Romantic Hausa Novels

Amfanin Soyayya Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Amfanin_Soyayya_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 2 of 4

Part din Mall
Wow suka ce suna shiga kasan duk parlour ne wamda girman sa ba amagana sai babban kitchen
tun kafin su hau suke cewa hawa nabiyu yafi na daya kyu duk da fentin iri dayane amma tsarin da bambaci

saida suka duba hawa na dayan shima yayi ba lefi d'akuna 5 ne aciki sai kitchen da parlour 2 iri daya dana Sahal

Suka hau na biyun ai bude baki sukayi yayi mugun haduwa har yafi part din iyayen su kyu gashi ba wabi tarkacen d'akuna daki 2 kacal sai kitchen duk parlour yacinye saboda girman sa dan falo ne iya ganin ka haka dakunan ma manya ne

"Kai ga kicin sai kace a turai har yafi kitchen din aunty abeed kyu ai nan zaki zafa sis."
inji Nafi
murmurshi Ruwa tayi da tatuno warning din Mall amma dayake itama kwanan kantace tace" Eh ."

Ayya tawarke ras sun dawo Hamrah ta koma adamawa dan shirye biki

Mall yayi mugun jin haushin yanda Ruwaida ta zabi part din su bayan HALIMA ya ginawa amma idan yatuna tarkon da ya dana mata sai yayi murmurshi

wai wacece HALIMA

Halima Musa y'ar gidan wani drive ne Musa wanda a gidan su Ruwaida da Ayya yake aiki na hutoro

Ayya ce tayi ta damun Ruwaida akan taje duba su Cabaliya dama ita suka barwa digan Ruwaida ita kadai ta tafi dan su Nafi suna makaranta

Tanayin horn megadi ya lek'o jiki na rawa dayaga Ruwaida dan mugun tsoronta sukeji

Shijaf har kasa tafito ta rufe kofan motan tana sanye da farin glass tayi kyu dan Ruwaida komai tayi kyu yake mata
Ita tafara gaida megadin da sauran Ma aikatan mutane 3 awajen harda Musa baban Halima

"Baba garba ina kwana ku."

Abin yabawa ma aikatan gidan mamaki
Ka rasowa tayi inda suke

Tasake cewa "Aunty Ayya tace a tambaye ku kowa yaga alert ko."?

Musa yace "Eh Hajiya mun gani har da Karin kudi aka mana wannan watan."

Murmurshi tayi tace "to kuyi Addua Allah yakara daukaka Aunty Ayya yakare tada shirrin makiyan ta."

Malam Tanimu me wanki yace " wannan kudi da ake ta bamu bama aikin komai anya halak din mu muke ci kuwa.?

Ruwaida tace
"Ai ita ta baku halak din kune
kuma ba kuna yiwa cabaliya aiki ba."?

"wallashi ranki yadade bawani aiki agidan nan yanzu"
inji Musa

Murmurshi tayi tace to shikenan Baba MUSA dama Aunty Ayya tace zata yi sharawa daku idan kun yarda zakuyi aiki a meduguri zata baku aiki a companyn ta amma sati me zuwa zata zo sai tazabi wanda zata dauka."

Godiya suka mata tashige ciki

Cabaliya tana ganin ta tace "wanake gani kamar uwar dakina Ruwaidatu."

bayan sun gaisa Cabali tace "ai bansan kinzo ba yajiki."

"da sauki nazo shikaran jiya gobe ne ma zan tare."

"wai ni uwar dakina acikin yaran walwala waye babban soja zaiyi aure kwanan nanne?

Rawa tace "Ismail ne."

Cabal tace "ai yar gidan Musa direban kune Halima
Shiko yaron me yake gani zai daukawa kansa jaraba ai sai da naje har gidan dan nabawa iyayen naku labari wacece HALIMA folisawan get din suka hanani shiga nayi nayi sun hana ai sam Halima bata dace da irin wannan gidan ba."

Ruwaida tace "to ai gwara da suka hana ki irin kune masu kai suka a bata sunnah ko?

"ba haka bane uwar dakina kinsan de bazan yiwa Musa bakin ciki ba kituna dan dakinane ni nakawo muku shi gidan nan ma amma hakan bazai bari na bari acutar da gidan kuba dan kunmin rana

Halima auren ta 3 duk ka mazan suna rabuwa da itane akan halinta na bin maza da mata ita

Daga nan tafara bata labari

Halima itace babba a yaran Musa tun tana budurwa tayi ciki aka zubar mata sannan akayi auren ta anyi aurenta da wata 5 ta haifu mijin yace ba nasa bane tazo gida tareni danta Sadik
Tasake aure Mijin ya kamata da wani yaro me shiga gidan dama ya kamata da wata k'awar ta suna madigo amma aka basa hakuri ya hakura sai da ya kama ta da namiji yasaketa tafito da yaro daya a nan ma

Duk cikin goron dutse waye baisan Halee kyan bariki a gani a gida ba

Yanzu haka bata jima da yaye yarda da ta haifa shegiya ba

Samari da matasa

Idan sun ganta kirari suke mata suce Halee kyan bariki

sai tace a gansu a gida suna yawo

Kin san ma anan a gani a gidan da take cewa."

Ruwaida ta girgiza kai

Cabal tace "to aga yaran shegu suke nufi idan suka ce kyun bariki sai tace a gani a gida

Yaranta 4 daya ne kawai dan sunnah

Danaji wannan sai da naje har gidan dan na tambaye ta wai garin yaya tasamu wannan Mijin me tsada
Kinsan gidan Musa ba bakona bane ko matan sa sunyi fada ni yake kaiwa namusu sa Santo sannan ina musu alheri sosai nasan kinsan tsakanin mu

Goron dutse
Gidan Musa
Halima murmurshi tayi tace "Mama Cabal zaki ce tayaya nasa meshi Allah yabani shi wata rana rashin kudi ya matsoni kona abinci banida shi kawai gidan yayar mamar mu ya fadomin a rai tunda gidan masu kudine nayi wanka nasa dogon shijaf dan nasan mijin ta malamine idan naje da shiga irin wanda nada nakeyi a nan ba barina zatayi ba

naje tsallaka titin yankaba zan shiga cikin sauna dan tunda ga bakin asbiti a daidai yace kudina ya kare a kafa natako na gaji ban kula da hanya ba na wuce kawai sai jinayi mota ya turani gefe Allah yasa bai takani ba yayi parking ya fito wani farin saurayi kamar balarabe yake ta bani hakuri yace nazo ya kaini asbiti

nace "ah ah Wllh banji ciwo ba wannan dan gurjewan ma faduwan da nayi ne zan iya tafiya."

"ok amma dakin bari na Kai ki ".

"ah ah bakomai"
nace dashi

"OK kibani numbar Mijin ki ko wani matsalan zai biyo baya nima ganawa yabude motan sa yabani katin sa."

nace "aini banida waya agidan mu ba a barin budurwa ta rike waya amma me yasa kamin kallon me miji."?

dago kansa yayi yafara kallona
Yace da gaske kike ke budurwa ce yanayin shigan kine yasa na zaci matar aure ce ke."

Murmurshi nayi nace "ai haka yan GIda mu suke

"To zan iya sauke ki a gidan ku dan naga gidan dan Wllh najima ina neman irinki."

"Gidan yana nan sauna idan kace gidan malam Zakar me azama kowa yasani."

"to shikenan amma wannan kam baki isa kice bazaki Karba ba".

yame kamin rafan dubu dubu guda 3 dubu dari ukku

naso namusa saboda na tabbatar masa ni salahace amma yamasa na karba mukayi sallama

Ina zuwa gidan aunty Kubra nazube a cinyar ta na tsara mata komai da bukatata na zama a gidan ta har nasamu na auri Ismail dan nasan idan a goron dutse ne bazai yuwu ba

Ta amince saboda tana son na shiryu Mijin tama ya abince zai zauna a matsayin Babana kinga tsakanin sauna da goron dutse ba mezuwa yamin muna furci yanzu haka nazo gidan uwar dakina Sa a zata rakani asbiti a min d'inki nakoma budurwa dan ba maganin da zan sha ya mayarni muburwa a yanda nake a fafaren nan sai de a dinkani."

"To kinji wacece HALIMA zaki so ta shiga Zurian ku."

Ruwaida ta numfasa tace kishiyata yar gidan driver na

Afili kuma tace Cabal Dan Allah kar ki hana auren nan kibari tayi wata kila tsilar shiryuwan tane kiduba kemafa kinyi bariki muma munyi ina tausayawa duk matar da take bariki kinga Halima mijina zata aura amma bazan iya sawa a fasa auren ta ba duk tsananin son da nakewa yamall kullum sai yamin abinda yaka mata ace na tsane shi amma sai naji son sa yana kara nunkuwa acikin zuciyata amma nafi karfin zuciyata bana nunawa kowa haryanzu ina son sa banda Ayya da Hamrah ba wanda yasan nayi murnan auren nan duk da ina son nemawa Affan mafita

Dan Allah karki tona asirin Halima kibari yacika gidan sada yan barikin."

"Shikenan uwar dakina yanzu gobe ne tariyan kibani number da zan sameki kinsan wadan nan folisawan naku sai anyi kira an tabbatar zasu bari a shiga."

Ruwaida tace "yi zamanki Cabal ban gaiyaceki ba da yawan magananki nan ai gobe kikace je gidan sai kowa yasan wacece HALIMA."

har wajen mota Cabaliya ta raka ta sai data fita takoma ciki
Ruwaida ta danyi nisa da gidan motan ta yatsaya cak
Tana dubawa taga danjan mai ne yakama dukan sitiyari tayi dan bata san ya zatayi ba gaba waya a hannun ta Ummi ta kwace
gashi duk titin anguwan ansanta shiyasa ta fito da mota me bakin glees
Aiko tana fitowa samarin anguwa suka dau ihu
KALA KALA ABASU KALA ABASU KALA RUWA RUWA

Duk idan sunzo wucewa sai sun mata wannan kirarin danma fuskan a murtuke yake batsa tsayawa

Wani tasamu da tasanshi ta aikashi yasiyo mata mai

tana tsaye wani mota yawuce ta motan tabi da kallin dan kamar tasan motan

Mall ne da abokin sa Mujashid acikin motan "Mujashi yace "dakata Mall wata nagani kamar Sis dinka Kharajina."

Mall da yaga Ruwaida sarai
murmurshi yayi yace "baka kalleta daidai."

Mujashid dama shine yake jan motan baya yayi dai dai sanda wasu samari suka zo wucewa suna kara yiwa Ruwaida kirari

Mall yace Kai kaji kirarin tama ina ga wannan wata me siyar da hajace fa kai ko dama dan hannune kasamu".

Mujashid yayi murmurshi yace" Wllh kuwa naga alama amma wannan macce .me tsada haka gakuma shigan mutumci."

"bakaji kirarin da yara suke mata ba kai de ka taya kozaka dace."

Mujashid yace "haka za ayi dan Wllh na kyasa."

Yabude kofan yafita

Sai da yabari ya karasa inda Ruwaida take
Dakarfi Mall yadaga murya yanda Ruwaida zataji

yace kafin kayi amfani da ita kaje a Amata Tast na HIV dan Wllh idan ka kaso bazan baka kanwata Nafisa ba."

Aiko taji dan saida suka hada ido da Ruwaida

Mujashid
Ya karasa inda take

Shikuma Mall yafito yazaga yashiga bazaunin direba yaja motan da karfi

Ruwaida ta Kalli Mujashid tace ba damuwa na amince inde Mall yaturoka wajenan

Har dare Mall shiru baiga zuwan Ruwaida ba kuma gashi abokin sa idan yakira baya dauka

Daurewa yayi yace Ummi wai ina Ruwaida tajene."

Ummi tace "Wllh fadan da mukeyi da Abida kenan tun dazu tafita wai zataje duba ma aikatan wancen gidan nasu nace ta dawo dawuri za amata kunshi amma shiru ba labarin ta gashi ba waya a hannun ta kuma agidan nan ba wanda yasan gidan Sai Sahal shikuma yana adamawa yanzu na tura masa Test yaturo min address din gidan baiyi Ripley ba ina gama bai duba ba kasan halin Sahal
Me kunshin har tagaji duk anyiwa kowa ita ake jira ni tsorona ma kar ta gudu dan bason auren take ba Wllh ina gudun aikin danasani......

Mall bai karasa jin maganan Ummi ba yafito yana cikaba da kiran Mujashid

sai asannan mujashid ya dauka cikin fara a yace Mall kana damuna fa kana rage minjin dadi....

cikin wani irin murya Mall yace "Mujad kana nufin wanan karuwa ta yarda dakai kuna tare kenan."?

Mujashid Yace "sosai amma kadena kiranta karuwa sunan ta Ruwaida kaga banzo ba ko yarinyar ce mezafi ce ta hadu karshe Ashe a Africa ana samun irin su."

"da gaske kake ta amince da kai.?

Mujad yace "sosai gamu ma a w w Hotel amma yanz.....

Awani irin tsawace Mall yace whattt!!!!!!? tare da jefar da wayan yazari key din motan sa kamar zai taka megadi yayi han yan hotel din daddy sa W2

*Tofa banji comment dinku sosai ba a pg 19 shiyasa ban kawo muku wannan dawuri ba na gaya muku yawan comment yawan typing*

*Wane mataki mall zai dauka*

*Da gaske ne Ruwaida tayi abinda mujashid yace*

*Ya Mall zanyi da halee kyan bariki a gani a gida*

*B JATTKO**AMFANIN SOYAYYA*
aure

*NA*

*BATUL ADAM JATTKO*
ASHBAT

Kainuwa writers association 🤝🏻

*21*

ikon Allah ne yakai Mall w2 yana yin parking ko kofan motan bai tsaya rufewa ba ya shigo afusace cikin reception
din gai dashi ma aikatan suka shiga yi cikin girmawa

yace "manager duba min list wane room Mujashid yakama."

"OK sir na wane rana zan duba."

"na yau Kamar misalin 12pm ."

girgiza kansa yayi yace "Sir ai tun 6 na karbi duty amma oga Mujahid bai shigo ba sai de ko kane meshi awaya k......

Mall awani irin tsawace ya katse manager
" stupid! kamin aikin da nasaka kawai."

jiki na rawa manager da sauran ma aikatan wajen suka shiga duba list din yau sun duba yafi soba dadi

da kansa ya fuskanci lalle babu fuuu yafita kamar gogowa
Ajiyan zuciya suka sauke daya yace "to yau kuma waya tabo oga Mall ne?
dayan yace "kaide Ciko yi shiru suna lek'en sa har yashike mota sannan su kayi hamdala suka Fara gulmansu

Mall Yana shiga mota yasake kiran Mujashid amma abin mamaki sai yaji wayan yana Ringing a seat din baya
Afusace yajiyo sai kawai yaga Mujashid akance sheme sheme da earpiece akunnen sa yana gyad'a kai idon sa arufe

Hannu Mall yasa zai shako wuyan mujashid mujad da dama yayi ready yayi wuf yaja baya yatura kofa da kafa ya duro waje sai da yagan shi a waje ya fashe da dariya harda rike ciki

Mall kamar zai bude yafito kuma yaga kar yayi abinda zai zubar da kiman sa a inda yake da kima kifa kansa yayi a sitiyari yana wani irin huci idon sa yamasa nauyi

Mujahid lekowa yayi ta Window yace "major mena maka kake son yiwa mommy da my Nafi asara na."?

Mall da yadago kansa sai da mujahid yaja baya dan yanda idon Mall yayi wani irin ja har yabawa mujashid tausayi dan bai taba ganin sa cikin wannan yanayin ba zagawa yayi yashiga motan

Dafa kafadan Mall da yasake zama abin tausayi yayi
"haba my friend yaushe muka fara boyewa juna tsirin mu ne kake shirin boye nin to ni da kake gani dani aka daura auren ka da Aisha Ummi da kanta ta kirani take gayanin nazo a daura amma kai ma baka sani ba kar nagaya maka kaga na rigaka sanin wacece Ruwaida awajen ka dan Sahal ya gayamin komai tsakanin kada Ruwaida ko dama nasanta duk da ban cika zama a kasan ba ina cikin hotoro na kasa sanin wacece Ruwaida
Ai dazu ganin yanda kabi inda take da kallo kuma yanayin fuskan ya sauya alokaci guda ne yasa na Kalli inda kake kallo ashe itace har kana cewa naje na sameta amma maganan bai kai zuciba dan nasan waye Mall katuna tundaga nursery tare muka fara har kan degree mu na farko kafin kowa yaraba kafa nasan waye kai dama Sahal yace min kanayiwa Ruwaida mugun so kuma gashi nan nima na goda na'

Bari kaji
Yanda mukayi da Ruwaida ina zuwa wajen nace "ah ah amaryar mu lafiya kike tsaye anan duk da munyi lefi mu abokai bamu gabatar da kanmu a wajenki ba saboda yanayi yanda abin yazo mana Amma ama na afuwa ina zuwa da wannan ranan?

Ruwaida kallona tayi rai abace tace "da abin da abokin ka yafada da abin da kai kazo dashi da banbanci. "

Dariya mujahid yayi yace "ashe kinjishi daga nan ya Kwashe yanda sukayi da Mall ya gaya mata

Kuka ta fashe dashi tace "bansan wane irin k'i yamall yake min ba yanzu koni ba matar sa bace a matsayina na yar uwa agareshi Ya kamata yamin haka koda acikin karuwancin nake ballema na shiryu."

"gaskiya bai kamata ba amma ni nasan yana sonki insha Allah wata ran komai zai wuce ai soyayya me tsada kukeyi duk soyayyar da aka masa wannan jayayyar tafi k'argo dan haka ina son duk abin da zai miki ki zuba masa ido wataran kina da riba

Yanzu ina son kibani hadin Kai mushirya masa wani plan din da zamu gane yana sonkin
Kinsan
Hassana kanwar Sahal ko."?

Ruwaida tace Aunty Sana yanzu ma agida na barta ai."

"to matar yayana ce dan Haha zan kirata tazo gidanta
zan kai ki gidan ki zauna sai dare ki koma shima Mall zai dauka muna tare

Yaron da ta aika siyan mai yana kawowa na karbi motan na kaita gidan an mata kunshi da gyaran jiki ka godewa Allah Mall kana da sa a ayaruwa dace da irin su Ruwaida AI.......

"dalla dakata malam kaji a baki na nace maka ina son tane har kaje kake gaya mata ai ita tasan bana sonta ko zuwan da kaga nayi da gigicewan da nayi dan saboda Kai ne bana son ka hada baki da kazamin bakin ta guntun cancer dako kyan gani babu ba hakori har 2 amma badan nadamu da ita ba."

Mujashid yace "to nagode dan reni hankari."

Hassana ce takira Ummi tace "Ummi kar ki nemi Ruwaida fa wai hayaniyane bata so kanta yana mata ciwo tana gidana ita tasa aka kirani ashe amma nasa an mata komai matar da ta mata aikin har tafi wanda tayi na gida iyawa sai anjima zan kawota."

"to yanzu Hassan tana gidan naki tunda baki kirani ba sai daren nan ga Mijin tama yana tambayanta yanzu yafita a nan."

"afuwa Ummin mu ita tace idan akasan inda taken yanzu su Farida zasu zo su dameta."

"to shikenan sai kunzo."

*Borno*

Ayya kam sai hamdala dan kowai yayi mata daida a rayuwanta sosai dangin mijinta suke sonta da tattalinta hatta kishiyar ta kwantar da kai tayi suna zaune lafiya dama Maryam kishiyar ta bata da matsala

Balle shi oga da ko ita Ayya bazata ce ga adadin sonda Grema yake mata ba

Kwace take akan cinyar sa rokon sa take akan yabarta ta tafi adamawa saboda shiye shiyen bikin Hamrah

"to wai yanzun me zaki jeyine? bikin da sai on 29
saura fa 2weeks ."

marairaicewa tayi tace "to ai muna wasu shirye shiye ne akwai abin da zan tafi mata dashi da kuma Hajja Batul zata mata gyaran jiki na sati biyu amma ni ko kwana dayane kabari naje nayi ga Barrat ta dameni zan wuce kaduna na kaita wajen Abdallah sai kuma inson samu ne nawuce Kano naga my Ruwa."

"caf kaji duk wannan yawon sai kace shanshani."
Shafo cikinta yayi yace "ban sani ba ko inada ajiya anan a wahalan minda baby kide aika Hajja Batul din namiki alkawarin zakije auren Hamrah sai kuhadu akanon Barrat kuma zan sa akaita wajen Abdallah dan Abban Ruwaida yakirani jiya ma wai dan Allah akawowa Abdallah Barrat."

*Kano*

washe gari Ruwaida tasha kuka dan sai asannan akace mata Abban ta har yanzu bai shuce ba akan abinda ta masa ba

cikin kuka tace
"Ummi dan Allah kar ku kai ni dakin aure mahaifina yana fushi dani."

Ummi wayan ta tadauko takira Abban yana dauka ta gaya masa komai tare da bashi hakuri

"shikenan Hjy Ruwaiya amma badan gidan aure zata ba da bazan sauko dawuri ba Amma bata wayan."

Ummi ta meka mata

Kuka Ruwaida ta fashe dashi
"Abba kayafe min Wllh tun alokacin dama bada niyar gaske na........

"stop AISHA na yafe miki nakuma samiki albarka kuma cikin satinnan za muzo nida Hajja da malama dan malama ta matsa tana son ganin ki."

"Abba malama kuma?

"Eh."
Yace

Haushi ne yasa Ruwaida cewa "to Abba nagode."
takashe wayan ta mekawa Ummi wayanta

Nasiha sosai su Ummi su kayiwa Ruwaida

Abida takama hanuta suka rakata adaidai get Ruwaida ta tsaya t
cek abin ya bawa sau Abida mamaki amma sai suka ji kamar addua take

Ruwaida sai da tayi dogon addua ta amfaci sunan Allah ta daga kafar dama ta shiga bakin ta dauke da addua har zuwa bedroom dinsu kokarin zaunar da ita Abida tayi amma taki zama

"Aunty abeed zan dan shiga bathroom."

Dariya su Kharajina suka ai dole cikin ki ya kad'a wannan k'iran na yamall

Aunty Hassan tace "bama son rashin kunya fa Nafi ku fice mana."

Farida tace caf "ai muna nan sai munga kokof."

Abida tace "a kofe kude inde yamall ne

Ruwaida alwala tayi tafito tace "aunty abeed ina sallahn da daddy yabani dama yana hannu Ashur kanin Farida har Qur ani da shijab ta karba ta tada ikkama tayi rakk'a 2 tare dogon addua har su abida suka gaji sukace mude zamu tafi kar wannan mugun ya taddamu dan dare yayi

Nafi tace "wai ita y'ar iska dan mubar mata gidan tane tawani share mutane ta dauki karatun munafurci to Wllh gobe da safe anan zanyi break."

Haka suka karaci mata tsiya su

Suna fita Ruwaida ta fara jin wani mugun ciwon mara wanda na period ne dan tana shan wahala gashi dama doctor ya hanata shan kowane magani acewar sa zai iya mata wani illan tunda shekarun ta yakai na aure tayi shine samun saukin ta saide tayi ta han ruwa mezafi dan samun sauki da wuri

fitowa tayi general Parlour na kasa dan ko zata samu ruwa dan kitchen din saman taga fanfon yaki kuma bawani alaman ruwa aduk fridge din

Tana fitowa ta zube a kan kujera tana dafe da maranta

Mall badan yanda Ummi tasa ido akan saba ba abin da zaisa yatare part din nan batare da Haliman saba

tana kwacen yazo ya wuce ta yashiga

Bayan yafito a toilet ne yagama shirin komai nasa yaja wayan sa zai tura wani sako ta email duk akan ashirin auren sane

Message yake ta shiko masa ta whatsapp sai da yagama abinda yakeyi

yashiga WhatsApp din bakon number yagani
Shiga yayi yaci garo da abinda ya firgitashi

Kamar haka harda video

_Mall me Sa a ko nace me sakaci ka ari mace me kyu bayan hausawa sunce mace me fasale ko tai aure bata dan gana ba kai ko ita ta dangana mu Mosoyan ta basu dangana_

Sai ya danna video din
Kansa ne yafara zuyawa amma yana cigaba da kallon yanda Ruwaida da Affan suke romance na mugun watsewa kuma a zir din su suke adaidai sanda Ruwaida ta kamo gaban Affan zata sa abaki

wani irin k'ara Mall yasa tare da mekewa kawai tsintan kansa yayi a parlour inda Ruwaidan take kwance bai karasa ba ya jefa mata wayan sai da yadaki goshinta ita ma k'aran tasa dan ko bata duba ba tasan ya fasa mata goshi

"kidauki wayan kigayawa kwarton ki ni Ismail Wllh na wuce kuntun su dan haka yadena bawa kansa wahala wajen turomin k'azanta cikin waya idan ganinki yake so yayi yane ma muku inda zaku na haduwa bani da damuwa."

yana gama fadan haka ya haye sama

zubewa yayi a gado yana wani irin numfashi abin tausayi

Ahankali cikin ma wuyacin hali ya furta
```Ummi idan kin rasani dalilin Ruwaida ne ai kinga irinta ga abinda yasa na hakura da ita ya Allah ka d'auke rayuwan baiwar ka AISHA dan zuciyar bawanka Ismail ta samu sauki ko kadauke nawa na huta```

Ruwaida saida taji rad'adin goshin yadan lafa ta dauki wayan da har lokacin videon ne yakeyi

"walahaula walakuwata illahbillah!."

Affan dama duk zamanda muke da kai daukana kake kana adanawa nashiga ukku ni AISHA zinah nadena ka baka dena bina ba duk da haka ba zinah nayi gaba daya ba
Asttafullah kuka take sosai tunanin bari takira mommy sa ta gaya mata abinda Affan yayi baikyu ta ba tayi dan tana da number ta Akanta

Sallama mommy tayi tace
"dawa nake tare."

cikin rawan murya Ruwaida tace "mommy nice."

"Ruwaida yawwa ai dama nemanki muke ido rufe saboda munfara aikin mu amma sai da hadin kanki zamu samu nasara da gaggawa yanzu haka ga son nan munturawa Ismail sak'o muna jiran Ripley ne ke kuma akin da zan baki sai mun hadu gaba da gaba dan haka ki san yanda zakiyi ki samu ki fito cikin kwanakin nan biyu
kuma dan Allah kar ki yarda ko hannunki Ismail ya taba dan ga son nan tunda yamma yakasa cin komai wai idan Ismail ya kusanceki bazai iya rabuwa dake ba
gashi ma Affan dinki dan lallasheshi......

"Hello my love. "

"Affan kana tunani abinda kamin shine soyayya yanzu kam banyi nadaman rasa kaba sai ma godewa Allah dan ku ba alkairi bane agareni."

"what Affan ne fa my love menayi miki."

"ashe Affan duk zaman mu dakai muna furtata kake kana daukana a video dan wata ran katuzarta rayuwa ta ko kamar yanda kayi yau."

Affan yace
"ada banyi da niyan wani abu ba kawai idan ina wajen aiki nayi missing naki idan na kunna nagani sai nasamu nusuwa yanzu haka na kunna ina kallo ina kuka mommy da tagani tace ai wannan ma makamine na turawa Mall kinji yanda akayi."

"Affan Wllh sonda mommy take maka zai kaiku ga halaka kuna rayuwa sai kace na ya hudawa nik...

Kar ban wayan mommy tayi tace "Ruwaida idan na fashimce ki kamar bazaki bamu hadin kaiba ko to Wllh idan kina shirin haka ma kiyi.......

"dakata mommy dama da hadin bakin ki Affan yamin haka na cire Affan a sawun masoyana masoyi bazai min abin da yamin ba dake da danki kufita min cikin rayuwa."

Tana gama fadan haka ta kashe wayan

Tashiga video din tayi detele din komai

Tsaban bacin rai ciwon ma rasashi tayi ajiye masa wayan tayi ta haye sama dan yanzu ita ma kunyan Mall takeji zata guji duk hanyan da zai hadasu

Bayan sati 2

Ruwaida da Mall tunda abin yafaru ba suga juna ba gashi har gobe dauren auren sa da Halima Sahal da Hamrah

abangaren Affan shida mommyn sa sai abinda yakaru suna shiri sosai dan ma sun rasa number Mall dan wanda suka turo na farko bai sake kallon inda wayan yake ba

Ruwaida tana babban gidan ana ta harka kannen ta sunzo ga Barrat har da Hajja

Khalifa ne yashigo
Ruwaida tace "ya khall yaushe kazo."?

"Lill momy ai tunsan da kika k'ule a gidan ki kika manta mu."

Dariya Ruwaida tayi tace "sorry yakhall Wllh ba waya a hannuna kuma lefin su Nafi ne ai kullum muna tare."

ganin wawulon Ruwaida yasa Khalifa ya dafa kansa alamun yayi mantuwa
yace "kahs kinga ko nakusa na manta doctor kin fa yamin waya yace zuwa yanzu za a iya miki aikin hakorin dan haka asa ranan komawa asa miki."

"yawwa yakall kamar kasan Wllh amatse nake ko bakina bana son budewa gaba daya."

Dariya Abubakar k'anin Sahal yayi
yace "kaci uwar gida wato kina tsoron amaryar mu tazo tana renaki da wawulon baki ko."

hararan sa Farida tayi tace "ai Wllh yabull ko duk hakorin ta rasa Wllh wuce nan wannan me bakin fuskan tarena ta."

Abubakar yace "ban da ky'ashi ai naganta a colander tas take."

Kharajina tace "caf ai Wllh kos korimace Wllh Laraba me aikin Mama tafita kilin gata daf da kas'a kamar tukuban tsire."

dariya akayi taci dan walwala family akwai fashimtan juna

Washe gari da misalin 9 na safe aka
daura auren

Ismail Muhammad Muhammad

Da HALIMA

Saboda za aje Adanawa adauro da Hamrah da Sahal

Ruwaida tace Ummi dan Allah nima naje Adamwan idan andaure sai muzo tare."

Ummi tace "wannan mijin ki zaki tambaya shiyake da iko."

Shiru Ruwaidan tayi ita ko ina zatabi hanyan da zai hada ta da Mall ma

Umman Ruwaida tace "to yaya abinda ita ma Hamrah nan zata zo me nata na zuwa muma manya ai godiya da karban amarya ne zai kai mu."

Kowa baki ya fude yake kallon yanda Ayya Hamrah Ruwaida suka dau makeup
dan wanda yamusu mekeup din ya kware sosai dan hatta kaman su iri daya ya maida kodan komai nasu iri daya ba ban bancin takanas a *India* Abida tayi hayan sa dan yayi musu mekeup din

Haka suma Nafisa Kharajina Farida shigan su iri daya gasu dama duk farare kyawawa suma

Sai aunty hassana da anty Fati da Aunty Abida suma shigan irin daya
Duk material ne

Sai yaran gidan dana dangin suma kowa duk anko iri daya maza da matan su

Ihu su Kharajina suka sa asanda suka ga su Ruwaida Wow sis
KALA KALA KALA ABASU KALA

Abida tace "gaskiya kam yau suka amsa sunan su Aisha ukku masu baiwan kyu Na BALAI
EN UKKU
yawar daya yar uwa hakori."

Fati tace " kar ki bude baki dan ma nasan ki da kamewa."

Hall din ba lefi yahadu Halima ana zare ido dan anzo wajen dako amafarki ba asan za azo ba ita ma balefi tayi kyu dan Mall ya kashe kudi sosai wajen daukan masu yimata makeup
Mall zaune da amarya sa
Sahal ko har yanzu zaman jiran isowan su yake

Wayan sa yazare yakira Abida yace "ke Abeed bana son wasting time ."

Hamrah da Ruwaida
Awaje suka barsu

suka fara shiga DJ din Abida tayiwa magana akunne aiko ya sako wani lafiyeyen kida wanda baitin wak'an Rara ne yake rerawa adaidai sanda Ruwaida ta shigo Hall din tare da wasu indiyawan yan mata daga bayan ta suna zuba mata wasu yan kakkun flavour masu kamshi

Asannan sautin wakan yayi k'arfi kunsan de rara ga kadan daga cikin wak'an

_kuzo mu wak-e amarya ango yaji dadi kauna idan tayi nisa riba aure_

wak'an ya bak'an tawa Mall rai dan sunan sa dana Ruwaida kawai aka sako ba asa na Halima ba amma yasan abida ce

Daga nan Ruwaida takoma tazauna acikin yan uwan ta dan bayan da satayi ta hau inda ango da amarya suke dan ba a tsara zaman da ita ba

Kamar yanda Ruwaida ta shigo haka Hamrah ma ita ma nata wak'an yayi amma Ali jita ne yabudo

Duk marokan da sukayiwa Hamrah da Ruwaida kirari Ayya kyutan kujeran makka ko key din mota take badawa ai take waje Ya kacame da aka san cewa Ayya ce
A K D
kuma Ruwaida yar gidan me kwano ce

Halima da yan k'awayen ta yan kallo suka zama Mall da yaga duk shirin na kankan tar masa sahibar sane hannun ta yakama suka fita

"Ismail da ma Ruwaida ce matar ka yan ukku balai da baba yake aiki agid......

dasauri ta rike bakinta dan takusa kwafsawa

Mall yace "ki karasa mana baban ki yake aikin zagin su agida kullum ko ai inaga bawani malami da bai zagesu ba."

Sai asannan ta samu bakin magana tace "Eh Wllh amma mamaki na ya akayi tazama yar gidan me kwano kuma meyasa kuke kama da ita?

"zan gaya miki kinga yanzu abokina yana kirana bari na gansa shiga mota yabude mata

yana barin wajen k'awarta Baraka da take boye tafito tace "ke Haly anya baki cusu kan ki inda yafi kar finki ba ki duba wadan nan larabawan ki shigo cikin su Wllh in badan abin namiji ba ko a yar aikin bazai kai ki gidan sa ma me kamar wannan matar de kaga yar me kwano da yafi shugaban k'asa kudi."

"Baraka kede bari wllh babban Matsalan ma kin san baban mu agidan su yake aiki drive din sune dan ma bawanda yasan ni y'arsa ce ni wani kyansu bai dameni ba tunda shi yagani yace yana sona ai yasan da ita ni ya
ce yana sona."

"ummmm nede ina jiye miki kishi da abasu kala

Adaren aka kawo Amarya Halima

Mall sai rawan jiki yake dak'yar yabari sukayi sallahn godiya

Amma me yana cikin shafata hannun sa yakarasa cikin bra din ta memakon yaji dum kamar yanda yake sammani sai yaji Abu luguf a kance gashi bawani tudu duk da shidin bak'on abin ne yayi mamaki dan ayanda yake kallon Boob's na Mace yana ji ajikin sa idan an taba za aji wani yanayi dan kallo da ido ma yana jefashi cikin wani hali idan yagan su kyam a tsayen tunba na Ruwaida

Amma ya share yaci gaba yaje kan me gaba daya wani ihu Halima tasa tana yarfa hannu sai gumi tage tana ihu ganin haka yasauka amma sai me jinin da yagani har yayi yawa har tsoro yabashi amma yayi murna tunda ance duk wacce ta fitar da jini a first night to takawo budurcinta
Tasha tarairaya awajen Mall amma ita ta kanta take dan zafi takeji sosai
Adare suka tafi asbiti

" doctor ban gane dinkin da aka Matane yafarke ba wane dinki kuma za ayiwa gaban macce kuma budurwa."

"Mall dinki aka mata bai kara sa warkewa ba wajen ya farke a haifuwa ne aka mata dinkin kome."

" wane irin magana ne Doctor jiya muka tare da ita dan naga baka gane ba."

What? Sir kana nufin wannan raunin a first night tasamu to ba haka bane asalima dinki aka mata bai karasa warkewa ba har wajen yafara b'aci kuma wannan ba budurwa bace dan naga wani tsohon operation na haifuwa a k'asan maranta in ma da sunan buduwar ka aureta...

Bai karasa ba mall yazuba masa wani wawan mari tare da sake shak'o wuyansa

"matar da na sameta mudurwa zaka ce har ta haifu kasan yanda nake da kishi kuwa."

"sorry sir muje na nuna maka kagani da idon ka."

Tunkuda doctor mall yayi sukaje har dakin da Halima take akwace

Doctor safan hannu yasa tukun ya budewa Mall zanin da Halima ta rufu yace kaga ga kan dinkin nan wanda ko warkewa baiyi ba

To kaga operation din nata kuma tabbas na haifuwa ne yakamata ka bincike ta dan da yawa mata idan zasuyi aure suna zuwa mu musu Dinkin ni da kai na nasha yiwa mata."

Cikin wani irin tsawa Mall yacewa Halima "ki gayamin gaskiya ya akayi aka miki dinki dakuma operation na haifuwa?

Kuka Halima tasa tace "Wllh tsautsayi ne Ya fadamin wata rana naje Iban....

*Tofa*

*B Jattko**AMFANIN SOYYAYA*
aure

*NA*

*BATUL ADAM JATTKO*

*NA HANA AMIN DOCUMENT AMMA YANA CIGABA DA YAWO*

Kainuwa writtes associate🤝🏻

*DOMIN KU NAKE MASOYAN ASALI*

*AYSHA GARKUWA GROUP NVL*

*JATTKO GRP NVL*

*KAINUWA FANS*

*ASHBAT JOOTGAR FANS*

*HUGUMA CONVERSATINS*

*SAWWWAMA GRP NVL*

*SUBAYA GRP NVL*

*AZRAA FANS*

*MEIMEI BEE FANS*

*MRS OMAR NVL*

*AISHA MACHIKA FANS*

*AISHA SADA GRP NVL*

*SADNAF GRP*
*SAJIDA MALL YAJI SAKON KI*

*RALLY GARBA K"AWAR HALLYMALL* 🤣

*DA DUK WANDA SUKA BADA SAK'O NA ISAR*

*DAN KUNA BANI KALA A COMMENT DIN KU🤝🏻*

*22*

naje gidan kakata a *K'ofan na isa* ta aikeni na ebo mata ruwa a makota zata tafasa tea dan rijiyar su ba dadi nasamu wani Yana jan ruwa kawai sai nace bari na zauna akan boket din kafin yagama zaman da zanyi ashe a tsinin bakin marik'in bucket din na zauna ya shigeni sosai dan kasa cire min ma akayi sai a asbiti aka cire aka min dinki shine lokacin da nace maka nayi tafiya Tarawa kaiwa alewan bikin dan ina jin kunya gaya maka ina asbiti ne."

Operation fa inji Mall cikin tausayawa dan ya gamsu

"tun ina yarinya nake da matsalan fisari a marata amma ina kara girma abin yana karuwa har sai da aka min aiki na samu lafiya".

Doctor Khalid shiru yayi yana jin renin hankalin Halima amma da yayi tunanin idan ya tona asiri zai iya b'ata sunnah shine yayi shiru

Mall yakali doctor yace" kaji ai ko."

"Yes hakan ne Sir".

matsawa Mall yayi kusa da Halima Ya gyara mata
zanin ya zauna a bakin godon cikin tausayawa yace " sweet meyasa baki gayamin ba nasake jimiki ciwo."

Halima Jan mayafin ta tayi tarufe fuskan ta alaman kunya."

Mall ya kalli "doctor yace" yanzu doc yaza ayi."

"Eh zamu mata aiki a wajen dan haka zamu dan riketa kwana 2 saboda sai muna dressing din wajen. "

"OK. "

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.