin kuma san ajizanci irin na
Dan-adam. Amma a yau ya gane, har ya
tuba........ Ta katse shi, tuban mazuru? Sau nawa
Naseer ke cewa ya tuba a gidan na ma kawai,
wanda na sani? Ai ba zan iya fadi ba. Yanzu wa
gari ya waya? Babu abinda ba mu gaya maka ba
D'an Inna, tun kafin ayi auran nan. Bayan anyi
kuma, ba mu fasa ba, sai dai in kafar ka bata
shigo da kai gidan nan ba, amma ba ka ji. A
fuska lafiya lau ka ke, halin ne kawai ka kasa
gyara shi, su yi dai-dai da fuskar ka. Me yasa? A
yanzu wa ka ke ganin zai iya tunkar Alhj? Babu
abinda za mu iya gaya masa, ya yarda, saboda
ka riga ka rushe ginin tun ranar zane. Naseer ya
ce,"To Inna shi kenan, haka za'a sa ido, auran ya
kare kenan? Ta ce, "Eh mana, ta riga ta gayawa
Babanta ba ka son ta, wa ka ke zaton zai je ya
ce, karya ne? Ya ce,"Gaskiya Inna ban yarda ba,
na san ana zuwa biko Inna. Sai dai in ba za ki je
min ba ne kawai<br />
Ta yi dan murmushin dole ta ce,"Dan Inna
manya, ga laifi, ga saurin tuba. To shi kenan, ka
bari Baban na ku ya dawo, za mu san yadda za'a
yi." Ya numfasa ya ce,"Wai ita ma Zarah don ta
kara min hawan jini shine ta bar gida ko? Ina
take, sai ta ci dan banzan duka yau, in ni sa'an
ta ne, za ta gaya min." Dariya suke da Inna da
Sageer, kafin Inna ta ce,"Yanzu ta shiga bayi, za
ta yi alwala ta yi sallah." "Ina nan ina jiran ta ta
fito,." Inna ta mike,"Bari in kawo maku abinci
Sageer. To Inna. Sageer ya amsa. Ta fice,"Sageer
ya ce, "Na ciro maka wayar Rediyon can ne?, Me
zan yi da ita? Dukan mana harka mance? Tsaki
yayi ya dauke kai. Inna ta shigo da abinci ta
ce,"Ka fa ci. Sageer ka matsa ma sa ya ci. Ya
ce,"Ai zai ci Inna." Ta yi waje ta koma daki. Shiru-
shiru Zarah ta ki fitowa daga bayi. Inna ta fito da
wannan mamakin, tana tambayar kanta,"Ita
wannan zaman me take yi a bayi?" Tana sa aya,
ta aje ido bisa buta a gefe. Ta leko dakin ta
ce,"An gama dukan?" To ai ban ji kuka ba, bata
daku ba kenan." Suna dariya ya ce,"Ai bata shigo
ba Inna.." Ta gintse fara'a ya ce,"Ban gane ba?
Ga shi ta aje butar a waje. Ta juya ta fito tana
kwala mata kira, yayin da dukkansu suka aje
cokula suka fito. Kamar wasa, babu Zarah acikin
gidan. Mamaki ya ishi Inna. Ta kama baki, tana
kallon igiya babu hijabin da ta shanya. Sageer ya
ce,"Wai ita Zarah da gaske take yi? Inna tayi
shiru abin ya girmi shekarun ta. Naseer ya
numfasa ya ce,"Inna ki gaya mata, idan ta ji ina
asibiti kar ta sake ta zo guna. Zo mu je Sageer.
Ya yi waje. Sageer ya ce,"Inna ki ce Allah ya bata
hakuri. Sai anjima." Da kyar ta iya amsawa,"Allah
ya ba mu alkhairi." Shi ma ya wuce. Inna ta ja
kujera ta zauna, yau na ga zamani ni A'isha. Kiri-
kiri yarinya ta ban kunya? Suna tafe a mota
Sageer, ya ce,"Yanzu ina muka nufa? Ya
ce,"Gidan za ni, duk ayi ta ta kare, idan ma
yankana ni za su yi, su yanka. Ba shi kenan ba?
Idan kowa yayi min, ai bai kamata Zarah ta yi
min ba. Duk saboda wa na shiga wannan halin?
Ba saboda sonta ba ne? Duk ba ta ga hakan ba."
Ya furta. Sageer yayi shiru domin ya lura abokin
sa ya zare gaba daya, kar ya tofa wani abu, ya
kara masa zafi. Ya ci uban birki a kofar gidan, ya
fito yayi cikib gida, bai ko saurari Sageer ba. Sai
dai yana shigowa ciki ya tsinkayi Ameer na ta
tsala kuka. Nan da nan ya yi turus, guiwa sa ta
kwa6e, a salu6e yai sallama falon. Umma na
kokarin goya Ameer a lkcn Abba kuwa na zaune
gefe iya wuya yake. Kuma yana ji da kowa, duk
wanda ya kuskura yi masa wata magana akan
Naseer. Yana shigowa. Abba ya mike ya debi
takalman sa ya bar gidan. Naseer ya bi shi da
kallo, ya kasa cewa da shi komai, har Umma ta
gama goyon, ta sa hannu ta dauke gwangwanin
(Prisso-cream) din da ta siyo ta dora bisa firij, ta
dauki fidar ta yi waje. Ita ma ya bi ta da kallo,
sannan ya bi bayanta. Tana famfo tana wanke
fidar da soso da omo. Ya bi ta, ya tsaya a gefen
ta ya sanyaya murya,"Umma!Ji ta yi tamkar ya
watsa mata wuta. Ranta ya ci gaba da k'una
kamar ta rufe shi da dukan fitar hankali. Ya
durk'usa ya mika hannayen sa gaba gare ta.
Idanuwansa dauke da kwalla. "Umma, ki yi wa
girman Allah ki amsa min. Umma ki dube ni ki
saurari rokona. Na yi laifi Umma, amma tuni na
gane kuskure na, ku ba ni dama ta karshe
Umma. Da yardar Allah ba zan sake saba maku
ba, Umma ki taimake ni." Ta gama dauraye fida,
ta yarfe ruwan, ta juya ta koma daki tana
daddaure su yadda suke. Naseer ya nemi wuri
nan ya zanau dirshan! Sageer ya matso zai masa
magana, yayi sauri ya riga shi." Je ka gidan abin
ka Sageer. Na gode." Ya yi dan jim, yana kallon
sa,"Ka ta fi na ce, babu komai, sai mun hadu."
Ya numfasa ya ce,"Shi kenan, Allah shi kyauta."
Ya juya ya fice, ba tare da Naseer ya sake cewa
wani abu ba. Nan yayi ta zama har ya tuno, bai
yi sallah ba. Yayi alwala a nan famfon, ya wucce
sasan su, yayi Sallah a falo ya ci gaba da zama
nan bisa sallaya. Babu abinda zuciyarsa bata saka
masa ba. Zarah kuwa bata dowa ba, sai bayan
sallar la'asar, ba shakkar komai. Ta yi sallama ta
shigi ta wuce Inna a tsakar gida ta shigo daki.
Inna ta tafa hannu ta ce,"Da izinin wa ki ka bar
gidan nan? Ina kuma ki ka je? Kai tsaye ta
amsa,"Inna ai na gaya maku ba zan koma ba. Kin
zaci wasa na ke yi ko? Ta ce,"To ba kuwa zama a
gidan nan ba, bari baban na ki ya shigo. Na lura
so ki ke ki kawowa mutane raini. Ta juya ya bar
dakin. Zarah ta matsa inda kulolin abinci ke aje,
ta buda ta zuba ta hau ci. Karfe 5 M.Umar ya
shigo gida, Inna ta feshe shi. Ya jinjina kai ya
ce,"Wai Zarah da na sani ki ke fadi? Ta ce,"Ka na
wasi-wasi kenan? Shiga tana nan a daki." Tunda
ya baro dakinsa yake balbala masifa har cikin
dakin."Ki hada kayan ki, ki koma inda ki ka fito!
Ta ki motsi, M.Umar har da barazara duka,
amma ko alama Zarah bata motsa ba, sai sharar
kwalla take yi. M.Umar ya cika da al'ajabi, yana
haki, ya koma dakin sa. Inna ta yi zuru tana
kallon sabon salo. Fadi take cikin ranta,"Zarah ta
kangare." Haka kowa ya kwana a wannan dare.
Babu barcin kirki.<br />
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....<br />
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473<br />
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi<br />
<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Washe gari bayan sallar asuba. Nusaiba ke zaune
bisa gado, tunani bisa tunani. Tun jiya take cikin
wannan yanayin. Musamman da ga Abbanta ba
shi cikin sukuni kuma tun isowarsu gida, babu
inda ya sake fita. Tashin hankalinta ya k'ara
tsananta, tun daga lkcn da ta ga nononta ya cika,
har ya fara tsiyayewa a banza. Bakin takaicin
dake cinta kenan, a halin yanzu bisa gado, ta
rasa inda za ta tsoma ran ta, ta ji sanyi sbd
tunanin dan kyakkyawan dan ta. Ta tabbata yana
can yana kukan neman nono, ga shi nan yana
zubewa a iska. Farkewa ta yi da kuka, sbd
tausayin rayuwar da Naseer ya je fasu ita fa dan
ta,. Ji ta yi an riko ta. Muryar Umminta ke
fadin,"Nusaiba! Daina kuka, ki yi hkr. Ta fado
jikin Ummi ta rungume ta. Ummi ta shafa kanta
ta ce,"Ki yi shiru na ce. Allah ne ya kaddaro miki
wannan al'amari. Yanzu dago fuskar ki ki ji. Ta
dago, Ummi ta sa hannu ta share mata hawaye,
kafin ta ce,"Abinda na ke so da ke Nusaiba, ki yi
hakuri mu je a dauko yaron nan.Bawan Allah ne
shi, bai da laifin komai. Sannan shayar da shi da
za ki yi, shine yake sanya shakuwar uwa da
danta, soyayya tare da jin kai.Ki sani Nusaiba
Ubangiji ne kadai ya san dubun ladan da uwa
take samu tun daga daukan ciki, haihuwa, raino
tare da bada tarbiya, ga 'ya'yan da Allah ya
bata,kar ki bari wannan gara6asar ta wuce ki
Nusaiba. Ki dauko dan ki ya shaku da ke, ya san
cewa ke ce mahaifiyar sa.<br />
Ta yadda zai ji kan ki, a cikin zuciyar sa, idan
Allah ya raya shi. Na yiwa Abban ki magana, na
rarrashe shi, na kuma yi nasara, ya amince,
yanzu yardar ki na zo nema, domin ya ce shi ba
zai matsa miki ba, duk abinda ki ka za6a shi
za'ayi.<br />
Shi kuma Naseer din muna nan muna jiran sa, ya
kawo miki takardar ki.<br />
Yanzu me ki ka ce?<br />
Ta goge kwallan da suka dararo mata, ta ce,"Ki je
ki dauko shi Ummi, babu komai."<br />
Ta tallafo fuskarta ta ce,"Yayi kyau. Allah yayi
miki albarka.<br />
Amma ki tashi ki shirya Direba zai kai mu, don ki
kintso kayan ku a natsa.<br />
Tashi ki daina kuka, ba na son ki na damuwa, kin
kuma san Abbanki hankalin sa ba zai kwanta
ba.<br />
Ta goge hawayenta sarai,. Umma ta kama ta ta
riko, ta raka ta hanyar bayi, sannan ta fice ita
ma, don shiryawa.<br />
Abban ke kwance a falon sama bisa kujera, shi
kadai yake kallon silin yana lissafon halayyar Dan-
adam mai abin mamaki.<br />
Nusaiba ta shigo cikin shirin tafiya.<br />
Kamar mai ciwo yake kwance, bai motsa ba har
ta zo gun sa, yana kallon ta.<br />
Ta tsugunna ta kwanto kanta jikinsa, ta yi
shiru.<br />
Ya daka kanta ya ce,"Bebina, ki je ki dauko dan
ki, ki shayar da shi.<br />
Allah zai ba ki lada, kin ji?Ta amsa da kai. Ya
ce,"Mike ku tafi, na ga Ummin ki ta gama
shiryawa.<br />
Allah ya kiyaye hanya." Ta ce,"Amin Abba na." Ta
mike ta wuce ya bi ta da kalllo, ta kai kofa, ta
waigo suka hada ido, yayi dan murmushi yana
mata (bye-bye) da hannu.<br />
Ita ma ta yi masa, sannan ta sauka, lkcn karfe
7:30am. Ummi ta matsa mata ta dan ci kayan
karin safe.<br />
Karfe 8 Direba ya dauko su, suka damk'i
hanya.<br />
Karfe 8 din dai-dai. Naseer ya shigo falon,
Umma, don gaishe su ko ba za su amsa masa
ba.<br />
Umman kadai ke falon,<br />
tana ta faman gyangyadi.<br />
Da alama Ameer ya sami barci, domin cikin dare
yana ta jin kukan sa.<br />
Bata kalle shi ba, ya durk'usa gaban ta, ya
ce,"Umma ina kwana?<br />
Kamar za ta kyale shi, sai wata zuciya ta ce,
amsa.<br />
Bata kalle shi ba ta ce, lafiya.<br />
Farin ciki ya lullube shi, ya ce,"Na gode
Umma.."<br />
Ta kyale shi.<br />
Yayi dan jim yana kallonta, kafin ya ce,"Umma
ina Abba?<br />
A fusace ta dube shi, ta yi masa tsawa,"Ga shi
nan a baya na a goye!<br />
Tabatacce maras kunya.<br />
Ka sake zuwa ka tambaye ni, ina Abba ya ke, sai
na ci mutuncin ka!<br />
Yasa hannu ya dafa guiwoyinta ya ce,"Yi hakuRi
Ummana, ba zan sake ba.Dama Zarah ce ta ce
ba za ta dawo ba, sai Nusaiba ta dawo, shine
nace ko za ki sa baki ta yi hkr ta dawo kafin a
shawo kan Alhj?<br />
Kai tsaye ta dube shi, tsakar ido ta ce,"Ban
zuwa." Kar mu yi haka dake Ummana. Wallahi na
yi nadamar abinda ya faru, ku sa ke ba ni dama
ku gani zan rike Nusaiba iya rayuwata.<br />
Ta dube shi a dage ta ce,"Bakin alkami ya riga ya
bushe maka Naseer, domin jiya da daddare su
M.Umar da M.Lawar sun zo. Amma Abbanka ka
ya rantse, ya masu, babu ruwan sa a cikin
maganar ka.<br />
Haka ni ma bai lamunce min ba.<br />
Saboda haka ka makara, dabara kuma ta rage wa
mai shiga rijiya. Ina fatan ka gamsu. Yayi zuru
kafin, ya numfasa ya dube ta ido sun kawo
kwalla.<br />
"Shi kenan Umma, na gode. Abinda na ke son ki
rokin min Abba, shine, don Allah yayi hkr, idan
na gaishe shi ya rinka amsawa. Ni zan fita, ga
wannan koda Ameer yana bukatar wani abu." Ya
ciro dubu 2, ya aje bisa hannun kujera ya tashi
ya fice.<br />
~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~­
~~~~~~~~~~------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....<br />
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473<br />
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi<br />
<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Karfe 9 ta gota kadan Jeep din su Hajiya Zulai ta
yi fakin kofar gidan su Naseer. Suka fito Ummi na
rike da hannun Nusaiba. Ummi ta yi sallama
tsakar gida. Umma ta amsa daga falo, a lkcn
kuwa ta kammala shirya Ameer tsaf!Yana ta
tashin kamshin hoda. Bata dauki murya sosai ba,
don haka ta ce,"Maraba, ku shigo mana." Ummi
ta yaye labule. Umma ta mike baki har
kunne,"Hajiya!<br />
Ah!<br />
Nusaiba!<br />
Sannun ku da zuwa."<br />
Suka zauna a kujera Umma ta mikawa Ummi
Ameer, ta karbe shi. Sai ta wuce firj za ta dauko
kayan sha.<br />
"Dama kin bar shi, kin san safiya ce." Duk da
haka ta kawo da Jus din kananan kwali da kufuna
2.<br />
Bayan sun gaisa, Umma ta tambayi Alhj? Sai
Ummi ta ci gaba da cewa,"Ba wani abu ya kawo
mu ba.<br />
Ameer mu ka zo tafiya da shi, ya zauna wajen
uwar sa ta shayar da shi. Ko dama 6acin rai ne
yasa aka aje shi."<br />
Kwalla suka cika idanuwan Umma ta ce,"Gaskiya
ne kuwa, na ji dadi, domin a gaba daya wannan
al'amari Ameer shine abin tausayi.<br />
Shi kuma wancan sakaran, ai kyale shi ya gasu,
duk da cewar ya ce yayi nadama." Ummi ta yi
dan murmushi ta ce,"Ai ba'a soyayya dole, mu
ma mun san haka shi yasa Alhj ya ce a gaya
masa, tana jiran takardarta, ko zuwa jibi. Insha-
Allah za mu turo mota akwashe kayan ta a dauki
motar ta."<br />
Umma ta goge kwalla ta ce,"Ba laifi, ki yi hkr
Nusaiba kin ji? Allah ya amfana miki dan ki. Ta
dan sadda kai ta ce,"Ba komai Umma.<br />
Idan kuma na yi miki wani laifi, ki yafe min." Ta
girgiza kai,"Baba abinda ki ka yi min Nusaiba,
Allah yayi miki albarka."<br />
Ta ce,"Amin." Ummi ta ce,"To bari mu je, za ta
debi wasu kayan kafin a zo kwashewa." Umma ta
ce,"To bari in kawo maku wani makullin, ya fita
da na hannun sa."Nusaiba ta ce,"Ina Antina
Umma?<br />
Ta ce,"Ita ma ta tafi."<br />
Suka dubi juna, kafin Ummi ta tambaya,"Saboda
me?------------------------------------------------------------------------------------------------
<br />
Sabon shafinmu na face book zai fara aiki daga
labarinmu na gaba,ku tallaffamana domin
habakashi....<br />
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C7370123473<br />
Akalla muna son Like daga mutum 20 kafin fara
gudanar dashi<br />
<br />
------------------------------------------------------------------------------------------------

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.