Romantic Hausa Novels

Amir Da Amira Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Amir_Da_Amira_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 1 of 2

[22/10, 22:31] MRS. MU'UTASIM: *๐ŸŒŸAMEER DA AMEERA*๐ŸŒŸ

*Assalam alaikum barkanmu da wannan lokacin yan uwa ina fatan kuna lfy*

๐™จ๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐‘ด๐‘จ๐‘ด๐‘จ๐‘ต ๐‘ต๐‘ผ๐‘บ๐‘จ๐‘ฐ๐‘ฉ๐‘จ ๐‘ช๐‘ฌโœ๐Ÿป

*1*

Gida ne babba wanda yake dauke da bangare uku ga yara nan suna wasa wata yarinya nagani an bigeta tana kuka yaran kowa yasoma guduwa suna shiga cikin gidan wanda ba yan gidan ba sun fita sunkoma gidan su

dayan yarinya ce ta tsaya akan mai kukan tana cewa yarinya kadan ma kika gani indai nice dama nace miki duk uban daya hadani da yaya Safiyan ya dakeni saina rama kanshi ko ance miki namanta ne to ina sani nace dama sai munfito wasa na rama

yarinyar na kuka tace saina hadaki da mama na
wata mata ce ta fito daga dayan bangaren tana fadin ke rashida wani dan iska ne ya tabaki agidan nan mu fidda reni nida uwarshi

wadda aka kira da rashida tana ganin mamanta tayo wajan ta tana cewa mama ba ameera bace ta ke dukana wai dan jiya munje gonar mlm bukar mun ciro mango shine yabiyomu kuma itace tace muje mu ciro idan bamu ciroba zata mana wankan qaiqayi duk wanda baije ba

mama ta banka wa ameera harara wadda ita kuwa ko ajikin ta mama tace yanzu ameera bazaki dena halin azzalumai ba na daukar maganar da kuke dauko mana kullin ana kawo mana karar ku musamman ma ke mai kunnen kashi

Ameera tace eh din baza adena ba kuma ai hadda diyarki muke zuwa wllh ko gobe tayimin gami da yaya safiyan saina jibgi banza ehee tana jijjiga jiki ita ala dole wai an bata mata rai sai masifa takeyi kamar ba gobe

Mama kuwa kama hannu Rashida tayi sukayi sashen mama ameer tana cigaba da masifa

Ameer kuwa nasashen innar ta ta nufa tana zuwa tayi sallama

sai wata tsohuwa ta amsa tana cewa ke kuwa kedawa naji kina daga murya tace nida rashida da mamanta" Inna tace to mai kika musu
ameera tace inna wallahi saina ci aban rashida wai jiyane munje gonar bukar shesuka shiga suna cire mango shine daya biyomu sukace wai ni na sakasu kuma ni ko gonar ma banshiga ba tana matso kwallar karya tace shine suka hadani da yaya safiyan yayi min duka da safe naje wajan umma gaisheta kawai yake dukana

Inna ta saka salati tana cewa shi dan banzan yaron nan shine ya dakeki to wllh bai bigi banza ba saina rama miki dan iska mugu, ita kuwa ameera tana murmushi tace kuma bakiga yadda yake dukana ba kamar wata yarshi

Inna tace zaizo yasameni anan badai ke ya dakaba zonaga wajan ta matsa kusan inna tana cewa wllh jikina ciwo yake yi tana kukan karya, Inna kuwa sai zuba masifa takeyi kamar ta aro baki. (nace ashedai su ameera gado akayo)

mama na shiga gida da isa wajan wata mata tace sadiya kiduba kiga yadda ameera ta yiwa Rashida gaskiya abin nan ya isheni haka dan tafi karfinta saitake zaneta kullin

wadda aka kira da sadiya ta dago kai ta dubesu tace kiyi hakuri nana wllh kinsan ameera inna ce ke daure mata gindi agidan ko abbansu idan yayi magana inna ke rufeshi da fada nima kaina abun damuna yakeyi kullin addu'a nake mata Allah yashirye ta yarinya bata tsoron kowa kisan da cewa mutum daya take tsoro safiyan shima wani lokacin saita mishi mugunta

Maman rashida tace to shikenan amma kija mata kunne gaskiya tace to insha Allah, suka juya suka fita

Umma tayi tagumi tana tunani rashi ji irin na ameera yarinya kamar aljana babu wanda take ragamawa ita batasan ya zatayi da yarinya nan ba kodayake ai lefin inna ne ita ce bata ganin lefinta
Tana nan abba yashigo da sallama amma yaji shuru ya sake wata nan ma shuru kawai saiya sayo kai ciki umma yagani zaune tayi tagumi da alama ta nisa cikin dogon tunani yazo yazauna akusa da ita duk batasan yazoba saida ya shafo fuskarta

Ta zabura da sauri yayi saurin riketa yana cewa haba sadiya menene yasaka kike wannan tunani ? Umma taja numfashi tace abban safiyan wllh lamarin yarinyar nan ne yayi yawa kaduba kaga yadda take dauko mana magana a garin nan amma inna bata gani duk wanda ma yazo sai dai suyita fada dashi

Abba yace kiyi hakuri umman yara mucigaba da mata addu'a insha Allah wata rana zata dena umma tace amin nan ta dauko mishi ruwa da abinci takawo mishi tace na hada maka ruwan wanka yana bayi

Abba yace to matata farin ciki na yana murmushi, Umma dinma murmushin tayi yazo ya rungumeta yamata kissing a kumatu tayi dariya tace oga ruwan fa zai huce

Ya saketa yana dariya yace ki fiddo min kayan dazan saka tace ai tuni na fiddo maka yana kan gado

Ya fice bayi ita kuma ta zauna tana jiransa,

Safiyan ne yashigo gidan bangaren inna ya nufa yana shiga banka mishi harara tayi dariya yayi zuciyar sa yace to inna gidan masifa kennan yau kuma komai nayi ake min wannan harara haka yana maganar zuci, yaji inna tace wato azzalumi ko uban me ameera tayimaka ka daketa inata magana ka wani ziramin ido kamar na uwarka da hanci kamar karass

dariya yayi dan ya saba da wannan ba'ar ta inna yace hajiya inna ikon Allah kaka ta ni kadai , Ameera na kan cinyarta tace tab wllh bazan yadda ba ta soma tirje tirje a kasa tana cewa itafa kakar tace ita kadai bada kowa ba

Inna tace butar uwaka safiyanu nace tashi kabar min gida ai nan ba gidan ahmadu bane da sadiya to tafiyar ka nace kazo kasaka min yarinya kuka

Safiyan ya kama baki yace Allah yabaki hakuri masifatu, Inna kuwa ta dauko wani filo akusanta ta jefa miki tace fice tin kafin na karya maka kafa

yace kai kaji karfin hali irin na inna ni har zaki iya karyani sabon jini ne nifa kekuwa duk kin tsufa

Inna tace uwarka sadiya ce ta tsufa baniba
Ameera tace inna kyaleshi ai yasan kinfi karfinshi, harara yamata ta koma bayan inna tana boyewa fita yayi daga gidan yayi bangaren umma yashiga da sallama

Suka amsa ya karaso yana cewa umma abba sunun ku da gida atare suka amma da yauwa ,, Umma tace har kadawo daga makarantar yace eh umma na amma Hajara fa da Ibrahim

Umma tace basu zoba tukun nan daiko mai suka tsaya yi ne, Abba yace ai zasu dawo

aikuwa basu rufe bakiba sai gasu sun shigo Ibrahim ne agaba yana kuka hajara na rike da jakar makarantar su umma tace a a lafiya kukashigo Ibrahim yana kuka

hajara tace umma wllh kamal ne da Hanifa suka dakemu wai mufadama ubanda zai rama mana

Umma tace to kuyi hakuri kunji wata rana sai labari, Abba yace kuje kucire kayan naku kizo kukai wa inna abincin su tace to
umma

sukashige cikin daki suna fitowa saiga ameera tashigo da sallama tana cewa abba sannu dazuwa

yace yauwa yar inna ya innar take tace lfy lau abinci mu nazo karba tana fada

Su ibrahim suka fito daga dakin nan yawo wajan ta yana cewa anty ameera yau aka dakemu nida hajara

Ameera ta janyo shi jikinta tana bubbuga bayansa tace wai wani dan iska ne ya tabamin kune wllh ko waye babansa saina yi masa b'alle b'alle

Ibrahim yace kamal ne da haneefa

Ameera tace kai kai kai aikuwa basu daki banza ba dani suke zancen

Umma da abba da yaya safiyan sukayi kuri da ido suna kallon yadda ameera take masifa

Abba yace haba yar inna kiyi musu hakuri kila suma tsokanar su sukayi shiyasa suka dakesu

Ameera tace haba abba ya za'ayi a dakesu kuma kace wai na hakura gaskiya bazai yiyuba saina rama musu

Umma tabige mata baki tace kiyima mutane shuru uwar neman rigima to karna ganki a hanyar gidansu ma

aikuwa ta saki kuka tana ihu waiyo Allah bakina inna umma ta kasheni

Abba yayi dariya yace kai wannan yarinya da neman rigima kike. yace mamana kiyi shuru mana ki dauki abincin ki tafi

Ai kafin ya karasa inna tashigo tana cewa iyee lalle sadiya ai dama nasan kece zaki daketa ba kowa ba to Allah idan kika sake dukanta yanzu zanyi tsukiya muci danbe nidake dan baki isaba kike dukarmin yarinya tafada tana huci

ita kuwa ameera tana ganin inna aikuwa ta kara sakin kuka tana rungume inna tace inna babu abinda na mata wai dan nace zan ramawa su Ibrahim dukansu da akayi shine ta dakeni

Inna tace wai sadiya nace uwarki ta haifeta ne kokuwa a kasuwa aka siyota ne da kullin saikin daketa to bari kiji duka dai saita rama musu dan basu isa ba suci bulus ta kama hannun ta suka fita

Washe gari tinda sassafe ameera ke shirin makaranta dan yau zata daukama kannanta fansar dukan da aka musu

Inna tace ameera fito mana ameera tace ganinan inna dan kwali dan daura ta fito

Inna ta kama hab'a tace a a kinga kuwa yadda kikayi kyau

Aikuwa ameera ta washe hakora tana dariya taji an yabeta tace inna ta to na tafi

Inna tace nadawo lfy tana fitowa bangaren umma ta nufa nan suma su Ibrahim anshiryasu ta gaishe da umma da abba da yaya safiyan nan suma suka gaishe da ita, ta kama hannu su suka fita

Sauran yaran bangaren suma suka fito da shirin makaranta nan suka fita daga gidan yaran suka isa makarantar su

tukun Rashida da ameera da nafeesa suka isa nan malaminsu yazo suka gaishe shi nan aka fara koyarwa

Ameera ce taga wani yaro yana kallon ta yana dariya dankuwa tasha kwalliya kamar aljana kuma kowa yasan halinta dan idan aka kama fada da ita bata barin bashi

aikuwa ta aika mishi harara mai nuni da zamu hadu anjima

Ana tashi ameera da kawarta khadija suna tafe suna hira

Ameera tace kawata ki rakani yau mu casa wasu yara

Khadija tace yauwa dama kwana biyu ban yi fada ba hannu na har kaikayi yakeyi mutafi amma suwaye

Ameera tace kamal da haneefa mana jiya suka kama min kannan suka zanesu nikuwa nace saina rama musu dan babu wanda ya isa ya dakar min yan uwa

Khadija tace aikuwa sun taba bala'i dan bazamu raga musu ba

can suka hangosu ita da kaninta sun tafiya aikuwa da sanda su ameera ke tafiya har suka zo wajan su

Carab sukaji an rikesu haneefa tace uban waye ameera tace ubankine nan suka bude musu idon aikuwa sukayi arba da ameera

Haneefa da yake itama mafadaciya ce cikin fada tace lfy kuka taremu a hanya muna tafiyar. Ameera tace maiyasa kuka dukar min yan uwa

Haneefa tace su suka zagemu , aikuwa bata idar ba ameera ta bade mata ido da kasa nan suka kama dukan ta kamar Allah ya aikota tana ihu tana cewa kiyi hakuri wllh bazan sake dukansu ba

Aikuwa ameera tace batasan hakuri ba saida suka nada musu duka sosai dan har an fasama haneefa baki da hanci kamal kuwa marin da khadija ta wanke masa har hudu

Shine ya gigitasa ya rasa inda zai nufa ya rike yar uwarsa suka tafi suna kuka

wani dan saurayine ya karaso wajan su ameera yace to iyayen fada

Ameera tamai harara tace ina ruwanka sarkin iyayi

yace ke wllh yanzu zan zaneki , Ameera da khadija suka tafa suna dariya ameera tace kama isa saidai muzaneka wllh , khadija tace kai yanzu lado in banda abinka ina ruwanka damu banza jaki alade

Aikuwa lado ya shaka yace nine jakin ? tace eh din anfada jaki bata ida ba ya wanke ta da mari

Aikuwa ameera ta dauko wani dutse tasamu bayansa ta buga mishi yasaki kara ya juya kan ameera

Itama khadija ta dauki dutsen ta buga mishi a kugunsa aikuwa yaji zafi cikin fushi yace wllh saina karya ku yanzu nan yafada yana huci

Da gudu suka bar wajan yana binsu dayake dukkansu basuda jiki aikuwa sukamishi nisa

duk inda suka fuce suna ihu suna wai mahaukaci gashi nan zai kashemu taimako jama'a

aikuwa duk inda sukabi indai akwai mutane suma mutanen rufa musu baya sukeyi kafin kace me tuni sun yaye mutanen layin kowa gudu yake yi nan suka yako kofar gidan mai gari

mutane ne a zaune ana hira a kofar mai gari ameera ta fara zuwa mai gari ya dauko lomar tuwo ameera tayo sufa ta tsallakeshi ta taka bayanshi

Mai gari ya wanke fuskar shi da miyar kwanon tuwo ga akwai zafi tuwon

Mai gari yasaki ihu yana cewa annoba ce ta yo nan bai ida maganar ba khadija itama tazo a mugun gudu tabi takan kafarsa ji kake kass ta dira akan kafar ta kara karfin gudunta

mai gari yakara sakin kara yace man liman taimaka min ka kaini gida wannan wani iftila'i ne yashigo mana gari

Liman ya yunkura zai mike

kowa yayi zuru zuru yana kallon mai gari hallau shesu kalli hanya dasu ameera suka fice

Liman yakusa mikewa lado yace ya angizashi kan mlm bukar

Sukayi gwaran kawuna kan mlm bukar ne ya bugu da gini aikuwa wajan ya fashe sai jini

Mlm bukar rike wajan yana fadin innalilahi wa'inna ilaihin raju'un munshiga uku wannan wani irin masifa ce bai gama fadar sauran magana ba ya hango wasu mataliyar na maza sunyo kansu da mugun gudu

liman na ganinsu yace jama'a kutashi ga wasu bataliyar nan

Suna kokarin tashi suka iskesu aka ringa tabin kansu ana ficewa

Su ameera kuwa suna ta gudu a hanya wata mata tana tafiya ashe mahaifyar su kamal ce aikuwa suka bangajeta sukayi gaba kafin ta tashi lado ma yazo yabi da kanta

Da sauri tayi ta maza ta mike tana komawa bakin hanya

Su ameera suna gudu suka samu wanu lungu anan suka boye lado yazo ya fice aguje sauran ma suka fice da gudu saida sukaga sunyi nisa sosai tukun suka fito sukayo gida

Acen kuwa kofar mai gari sai bayan sun tafi liman yayi karfin halin tashi ya tada mai gari da mlm bukar yana musu sannu duk da shima yaji ciwo a hannu

Amma raunine yayi

mlm bukar yace wllh ko tambaya ba'a yi wannan yarinyar ce data addabi mutane itace ta tabo wani suke wannan tseren

Mai gari kuwa sai share ido yakeyi yana jan numfashi yace wllh saina mata hukunci aje a kiramin inna tazo sai tabiya kudi an mana gyara

Dan aike aka tura kiran inna gidanta

Inna tana zaune saiga khadija da ameera sun shigo kamar wasu na Allah sukayi sallama inna ta amsa tana fara'a tace harkun dawo

Sukace eh inna suka shige daki dan sungaji sosai gudun dasukayi ba kadan bane a kan gadon inna suka zube

Ameera tace khadija kisan kuwa ameer ya kusan zuwa hutu nan kauyen ? Khadija tace da gaskiya , eh wllh ta bata amsa suna haka shesukaji ana sallama da inna ameera tace ke kin manta dazun muna gudu ta kan mai gari mukabi

khadija tace to sai me dan munbi ta kansa mu mukace yazauna a waje

Ameera tace shegiya kawata kina wuta suka tafa

Inna na fita waje akace mata ana kiranta a fadar mai gari , tace to uban shi mai garin zai banii da yake kurana ko wani akace yana bina bashi tana hararar dan aiken

Wanda aka aiko yace inna gaskiya ban saniba kawai kizo mutafi idankinje zakiji ko menene ma

Tace to jirani na fito

ya kalleta yace badai guduwa zakiyi ba yana kallon ta

Inna tace kai ya naga kana kallona da fuska kamar an kona jarka to ba guduwa zanyi ba tashiga ta cewa su ameera wai ana kiran ta a kofar mai gari

Ameera ta zaro ido tace inna mai kikayi

Inna tace babu abinda nayi yanzu zanje naji naga dan iskan dayakai karata ta fada tana fitowa tace dasu kufito mutafi , sukace to suka tafi zuwa gidan mai gari inna kuwa she surfa ruwan bala'i take ita ala dole an bata mata rai tana son taji wani yan banza ne yakaita kara wajan mai gari....

๐™–๐™ฃ๐™–๐™ฃ ๐™ฏ๐™–๐™ฃ ๐™™๐™–๐™ ๐™–๐™ฉ๐™– โœ๐Ÿป
[23/10, 00:40] MRS. MU'UTASIM: *๐ŸŒŸAMEER DA AMEERA ๐ŸŒŸ*

๐™จ๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„ โœ๐Ÿป

*2*

Suna tafiya a hanya inna tace to waima wani kaniya mai garin zaibani da yake kira sai wani sauri kakeyi kamar zakaje daurin auren ka,

wanda aka turo kiran inna yace idan munje dai zakiji

Ameera tace khadija anya kuwa ba gudan da muke bane sbd kinga munbi dakan mai gari , khadija tace hmmm kedai kibari idan muka je zamu gani ameera tace ni kinga inna tace jiya ameer dina zaizo daga birni kuma yau ne zaizo gashi an kira inna gidan mai gari ahaka dai suna hira suna tafiya

Lado kuwa gajiya yayi da gudun ga kuma bayansa da yake masa ciwo kamar zai tsage zagi da tsinuwa kuwa su ameera sun shashi kamar mai yayi alwashin duk ranar da taje wajan wasa dandali to saiya rama shi idan yatashi ma kafafuwa zai karya mata

Su inna na zuwa taga su mai gari yayi dai-dai akan tabarma yana zare ido kamar wani tsohon maye

Inna tace ranka ya dade gani naji ance kana kirana shine nazo naji ko lafiya tin kafin ta dasa aya

Mai gari yace ba dole kizoba saboda wannan shedaniyar jikar taki ta kakkarya mana jiki gata kamar kara amma sai shegen karfi kamar na doki

Inna ta hade kirar sama data kasa tace wllh a shirdinka karka kuma cewa jikata shedaniya dan ba karamin aiki na bane nayi tsukiya muci dambe awajan nan tana aika masa da harara

Mai gari yace dama ai nasan da haka ke kike daure mata gindi take fitsararta son ranta

Nan inna ta rufesu da ruwan masifa tace ba'a isa ya aibata mata jika ba

Su ameera kuwa suna gefe ita da kawar ta suna kwasar dariya harda rike ciki , Ameera tace Inna tace bazata bari a dakeni ba a
kofar mai gari

khadija tace aikuwa naga alama yanxu dai da dare zakije dandalin ne
ameera tace zanje mana

Ankawo mai gyara mai gari yace inna tabiya kudin gyara ko kuwa ayima su ameera bulala ashirin

Inna tace wllh baka isaba kace zaku zanemin yarinya , ta fiddo kudi dubu biyar ta watsa ma mai gari tace gashi nan anbiya to ko harara kamata saina sakata ta rama tace musu muje gida kunji suka kama hanya

Wata mota ce take shigowa layin sainaga tayi gidan su ameera ina lekawa naga wani mutum da bazai wuce shekara 47 yana dravin sai wani saurayi kyakyawan gaske wanda yake kamar sa da baban sa fari ne tas bazai wuce shekara 25 sai wani shan kamshi yake ameer kennan suna isa gidan yaran gidan suka fito suna ga baba na birni cikin fara'a baba na birni yafito yana dariya suka ce sannu da zuwa yace yauwa yarana nasameku lfy suka amsa a tare da lfy lau

Ameer ne ya fito daga motar ganin yaran yasa yasaki fuska nan sukayo kanshi suna yaya ameer sannu dazuwa yace yauwa kanne na nan sukayi sashen inna lokacin bata jima da dawowa daga kofar mai gari ba tana ta fada

ganin su ameer yasa ta washe baki tana lale barhabin mutanen birni suka shigo da sallama ta amsa musu ameera ce tafito da gudu tana cewa oyoyo baba taje rungume shi yana dariya yace a a kaga yar inna an girma

cuno baki gaba tayi tana shagwabe fuska tace Allah baba ban girma ba ni

yace to shikenan naji

Tana juyawa wa zata gani ameer aikuwa da sauri tayo wajan sa ya tsaya yana kallon ta yarinya har tayi saurin girma yana zancen zuciya yaji ta a jikinsa suka sauke ajiyar zuciya a tare

ta dago kanta ta marairaice fuska tace yaya ameer shine ka wani daure fuska ko bason zuwa garinmu kake ba

Sai lokacin yasaki fuska yace waya ce miki ai ina son zuwa sosai naga granny tsohuwa da ke dasu abba da umma

Ameera tace to na yadda yaya

Inna tace mai gida na ni manta ni kayi ne kodan kaga ameera ne,

Yace a wane ni hajiya inna mai duniya taya zan manta ki, dariya inna tayi tace to zo ga abinci da ruwa sadiya tayi girki irin naku yan birni

dariya yayi yace to suka zauna ameera na manne da ameer tana ta zuba mishi surutu shikuwa sai murmushi yake yi dan baya gajiya da surutun ta

Ameera tace daddy yau saida aka kaimu kara wajan mai gari

daddy yace kara kuma ?

Inna tayi caraf tace wllh kuwa Muhammadu wai ameera tabi wajan da gudu ta taka mai gari shine fa akace kona bada kudin gyara ko ayi mata bulala ashirin

Daddy yace ashirin fa,

Ameera tace eh

Ameer yace yanzu kun biya kudin

Inna tace nabada ai bazan bari a tabamin naman jikin ameera ba

...Ameer yace to shikenan nan suka ci gaba da cin abincin su suna hira cikin nishadi

12:30PM abba yadawo daga kasuwa yana shigowa yaga mota agidan yace a ashe Muhammad sunzo ya wuce sashensu yashiga su Ibrahim suka tarosa da oyoyo ya rungume su yayi

Suna dariya hajara tace abba daddy yazo

Abba yace ai naga motarsa a tsakar gida

Umma tayi masa sannu da zuwa ta cedasu su tafi dakinsu abba zaiyi wanka idan yagama shesuci abinci suka tashe da gudu suna murna .Umma tace muje abbansu kayi wanka kaci abinci kafin muhammad yashigo

Abba yace to yau kuma kodan oyoyo dinma babu, Umma tayi murmushi tace akwai mana amma sai anjima , abba yace to shikenan , matata yafice yana murmushin shima

Abban su Rashida ne yashigo shima gidan yaga mota yayi murmushi yace yau munyi baki ashe yayi sashensa yashiga da sallama yaran nasa suka tareshi suna abbu sannu da zuwa yace yauwa

Mama nana ce ta fito tasha waka ta kashe dauri ta iso wajan su tana yiwa abbu sannu da zuwa

Abbu yace yauwa yana kallon ta yace wannan duk ni aka yiwa ,

Mama nana tayi farr da ido tace sosai makuwa , yayi dariya yace aikuwa kinyi kyau sosai

tace ngd mai gidana nan suka shiga ciki

Ameer tinda yagama cin abinci yaja ameera kauye suka dasa hira yana kwasar dariya tana bashi labarin damben dasukeyi idan mutum yakawo mata reni tana ta zuba kamar kanyar data nuna

Ameera tace kaga yaya akwai wani da yake tareni idan zanje makaranta wai sai yake cewa yana sona ta shagwabe fuska

Ameer ya b'ata fuska yace ke kuma mai kika ce mishi

Ameera tace ai ni bana sonshi sbd k'azami ne ranar a makaranta koroshi akayi sbd kazantarshi baya wanka ga kafar da kaushi kamar bayan bishiya

Murmushi ameer yayi sai kallon ta yake yana ta sak'a da warwara da zuciyar shi

taci gaba da cewa kasan yaya wllh adamu dan iska ne tana dariya

Ameer yace kamar yaya ?

tace wani lokacine naganshi a dandali yana taba nan din budurwar sa ta nuna mishi kirjinta

Ameer ya zare ido

kwashe da dariya ameera tayi tace shine nida khadija mukayi sanda muka karyo bulala biyu muka shafa gawayi a fuskar mu muka saka mayafin inna da dare mukaje gidansu har dakinsa yana bacci,

Na tsula mishi bulala da sauri yatashi yana kallon mu yana cewa dan Allah kuyi hakuri ku kuke ganinmu bamu muke ganinku ba

khadija tace wato kaine dan iska mai taba jikin mata ko toyau zamu tafi barzagu da kai

.yana kerma yace waiyo Allah na shiga uku wllh bazan sake ba

ameera tace shiiii bamason kana daga sauti idan wani yajika to mutuwa zakayi

Adamu na zare ido baki na rawa yace nadena wllh bazan sake kama hannun wata ba inba matar dana aura ba

khadija tace ai kasan idan anje barzagu walakiri zaiyita jibgar ka,
Adamu saboda tsoro baisan lokacin daya saki fitsari ba

sarai ameera tagani tana dariya kasa kasa..Ameera tace yanzu abinda zakayi mu kyaleka shine kayi tsallen kwado guda dari saimu barka da ranka

ya fitoda ido waje yace dari kuma

Ameera ta hade rai tace eh haka nace idan kuma ba haka ba saimu tafi dakai

Cikin kaduwa da tashin hankali yace zanyi kuyi hakuri mutanen boye zanyi

khadija tace to soma yanayi harya gaji kuma suna zuba mishi bulala ga sunce idan yayi ihu mutanen gidan su suka fito shima yasan gabar ya rufe bakinsa da hannun sa saida suka miki dukan tsiya tukun sukace miki rufe idon tinda kayi biyayya zamu barka

Haka adamu jin ance za'a barshi sai ya ji dadi yace na rufe

Ameera tace idan kasake ka bude da wuri to zaka ganka a k'ungunmin daji mai kuraye

Da sauri yace bazan bude da wuri ba

nan suka fita da sond'a suna fita suka kama dariya,

khadija tace wllh ameera ke muguwa ce kinfini dukansa Ameera tace ai yabani haushi ne yadda yake tare yan mata yake taba musu kirji ko wani kalar iskan ci ne wannan oho?

khadija tayi dariya tace ai ya fitini kowa a garin nan yaudai munyi maganin dan banza

Suna tafiya a hanya wasu mutanen sun taho suna hira ameera tace khadija bari mu baiwa wadancen mutunen tsoro tace to

suka rakube a jikin wata bishiya suka saida mutanen suka tunkaro kawai suka fito fuska bak'i k'irin jiki kuma fari kamar fatalwa

Mutanen sukayi baya ameera ta makale murya ta juye hannu tace idan kuka kuskura kuka gudu to zaku mutu

Ai da sauri suka dunk'ule a waje daya suna mazurai suna kerma

......Ameera tace daga ina kuke ? wani acikinsu yace daga dandali muke shine muka taho gida

ameera tace kune marassa kunya har kuka tsaya har wannan lokacin baku dawo gidaba ko

nan suka soma cewa dan Allah kuyi hakuri bazamu sake zama dare ya mana ba awaje

khadija tayo kansu tana wani gurnani kamar wata aljanar gaske tace daga yau idan kuka sake bari dare yamuku to zamu tafi daku duniyar aljannu

Cikin tsoro sukace baza musake ba amana afuwa nan dai basuyi muguntar ba suka barsu suka tafi....

khadija tace bacci nakeji mutafi gida .....

Ameera ta dawo daga labarin da take baima, Yaya ameer shikuwa sai dariya yakeyi harda rike ciki yana jin mugunta irin tasu

ameera ita ma dariyar tayi tace amma yau zaka bini muje dandali ko yace sosai makuwa dan naga adamu

Dariya tayi tace zan nuna maka shi

*SHIN SU WANENE AMEER DA AMEERA*

Mlm shareef shine asalin baban su abba auren gidan aka musu shida matarsa maryam wato inna

Ahmed shine dansu na farko wato abba. Bayan shekara uku maryam tasake haihuwar namiji muhammad wato daddy na birni bayan shekara biyu tasake haihuwar wani namijin Abubakar wato abbu sai autar su Mufeeda ..Abba shi yafara gama makarantar sa yasoma kasuwanci yana da shekara 27 years suka hadu da sadiya wato umma nan suka saba da juna basu wani jima ba suka yi aure

Bayan aurensu da shekara uku muhammed yagama karatun sa yace shi birni zaikoma yaci gaba da karatu nan aka bashi dama mlm shareef yanada abokin a cen kano nan ya mishi waya yace mishi ga muhammad nan wato daddy na birni

yana karatun nan yar gidan wadda ake kira da fadila suka kulla soyayya aikuwa babanta yaji dadi nan da nan akayi auren su

sai Abubakar wato abbu shima yagama karatunsa ya kama kasuwanci Allah yadashi da nana yar cikin garin katsina suna fara soyayya babu bata lokaci aka musu aure

Abba yana yara hudu
safiyan
ameera
hajara
Ibrahim

Sai daddy na birni yana da yara uku

Ameer
Fauziya
Fatima autarsu

abbu kuwa yana da yara biyar

Rashida
Usman
Abdul rashid
Nasser
sai kausar auta

.....yanzu mlm shareef shekarar sa goma da rasuwa lokacin ameera tana yar shekara 2years ya rasu

*wannan kennan*

CIGABAN LABARI

Abbane da abbu da daddy na birni suka shigo sashen inna nan suka gaishe da inna ta amsa

Abbu yace inna dama munzo ta wata magana ne

Inna ta gyara zama tace to ina jinku

Sai abbu yace ameera da ameer ku je wajan umman ku na kiranku

nan suka mike suna fita abbu yajuyo kan inna yace,Inna munaso za'a daura auren ๐™–๐™ข๐™š๐™š๐™ง ๐™™๐™– ๐™–๐™ข๐™š๐™š๐™ง๐™–

Gobe saboda ta koma birni taci gaba da karatun ta acen

inna ta dago tana bankawa abbu harara tace....

TO ANAN ZAN DASA AYA SAI MUN HADU DAKU A GOBE INSHA AND kuyi comments da share ko like ngd๐Ÿฅฐ
[23/10, 09:25] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐‘จ๐‘ด๐‘ฌ๐‘ฌ๐‘น ๐‘ซ๐‘จ ๐‘จ๐‘ด๐‘ฌ๐‘ฌ๐‘ฌ๐‘น๐‘จ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐‘ด๐‘จ๐‘ด๐‘จ๐‘ต ๐‘ต๐‘ผ๐‘บ๐‘จ๐‘ฐ๐‘ฉ๐‘จ ๐‘ช๐‘ฌ โœ๐Ÿป

3

Inna tace amma kai kuwa bukari kazama mahaukaci taya zakace ameera yarinya da ita kace wai ayi mata aure

....Abbu yace inna bawai tarewa zayi ba za a daura auren ne idan takoma birni sai taci gaba da karatu tinda kinga sai ta zama likita da kike fatan zaman ta

Inna tayi jum kafin tace to shikenan na yadda tinda dan uwanta ne shi nasan zai kulamin da ameera

.....Cikin jin dadi abbu yace mungode
Allah yakara girma

tayi murmushi tana kallon diyan nata tace ku fada ma Mufeeda dai suka ce to nan suka fita daga sashen inna

Ameera kuwa tinda taja ameer suka fita ta kaishi wajan umma suka gaisa tana tambayar sa maman sa

Kasa yayi da kai yace suna gaishe ta nan dai suka fito suka nufi sashen mama

suka shiga mama tace a a ga mutanen birni isowa sukayi ya durkusa ya gaisheta

Mama ta amsa da fara'ar ta tana tambayar sa yan gidan yace lfy lau suke sunce agaishe ta

Su rashida ne suka fito daga ciki suna ga yaya ameer

Murmishi ameer yayi yace yan k'annan na

zama sukayi suna bashi labarin school yana dariya sun jima tukun suka fito

Waje suka fita ameera tace yaya kasan kawata khadija kuwa ?

Ameer yace a a ban santa ba

Tace to muje ku gaisa

Da yake yana son zaga garin yace ok muje

suna tafe suna hira har kofar gidansu khadija duk inda suka bi sai mutane sunce la kalli wani saurayi mai kyau kamar balarabe kuma suna kama da ameera

Ita kuwa babu ruwanta sai zuba zancen ta takeyi

......A hanya ne sukayi arangama da lado

aikuwa yayi kanta dama shi kullin da makamin sa yake yawo sbd karma ya hadu da ameera ta gudu

ameera na ganin lado ta labe a bayan ameer

Jin ta rikeshi yace menene ?

ameera tace yaya gashi nan zai dakeni

Ameer yace wanene da hannu tayi mishi nuni da inda lado ke tunkaro su

Lado yace yarinya wana kama dama nace miki duk lokacin da muka hadu saina karya miki kafa

Ameera na zare ido tace please yaya karka bari ya dakeni

Shikuwa ameer so yake yaga bakin kokarin lado

yana matsowa kusan su ameera ta kara kamkame yayan nata

ameer yace kai dakata cikin tsawa

Da sauri lado yaja birki ya tsaya

Ameer yace lfy ?

lado yace wannan yar iskan yarinya jiya saida suka yimin targade ita da kawar ta khadija yana nuna ameera data cakume ameer

Ameer yace to kayi hakuri nawa ne kudin gyara

......Lado yaji kudi saiya saki ransa yace raina dari biyar ne

Ameer ya ciro kudin a jakar sa yabasa yace karka sake koda ka ganta a wani wajan ka daketa

Cikin jindadi lado yace ai ranka ya dade bazan ma ko kallon taba bare duka

Ameer yace to shikenan tashi kaje nan yabar wajan

Ameer yace wai maiyasa ke bakijin magana ne kullin kina fada kamar baki gajiya

turo baki gaba tayi tace to yaya bashi bane yake zagina shine jiya muka rama

kunnan ta ya murde ta saki kara tace waiyo Allah yaya akwai zafi tana yarfa hannu

Harara ya aika mata yace ai daukeki zanyi mukoma birni kowa ma ya huta da wannan fadan naki

Da sauri ameera tace da gaske yaya tana tsalle

yace gobe kuwa zamu tafi nan ta kama murna suka yo gidan

Abba ne zaune shida umma yana fada mata shawarar dasuka yanke na hada auren ameer da ameera

Sosai umma tanuna farin cikin ta taji dadi dan ta gaji da wannan fitinar na ameera tace Allah yasa haka shine mafi alkhairi kaga idan ta kara girma saita tare kafin lokacin tayi hankali

Abba yace hakane kinga zataci gaba da karatun ta acen

Su Ibrahim ne suka shigo shida hajara na biye da shi suka haye kan cinyar abba

Ibrahim yace abba wai sai yaushe zan girma nima kamar yaya safiyan

Umma tayi dariya tace sai ka kara shekara ashirin

Ibrahim yace to umma yaushene gobe idan natashi daga bacci zanganni babba kamar malamin mu na school

Hajara tayi caraf tace hmmm dallah cen bakauye kawai waya cema gobe zaka girma kuma malamin school dinmu uncle mustapha kake hada kanka dashi wannan garjejen k'aton dashi ta karashe maganar tana cuno baki gaba

Ibrahim yace yarinya idan nazama babba jirgi zan siyawa umma da abba suke zuwa saudiya da Dubai

Hajara tace to sai kayi tayi ai yaro

Umma tace to ya isa haka kufice kuyi wanka duba kuga yadda kukayi da kayan jikinku

Ibrahim yace umma anty hajara ce tace muyi gini na kasa shine fa muka bata kayanmu

Hajara a masifance tace mai karya asaka mishi rigar fatalwa ya kwana yana bingel bingel

Abba yayi dariya sudai kullin sai shirme akama gardama nan suka fuce

Abbu ma gidan yanufa shima yafada ma mama cewa gobe za'a daura auren ameer da ameera

Itama ta nuna farin cikinta tace Allah yasanya alkhairi cikin farin ciki abbu yace ameen masoyiya

dariya tayi dan tasan mijin nata badai barkonci ba yace ni ina su rashida kuwa

Tace suna daki yace ok nan suka kama hirar su na miji da mata

Daddy masaukin su ya nufa nan ya tarda ameer da ameera suna ta zancen su yaji dadi dan kuwa yasan irin son da ameer yakewa kanwar tasa

Sallama yamusu suka amsa gaishe shi ameera tayi tace natafi

Daddy yace to yar gidan inna, nan ta fice abinta

Daddy yace ameer gobe zaa daura auren ka

A razane yadago yana kallon sa yace dad aure na kuma nidawa

Murmishi daddy yayi ganin yadda ya rude alokaci guda yace kaida ameera

Ai tuni ameer yasaki fuska yace to amma dad ai ameera karama ce dukafa 12 years gareta saidai tayi school acen kafin tagama tayi hankali

Daddy yace nima haka na yanke shawara nan ya kira mommy yafada mata itama ta nuna farin cikin ta dan tana son ameera nan sukayi sallama

Da dare bayan sallar isha'i ameera tayi d'amara a kugunta taci kwalliya kamar wata aljana tafito tace inna zanje dandali bazan jima ba

Inna ta dubaita tace a a hadda kwalliya haka
Ameera tace eh

Inna tace adawo lfy nan ta fita abinta tana wakar karo taci da ameer taja da baya tana dafe kirji tace sannu ban ganka bane yaya

shikuwa ameer k'uri yamata da ido dan yaga ta caba uwar kwalliya kamar aljana yace ina zakije

Cuno baki gaba tayi tace dandali

Ameer yace daukan magana dai ?

Sake turo baki tayi

Yace idan kika sake turomin baki saina cire miki shi

Da sauri ta mayar tana dariya tace to shikenan matsa na wuce

yace karfa ki jima

tace bazan jima ba

Yabata hanya tafice

Tana fitowa saiga khadija itama tasha kwalliyar irin na ameera taci damara a kugunta nan suka tafi dandali

wajan yan mata ne da samari wasu na hira wasu na wake wasu na kallon su.

...Kafin su ameera su iso wajan wani saurayi ya tare ta yace a a su ameera kune sai yanzu

Kallon tara saura kwata tayi mishi tace eh mune ya akayi , yace dama jiranki nakeyi gashi kuma kinzo
Khadija tace buba kabamu waje mu fice

Wanda aka kira da buba Yace ke dallah cen danma kunga ana kulaku waye baisan halinku ba hatsabibai yana aikawa harar

Ameera tace khadija kyaleshi ai yaya yacemin kar nayi fada bata idarba ya buge mata baki aikuwa taji zafi

khadija tace aikuwa sai mun rama yana hararar su yace mugani mana, ameera ta jumke kasa a hannun ta tace inka isa juyo yana juyowa ta watsa mishi kasar a idonsa
Ihu ya saki ka yana dafin kin makauta ni, sukuwa dariya suke Dan su ganima sukayi kadan suka mishi sai gobe zasuje gidansu da dare sumishi balle balle da reza nan suka wuce

Yau dai basuyi fada sosai ba suka dawo gida ameera tafara shiga gida tukun khadija

Washe gari

Misalin karfe 3:pm bayan sallar jumma'a aka daura auren ๐™–๐™ข๐™š๐™š๐™ง ๐™™๐™– ๐™–๐™ข๐™š๐™š๐™ง๐™– akan sadaki raina dubu hamsin bayan angama su daddy suka iso gida ameer sai washe baki yakeyi

Ameera da aka fada mata an daura mata aure da ameer dinta aikuwa tahau tsalle tana taka rawa ita ala dole tayi aure kuma da ameer dinta duk wanda tagani sai tace anyimin aure tana dariya baruwan ta da damuwa ita ko ajikinta

Babu bata lokaci aka soma shirya musu kayansu na tafiya kano daga kauyen karkara

Inna na kuka tace ameera shikenan zan dena ganin ki , Ameera na dariya tace to kekuwa inna meye na kuka idan naje birni zanzo ina ganin ki kinji innata

Kowa na wajan dariya yayi dan ita batasan mai ake nufi da aure ba nan aka rakasu bakin kofa

Ameera ta soma gada musu hannu tana fadin sai wata rana umma da abbana natafi kano wajan mommy nake kwalliyar yan gayu ina kashe dauri ina hawa lilo tana ta surutun ta aka ja mota

Daddy ne ke jan su kuma suna baya shida ameera suna hirar su

MUHADU A GOBE INSHA ALLAH KUYI COMMENTS DA SHARE DIN NOVEL YAWAN COMMENTS DINKU SHINE KARFAFA MANA GWIWA NGD
[23/10, 23:12] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

4

Tin kafin suyi nisa ameera ta fara bacci nan ameer ya gyara mata kwanciya sukaci gaba da tafiya basu Jima ba suka kawo kano ta dabo tumbin giwa anguwar nasarawa J R A wani gida mai kyau daidai misali naga sun nufa nan aka bude musu suka shiga gidan ameer ne yasoma tashin ameera bude idonta tayi akanshi yace my ameera munzo kano

Ameera tace da gaske?

yayi murmushi yace tashi kigani

tashi tayi akan shi taga dai ashe dai da gaske yake yi sunzo cikin murna ta rungume shi tace yanzu zan ga mommy ko

Ameer yace sosai makuwa keda zaki zauna tare da mu

Ameera tace to amma zan ke lilo irin na gida ko

Yace zanke kaiki wajan wasa nan suka fita

Fauziya ce ta fito daga wata kofa ita da fatima suka yo inda ameer yake suna oyoyo yaya nan suka rungume sa suna murna

Fati ta juya gefen ta kawai sai taga ameera tana cika sai hura hanci sama take ta rike k'ugu ita wai an share ta taga basu ganta ba

Fatima tace la anty ameera fuskar ta dauke da farin cikin ganin ameera

fauziya ta juya itama nan suka rungume ta suna cewa dama dake za'a zo mommy bata fada mana ba

Sai alokacin ta saki fuska tace eh ai tare daku zan zauna tana yar dariya

Fatima tace aikuwa munji dadi

Ameer yace to iyayen surutu sai kuzo mu shiga daga ciki ko yayi gaba suna binshi abaya wata kofa naga sunbi wadda zata sadasu da falon gidan da sallama suka shiga mommy ta mike tana musu oyoyo yarana

Da gudu ameera taje ta rungume mommy tana dariya tace mommy na munzo

Murmishi mommy tayi tace to sannunku da zuwa ya kauye yasu inna da umman ki da sauran yan gidan

Ameera na dariya tace ai in gaya miki mommy harfa kofar gida suka rakomu , kinga kuwa yadda inna take sharce hawaye kamar fa ance mata bazan dawoba kuma ma kin me mommy

Yar dariya mommy tayi tace a a saikin fada

Ameera tace nifa banyi kuka ba yayana yacemin zaike kaini wajan lilo shiyasa banyi kuka ba

Mommy tace to masha Allah mu zauna ko , zama suka mommy tayima su ameer barka da hanya

gidan yana da part uku

daya a sama

biyu a kasa
na saman shine na ameer
kasa kuma daya nasu mommy daya na Fauziya da fatima

Mommy ce ke jera abinci akan danner da

Suna zauna a falo fatima na bakale da ameera sbd itama indai surutu ne ba'a bayaba

Tace anty ameera a dakin mu zaki zauna ko

Ameera tace eh

Ameer ne ya harari Fatima yace kedai yarinyar nan kin cika magana

dariya fatima tayi tace yaya ai zamuke hira idan mun shiga daki

Ameer yace to naji

...Mommy tace "idan kungama surutun kikai ameera tayi wanka sai kuzo muci abinci

Da murnanr ta tace to mommy

Fauziya ta rakata da kayan ta a jaka nan ta nuna mata yadda zata yi wanka da ruwan dumi tace "idan kin gama ina jiranki

Ameera tace to nan dai ta soma kalle kalle tace tab wllh wannan bayin na aljanune ko kuwa a aljanna ake ganin irin wannan bayin ahaka dai ta fidda kayan jikin ta wanka ta soma duk abinda ake anfani dashi fuziya ta nuna mata

Kuma tagane haka take dan akwai ta da saurin fashimta saida ta gama wankan tazo wanja alwala aikuwa taganta ta zama biyu idan ta taba fuskar ta sai taga wadda take gabanta ma ta taba idan ta zare ido itama saita zare ido tsoro ya kamata tana ja da baya itama ta jikin bangon tana ja da baya

Aikuwa ta saki uban ihu a guje fauziya da fatima da ameer wanda zamansa kenan yaji karan ameera aikuwa da sauri fauziya da bude toilet din taga ameera sai kerma take bakin ta na rawa

Fauziya tace lafiya dai kike wannan uhi !haka

Ameera tace wllh anty fauziya aljana ce nagani mai kama dani tana kallo na duk abinda nayi itama sai tayi

fauziya tace ina take aljanar

Ameera tace gata cen jikin bango tana nuna mata da hannu

Kallon inda ameera ta nuna fauziya tayi mirror din jikin bangon ta kalla anan ne taganta ajiki

Fatima ta kwashe da dariya tace amma anty ameera kedai kauyencin ki ya miki yawa madubi ne fa

Ameera ta turo baki gaba tace to ai mu a garinmu ba'a saka madubi a bayi

Fauziya tace to mu muna sakawa

Ameer ne ya karaso toilet din yaga ameera bako pant a jikinta yayi murmushi yace rigimanma yanzu saboda wannan ne kika saka mu gudu

fuskar tausayi ameera tayi tace to ai dai tsoro naji

nan suka fito daga toilet din fatima namata dariya

itama fitowa tayi bayan ta shirya suka fita falo suka tarar daddy da mommy a zaune suna jiran su

Daddy yace yar gidan inna ihun mai kike yi

Tace daddy wai madubi ne suka saka a bayi ni kuma da farko ban ganshi ba saida nagama na nazama biyu shine naji tsoro ko aljanu gareku agidan

Dariya daddy yayi yace to kidena jin tsoro

tace to nan suka fara cin abinci bayan sun gama

daddy yafita shida ameer ana neman sa a kasuwa

Ameer yanzu yagama karatun sa yana koyar wa a wata makaranta kuma nan yake so yakai ameera saboda ya kula da ita sosai dan ta nutsu tayi karatu

Da dare bayan an gaba cin abincin ne aka soma hira inda ameera keta basu labari irin barnar da sukayi a kauye ita da khadija kawar ta

Sai dariya suke ba kamar Fatima ma harda rike ciki takeyi

Ameera ta juya wajan mommy tace mommy kinsan harna tuna lokacin da muka yima malamin mu na school wankan kaikayi

Mommy tace kaikayi kuma ameera

,Dariya tayi tace sosai makuwa lokacin muna cikin aji sai malamin namu ya riga mu shiga shine fa da mukazo sai yace mu tsuguna a gabansa yayi ta zanemu da bulala ranar har ruwan zafi inna tayimin kuma tace sai taga waye ubansa da har zai ke zaneni haka nida khadija mukace zamu rama inna tace tana bayanmu mu rama tinda bamu yafe masa ba

Washe gari , muka je gonar mlm bukar muka cire mana mango sai gashi ya biyo mu zai zane mu muka boye a wani bayan bishiya yana isowa muka zuba masa kaikayi acikin rigar sa khadija ce ta hau sama ta zubo masa aikuwa ya soma zazzaga rigarsa baiga komai ba kuma jikin sa yana mishi kaikayi kafin wani lokacin tuni yacire rigar sa da wandon sa saina

Mukayi ta masa dariya ganin abin na karuwa ya yabar gonar yana zaginmu

Bayan yatafi muka fito nida khadija ta sauko daga sama nina fito daga inda nabuya , sai muka rankaya school din mu

Muna zuwa mukaga mlm kamar da gaske gaisheshi mukaje sallama muka mishi ya amsa gaishe shi mukayi nanma ya amsa da fara'arsa

Yace mana su khadijatullah ne da ameeratullah kijifa mommy dan shegen iyayi hadda mana karin suna

Khadija tazo tabayanshi ta zuba mishi kaikayin mukabar wajan

Ko minti goma ba'ayi ba akaji tana ihu asosa mishi

Shima yayi irin na mlm bukar yacire kayanshi ganin zai haukace aka kaishi gidanshi mu kuwa muna mishi dariya

Mommy na dariya tace kai ameera bakida da dama

Fatima tace ashedai kedin indon kauye ce

Ameera tace ba ruwanki yarinya

Hira akaci gaba dayi

10:00 PM ameera tasoma bacci mommy tace kowa yaje ya kwanta nan suka nufi daki akayi saida safe

๐™—๐™–๐™ฎ๐™–๐™ฃ ๐™จ๐™–๐™ฉ๐™ž ๐™™๐™–๐™ฎ๐™–

Aka nemawa ameera school a inda ameer yake koyawa aka kaita

Yaune zata fara zuwa sai murna takeyi saboda farin ciki ko baccin kirki batayi ba

Shiryawa tayi cikin uniform dinta blue and rid tayi kyau sosai tana fitowa falo ta zauna jira ameer bata jima da zama ba yafito cikin shirinsa

Murmishi tamishi tace good morning yaya

Shima murmishin yamata yace morning my wife kintashi lfy

Ameera tace Alhamdulillah , yace to muje mikewa tayi suka wuce

Suna zuwa school din yakaita ajin da za'a koya mata karatun tana shiga bata kula kowaba kowa yayi shuru jin malamin nasu tana tafowa
[24/10, 00:08] MRS. MU'UTASIM: https://chat.whatsapp.com/Gu2Mxr0SRlx8Da4tv0J2AR

๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™จ๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

5โ€”6

Suna a haka Malamin "nasu ya shigo nan aka yasoma yimusu lecture,

Bayan antashi ameera ta fita domin zuwa wajan yayan nata tana karasawa wajan motar shima ya iso, tace yaya yunwa nakeji

Ameer yace to raguwa ai yanzu zamu tafi gida

ta turo baki gaba tace" nidai muyi sauri

yace to shikenan, nan suka fice gida

Suka zuwa gida ko dai-daita motar baiyi ba ta bude ta fita a mota

Ameer yace a wai Ameera duk yunwar ce ?

tace eh itace

yabi bayan ta suka shiga ciki

mommy suka tarar a falo fatima da fauziya ma sun dawo

Fatima tace sannunku yaya,

Yace yauwa

Mommy tace har kundawo ?

Sukace eh

mom tace to "idan kunyi wanka kuzo ga abinci angama suka amsa da to

Bayan sun gama ne kowa yafito sukaci abinci 'bayan sun gama cin abincin suka koma falo

Fatima tace anty Ameera wai da ni shekarar ki nawane?

Ameera ta mata kallon tara saura kwata tace ki tafi kauyen mu ki tambayi mana inna ko umma

Fauziya tayi dariya,tace kai kudai baku rabuwa da shirme

Ameera tace to ba ita bace ke nenani

mom kuwa na kallon su sai murmushi take dan ita yaran nata burgeta sukey

"Ameera tace to shekara ta 13 years na kusa cike 14 years tana kallon ta,

Fatima tace kai nifa nadauka kinkai kamar 15 years din nan,

Ameera tace to kuma sai kiyi ai

Ameer ne yasauko tin daga sama yake jin surutun su yana saukowa yace kai wannan yara Allah yashirya ku, ku kennan sai shegen surutun tsiya. Yakare magana yana zama

......Fatima tace nifa yaya tambayar ta nayi nawane shekarun ta wai duk ma a 13years take ,tana kallon sa

Ameer yace to da jikike shekarun ta nawa ?

tace kamar 15years haka

murmushi yayi yace to haka ma ai tafiki da shekara uku

turo baki gaba tayi tace, tab injiwa wannan har zata fini

ganin fuskar Ameer a hade yasa tayi shuru bata idar ba ya tashi zai fita

Ameera tace yaya zanje tare dakai

Ameer yace a a wajan abokina zanje

Ameera tace haka nan ma zanje

mom tace kutafi mana tare

Ameer yace to shikenan sako shijab dinkin mutafi,

Tayi daki da gudu dan karma yamata wayo ya gudu a mota ta tarar dashi nan suka fita a gidan

Suna tafiya suna hira har suka isa wani gida mai gadi yabude musu suka shiga,

Ameera tafito shima fitowa yayi sukayi kofar gidan suka shiga "da sallama suka saka kai cikin falon

wata dattijuwar mace magani zaune a falon tana ganin ameer tace a awanake gani kamar ameer koda idona ne keyimin gizo

Murmushi Ameer yayi yana rike da hannun Ameera suka karaso har kasa suka durkusa suna gaisheta tace, lfy lau alhamdulillah ya maman ka yace lfy suna gaisheki tace "ina amsawa tace wannan mai kama da kai din fa ko ita ce wadda aka daura muku auren,

Cikin jin kunya yace eh mama itace ina abokina yake

tace yana dakinsa nan suka nufi dakin,

Ameer ne agaba Ameera nabiye dashi har suka shiga da sallama

abokin nasa ya rungume sa yana kai wai yau wata rana ce!!!

Harara yabanka miki ta wasa yace oho dai koma meye,

Juyowa yayi nan yaga ameera yace madam shigo mana

Kara rungume ameer tayi ta bayan shi

Dariya sukayi tare, ameer yace kaga Anass kaifa dan iska ne yanzu saika taromin ruwa kasaka min mata tsoro

Zaro ido Anass yayi yace to ikon Allah dama wannan itace amarya tamu!!

Ameer yace eh itace yabashi amsa yana hura hanci saboda kar arena mishi mata,

Dariya Anass yayi yace madam bako gaisuwa ma

Ameera da take a bakale a bayan" Ameer tace nidai yaya kace mishi karya kara cemin madam kamar wata babba

Dariya sukayi Ameer
yace to kaji dai kadena

Anass yace to shikenan tinda baki so yakai karshen maganar tasa yace to fito mana mugaisa"

Kanta ta leko taga Anass da askin nan irin wanda gayu keyi ita kuma bata taba gani a zahiri ba sai yanzu,,dafe kirji tayi tace kai kai kai yaya ?

Ameer ya kalle ta yace "manene

Tace dama shi abokin naka dan iska ne ,,

kallon anass ameer yayi don yaga menene na yan iska ajikinsa nan yaga sabon askin daya yi,,

Kawai saiya kwashe da dariya yace abokina kasan meye yasa my ameera tacema dan iska

.....Shikuwa harya hade fuska yace a a saika fada tinda kun maidani mahaukaci,

"Ameer yace wannan askin naka ne da kayi shine yasa take ganin kamar kaidin dan iska ne,,

Dariya anass yayi yace kai amma yarinyar nan kincika abin dariya"

Tsuke baki tayi dan ita "idan kanason ganin bacin ranta kace mata yarinya ita dai tana son girma..tace yaya mutafi gida

Anass yace to daga zuwa

ta murguda baki tace, to kai ina ruwanka

Anass yace ba ruwana kuwa

Ameer yadan hade rai yace Ameera wannan abokina ne ba dan iska bane karna kuma ji kince mishi "dan iska

Ganin babu wasa a fuskar shi tace to yaya nadena basu jima sosai ba suka koma gida

Suna shiga suka tarar da daddy yadawo, Ameera tayi wajan daddy da sauri ta zauna a kasa kusa da kafarsa ta daura kanta akan cinyarshi tace; daddy wani gida mukaje nida yaya

Murmushi daddy yayi yana shafa kanta yace kennan yau kinga gari

tace a a fa gida daya mukaje shima yace abokin sa ne

Mom tace to kije ki shirya kutafi islamiya keda Fatima

Ameera tace to mom

tayi dakinsu basu jima ba suka fito cikin shirin islamiya sunyi kyau sosai" sukace mom muntafi

Mommy tace adawo lfy

Ameer yace mom kinsan kuwa muna zuwa wajan abokina Anass kawai ameera taganshi yayi sabon iska tace wai dama abokin nawa dan iska ne"

Dariya sukayi mom tace gaskiya bana gajiya da surutun ameera musamman ma "idan fatima tana nan

Daddy yace yar gidan inna su inna yanzu ko andena kewar jikar ta ta mom tace to kila

Kusan magarib su ameera suka dawo a gajiye dan yau ameera tilawa tayi kuma tayi sosai,, suna shigowa ko zama basuyi ba aka soma kiran salla nan sukayi daki domin yin salla bayan sun gaba fatima tace""Anty ameera yau zamu zo muyi magana hausa cikin hausa wato karin magana,

Ameera tace to shikenan "idan mun gama cin abinci muka zauna hira sai na miki tambaya kibani amsa tace to

,, Bayan sallar isha'i suka fito falo harda daddy da ameer sukkansu, mommy ce tafito daga kitchen rike da kular abinci tace "idan kun shirya abinci yayi ready

suka ce to,,nan sukayi darning suna cin abinci fatima na mintsinar ameera

ita kuwa sai hararar ta takeyi tana mata nuni da zama rama,

,Murmushi tayi bayan sun gama ne suka koma falo fauziya ta kwashe kwanukan tayi kitchen dasu "ta wanke itama ta dawo falon

,,Ameera tace to yaudai karin magana za'ayi nida fatima mom idan ta fadi ba daidai ba kice yati error mom tace to muna jinku.

Fatima tace to bari na lissafo miki questions kibani amsa gyara zama ameera tayi tace, ina jinki

fatima tace to gasu kamar haka

Abun da ka shuka?

Kowa ya deboda zafi?

Mutu ka raba?

Dan hakin daka rena?

Kowa yabar gida?

Fatima tace to bani amsa

Sudai su mom kallo ne nasu,

Ameera tace yarinya yanzu kuwa

Abin ka shuka =shi zaka ba shanunka

Kowa ya debo da zafi =yayi wanka da ruwan sanyi

Mutu karaba =akwatin karfe

Dan hakin daka rena =shi zaka kakkarya

Kowa yabar gida =gida ya rushe

Aikuwa me zasuyi inba dariya ba fauziya harda fadowa daga kan kujera tana dariya

,Fatima kuwa burgima take dariya ce taci karfinta

" Daddy kuma da ameer suma dariyar sukeyi,,

Aikuwa ameera ta shaka ta hade rai ta mike tace shine kuke min dariya tana bata fuska kamar zata yi kuka

wajan ameer tayi shima yana dariya yace to kece kika bamu dariyar "wannan amsa haka ,

Tace shine kaima kake min dariya ai haka naji kaka na fada

Fatima ce har yanzu bata dena dariyar ba

dama ameera haushinta take ji,,nan tayi kanta suka fara tsere

Mom nacewa kubari kunji kema zo ki mata tambaya ta baki amma basu kulata ba "

nan aka soma dambe ameera tace ni kike wa dariya saina lallasa ki a gidan nan

Ameer zai tashi daddy yace kyalesu tukun musha kallo

Fatima tasamu ta kwace daga rukon da ameera tayi mata tana mata gwalo

"Aikuwa suka ringa zagaya su mom fatima na dariya

Ameera kuwa har ta soma kuka tana cewa,,yarinya ki tsaya ko kuwa sai kinyi bacci na yanke miki gashin kanki irin na maza

Fatima tace anki din,,

Ameer ne ya tashi yayi caraf da ameera sai ta rushe da kuka janyota yayi suka koma kan kujera ya soma rarrashin ta,,yace to kiyi shuru mana

Tace yaya ba ruwana da Fatima tinda take min dariya

Ameer yace kiyi hakuri kinsan fa kece babba,

daddy yace to shikenan ameera kuje ku kwanta gobe kuna da school,

,Ameera tace daddy nidai bazan kwana da Fatima ba wajan yaya zan Kwana

Mom tace daddyn su gyara taje cen ta kwana idan aka barsu hallau fadan zasuyi

Yace to shikenan kuje kowa yaje yayi bacci,,

Ameera da ameer suka yi sama su Fatima suka yi dakinsu .....

.Suna isa yace baki dauko kayan bacci ba tace bari nadauko, sanin halinta yasa yace no bari na dauko miki tace to yaya "nan yafita ita kuwa sai kallon dakin takeyi tsarin dakin ya burgeta sosai ahaka yadawo ya sameta ,

,yace cire na jikin naki ki saka wannan tace to" nan tasoma cirewa shi kuma yayi toilet dan yayi wanka dama ita tuni tayi nata

,,A kan gadon yaganta tace nima zanyi nafilar yace to dauro alwala ta mike tayi toilet tayo alwala suka tada iq'ama

Bayan sun idar ne sukayi addu'a suka koma gado"

Ameera tace yaya ?

yajuyo ya kalleta yace na'am

Tace, dama namiji da macce suna bacci a waje daya ?

Murmushi yayi yace sosai makuwa idan miji da mata ne

Kallon sa tayi tace to kaidin mijina ne ?

yace eh nine mijin ki

tace amma maiyasa bama kwana a gado daya?

yace ke kikace awajan su fauziya za kike kwana shiyasa na barki,,

Tace to daga yau zamuke kwana tare "

Yace eh idan kinaso ba

Tace inaso nan suka kwanta ya janyota jikinsa,a tare suka sauke ajiyar zuciya ita ta gajiyar gudun da tayi "

shi kuma saboda yaji dumin jiki ta saboda ba karamin so yake mata ba tin tana jaririya yake sonta,..

Haka sukaci gaba da rayuwar su cikin farin ciki kuma yanzu ameera tana fashimtar karatu sosai daga boko har islamiya, ta dena kwana a wajan su fatima tare suke kwana da ameer shikuwa haka yayi mishi dadi dan yana jin dadin dumin jikin ta "ita kuwa sarkin son jiki kullin ajikin shi take kwana shine katifar ta,

Yau sun dawo daga school ameera tace mommy munyi hutu akaini naga Inna ta

Ameer yace,ba yanzu ba aikuwa tasaka kuka tana zama a kusa dashi tace,, nidai akaini naga inna ta

Mom tace kyaleshi kinji daughter ni zan sa akaiki kokuwa shi yakaiki kuje cen kuyi hutun,,

Sai tadena kukan tace yauwa mommy na nagode "

Harara ameer yamata ta murguda mishi baki nan yace zan kama ki ai

Dariya tamishi

kyaleshi ta yayi

sama tayi zatayi wanka "dan ta jima da komawa wajan ameer har kayanta dukansu,..

Bayan kwana biyu yau ne kuma su AMEER DA AMEERA zasuje kauyen su ameera sai murna take dan so take taga inna,,nan mutanen gidan suka zo har bakin mota

Fatima na kuka tace itama dole sai an kaita ameer kuma yace bata bisuba, daddy ne yace saita je

Ta dauko kayanta suka tafi,,

Suna hanya Fatima da ameer sai surutu suke kafin wani lokaci sunyi bacci,

Ameer yajuya dan yaji sunyi shuru kawai saiya ga sunyi bacci murmushi yayi yace iyayen zance surutu anyi bacci

ANAN ZAN TAKATA KUYI COMMENTS DA SHARE DIN SA NGD
[24/10, 01:45] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

7-8

Suna isowa kauyen su Ameera yayi anguwar su nan yashiga gidan,,

Yaran gidan suka yo wajan su "suna ga ameera ga ameera

Zantukan yaran ne ya tayar dasu ameera bude marfin motar sukayi suka fito,

Aikuwa kafin su yo kanta tayi sashen inna da gudu tana cewa,,Inna ta gani nazo

Inna na zaune jita kamar a mafarki takejin muryar ameera
bata yadda ba saboda ta saba jin murya ameera na mata gizo "dan kullun sai ta takurawa abba tana cewa yakaita kano gidan muhammadu sai ansha fama ake shawo kanta,, tace "idan ma siyar mata da ameera sukayi to wllh bazata yadda ba su koma inda suka siyar da ita su basu kudin su akawo mata ameera ta kullin haka takeyi bata idar da zancen zucin da takeyi ba taji mutum ya jikin ta da sauri tadawo,,takai dubanta da wanda ya rungume ta wazata gani ameera ce "ta murza idon ta dan tabbatar wa tagadai ba gizo bane ita din cedai aikuwa ta rungume jikar ta 'ta tana cewa dama ai nace musu babu wanda zaiyi min mafiya da jikata yazauna lafiya ya akayi kika gudo,

,dariya ameera tayi tace to inna yan mafiya kuma nida nake gidan daddy maiya hadani dasu

,,Ajiyar zuciya inna ta sauke tace a ni maryam Allah na gode maka daba siyar min da jika aka yi "

Ameer ne yashigo da sallama jin inna na zantuka kamar an jonata yace,,Hajiya inna ikon Allah kaga kakar, ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ yana zama kusanta

Dariya fatima tayi tace to inna mu baki ganmu bane '?

'kallon su tayi da mamaki tace a a harda ke aka zo ashe kuna tare

Tashi tayi kawo musu tabarma suka zauna nan aka gaisa, take tambayar yasu mommy suka ce sunce ma a gaisheku

...Inna tace ina amsawa

Su Ibrahim ne suka shigo hajara tace anty ameera sannunku yaya ameer la hadda fatima tana tsallen murna

Ibrahim ya zauna kusa da ameer ita kuma Hajara tayi wajan su ameera suka kama hira.

....Bayan sallar azuhar suka yi sashen umma suna zuwa ameera ta zauna ta kwanta kan ciyar umma tace,,umma na nayi kewarku

Murmushi umma tayi kuma taji dadi sosai ganin yar ta, ta takara girma tayi kyau sosai

""Ameer ne ya durkusa har kasa yake gaishe da umma cikin jin kunya yake gaisheta

Umma ta amsa tace ya maman naku yace lfy,,umma tace to su fatima ne a garin namu zo kusa na kizauna

,,ta matso kusa da umma ta saki jiki aka suka soma bawa umma labari dan fatima babu ruwan ta da bakunta

,,Yaya safiyan ne yashigo yaga su ameer yace a a yau mutanen kano ne a garin namu

Ameer yace mune dan uwa jan ameer yayi sukayi dakin yaya safiyan yabar su ameera anan ,,

Umma tace kuje ki gaishe da mama nana tace to umma na

Nan suka fita sukayi sashen mama ,,da sallama suka shiga kausar ce da Usman zaune suna wasa, suka amsa sallamar kausar tace ga anty ameera da Fatima oyoyo

suka isa ciki mama ce ta fito daga dakin ta jin kausar tana cewa ameera tazo gani tayi da gaske take ""

tace marhabin ku mutanen kano nan suka gaishe ta ta amsa da fara'ar ta dan itama tayi kewar ameera duk da rashin jin da takeyi agarin amma tana da dadin zama

Tace,,bari nadauko muku abinci

Ameera tace a a mama munci abinci a wajan inna, Mama tace to shikenan amma da dare kuzo nan kuci tace to mama ina, Abbu da rashida da sauran ?

Mama tace abbun ku baidawo daga kasuwa ba Rashida kuwa suna makaranta basu tasoba nasan yanzu sun kusa zuwa gida

Ameera tace shikenan idan sunzo kice mata muna wajan inna,,,Mama tace to shikenan zan fada mata nan suka fito daga sashen mama sukayo na inna

Suna zuwa ameera tace inna idan anyi la'asar zanje gidansu khadija inna tace to shikenan kinsan kullin sai tazo tana cewa baki dawo ba nace mata ai su bukari ne suka siyar dake,,

Dariya sukayi tace inna bafa siyar dani aka yiba""ina cen ina karatu na hadda na islamiya fa nakeyi ko fatima ta ida zancen zuwa kallon fatima,,

Fatima tace eh inna karatu takeyi sosai

"" Inna baki har kunne dan taji dadi sosai tana son ameera tazama likita

....Bayan sallar la'asar ameera da fatima suka tafi gidan su khadija suna shiga da sallama,,khadija ce zaune tana kunce kitson kanta taji muryar kawar ta, ta kamar daga sama ta kalli kofar gida taga ameera ce dai da gudu ta tashi tana cewa,,waiyo Allah kawata nayi kewar ki

Ameera na dariya tace nima haka kawalliya na ""nan suka karasa

Fatima ce ta tsaya tana kunbura baki ita anshare ta duk da bata taba ganin khadija ba amma taji tana sonta,,juyawa sukayi ameera na cewa fatima wannan ce kawata khadija tayi shuru shine suka juyo "ganin ta sukayi tana turo baki gaba sai harara take banka musu

Dariya sukayi, Khadija tace wai dama da soba kikazo shine kikaki nuna min ita,

Ameera tace eh kanwar yaya ameer ce suka koma Fatima ta juya musu baya

Ameera na murmushi tace waiyo my kanwa am so sorry kinji ta , juyo tace shine kuka shareni

khadija tace kiyi hakuri ai yanzu kin zama kawar mu, tasaki fuska suka shiga tare "suka gaisheda maman khadija tace a su ameera mutanen birni ina ameer din naki

rufe fuska Ameera tayi tana dariya wai ita taji kunya,, dariya khadija tayi tace mama kunya fa takeji

murmushi maman khadija tayi tace to shikenan aka rufe fuska

suka koma gindin wata bishiya wanda take a tsakar gidan

khadija ta kalli ameera tace, ,Ameera kinsan kuwa bayan kin tafi kano maman su kamal tazo neman mu takawo kashe gidan mu wai munyi wa yaran ta duka harfa gidan ku taje kinsan me inna tace mata

""girgiza kai ameera tayi alamar a a khadija tace inna cewa tayi wai su abba sun siyar dake jin haka yasa ta koma gida amma fa tace duk ranar,,da kika dawo sai su kamal da Haneefa sun rama dukan da muka musu,

Ameera tace to mugani idan har zasu iya ramawa inda rabon musake zanesu ba

Dariya sukayi nan sukaci gaba da hirar su,,Khadija na bata labarin abinda akayi bata nan

tace yau ai kinzo muje wasa ko ?

Ameera tace,,eh mana hadda kema fatima zaki bimu ko ?

Fatima tace eh zanje naga yadda kuke wasan

Sun jima gidan su khadija har kusan magarib kafin suka tafi akan cewa "' bayan sallar isha'i zasuje wasa

suna zuwa gida wajan inna sukayi , salla suka faraji tukun suka zauna sai ga su Ameer da safiyan sun shigo da sallama nan suka amsa,

,Fatima ta tashi taje wajan yaya safiyan tace la yaya safiyan kai kaga kuwa yadda kake

yana murmushi yace mai nayi,,

Fatima tace kazama babba kamar yayana

dariya sukayi yace to ai yayan naki nafishi

Fatima tace shiyasa kazama babba kamar irin sharukhan na tv

"dariya suka sake yi yaya safiyan kuwa yace eh lalle su Fatima dama haka kike da zaro magana kamar BBC ,,

Dariyar itama tayi tace nidai bankai kaba nan suka zauna

Inna na bankawa su yaya safiyan harara tace,,ku masu kirar mutanen farko kun wani zomin gida kun zaune min kai dama sangangamin banza da wofi, yaushe rabonka da kazo nan ka gaishe ni

Dariya yaya safiyan yayi yace kai inna, wannan ba'a haka ke yanzu kinga kirar mutanen farko din

Tsuke fuska tayi tace to zaneni zakayi saina fada ma,,kai safiyanu wllh kafita idona inba haka ba yanzu zan, tumurmusa ka anan, marar kunya kawai ni wllh nama rasa maiyasa ba'a maka aure ba kabar mana gida kaje cen wani gidan,,

Ameer na dariya yace inna kinsan fa bashida budurwa kuma shida zai koma kano wajan daddy dan yayi karatu sosai yasamu aiki irin na daddy na,,

hararar shi inna tayi tace to shikenan ai iyayen boko nidai bada niba babu ruwana da bokon ku suna haka aka kira sallar isha'i. Su ameer suka tafi maseejit don yin salla

Bayan su ameera sunci abinci suka fito daga dakin inna ameera tace inna zamuje wasa hadda Fatima

Inna tace to karku dade kuma kada kibari a taba Fatima tana murmushi tace to inna nan suka fita

,,,A hanya suka hadu da ameer yadawo gida Fatima na ganinshi tace, yaya wasa zamuje

da mamaki yake kallon su lalle har yanzu yana da aiki agaban sa da auren nasa akan ameera zata fita tace wasa zataje,,

Ameera ta matso kusa dashi tayi fuskar tausayi tace please yaya ba jimawa zamuyi ba

kallon ta yayi yaga yadda tayi dariya yayi yace, to kada ku jima suka amsa da to,,suka yo waje, gidan su khadija suka nifa suka sameta ta caba kwalliya

Abin ma. dariya yabawa Fatima tace to wannan kuma bak'in na baki fa

tace haka muke yi nan suka tafi,,tin kafin su isa suke haduwa da mutanen dake hira da yan matan su,,

Ameera tace a wai yanzu kuwa adamu yana bin yan mata kamar da

khadija tace a wane shi ai tinda muka jemishi bana ganin sa yana tare mata a layi,,

Dariya ameera tayi tace wllh da ace yana yi sai mukoma muyi masa balle balle sukayi dariya ,,,basu jima ba saiga kamal yazo shida Haneefa

idon kamal yasauka kan ameera,,yace yaya Haneefa kalli ameera tadawo

inda yake mata nuni ta kalla aikuwa taga ita ce suka koma dan nemo makami,,

wata sanda kamal yasamo shida haneefa kafin su dawo tuni su ameera sunbar wajan"" dubawa suka ringa yi amma basuga su ameera ba,

,,,Ita kuwa ameera tana juyawa ne taga su kamal na neman abinda zasu dakesu tace wa khadija kalli su Kamal,,sunganni shine suke neman abinda zasu dakemu,

khadija tace mu buya wllh yau sun tarowa kansu fadan dayafi karfinsu suka koma hanyar gida suka labe!!!

Suna kallon lokacin da suka dawo neman su da suka gaji da neman suka bar wajan wasan suka yo gida,,suna tafiya haneefa tace kasan da sun bari mun kamasu wllh saina karya kafan ameera dan nafi jin haushin ta

,,Kamal yace nima haka wllh,,

Ameera suna jinsu saida sukaga sunzo wajan da ba kowa ga duhu suka damko su kamal kafin suyi ihu, suka rufe musu baki

Ameera ce ta cenja murya tace ku dama kune kuke zagin min yar uwa ko,

,Cikin rawar murya da mugun tsoro kamal yace dan Allah kuyi hakuri baza mu sakeba mu mun yafewa su ameera ma

,,kara cenja murya ameera tayi tace mu aljanu ne kuma dole ayi muku hukunci dan bama yafewa wanda ya taba ameera,,,

kuka suka soma tsawa ameera ta daka musu tace kuyi shuru munafukai ""nan suka kyale kafin kace me tuni su ameera suka kama jibgar su Kamal kuma sun haka su yin ihu ko kuka,,,saida suka farfasa musu jiki da duka kafin Fatima taji tsoro a hankali tace ku barsu haka,,,

ameera tasake makale murya tace idan kuka je gida idan an tambayeku kuce,,aljanun ameera ne suka zaneku saboda kunki yafe mata abinda ta muku suka ce to,,suna tafiya ahankali dan ba karamin duka sukaci ba

,Ameera kuwa dariya taringa yi tana cewa wllh khadija harna hada zufa mutafi gida dama hannu na kaikayi yakemin,,wannan watan nin dana dauka ban daki mutum ba

"Itama khadija dariya tayi tace muje

Fatima tace anty ameera yaya bazai dakemu ba idan aka ce mune mukayi musu wannan dukan,

,dariya ameera tayi tace babu abunda zaiyi karki fadama kowa tace to nan suka wuce gida...

Suna zuwa gida suka tarar da ameer a zaune yana danna wayar sa sallamar su ce tasaka ya dago kanshi yana kallon su,dama jiransu yakeyi

yanzu yasaba kwana da ameera,, ya amsa yace kundawo sukace eh yaya

Fatima tace saida safe ameer yace Allah yakaimu tayi dakin inna

ita kuma ameera tace yaya muje bacci nakeji,,yace to sukayi dakin da aka sauke ameer tana shiga tace wanka zanyi yace to bari nayo alwala yashiga ita kuma ta zauna zaman jiran sa,,,bai jima ba ya fito ita kuma ta cire kayan jikin ta tashiga wanka nan da nan tafito itama tayi nafila sukayi addu'a sosai tukun suka kwanta,,,,

Suna kwanciya ya janyota jikin sa ita kuwa mage ta shige jikinsa abinta dan har ta saba da kwana a jikin sa ,,

Shafata ya yasoma yi yana hura mata iska dadi taji, ta kara rungume shi sosai sumar kanta yake shafawa bata ankara ba taji ya hada bakin shida nata yana tsotsa,,itadai jinta tayi awani yanayi na da ban,,dan bai taba mata haka ba ganin yana neman rabata da kayan jikin ta yasa tace yaya!!!

Ameer ya dakata da abinda yakeyi tace kayana fa kake neman fiddamin

bai amsa ba,,dagowa tayi tana kallon shi duk duhun daya mamaye dakin,,tace yaya

yace na'am

tace bacci nakeji

yace to zo ki kwanta sake shigewa tayi, jikinsa bata jima ba bacci yayi gaba da ita"

shikuwa kasa bacci yayi yana tunani anya kuwa zai iya jure renon ameera sa sbd yanzu kullin ajikishi take kwana kuma gashi yarinya ko yan matancin ta basu gama bayyana ba,,zai dai bari takai shekara 15 years amma bazai iya hakurin 20years ba gaskiya ahaka bacci yayi gaba dashi,,

Da safe ameer ya tashi ameera tayi salla shikuwa ya fita masallaci bayan an gama yadawo,,

Ameera tace ina kwana yaya ya amsa dauke da murmushi akan fuskar shi

,,tace yaya "dagowa yayi yace na'am tace wai ya sunan wannan abin daka min jiya da dare

,,kallan ta yayi saboda tabashi dariya dama yasan zaa rina,,,yace wannan sirri ne daga ni sai ke ko inna da mommy karki fada musu""

tace shikenan yaya bazan fada

yace good girl nan tafita..

...satinsu daya a kauye suka shirya komawa,,,aikuwa anyi drama da inna dan cewa tayi babu wanda zai maida mata jikarta wani wajan saida abbu yazo ya lallashe ta,,,

yace haba inna wai ko kin manta ameera yanzu an mata aure kinga kuwa saiki barta ta bi mijin ta,,kuma nan da wani lokaci zata zama likita "

' Jin ance haka yasa tace to shikenan amma take zuwa ganin ta abbu yace to inna nan,,su ameera suka bar kauyen ko digon hawaye ameera batayiba,

,shi ameer har mamaki ma take bashi dan bata da damuwa,,sun iso gida lafiya mommy ta taresu da murna

suka yi wanka sukaci abinci aka zauna zaman hirar kwana biyu anyi kewar juna......

MUHADU A FAGE NA GABA kuyi comments da ra'ayoyinku da share
[25/10, 23:01] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐‘จ๐‘ด๐‘ฌ๐‘ฌ๐‘น ๐‘ซ๐‘จ ๐‘จ๐‘ด๐‘ฌ๐‘ฌ๐‘น๐‘จ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

9/ 10

Fatima tace, a gaskiya mommy kauye akwai dadi kayi yawo son ranka""

Dariya ameera tayi tace ai birni ba dadi kullin kana gida kamar wata wuka

''Ameer yace zaku soma ko ni wllh yaran nan bansan yaushe zasuyi hankali ba!!,

Ameera tace nan da wata ashirin da goma ai lokacin mun zama manya sai muyi hankali ko mommy

,,,Murmushi mommy tayi tace sosai makuwa yarana ai lokacin kun zama manya ""

Fatima tace "idan nazama babba police zan zama, amma ta fararen kaya wato jami'an sirri,,

Ameer yace tab wayaga D.S.P.,,Fatima

Ita kuwa ,Ameera tace likita zan zama idan kika je kama mutane aka jibgeki saina miki magani da allura

Harara ta banka mata tace to baki isa ba wllh kennan ma mugun fata kike min "

Ameera tace a a fa ai naga haka suke yi masu aikin irin wannan

Ameer yace kunga yanzu dai kuje ku kwanta ku huta da dare zaku rakani wajan abokina,,

Ameera tace tab wannan mai askin yan iskan

Hade rai ameera yayi yace bana hanaki ce mishi dan iska ba

Ameera tace yi hakuri yaya na manta ne,,

Mommy da taka bazata iya wannan labaran ba tayi sashenta "

'Fauziya ce tashigo da sallama ganin su ameera yasa tayo wajan su da sauri tace a a yaya ameer yaushe kukazo

Yana murmushi yace tin dazun mukazo ina kikaje ?
ya tambaye ta

tace gidan su kawata kasan ta kusa yin aure ,,

Ameer yace to saura naki, zamuyi nan da wani lokacin,

Rufe fuska tayi tana dariya tayi dakinsu,,

Ameera tayo wajan ameer ta zauna kusa da shi tana kwanciya kan kafadar shi numfashi yaja ya shaki iska,, shafa fuskar ta yayi yace yadai yan mata na

kallon Fatima ameera tayi tace
Yaya nima yaushe za'ayi nawa bikin muyi anko muyi wake

,,dariya tabashi yace sai kun girma tace to

Su kamal da haneefa kuwa tin lokacin da su ameera suka musu dukan tsiya da sukaje gida cewa suka aljanu ne suka taresu sukayita, jibgarsu

Maman kamal tace waiyo Allah na shiga uku ni talatu

Kamal yace mama aljanun fa sunce idan muka, kara cewa, zamu rama "abinda ameera tayi mana to zasu kashemu hada ke

Maman kamal na zare ido tace wllh mun yafe karsu kashemu ""nan aka gasa musu jikin su

kwana shida sukayi suna jinya kafin suka dawo nomal,,

Baban kamal ne yaji labarin ai. ,kwana ki ameera tazo kauye kuma jiya takoma,,aikuwa yace shi bai yadda ba sai yaje yakaiwa inna kashe

Yana zuwa aka mishi sallama da inna tafito tana wani yatsina fuska ganin baban kamal yasa ta tsaya agabansa ,ta warware dan kwalinta ta daura ta turoshi gaba, ta gyara saurin zaninta "duk yana kallon ta da mamaki ta kunto goron ta a jikin zanin ta tasaka abaki tana ci,,

kallon tara saura kwata tayiwa baban Kamal tace,,mlm lafiya dai ko ?

Baban kamal yayi karfin hali yace ance ameera tazo harta koma jiya

Inna tace eh wani abune ko kazo ne kayimin rashin kunya bayan wadda matarka tazo ya gida tayimin

Baban kamal yace a a inna ko daya,,ameera ce tasake dukarmin yara shine nazo nafada miki dan Allah karta kuma,,

Inna tana hura hanci tamai kallon sama da kasa tace, uban waye yacema ameera ce ta dakarma yara iyee nace waye yagaya maka, tinda tazo sau daya ta fita shima itada khadija ne, amma saboda Sharri irinn naka kazo kace wai ta dakar maka yara

Baban kamal yace haba inna meye na fada nifa bada fada nazoba

Inna ta dauko
goron ta tasake gutsira ta kalle shi tace, to mai kazo yi in dai yarinyar nan masifar ku kuka sa aka dauke min ita to ka tafi kabarmin gida

Kowa so kake na karya maka wannan kafar naka mai kama dana zabuwa ta zabga miki harara

Baban kamal yaga inna taki tsaya wa suyi magana kawai ya koma gida,,

Inna kuwa taci gaba da masifar ta dan dama kwana biyu bata yi ba neman soba takeyi ,sai gashi baban kamal yakawo kanshi haka dai takoma ciki ,,,wannan kenan

Su ameera yan school yanzu karatu suke yi babu kama hannun yaro dan exam suke yi wannan shirmen duk tadena wasu dai amma surutu yana nan ,babu abinda ya ragu saima karuwa yau daga school suka dawo ameera da ameer agajiye suka isa gida nan sukaga wata mota ameer yace to bilal ne yau agidan mu,,

Abokinsa ne su uku ne da bilal da ameer da Anass abokan juna suna mutumta juna saidai banbancin halayya

Shi ameer miskili ne na gaske dan yan mata kowacce
Sai binsa takeyi dan ya hutu da ita ko suyi soyayya amma shi baya ganin kowa sai ameera sa da tin yana cikin tsumma yake kaunarta baya son reni

Shikuwa Anass yana son soyayya sosai ya iya yaudarar yan mata da kalaman sa na karya sai yarinya tace yafito ya gudu amma yana hakar lalacewa

Shikuwa bilal dan iska duniya kennan manemin mata mace ke ko wacece indai Bilal yace yana sonki to sunan ki sorry ko baki yadda ba fady zai miki kuma babu wanda ya isa yayi magana, sbd babanshi, mai kudi ne saidai shi baban nasa baisan yana wannan harka banzar,,ba sbd yayi karatu a turai

Wannan kennan

Suna shiga falon suka ga bilal a zaune yana murmushi ya amsa sallamar su,,yace abokina baka da kirki shiyasa nazo gidan ku ni naganka "

Dariya ameer yayi yace to shikenan na yadda nan suka gaisa,

,Ameera ita kuwa tinda tayima Bilal kallo daya taji ta tsaneshi ,,,a bayan ameer ta labe tana daura kanta a bayansa yana jinta,,sai kuma yace "' my ameera juyo ku gaisa da abokina mak'e kafada tayi

Murmushi Bilal yayi yace beauty zomu gaisa haba amaryar mu

Harara ta banka mishi,,tace niba amaryar ku bace nidai "amaryar yaya ameer ce

Dariya suka saka yace, to amaryar ameer zo mu gaisa "

' Jin haka yasa ta saki fuska ta fito daga bayan sa ta durkusa tace ina yini abokin yaya

Yana murmushi yana kare mata kallo yace lafiya lau ameera ya school ?

tace alhamdulillah nan ta mike ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka tace yaya

dagowa sukayi a, tare suka zuba mata ido

Harara tayiwa Bilal
shikuwa bai damuba,,dan yarinya daga kallon ta yaji ta shiga ransa sosai,

Ameer yace ya akayi tace yunwa, bacci, wanka,,bitar karatu duk tajero mishi su a lokacin daya tana gwabe fuska

Dariya yayi yace to sarkin rigima yanzu duk wannan abinda kika zano min lokaci daya zanyi miki

Dariya tayi wanda kyanta ya kara fito wa da hakoran ta masu kyau tace to afara, da abinci

"shidai Bilal kallon ta yake da sha'awa dan tayi mugun ,,tafiya da imanin shi,,

Ameera tasoma dura kafa tana kuka tace nidai yunwa

Dariya bilal yayi yace abokina katashi ka bata abincin mana

Tashi yayi yace to bari
na dauko miki ko tinda mom bata nan yau naga takaina

Dariya tayi tace to ba kaine miji ba

Yace kindai ji dashi,

Abincin yakawo mata ya zauna kusa da ita yakawo ruwa ya ajiye,,yace wanke hannu "ta wanke yace to kici ko

Kuka ta saka tace nidai, bazan iya ba,,"hannu na ciwo yakeyi

Dariya bilal ya kwashe da ita yace kaga MIJIN KWAILA

Harara ameer ya aika mishi yace ina ruwanka ai matata ce dan sa ido

Dariya yasake yi yace bari na zauna nadau, darasi yadda ake kula da mata,,,

Banza ya mikishi yace kadai jidashi dan iska kawai,,,nan yaci gaba da bata abinci harta koshi yace taje tayi wanka,,nan ma tace ita fa tagaji yace tayi hakuri bako yayi taje ta yi wanka zai shigo gashinan, ""

Sama tayi

Shikuwa Bilal yace abokina kaga kuwa yadda kuke mugun kama da matarka,

Dariya ameer yayi yace to jini daya lafiya ne,

"Bilal yace a a gaskiya basu jima sosai ba bilal yace zaikoma

Ameer ya mishi rakiya yabar gidan shikuwa,,yakoma ciki,,

Yana shiga yaga bata cikin room din yayi,,toilet, yaganta ta tara ruwa sai wasa takeyi jin karar rufe kofa yasa,,tayi saurin dagowa

Ganin ameer yasa tace yauwa yi sauri kayimin yace to ,,,ya wanke ta suka fito,,ya shafa mata mai da gyara mata gashin kanta ya daure mata yana yaba,,bakin gashi irin nata ,,

Juyawa yayi yadauko mata kaya marar zauyi tasaka,,nan suka koma kan gado ta dauko,,kayan karatunta, ta zubesu, a gadon.

Zama ya gyara yasoma koya mata tana binshi har suka gama,,,

Suna hira yaji shuru dama tana kafadanshi

Juyota yayi yaga tayi bacci ,janyeta yayi daga jikinsa ya shinfide ta,,shima ya kwanta...

Bilal kuwa tinda ya kama hanya tunanin ameera yakeyi yana tunano fuskar ta mai kyau da haske, yace she is a beautiful girl gaskiya dole na d'ana da yarinyar nan idan ta girma,,dan wannan idan ta kai 20 years gaskiya,,za'ayi babbar mace ahaka dai yana karatun jaki harya kai gidansu,,

Ameera ce zaune ita da kawar ta nafeesa suna duba litattafai wani saurayi ne kamar ya girme su sosai yace hello,, suka dago murmushi yasakar, musu suma suka maida musu

yace..Ameera wajanku nazo kallon sa sukayi

Nafeesa tace,,muna jinka

yace dan Allah zakuyi frend dani,

,Harara ameera ta mishi tace,,a a nidai yaya yahana ni kula maza yace karna sake nayi mu'amala dasu ""

Dariya yayi ganin yadda take turo masu baki,,

Yace a a haba dai ameera kamar fa irin mudanyi karatu tare ko idan wani bai zoba saika bayi naka yayi copying

Ameer ne ya fito daga office dinsa yaga wani saurayi yana yiwa su ameera murmushi

Wani zafi ne ya ziryaci zuciyar sa sai kuma yakai dubansa ga fuskar ameera yaga itama murmushin take masa ne sai yaga akasin hakan,,dan kuwa ameera ta zuke fuska tana aikawa wannan frend nasu harara shi kuma sai murmushi yake dan tabashi dariya ,,wani sanyi ameer yaji, ganin abar kaunar tasa,,bata bada fuska ba

Karasowa yayi, da sallama suka gaishe sa ameera tayi saurin zuwa inda yake ta shige jikinsa dan dama wani zazzabi takeji,,""

Wani dadi yaji yakama shi murmushi yayi yana shafa bayan ta yace,,my ameera ta ,ya akayi ""

Tana jikinsa ta turo baki gaba tace,,,yaya wancen ne 'ta nuna mishi da hannu

Kallon saurayin yayi yaga dai har yanzu murmushi yake karasawa yayi wajansu. ,rike da hannun ta yace mlm lafiya kazo wajan mata

Kasa yayi da kansa yace ina yini

yaya ameer ya amsa da lfy lau

Yace sunana,,Salim mustapha ni dan kano ne,,anguwar kabuga,,

Ameer yace masha Allah ,,Nafeesa tace yaya ina yini

,ya amsa da lfy lau

Salim yace dama nace musu inason muzama friend saboda ni bakone a school din,,shine fa,,take hura min hanci, harda harara

Dariya ameer yayi yace to salim banki frend dinku ba ,amma ameera matar aure ce kuma nine mijin ta..

Baki asake yake kallon ameer yace yaya ameer wai kana nufin, wannan yar karamar yarinya aure gareta,?

Ameer yana murmushi yace sosai makuwa yau 6 month da auren mu,,,

Salim yace to Allah yabada zaman lfy ya amsa da ameen,,

Salim yace to amma yaya zaka bari muyi frend ,,murmushi yayi yace na amince saboda maga kai kana da nutsuwa kuma ko bana school din, bazaka bari ataba ameera ba

Salim yace nagode yaya ,kallon ameera ,yayi yace to frend ku gaida gida murmushi tayi tace to shikenan nan sukayi sallama,,dasu suka shiga mota zuwa gida.

Da dare kowa zaune yake a falo

Fatima tace ameera saura kwana biyu birthday dinki ko,?

Cikin jin dadi tace eh Fatima

Mom tace zamusha birthday ranar

,Ameer yace to Allah yakaimu lokacin insha Allah,, nan aka ci gaba da hira tukun kowa yayi ma kwancin sa,,,

Ameera ce tafito daga wanka daure da towel tana cewa yau bacci nakeji yaya sosai

kallan ta yakeyi yace to kizo mu kwanta,

tace to, nan tagama suka kwanta tana bacci taji ana shafa mata kirji, cikin mayen bacci tace please yaya bacci ta koma abinda

Shikuwa yaci gaba da tunani,a zuciyar sa yace gaskiya bazan bari kikai shekara 20 ba ina kallon ki, ahaka har yasamu nutsuwa tukun yaje yayi alwala, yakama nafila,,

Yauce ranar birthday su ameera ansha kwalliya,,kamar ba ita ba a felin gidan aka yi taron, birthday hadda su anas bilal sai kawayen ameera, Salim da nafeesa sai kawayen fatima da fauziya ana zaman jiran fitowar ameera

Ameera tafito tin daga nesa ameer ke kallon sanyi idaniyar tasa har suka karaso ,ta zauna kusa dashi

Aka soma, happy Birthday to you, aka yanka cake ameera ta sakawa ameer abaki,,tukun tabawa mom da Fatima sai fauziya,,tukun tayi taba nafeesa sai Salim zata bashi ya girgiza mata kai alama a a bata fuska ,tayi,

,Ameer kuwa yaji dadi, da salim bai bari tabashi abaki ba saiya karba yasawa Salim a bakinsa nan akasha shagali,,,ana kiran sallar magarib aka tashi

Bilal sai lashe baki yakeyi kamar tsohon maye, yace kai yarinyar nan akwai kaya ""

Anass yace wacce yarinya da sauri ya rufe bakinsa yace ba komai...

BAYAN SHEKARA TWO YEARS 2

Abubuwa dayawa sun cenja sosai a cikin wannan shekarun dan kuwa yanzu idan kaga ameera bazaka gane taba saboda girman da tayi da cika komai na mace ya bayyana ajikin ta masha Allah,,

Sauri take yi ta fito daga room din aji nafeesa na biye da ita da Salim,

Nafeesa tace ameera ina zakije kike sauri ko gamawa bamuyi ba banza tayi musu,

Salim yasha gaban ta,,yace haba ,Ameera wai lafiya

cak ta tsaya tana kallon Salim sai kawai ta fashe da kuka

Nafeesa ce, ta karaso tace maiya faru ne wai ?

jikin nafeesa tafada tana kuka cikin tashin hankali

Tace wani mugun mafarki nayi wasu mutane,,,ne da bakaken kaya suka biyo mu mida yaya suka kashe shi ni kuma suka dauke ni suka kaini, wani gida,

Bayan ta,Nafeesa ta shafa tace haba ameera duk kin tada mana hankali akan mafarki

Ameera tace wllh da gaske ne yau na fito zanje school naga irin mutanen, dana gani a mafarki na suna ta binmu abaya saida muka kusa zuwa ,,school suka dena binmu...

Salim yashiga office din ameer cikin damuwa

Ameer yace lfy dai salim ?

Salim yace ameera ce yaya sai kuka take yi amma taki yin magana, da sauri suka fita

Tana,,hangoshi tayi wajan sa da gudu ta fada jikin sa

Zuciyar ameer ce ta buga da karfi dan yasan bai taba ganin ta cikin wannan halin ba, yace ameera lfy ?

dagowa tayi tana kallon sa tace yaya babu abinda yasameka

Ameer yace eh wani abu kika gani ?

tace " eh nan ta fada mishi mafarki datayi harda,,wanda suka biyosu da safe,

Rarrashin ta yayi yasakata a mota sukayi sallama dasu Salim suka tafi gida

A hanya ne ameer yaga wata mota bak'a tana binsu saida sukayo anguwar su tukun motar tadena binsu

shiko ameer tunani yake yi to waye yake binsu haka,, da haka suka isa gida

Wani gardi ne babba mai jiki ,,da bakaken kaya yaciro wayar sa,,yace hello,,oga wllh yarinyar nan munkasa kamata, wannan dan uwan nata yana tare da ita kuma ba motar haya take hawa ba

Wanda aka kira da oga daga cikin wayar yace,,,aikin banza amma goje kabani mamaki yanzu wannan yar karamar yarinyar kuka kasa kamawa to nabaku nan da sati duk abinda zakuyi kukawo min ita nan kasan kuwa irin son da nake mata

Goje yace to,,oga kafin lokacin ma zan kawo ta nan ya kashe wayar,!!!

ANAN ZAN TSAYA NAGODE DA COMMENTS DINKU DA SHARE ALLAH YABAR MU TARE takuce har kullin MAMAN NUSAIBA ๐Ÿฅฐ๐Ÿฅฐ
[25/10, 23:45] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

11โ€”12

Suna zuwa gida da sallama suna,,isa,gidan. Fatima suka gani a falo

Tace,,sununku yaya

ameer yace yauwa Fatima mommy fa

,Tana ciki tabashi amsa

Ameera ta zauna jiki a, sanyaye duk tayi laushi kamar ba ita ba

Fatima tace lfy kuwa anty ameera ?

Murmushin yak'e tayi tace ba komai yunwa nakeji ga, gajiya

Fatima tace ayya Allah sarki to kije kiyi wanka,mana

tace to nan tayi sama,,

Goje ne da yaransa yace,,inason nan da kwana duhu'" ku kawo min wannan yarinyar dan idan bamu kamata ba to akwai matsala oga yace yabamu nan da sati daya,

,yaran suka amsa da to,

,yace aduk inda kuka ganta ku rufe fuskar ku kusato min ita

Sukace yes sir nan kowa yakama gabansa

Bilal ne zaune yana ta karatun jaki,,tunanin abinda yasan ba nashi bane yakeyi,,amma saboda bakar zuciya irin ta bilal,,da son zuciya,,ya qudurta a ransa ko ana ha maza ha Mata,,sai ya lashi zumar ameera, dan yasan yarinya akwai abin more rayuwa

Wata mata ce tashigo daga ganinta kasan mahaifiyar,,Bilal ce saboda kaman nin dasuke ,,da juna tace, my son lafiya,,naganka jiki "a sanyaye,

Ajiyar zuciya ,ya sauke yace ammi na babu,,komai,

Tace to shikenan tinda kace haka,,amma nasan da "abinda yake damunka yace babu fa mom tace,,shikenan kazo muci abinci yace to,,

Ameera kuwa tana hayawa sama,,Ameer yafito daga wanka daure da towel kallon sa take bako kibtawa,,

Iska ya hura mata yace yadai my heart

Lumshe ido tayi jin ya taba kafadan ta, ahankali yace to zo namiki wankan muci abinci

Ameera tace to ta cire, kayan jikin ta,

Shikuwa ya kura mata ido kamar wani soko yake kallon duk ilahirin,,jikinta juyowa tayi tace yaya muje, jin shuru yasa ta dauko towel din daya cire ta daura,takama hannun sa tace muje mana

Sai alokacin ya dawo daga duniyar tunanin daya lula, ya kama hannun ta suka yi toilet

Basu jima ba yafito da ita,ya sab'a ta a kafadar sa kamar wata jaririya,,

ita kuwa sai dariya take dan ita dai badai "son jiki ba kamar mage shirya ta yayi suka,sauka kasa,

A darning suka tarar dasu duka

fauziya tace, kaga miji da mata "

Dariya fatima tayi tace,,anty fauziya saidai kice ,Romiyo da Julio

,Ameera najin su ta boye abayan ameer, tana dariya ta ma manta da damuwar ta na safe,,

Murmushi daddy yayi yace to daughter fito mana muci abinci

kara shigewa tayi "jikin ameer tana boye fuskar ta a bayan shi,;

Shikuwa sai tabashi dariya

Mommy tace to kukoma sama tinda bazaku zauna ba

Ameer yace,,ameera fito mana yau kuma su daddy ne akewa kunya

Ta turo baki gaba tace,,nidai ba anty fauziya bace tace mana, wai miji da mata tana hararar inda fauziya take

Dariya sukayi

Ameer yace to shikenan ki kyaleta, zanyi maganin ta

Fitowa tayi suka zauna,,amma tana bakale da ameer

Kowa yana cin abinci amma ita ta hade girar sama da kasa,

kallon ta,,ameer yayi ya ja kunnen ta kara ta saki,

,mom tace lfy kike kara

shagwabe fuska tayi tace,,mommy kinga yaya ko,yake jamin kunne

Hade rai mommy tayi tace meye, naja mata kunne, iyee ,so kake ka cire mata,,kunnen ne yanzu zan rama mata, tana tashi daga kujerar ta wajan ameer tayo shikuwa ya dauka wasa take miki sai yaji,,anja mai kunne,,

Kara yasaki, yace ashh wllh mom zafi

Mommy 'tace ashe akwai zafi,,shine ita kake ja
mata "tana aika mishi harara

Dariya ma tabashi amma ya hadiye abinshi dan yaga ya sanyin idaniyar,,tashi zata yi "

Ita kuwa ameera kuka ta saki tana zuwa wajan sa ,,ta rungume shi,,

Da kallon mom tabisu da mamaki tace meye kuma na kuka bana rama miki ba,,

Ameera na kuka tace,,mommy ai bance ki jamai nashi ba kinga fa yaji zafi,,

Baki asake mom take kallon su

shikuwa ameer dadi ne ya ziyarce shi yasan matar shi na tausayin sa,, duk da shirmen ta amma batason,,wani abu ya tabashi,

Mom kuwa wajan ta bar musu dan idan "tabiya su shesu saka mata ciwon kai

Ameera tace am so sorry yaya, kaji,

Dagota yayi daga jikinsa,,yace ba komai ai kici abincin

cewa tayi nifa kai zaka bani,,tana turo baki gaba

Dariya yayi yace to oya rigimanma,,

dariya tayi Ta zauna

yace "ha,, ta daga bakin nan yaci gaba da bata,, harta koshi

Duk abinda suke yi mom da dad na kallon su abin,, burgewa mom tace daddyn su,,wllh yaran nan suna bani sha'awa,,

Murmushi yayi yace nima haka Allah dai yamusu albarka,,,tace ameen

Yau weekend ne duk suna gida kowa yana zaune ,,( sukuwa mutanen naku suna nan a waje daya)

Fatima ce tace hmm su yaya manya kennan

Kallon ta kowa yayi ,,Harara ameer ya aika mata yace ke ina wasa, dake ne,

Ameera tace ina ruwanki,,yar sa'ido,,"

Fatima tace kuyi hakuri,,fa gani nayi kuna wani dunkule,,da juna kamar wani maggi,,dunkule ,

,Dariya fauziya tayi tace ,fatima kennan kaidai ba'a, rabaki da tsokana

Mommy tace kundai jidashi,,duk kubi kudami mutane, da shegen surutun tsiya

Murmushi ameer yayi yace to mom ai kawai kibarsu, suyi wata rana zasu dena

fauziya tace hakane fa

Ameera tace sai munyi wata ashirin da goma zamu zama manya kamar anty fauziya ko,mom??

Mommy tace eh ameera

Fatima tace
Idan nazama babba zakuga yadda ake daukar wanka dariya tabasu,, wato ke daukar wanka ma ya dameki,,tace a a 'idan nayi aure fa "

Ameera tayi caraf tace,,tab wama zai aure ki da bakiyin wanka kullin,,,jiya fa ina matsawa,, kusan ki naji kina,,warin daud'a ,,

Ameer ne ya kwashe da dariya yace kai, amma kin iya wulakanci

,Fauziya ma dariya take dan yau, tasan akwai dambe a gidan nan

Ita kuwa fatima ta shaka dayawa,, sai hura hanci sama,,takeyi tana kunbura baki,,tace yarinya inba tsoro ba zo mu fidda reni mana raguwa kawai, sai cika baki ai nasan yanzu ke raguwa ce,,

Aikuwa ameera taji ciwon ce mata raguwa da, akayi ta mike daga jikin ameer,,

Ameer da fuziya babu abinda suke sai dariya dan yau zasusha, "" kallon a falon nan

Fatima ma tashi tayi ta ,nade kafar wandon ta,

Ameera ma ta nade ,nata nan aka kama ,,

Dama mom ta jima da ficewa "'ita da dad!dambe aka kamayi dama fatima cika baki ne tayi, da taga ameera zata fi karfin ta kawai ta fisge, rikon da ta mata ta saya ata kare,,suka soma, zagaje falon

,,fuziya na dariya hadda rike ciki take ganin yadda yanzu fatima take cika baki amma taji riko,,irin na ameera,,kawai ta ware,,suke zagaye,,

Ameer ma dariyar yake ya maidasukamar,,tom and Jerry,,

Waje Fatima tayi ameera ta bita, suka ringa zagaya gidan

Mai gadi. ne yagansu shima dariyar yayi dan yasan ,idan suka hadu duk week sai anyi wannan damben,,

Fatima ce tagaji ta tsaya tace please antyna nagaji haka

Ameera kuwa damkar rigar fatima tayi,, suka soma dukan juna,,,

Mai gadi ganin bazasu dena ba ga kuma fatima ta gaji yasa yaje inda suke yace,,haba ameera ta ameer kubari mana

Ameer ne yafito yace wai ku baku gama fadan ba ne

Su anass ne da Bilal suka sayo motar su cikin gidan ,,,tsayawa sukayi da,,fada,

,Fatima ganin ansake ta yasa ta koma bayan ameer tana haki,

fitowa su anass sukayi suna kallon su anas yace

Wai lafiya na ganku a tsaye dariya Bilal yayi yaji dadi zuciyar shi ganin ameera kuma ba dan kwali gashin ,,kanta yayi baja baja,,sai zufa take tana hura hanci

,Ameer yace babu komai ai kasan agidan nan muna da yan dambe

Dariya Bilal yayi yace kai gaskiya zanke zuwa gidan nan ina kallon tom and Jerry

Harara ameera ta banka mishi ta koma bayan ameer

Fatima kuwa tuni abar wajan,,

Ameer yace to kumuje,,

Ameera ta makale

Ameer yace my wife cika ni mana muje ciki, kiyi wanka,,

Ameera tace to nan,,suka tafi

'"Bilal ko duk hankalin sa akan ta, yake ,,yana so yasamu,,,hanyar mallakar ", Ameera dan ba hakuri zaiyi ba,,( kai jama'a kunji fa karfin hali awajan,,Bilal wai barawo da salla ma)

Suna shiga suka gaishe,,da mom ta fito zata yi kitchen nan sukayi sama ',,

A falon sama suka zauna,, dakinsa ameera ce take wanka,, suna hira,,ta fito ta sunkuya,,,tace ina yininku ""suka amsa da lafiya lau,,,nan sukayi ci gaba da hirar su

Yau da wuri suka tafi school suna zuwa, suka hadu da nafeesa, da Salim suka gaisa da su,,

ya fice " office dinsa suma suka shiga

.Bayan sun tashi ne sun fito ameer suka gani fuska dauke da damuwa,,

Ameera takarasa garesa,,tace yaya lfy,

yace yau zan bar wannan school din,

Ameera tace sbd mai yaya

yace nagama dama saves ne nake kuma lokacin da aka dibamun yacika yanzu sai aiki zan soma,

,Cikin murna tace alhamdulillah yaya Allah yakawo maka aiki mai anfani yace ameen ,,

Su nafeesa suka musu sallama suka tafi suma gidan suka nufa,

Bayan sun huta ne yake cewa,,su mom yagama saves din sa, yanzu sai aiki, zan fara suka mishi fatan alkhairi da addu'a,,,

Goje ne yake waya yana cewa, oga,,yaron nan fa yau yabar school din

Daga cikin,,wayar,,yace very good yanzu kunsamu damar daukota ,,,goje yace eh oga yace to kubari,,kuga ina zai koma "da aiki yace to oga,,saika jimu,,nan suka aje waya

Bilal ne zaune,,yanzu ameer yakira shi yake ce mishi yagama,,saves sai aikin sa zai kama,,,nan ya mishi,,fatan alkhairi yanxu kuma yanason yadda zai kulla alaka da ameera, saboda tasaki jiki dashi murmushi yayi saboda yasamo solution,,,yace "yes yauwa wannan hanyar tayi,,

FAN'S bafa Bilal bane yake bibiyar ameera yake so akamo mishi ita ,,,shi yanzu,,baima soma neman hanyar dazai kamata,,ba

Da Dare su ameer sun kwanta ameera ce,, cikin baccin ta,,tasoma mafarki,,,

Ganinta tayi acikin,,wani "daji mai yawan bishiyo murya ameer,,takeji yana kiranta inda muryar take magana ,tabi tana bin gindin bishiyoyin,,

Ameer tagani wasu mutane sun rikeshi yana cewa please ameera kada kibari,,,su rabamu

cikin kuka tace,babu wanda ya isa ya rabamu yaya ameer!Bata idar ba wasu mutanen sukayi baya da ita, tana ihu tana cewa,,yayaaaaa???karka bari su rabamu please banason ,rabuwadakai

Ameer cikin bacci yaji muryar ameera tana cewa,,kada yabari a rabasu,,cikin kidima,, ya tashi yaga har ta fado daga gadon,,tana tirje tirje sunkuyawa ,yayi ya sunkuce ta yayi kan Bed da ita iska yasoma hura mata nan ta bude idon ta,, tana ganinsa,,ta shige jikinsa,,,ta fashe da kuka mai tsuma,,zuciya,,

Bayan ta yasoma bugawa saida tayi, mai isar ta, san nan tace yaya

Dagota yayi yace na'am,,,

Tace babu abinda yasameka ko

,,yace, babu 'komai, maiya faru, nan tafada mishi abinda tagani a mafarkin ta

Murmushi yayi yace ai mafarki ba gaskiya bane , kinyi addu'a dazaki kwanta,,

Tace nayi yace to muje ,, kiyo alwala muyi nafila kinga ankusa asuba,,,tace to nan sukayi toilet,,

THANK YOU SO MUCH FOR COMMENTS AND SHARE muhadu a gobe insha
[26/10, 19:34] MRS. MU'UTASIM: https://chat.whatsapp.com/Gu2Mxr0SRlx8Da4tv0J2AR

๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

*13โ€”14*

Basu,jima ba sukq fito, tayar da nafila sukayi "suna gamawa,,aka kira "'salatul fajir ""nan ameer yace,,Ameera bari naje masallaci,, fuskar tausayi tayi tace,,nidai yaya banaso,, kafita ""wani abu yasameka,,,

Zama yayi akusa da ita hannun ta yakama yace ,My wife ki kwantar da hankalin ki babu abinda zai sameni kinji,,bana son, kina saka damuwa a ranki,,,

Kallon sa tayi

Murmushi ya saka mata mai saka nutsuwa,,,

Itama ta mayar masa"" tace to insha Allah ya Allah ga bawanka,,, Allah dan sunayenka,, tsarkaka ya rabbi ka kiyaye min shi,,, duk inda yaje,

Dadi ne yakama ameer yace amin ya Allah my heart dina,,,nan ya fice daga dakin,,, yayi kasa daddy ne yafito,,suka tafi

7AM su Fatima suka fito daga dakinsu suka gaishe da su mom amsawa sukayi,,cike da kulawa murmushi daddy yayi ya kalli Fatima yace,, auta abokiyar dramar taki bata tashiba""

Murmushi tayi tace daddy kila suntashi,,saukowa ce basuyi ba mom tace gasu nan ma

Karasowa sukayi cikin falon,,,Ameera tace good morning daddy and mom ""amsawa sukayi da morning my daughter,,

Ameer ma ya gaishe su shima suka,, amsa mishi nan aka soma cin abinci ""

satar kallon juna sukeyi,,

mom na murmushi tace to kuyi sauri kuci abincin mana

Kunya ce takama ameer ya juya,

Ita kuwa ameera so take yabata da kanshi , tayi kicin kicin,, da fuska kamar zatayi "'kuka

Daddy ya kula da hakan,, yace " daughter yadai ?

Kallon ameer tayi

Daddy yace,,, to kai ameer mai ka mata,?

Da mamaki yake kallon daddy yace wllh babu abinda namata ,,,

Ita kuwa ameera jin yace haka ,,,aikuwa sai hawaye suka soma zarya kan fuskar ta,,

Cikin damuwa mom tace ameera lfy ?

kuka ta saka

Ameer ya janyota jikinsa bako kunyar su dad da mom
saida tagama

Mom tasake tambayar ta wajan mommy takoma tana kwanciya kan kafadar mom bubuga bayanta ,,, take har ta dena kukan

dagowa tayi tace mom "amsawa tace da na'am daughter

,,Ameera tace bana son, surabani da yaya,,cikin kuka take maganar,

,ita kuwa abokiyar dramarta wato Fatima ,,itama tuni tasoma kuka,,saboda tana son ameera,, shiyasa data soma kuka itama tasoma nata kukan

Mommy tace waye zai rabaku nan ameera ta fada mata mafarkin da takeyi harda motar da take binsu kwana biyun nan,

Salati mom da dad suke,,kallon su suka maida ga ameer,

Dad yace son da gaske ne ana binku,,idan kunfita

Ameer yace eh daddy ,, amma bansan waye ba

Daddy yace,,,zankai,,report,,wajan yan sanda suke "' saka ido akanku,,, nan suka tashi ameera tayi sama

Anass ne ya kira abokin nasa ,,yace hello my friend

Dariya ameer yayi yace na'am ,yakake yace alhamdulillah,,, Ameer yace aboki inason ganinku inason muyi magana,,"wata matsala ce ta taso

Anass yace to shikenan,,nan sukayi sallama,,, haka yakira , Bilal yace zasuyi, magana "shima yace to ,,su hadu a gidan, su ameer

Yau sun fito,,, daga cikin aji Salim yace ameera wai jiya yaushe,,,kika dena kuka"" yana murmushi,, ya idar,, da maganar shi

Ameera tace ai nadena

Nafeesa tace wllh bestie jiya kinsaka mu,cikin damuwa, da harnace 'idan baki zoba zan je gidan ku,

Dariya tayi tace ' babu komai kada kudamu,,suna a haka direba yazo daukar ta nan sukayi sallama, ta yi wajan direban ta gaishe sa nan suka bar wajan

Su ameer da anass da bilal,,zauna suna gaisawa suka ce mishi ya akayi,,

Ajiyar zuciya ameer" yasauke yace wasu mutane ke bibiyar ,rayuwar mu

Atare sukace ,, what??

Anass yace suwaye ke binku ""

Bilal ma tashin hankali yashiga,yana tunanin to waye ke wa, abokin nasa barazana,,, da rayuwa,,,nan suka shiga jajantawa""

Suna nan ameera yashigo gidan a,, firgice,,sama tayo tana cewa,,yayaaa ina kake,,,waiyo ni ameera nashiga uku na,,tana kuka ,,ta haya samar,," kara kiran sunan sa tayi da cewa yayana,,shikenan sun daukemin shi ""

Da sauri ameer yayi falo jin tana sambatu,,,wajan ta yazo daga bayanta dafata yayi,,da sauri ta mike ganin ameer ne yasa tasake rufe idonta, dan tabbatar wa shi din ne dai da sauri ta zagaya inda yake ta rungume shi yana kuka, tace alhamdulillah Allah nagode maka daba'a sacemin,,,yaya ba

Tausayi tabashi,,yace menene ?

Sake shigewa tayi jikin sa,,

Su Bilal ne suka fito shikuwa Bilal ganin ameera yasa yaji sanyi aranshi dan yanzu ba karamin,,, so " yake mata ba sai kuma tabashi tausayi ganin yadda take kuka da gaske,,,

Anass yace aboki lfy wai,,,

Kallon sa ameer yayi da fuskar tausayi ,yace nima bansan me tagani ba najiyo muryar tadai,,tana cewa wai ta shiga uku ansace,,ni,,

Cikin damuwa Bilal yace ameera please maiya faru a school din ,,,

Dagowa tayi tana k'are musu kallo,, da tazo kan Bilal ta aika mishi harara ,,, dariya ma tabasu""murmushi sukayi yace to shikenan,,, fada mana kinji yar kanwarmu ajiyar zuciya ta sauke tace,,

Alokacin da muka taso daga,,school na fito bakin get ""sainaga wani,,mutum babba kamar irin na tv,,, yana kallo na sainaga yaciro waya,,, yana magana kasa kasa bansan mai yace,,ba na fice na siyo buskota na,, najuya kadan, "sainaji yace eh oga kaganta,,nan tafito amma wajan,,, akwai mutane sosai bazan iya sace taba,,, bansan ""mai na wayar yaceba sai,,yace oga saidai mubisu,,,abaya idan suhau,,, kan titi ,,saimu kwamushe ta kaga idan ameer yaga haka zai zo da kansa wajanmu saimu kashe shege ita kuma mukaiwa oga,, ko

Ban tsaya jin sauran ba maganar ba nayi sauri nacewa,,baba direba yayi,, sauri ""mutafi,, nan muka taho"" tinda mukayi nisa nake kiran wayar,,,ka baka dauka,,, hankali na ya tashi sbd bana,, samunka,, bamu jima ba mutanen nan,, suka biyo mu abaya nacewa,,baba binmu akeyi yakara gudu suma suka,,,gudu da sukaga haka shine suka harbi motar mu amma basu same,,mu ba,, ana haka cikin,, ikon Allah wata babbar mota tashiga tsakanin mu dasu,, shine baba yayi sauri muka karaso,,gida, takai karshe maganar. tana sake komawa jikin ameer tasaki wani,,, sabon kukan mai taba zuciyar mai karatu

Anass yace dole naje office nasaka yara na su binciko,, wannan mugayen mutanen

,Bilal ma yace nima zan tayaku bincike sosai sukayi,, ta alhinin,, lamarin tukun suka tafi gida har waje ameer yaraka su

Ameera na makale dashi wajan, baba direba yaje ya tambayesa abinda ameera tafada mishi haka shima yafada mishi duk abinda ameera tafada mishi

Komawa ciki dukayi sama sukayi don ya kwantar mata da hankali,,tadena damuwar

Koda su Bilal suka fita kowa da tunanin dayake sakawa a ransa Bilal na mamakin, waye wannan ke takurawa ameera,,

Shikuwa Anass tunanin yadda zasu bullowa lamarin,, yake (saboda,,shi, anass police ne kuma babba shine D,P, O a cikinsu )

Suna zuwa ya zaunar,,da ita ya dauko ruwa,, yabata tasha taji sanyi kuma,, kirjinta "yadena mata zafi ""kayan school din ya cire mata ya cire takalman,,, tukun ya sauya mata wasu toilet yayi,, yahada mata ruwa,,, yace tashi kije,,,kiyi wanka tashi ""tayi, taga ya zauna tace muje kayimin,,,

Ameer yace to nan sukayi toilet,,, bayan sun fito,, bata jimaba bacci yadauke ta shikuwa zama yayi,,yana kallon ta cike da so,, da kauna dakuma tausayin,,halin da take ciki,,

Ameer ne yasamu daddy da zancen abinda ameera ta fada miki "da kuma tashin hankalin, data shiga ,,

Damuwa ce kwance,, akan fuska daddy and mom,,

mommy tace wai ni na rasa,, waye yake,, neman rabaku da nutsuwar ku,

,daddy yace,, ai yanzu na kira Anass nake fada,, mishi nan ya shedamin,, cewa,,suna nan lokacin da ameera tashigo,, gida a firgice,,

Mom tace ina take ameer yace tana sama,, basu rufe baki ba ta sauko fuskar nan ta kunbura,, idon ta yayi ja saboda kuka

Mommy tace zonan daughter

Ahankali taje wajan,,mommy tasaki kuka tace mom wai mai muka musu ne suke damun rayuwar mu,,

Rarrashin ta ' mom take saida tayi shuru
mom tace kiyi shuru ai yanzu mun sanar wa da yan sanda komai insha Allah babu abinda zai faru

Da dare bayan anci abinci to dama gobe ba school suma,, su fatima da fauziya,, sunji ""komai gashi ameera takasa cin abinci sai kuka duk inda ameer yayi tana,, makale da shi kowa agidan yana cikin damuwa,,,

Cen fatima ta je wajan ameer tace yaya ahankali dan kar ajita tace yanzu zan saka anty ameera farin ciki,,

ya kalle ta yace to tayaya fatima ?,

Tace kaidai bari kagani,, idan kaga ta warware,, to kace muyi kafce irin film kai zaka dauke mune a wayar ka,,, murmushi yayi yace to

Duk abinda sukeyi,,su mom najinsu "'kuma sunji dadi da fatima zata saka ameera farin ciki,,,

Fatima taje daf,,da ameera tace antyna wai kin manta gobe,, week ne kin manta ""da damben mu

Tashi ameera tayi kowa kallon ta yake tace kinga na manta to gobe mai zamuyi idan mukazo yin damben

Dariya,,Fatima tayi tace ""yanzu zamu soma ne

Ameera tace,,da gaske

Fatima tace eh yau kafcen film zamuyi nice matar gida,,, kece mijin "'

Dariya tayi,, tace to shikenan amma na kauye zamuyi

ganin tana dariya yasa ameer cewa,, eh a kafta mana,, na kauye suma su mom sukace eh,, muna so

Ameera taje dakin su fatima ""da dauko kayan kwalli tayiwa fatima,, itama tayi,, na kauye ""

Su fatima ansha bakin baki da wata gira kamar zamiyar zakara,,

Dariya duka falon sukeyi

Ameer yafiddo wayar shi yace idan na kirga uku saiku soma sukace to,, nan yace,, daya ""biyu ""ukku...

Ameera ce ta nada wani mayafin ta akai wato alamar malam,,

ita kuwa Fatima ta yafa wani zani itace matar gidan zama tayi tana daukar kwanon gabanta tace,,
Kai nima Allah yahadani da miji mai shegen rowa,,, kalli fa wannan dan amincin ,, to ko ni bazai,, isa ba na koshi,, bare yaran nan da suke ""dab da dawowa ""daga islamiya,

Ameera ce ta bude ta fito daga inda ta rufe kanta da labule,,tayi gyaran murya,,,

Fatima ta banka mata,, harara,, tace haba malam wai ni kai wani irin wulakanci ne wannan,,

Ameera ta kalli fatima tace, ban gane ba kefa Wllh jummala bakida godiyar,,,Allah kullin sai kinyi masifa duk makota na jinki sai zaginki,,,ake yi a anguwa

Mikewa Fatima tayi tayi tsukiya da zanin data yi lullubi dashi,,,tana jijjiga tace,
Iyee to sannu malam nace sannu bakin munafuki,,,algungumi kennan zuwa,, kake kana bazani "a gari ko to wllh yau bamai rabamu nidakai

Ameera tace,,kinji dai dashi masifaffiyar,,, mata kawai kullin idan zan shigo gida har gabana faduwa yake yi saboda fitinarki,,

Fatima tace to,, baka isa kaci abinci agidan ba

Ameera tace wannan kuma ya rage naki,, sakarya kawai,, aure ma zan kara na huta dake,,

Fatima ta cakumi rigar ameera ,, tace wllh kayi kadan baka isaba,, kayi min kishiya...

Dariya suka kwashe ,, dashi har su mom da dad fauziya kuwa dama ba'a magana

Ameer ne,,, yace wannan kafce yayi kuzo mugani nan aka zauna gani sai dariya sukeyi,, hamdala kowa,, yayi "' ganin ameera ta dena damuwa

Hhhh bari dai na hau mota naje na gano hajiya inna ikon Allah,,

Inna ce zaune ita da abbu sai fada take kamar ba gobe ,, tace bukari,,wllh kakaini kano yau ko na tafi dakaina,,

Abbu yace kiyi hakuri inna ai ameera takusa zuwa hutu,,, fir inna tace batasan zancen ba

Umma dataji taje bata baki tass,, ta wake ta da ruwan masifa tace wai ni sadiya wllh daba a hannuna kika haifi ameera ba sainace bake ce uwar ba,, yoto inba shirme ma ba hadda zuwa bani baki to bazan jiba

Abbu ya ce to inna fito mutafi da murna taje ta musu sallama hajara ma tace saita je

Inna tace yauwa zo mutafi ba yadda umma ta iya tabar hajara suka tafi sai kano tadabo....

MUHADU a gobe insha Allah domin taryar hajiya inna zata je birni

Kuyi comments da share
[26/10, 20:11] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

15โ€”16

Daddy ne,,,zaune shida mom sauran yan gidan duk suna daki "" Abbu ne ya kira daddy,,,a waya yana,,shida mishi zuwan"" hajiya inna,, murmushi daddy yayi yace ,, eh lalle Abubakar ""kace yau munada manya,, baki agidan nan" dariya shima abbu yayi yace wllh tinda,,, su ameera suka "" koma kullin inna saita zageni tass 'tace naje nakawo mata diyar ta wai munsiyar ,, mata jika

Dariya daddy "" yayi yace,,,to muna kallon hanya bari mutanadi tuwo da miyar"" saboda kar a sauke mana gajiyar,,hanya, ahaka sukayi sallama

Su ameera kuwa,,ana kurya "adaki sai dariya take saboda video su na jiya da suke kallo,, ita da ameer ,,,tace yaya , kallon ta yayi ya mata murmushi,,, tace wllh video nan yaban nishadi,,, musamman ma "" inda fatima take cewa wai ban isaba na mata kishiya

Shima dariyar yayi dan yaji dadin ganin yadda take cikin jin dadi ,,, yace nikuwa kinsan ina yake bar dariya,,, tace a a ""yace inda kike cewa fatima masifaffiyar mata kawai,, aure ma zan kara na huta,, da masifar ki ""

Dariya sukayi a tare ,,, kiran wayar shi ne ya katse musu hirar dasuke ,,, ganin mom ne yasa yayi saurin tashi daga kwanciyar da suke ,, ita kuwa mage lafewa tayi ajikin sa dan ita dai,,, a rayuwar ta tanason"" kwanciya,, a jikin ""yayan nata,, kuma mijin ta,,

Ameer yace, hello mom sai kuma yace, batayi ba,,, yace ok gamunan,, sauka,, nan yakashe "" kallon shi tayi tace yaya wanene,, yake kiran ka ,, kumatun,, ta yaja yace "my wife mom tace mu sauka zata mana albishir, mai dadi da sauri ta mike tace to muje yaya nan suka sauka

Anass ne zaune,, a office yana tunanin ""ta ina zai fara wannan bincike,, kofar ce aka,, buga "" nan yace yes come in ,, wani dan sanda,,, ne yashigo"" yace good morning sir,, amsawa yayi da morning "

Anass ya tsuke fuska kamar bai taba dariya ba yace ;,, ishaq, ina son ka binciko min sashen Camara bakin babban titin,, dazai sadaka da unguwar nasarawa J. R.A. yace yes sir ya kame,, tukun yabar wajan

Hajiya inna ikon kennan,,kakar, *AMEER DA AMEERA*,,, ankaraso kano""ta dabo ,, sai raba ido take,, tace kai "" Rabe to amma,, dai baka kaine gidan Muhammadu,, din ba ko

Murmushi ,, rabe yayi yace kai inda kin ,, cika surutu,, ai gamu a anguwa,, mun zo gidan ne "' dai bamu karasowa,

caraf inna ta,, amshe zancen,, da cewa ""saidai in uwarka ce ladidi,, mai surutu,, gaka nan kagirma "kazama gardi ba ,, aure ai wllh su ladidin su suka kyaleka,, yoto,, dama wacce '" yarinya zata soka a haka garjejen basamude,, ai dole ""mata suke tsoronka,,, dan iska,, marar mutumci,,,wllh yanzu ""sai infita,, in kakkarya maka,, kafafu,, hadda cewa,, wai nacika,, surutu,,,

Shikuwa ""dariya yakewa inna wai shi, zata karya,, hadda kiransa,, da basamude, kai tsohuwan,, tacika neman masifa,,

Suna zuwa wajan,, mom suka zauna a falo ""nan mom take sheda musu,, cewa inna tana hanya ""dan har ta saka mai aikinsu tayi Mata,,tuwo da miya ,, aikuwa ameera kamar tayi waje ta taro inna haka take ji

Shikuwa ameer bata fuska yayi sbd yasan halin inna yanzu nan zata ce ameera awajan ta zatake kwana shikuma bazai iya kwana a daki ba batare da ameera

Karar mota ne yasa,,Fatima da ameera fitowa,,, da gudu domin tarbar inna,,,ita kuwa inna fitowa tayi tana karewa gidan kallo nan sukayo kanta, suna oyoyo granny,, kallon su tayi taga Fatima da ameera ,, itama murna tayi ""na ganin ameera nan sukayi cikin gidan da sallama suka shiga ciki,,

Mom ce ta tashi tana yiwa inna sannu dazuwa nan aka kai kayan inna dakinsu,, fatima ta hada mata ruwan wanka

Bayan tayi wanka ne ta zo falo daddy yafito yana,,murnar ganin inna,,""Inna tace ai nadauka siyar min da jika kukayi,,ashe tana nan lfy

Dariya sukayi"'ita kuwa ameera tana zaune kusa da inna sai dariya take tace kai inna nafa ce miki,, babu wanda yasiyar dani ina nan

Ameer ne yashigo yace ,, kaka sannu da zuwa tace yauwa ameeru

Bata,, fuska yayi yace haba inna ""meye kuma ameeru

Harara ta aika mishi"" tace bansani ba dan butar uwa,,

Dariya yayi yace su kaka anga birni filo ta jefa mishi,, tace ""eh angani din ai dai gidan danane,, dariya sukayi dukkansu

Ameera ta baro kusa da inna tadawo ga ameer,, shikuwa ya janyo ta jikinsa,, ko a gwalar rigar yana mata zance da rada

Inna kuwa salati tasaka,, tasanarwa""Allah tace a ni maryama,,wannan lalacewa har haka takai wato ka koya mata iskanci ko

Dariya sukayi ameera tace inna aiba komai

Inna, tasoma,, fada tashi sukayi "'asace suka gudu sama

Binciken da ishaq yayi ne ya shigo office din,,yace sir,,

Anass ya kallesa yace yaya andace ,,, ishaq yace sir gashi "'nan yaduba computer yaga,,wasu mutane ne guda hudu har wajan da suke biyosu ameera,, amma abun damuwar shine,, basuga fuskokin suba

Anass yayi iya kokarin sa dan gano "fuskokin mutanen,,,nan yace jeka zan nemeka nan yayi gaba abinsa

Su bilal kuwa masu ciwon son hauka yau a zaune yake ya rike waya a hannun shi da alama,, bai jima da gaba waya,, ba,, Ammin sa,, ce tashigo tasameshi ya juyo tace magana zamuyi,,

Ganin ba wasa ""a fuskar ta yasa ya tattaro hankalin shi baki daya,, akanta""

tace son yakamata,, kayi aure nan ya tsuke,,fuska ""yace haba ammi na "',nifa yanzu ina cikin,,tashin hankali ""

Ammi tace maiya faru,, nan yafada mata,, matsalar su ameera da ameer "'ya kai karshen zancen da cewa, ammi wai kinsan"'ma meye abin daure kan , tace a a saika fada yace ankasa gano ,, ko suwaye ke bibiyar 'su ameer musamman ma ,, ameera narasa maita,, tsare musu suke binta har school ammi

Ajiyar zuciya ta sauke tace ,,, lalle abin nan akwai rikitar wa to kun tambayi shi ameer din bashida abokin fada,, Bilal yace gaskiya babu,, mun tambaye sa yace shi bashida abokin fada,,

Ammi tace Allah yakiyaye su daga shirrin ko waye da ameen Bilal ya duk,, ranshi babu dadi sbd ganin abinda ke faruwa ,, da abokin nasa,,, nan ammi ta fito daga sashen sa

Wani gari ne babba amma ba sosai,, ba (wani babban gida na shiga dan kawo muku rahoto ) mutane ne sosai a wani daki,, baka jin komai sai kukan,, mutanen dake "" wajan kutsawa nayi wata mace nagani matashiya wadda batafi 22years ba a, kwance ga jaririya,, a gefen ta sai wani namiji da dan karamin yaro sun,, rungume,, matar suna kuka,, mai ""sosa zuciya wato, da alama mutuwa tayi ,, yaron ne yace mommy please kitashi,,, yana kuka duk wajan yabasu tausayi sosai ""namiji dake rungume da ita yace haba jenifer maiyasa zaki tafi kibarmu please ki taimake ni ki tashi kiga yaran mu gasu nan a kusa dake ,,, amma ko motsi bata yiba wata tsohuwa ce tace my son,, comedown mana please,, itama kukan take dan ba karamin rashin suruka tayi ba ,,,

Dagowa yayi yace mama kice mata ta shi karta barni janyeshi tayi tace jesus,, ya albarkace ki jenifer ,, nan aka dauke ta sai aka sakata a cikin akwatin karfe sukayi wajan botarsu da gawar ta suna ta surutai irin nasu kai da gani kasan ba musulmai,, bane

shikuwa mijin nata,,babyn dake kwance ya dauka tana kallon sa yanzu tadena kukan sai kalle kalle da takeyi hawaye,, yashare yace little baby,,, ni nasan maman ki bata mutu ba wata rana zata dawo garemu,,, shiyasa suka hanani,, tafiya ya kara goge hawayen fuskar shi akaro,, na ba ""adadi abin gwanin ban tausayi

Inna ansamu hutu tace aikuwa,,, bazata koma kauye ameer yace,, dama ai ""kece gardama,, saida daddy yace kidawo,,, nan amma kika,,, kiyarda"

'tace to ina ruwanka,, ka shigo maganar daba taka ba

yace Allah yabaki hakuri nan yabar falon yayi sama

yau ameera,,,cikin fargaba take shiryawa gabanta sai faduwa yakeyi sosai ta rasa nutsuwar ta,, ahaka ameer yabata baki yace babu abinda zai sameshi hakuri kawai tayi ta danne zuciyar ta tafito,,, shi da kanshi yaja su zuwa school din daga cen zaikai,, takardun sa na neman ""aikin likita dan shine abinda ya karanta kennan

Suna isowa school din su nafeesa suka taresu suka gaisa

Salim yace yayan mu yanzu,, kuma kabar school "dinmu

Dariya ameer yayi ,,, yace,, eh mana dan kanina"" yanzu ma zanje,, yin aikin ne nan sukayi sallama ameera taje tamiki kiss a mukatu yace mutane fa na kallon mu dariya,,, tayi tace to shikenan Allah yabada saa yaya ameer yace ameen wife na nan yafice

Yaron goje ne yaga,,, fitar "" ameer yace oga yaran nan fa yanzu yakawo ameera school,,, din kuma yatafi "" ogan yace to ka tsaya a tashi idan ta fito kafin yazo ku dauko min ita,, yace to oga angama yau ai nasara tamuce nan ya kashe wayar yakoma kauye yazauna

Anass ne ,, yasamu ameer a waya yace frend idan ba damuwa kadawo daga internet din kazo inason baka wani abu yace to ,,, bai jima ba sai gashi yazo nan,, yanuna masa mutanen ""daya saka akamishi bincike amma ankasa gano fuskar su

Cikin damuwa ameer yace to yanxu menene abin yi ameera na school,,

Da sauri Anass yace what?
Ameer kana da hankali kuwa maiyasa kabari taje school

Cikin kidima yace aboki da matsala ne

yace babba makuwa ai yanzu ishaq yacemin yaga wani daga cikinsu a bakin get din school

cikin tashin hankali,,Ameer yace to bari nayi saurin zuwa daukota yanzu saura minti 10 su tashi da sauri anass yadauki bindigar sa yasaka a cikin aljuhunsa da alburusai yace let's go nan sukayi waje shima ishaq binsu yayi suka fita su uku

Bilal kuwa yana zaune agida kawai saiya kejin kamar akwai abinda zai faru da abokin nasa bai gama zancen zuciya ba,,, Anass yakira cikin sauri yadauka,, yace frend tell me naji kamar akwai matsala,, Anass yace babba makuwa ,, kabar komai kataho school din su,, ameera tinda kafi kusa da school din yace to

Ita kuwa ameera bayan sun fito da frend din nata yau she suka rigata tafiya ga kuma ta kashe wayar ta ameer na kira amma a kashe kamar zaiyi hauka yace wayar a kashe take

Tana nan zauna da school back din ta a bayan ta sai cika take tana batsewa saboda yunwa da takeji fitowa tayi waje tana waige waige a tsorace take batayi auneba aka shafa mata wani dan kyelle a fuska nan take ta zubai a kasa shikuwa yana ganin haka yayi maza ya dauketa yasaka ta a mota babu wanda ya lura dashi ya fice abinshi

Yana barin layin su Anass a tare suka iso da bilal school din suka gani har anrufe babbar kofar

Ameer yazube a kasa yasaki wani kara yace,, no ameera no no kada kibarni

Anass ne ya tashe sa yace bari mu tambayi mai gadin ko tana ciki bacci take ne

MUHADU a gobe insha and kuyi comments da share din labarin mu
[26/10, 20:37] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฃ๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„ โœ

17โ€”18

Ciki,suka shiga suka tambayi, " mai gadin ,, cewa baiga ameera ba ,,,

Yace gaskiya yallabai"" Ameera tajima da fita ita da kawarta,, da wani namiji ,,,

Anass yace baba bakaga ko ta dawo ba yace a a gaskiya nan suka yi mishi sallama. Suka tafi gida,,

Suna tafiya dukkan su,, bamai magana acikinsu,, kowa da abinda, yake sakawa aransa ga tashin hankalin. Dasuka shiga. suna shiga daddy,, ya tarosu"" yana tambayar su,,ko sunganta,, ne sukace bamu ganta ba gaskiya

Daddy tashin hankali Sosai sukashiga, zama sukayi a falon,,

Mommy tafito itama hankali a tashetake tambayar su ameer nan suka,, mata bayani share hawaye takeyi tace ,, ya Allah katona duk wanda. Yake. Da sahannun,, sa aciki sukace ameen.

Inna ce tafito tana hura hanci. Tace kai ameeru ina ameera. Ne ,

,kallon ta ameer yayi sai kuma Sadda,,kai sai ya fashe" da kuka,,

Inna tace ,, kai jama'a ni maryama,,, to kaikuwa,, wllh ankai ragwon banza.

Ameer yace inna ansace min matata. Itace farin ciki na,,,

Mom ce tadawo kusa da shi tana shafa"""bayansa

Inna tace nashiga uku ni. Maryama,,, waye yasace"' min jikata,,,

Anass ne yace daddy bari naje nakai rahoto gidan radio daddy yace to yafice daga gidan,,, nan inna ta fashe da kuka mai ban tausayi su dukansu"" kowa a cikin damuwa yake ,,

,Ameer yace mom zuciya ta kasa yazamo ya daura kansa a a cinyar,, mom tana shafa kanshi yace,,

Mom mutuwa. zanyi idan suka tabamin "matata itace farin ciki na ameera tana min soyayyar da babu abinda,, zai tabamin"" itaba mommy,, kirjina zafi yakemin inajin kamar, zuciya ta. zata faso kirjina ta fito ,,, kokarin tashi yakeyi "" kawai saiya zube akasa nan sukawo kansa amma babu,,, numfashin a jikinsa a kidime"" sukayi waje sai asibiti

Bude idonta,, tayi " taganta, a wani daki,, nan ta tuna da binda. Yafaru da ita. ""Tsoro ne yakamata tace ku suwaye da kuke neman saka rayuwa ta a matsala

,,kwashewa,, yayi da dariya yace ni bani bane oga na ne zaizo,,,, bai gama bata. Bata amsa ba wani matashi yashiga shikuwa Yaficce adakin ,,

dagowa ameera tayi zaro ido tayi ,,tace kaine dama,

,, zama yayi ""yana mata murmushin mugunta yace,,, eh fa nidai ,, kina bani wahala

Harara ameera ta aika mishi tace mai kuka,,, yiwa yayana,,

Kallon ta yayi,, yace idan kinason,, kikoma wajan sa to kiyarda,, nahuta dake

wani,, kallon,, sakarai"" ameera tayi masa,, tace iyee to sannu munafuki. Nace sannu,, to "wllh ashir dinka baka isa ba kataba jikina,,,

Haushi,, yaji nan yayo"" kanta aikuwa da sauri ta goce,,, suka kama tsere adakin yace idan baki tsaya ba zan kashe,, yayanki cak ta tsaya yazo zaikai,, hannun shi kanta sai yaji ana buga kofar ,,, cikin jin haushi. yace. waye yaron nasa. Yace ,, oga daddyn kane yake kiranka awaye saurin fita yayi,, tabar dakin,

Suna isa hospital din emergency room,,,akayi dashi ' aka shiga bashi taimakon gaggawa,, su mommy sai safa da,, marwa sukeyi. Tana share hawaye,, sunfi awa daya kafin sukayi nasarar saita ,mishi numfashin sa wani. Dr. Ne yafito,,, daga cikin dakin da sauri,, sukayo kanshi suna tambayar,,, ya mai jikin yace,, kubiyo ne office dina

Bilal yace mom nizanje,, gida ""anjima wajan magarib zan dawo ,,, suka ce mishi to nan ya tafi

Dr ne yagama,, rubuce rubucensa"" tukun yadago kai yace , gaskiya yallabai yaron nan yana cikin babbar damuwa ,,, saboda a lokaci daya zuciyar sa ta buga da karfin. Gaske

,, daddy yace DR. Wani mummunan,, abune yafaru nan yabashi labarin,, komai ""jinjina kai DR. Keyi yace to ranka yadade kunkai rahoto ne yace eh nan yace. Gaskiya,, ahalin "" Yanzu ameer saiya yi kwana biyu tukun ya farka,, dan haka kuyi kokarin ""nemo masa matar sa nan su sukamishi,, godiya sosai ""san nan suka fito daga office din

Anass yana, shiga office dinsa "' yabasu member ameera,, yace su duba masa a inda take ya shige office dinsa,,, yazauna duk ransa a jagule yake saboda wannan. Abu kamar almara,, turo ""kofar akayi nan mai binciken yace,,sir gaskiya. munduba wayar,, akashe take amsar computer yayi yaga kuwa haka,, zancen "" yake ,,nan yabasu suka fice daga office din yacewa ishaq yakai rahoto gidan. Radio yayi sauri nan yace to yafice shima,, gida yanufa

Su ameera. jiki yayi sanyi ganin,, har yanxu sunki,,, fidda ta daga cikin wannan bakin dakin mai tsaron ta ,, yashigo a tsorace take kallon sa ,, yace babu abinda,, zan miki nazo ne nace miki zakici abinci, tace eh,, fita yayi yakawo mata ,, tace dan Allah bawan Allah,, kafidda ni daga,, nan yace hakika ""yarinya dana,, ga ankawo ki"na tausaya miki ,, saboda ogan mu bashida mutumci ""amma kibari anjima,,idan yatafi zan fitar take sbd kina bani,, tausayi,, share. hawaye. tayi yace ngd murmushi,, yamata ya fice daga dakin

Bilal ma. Allah ne,, kadai yakaishi"" gida ummi shi yasamu,, afalo tayi tagumi ""ahankali ya iso kusa,, da ita yadafa,, kafadar ta,, da sauri ta dago tana kallon sa tace,,, son lfy naganka haka naje sashenka,,, mai aiki,, take. cemin ,taganka kafita hankali tashi maiya faru ne??

Shuru yayi sbd zuciyar sa zafi,, take masa sosai. Ganin. halin da abokin nasa ,, y3ake ciki ""Ammi tace son magana fa nakeyi

,dagowa yayi yana kallon ta yace,,, ammi na sun dauke ta ,, sun sace mishi ita ,,

Cikin damuwa tace,, son wacece aka,, dauke"kayimin bayani yace,, Ameera mana yanxu haka ameer yasuma,,, yana asibiti bansan ""wani hali yake cikiba,,,,salati ammi tayi tana share hawaye tace,, wai suwaye keson takurawa,,,, rayuwar sune wai ""mai tayi musu haka,, dazafi ya Allah ,, katona asirin duk wanda yakeda hannu,, acikin wannan lamari,, ameen Bilal yace yamike;;:yace bari,, naje nayi wanka anjima saina zo mutafi ki dubashi tace to

daddy yafada wa abba cewa,, ansace,,ameera tashin hankali yashiga,,, ya kira abbu yafada mishi,, nan sukayo gida abba da kyer,, yasamu karfin"' gwiwar fadama umma aikuwa tasha kuka,, kamar ance mata ameera mutuwa,,, tayi tace abbansu,, mutafi kano din yace yanzu kinga dare yagaba to kibari gobe saimu tafi muduba ameer,, da jiki saida,, abba yasha fama,, kafin umma ta yadda sai gobe

Bangaren. abbu. ma haka ne saboda mama,, itama cewa,, tayi sutafi ""kano yace sai gobe,

Ameera tagaji da zaman tana,, kaiwa""da komowa taji anbude,,kofar mai gadin ta yashigo da leda,, a hannun,, shi mika mata,, yayi yace kicire,,kayan naki ga wannan,, nakawo miki ga kuma abinci amshi,, wannan keys din ki kulle kofar koda,, oga yazo kada kibude ga toilet nan ,, har an yi isha'i nan, ta amsa tayi,, mishi godiya yafita daga,, dakin taje. takulle toilet. ta. nufa tadauro alwala tayi sallar isha'i tukun tayi shafa'i da wutiri tana lazimi bacci. Yayi gaba da ita

Bilal ne suka zo,, shida""Ammin sa nan,, suka gaisa dasu,, mom sun jima tukun,, suka musu sallama suka tafi gida,,

Sai 7AM ameera ta farka taga hasken rana yafito da sauri tayi toilet ta dauro alwala ta tayar da salla,,

Su mommy ne suka karaso asibitin,, suna gaisawa da inna da idon ta ya kumbura,, saboda,, kuka sukayi. jugum DR. Ne ya fito daga dakin da aka kai,, ameer,, karasowa yayi suka gaisa da shi yace,, musu numfashin,,,ameer yasoma daidai ""ta nan sukayi hamdala

Ameera ce ta. Tuna da,, wayar ta"'Da sauri ta mike taje,, tabude jakar ta budewa,, tayi taga akwai caji,, hamdala tayi tashiga kira nember,, ameer amma tafi,, sau ashirin baa dagawa fashewa tayi da kuka tace,, haba yaya please,, mana ka daga shuru,, tayi jin ana kokarin bude,,, kofar maza tayi taboye wayar abayan,, ta ,,shine yashigo,, yana murmushin ""mugunta ganin ameera,, na kuka yace baby kibani hadin,, kai kawai "'idan kinason tafiya gida

kallon banza,, ta aika masa kanta,, yayo da gudu,, tabar wajan shikuwa yabita suka ringa zagaye,,, dakin harya,, damko,, hannun ta,, yana kokarin,, hadata da ""jikinsa ta saka mishi hakori, a hannu,, aikuwa yasaki kara wani gigitaccen mari yamata,,amma saboda dama,, tasaba,,,wajan ""tarike ,, tace daka ketamin mutumci gyara kayita marina,, buge mata baki yayi,,ta matsa ya bar daki,, yace zakisan kin cijeni'

Fauziya ce taciro,, wayar ameer mikewa,, tayi tana cewa "" ameera kowa kallon ta yakeyi,, harsu abba da abbu da sukazo,, yanzu

mom tace, kirata lokacin data,, kira ameera tana ta kuka,, kafin fauziya tayi,,,magana

Ameera tace,, haba yaya inata kiran ka baka,,, dauka "" ina katafi please yaya ,, ka taimakeni,, kazo kafidda ni agidan,, nan gashi nan yazo zai ketamin mutumci na,, tasake wani kukan,,

Inna ce ta amshe wayar tace,,Ameera babu abinda zai faru kinji yanzu zasuje,, su daukoki ,,,kinji kukan tasake saki. tace innata,, kuzo ku daukeni kasheni ""zaiyi ,,,

Anass ne yakaraso,,, jin maganar "da akeyi ya mashe wayar yace,, ameera,,kishiga WhatsApp,, kituromin location,,din gidan kuma"'ki boye wayar karki kashe datar,, tace to" nan takashe , ta tura,, miki location din nan yafita,,da wayar ,, ishaq yakira yace maza su hada musu kayan aiki , yace to nan,, suka hau hanya wayar na. nuna musu hanya

Kuka take sosai ""ganin mutum tayi yashigo dagashi,, sai wando bakin gwiwa da sauri tayi baya yana,, binta har takai bangon daki yaje zai fada mata kai,, tayi saurin mikewa,, yabita

kuka take sosai tana kiran yaya ameer kazo kaceceni,, kada yaketa min mutumci na ga shi tagaji,, shikuwa mugun dariya yakeyi,,

MUHADU A GOBE INSHA kuyi comments da share

Ban dayawa ba banida lfy ne
[26/10, 21:10] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„ โœ๐Ÿป

19โ€”20

Su Anass suna bin duk inda na'urar tayi nan,, suke bi"" kuma yana,,ta kira ""akan akaro musu"" kayan aiki ""saboda, yaga. Inda , akakai ameera, kamar wajan ""garine" ya kira,, Bilal yace ,, maza yabiyo su wajan,, gari" da sauriยฒ yake fita yace. Ammina Anass ne yakirani. Yace. Ameera takira yanxu suna hanyar zuwa,, ammi tace to Allah yabaku""saa yasa muyi nasara,, dafa kanshi,, Ammi tayi tasoma karanto mishi,,addu'ar neman tsari daga mugaye,, yake, amsawa"" da ameen my sweetheart ammina,,,

Murmushi tayi nan yafice, kafin wani lokacin. Tuni harya tarar,, dasu,, Anass nan yashiga,, motarsu ,, yacewa direban "'nasu ya koma gida ,, nan yajuya.

Umma kuwa. alwala,, tayi yasoma jera nafila tana, gamawa"" Tasoma jero,, addu'a kamar haka,,, ya Allah. Nayi, tawassali da sunayen ka tsarkaka,, nasan kafini sanin. Halin da ameera take ciki ,," ya Allah ka kare min ita daga sherin mutum da aljani da saura abin cutarwa nan tashafa,,,, ta share hawayen dake,, bin,, fuskar ta,,

A asibiti. kuwa suna nan,, zaune kowa,, yayi "" jugum jugum,,, masu, kuka nayi masu kukan. zuci nayi,, inna kuwa baiwar Allah takoma,,, abin tausayi ko abinci "" takasa ci. Saboda,, tashin hankali '" datake ciki

,, Fatima ce tazo kusa da,, mommy,, tace mommy,

,kallon,, ta mommy tayi itama hawaye,, ne ke bin "fuskar ta

Fatima,, tace, mom dan Allah idan ameera mutuwa , tayi kifada mana

"bayanta ""mom take bubbuga wa alamar rarrashi,, tace auta ameera ba mutuwa,, tayiba " saceta akayi kuma yanzu haka su Anass, suntafi " su daukota ""kinji kidena kukan ,

, share hawayen ta tayi tace,, to shikenan ""mom nadena"'Allah,, yatsare ta daga sherin,,, mugaye""

" Mom tace ameen auta kowa na wajan,, tausayi tabasu ""

Dr. Ne yafito wajan su daddy da su abbu yayo,, yace " ranka,, yadade"" Ameer ya farka,, amma yaki bude,, idonsa nayi ta"" fama yacemin,, shifa inba ameera ba,, bazai bude idoba"nan su,, mom,, suka je dakin,,

Mom tafara"" zuwa, wajansa tace son kabude,, idonka,, nice, ""idon yabude ya sauke su akan mom dinsa,,, yinkurin, tashi yayi saiya kasa,, rikeshi "mom tayi tace zauna son,

Kuka ya fashe da shi,,, harda ja numfashi,, kanshi mom tace shafawa,,,

yace " mommy ina ameera ta ina suka,, kaimin"" ita mom,, kuce subar min matata,,, mom idan wani abu yasame ta,, nima mutuwa,, zanyi"" kowa, na wajan hawaye,, yake,

Inna kuwa duk kukan da take dataga,,, Ameer sai yabata tausayi tadena,, kukan,, tazo,, kusa dashi tace,,, ameeru'"" kayi shuru, insha Allah, zata, dawo ""kaga yanzu takira,, ka ba"asan ta kiraba,,

zabura,, yayi yatashi"" yace",, a ina tace, muku take

Inna tace su abokin ka suntafi,, sukawo "" maka ita ,, sai alokacin,,ya zauna,, yasoma ""sauke ajiyar zuciya,,

dr. Yace abashi,, ruwa" mai sanyi "" nan aka bashi ,,allura dr. Yamishi,, bai jimaba yana ambaton sunan ameera,, bacci yayi gaba dashi,,

Ameera kuwa,,, ta gaji iya,, gajiya,,,amma saboda,, karfin, hali yasa take,, gudu tana zagaye ""dakin,, cikin sa'a ya cafkota,, kokowa,,, suka somayi"" yacire mata hijab din ,, kuka take tana zaginsa,, amma shi ko jikinsa,, rigar ta yakeson,,, cirewa,, yakasa cizonsa,, tayi amma. Dan jaraba irin tashi,, yayi banza da ita,,

Su Anass sunzo gidan da aka kawo,, ameera,, suka,, rarrabu,, wasu,, tabaya wasu,, tagaba wasu kuma,, ciki, suka kutsa" kansu anass, ne da, Bilal sai ishaq, "' suka shiga, cikin gidan daret, Suna, masu saita, bundigarsu,,

Ita kuwa ameera,,, ta saddakar,, wannan mugun mutumci ta zai keta,, ya yaga,, mata riga , Allah ma yasa tana da wata daga ciki karama,, wadda take hawadawa"' da kayan school,, yanason ya taba na fulanin ta amma,, yakasa,, saboda kaucewar datakeyi shiyasa,, har yanzu ""bai taba jikin. Taba illa hannun ta, kokowa,, suke sosai inda,, shiyakeson"" rungume ta itakuwa ta kiya,,, yanzu har tagaji,, da kukan,,, ma karfin hali,, kawai take tana anbaton sunan Allah

Su, Anass da sukazo shiga ciki fadane ya kaure,, a tsakanin su sosai saboda yaran majiya karfi ,, ne saida suka dauki kunsan minti shabiyar, tukun Anass yayi. Nasarar zare bindigarsa"' ya harbe su nan suka suma yan bayansu,,, suka kaisu mota suka shiga. Ciki ,, daki daki suke bi ,,

Bilal ne yayi,, wani lungu, nan yaji,,muryar ameera tana kuka,, da gudu,,yaje bakin kofar,, bankawa "'yayi da karfi nan kofar ta bude aikuwa.

zare. ido yayi. Ganin wanda yake kokarin raba ameera ,, da kayan jikinta,, tana, jin 'an banko kofar,, , tayi,, saurin kwacewa daga rikon daya mata ganin, Bilal yasa tayi wajansa,, da gudu ,, tana cewa "" yaya bilal please ka taimakeni zai,, ketamin haddi

Bilal. kuwa runtse idansa yayi jin ta saki kara. Yasa yayi,, saurin" bude,, idonsa, ganin shi yayi, ya riko, ameera yana son tabata,, wani irin,, bacin. Rai ne yaji aikuwa, yakai mishi naushi, suka,, kacame""da dambe bilal yayi saurin,, zaro bindigar,, yace wait,, ,munafuki,, ashe kaine " kasace ameera dan,, iska ,

Itakuwa, ameera da gudu,, taje ta fada, jikin bilal,, ta saki,, kuka runtse, idonsa,, yayi sai,, kuma ' yayi saurin,, bude idonsa ,, yana kokarin bugawa,, bilal wani karfe. yayi. saurin harbinsa,, a kafa kara yasaki ita kuwa,, ameera ta kankame,, shi "" sai kuka takeyi ""janyeta,, yakeson "yi amma takiya yace,, meera,, please mana dagowa tayi,, tace yaya Bilal please ka, kaini gida tasake rungume shi

zaro ido,, yayi yana jin bugun zuciyar sa na,, karuwa ""sai kuma yaji,, nadama tazo mishi yasoma,, cewa ', astagafurullah,, yana maimaita,, wa janye,, yayi zata koma ""yace please ameera kinga fa,, ni abokin mijinki ne karki sake,, tabani,, tsayawa tayi tace to sorry

,,Anass ne yashigo yaga ameera Bilal kuma,, ya dauko mata,, hijab da jakar ta yabata tasaka,, nan aka dauke wannan saurayin,,

Da mamaki,, Anass yake kallon shi yace duniya batada,, tabbas yanzu "kai,,Aliyu saboda rashin tsoron Allah ashe kai ne. Kasace. Ameera me, suka,, tsare maka ""zakayi bayani,, mugun aboki ,, kawai,, nan suka fice agidan,, waya Anass yayiwa daddy yace sunkama wanda, yasace "ameera,, aikuwa daddy,, yaringa saka musu albarka,,

Mommy ce ta tambaye ,,, shi yace, ansamo,, ameera nan suka kama murna,, ba kamar inna ma ,, har sujjada,,, yayi. ta godiyar Allah suka zauna zaman jiransu,,,

Ba'afi minti ashirin,,ba ameer ya farka,, nan sukayi dakin,, dukkansu,, suna shiga,, "su anass suka,, shigo cikin,, dakin "" suka shiga, ciki,,

Wajan,, inna, ameera "" tayi ta rungume ta tana kuka duk jikinta ,a" kukkuje,, yake saboda,, kokowar dasukayi,,, itada,, Aliyu ,, sosai inna taji,, dadi"" ganin,, jikar tata,, nan,, tasake ta tayo kan mom

,, tace mommy,, ina yayana shikuwa,, ameer sai murmushi,, yakeyi ganin matar tasa,, , ganin mom takiyi,, mata magana

Aikuwa,,Ameera tayi kasa,, zaman yan bori,, tayi tana daura hannun ta, akai""tasaki. sabon kuka,, mai. tsuma zuciya tace,,

Waiyo Allah na ni ameera,,, nashiga uku,, waiyo yaya ameer please,, ina kake kardai "ace sun daukeshi, kamar 'yadda suka, saceni mommy dan Allah ina yaya ameer dina,, dan Allah kada kicemin,, mutuwa,, yayi ""idan kuwa,, hakane mina,, mutuwa. Zanyi

Sariya tabasu,, harda shi ogan,, yanajin zafin,, zuciyar shi,, nasauka sosai,,, mom ce ta mike,,daga inda take,, zaune tazo wajan,,, ameera, tace daughter,,kalli cen,, "dagowa tayi aikuwa,, wa zata gani ""yayan ta mijin ta, ai,,da " sauri tamike,,, wajan sa, taje ta fada,, jikinsa,, tace alhamdulillah "'yaya kana lfy daiko,,,

dagota,,, yayi yasakar mata,,, kiss a mukatu "" murmushi tayi mishi ,,

Fatima ce ta turo baki gaba,, tana bankawa"' ameera,, harara tace iyeee sannunku,, masoyan,, duniyar Nigeria wato,,,ma har mu,, baki ganmu ba ko ameera,

,Dariya sukayi har ameera,,, tace" haba dai tom dina,, taya zan manta dake

Kara daure fuska,,,tayi tace,,,, baga shi, nan,, ba kinyi hogging din yaya,,amma ni kinki ko kallona, sauka ameera tayi tazo ta rungume,, ta tana cewa,, haba dai abokiyar,, fada na ai kinsan,, kema nayi kewarki""

Sai lokacin ameera ta lura dasu abba da abbu da daddy tsalle,, tayi,, tace, waiyo abbu abba daddy,, wllh bansan kuna nan ba,,

Abbu ne yayi dariya. Yace,, ina kuwa zakisan,,, muna nan sbd ga,,, mijinki rufe fuska tayi,, tana dariya,, tace "nifa ba haka,, bane abbu, na
Kuma fa abokinsa ne yasace,, ni

Ameer ne yace" zo nan, ameera wajan shi taje tkwantawa,, tayi akafadar,,shi yace,, my princess wanne abokina,,

tace,, abokinka aliyu, mana shine yasa aka saceni,,, suka kaini,, wani,, gida a wajan gari

Cike da mamaki yake kallon ta. Yace yanzu,, aliyu ne ya dauke ki maina masa ,,, haka,, da zafi""

Anass da Bilal,, sukace,, ai wllh muma,, kanmu abin yabamu,, mamaki"" sosai sbd,, wani lokacin dashi ""muke aikin nan,, ashe shine,, yasace"" Ameera,, nan kowa yashiga,, jajanta,, wannan mugun aboki,, ,,

Ameera tace yaya kaga,,, duk ""yajimin ciwo", har rigata,, ya yagamin, ,wai zai ketamin,, mutumci,

,Zare,, ido. Yayi,, yace "what shi aliyu,, din ne yake neman,, taba min mutumci ki,, kokarin tashi,, yayi, daddy yace,, comedown ,, mana yanzu ai yana,, hannun, su Anass,, yanzu zasu,, mishi hukunci daidai,, da abinda,, ya aikata"' komawa yayi. Yazauna"" yana huci

SHIN WAYE ALIYU???

Kubiyo maman Nusaiba domin sanin waye aliyu
[26/10, 21:42] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

JARUMAI WRITERS ASSOCIATION ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ

๐™ˆ๐™–๐™ง๐™ช๐™—๐™ช๐™ฉ๐™– ๐™ข๐™–๐™จ๐™ช ๐™–๐™ž๐™ ๐™ž ๐™™๐™– ๐™Ÿ๐™–๐™ง๐™ช๐™ข๐™ฉ๐™– ๐™™๐™ค๐™ข๐™ž๐™ฃ ๐™›๐™–๐™™๐™–๐™ ๐™–๐™ง๐™ฌ๐™– ๐™ž๐™ก๐™ž๐™ข๐™–๐™ฃ๐™ฉ๐™–๐™ง๐™ฌ๐™– ๐™ฃ๐™ž๐™จ๐™๐™–๐™™๐™–๐™ฃ๐™ฉ๐™–๐™ง๐™ฌ๐™– ๐™ฉ๐™–๐™ง๐™š ๐™™๐™– ๐™ฌ๐™–'๐™–๐™ฏ๐™–๐™ฃ๐™ฉ๐™–๐™ง๐™ฌ๐™– ๐™œ๐™– ๐™Ÿ๐™–๐™ข๐™–'๐™– ๐™—๐™ž๐™จ๐™– ๐™๐™–๐™ง๐™จ๐™๐™š๐™ฃ ๐™๐™–๐™ช๐™จ๐™–๐Ÿ’ช๐Ÿป

๐Ÿ’ซ(๐Ÿ…™๏ธŽ.๐Ÿ…ฆ๏ธŽ.๐Ÿ…๏ธŽ)๐Ÿ’ซ

21โ€”22

๐™’๐™–๐™ฃ๐™š๐™ฃ๐™š ๐™–๐™ก๐™ž๐™ฎ๐™ช ?

Aliyu haidar alhaji hashim,, da' ne ga alhaji hashim dan gata mai jida kai, ga kudi, ga izza saidai bashida,, mutumci saboda ""shikadai ne namiji, a yaran Alhaji hashim, shiyasa yake kafta rashin, mutumcin son ransa", babansa, yadaure, masa gindi ,, saboda ""shi aganinsa, gata ne yakewa aliyu haidar dansa saidai kuma, ita mahaifiyarsa, batason wannan dabi'ar dayakeyi, irin ta azzalumai,, ko yan aikin,, gidan ma bai bariba, duk wadda, yadaga ido yagani acikin yan aikin gidansu, indai, yaganta, kyakkyawa ce komai , nata yaji, to saidai fa a ganta da cikinsa, idan kuma tace"shine sai a wulakanta ta itada, iyayenta" abata, musu suna ko a ina,, suke koda basa kasar ne sai anbinciko' su mom dinsa, kullin, cikin yimasa" addu'a take tana , neman masa shiriya, wajan, ubangijinsa""yanzu haka tana dauke, da hawan"" jini duk ta dalilin aliyu, ne sbd in ta kawo yan aiki shike keta musu, mutumci, idan tayi magana Alhaji hashim shima yamata rashin mutumci kullin cikin damuwa take da zubar, hawaye, akan aliyu yanzu haka basu, jimaba"" da kashe wani kees , yayiwa yar aikin su ciki ita kuma tayi, alwashin insha Allah saiya wulakanta, aduniya,,,

Dalilin, zaman su abokai, shida ameer da anass da Bilal, a wata school suka hadu, ta kasar London, wadda gwamnati, tadauki nauyi, karatun" su sbd sune, wanda aka, dauki nauyin karatun su zuwa London anan, suka daura Friend su hudu, suke komai tare har suka dawo gida Nigeria, to bayan" sun dawone , gida wata rana bayan auren, ๐˜ผ๐™ข๐™š๐™š๐™ง ๐™™๐™– ๐™–๐™ข๐™š๐™š๐™ง๐™– , ne sunje wani ,, wajan shakatawa, anan suka hadu, da aliyu suka gaisa suna hira ne,

Ameera tazo da gudu, ta haye cinyar, Ameer tace, washh" yaya nagaji kanta yasha6 yace my ameera to zauna, kihuta. ta lafe ajikin shi tana shakar,,, kamshin jikinsa,, ,

Tinda tazo,, Aliyu yake kallon ta yaga,, sunyi mugun kama, da ameer,yace friend wannan fa. beautiful baby girl. dinfa

murmushi, Ameer yayi yace, she is my princess wife

,zaro ido yayi yace, kai friend bafa nason iskanci, wannan yarinya, yar shekara 14 zuwa 15years zakace, matarka,

Ameer yace, sosai makuwa, kanwata ce diyar, yayan daddy dina, tinda tazo duniya, nake kaunar ta to yanzu zancen danake maka,, shekarar mu biyu da aure, tin tana, 13years aka daura, mana, aure ,

, jinjina kai yayi yace kai amma , abokina kayi dacen,, mata kaga kuwa yadda kuke, mugun kama

dariya yayi , yace eh haka ne kowa kamar daddy ne yayo, ,

Ita kuwa ameera tuni tayi,, bacci tashinta yasomayi,, turo baki gaba tayi, tace ihimm please yaya bacci, tasake komawa, ta kwanta,, a jikin sa

Wani mugun, yawu, aliyu ya hadiye, , yaji kamar shima ya rungume ta, bai gama dawowa ba yaga ameer,, ya sake daga ameera, yace my wife please kitashi, mutafi gida mana nanfa,, a waje muke idan munje gidan saimu kwanta ko ,,

Bude idon tayi, tace yaya nidai chocolatier nakeso,

tsuru, da ido aliyu yayi mata

, Ameer yace to muje nasiya miki mutafi , sai lokacin ameera taga,, aliyu waro ido, tayi tace yaya wannan wanene,

murmushi ameer, yayi yace dama, ina zaki sanshi kina wannan tabarar,

Turo baki gaba, tayi, yace to sunansa, aliyu abokina, ne shi

washe baki tayi tace la abokin yaya barka da warhaka,

murmushi "yayi yace barka dai baby girl,,

Harara, ta banka mishi tace niba sunana, ba baby girl, ameera ake cemin, amma yaya, yanacemin" my heart ko my wife, kama dena cemin baby girl, takai zancen,, tana murguda, baki ita ala dole, anmaidata,, karamar yarinya,

dariya sukayi"" nan sukayi sallama da aliyu, tindaga, ranar aliyu, yayi alwashin saiya mallaki,, ameera ko ta halin yayane kullin da tunanin ta yake kwana yake tashi,,.... WANNAN SHINE TARISHIN ALIYU,,,

MUNDAWO CINKIN LABARIN

Ameer yace, please , DR. Kiduba min ita, yana nuna mata ameera,, hannun ameera takama tace, kanwata,, zomuje,, kallon ameer ameera tayi tace,, yaya " badai abinda zai sameka, nabita,, bazata, kaini wajan abokin kaba,, da yake son ketamin haddi,

, Murmushi ameer,, yayi yace babu inda, zataje dake kawai zata wanke, miki ciwon dakikaji, ne, , jinjina,, kai tayi alamar tayadda, nan suka bar wajan,

, DR. Din ne yayi murmushi, yace to, angon ameera, yanzu shikenan,, sai adena mana kuka ko, dacewa,, za'a mutu idan babu ameera,,

Dariya suka kwashe da shi , shima ameer dariyar yayi yana mai godewa Allah daya dawo, mishi da,,matar shi, lfy lau,,

DR. Yace yauwa ranka ya dade, muje nabaku, sallama,, daddy yace to,, mungode, sosai, nan suka fita""

Fatima ta matso kuda, da ameer, tana cika tana batsewa,, ita wai an bata, mata " rai,

yace, yadai auta, turo baki gaba tayi tace yaya shine kuka manta daniko,, tana matso kwallar karya,,

Janyota, yayi yana bubbuga , bayanta, yace haba dai, auta, ai bazamu. Manta da keba,,,

tace to maiyasa, kashare ni dankaga anty ameera, dariya,, yayi yace to shikenan kiyi hakuri kinji,, rungume sa, tayi tace yauwa yayana ,

Ameera anmata, wanki raunikan, dake, jikinta, sai kuka take, tana yarfa,, hannu tace anty kibar min ciwo. nakeji murmushi tayi saboda ameera ta burgeta, sosai tace,, kiyi hakuri kanwata, ankusa gamawa,,tace to, nan aka gama mata, taga andauko, allura, aikuwa suka soma zagaye dakin, nusee din tana. Cewa kitsaya, namiki,, allurar zata kashe miki ciwon dakikeji

sa'a akaci ameera tayi wajan kofa,, tana kuka, aguje, tanufi, dakin "da aka saka ameer nusee din nabinta, itama sai dariya take dan taga ameera tsoron allura ne yasa, take gudu banka ,, kofar tayi tana cewa waiyo Allah yaya karka bari,, tayimin. Allurar,,

Da sauri ya sauko daga, kan gadon ya bude. mata hannu tana karasowa tashige jikinsa tana kuka tace, please yaya banason allurar kace kartamin,, nusee dince, takaso tace kaga taki,, yadda namata allura saboda takashe mata ciwon,, alama yamata datazo ta mata,, nan tazo ,, hannun ta,, ya mikawa, nusee din,, ta tsira mata,,allurar kara, tasaki jinzafin yashigeta,, ta kankame,, Ameer tana kuka aka mata allura biyu,, mom ce ta shigo nan ameera tasaki ameer tayo, kan mom,,

Mom tace maiya faru,,daughter menene,, cikin kuka tace mom ba yaya bane yabari aka min allura har biyu,, nima ba ruwana dashi tinda, yabari akamin,,

Murmushi tayi tace, ai dan kidena jin zafin jikinki turo baki tayi tace nidai ba ruwana dashi , daddy. suka shigo,, yace su hada kayansu,, zasu wuce gida nan suka gama komai, suka tafi gida, ita kuwa ameera ko kallon ameer batayi wai tayi fushi dashi

Tinda aka kai aliyu police station,,, suke jubgarsa,, sunmishi " dukan tsiya ba kamar, Anass ba dayake jin haushin cin amanar dayawa ameer,, nan suka aikawa,, baban shi yazo cikin tashin hankali,, yanemi bailinsa amma anass yace baisan zancen ba , , dole a hukunta,, aliyu zasu kaishi kotu sun gama komai dan, haka, yace bazai bada bailinsa ba,, yace gobe su, hadu a kotu, sunshigar,,, da, kara, babu yadda Alhaji hashim ya iya saboda anas ya kekashe da kasa,, yace baisan maganar ba haka alhaji hashim yakoma,, gida, da wannan damuwar ganin gudan, jininsa a cikin wannan halin,,, yana zuwa, gida yashedawa mom din aliyu tashiga damuwa amma a zuciyar ta, hamdala takeyi,, ganin zaa hukunta,, aliyu, tana son akaishi gidan gyaran, hali, kila ya gyara halayensa,, tace Allah yakaimu goben insha Allah, haushi yaji ganin bata nuna damuwa,, ba akan kamawar, da akayiwa aliyu harara ya aika mata,, yace kedai,, Rukayya kinji, ciwon ranka, yanzu akama,, dan naki amma ko, kinuna"" damuwar, akai

murmushi, tayi saboda,, bazata, iya masa, magana ba, saita mike tayi sama abinta,

Su daddy suna, zuwa gida ana, kiran, sallar magarib,, ko shiga gidan, basuyi;ba suka fice su kuma suka shiga, ciki nan kowa yayi, dakinsa, ita kuma, ameera sama, tayi tayi salla tukun ta sauko kasa, lokacin harsu,, daddy sundawo,, kowa yana zaune, a falon kasa,,, ameer kuwa waigawa,,yakeyi,dan yaga ameera, amma, bata, nan, yaji saukowar, ta kallon ta yayi ta akaci, sa"a suka hada ido murguda, mishi baki tayi tana hararar, shi

Murmushi, yamata yana, nuna kanshi " jinjina kai tayi, ta zauna ,,su abba sukace,, gobe da asuba zasu koma gida,

,Inna tace to nima jibi zamu, tafi nida ameera,, wani kallo ameer ya aikawa inna, yace tab lalle ma innar, nan babu inda zakijemin, da mata

Inna tace kai ameeru butar ,,ubanka kaga nasaka dakai to wllh ka kiyaye ni

murmushi yayi saboda,, so yake yatsokane ta yace why granny zaki, tafimin, da mata,,

Hannu " Inna tadaura,, aka ta rushe da kuka tace innalilahi wa'inna ilaihin raju'un, a ni maryama, naga takaina kishiya tara rana daya, yanzu ameeru ni kake zagi ,, incedai " auren naku ma nina amince akayi to tinda hakane wllh anfasa , auren tinda harni zaka zaga,,

dariya sukayi, daddy ne yace kiyi hakuri inna bafa zaginki yayiba ,,cewa yayi maiyasa zaki tafinmishi, da mata,,

Inna tace ingo nan ameeru,,kallon ta yayi,,ta mishi dakuwa tace" bature ma yaci ubanshi,,dan kan uwa,, gunkima ubanshi,, nan ta ringa jerewa ameer zagi, kala kala tace kuma ana gama shari'a zata tafi, da ameera babu wanda, ya tanka mata ,, sai ameera tace nidai inna babu inda zanje ina wajan mommy

Baki inna tasaki tace shikenan ya asircemin jiki yanzu ameera ni kike cewa bazaki biniba , shikenan ai.

Dariya su fatima sukayi, aikuwa inna har bacci yasoma daukar ta tana masifa,, nan kowa yayi makwancinsa ,, ameera kuwa da tajema, saman kinyiwa,, Ameer magana tayi,, shi kuma duk yadamu dan so yake yaji dumin jikin ta mai sakashi nutsuwa, tafito daga wanka, daure da towel wajan mirow din taje tazauna tana duba wajan da aka mata allura sai turo, baki gaba takeyi, ita ala dole fushi takeyi ji tayi antaba ta banza tamishi

yace ,, wife duk fushin ne,, nan ma shuru tayi masa,, daukota yayi yakawo ta saman gado kwantar,, da ita yayi,, yace haba ameera wai miye na fushi tashi, tayi zaune baiyi auneba yaji ta fado jikinsa tasaki kuka,, rungume ta yayi yana shafa bayanta, yace am sorry nine,, nabari aka miki allura, to bazan sake bari ba,

sake shigewa "" tayi jikinsa shikuwa dama, abinda yakeso yashiga aika mata da zafafan,, kiss lamo, tayi ajikin sa, tana amsar sakonninsa,,jin yana taba na shanunta,, numfashi ta dauke taja ajiyar zuciya,, jinta,, a wani yanayi,, ganin yahaukace, mata gashi kuma ,dama ba kaya bane ajikinta matseta yayi kamar zai maidata ciki,,,

zafin matsar taji yasa ta saki kuka, jin haka yasa ameer bude idanunsa, yana kallon ta yace meye

, tace yaya zafi jikina yake kuma shine ka bugemin, janyota yayi jikinsa, yace, to shikenan nadena,, zo kiyi bacci kwantawa tayi a jikinsa, baa jimaba bacci yayi, gaba da ita shikuwa ameer kasa bacci yayi yana kallon yadda take bacci ajikinsa, yace, gaskiya bazan iya jurewa, ba tinda matata, ce aiba haramun, bane zan dai barita warke nan da wasu kwanakin,

Muhadu a gobe insha Allah muyi comments da share
[26/10, 22:41] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€๐ŸŒŸ

*RUBUTAWA DA TSARAWA*

๐๐€
๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๏ธ

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ
*๐Ÿ…™๏ธŽARUMAI ๐Ÿ…ฆ๏ธŽ WRITERS ๐Ÿ…๏ธŽSSOCIATION๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ*

https://www.facebook.com/108544471437073/posts/108546644770189/?app=fbl

_*Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa๐Ÿ’ช*_

*๐Ÿ’ซ(๐Ÿ…™๏ธŽ.๐Ÿ…ฆ๏ธŽ.๐Ÿ…๏ธŽ)๐Ÿ’ซ*

Follow this link to join my WhatsApp group::https://chat.whatsapp.com/Gu2Mxr0SRlx8Da4tv0J2AR

23โ€”24

Ahaka bacci barawo,, ya yi gaba dashi, cike da mafarkai,, kala-kala, kiran salatul farij ne, yatashi,, Ameer, da kyar, yamike "saboda mugun ciwon da mararsa take mishi kamar zata rabe,, biyu "" Ameera ya kalla bacci ta takeyi, hankali kwance, a jikinsa, iska, yasoma "hura mata, a fuska, a hankali tasoma bud'e idonta, ta koma bude su akan Ameer, turo baki gaba tayi tace,, Yaya, bakada, lfy ne murmushin yake ya yi mata, ya ce lfy lau nake, babu abinda yasameni, ,tashi ankira sallar asuba mika tayi, dan ita tama manta babu ko pant, ajikinta,,saida tagama"tashi ne taganta, babu komai maza, tayi takoma jikinsa tasaka,, kuka janyota ya yi sosai ta shige jikinsa saboda zafi sosai jikinsa, yake zazzabi ne, ajikinsa,,

Murya cen kasa tace "Yaya,, zazzabi ne,, ajikinka"

shuru, ya yi ,itakuwa jin ya yi, shuru takara " sakin kuka, tace "nidai, yaya katashi,, muje mom tabaka magani "" shafa gashin kanta yayi mai santsi da tsayi sai kamshi yake zubawa,,, yace , to shikenan bari nasauka, kasa idan nadawo daga sallah sainasha,, ahaka ta yadda ya dauketa, yakaita toilet, sukawo alwala ya jasu raka'a tainun farij,, suna, gamawa, yasauko kasa , da sauri, dan " su daddy sunbarshi,, ,,itama ameera sallar ta, tayi bayan " tagama ne tayi azkar din safiya, tana idarwa yashigo,,

Dagowa, tayi tace "good morning my sweet yaya,, murmushi yayi, yana zama bakin gadon, yace morning wife na dafatan kintashi,, lafiya,, itama murmushin ta mayar mishi tace alhamdulillah, mungode wa Allah, yace to, zo mu kwanta,, kafin karfe,, goma tayi mutafi kotu, ,kayan, sallar tacire,, taje tasaka riga bakin gwiwa, tazo suka haye gadon,, nan yaja musu bargo,

A gidansu, Aliyu kuwa tin jiya Alhaji hashim baiyi bacci ba sabida tashin hankalin, dayake , ciki ganin dan gwal din nashi a hannun yan sanda, kuma gashi, D.P.O. , Anass yace, bazai bada belinsa, ba , yakasa koda cin abinci da, yunwa, ya kwana' yanzu ma yakira, lauyansa, ne yana fada, mishi komai "" bayan yagama ya dasa, aya, daga, cikin wayar aka ce ranka yadade karka, damu, ai, babu wanda ya isa yataba, aAliyu, yazauna lfy, murmushi alhaji hashim ya yi, yace ai nasan idan inadakai,, bazaka bari wani yaci galaba akaina ba yace haka ne yallabai,, nan sukayi sallama, itakuwa mama tana jinsa amma tayi, kamar, batajinsa,, taci gaba da karatun, ta, bayan " tagama ne, yace kishirya, "anjima zamuje,, kotu, wajan shri'ar su aAliyu fatiha ta shafa tace to Allah yakaimu anjima din nan tafice a , dakin tana jinjina, hali irin na mijin nata, shi baisan damuwar kowaba, inba tashiba, data dansa ba, haka tashige dakinta bayan ta gaisa da masu, aikin gidan tashige dakinta

A gidansu,, Ameer kowa yashirya sun fito, falon gidan harda, hajiya inna sai cika take tana, batsewa wai jiya Ameer ya zageta, shikuwa, ko, a" ajikinsa, dan babu wanda zai tafin masa da mata wani kauye,, su , abbane sukace zasutafi, nan daddy yace subari adawo daga kotu inyaso shesu tafi gidan, da haka suka fita zuwa kotun saboda,, 10AM za'a saurari kararsu,

Bangaren Anass ma da ,, Bilal suma cikin shiri suka, fito kamar hadin baki, atare sukayi fakin bakin,, felin kotun, nan suka shiga gaisawa, nan , suka shiga, ciki ,, kowa ya zauna kotun tacika bak'il, da mutane,, nan aka kawo Aliyu, duk jikinsa ya yi bak'i kamar bashi , bane Aliyu , dan gata maiji, da izza yayi zuru-zuru,, bayan alkali, ya zaune aka soma gabatar,, ta kara,, saboda akwai wani karar,, kafin nasu ,, bayan angama ne mai gabatar,, da kara yatashi yasoma, da

A yaune ranar alhamis zamu saurari karar,,Ameer Muhammed da kuma Aliyu Haidar alhj hashim, akan zarginsa,, dayake yasace masa mata yana kokarin keta mata haddi, ,nan kotun tayi shuru jin sunan dan wanda ake kara,, yaron da baya ganin mutumcin kowa agarin nan alkali, yace lauyoyin, masu kara da wanda ake kara,,nan, wani yatashi , yace"" ranka ya dade ni sunana ,, barrister mansoor usman, nine lauyen wanda yake kara,, tukun ya zauna,, wani yatashi,, yace ranka "yadad'e ni sunana,,, barrister mustapha kamal, nine lauyen wanda ake tuhuma ,, shima, yakoma ya zauna, alkali yayi rubutu kafin, yadago yace ko lauyen wanda yake kara, yana da magana barrister mansoor Usman, yamike yace eh, inadashi ranka yadade yamike nan yayi wajan Aliyu , ya gyara,, tsayuwarsa,, kafin yace,, kozaka fada, wanene kai, ,,Aliyu yasaita, kanshi yace,

Sunana Aliyu haidar alhj hashim, anhaifeni,, a karin kano anguwar, nasarawa, J R A , , barrister mansoor yace, masha Allah, kozamu iya sanin menene alak'arka da, Ameer, Mohammed , aliyu yace abokina ne munyi, karatu dashi, a London, anan muka daura, abota,,,barrister mansoor yace to menene yasa, kasace mishi yar, uwa kuma mata, , yace saboda, inasonta,

Kowa na wajan sai kuskus, akeyi lauyan,, Aliyu ne zai tashi yin korafi, akaci sa'a Aliyu yana kallon shi yadaga mishi hannu, alama, bayason, lauyan, nasa yayi magana , saiya koma yazauna shikuwa Alhaji hashim sai zufa yake sharcewa, kamar, wanda yayi gudun tsere ita kuwa mom dinsa sadda,,kai tayi, saboda"" ciwon ta yanason tashi, barrister mansoor yace to daka saceta mai zaka mata,, ba tsoro aliyu yace , tin lokacin dana ganta nakamu da so da kaunarta, kullin sonta, kara shigata yake, gashi ,,afarkon haduwarmu,, abokina, yace matar sa ce ni kuma ban yadda ba da zancen sa danaga,, nakasa samun haduwa, da ita shine nasa, aka satomin ita amma sai taki yadda dani ,, shine nace tabani kanta,, amma ta kiya ina shiga inda take,, zata fara gudu ,, lokacin,"" da naso yimata fady ina kokarin mata, saiga police " sunzo shine suka kamani,, wannan shine abinda yafaru, yakai karshen zancen yana share hawayen fuskar shi saboda, yanajin, nadama "" na kara shigarshi, barrister mansoor, yace,

Dama kataba yiwa wata kokarin, fady ko kuwa Ameera ce farko, Aliyu yace, ba ita kadai bace wata yar aiki gidan mu harda, cikina ajikinta, amma yanzu bata gidan dan daddy na yakoreta,, saboda tace nine namata cikin shine daddy yakoreta, yace tana min sherri ,ita kuma dazata fita tace min insha Allah saika wulakanta saika tozarta a duniya kafin ka mutu, kuma sai duniya baki daya, tasan kai tantirin dan iska ne ,, banza namata saboda alokacin ko a jikina sbd daddy na shiya dauremin gindi nake duk abinda nakeso a garin mutum ko wayeshi, idan yashiga gonata, zan kafta mishi rashin mutumci, komin shekarun sa sbd babana ya nunamin cewa babu abinda ,zan nema na rasa, yanzu kuma naji tsoron Allah yashigeni, nayi nadamar abubuwan danake aikata mahaifiyata,, kullin cikin koka halina, take amma sainake cemata,, ita bata sona kamar daddy " sai tace aliyu wannan fa ba soyayya,, bace babanka yake nuna ma idan kaci gaba da wannan dabi'ar to wllh karshenka bazaiyi kyau , idan tabafadi haka daddy na zai rufeta da fada,, na fadawa kotu gaskiya ne saboda karna bata wahalar Shari'a alhalin nasan komai,, kuma nayi nadamar abinda na aikata,, yana kaiwa karshe ya rushe da kuka mai tsuma zuciyar mai karatu

Alkali yayi rubuce rubuce kafin ya dago yace ko lauyan wanda ake kara yana da magana,, saboda karfin hali,, barrister mustapha, yamike yace eh inada ita, alkali yace to zaka iya tambayar ka barrister mustapha yace inason kotu takira mana, ๐™–๐™ข๐™š๐™š๐™ง ๐™™๐™– ๐™–๐™ข๐™š๐™š๐™ง๐™– , juyawa akayi mai kira yace kotu tana neman ameer da ameera,, nan ameer yamike ameera, na manne ajikinsa, yace mata babu abinda aliyu zai mata tinda gashi amma taki yarda, sai kuka take, ahaka suka je kusa da aliyu sake kankame ameer tayi tace yaya kada kabari yataba,, ni please tsoron sa nake ji rungume ta, yayi yanajin kunyar mutanen dake wajan yace , babu komai please kinutsu, tambaya zaa miki,, tukun ta dena kukan

Barrister mustapha yazo kusa dasu yace kozamu iya sanin cikekken sunanka, , Ameer yace sunana ameer Muhammed,, an haifeni a garin kano a anguwar nasarawa J R A,, amma babana dan asalin jahar katsina ne barrister mustapha yace menene alak'arka da Aliyu ,, Ameer yace abokina ne shi munhadu a London wajan karatu ,, barrister mustapha, yacewa, ameera yarinya, ko zamuji cikekken sunanki "" dagowa, dayi,, daga jikin ameer tace sunana ameera Ahmed,, anhaifeni a garin kankara jahar katsina, , barrister mustapha yace kokinsan,, wannan yanuna mata aliyu ,, da sauri takoma jikin ameer kamar zata koma cikinsa ,, tana kuka tace shine, yasa aka, saceni"" zai ketamin mutumci na danaki yarda, shine yace zaisa akashemin, yaya ranar, da yazo yafi karfina har rigata ya yagamin,, da hijab dina, alokacin harna saddakar mutuwa zanyi saiga, yaya bilal ya banko kofa nan naje wajan sa shine suka kamashi,, ta dago ,tana kallon aliyu tace azzalumi macuci dan iska fasik'i, ,, sai Allah yasaka min raunikan, daka min da kataba jikina ban yafe makaba ,, shine, bayan nadawo gida yaya yace ayimin wankin ciwon har akamin allura,, yanzu ma hannuna ciwo yake,, duk kai kasa yaya yace sumin allura to wllh kaci wuta balbal,, ta kai karshen magana tana murguda,, baki mutanen wajan sai dariya suke saboda ameera tabasu dariya,

Nan akace sukoma sukoma wajan zamansu suka. zauna ,, alkali yayi gyaran murya, yace bisaga yadda wannan kara yakaya kuma wanda, ake zargi yace, ya aikata, kuma yafadi gaskiya,, batare daya baiwa kotu wahala ba,, alkali yace,, kotu ta,, yanke,, mishi hukuncin ,,, aliyu yayi kasa dakai,, yana sonjin wani hukunci zaa yanke mishi ,, alkali yace anyanke mishi hukunci shekara biyar agidan yari,,tareda aikin horo mai tsanani, nan alkali yabuka, gudumarsa aka mike kowa yafita, waje mahaifiyar aliyu ce taje wajan su mommy,, da sallama takarasa, nan suka amsa, mata, tashiga basu hakuri tana kuka mommy,, tace babu komai sun yafe mata tukun ta fice aliyu kuwa yana ganin babansa na mishi magana amma yayi saurin shigewa, motar police kowa yabar wajan

Suna zuwa gida,, daddy yakira su Anass yayita saka musu albarka shida Bilal, tukun yakashe, wayar su abba sunci yanzu, zasu wuce gida , bayan sallar azuhar, su daddy suka musu, rakiya, abbu yace, yar gidan, Inna bakice, agaishe miki dasu umman kiba rufe fuska tayi tace abbu kace,, ina gaishesu " idan aka bamu hutu zanje musu,, Abbu yace to shikenan, tukun suka fice agidan, kowa yazo falo,, yazauna " ita kuwa ameera tana nan manne da ameer dinta,, Inna ce tajuyo taga ameer yana saka kanshi tsakanin wuyar ameera da kafadunta,,

Salati inna tayi tana tafa, hannu, tace a ni maryama,, wannan iskanci, dame yayi kama kai, ameeru,, haka dama kake ban saniba,, banza yayi da ita su fatima kuwa sai dariya,, suke kasa kasa,, dankar inna taji tasauke musu ruwan masifa,, Inna tace to wllh gobe zan tafi da ameera,, itakuwa""" Ameera ta lafe ajikin shi sai shakar kamshi mai sanyin dadi take,, tace yaya, dagowa yayi yana kallon ta yace,, my wife,, menene, shagwabe fuska tayi, tace nidai bacci nakeji mutafi,, daki,, murmushi yamata yace to shikenan,, muje na kwantarki,,, kuka inna tasaka tace yau naga takaina shikenan ya asircemin jika, su mommy tuni, sukabar falon, shesu ameer bai kula taba ya dauki ameera kamar,, jariri yayi sama da ita yabar inna na fada tana zaginsa,,, wai ya iskanta ameera,,

NAGODE DA COMMENTS AND SHARE DINKU FANS INAYINKU, SOSAI
[26/10, 22:57] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซ
JARUMAI WRITERS ASSOCIATION ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ

https://chat.whatsapp.com/Gu2Mxr0SRlx8Da4tv0J2AR

MARUBUTA MASU AIKI DA JARUMTA DOMIN WA'AZANTARWA ILIMANTARWA NISHAD'ANTARWA TARE DA FAD'AKARWA DA JAMA'A BISA HARSHEN HAUSA ๐Ÿ’ช

๐Ÿ’ซ(J. W.A)๐Ÿ’ซ

Follow this link to join my WhatsApp group::https://chat.whatsapp.com/Gu2Mxr0SRlx8Da4tv0J2AR

25โ€”26

Hajiya inna ikon Allah kennan,, tana wannan masifar "" har bacci barawo, yayi gaba,, da ita,, su ameera suna, shiga daki, tace yaya,, kallon ta yayi,, cike da so da kauna,, da kuma soyayyar jinin, yan uwantaka" dake yawo,, yajikinsu,, itama-" shidin take kallon tana jin wani,, irin yanayi, nashigarta tako wani kofa " na jikin ta,, sannan tasake cewa yaya " yace na'am wife tace, yaya inajin ajikina,, kamar za'asake nisantani dakai ,, wani wajan

Cike da mamaki, Ameer yake kallon ta yace haba ameera waye kuma zai rabamu cikin, kuka tace

Jiya nayi irin mafarkin dana saba yi a kwanakin baya,, wannan mutanen "" na rike dakai suna son daukeka amma kasan me

, girgiza kanshi, yayi alama,, a a,,, tace kana kirana,, sunayin,, baya dani saiga, wata mata da fararen kayanta ina kallon ta ta yimin murmushi,, nan ta kashe masu son rabamu dakazo,, wajena kai baka ganinta amma ni ina ganinta, dataga,, ka rungume, ni sai naga " tana share hawayen fuskar ta tana kuka,, amma, bata cemin kaomai ba sai hade hanayenta,,, da take min alama rokona,, dai take,, amma "" kuma batacemin komai ba nake kallon ta saina zare ido kasan maina gani yace a a

Tace naga muna mugun kama da ita kamar ita tahaifeni inason mata, magana sainaga ta matso kusa da ni tace,, min ya ke kanwata kisani cewa nan da wani lokacin " zaku rabu da mijinki amma idan zaku rabu zaki,, tafi da cikinsa ne ajikinki,, zaki dauki dan lokaci mai tsayi kafin kusake haduwa, cikin kunnena, take fada, maganar, amma kai bakajin abinda take fada,, ina juya kaina,, naga style dai kukan take sosai,, saita bani tausayi,, duk da, bansan wacece ba kawai naga,, tabace kamar bata, bayyana, a wajan ba tana kai karshen, magana tasaki kuka ,mai rabashi da nutsuwar sa, sama yayi yana nazartar magana ameera,,

To wacece wannan mata kuma, mai take nufi da haka,,, tayama za'ace "" rabasa da matar sa, jin ameera takara sautin, kukan ta yasashi dawowa daga duniyar tunanin nasa, hannu ya ware mata alama tazo, aikuwa, dama kamar jira takeyi nan tashige , jikinsa,

Lumshe idonsa yayi yana kara shiga da ita, jikinsa, yace wife dagowa tayi tana kallon,, yace kikeyin addu'a idan zaki kwanta, tace yaya bana bacci sainayi,,,, addu'a sosai, tukun kwantawa,, sukayi yaja musu bargo,, yana shafa kanta tasauke, ajiyar zuciya, baa jimaba, yaji saukar numfashin ta a kirjinsa,,shima bacci yasoma, amma kana gani kasan bayajin dadin baccin.

Zaune yake yafada duniyar, tunanin "" nadama , da damuwa,, tayi masa. Yawa, cikin, Kwana daya yarame, yafada yana neman gafarar ubangijinsa""yanzu Allah, yanufesa da shiriya kuma yayi alkawarin,, insha Allah yadena son ameera saboda,, itadin matar, abokinsa ce amma ,, saidai yanajin ta ajinin jikinsa,, yace to mai hakan yake nufi , fesar, da iska yayi mai zafin gaske daga, bakinsa " yace istagafurullah, Allah kayafe min zunufaina, insha Allah bazan sake saba maka,, ba Ammi ce tashigo,, tun dazun, take kanshi amma tayi maganar duniyar nan, amma yayi shuru she sauke tagwayen ajiyar zuciya yakeyi,, dafa kafadar shi tayi tadan,, bubbuga, bayansa " afirgice, yajuya dan ganin waye, Ammin sa yagani, kawai saiya fada jikinta, yasaki kuka mai tsuma zuciya,

Mamaki ne kwance samar fuskar,, Ammi bata hanashi kuka ba saida yayi mai isar shi kafin tazuba, ruwa mai sanyi, tadago, kanshi, ya kasa mishi cof din abaki,, baiyi muso ba yashanye,, ruwan tass,, ajere yake sauke ajiyar zuciya, kara, shigewa yayi jikin ammi itakuwa ammi tunani takeyi, maiya saka dan nata kuka tinda ya girma bata, taba ganin kukan, saba ahankali da dagoshi,, ganin muguwar ramar,, daya yi tace,

Son yanzu har akwai abinda zai hanaka sukoni, bazaka fadamin ba a matsayina na wadda ta haifeka, sake komawa, yayi jikinta, yasaki wani kukan harda,, jan zuciya, yace ammi narasa, ta ina sonta ina kaunarta,, ina jinta a cikin jinin jikina, dagosa, tayi, tace wacece karasa,, a ina take, Bilal yace ammi bazan taba samunta taba, saboda, tayi aure nacire ta daga zuciya ta amma inajin ta acikin jinin jikina, yanzu bana mata soyayyar aure inajin, kamar itadin, jininace, amma, na rasa ta inda,, muka yi gamin jini,

Cike da tausayi take kallon dan nata sosai yabata tausayi, tace masa, son kayi hakuri, duk abinda kakeso baka samesa, ba to " ka kaddara a ranka cewa dama ba alkhairi bane agareka, idan kuma rabonka, ne ko wani irin juyi, zaayi to saika mallaki, wannan, abun, kayi hakuri da rashinta kaji insha Allah zaka samu wacce tafita ,, haka ammi tayi tayiwa, Bilal nasiha har , bacci yayi gaba dashi, kwantar, dashi tayi tarufe, tafice a dakin, tana jin tausayin dan nata

A falo zuke a zauna dukkansu, Inna kuwa tana bankawa ameer da ameera harara ganin, daddy yasa tace, yauwa Muhammadu,, dan albarka dama, jiranka nake kusa, da inna yazauna yace gani inna,, kallon sa tayi tace gobe zantafi, gida, daddy yace haba inna kiyi hakuri kizauna damu anan, mana cendin ma ai ' duk,, daya, ne " inna tace, a a wllh bazan iya zama da sallamenmu, ba wllh, daddy ya danne dariyar sa yace to suwaye kuma sallamenmu, tace gasu cen yan kan uba she iskanci suke yi agidan nan amma kayi, shuru, daddy yace to kiyi hakuri,, zan tsawatar, musu baki inna tawashe tace yauwa ' dan albarka nagode, kallon su ameer yayi, wanda suke kallo ameera har tayi bacci ajikin sa daddy yace, son maza kutafi, part dinku, da to ameer ya amsa nan yayi gaba, da matar sa

Daki yayi, da ita yana kwantar da ita zai mike tayi saurin,, saka hannun ta a wiyanshi, tace please yaya, kallon ta yake yi, saboda baccin ta takeyi,"komawa yayi ya kwanta, tashige, jikinsa, tana shakar kamshim jikinsa,, sai kara cusa kanta tayi a kirjinsa,, rintse ido, yayi saboda wani mugun murdawa da mararsa tayi , sunayen Allah yake, karantowa, da duk addu'ar datazo, bakinsa"" a hankali, kuma tabude idonta, wanda bacci ne a cikinsa,, yace Ihimm nidai, kallon ta yayi "yace kedai me tace, zafi nakeji,, mikewa yayi ya kunna, AC din dakin, fuska ta kwabe kamar, zatayi kuka, tace yaya please, yace mekike so kayan jikinta ta nuna mishi zuwa, yayi yadagota " kayan nata ya cire mata, yadauko,, wata yar rigar bacci yasaka ""mata yace to sleep ,wife

Nan suka kwanta, cikin bacci taji, Ameer yana ta juyi, sai juya kanshi yakeyi, a kafadarta,,mude ido tayi, cikin tashin hankali,,Ameera tace, yaya!yaya! ,, shuru yayi saboda ahalin dayake ciki bazai iya amsawa ba, kusa, dashi ta matso " tace yaya meke damunka, bude idonsa yayi wanda yayi sauya kala saboda, tsananin azaba " yace ameera mutuwa, zanyi kuka, tasaka tace please yaya banason,, wannan zancen mutuwar dagowa, yayi yace, wife ai maganin yana wajan ki zaki, iya taimakon, mijinki, ya rage azabar,, da yake ji da sauri, tace eh yaya,

Janyota yayi jikinsa yana hade bakinsu yana bata kiss mai zafi tana jinsa, yake ta shafeta na shanunta ya kama, shuru, tayi

Jin yayan nata na kokarin, wuce gona, da iri yasa tarike hannunsa tace yaya kabari mana baima san tana yi ba saida yasamu nutsuwa yana romantic dinta tukun yabari shima yaso ace yau tabashi hakkinsa da aure amma, kukan datake, yasa shi, barinta, yana, sauke ajiyar zuciya, janyota yayi,, yace sorry wife, yaya ne yataba miki kirji, rufe fuska tayi tana dariya,, jan hancinta, yayi yace to muje muyi wanka tace"" yaya menene, sunan wannan abinda, dakake min" yace wannan sirrinmu ne dagani saike sai mahaliccinmu', kada koda,, wasa kifadama kowa 'tace to, yaya nan sukayi toilet, sukayi wanka kafin, suka, dauro alwala"" suka ringa nafila dan, ameer da ameera akwai ibada sosai

Yau ameer yace zasuje, shan iska sosai ameera take murna, nan suka, yiwa su mom sallama har sunje bakin kofa, Inna, tace gantalallu a haka dai kuke yan iskan banza kuma wllh kasake kadirka mata, ciki a wannan kananun "" shekarun nata to saina kaika kara kotu, jarababbe yo inba jaraba ba, ace kullin kuna like kamar wanda kukazo duniya atare toko tagwaye bazasuyi ""' wannan dan banzan shirmen ba kunyace takama,, ameer ya kama hannun, ameera da, Fatima sukabar, gidan

D.P.O. , Anass kuwa anmishi karin girma ga kuma kyauta daga, gwamnati saboda yayi, namijin kokari daya kama aliyu yaron, daya addabi mutane,, yayi farin ciki sosai,, su mommy ma da su ameer, sunzo tayashi murna , ameer ya kalli,, Anass yace my dear frend,,murmushi Anass yayi ameer yace congratulations dan uwa nayi farin ciki sosai Allah yakara daukaka,, cikin jin dadi, Anass yace ameen my friend,, Ameer yace sauran, aure ko dan ware ido Anass yayi yace, aini, matata, bata gama girma ba dariya, ameer yayi kafin yace,,, tab lalle kuwa, kilama, sai my ameera ta haifamin yara biyar,, zaka yi ko,, dukan wasa , yakai mishi yace to ahakama zan auri kayana, ameer yace wacece ita hankali kwance, yace Fatima mana,, dariya, ameer yake sosai dan ba karamin, bashi dariya, yayi"" wai Fatima yakeso bama fuziya ba

Hade rai anass yayi yace kaifa dan iska ne kallonsa yayi yace ai kabani dariya ne kana ganin yadda nake fama da ameera amma kaima kace Fatima, kakeso anas yace, a haka
Nakeson kayana basu idar,, da magana ba, saiga ameera da Fatima, jikinsa, suka shiga, shikuwa yakara bude musu hannu ameera daga gaba Fatima daga baya ,,

Fatima tace, yaya muke ta nemanka, murmushi yayi yace gani ai, ameera tace, mama ce tabamu, cokotie hadda kayan kwalliya ameera tace eh yaya kuma munce mata mungode sosai,

Murmushi yayi yace to naji dadi, tinda sukazo Anass yake kallon Fatima juyawa tayi suka hada ido wani bakon yanayi taji, duk da ita karama ce amma kawai sai taji tana kunyar, sa Anass yace Fatima duk baku ganni ba sai alokacin ameera da dago tace, la abokin yaya barka da warhaka, yace ykk tace lfy lau, nan suka koma ciki Anass yace zankai kokon barata,,ameer na murmushi yace badamuwa nan sukayi sallama suka tafi, gida,

Zaune suke akan wasu kujeru, awani restaurant, tace, yaya " mai zakaci yace kefa tace, duk abinda kakeso yace to, nan mai kawo, abinci yace maiza'a kawo muku, ranka yadade, ameera yace wainar shinkafa da, miya, nan aka kawo musu,,tura mata nata, yayi saita,, kalleshi ganin, ya sunkuya " yana cin abinci yasa, tature, abinci nata,, kuka tasaki,, tana saukowa daga, saman, kujeran,, dura kafa, tasomayi ""tana rera kuka, da sauri,, ameer ya dago yana kallon inda yayi zaman yan bori tana kuka kusa ita,, yazo "yace menene,, yafaru, tuni hankalin mutanen wajan yayi kansu kowa na mamakin , abinda yasakata, kuka wata ce wanda take kuda dasu ameer ita da kawayen tace kai amma fa gayan nan ya hadu iya haduwa,"" daga ganinsa ya iya,, kula da mace,, dayar, tace wannan kuma kanwar shince,, takusan ta tace kila autarsu suce kalli yadda suke mugun kama dashi, daya, tace wllh inasonshi,,, kuma saina gabatar mishi da kaina, kar aje wata tayimin kwacen, sa basu gama zancen, ba sukaga yana tashinta

Yace haba ameera menene yasameki,, shigewa tayi jikinsa tace nidai bazan, iya ciba kabani,, yar dariya, yayi yace to saboda hakane, kike wannan abun, wllh kincika" rigima, turo baki gaba tayi tace, toba kaine ba, bakin nata ya buge,, aikuwa tasake sakin sabon kuka shikuwa, murmushi yake yi,, yan matan nan suka maidasu ameer kamar tv, dayar tace kai gaskiya anyi hadaddan handsome boy anan, , Ameera kuwa juya mishi baya tayi saiya je wajan ta yakama kunnen sa harara, ta banka mishi,, murmushi yayi yace, haba wife na haba matar ameer farin cikin ameer dama rayuwar sa baki daya,, wani sanyi taji bude mata hannu yayi dama, abinda take so tashige abinta, mike, daya daga cikinsu tayi tace waiyo Allah ni jamila kardai,,,ace matarsa, ce wata tace haba,, jamila wannan hadaddan handsome din zakici matarsa, ce tama lalace, a wannan, kwailar, ajiyar zuciya yasauke, tace kinji, yace, wife, kuma yace itace farin cikin sa dama rayuwar,, gaskiya inajin tsoro, dan ba karamin. ฤถsonshi, so nake mishiba, na taba ganinsa, a school, tace amma zanje, na gabatar mishi da kaina idan,, sungama"' dariya suka kwashe da shi sukace wata dai takamu, da soyayya,, banza tamusu suma shuru sukayi, suna kallon yadda ake zuba zallar soyayyar gaskiya,,,

Sukuwa basuma san sunayi ba,, , dan, ameer ya, zaunar da ameera akan cinyarsa, yana, bata abinci,, sai shagwaba take zuba " mishi yana biye mata,, " ahaka suka gama yabiya kudin nan yamike,, Ameera ta makale sa,, wai saiya dauketa,, bazata iya tafiya,, ba dariya yayi, yace lalle "yau yan rigimar ne akanki, kuka tasoma tana rungume shi, tabaya""dariya kawai yake mata dan yagano yau dai, da rigima ta tashi,, suna ahaka, sukaji ance,

Assalam alaikum juyawa ameer yayi yace amin wa'alaikum salam,, jamila tace,please zan iya magana dakai,, kallon daya yamata "" yadauke kai yace inajinki,, tace wllh tin ranar, dana fara ganinka, nakamu dasonka,, "'ina ta nemanka sai yau Allah yahadamu , Ameera tajuyo tagaban ameer ta kwanta ajikinsa kafin tace, yaya mitake cewa, murmushi yayi wanda yasa jamila lumshe idonta,, yace my wife wai cewa tayi, tana sona,, da sauri""ameera ta dago daga, jikin Ameer tace to yaya kai mai kace mata,, yace bance komai ba,, ita kuwa jamila,, ganin ameera ajikin ameer yasa taji wani bakin ciki, ya rufeta,

Ameer yace kiyi hakuri baiwar Allah ni, ina da mata""kuma ita kadai nakeda, burin rayuwa a duniya ta,, da karfi zuciyar jamila tabuga,, tace to ina matar taka ne,, yace gata kina,,, ganinta ita matata,, girgiza kai jamila tayi tace haba dai,,, taya zakace kanwarka ciki daya kace matarka ce, ko fuskar ku aka kulla ai ansan,, kanwarka ce murmushi,, yayi yacewa, ameera my wife, fada mata ni waye, agareki ""dagowa ameera tayi suka hada ido da jamila taji wani zafi a zuciyar ta tace shidin mijina ne kuma yayana ne shidin jinina dan haka kada, kiyi mamakin " kaman ninmu domin jininane,, shi,, shuru jamila,, tayi tace, ban yadda ba,, ita kuwa ameera haushi "" taji tace yaya please zafi nakeji muje gida,, kayimin wanka,, saimuyi bacci,,Ameer yace to ,, ya kalli jamila yace ina mai kara baki hakuri, ni inada, mata ๐™–๐™ข๐™š๐™š๐™ง ๐™™๐™– ๐™–๐™ข๐™š๐™š๐™ง๐™– miji da mata ne,, nan yakama hannun ameera sukabar, wajan

Kamar wacce kwai yamace a ciki tayi wajan,, kawayen nata,, tace wai yace matar sace kuma bashida burin, kara, aure ita, kadaice "' zuciyar sa keso tausayi tabasu, saboda akwai ciwo kaso wanda baya sonka,, ahankali tace zanci,, gaba da addu'a idan harshi,, mijina ne to insha Allah, zai aure ni nan itama tabar wajan

Bawan Allah, Bilal sosai yakejin jiki har asibiti aka kaishi, dr. yace yarage, damuwa, da, tunani daddyn sa kuwa nasiha yashi yimasa mai ratsa jiki ahaka har, yafara rage damuwa,, ,

Yau ma suna bacci cikin tsakiyar dare,, tasoma bafarkin, , ganin matar tayi tasake zuwa inda take yanzu kuma a wani karkashen,, bishiya suke,, zaune ita da ameera,, matar tace yar uwa ta dan Allah ki taimakeni kije ki ceto ahalina daga cikin duhu kikawosu haske wanda zai zame musu dalilin shiga aljana ameera ta kalli matar dasuke tsananin kama da ita tace anty ina ne garinkun naje inason na taimaka wa ahalin naki saboda naji ina sonki shafa kan ameera tayi tace ba yanzu ba zaki sani sai kinzama cikakkiyar mace,, tace to yasunan antyna murmushi tayi tace,, a garinmu da jenifer aka sanni amma,, lokacin dana kusa mutuwa sunana karima, dagowa tayi taga ta bacce,, da sauri tamike tace anty karima please come in,, da karfi kuma tace anty karima, da sauri ameer ya tashi yaga ameera tana tirje tirje tana kiran , anty karima,, janyota yayi,,yana tofa mata addu'a cen tabude,, idonta "" ta kalli ameera tace yaya,, naganta tace naje na taimaki ahalinta,,, nafiddasu daga hudu zuwa haske,, , bata ida maganar ba marar ta tayi wani murdawa,, mukewa tayi ajikinsa cikin jin azaba tace yaya mutuwa,, zanyi cikina kaina marata duka ciwo suke cikin tashin hankali,,Ameer ya dauketa yayi kasa,,

Thank you for comments and share inayinku FAN'S
[27/10, 19:10] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€โœ

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซJARUMAI WRITERS ASSOCIATION ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ

MARUBUTA MASU AIKI DA JARUMTA DOMIN WA'AZANTARWA ILIMANTARWA, NISHAD'ANTARWA TARE DA FAD'AKARWA DA JAMA'A BISA HARSHEN HAUSA ๐Ÿ’ช

๐Ÿ’ซ(J.W.A)๐Ÿ’ซ

27โ€”28

Da sauri yake tafiya, kamar, wani " zaucecce, kofar, dakin " mom yake bugawa,, da karfi, yana mom daddy please, come in ' cikin bacci mom " taji karar bugun kofa a firgice, ta mike ' tasaka,,doguwar rigar ta, daddy ma yamike mom,, kamar muryar"" Ameer nakeji mom tace muje, mugani ",suna mude,,, kofar ameer, sukagani " yana durkushe,, ameera kuwa sai mika takeyi, tana cewa yaya mutuwa zanyi please,, kakaini,, wajan mom,, da sauri "" mom ta amsheta tana cewa maiyasa meta,, daddy yace,, maza muje, hospital " waje suka fita da sauri,, daddy yaje wajan,, dakin baba mai gadi,, yace baba fito budemana,, kofa,yi sauri, da gudu gudu, yaje, yabude, ""daddy ya,, fige motar a guje, sikabar gidan, gudu yake sharara wa "dan tuni ameera tayi suma yakai sau uku " saboda azaba , suna, isa akayi emergency room da ita, " su daddy sai kaiwa da komowa sukeyi, ba kamar ameer ma da yake tunano maganar ameera da tace mishi ance za'a rabasu girgiza kai yakeyi

Mom kuwa, ita a tunanin ta " Ameer yayiwa ameera aika aika ne, gabanta sai faduwa yakeyi, da zullimi tayi tagumi tana tausayawa,, Ameera

Cen kuwa inda suka shiga da ameera kokarin saita mata numfashi, suke saida suka kwashe awa daya kafin numfashin ta yadawo nomal, nan suka mata allurori da karin ruwa,,

Wani doctor ne yafara fitowa, da alama shine babba nan sukayi wajan sa suna rige rigen tambayar sa,

glass din idonsa, yacire yakare musu kallon ,, kafin yayi magana

ameer yace please doctor maiya samu ameera ta idan har tamutu nima binta, zanyi

dafa kafadar doctor yayi yace comedown mana abokina bata mutu ba tana nan lfy kubiyoni office nan suka rankaya,

DR. Yace waye baban yarinyar

Daddy yace nine

Dr. yace yarinyar ku, ciwon ciki ne take fama dashi mai tsanani period ne yazo mata, yace amma wannan shine yinta na farko ko ?

mom tace eh DR. Na farkone

Dr. yace to idan da hali , nan da wani lokaci kuyi mata aure, saboda inba yimata, aure da wuri ba hakan kullin zatake yi idan lokacin period dinta yazo,,

da sauri mom tace to dr. Mungode, sosai yanzu zamu iya ganin ta yace eh zaku iya, ganinta,, nan suka fita "

Tin , daga nesa ameer yake kare mata kallon ta rame sosai tayi haske kamar ta jima tana cutar, suka isa basu jimaba daddy yace, wa ameer su je maseejit dan ansoma kiran sallar asuba, badan, ranshi yasoba, suka fice a dakin,,

Yana kwance sai juya kai, yake yi ganinta yayi kwace ta rike cikinta,, da alama ciwon mai tsanani ne, cen kuma yaga tadena motsi , kafin yazo wajan da karfi yace please ameera kada kimutu kibar, abokina kece farin cikin sa, a firgice ya farka, daga baccin da yake, sai zufa yake sharewa, yace tabbas akwai abinda yasamu, ameera inajin ajikina, karar buga kofa yaji ammi ce tace my son ankira salla katashi, katafi salla, daga zaunan yace to ammi na, yamike yayo alwala yafito, suka tafi maseejit da babansa, koda aka gama sallar,, tunani yake koya kira ameer ne yaji ameera tana lfy nan dai yace anjima zai kira shi da haka ya koma gida

Bayan angama,, salla suka dawo hospital din a zaune suka samu ameera mom na gyara mata riga da alama bata jima da tashiba gaishe da mom ameer yayi kafin ameera ta kalle shi tace morning daddy cikin, kulawa ya amsa yace ya saukin, jikin tace naji sauki yace masha Allah,, juyawa tayi kan ameer tace yaya barka da safiya,, yana murmushi yace yauwa ameera barka dai ya jikin naki tace naji sauki yace to alhamdulillah,,

Dr. dinne, yashigo yacewa daddy za'a rubuta,, musu sallama,

Ameer yabishi, suka biya kudin da, aka rubuta "" musu tukun yadawo , suka fita zasu,, shiga mota wayar ameer tayi kara yana dubawa yaga, Bilal yadauka yace assalam alaikum,, ameer ya amsa da amin wa'alaikum salam, suka gaisa,, ameer yake sheda mishi suna asibiti,, cikin damuwa yace, wanene ba lfy yace ameera,, amma yanzu mundawo gida Bilal yace Allah yakara sauki,, Ameer yace ameen frend, nan suka aje waya suma suka tafi gida,

Acen gida kuwa inna ce tafito bataga daddy yadawo,, daga salla ba, yaje gaisheta kamar yadda,, yasaba mata tana nan zaune, tana,, cewa kai wannan ai renin hankali ne kila ba Matar tashiba tahanshi , zuwa gaisheni, ga wannan futsararrun yaran nan na gidan nan,, tana haka su fatima suka, fito, suna gaishe da inna kallon su tayi tsab kafin ta turo dan kwalinta, gaba ta kunto goron ta tasaka abaki kafin, tace da bankwana ba zaku,, ganni ne wai ina, iyayen naku ne,

Fatima, tace to inna muma ina muka sani su a haka suka shigo, gidan da sallama,,

Da ido suke binsu, nan suka zauna ameera kuwa na kwance jikin ameer sai damke baki take saboda ciwon da takeji suka gaishe da inna,

Harara ta aika musu tace ina kuka je banganku ba

mom tace inna, kusan asuba mukabar gidan nan,, saboda ameera ta farka, da ciwon ciki mai tsanani,,

Da sauri inna tamike tace shine, baku tasheni, ba yanxu da mutuwa"" tayi saidai naga gawarta, kunkawo min, ita ,, tace zo nan ameera,

, Itakuwa batajin zata iya barin jikin ameer saboda dumi takeji tayi lamo sai lumshe ido, tayi , tace inna bacci nakeji,, Idan natashi zanzo dakinki, mukwana, baki a washe tace to,

Mom tace wai laraba bata gama, breakfast ba,,

Fatima tace kila tana kichen ta kuya tana kallon ameera tace tom Jerry yajikin naki,

murmushi, ameera tayi tace zan kamaki ne yarinya, dariya fatima tayi tace kiyi,, mugani mana,, hade rai ameera tayi tace yaya bacci nakeji,, dago kanshi yayi yaga mom da dad basa nan mikewa yayi ganin yamike , zai fice ameera tasaka kuka kallon ta duka sukayi, inna tace ke kuma lfy

Dagoda kanta tayi taga ameer yajuya mata baya sai danne dariyar sa yakeyi,,,

Ameera tace, yaya please daukeni shuru yayi aikuwa tasake sakin sabon kuka

Fatima da fauziya dariya suka kwashe dashi

A hankali, ta mike tana runtse ido , kusa dashi ta karasa a bayansa ta kwanta tace, please yaya

Salati inna tasaka tana cewa kai wannan yara Allah yashirye ku ban taba ganin tantirai sallamenmu irin kuba , dariya fatima da fauziya sukayi fatima tace kefa, inna bakisan soyayya, ba ashe,,

Kuka , Inna tasoma tace yanzu fadima ni kika zaga wai bansan soyayya to soyayyar ma taci ubanta

juyowa,, Ameer yayi yana share mata hawaye yace sorry abinci fa zan dauko mana shine na tashi

Shagwabe fuska tayi tace please kaje dani yace to, nan ya sunkuce ta sukayi kictchen inna sai zazzaga masifa take, fadan nata dai yana da manufa yunwa takeji sosai shiyasa , masifa ke cinta,

Suna shiga suka gaishe da laraba,, cikin kulawa take amsawa tace a a yar, lelen ameer waya tabaki, kike kuka murmushi ameer yayi yace baba laraba,, rigima ce takeji,, shafa kanta laraba tayi tace wai hakane yar lele,, turo baki gaba tayi tace baba laraba ba haka, bane ' banida lfy,, bana iya tafiya "" shine yaki daukana,, dariya baba laraba tayi tace to kiyi hakuri kinji yar lele,, Ameera tace to shikenan na hakura kara shafa kanta,, tayi saboda itadai,, tana son kasancewar,,*AMEER DA AMEERA* nan suka fice da abinci sama goyata "yayi suka yi sama inna na zaginsu amma basu kula taba

Suna zuwa ya sauke ya yakaita toilet ya wanke mata jikinta suka fito yashiga bata,, abinci tana ci sai mita take mishi shikuwa yana rarrashinta haka suka kasance kafin ya kwantar da ita nan bacci yayi gaba da ita

Washe gari da yamma Bilal ne da anass sukazo duba jikin ameera,, suka gaisa da yan gidan,, Bilal ne yasaci kallon ameera sai kuma yace istagafurullah,, ya kauda shedan basu jima ba suka bar gidan

BAYAN SHEKARA DAYA

Yanxu su ameera angirma sosai,, idan ka ganta bazaka ce 16years gareta ba, tayi saukar alqur'ani mai girma yanxu tana Jss 2 saboda ilinminta,, sosai take maida hankalin ta kan karatun ta ga kuma kulawar da take samu awajan yayan nata dakuma, yan uwan nata, kuma har yanzu babu abinda yashiga tsakanin su saidai,, idan ameer yajin bukatar mace zai rage zafi da ameera saboda tausayinta yakeji , sosai,,

Jamila kuwa, tayi bincike an tabbatar mata da ameer da ameera miji da mata, ne kuma yan" uwane, amma bata hakura ba kawayen ta na bata shawarar zasu kaita wajan,, boka a kashe ameera daga nan ai dole ya aureta,, da suka fada mata "" haka tamusu rashin mutumci tace saboda soyayya bazan kai kaina wuta ba,, nasabawa Allah,, saboda da son zuciya ta bazan taba aikata sab'o ba dan wani biyan bukata naba,,, ko kinsan cewa idan kuka je wajan boka ,, sallar ku takwana arba'in da kukayi,, bakuda ladanta,,kuma sai kunyi kwana arba'in kuna salla, Allah bai karba ba,, ta wannan hanyar kuke tunanin,, sakani ashe ku ba kawayen,, gaskiya bane "" badan Allah kukeso na ba dan kudi kukeso na,, kowa shuru yayi sai daya daga cikinsu, ""tace ai dama na fada miki badan Allah suke, sonki ba

Jamila tace ai sai yau nagane,, samira ke kadai ke fadamin maganar gaskiya,, nan ta koresu tace ko a hanya kada su nuna sun santa,, hakuri suka,, soma bata amma ta kiya nan suka bar wajan

Wani sabon mlm ne aka kawo school dinsu ameera tinda ya daura idonshi akan ameera yaji yana sonta yana tambayar wani dalibi yace gaskiya ameera tana da aure kuma mijinta likita ne,,bai yarda ba saida wata rana ameer yazo daukar ameera,, da gudu tayo wajan ameer,, "bude mata hannu yayi tana zuwa ta shige jikinsa shafa kanta yayi yana yar, dariya yace babyn yayan ta,, ya karatun dagowa, tayi tace alhamdulillah yaya muna shan karatu,, yace to naji dadin hakan sosai my wife,,

Duk abinda sukeyi bashir malamin su ameera yana kallon su,,amma bai yarda ba saboda yadda yaga suna kama sosai ""bai gama tunanin ba yaga ameer yana sumbatar kumatun ta da koshim ta itama mayar masa tayi nan ya dauke ta cak yasaka,,a motarshi, nafeesa ce ta karaso tace yaya barka da warhaka da "" murmushi ya kalli,, nafeesa yace, yauwa feena yakike, tace alhamdulillah "yace to masha Allah nan ta leka tace meera beyy saimunyi waya nan su ameer suka fita daga school din,,

Nafeesa na komawa yakira ta yace wai da gaske wannan shine mijin ameera,, , murmushi nafeesa
tayi tace,, eh mijin tane jinjina kai yayi'" yace to shikenan jeki,,

Yau ma kamar, kullin bacci tasoma,, kawai saita ganta a inda suke, haduwa ' da anty karima,,tana nan tsaye taji tace assalam alaikum yake kanwata,, da sauri mike tana murmushi ta rungume ta tace anty karima kwana biyu tace alhamdulillah ai naga kina busy ne shiyasa,, banzo ba nan suka zauna tace anty kince zaki fadamin sunan garinku da kuma taimakon na kike so na yiwa ahalinki anty karima tace yanzu kuwa

WACECE KARIMA

ni yar cikin wani daji ne wanda yake cikin jahar legos,,, garinmu ba musulmai bane suna bautawa gunki ne wanda ake kira da, balbu,, ni sunana jenifer kafin nakoma karima kullin ake zuwa wajan bautar,, amma ni haka, kawai bana son, zuwa,, kullin idan anje Wanjan bautar ni banayi, haka kawai naji na tsani balbu abin bautar mu,,, ahaka har muka kalla soyayya da joshow yana mugun sona kamar mai nima naji ""ina kaunarshi,,, dan uwana ne ahaka har mukakai,,, lokacin "'aure bayan aurenmu da shekara uku,, nasamu ciki murna,, wajan joshow kamar yamaidani cikinsa shida,, danginsa"" suna sona,, sosai ""ranar dana haihu,, kamar, a danginsu baa taba haihuwa ba,, haka suka ringa farin ciki, sosai nake samun kuluwa,,, saboda kawai na kasa samun nutsuwa da abin bautar mu,,kullin ina tunanin bayan addininmu,,akwai wani addini mai tsaki,, haka kullin naketa tunani ahaka har yarona ya shekara uku ,,ina kokarin komawa school ne aka kawo mana wani malamin karanta wanda na lura ba irin addinin mu yake ba

Wata rana na ganshi yana kai fuskar shi kasa,, naji yana zano wasu yare "wanda ban sanshi ba haka kawai, naji ina samun nutsuwa da wannan yaren nashi,, kullin nake rabewa idan muntashi daga school saina je inda yake,, wannan yaren nashi,, ina karatun nasamu ciki na biyu,, , shima mijina yasha murna da yan uwan sa,, inason tambayar malamin nan namu nako sunanshi nakasa rikewa amma ina tsoro wata rana nace zanje namishi tambayar

Ina zuwa nasameshi da wani,, littafi yana karantawa,,inaji naji duk nutsuwa tazomin saida yagama kafin na tambaye shi shin wani addini yakeyi,, yace min jenifer kennan addinin gaskiya nake mai tsaki mai tsabta mai cike da farin ciki da nutsuwar zuciya dama duniya da lahira nace,, menene ita lahirar yace lahira gari ne wanda idan aka je ba'a dawowa nan ne inda ake auna aiki dan adam inda zaa saka,, mutum ""awuta ne ko aljanna,,cike da tsoro nace dama,, bayan"" wannan rayuwar akwai wata idan mutum ya mutu,, yace sosai makuwa,, rayuwa ce wanda ba tsufa ba mutuwa a cikinta

Dana koma gida kullin cikin tunani da damuwa nake akan nima wutan zaa sakani, haka na kasance kullin sainaje yana ta yimin nasiha har wata Rana nace,, inason musulinta,, cikin farin ciki yabani kalamar shahada na amsa yafada min,, yadda zanyi komai a haka yake kowa min karatu kuma idan zanyi salla boyewa nakeyi sbd kar mijina yagani wata rana yayi tafiya,,nasamu,,damar ci gaba da addini na mlm na koyamin addu'a,in kare kaina,, kuma cikin ikon Allah nake haddacewa,, tinda na musulinta na tsabi sunan karima dashi yake kirana,,,, wata rana ashe abin bautar garin sungano ina bautawa Allah daya,,shine suketa aikamin da aljanu da abubuwan tsoro,,amma ina addu'a bazasu iya cutar daniba

Lokacin dana haihu ne bana salla alokacin sukaci galaba akaina,,suka kasheni ta hanyar shanyemin jinin jikina,,miji na yaji haihu ta kafin yazo ciwon mutuwa yamani na mutu,, , hauka ne baiyiba saboda tsananin kaunata dayakeyi,, inason zuwa, masa a mafarki amma banason ya zauce ne,,kece hasken garinmu ameera kece zaki yi jahadin musulintar da ahalina,, amma sai kaddara ta rabaki,, da mijin ki na dan wani lokaci ,, ,tana kaiwa karshen magana idonta yayo ja saboda kukan da takeyi,,

Numfasawa ameera tayi,, tace to anty ta wani hanya zan je garin

karima tace nima ban sani amma zaki je garinmu tabbas amma ina rokon kada kifadawa koda mijin ne wannan maganar kinji,, zatayi magana taga karima ta bace nan tafarka tana tunanin labarin Karima,, tamike tayi toilet ta dauro alwala tafara jera nafila,

Thank you for comments and share ina yinku
[27/10, 19:29] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซJARUMAI WRITERS ASSOCIATION ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ

MARUBUTA MASU AIKI DA JARUMTA DOMIN WA'AZANTARWA ILIMANTARWA, NISHADA'ANTARWA TARE DA FAD'AKARWA DA JAMA'A BISA HARSHEN HAUSA ๐Ÿ’ช

๐Ÿ’ซ(J.W.A.)๐Ÿ’ซ

29โ€”30

Tana idarwa,, aka kira sallar, asuba nan,, Ameer shima yatashi, , ganin ameera yayi tana,, jan tasbaha, murmishi yayi, saboda yasan matar tashi,, badai ibada, ba da bayan ta "" ya kwanto murmishi tayi ta shafo kanshi tana,, cewa katashi,, yace eh my wife,, natashi,, nan yatafi toilet yayo alwala,, yagabatar da nafila tukun yasauko,, kasa suka fice shida daddy,

Ita kuwa ameera tashiga tunanin taya zataje,, garin su anty karima, kuma wata irin kaddara ce zata rabata da mijinta,, haka dai takari tunanin ta bata gano komai ba nan tashiga wanka dan tana da lecture karfe 10:00 AM, da sauri take shiryawa ta gama shiryawa,, Ameer yashigo, da sallama,,"amsawa tayi ""bata dago ta kalle shiba,, tace yaya Fatima tafito,, yace eh ke suke jira nan ta mike,, daga "balla takalmin da take,, tace to muje ""

Kallon ta ya tsaya yi, tasha kyau sosai kayan sun amsheta kamar asaceta agudu,, hannun shi ta kama jin shuru yasa ta shige jikinsa tana, cewa yaya nidai, "" muje "sai alokacin yadawo daga,, duniyar tunanin yace to muje nan sukayo kasa

A falo suka samu inna ameera tazo wajan,, ta tace inna ta ya kike kin tashi lfy saita kwanta a cinyar ta shafa, kanta " Inna tayi tace, lfy ameera ameer yace antashi lfy inna saida ta banka mishi, harara tukun tace daban kwana ba zaka ganni,, jin haka yasa ameera tace kai inna yaya ne fa ,, ta mike daga " jikin inna ta koma ta rungume ameer tace yaya muje,,

Muhammad rasulullahi (s .a.w.) a ni maryama,, wannan yara wllh kun isheni,, Ameer yace to kice daddy yabani matata saimu koma,, gidanmu ""tagumi inna tayi, tace, hmm, dariya "" su Fatima sukayi,, nan subar inna tana fada,,

Nafeesa ce tafito itada ameer har da salim suna hira,, saiga jamila, tazo wajansu,, tace musu assalam alaikum,, juyowa sukayi a tare suka amsa mata,, wajan ameera tazo,, daure fuska,, murmishi tayi tace haba kanwata "" lefin me namiki, murguda baki ameera tayi tace,, ba ruwana,, dake ,, Jamila tace to kiyi hakuri,, bazan kuma ba "" sakin fuska tayi suka gaisa da jamila,, tace tabata member wayar ta shesuke gaisawa,, nan tabata, suna nan zaune saiga ameer yazo,, yana baking da gudu ameera tayo wajanshi,

Mude mata hannu yayi tashige,, dariya sukayi tace yaya i miss you dagota yayi yace,, sure tace yes su salim ne,, suka ""karaso wajan jamila tace kaga,, masoyan asali,,da sauri ya kalleta,, sai ya daure"" fuska yace lfy murmishi tayi tace ba komai ya kawoni ba nima anan nake koyarwa,, kuma sainaga ameera,, shine muka gaisa,, tace"" kayi hakuri, da waccen lokacin, sai a lokacin yasaki ranshi yace,, shikenan nafice,, nan suka musu sallama,, suka tafi gida""

Yau ameer duk murna yakeyi yakosa dare yayi dan yadda yakajin sa babu abinda hanasa amsar hakkinsa,,, a falo yasamesu,, ganinsu yayi duk cikin shiri. Da mamaki,, yake kallosu "yace to mom ina zakuje,, Fatima tace wai kauye zasuje,

Inna ce tace kozaka hanamu zuwane gatalalle,, murmishi yayi na jin dadi wato yau zaiyi bidirinsa ba babba agidan,,, yace,, haba inna nina isa, nace zan hanaku tafiya kauye" Inna tace da ameera zamu tafi maza,, jeka kira min ita "" tana zancen ameera tafito,, tace gaskiya babu inda zanje sai anbamu hutu,, baki sake;;; inna take kallon ameera tace dama ai nace ya asircemin ke amma baku dauki,, zancena " da muhimman ciba,, kowa shuru yayi ya kyaleta,,

Mikewa sukayi nan su ameer suka musu,, rakiya" har bakin mota anbar Fatima da ameera da ameer banyan suntafi su kuma suka dawo ciki,

Bayan isha"i suna zaune fatima da ameera suna jikinsa fatima ce ta soma bacci,, tashin,, ameera yayi yace zaikai Fatima dakin su nan ta zauna bayan,, yadawo yace mata my wife, kije kidauko hijab dinki muje wajen shakatawa, kafin goma tayi,, da gudun tayi sama sai murna takeyi,, yana nan zaune har tadawo tsalle tayi ta haye, bayanshi"" suka fita

Wajan yatsaru sosai ya birge ameera,, sai dariya take " yi yana zagaya,, ameer shikuwa yana zaune,, sai murmishi yake,, tana haka,,, a hango "" Jamila ai da sauri tayi wajansu,,ita kuwa jamila bata ganta ba,, saiji tayi " an rungume ta tabaya,, da sauri "ta juya,, wazata gani ameera "' itama da murna da rungume ta tace,, iyee kaga yar gatan ameera,, kedawa""kukazo tace nida yaya ne,, da hannu ta nuna mata shi,, ameer kuwa jin shuru,, yasa yayi saurin "" juyawa amma baiganta ba,, hankali "" atashe yake ,, kiran sunan ya hango yayi, itada, Jamila "" murmishi yayi kawai,

Su kuwa kawayen,, ameera wata mai gajen hakuri ,, tace kai amma anyi kyakyawa anan,, masha Allah, dayar, tace,"" wannan fa matar wanda jamila keso ce amma kalli yadda suka,,, rungume juna "' daya tace jamila fa yanzu ta hakura da, waccen gayen,, suna haka,, ameer yakaraso,, da sallama "" barin jikin, Jamila tayi ta isa ga ameer ta shige cikinsa,, shafa kanta yayi yace,,, har kinsa hankalina yatashi,, ashe keda "' antyn nakine, baki a sake suke kallon su ameera, daya tace kai gaskiya wannan soyayya tasu "" tana burgeni sosai, dayar tace,, wllh kuwa,, "" murmishi jamila tayi tace ayya Allah sarki,, ai ganoni,, tayi shiyasa,, tazo, murmishin shima ya mata, yace to muzamu koma, gida

Jamila tace da wuri haka haba dai yace eh, kinsan, kanwar taki "" shegen bacci ne da ita da wuri, turo baki gaba,,tayi"" tace anty jamila kina jinsa ko dariya tayi tace,,ai dama " nasan bakiyin , bacci da wuri. Gyada kai tayi,, Ameer yace to beyy da sauri,, Jamila tace dan tsaya kadan chocolate,, ta dauko"" a leda dayawa tabawa "" Ameera tace kanwata ga wannan da,,, murna ta amsa,, yana jin dadi "" nan suka musu sallama,,, Ameera na dagawa jamila hannu itama tana daga mata hannu,

Saida sukayi nisa tukun,, kawar jamila tace,, ikon Allah,, kinga yarinya kamar kun shekara,,goma,, murmishi tayi,, tace"" ai yarinyar akwai shiga rai

Tin kafin sukai gida ya siya musu kaji " guda uku nan , sukayo,, gida;; bacci tayi sai daukota,,, yayi suka shiga"" ciki bai tsaya ko ina da itaba,, sai a kan gado, saida yaje yahada musu ruwa mai dumi tukun yadawo,, tashinta,, yasoma "" turo baki tayi tace plus yaya bacci murmishi yayi,, yace zanyi maganin bakin wannan,, daukarta yayi ya kai toilet

Jinta tayi,, a ruwa bude,, idonta "' tayi, kamar zatayi kuka tace,, yaya ruwan akwai , zafi " yace am sorry ahaka suka yi wankan cikin,, wayo yake shafeta,,bayan sungama,, sukayo ' alwala bayan "" sun fito, suka tada salla,, ,

Suna idarwa da kyer ameer sukaci kazar,, wanke hannun su sukayi sukayo brush,, suna hawa gado,, ya janyota jikinsa,,, ita kuwa sarkin son jiki ,, tashige abinta,,

Kiss yasoma ,, bata mai rikita tunanin ta,, ji tayi abun yana neman,, wuce tunanin ta " kuka tasaka,, amma ameer baima San tanayiba,,, dan yafita daga haiyacinsa,,,Ameera kuwa duk dangin ta babu wanda bata kira ba har,, da,, kakansu"" baffa, nalahirashima,,,yasha kira,,, Inna kuwa da umma kiransu,, da ameera. ,, take,, yafi sau dari ,( ni kuwa ina ganin wannan lamari na dauki takalmina a hannu,, ya fita )

Duk wata soyayyar da yake mata tin,, daga" jaririyar " ta har,, zuwa yanzu " saida yasauke,, mata ita ,, su ameera fa baki yamutu,, ko magana takasa"" sai hawaye da takeyi,, har azabar " da takeji yasa tayi suma ""yafi sau biyar,, saboda azabar da ameer yake gana mata,,

Sai bayan awa ,, daya da rabi,, nagano su ameera,,, kamar gawa "" da sauri ameer ya janyota,, jikinsa,, yana saka "mata albarka,, yana shafa kanta,, jin shuru "" yasa,, yadagata yakira,, sunan ta amma yaji shuru,, saurin mude ido yayi,""yaga ameera kamar gawa,, nan ya rikice kamar wani mahaukaci "" ya rasa,, inda zaibi shi yama manta shi doctor ne,,

Da gudu yayi toile yahada ruwan zafi ya dauko ta,, jin ta tayi zafi yana ratsa ta wani kara tasaki ,, tana son" mikewa amma,, ya riketa ""saida ya mata ruwa yafi sau biyar,, yana gasata "" har bacci yadauke ta,, a cikin ruwa tukun,, yamata "wanka tsaki ya nadauta a,, towel kamar wata jaririya"" ita kuwa tuni tayi bacci,, abinta

Shikuwa ameer kasa komawa,, bacci yayi farin cikin, da yake ' ciki bazai musalta shiba, yana tunanin wai yau shine ameera ta dauke nauyinsa,, ya sauke duk wani abinda ke damunsa,, ,, tin yana dan 20years yake bama,,, da ciwon mara amma dake Allah ya tsiratar,,, dashi;; har yayi rayuwar london bai taba tunanin kasancewa,,, da mace ba inba,, Ameera saba,

Da asuba da wuri,, ameer ya farka kasa yaje,, yatashi "" Fatima,, tayi salla,,, nan, yadawo "" kusa da ita, yadawo " soma tashinta yasoma yi,, ahankali tasoma bude, ganin shine yasa,, ta saki kuku,, dan bata manta abinda yamata ""ba rungume ta yayi yana bubbuga bayan ta,, yace am so sorry my wife Allah"" yamiki albarka,,, yadda kika faranta min rai Allah ya faranta,, miki, Allah yabarmu,, tare, yasa fada,, mata ""zafafan kalaman soyayya,,

Su hajiya, Ameera kuwa anji zallar,, kalaman soyayya,, saima ta manta da ciwon amma tsoron yayan nata takeyi,, yace yaya amma bazaka,,, sake " yimin irin,, wannan abin mai ciwo ba ko ""murmishi yayi yace eh bazan sake ba,, yace to shikenan"" nan yayi mata wanka yazo,, kwantar, da ita yayi, yace zai duba "ta batayi muso ba dan yanzu bata jin ciwo,,,, sosai "" dubata yayi,, yaga aika aikar,, daya yi "" cike da tausayi yake kallon ta,, nan yabata shayi mai zafi tasha "" tasha magani,, yamata allurar bacci,, shima saida,, sukasha kokowa kafin yamata tana kuka har,, tayi bacci. Zaman gadin,, ta yayi ahaka shima bacci ya daukeshi,,

Kwanan ta uku tasamu sauki,,, su mom kuwa tana cen kauye "" daga cen zasu wuce ummara,, Inna sai washe baki akeyi,, yauma suna zaune zazzabi ya rufeta,,, gasu nafeesa sun rigata tafiya gida,,,tana tsoron yayan nata sbd jiyama,, bai barta "" tayi bacci ba,, tana nan,, zaune saiga,, Jamila ,, tafito""

A hankali take tafiya saboda muguwar gajiyar,, data yi jamila tana tsaye ita da mlm basheer,, sai ji tayi an rungume ta ansaki,,kuka""" mamaki ne,, yakama jamila,, shikuwa mlm basheer tuni yaga ameera,, ce amma ya rasa maiya sakata, kuka"" juyawa, jamila tayi tace,, Ameera lfy,,sake shigewa tayi jikinta tace,, anty mutuwa,, zanyi da sauri ta dagota tace,, subhanallah,, ameera mutuwa,, kuma,,taba jikinta "tayi taji, zafi sosai kamar,,wuta da sauri,,,tace ai zazzabi ne,, ajikinta"" Jamila tace mlm basheer sorry fa,, bari ' nakai kanwata ""asibiti yace to,, nan ta kamata"" suka bar wajan, suna shiga mota sunbar wajan saiga ameer yayi faking,, nan yaga bata;; nan tambayar wani student yayi yace,, shine "" yaganta tana kuka, amma yaga ta tashi baisa ina ta tafiba,,,

Mlm basheer ne,, yagano shi, da sauri yagarasa "" wajan ameer yayi masa, sallama "" nan ya amsa duk,, hankalin sa a tashe yake,,yace kaine "" Ameer yayan ameera yace,,,eh eh nine, mlm basheer yace yanzu tazo,, wajan malama jamila,, cikin tsananin "" zazzabi,,, da sauri yace please,, dan allah ina suke, yace suntafi;; asibiti,, ameer yace ya sunan asibiti mlm,,, yace gaskiya bansan ina zasuje ba,, nan ya mishi sallama,, yakoma ,, hospital dinshi,, ga marassa,, lfy nan amma ya kasa dubasu,, ya kira ameera yafi "" sau goma ba'a dauka, gashi bashida member jamila,, abin duniya "" ya taru, yamishi yawa , gashi,, yana son kasancewa, da matar ' shi amma bata nan,, duk ya hada gumi kwanci yayi a offer dinshi kanshi sai,, saramishi"" yakeyi

Thank you for comments and share my fans

[27/10, 20:19] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„ โœ

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซJARUMAI WRITERS ASSOCIATION ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ

MARUBUTA MASU AIKI DA JARUMTA DOMIN WA'AZANTARWA ILIMANTARWA,
NISHAD'ANTARWA TARE DA FAD'AKARWA DA JAMA'A BISA HARSHEN HAUSA ๐Ÿ’ช

๐Ÿ’ซ(J.W A.)

31โ€”32

Su inna fa yau ansauka,, kasar mu " saudi Arabia, a madina, aka sauke su, suna zuwa, ziyara" sosai inna takewa ameera addu'a yau kuma,, zasu fice makkah "" domin yin ummura suna,, isa daddy yakama;; musu hotel daki, da biyu,, bayan, sun gama hutawa suka fito,, domin zuwa harami,

Suna zuwa,, Inna na ganin mutane wanda basuda, iyaka "" duk inda tajuya taga mutane ne,,,, tin kafin taje,, gindin ka'aba kawai sai ta tsaya suna tafiya,, ita dasu mom,, ta tsaya hannu biyu ta daura, akai ta rusa kuka, kamar anturo mata mutuwa, mutanen wajen saii,, kallon ta sukeyi "

Mom ce ta juya. taga inna tana kuka,, da sauri tadawo,, inda take tace inna, lfy, sharce hawaye, inna tayi ta face majina tace,,, wai kuwa ni yar nan, anya ba tashin kiyama bane akeyi,, murmishi mom tayi tace,,a a inna taron yan ummura"" ne tace Allah sarki ameera inna mutu ina zakije.

Mom tace kiyi hakuri inna,, bafa mutuwa zakiyi ba, saida '"" tasha fama,, kafin inna,, ta yarda ba, tashin kiyama, bane akeyi " mutane, sai kallon su suke,, suna dariya,

Kofar,, aka buga ko kallon,, inda kofar take baiyiba saboda yanzu abu goma da ashirin,, yataru, ya mishi yawa, har aka gama buga kofar amma yayi shiru ga zuciyar sa na mishi zafi yanzu , ina ameera " wani hali take ciki

Su jamila na tafiya,, hospital takai,, ameera inda yayan ta,, ke aiki "" kafin taje , ameera har ta suma cikin tashin hankali,, Jamila"" ta daukota,, daga motar," tana kiran, yayan nata,, yaya kabeer! Yaya kabeer,, wata nosee ce tayi saurin,, shiga offer din, dr. Kabeer a tare , suka fito,, yana ganin kanwar tashi da sauri yazo ganin wata yarinya yayi ahannun ta kallon ta yasoma,, cikin kuka jamila tace please yaya,,, kaduba min ita da sau,, yabada izini aka amsheta,,

Tin daga school,, anty karima ke,, binsu ganin namiji,, zaiyi aikin " saitaji ba dadi,,dan haka,, karima ta baiyana,, da kayan likitoci,,, ajikinta "" tayi dakin har kabeer. zai taba,, Ameera da sauri tace dakata, dr. kabeer da sauri"" yajuya ganin wata,, matashiya dr. yayi ba musu yabata waje " tace duk su fita,, haka suke fita bako muso "

Jamila na ganin, yayan nata tace yaya ya,, jikin ameera " kallon ta yayi yace ana dubata zo muje,, nan suka tafi,, office din sa

Bayan kowa, tafita,, ajiyar zuciya ta sauke kafin, , ta shafa"' kan ameera nunfashin ta,, yadawo, kara hannu tayi a kirjin ameera ta bude,, ido, cike da mamaki take kallon anty karima, murmishi,, tayiwa ameera tana share hawayen fuskar ta ,

Ameera tace anty yaushe kikazo,, karima tace tin,, lokacin dakike"" a school,, nake tare dake,, yanzu dai kwanta ki huta,, zan kira yayan ki sai,, yazo kutafi,, riko,, hannun,, karima tayi, tana zubda kwalla, " tace anty, banason zuwa wajan yaya,, bacci yake,, hanani koda yaushe

Dagota, karima tayi,, tace kiyi hakuri ameera haka,, aure yake sai kina jurewa,, rungume,, karima tayi "" tace jikina ciwo yake min idan nabishi,, zai hanani hutawa shafa kanta tayi tace haba,, Ameera kefa jaruma,,, ce kada kizama "" mace mai raki mana,, idan kika saba bazaki sakejin ciwo ko gajiya ba , gyada,, kai tayi " tace to anty,, zanyi hakan inasonki,, murmishi tayi tace nima ina sonki
Ameera,, tace, bari na kira miki ameer din ko tace to

Yana zaune ya kasa sukoni,, yaji ana kira da har yayi,, kamar bazai dauka "" saiya duba,, da sauri,, ya dauke,, yace ,he hello,, wifi kina ina ne,, wata murya yaji tace ba ita bace ameera gata nan a kwance,, bata da lfy"" da sauri yace ina ne, nan tafada mishi,, sunan asibitin,,

Bayan takashe ne,, tace wa,, to ameera, sai gani na biyu"" nan , sukayi sallama,, tana, fitowa " taga jamila,, da sauri tazo wajan karima,, tace dr. Ya jikin kanwata,, murmishi,, karima "" tayi tace Alhamdulillah taji sauki zaki iya shiga,, nan tashige,, taga ameera,,, a kwance da sauri tazo inda,,, take dagota tayi, tace sannu,, sister murmishi,, tayi mata,,

Ita kuwa karima,, tana fita harabar,, asibitin taga ameer yayi faking,, tsayawa "" tayi tana kallon shi cike da tausayi,, ita abinda yake bata,, mamaki,, yadda suke kama " ita da ameer da ameera,,, kuma "" tana jinsu har cikin zuciyar. Ta,, nan ta bace abinta

Ameera ce tace anty yunwa,, nakeji,, Jamila tace yaya zai kawo miki abinci,, bata kai karshen maganar ba,, sukaji,, an bude,, kofa " dr. kabeer ne yashigo da sallama sai kallon,, ameera yakeyi "" ita kuwa tana mishi,, kallo daya ta daukai,, tasan dai " yayan tane,, ahankali yace beauty sannu, ya jikin,, kai akasa tace da Sauki murmishi,, yayi yace sister ga tea kibata,, amsa,, tayi tace mungode "brother zama,, yayi anan yana kallon su,

Dagoda,, Ameera,, tayi, ta soma,, bata "" kwabe fuska tayi,, tace anty,, sai kuma ta turo, baki gaba"

Murmishi jamila, tayi tace sister badai,, rigima ba""

Shima kabeer dariya,, yayi yace kai wannan " kanwar taki akwai shagwaba,

Harara ta aikawa,,, Kabeer,, tace kaidai baruwanka,, ai antyna nace tana murguda,, mishi baki "

Dariya yayi saboda tayi mugun tafiya,, da imaninsa""

Jamila tace,, menene kanwata,, kuka,, ameera tasaki,, ta sauko daga kan gadon na marassa lfy

Wajan jamila,, ta isa ta fada jikin ta,, rungume ta

Jamila " tace waya taba yar lelen Ameer, ne cikin kuka ,, tace ba yaya bane baizo ba,, kuma yunwa nakeji ""

Dariya tayi, tace to nima ai zan baki abinci,, tace,, ai ba irin nashiba"" murmishi jamila tayi tace to bari,, na kirashi kawo wayar ki "" dagowa tayi tace ai anty karima takirashi yana hanya,, jamila tace oh "" wannan dr. Din gyada kai tayi, shikuwa,, dr. kabeer sai kallon ameera yakeyi,, yace gaskiya yarinyar nan ta hadu, sosai,, zan bari sister saita shigar dani,,

Suna a haka suka ji an bude,, kofar da sallama, jin muryar yayan nata yasa,, ta dago daga jikin,, Jamila,, mikewa tayi,, da dan gudun,, ta ta fada jikinsa "" ta saki kuka,,

Ajiyar zuciya yasauke,, yana shafa bayan ta ,, dagowa tayi tace,, yaya shine kaki zuwa da wuri,,

Murmishi,, yayi yace,, am so sorry wife na,, suka karasa "" bakin gado, zama yayi tana bakale,, dashi

Murmishi jamila tayi tace, sannu,, da zuwa shima murmishin ya mata yace yauwa,, jamila thank you very much,,, Allah, yasaka da alkhairi"" jamila tace,, ai basai kayimin godiya ba,, nima kanwata ce,, , tace ga yayana,, ku gaisa kabeer kuwa ganin,, yadda suke mugun kama ne da ameera,, yabashi mamaki,, kuma yaji " yace mata wife,, nan suka gaisa da kabeer

Kuka tasake saki,, ta kara,, shigewa jikinsa shikuwa, dama dauriya " yakeyi, kabeer kuwa yama rasa shin ameera sister dinsa ce ko kuwa matarsa ce,,

Ahankali ta dago tace yaya yunwa da sauri,, ya mike yace bari,, nakawo miki jamila,, tace gashifa yaya nakawo,, ya amsa "" ya soma bata,, abaki ita kuwa,, jamila tana jinjina, soyayya irin wannan,, ,, ahaka har,, takoshi ""

Sallama suka musu,, kafin suka tafi gida,, suna zuwa,

Fatima tazo da gudu tana fadawa jikin ameer tace,, yaya kuka barni ni kadai a gida ,, baba laraba " ta jima da fita,, dagota yayi yace kiyi hakuri kanwata,, Ameera ce ba lfy shiyasa, da sauri tasakeshi,, tayo kan ameera tace sister yajikin naki "" murmishi ameera tayi tace, ai naji sauki sosai "" nan suka zauna,,

An soma kiran salla ameer yace suje suyi salla shima,, yafita bayan yadawo ne,, yake ce musu,, su mom gobe zasu dawo,,, aikuwa suka kama murna,,, sosai basu jimaba yace suje suyi,, bacci saida yakai fatima, daki,, yace tayo alwala tayo bayan tafito,, ta kwanta yamata,, addu'a "" sosai yaja mata barko tafita,,

Yana fitowa bai samu ameera a falo ba sama, shima ya haura,, , yana shiga room din yaji karar,, ruwa,, shima yacire kayansa,,, yashiga, toilet din,, tana wanka "" ji tayi an rungume ta murmishi tayi,, tace yaya, kissing din ta yayi,, nan sukayo wanka suka,, fito ,, nafila suka gabata kafin,, suka koma gado, ita dai
Ameera tana shan wahala,, awajan ameer baya raga mata,, da tanayin,, kuka amma,, tinda karima ta karfafa mata gwiwa,, jurewa, takeyi, koda kuwa wani lokaci zasu dauka

Tinda asuba ,, basu komaba " bacci saboda murnar,, su inna zasu dawo ameer ne yake shirya ameera,, sai mita,, take mishi wai bai iyaba,, murmishi yayi,, yace ai zan koya;; nan suka sauko,, Fatima itama cikin doguwar riga,, take, ta atamfa blue da mayafinta,, shima haka,, ita kuwa ameera riga da sket ne,, ajikinya nan suka fita,,

Suna nan jirgin su,, inna yasauka,, a felin,, girjin,, ,daddy yafara fitowa sai inna da mom,, fauziya ce karshe nan sukazo wajan su,, ameer ,,,

Ameera taje wajan daddy da gudu ta rungume shi,, tace oyoyo daddy,, shafa,,, kanta, yayi yace my daughter munsame ku lfy,, tace lfy lau,

Wajan mom tazo itama ta mata welcome back,, tukun inna,

,ameera tace oyoyo inna ta,, nayi kewar ki murmishi inna tayi,,, tace nima haka yar albarka,,

Ameer ne ya zo wajan,, su inna yace welcome back inna,, shima rungume shi tayi tace yauwa ameeru,,, nan suka "" rankaya,, sai gida

Bayan sun hutane,, aka soma raba,, tsaraba,, sarka mom tasiyowa,, ameera mai kyau,,murna kuwa wajan ameera baa magana,, shikuwa daddy, lefenta, ya hado mata,,Inna kuwa,, dogayen riguna,, tasiyo wa su,,, ameera da darduma,, hadda ta karmi,, sosai gidan ya kacame da surutu,, ajiyar zuciya ameer yasauke,, yace lalle "" jama'a ma rahama ne

Yau su inna kwana nansu,, goma,,da dawowa "" sosai mom taga cenji daga ameera,, bata yawan, shirmen magana,, ita har mamaki,,, takeyi,,

Yauma suna zaune a falo sai hira akeyi,

,Inna tace yar albarka,, ai insha Allah asirin da wannan,, gantalallen,,, yamiki,, namiki addu'a sosai,, kinma rabu da sihirin,, daya miki,, dariyar su suka danne,, dan kar inna asoma,, masifa,

Da dare suna zaune basu wani jima ba

ameer yace musu saida safe nan ameera ta,,mike suka tafi,, inna kuwa cewa tayi andai ji kunya

Thank you for comments
[27/10, 20:35] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

33โ€”34

Suna zuwa,, tin kafin su, karasa" cikin room din ameera,, tasoma tafiya ' a hankali saboda muguwar "" gajiyar datayi,, suna zuwa, ta zube akan bed din,

Tace wash yaya wllh nagaji jikina ciwo yake, kusa, da ita yadawo ya kalleta, da tausayawa yace ayya sannu wife,, murmishi tamishi " saboda maganar ma bazata iyaba

Janyota yayi zuwa jikinsa,, yaji zafi sosai zazzabi ne ajikin ta,,, ita kuwa ameera dama,, abinda takeso kenan " ta kara rungume shi,, murmishi yayi tace,, wife badai son jiki ba itama murmishin tayi,, tace yaya Allah kwanciya ajikinka,, akwai dadi sosai,, ina jin dadin baccina idan na kwanta,, ajikinka "" gashin kanta, ya shafa, yace nima haka wife,, na

Ina samun nutsuwa idan ina tare dake,, yace yanzu dai " tashi muje muyi nafila sai mu kwanta,, tashi tayi daga jikinsa,, suka, shiga toilet "sosai takejin zazzabin,, amma haka ta daure suka yi nafila,,

Bayan sun gama ne,,, suka koma gado" da sauri,, ta shige jikin ameer shi dariya ma tabashi,, yace kai ameera kamar kinajin,, tsoro, kasa da murya tayi tace sanyi ne,, nakeji,,

Kallon ta yayi, yaga yadda take fitar da numfashi,, mai zafi, dagota yayi yatashi wani waje abude acikin,, dakin inda kayan sa na hospital ,yake aciki allura yadauko,, yazo " idonta a rufe bata budeba,, janyota yayi ya matseta,,

Batayi aune ba , taji an cira mata,, allura,, kuka ta saki,,, tanason " ta gudu,, amma ya rike ta,, sosai, kuka tasoma yi,, rarrashin ta yayi,, yace wife dago kai tayi,, yace please kiji dani, mana kallonsa tayi tace da mai,, yace yau a dan,, barni huta " kozan samu nutsuwa "" murmishi tayi, taboye fuskar ta,, wai taji"" dariya yayi,, yace please,,, mana wife wllh ina cutuwa, kwana biyun,, bai gama ba yaji,, saukar numfashin ta,,, yace to har bacci ne haka ya hakura,, amma yaji ciwon mara ya soma taso mishi,, saboda ameera da take yamutsa shi,, tana bacci

Afalo,, kuwa, , Inna sai masifa takeyi tace,, wannan yara,, nidai bansan "" wasu aljanune suka shigesu,, ba a to nidai baruwana, "badai na fada muku gaskiya ba kunki to shikenan,,,, ai dama "" baku daukeni a matsayin babba ba,,, tana fadan,, batasan duk sun barta,, a falo ba,, saida ta juya taga ba kowa,,, daki nufa itama,

Yau da sauri,, yake shiryawa,, ya, sauko kasaa ko break bai yiba,, ya fice agidan,, saboda ankira shi da asuba,, akan akwai emergency"" wadda take,,, bukatar taimakon gaggawa,, a hospital dinshi,,, yana zuwa,, da sauri wata nosee "" tace good morning sir,, amsawa yayi,, yace maza kije,, kihada kayan aiki ganinan zuwa "" da to,, ta amsa, shima yayi office dinsa,,, " bai jima ba,, ya shigo emergency room din turus yayi ganin marar lfy

A hankali ya karasa,,, baki na rawa yace,, Bilal,, dagowa bilal yayi yana murmishi,, saboda tsananin ciwon , dayake" ji da sauri ameer,, ya hada,, kayan " aiki suka soma masa "" allurar, kashe ciwo , sosai yake mamakin,,, to minene,, yasa abokin nasa accident,, haryaji,, raunika haka,, "" saida suka gama,, yadawo,, kuda dashi, yazauna "" akan kujera,

Yace abokina,,, maiya saka yin accident, ahankali bilal yadago yace,,, wllh kawai " da fito daga,, wajan aiki ne, zanje,,, gida da acen zan kwana ma kawai sainaji "" bazan iya ba shine fa nataho,, ahanya, mukayi karo,, da wata mota,, shine naji,, raunika "

Numfashi ameer,, yasauke " yace Allah yakiyaye gaba bari na kira,, Ammi nafada mata,, nan yakira hankali,, tashe ammi tace gata nan zuwa

Yana fita office dinsa,, ya nufa"" wata,, mata,, yagani, a zaune da, alama"" shi take jira,, tana ganinsa tace welcome back doctor ameer,, kallon ta,, yayi yace yauwa suka gaisa yace mata,, meke damunta murmishi tayi,, tace rashin,, haihuwa,, dagowa "yayi ya kalleta,, yace kamar yaya,,

Kallon sa,, tayi idonta,, ya kawo ruwa,, tana "' hawaye tace yau shekara,, goma sha shida,,, Keenan da aurena,,,amma ban,, haihuba ba dangin mijina duk sun tsaneni,,, mijina kadai kesona" yanzu haka,, auren dayayi,,, yafi goma amma "" baa dace,, ba kuma lafiya lau muke,,, kawai ,, haihuwa ce,, taki zuwa "" nima inason,, na haihu "" nasamu yara,, jinina,, babu likitocin da bamuje ba amma sunce,,, bamu da matsala,, komai,, amma dangin,, mijina,,, sunkasa ganewa,, lokacin haihuwar ne bai zoba,,tana, kaiwa nan ta rushe da kuka wanda,, kanajinsa"' kasan daga zuciyar ta yake fitowa dan kana ganinta,,, kasan tana cikin damuwa,, marar,, musaltuwa,

Abin goge fuska,, yabata ta goge, hawayen ta""

Ameer yace kiyi hakuri hajiya su,, mutane dama,, haka " suke ba'a iya musu sai Allah,, yanzu da ace duk shekara za kike haihuwa cewa,, zasuyi "" kincika gida da diya, amma ki sharesu,,, kawai kiyi " harka gabanki,, tinda mijinki,, nasonki,

Dagowa,, tayi ta kalle shi tace,, kanina bakasan "" irin ciwon danake jiba,, idan anamin gorin haihuwar nan,, yace kiyi hakuri,, yanzu ya sunanki,, tace "" sunana,, Ikram sulaiman,, ni matar,, dan majalisa ce, Alhaji Abubakar Abdullah,, da mamaki ya,, kalle ta yace kece,,, matarshi,,eh tace,, dan Allah kanina,, ka taimake ni koda kasan wani malami,,, na addini "" mai aiki da alqur"ani, kozai bani wata addu'a,,

Dagowa yayi,, ya kalleta,, yace "" eh gaskiya wannan lamarin naki,, yakamata,, ki gwada " addu'o'i buga kofar,, akayi, a hankali yace, yes come in,,,

Da sauri, Ameera ta turo kofar,, da sallama,, juyawa,, Ikram tayi tana kallon ameera,,, wanda ta kwabe fuska kamar,, zatayi, kuka tsayawa,, tayi a bakin,, kofar,, mamaki ne,, yakama Ikram, saboda ganin taki karasowa,,,, kuma tana kuka yanzu ,, murmishi taga ameer yayi "" sauka yayi daga,, kan kujerar,, yakoma wajan hutu,, ya zaune,, kuka ameera ta rushe dashi,, ita dai ikram tana ganin ikon,, Allah

Hannu,, ya bude mata da sauri ameera,, taje wajan sa fadawa,, jikinsa,, tana kuka bayanta yake bubbugawa, yana murmishi,, dagota,, yayi yace""haba wife kefa kincika rigima,, kinga fa bakuwa nayi,,, ko gaisawa bakuyi,,, tace, yaya kallon ta yayi,, yace na'am waya taba,, min yar lelen yaya,, turo baki tayi" tace ba kaine ba,,

Baki ya, rike yace, to ni kuma,, menayi,, kwanciya tayi,, ya gyara mata kwanciyar,,, ajikinsa,, tace ina,, bacci katafi kabarni, ko school baka,, kaini ba"" kuma yunwa nakeji,, murmishi yayi yace to kiyi hakuri aikin gaggawa, ne yasa" nazo da wuri,, tace to shikenan,

Ita dai, Ikram yau tana kallon ikon Allah,, sai taji suna,, burgeta"" taji yace wife matarsa,, ce ita kuma,, daga gani auren gida ne aka musu,,

Ameer yace to tashi ku gaisa da bakuwa dagowa tayi,,, tasauka daga jikinsa"" taje inda ikram take,, tace hajiya barka da warhaka,, murmishi ikram tayi. tace,,, yauwa ya'ta ykk tace Alhamdulillah,, kafin tadawo,, wajan ameer,,

Ammi ce tazo,, hospital din ta kira, ameer tace ina ne dakin da,, Bilal yake nan ya fada,, mata ta kashe wayar ta shiga ciki,,

Kallon ikram,, Ameer yayi yace,,, zan baki addu'a yanzu kike yinta zaki,,, kwanta ki shafe jikinki,,idan kintashi da safe haka zaki sake yi,,, cikin farin ciki tace to kanina,,,nan yabata, yace, ga member wayarshi,, idan bata haddaceba,, zai mata voice ta,, WhatsApp godiya take mishi,,,, sosai hadda hawayen ta,,, zata tafi tace ameera,, babu,, bey bey "" kusa da ita ameera tazo ta rungume ta,, itama ikram rungume ameera tayi sosai tana kara jin dadi,, kafin,, ameera tace ""bey bey momsy,, wani dadi ne ya ziyarci, Ikram jin ance mata momsy,, kissing din, ameera tayi tace beyy baby sai anjima,,, kici abincin kinji,, to ameera tace kafin,, ta fice a office din,, Ameera tace yaya,, itama bayada lfy,, ne yace eh

Yace muje ki gaishe da bilal,, bashida, lfy "nan suka fita zuwa dakin,, inda aka kwantar da Bilal,, da sallama suka shiga,, da sauri ameera tayo wajen ammi tace ammi na,, kwana biyu,,murmishi , ammi tayi tace, Alhamdulillah ameera yau,, dake akazo aikin,

Murmishi ameer yayi yace,, Ammi rigimar tadai,, turo baki gaba tayi tace,, nidai bana rigima,,Ammi kinji yaya, ko dariya tayi tace,, kada kasake fada mata,, ,, ameera ta kalle bilal, tana turo baki tace""yaya bilal sannu ya jikin, murmishi yayi yace Alhamdulillah ,, tace Allah yakara sauki,, basu jima ba,, suka fita,,

Ganin ikram sukayi da, mamaki suke kallon ta,, ameera tace,, momsy baki tafiba,, hannu ta mikawa,, Aneera tace zo baby, nan ta karasa " wata leda ' tabata tace baby wa wannan kinji, bani member ki, Ameera waya ta fiddo ta bata, nan suka tafi itama, tashiga motar ta ta fice a wajan

Kullin su ameera ke zuwa,, ganin bilal har aka sallamesu ,, Ammi tace wa, Ameer idan,,, su Fatima sunyi hutu akai mata su ita da ameera,,

Sosai, Ameera ta saba da, Ikram suna waya, kullin " kuma tana aiko mata da kayan dadi,, ita kuwa dama ameera abinda take so , kenan,, yau ma ta, kira ta tace ,, hello baby ga direba nan a waje kito, gashi nan dayar,,, ledar kibawa" fatima da murna ameera tace,, yauwa momsy na,,, ina sonki,, daga wayar,, itama Ikram " tace nima ina sonki baby maza,, jeki, nan ta kashe wayar,,

Tana, fitowa nan yabata, da sauri, tayo gidan tace,,Fatima zo ki amsa, da sauri, Fatima ta zo wajan ameera,, ta amshi ledar " tsalle ameera tayi tace yauwa nawa dayawa,, ne ledar ameera bude nan , taga " dambun nama, ne dayawa" nan sukayi ta murna

Itama,,, Ikram tace wa ameer idan ameera,,, tayi hutu,, akai mata ita,, to shidai "" Ameer ya rasa wazai kawai,,, sai yafadawa mom,

Mom tace to tinda haka ne suje, ko ina suyi sati nan ameer ya mince da shawarar mom "" su Fatima murna sukeyi zasuje week har,, gida biyu, yau saura"" kwana hudu,, abasu hutun;;

Suna kwance ,, yace ni sai wani shareni kikeyi, ,, tayi tace haba dai yaya ni na isa,, na shareka, ai bazan iyaba " yace to meyasa yau kusan sati kin,, hanani jin dadi,, boye fuskar tayi,, tace, to na hana kane bare kace ma,, nice da lefi kallon ta yayi yana yana zancen zuciya, yace kaji wai bata; hanani ba kamar ba ita bace kullin take kwana da zazzabi idan,,, yasauka "" saidai tayi ta juyi akanshi, tofa yau,, hakurin shi' ya kare

Fuskar shi ta shafa tace,,, yaya kallon ta yayi,, yace to yau nace abani hakkina,, turo baki gaba tayi tana son yin korafi, saita " tuna da maganar karima,, tace kada kikewa mijin ki korafi idan yana bukatar ki,, shigewa tayi,, jikinsa " tace yaya kayi duk abinda, kakeso ni takace,, da sauri ya rufesu da bargo,,

Yana zaune yaran,, nasa sunyi bacci ajikinsa,, ajiyar zuciya " yasauke,, yace jenifer"" yaushe zaki dawo ne yaranki na bukatar ganinki,, , ta bayansa yaji " ance masoyi da sauri ya juya jin muryar jenifer,, amma baiga kowa ba,, ita kuwa karima tana ganinsa,, sai kuka take,, ganin baby girl dinta " ta warware,,, sosai ga yaron ta,, duka bacci sukeyi ajikin,, baban nasu,

Joshow yace jenifer kece dama ai nace baki mutu ba,, amma " suna daukata a mahaukaci,,,, kusa dashi tazo,,, ta sha kan yaran nata tana musu addu'a sosai,,,

Tace masoyi ka kara,,, hakuri mai ceton ku na nan zuwa,, ina jin ajikina,, kamar zan kuma yin,, rayuwar irin tabaya,, , ko kasan cewa baa binne ni ba,, masu gidan abin bauta suka,, shanye,, jini na lokacin da akace na mutu,, suka dauke ni,, suka kaini wani waje mai,, duhu " anan suka ajiye ni amma sun hanani,,, komai ruhina ne " kawai basuyi,,nasarar daukewa ba,, saboda karfin addu'a

Cikin kuka take masa bayani shima,, kukan " take saboda yana ganin ta hannu tasa ta shafi fuskar shi tace ina jin ajikina,,, nakusa dawowa gareku,, insha Allah sai hasken musulinci,, ya bayyana "" agareku tukun hannu joshow ya mikawa karima yace please jenifer,, kada kitafi kibarmu "" yana kuka mai taba zuciya dan ba karamin so yake mata ba,, kai ta girgiza tace kayi hakuri mijina,,, sai wani lokacin zan dawo gareku,, tana fadin hakan ta face,, kuka yaje sosai yana,, cewa no jenifer no please come in kada ki barmu "" haka yayi ta kuka kamar yanzu yake ganin jenifer a kwance

Yau fa su,, Ameera za a tafi visitation,, sun hada kayansu ,, sallama sukayiwa mom da inna fuziya kuwa itama ta tafi,, gidan kawar su daddy, Mufeeda,

Suna zuwa,, ammi ta taresu sosai taji dadin zuwansu bayan sun huta,, ameer yatafi gida,, " yabarsu cike da kewar,, matar sa,,

Thank you for comments fans
[27/10, 20:45] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„โœ๐Ÿป

35โ€”36

Tinda sukazo,, suke ta wa ammi surutu,, kamar aku "" itadai ammi sai dariya take yi tace to kuje kuyi wanka kuzo muci abinci tinda yayan naku yaki zuwa da to suka amsa suka nufi dakin da aka saukesu wanka sukayi suka lokacin,, ana kiran sallar azuhar " saida sukay salla,, kafin suka dawo,, lokacin bilal ma yadawo,, yace a a kaga yaran,,mom yaushe kuka zo,, Fatima tace yaya munjima , da zuwa nan suka koma wajan cin abinci

Shi kuwa ameer duk yazama abin tausayi yak'i sakewa saboda babu sahibar tashi a kusa dashi,, dayaje aikin ma bai wani jimaba, yadawo gida har dare yana,, nan ko abinci yakasa ci,, kiran ta yayi

Itama ameera sai,, yanzu takijin kewar mijin nata duk ta kasa bacci ,, karar wayar ta ne,, ya katse mata tunanin da takeyi,

Dauka tayi tace assalam alaikum ya yaya,, amsawa yayi da amin wa'alaikum salam wife,, wllh nakasa bacci,, kuka tasaka mishi,, da sauri yace " maiya faru ne tace yaya,, nima nakasa bacci murmishin jin dadi yayi ashe matar tashi,, tana kewarshi "" yace to ko naje gobe na daukoku ne,, a hankali tace a a hira sukasha, sosai kafin,, bacci yayi gaba da ameera "" saida yaji saukar numfashin ta tukun yakashe wayar, yatashi yadauro alwala ya soma jero nafila "" bayan,,ya gama ne yadauki alqur"ani mai girma,, yasoma karatu,, har kusan, harfe ukun dare tukun bacci yadauke shi

Yau suna fitowa ammi tace zasuje shan iska da yamma rungume juna sukayi ameera da Fatima sukace, yauwa ummi mu ,, dariya tayi tace kudai bakuda dama,,

Ikram ce tafito daga,, sashenta kitchen ta nufa,, ko karasa wa, batayi ba warin abinda ake dafawa tacika mata hanci,, da gudu tayi toilet din falon tasoma kwara amai,, tin daga, nesa mijin nata yakeji,, karar nishinta " da sauri yashigo toilet din yace, subhanallah ikram maiyasa meki,, bata masa magana ba wanke mata jikinta,, yayi suka dawo,, falo " kwantowa tayi a jikinsa tana lumshe ido tace,,dear banason,, warin wannan abincin da sauri ya kira yar aikin yace ta dena girkin,, ,, family doctor dinsu, yakira ba'afi minti goma ba sai gashi yazo nan yasoma dubata,, da murmishi ya dago yace albishirinku,, a tare sukace goro yace sai anbani tukun nan mijin Ikram yaciro kudi yabshi

Doctor yace congratulation sir madam tana da juna biyu harna wata,, uku, " baki abude yake kallon doctor din yace ka tabbata yace sosai makuwa nan, yajuya ya kalli, Ikram wadda itama shi take kallo,, farin cikin da suka shiga baa musaltashi , Ikram tace batason yafada wa mutane abari sugani da kansu badan yasoba ya hakura sai nan nan yakeyi da ita ,, ita kuwa godiya takewa Allah har sujjadar godiya ga ubangiji sukayi, nan take fadawa mijin nata,, ai wani doctor ne yabata addu'o'i takeyi safe da dare, yace koda sihiri ajikinta zata rabu dashi,, kuma insha Allah zata haihu,

Da sauri yace kinga kuwa duk neman maganin damukeyi, bamu nemi ilimin alqur"ani ba amma,, yanzu gashi da taimakon Allah da addu'ar da bawan Allah nan yabaki yanzu gashi Allah yaji rokon mu kai, gaskiya ina cikin farin ciki murmishi tayi tace na manta ban fadaa ma ba saura kwana biyu baby zatazo hutu yace to shikenan Allah yakaimu,,

Ikram tace dear ko kasan babyn danake fada matar wannan likitan ce,, yarinya ce yar karama gata da shiga rai sosai,, murmishi yayi yace to ashe bakuwar ta mu ta musamman ce, tace sosai makuwa,,

Ameer ta kira tafada miki tasamu ciki,, farin ciki shima ya nuna sosai dan yaji dadi yace congratulation anty Ikram,, Allah yaraba lfy tace to ameen kanina,, ni harna kagu ka kawomin, baby murmishi yayi tace,, baby ko rigima yanzu tagama yimin kuka wai bazan kaita gidan momsy ba,, nace saura kwana biyu,, saida nasha fama tukun "" tabari sai jibin dariya,, Ikram tayi tace oh ni baby,, gaskiya kana shagwaba ta murmishi yayi yace ba dole,, ba

Tace ga mijina,, ku gaisa nan" mijinta ya amsa yanayi wa ameer godiya yace bakomai nan sukayi sallama ""

Yau su ameera zasuje gidan,, Ikram ammi ta musu tsaraba mai yawa " hadda Bilal ma yasuyo musu kayan sakawa,, harda takalmi da jaka " sosai suke murna " suna nan zaune suna yima ammi surutu,, Ameer yayi sallama,, agidan " da sauri sukazo a tare suka rungume,, suna cewa oyoyo yaya shima hadasu,, yayi ya rungume yana shan numfashi

Ciki yakarasa,, yace ammi sannu da hutawa murmishi tayi, tace yauwa son kazo,, ka daukemin yarana "" dariya yayi yace to ammi ayi hakuri, nan suka taba yar hira,, tukun suka musu rakiya har bakin muta

*Anan zan dakata*
[27/10, 21:01] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„ โœ๏ธ

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซJARUMAI WRITERS ASSOCIATION ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ

MARUBUTA MASU AIKI DA JARUMTA DOMIN WA'AZANTARWA ILIMANTARWA NISHAD'ANTARWA TARE DA FAD'AKARWA DA JAMA'A BISA HARSHEN HAUSA ๐Ÿ’ช

๐Ÿ’ซ(J.W.A.)

follow this link to join me my WhatsApp group:https://chat.whatsapp.com/KMuyxRBLx5iI93EEYIGlVX

37โ€”38

Gidan ikram suka, nufa ,, da murna ikram ta taresu,, ta fito daga,, cikin gidan zuwa inda motar su, take yana faking da gudu sukayo wajan ikram,, ita kuwa tana cewa oyoyo,, yarana ,,hannu ta bude musu suna zuwa suka rungume ta a tare,, yar dariya tayi tace iye yaran nawa ashe sun girma haka ,, dariya sukayi ameer ne ya karaso "" yace to maguna kardai ku gajiyar ta harara ameera ta aika mishi tace lalle ma yaya mune,, kuma maguna,, momsy kina jin yaya,, ko yana ce mana,, maguna"" murmishi tayi tace , kyalesa ai dai ba jikinsa,, suka taba ba " dariya sukayi tukun,, ikram ta musu izinin shiga ciki

Suna zuwa zama sukayi" nan takira yar aikin ta tace takai kayansu ameera ciki dakin da aka gyara musu ,, tare suka tafi,, Ameer sai kallon ameera yakeyi cike da so da kauna ga kuma ,, yana bukatar " kasancewa da ita saidai babu dama " ajiyar zuciya ya sauke , duk abinda yakeyi ikram na lura dashi yace to anty zan wuce kallon sa tayi tace yadai kanina kanshi ya saddar kasa,, dan bazai iya kallon " taba

Tsab ta ganosa tace kodai kewar baby kake ne,, murmishi yayi yashafa sajansa wanda yake , kara masa " kyau da kwarjini,, yace aikuwa "" anty kamar,, kinsani, murmishi "tayi tace kada kadamu idan kanason ganinta, kullin sai,, kake zuwa sosa kansa yayi,, yace ai anty zan iya jurewa " dariya tayi tace to bari akira maka ita kuyi,, sallama, mai aikin gidan ta kira tace takai ,, Ameer masaukin baki taje sashenta takira ameera,, nan suka fice,,

Da sallama tashiga,,, dagowa yayi yana kallon ta hannu yabude mata "" noke kafada,, tayi kira daya ya daga mata,,, da hannu yamata,, alama da tazo " hade rai tayi wai ita ala dole,, yabata mata rai,, dariya ma taso bashi " yace wife please mana kizo,, ahankali,, ta karaso"" inda yake janyota, yayi jikinsa,, a tare suka yi ajiyar zuciya,, yace yau kuma,, babyn momsy ni,, kike gudu

Murguda baki tayi tasake shigewa,, jikinsa tace ,, bakai bane " ta shagwabe fuskar kamar zatayi kuka, kiss yamata,, a koshi,, lumshe ido saboda,,, yadda taji kiss din yasheta "" murmishi yayi yace

Wai bazaayi min magana, ba turo baki gaba tayi tace ,,,ai maguna kace mana dazu "" murmishi yayi yace to shikenan sorry bazan,, kuma ba kallon sa,,, tayi " taga yadan rame kuma kamar yana cikin damuwa,,, saidai yarinta tahanata,, tagane ita yake bukata, tace yaya ,, amsawa yayi tace"" bakada lfy ne

Girgiza mata, kai yayi sbd bazai iya magana ba ,, a wannan time din,, kara rungume ta, yayi yace " wife please ki dan barni,, na rage zafi "" kallon sa tayi tace yaya menene shi rage zafin,, rauni kayine" ko zafi kakeji a karawa AC gudu,, kallon ta yayi yace ,,lalle bata fashimci komai ba tace "" eh yay..... Bata kai karshen, sunan ba , ya hade bakinsu " yana kissing din ta sosai,, kamar zai maida ta ciki " sai nunfarfashi yake saukewa,,, kamar Wanda yadawo daga,, gasar tsere, jin yana neman " wuce gona da yasa ameera,, tureshi,,, " amma takasa kuka tasa amma yayi banza da ita

Da karfi ta tureshi dayake yakai gabar rashi karfi saita kwace,, idonshi a lunshe yace, no wife,, babu abinda zan miki fa inason nasamu "' yar nutsuwa ne zanyi iya aiki yau,, tausayi yabata saita,, matsa kusan shi, ta kwanta ajikinsa, saida yasaita kanshi,, tukun ya saketa,, luf tayi a jikinsa,, kamar wata jaririya"" tace yaya rage,, zafin,, naka akwai dadi,,ba kamar irin na gida ba "" tace yaya menene sunan na gida wanda. kakemin,, amma wannan yafi dadi,,, mamaki yakama,shi ,yace tab lalle wife " da sauran ta ashe wato duk wannan abubuwan da mukeyi batasan sunan su ba,, ajiyar zuciya ya sauke,, yace shi waccen mai sunanshi,,,akwai wahala,, " wannan kuma,, sunan shi rage,, zafi,,

Murmishi tayi tace yaya idan mukaje gida zakake minshi kullin yace mai,, zai hana, hira sukayi sosai ameera na ta zuba shirman zance,, wata maganar ma shi sai ya rasa " daga ina take antayota,, yana bata labari saijin 'saukar numfashin ta,, yayi " yace bacci kikayi daukar yayi yafito falon nan yaga ikram na zaune tana ganinsu,, tace ""kaga ,AMEER AND AMEERA,, murmishi yayi yana sadde kanshi kasa , ikram tace to bacci ne tayi yace eh muna hira kawai naga,, tayi bacci,, Ikram tace kawota "" nanya kwantar da ameera a kujerar da ikram take kai,, kanta "ta saura, akan ciyar ikram,, ta turo baki gaba,, tace,, ihimm yaya bacci,, dariya ikram tayi tace lalle wannan kauna haka

Murmishi,, Ameer yayi yace, anty ai ameera tin tana jaririya nake sonta""itama da sona ta tashi, saboda kaunar " damukewa juna,, tin tana yar 12years zuwa 13years,, aka mana, aure da mamaki ikram take kallon shi, tace eh lalle gaskiya soyayyar ku,, acikin jininku "" take ba a zuciya ba yar dariya,,,Ameer yayi yace to nidai bari na wuce nan,, sukayi sallama"" yabar gidan,,

Yauma,, kamar kullin yana zaune yasaka yaranshi gaba,,, yashiga duniyar tunani ,, yana tunano,, maganar da,, jenifer ta fada mishi,, yanzu kenan abun bautarsu "" shine ya yasauke masa matarsa,,ake tunanin ta mutu,, yanzu dai tana,, cen ita ba rayayya ba ita ba gawa,, ba "" wani ,, irin ciwo, yakeji,, a zuciyar sa; bazai iya jure rashin,, jenifer ba,, " yana so yaga ranar da zata dawo agaresa,,,ajiyar zuciya yasauke,, mai nauyi tare da fitar da iska daga bakinsa mai zafi,, juyawa " yayi ya kalli mahaifiyar tashi,,

Cike da tausayi take kallon dan nata,, zama tayi,, tace joshow wai,,yanzu kai bazaka,, dena wannan tunanin ba,,,why kake haka ne,, kanshi,, yadaura akan kafadar,, shi yace,,

Mama ya zanyi,, nakasa dena tunanin " daurewa itama takeyi tace kayi aure kasamu wadda zatake,, rike maka yaran nan girgiza kai,, yayi yace " yace bazan iya aure ba mama,, please kidena,, wannan " maganar bana bukatar ta,,, shafa kanshi ""tayi tace,,, to shikenan nadena,,, amma kadena yace to,, mama tana tafiya, yasoma hawaye taya ma, zaa ce wai yadena,, tunanin matar shi " wannan ma ai bazai yiyuba,, haka kullin yake fama da,, kuka da tunanin,,idan kasanshi,,abaya bazakace shi bane, ,, saboda bashida komai,, sai tunanin damuwa "" tahanashi,, sukoni ga baya cin abin,, sai kuka,,

Ameer ne zaune office dinsa,, yana rubuce rubuce,, kofar aka yi noking,, izini yabada,, aka turo, kofar ganin jamila yayi,, da sallama tashiga,,amsa mata "" yayi yace barka da zuwa,,, yau kece agidan namu "' murmishi jamila tayi tace eh nice fa ainaga kirkin nakune yayi yawa, shyasa nima nazo da kaina,, murmishi ameer yayi nan yakawo mata ruwa,,

Bayan tasha ruwan,, tace waini ina kanwata,,, naga daga bada hutu nadena "" ganinta,, shiyasa nazo na ganta,, Ameer yace ayya ai kanwarki wllh nima kewarta nakeyi,,, sunje visit ne,, murmishi tayi tace to,, Allah yakawo su lfy yace ameen nan, sukaji ana,, noking,,Ameer yace yes come in,, ,, shigowa,, yayi da sallama amsa mishi sukayi,, idanshi, ne yasauka akan jamila,, wadda takewa,, Ameer murmishi ""

Shi kuwa ameer,, abokin nashi yake, kallo dan dama yanason yayi wannan hadin saigashi,, Allah yahadasu 'gyaran murya ameer yayi yace to kashigo,, mana, gemunsa,, Bilal yashafa yana,, murmishi ya karasa ciki,, gaisawa ""sukayi jamila ta gaishe sa tukun,, tamike tace " to kabani,, nember wayar "" Ameer yace to ba matsala nan yasa mata,,a wayarta tukun tace masa,,, sallama,, har taje bakin kofa taji sautin murya bilal nacewa,,bari,, nazo nakaiki gidan " ,, girgiza kai tayi tace no ka,, barshi ngd "' nan ta fita a office din ajiyar zuciya Bilal ya sauke,,,

Dariya sosai ameer keyi, harara bilal ya aikawa,, Ameer yace kai kuma,, lfy , cikin dariya yace "" a wani dai ya kamu,,murmishi yayi, yace wllh kuwa abokina,, yarinyar ta hadu,, murmishi ameer yayi,, yace to kake kirana " da yaya, kayi kamun kafa dani,, dariya shima bilal din yayi yace,, please friend wllh inason ta,,, ka gabatar dani " awajan ta ameer yace to shikenan ba damuwa,, dama " kaina yiwa kamunta,, , sai gashi yau,, kun hadu,, murmishi yayi yace Allah yabar mu tare,

Yace wai shi anass har yanzu bashida,, budurwa ne,, saida,, Ameer yayi dariya sosai kafin yace "" ai wannan tuni ya gabatar da kanshi,, a wajena,, Bilal yace ban ganeba ,, dariya yasake yi yace Fatima yakeso "' shima Bilal din dariyar yayi, yace eh lalle kace mun kusa shan biki,, ashe " Ameer yace sosai makuwa, haka suke ci gaba da hira tukun bilal ya yiwa, ameer sallama,, yatafi cike,, da kewar " Jamila

Su ameera, ansamu,, waje sai " katobarar su sukeyi son,, babu mai hanasu idan ikram zatayi" girki haka take jansu, suje suna, ta mata surutu, "tana koya musu girki da dubara,, Ikram kullin tana gyara,, Ameera saboda taga mijin nata ba sauki,, shiyasa take gyareta,, ciki da waje,, wani lokacin ma sai tana kuka ikram ke,, bata maguguna wanda ita take hadawa,, da kanta,, shiyasa yanzu,, Ameera tayi kyau kamar kasaceta,, ka gudu tayi qiba ta haska masha Allah,,da ita,,

Yau ma suna,, zaune saiga wata mata,, ta shigo tare " da wata budurwa na binta "" a baya da sallama suka shigo,, da fara'a ikram " ta taresu,, amma sai matar nan take bankawa, ikram harara ""murmishi tayi tace anty haleema barka,, da zuwa ya gida,,, ko ci kanki bata ceba "" bare tasa ran zata amsa,, sudai su ameera na kallon ikon Allah,, "

Anty haleema tace wllh ko mutum zai mutu,,dan uwana dai saina masa, aure,, da wannan tsaleliyar budurwar da,, kike gani " yar kawata ce,,, ita zata haifawa, kanina abubakar,, yara, ba irin kiba " juya shekara goma sha shida,, amma " shuru kamar an aiki bawa garinsu " saidai kici kisha kiyi mika,, ki kwanta, kiyi kashi,, " shine abinda kika iya "baki iya haihuwa,, itadai ikram murmishi,,, takeyi da Allah yabata ciki kuma zataci gaba da addu'ar da ameer,, yabata "

Ikram tace,, ai anty indai wannan ne banida, matsala " Allah yakaimu lokacin bikin, wani kallon ta aikawa ikram tace,, to munafuka " makira,, kunnukus,, lunbu lunbu wutar kaikayi,, to bari kiji in fada miki " duk bin bokayanki,,da malaman ki bakifi uwar,, wannan yarinya dan "" haka kashinki yabushe ,,a gidan nan,, yar mutsiyata,,,yar talakawa, ,, to wllh ashir dinki kuma bazan "" tafi ba sai gobe zamu tafi ,, sai yazo,, shi Abubakar din yaga,, sabuwar matar sa ba guzuma ba ,, irin ki,,

Ameera da fatima sunfa shaka sosai ran ameera,, a bace yake "" ganin hakan yasa ikram tace baby kuje daki ganinan zuwa,, badan tasoba suka"" tafi nan anty haleema tagama yinwa" ikram rashin mutumci son ranta,,, ita kuma yarinyar sai wani yauki takeyi,,, wai zata auro babban mutum"" sai wani iyayi take,, koda Abubakar yazo "" yaji haushin zuwa yayar tashi,, yasan kullin ba alkhairi,, yake kawota ba,, amma ikram ta bashi baki,,

Da dare su ameera sunkasa " bacci ameera ta tashi "" tace Fatima wllh zuciya ta zafi takemin,, saboda cin mutumcin da akayiwa,,, momsy na,,mikewa fatima tayi " tace koni bacci ma ya gagare ni,, ameera tace gaskiya inba,, ramawa,, momsy nayi bazan iya " bacci ba,, ashe haka rashin haihuwa yake mutane,, aketa cinmaka "mutumci babu,, abinda kayi,, Fatima ta dago,, ltace Allah yabamu da,, rashin haihuwa,, Ameera tace amen nan ameera tace,, kawo kunnan ki,, jiki " tana mikawa,, dariya Fatima tayi,, tace " yau zamu more,,nan sukayi falo

Wata wayar,, tv suka,, samu nan suka nufi kitchen suka,, shafa fulawa,,a fuskar su,, tukun suka saka fararen kaya,, sukayi dakin dasu anty haleema suke,,

Ahankali suka shiga ganinsu sukayi suna ta sharar bacci,, Ameera kuwa,,wani karfi taji yazo mata "jikin labulaye,, suka boye da karfi suka ,, zabga musu wannan wayar,, afirgice suka tashi,, a tare to dama duhu,,ne da dakin,, aikuwa sukayi ta jibgar su,,, gashi " kofar tasu idan aka rufe,, baa jin mai naciki yake fada " ga tsoro da sukeji, shi yahana su koda motsine,, , saida,, suka gaji dan kansu tukun saikayi lallab suka bar,, dakin dariya ameera take sosai yau ta tuna da kauyensu,, nan suka kwanta,, da farin ciki,, tinda sun ramawa ikram cin zarafin da aka mata

Comments and share,, comments dinku shine kwarin gwiwar mu fan,,
[27/10, 22:20] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„ โœ๏ธ

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซJARUMAI WRITERS ASSOCIATION ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ

MARUBUTA MASU AIKI DA JARUMTA DOMIN WA'AZANTARWA ILIMANTARWA NISHAD'ANTARWA TARE DA FAD'AKARWA DA JAMA'A BISA HARSHEN HAUSA ๐Ÿ’ช

๐Ÿ’ซ(J.W.A.)๐Ÿ’ซ

39โ€”40

Yau ikram ta, riga, kowa tashi , agidan dakin " su ameera ta nufa,, da sallama ta shiga ganinsu "tayi a jikin madubi suna kwalliya,, bama kamar " ameera tayi wata zabgegiyar,, gira kamar kura " ga digon da tayi afuska "" dariya ikram tayi tace kai haba baby yau,,, kuma kauye kika tuna "

Juyowa ameera tayi tana kunbura,,, baki tace " momsy yanzu banyi kyau ba,,

Dariya fatima tayi tace, tab kalleki kamar wata kura wllh irin,, kurayen nan masu neman abin nan ko sunga nama,,

Hade rai ameera tayi, tace " momsy kinga fatima ko dariya itama ikram keyi dan ameera kwalliyar datayi "" ko a kauyen ma sai ita,, Ikram tace kyaleta baby, wasa take miki Fatima tace Allah momsy bata, iya kwalliya ba koni nafita iyawa,, kalleta " kamar inna idan tana masifar nan,, dariya ikram takuma "" yi tana cewa yaran nan koda, mutum nada hawan jini,, idan kuna tare dashi,, zai sauka,,

Ita kuwa ameera tacika taci fam kamar fulawa,, sai huci takeyi,,Fatima tace,, "" waima ahaka yaya ke cewa babu wata sai ke to wllh nizan,, mishi budurwa " kima kama kanki,, yarinya,,kafin ikram tayi,, magana, tuni ameera tayo kan Fatima

Aguje, suka fito falo mijin ikram abubakar na zaman jiransu suzo, ayi break amma yagansu suna tsere,, dayake fatima jiki gareta,, amma ba sosai ba,, nan da nan ameera tacin mata,, ta shaketa,, shidai Abubakar yana ganin ikon Allah yace tab lalle yaran, nan basa rabuwa da rigima

, dambe suka kamayi "ameera nakai duka,, amma kuka takeyi " tana cewa uban waye zakiyiwa,, kishiyar kinma " isa mu biyu kadai zamuyi rayuwar mu,, Fatima tace sai anyi din ,, masifaffiya,, kawai,, sake binta tayi, suka kama zagaye,, a falon

Ikram ce tafito tana dariya,, ganin har yanzu suna "" fadan yasa,, tayo wajansu "" da sauri takama hannu ameera tace haba baby,, meye haka kefa babba " aike yayar tace,, tinda kin auri,, yayanta,,jikin ikram tafada ' ta saki kuka, tace momsy wai kinji tace,, wai zata min kishiya "" dariyar ta ta danne tace " babu wanda "" zai miki kishiya,,Fatima tace ba dole ba mata hudu, yaya zaiyi "" aikuwa ameera tabar jikin,, ikram tabi fatima " da sauri fatima taje bayan Abubakar ta boye tace,, please 'uncle kada, kabari tadakeni "" masifa gareta,, irin ta inna,, da sauri takaraso,, inda suke tace,, ni kika cewa masifaffiya to saina fadama yaya,, saita kuma sakin kukan "tana so ta kamo,, Fatima Abubakar yace haba,, baby ki kyaleta ai kinfita ita, da bata da mijin,, ma

Jin haka yasa ameera, dena kuka tace da gaske uncle nafita,, murmishi yayi yace sosai makuwa kinfita,, wajan ikram tadawo " da daura kanta a kafadar ikram tace momsy,,, aidai nafi Fatima ko,, tinda ina da miji"" shafa kanta ikram tayi tace eh mana kidena kukan,," fitowa fatima tayi "daga bayan Abubakar taje wajan ameera,, itama daura,, kanta tayi a kafadar ikram dayar "" dadi ikram takeji sai ta kallesu takuma kalli mijin,, nata, shima murmishi yayi, mata, fatima tace kiyi hakuri anty ameera,,nifa tsokanar kifa ' nakeyi yama,, zanso ayima " yar uwata kishiya,, dayake,,, Ameera bata rike fushi sakin fuskar ta tayi nan suka rungume ikram,, tace yauwa ko kufa amma kuna ta fada kamar kaji,, dariya sukayi,, Abubakar yace to kuzo muci abinci,,

Bayan sun zauna,, ne Abubakar yace waiko su anty haleema sunfito kuwa,,, ameera tace uncle kila basu tashi ba,, nan yace jeki kirasu,, kinji baby,, Ameer tace to mintsinin Fatima tayi,, nan ta kalleta "a kunnen ta ta rada mata,, cewa ke bakiga wannan kwalliyar zanje nasake tsoratasu,, Fatima tace to jeki,, nan tamike,, babu wanda yajisu, daga ikram har Abubakar

Tana zuwa kofar ta buga nan taji ,, shuru turawa tayi, shiga ganinsu tayi acure a waje daya,, ,, dariya tayi ta rufo kofar, nan ta yo wajansu,,, anty haleema ce tafara daga kai,, ganin mace kamar,, aljana yasata " bakale yarinyar data kawo,,

Kusa dasu,, ameera takaraso tace" wato ke gaki mai kani ko to wllh kika kuskura,,kika ce zakiyiwa, uncle aure,,abinda yasameki,, jiya saikinga ninkishi idan baki janye,, wannan maganar ba ,, ko harara kika yiwa momsy na "'zakiji a jikinki,, da sauri anty haleema tace ai daga yau ma bazan sake zuwa ba,, nadena

Ameera tace takidai ta ragemiki,, tace uncle na nemanku,, idan kukace kinga wani abu " to zan karya miki wannan kafar nan ta fice a dakin

Basu jimaba suka zo nan Abubakar da ikram sukace anty ina kwana antashi,, lfy da sauri tace lfy Abubakar yakuke suka ce Alhamdulillah,,,kallon ta yayi yace anty yamaganar aure,, da sauri,,anty haleema tace,, ina ai nafasa baka ita, nayi bincike, naga yarinyar " batada kamun kai,, murmishi Abubakar yayi,, yace to shikenan,, nan suka ce gida zasu tafi,, ikram tace dawuri ,, anty haleema tace eh da abinda zanyi nan suka musu sallama,,bandir din budu guda biyu yabasu nan suka mishi godiya suka bar gidan,,

Ameer na zaune yana,,,duba wasu takardu wayarshi,, ce tayi kara sunan, bilal yagani dauka,, yayi,,nan suka gaisa ameera yace friend please muje kakaini wajan ta wllh jiya banyi bacci ba,,murmishi ameer yayi yace wai gidan suwa,

Tsoki bilal,, yayi yace,, jamila muje na gabatar, dakaina,, dariya ameer yayi yace iye lalle,, wani yakamu da ciwon so,,, haushi ne, yakama, bilal yace, eh anji din,, nidai kakaini,,, Ameer yace ok to shikenan saikazo mutafi ko, nan sukayi sallama

Yana saukowa kasa yagansu,, zaune kusada inna,, yazauna yace granny andena" tafiya kauyen,, ko kallon sa batayi,, tace kaga ameeru ka kiyayeni,, meye kuma grady,, dariya ce ta subcewa ameer,,

Yace kai inna bafa haka ake cewa,, ba ,, cen kuma yace kinga inna da ina da,, aboki bature,, zan kawo miki shi nan yagaisheki ,,, Inna kuwa kallon tara saura kwata tayiwa "Ameer ta kunto goron ta,, ajikin zaninta,, ta rabashi a biyu, ta saka daya,, a baki ta maida,,dayan ta daure abinta,, duk suna kallon ta hade kira inna tayi tace

Kace zaka kawomin,,, abokinka ? Ameer yace eh inna,, Harara ta banka mishi tace,,

Postom ma yaci ubanshi,, shine ai shugabansu " ja"iri mai tsayi kamar nakumi,, sakaran hanza to kafita,, harka ta konama " wankin babban bargo,, ni zaka kalla kace wai abokin ka bature,, sangangamin banza mai kirar samudawa,, mai hankalin mutanen farko,, kallon ta yayi tace,, dena kallona "" hanci kamar karass,, shiyasa nace,, daga kai har ameera babu wani mai hankali,, ka maidata "" irinka,, takai karshen maganar tana hararar shi

Dariya ameer yayi aikuwa inna,, tace kayiwa ubanka dariya gashinan,, a zaune " yasake wata dariya,, tace wannan " kuma uwarka fadila kayiwa,,, gata nan a zaune,, kai bari kaji,,, idanfa " kadameni,, saina nakada maka dan banzan duka agidan nan na karya kafar,, naga ta yawon ,

,Ameer yace Allah yabaki hakuri,,

Inna tace da hakurin yamutu sadakar nawa kabada,,

kyaleta yayi " yamike saboda tin dazun Bilal yashigo inna,, nata masifa " gaishe dasu mom yayi tukun,, suka bar gidan inna "' na rakasu da zagi

Unguwar jan bilo
Gidansu jamila suka,,nufa " sai dariyar inna sukayi suna tunano ba"ar da takewa,, ameer,, har suka isa ameer yakira jamila yace sunkaraso,, nan tafito,, daga gidan zuwa inda suke da sallama ta iso amsawa,, sukayi " nan tagaisu,, tukun tamusu jagorar shiga ciki,,

Gidan su jamila yatsaru sosai,, part hudu ne agidan,,daya ba mamanta,, daya nata daya na baki,, daya na dr. kabeer,, nan tayi,, dakin baki dasu " suka zauna,, kara gaisawa sukayi,, Jamila duk sai sadde kai takeyi sbd kallon da,, bilal ke mata,, " nan ameer yace kanwata bari,, nabaku guri " kudan zanta "" nan yafice a room din

Bayan fitar,,Ameer, finsu minti Goma tukun bilal yace beauty yakike,, tana murmishi ta amsa mishi da lfy yagida yasu ammi,, murmishi yayi shima yace lfy lau nan suka sake yin shuru,, cen bilal yace

A gaskiya jiya, nafara ganinki amma naji kin kwanta min,, a zuciya naji ina sonki,, soyayya ta gaskiya ,, shiyasa " na matsawa abokina yakawoni,, na gabatar dakaina a wajanki da wajan " su baba,, ,, Jamila inason mukasance a cikin inuwa daya ma'ana muraya sunnar annabi Muhammad (S.A.W.) ,, jamila ta karasa fadin haka,,

Ajiyar zuciya tasauke tace,, na amince dakai,, dan nasan " yaya ameer bazai yimin abinda,,, zai cutar dani ba kuma yayimin, bayanin komai,, kuma na fashimta,, cike da farin ciki,, yace Alhamdulillah beauty inason ki,, rufe fuskar ta tayi,, tana yar dariya,, basu jima sosai ba " yace muje na kira ameer ki mana iso,, wajan su mama ko da to, ta amsa suka " fita ita tayi part din mama shi kuma ya fita waje

Yana fita yaga ameer shida dr. kabeer suna magana nan,,, yakarasa " wajansu suka gaisa da dr. kabeer tukun shiga gidan,, mama taji dadi,,da taga, abokin ameer ne yakeson jamila,, nan suka fito daga gidan, har bakin get ta rakosu " tana daga musu hannu dama sunyi,, masanyar member ita da bilal,, sai murna take tasamu saurayi hadadden gaye " kamar ameer

Bayan sallar isha"i zaune suke sunata dariya,, ikram tace waiku lfy kuke wani "gaman ido kuma dariya,, Fatima tace momsy ai munyi,, maganin yan iska ne,,

Ameera tace momsy,, ikram tace,, baby "wasu yan iska kuma,, suna dariya suka bata labarin komai,,, cike da al'ajabi da mamaki take, kallon, su tace haba koda najifa "" anty haleema bata amsa gaisuwa ta yau naga ta amsa,, ashe kune kuka,, rikita su " Ameera tace wllh momsy " munkasa bacci ne,, saboda rashin mutumcin da,, tayimiki ""shine muka mata kashedi tace har abada bazata sake yiwa uncle aureba "" dariya ikram tayi tace,, yaran nan gaskiya bakuda dama,, haka suka ringa hira har bacci yasoma daukar,, Fatima ikram tace, suje su kwanta,,

Yau zasu tafi gida duk sun hada kayansu suna jiran ameer,, Ikram tace zanyi kewar ku sukace muma haka momsy,,ai zamuke, zuwa duk week murmishi,, tayi tace to, ana yin la'asar saiga,, Ameer yazo daukar su,, da gudu suka karawa inda yake suka rungume shi a tare,,, yace iyee kaga yaran,, momsy " dariya sukayi tukun suka shiga,, ciki,, gaisawa sukayi suka taba yar hira tukun suka fito,, zuwa waje "da kayansu da tsarabar,, tuni ansaka musu,, ita a mota,, suna dagawa,, ikram hannu har suka fita

Ikram harda hawayen ta saboda sati dayan nan ba karamin sabo sunkayi, ba nan takoma ciki,,

NA GODE DA COMMENTS DINKU
[27/10, 22:39] MRS. MU'UTASIM: ๐ŸŒŸ๐€๐Œ๐„๐„๐‘ ๐ƒ๐€ ๐€๐Œ๐„๐„๐‘๐€ ๐ŸŒŸ

๐™Ž๐™ฉ๐™ค๐™ง๐™ฎ ๐™–๐™ฃ๐™™ ๐™ฌ๐™ง๐™ž๐™ฉ๐™ž๐™ฃ๐™œ ๐™—๐™ฎ

๐Œ๐€๐Œ๐€๐ ๐๐”๐’๐€๐ˆ๐๐€ ๐‚๐„ โœ๏ธ

๐Ÿ’ซ๐Ÿ’ซJARUMAI WRITERS ASSOCIATION ๐Ÿ“š๐Ÿ–Š๏ธ

MARUBUTA MASU AIKI DA JARUMTA DOMIN WA'AZANTARWA ILIMANTARWA NISHAD'ANTARWA TARE DA FAD'AKARWA DA JAMA'A BISA HARSHEN HAUSA ๐Ÿ’ช

๐Ÿ’ซ(J.W.A.)๐Ÿ’ซ

41โ€”42

Suna, isa gida da sauri su ameera suka,, fito daga motar " sukayi,, gidan , mommy , mommy suke cewa,, da sauri,, suka rungume,, ta suna dariya " sukace, i miss you mom,, kara rungume su tayi tace , miss you too,, sakinta,, sukayi sukayo,, wajan inna,, da take kallon su , kwanciya "" sukayi

,Ameera tace , Inna ta nayi kewarki,,, murmishi, Inna tace nima haka, yakuke, nan suka tashi ajikinta suka tafi wanka ameera tayi sama Fatima tayi dakinsu

Ameer ne yashigo da sallama ,, amsawa mom tayi, tace sannu, da zuwa yace yauwa,, mom sannu da gida, kayansu aka kawo mai gadi ya, yashigo,, dasu

Baki mom tarike tace wai, Ameer duk wannan kayan fa,, murmishi ameer yayi yace anty ikram ce fa mom, nace , sunyi yawa amma tace bata rageba " murmishi mom tayi, tace to Allah yayi albarka,, ameen yace nan ya zo wajan inna,, yace barka da warhaka inna ' dangware, mishi goshi tayi yace wash,, kai inna wllh akwai zafi fa, yar dariya inna tayi tace " sallamenme,, to ba yarda badai zanyi ka, kawo mana abokin ka bature gidan nan ba,

Dariya yayi, yace kefa inna baki mantuwa,, ai tinda, bakiso bazan kawoshi ba nan yamike yayi sama

Yana shiga,, tana fitowa daga wanka,, suna hada ido murmishi tasakar,, mishi shima murmishi,, ya mayar mata,, kusa da ita yazo " man ya amsa yace oyaa,, zauna nashafa miki, ba musu ta zauna, , tace yaya kallon ta " yayi ta cikin madubin tace nayi kewar ka, murmishi yayi yace,, aina fiki,, tace anya kuwa yaya,, yace sosai makuwa,, tace to shikenan ,,yagama shirya ta cikin doguwar riga suka sauko kasa,,

Su bilal soyayya ake zubawa shida jamila,, sosai suka saba da juna, hakan yasa, Bilal fadawa ammi ,, cike da farin ciki take saka mishi albarka,, tace da zarar babansa yadawo zata fada mishi don aje nema mishi auren ta sosai,, yaji dadi " da maganar ammin nashi,

Haka kuwa akayi, daddyn bilal,, daya dawowa ammi ta sanar dashi komai ,, shima da farin ciki yace,, zan kira Alhaji Muhammed,, sai muje da abban anass,, ammi tace to Allah yakaimu lokacin ,, yace ameen

Bayan kwana biyu, aka je tambaya wa bilal auren,, jamila baban jamila babu wani,, gardama " yabada ta,, aka saka biki, wata biyu masu zuwa ,, nan suka dawo " gidan cike da farin ciki , aka shedawa, dangi bikin bilal nan da wata biyu masu zuwa,, sosai kowa ke nuna farin cikin sa

Da sauri ameera, ke saukowa daga,, kan bainan,, Fatima ce tafito itada fauziya " suka gaisheda,, mom inna tana dakinta,, komai cikin sauri suke saboda yau islamiya ,, zasu tafi malamin su yace, kowacce zata,, amsa mishi tambayoyi dazai,, wa duk daliba,, acikin su,, basu ci na kirki ba suka tafi,, mom na musu addu'ar samun nasara ,, direba yakaisu yau saboda,, ameer shima tin da 6:30am yabar gidan

Kowa yazauna cikin aji suna,, yar hira nafeesa,, tacewa ameera besty, Allah yasa dai ayi mana tambaya,, marar wahala,, dariya ameera tayi tace to amen dai ke uwar " yan tsoro itama dariyar tayi tace bazaki ganeba bane besty shiyasa,, basu gama magana malamin yashigo cikin ajin kowa,, yayi shuru yana sauraron jawabinsa,,

Gyaran murya, malamin yayi yace " yau zamu bada tambayoyi daga cikin abinda ake muku,, zaku amsa yace ,,Ameera Ahmed ki fada mana shikaโ€”shikan musulinci guda nawa ne?? , muna jinki

Mikewa ameera tayi tace assalam alaikum yan uwa,, kamar yadda,, yake acikin littafin kawa'idi,,shikaโ€”shikan musulinci guda biyar ne gasu kamar haka

ุจุงุจ ู‚ูˆุงุนุฏ ุง ู„ุฅุณู„ุงู…:
ูˆุฃู…ุง ู‚ูˆุงุนุฏ ุฃู„ุฅุณู„ุงู… ูุฎู…ุณุฉุŒุฃูˆู„ู‡ุง:
ุดู‡ุงุฏุฉ ุฃู† ู„ุง ุฅู„ู‡ ุงู„ุง ุงู„ู„ู‡ ูˆุญุฏู‡ ู„ุง ุดุฑูŠูƒ ู„ู‡ ูˆ ุดู‡ุงุฏุฉ ุฃู† ุงู„ุญู…ุฏุง ุฃุนุจุฏู‡ ูˆ ุฑุณูˆู„ู‡ุŒ ูˆุจุนุฏู‡ ุฃู„ุตูŠู„ุงุฉุŒูˆุงู„ุตูŠุงู…ุŒ ูˆุงู„ุฒูƒุงุฉุŒูˆุญุฎ ุจูŠุช ุงู„ู„ู‡ ู„ู…ู† ุงุณุชุทุงุน ุฅู„ูŠู‡ ุณุจูŠู„ุง. ูˆู…ู† ู„ุง ูŠุนุฑู ู‡ุฐู‡ ุง ู„ุงุดูŠุงุก ู„ุง ุชุฌูˆุฒ ุดู‡ุงุฏุชู‡ ูˆู„ุง ุฅู…ุงู…ุชู‡ ูˆู…ู† ุตู„ ุฎู„ูู‡ ูŠุนูŠุฏ ุงุจุฏุงุŒู‡ูƒุฐุง ุฑูˆูŠ ุนู† ุณุนุจุฏ ุจู† ุงู„ู…ุณูŠุจ ุกุงุฎุฑ ุงู„ู…ุชู‚ุฏู…ูŠู†.::wato ma'ana

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.