Abadan Daiman Complete Hausa Novel
Reading file: Abadan_Daiman_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 2 of 4
ci gaba yayi da lallonta kamar yadda take kallonshi,tuni oily eyes dinta suka qara sheqi da sakamakon tsoro da qwalla da ta tarar mata,zuciyarta na raya mata mummunan abu abdallah ya yiwa abida,cikin hanzadi ta juya da nufin komawa dakinta ta banke saidai taku daya biyu ana ukun ya cafkota ya maidota baya,take jikinta ya soma bari,bakinta na rawa ta soma fadin
''don.....d....don Allah kayi haquri,ka fufamin asiri''
galala yake binta da kallo,tuni ya gano manufarta,ganin taqi nutsuwa ya sanyashi daka mata tsawa
''me zayi dake da har kike tsammanin wani abu zan miki?,koyin ma zanyi kin min kadan 'yar tsakuwa,abinda nakeso dake kada ki kuskura wani yaji abinsa kika gani?,ina fatan kin fajimceni?''
kai kawai take gyadawa babu qaqqautawa,burinta kawai ya saketa ta samu ta tsere,yana sakin nata kuwa ta shige dakin jiki na rawa ta murza key
binta yayi da kallo cikin mamkin mummunar fassarar da tayi masa tashi guda,koda ya koma daki sai yaji abun ya tsaye masa a rai,ta tuhumeshi da laifin da bai taba sha'awar aikatawa ba,hasalima ya tsani mai aikata shi,gefe guda kuma tsanar abida ce fal cikin zuciyarshi,yaci alwashin koda zata rasa rayuwarta bazai iya aurenta ba,yana da tsananin kishi ya tabbatar koa ya aureta din bazaya samu kwanciyar hankali ba
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
kusan dukkaninsu kwanan zaune sukayi babu wanda ya runtsa,kowa da abunda ke yawo cikin rai da zuciyarshi,duk da hakan maryam bata kasa tashi yadda ta saba ba ta hada breakfast,saidai babu wanda yaci,bata san da hakan ba sai da mami ta dawo ta hau sama ta kintsa kana ta sake dawowa qasa don yin karin safe,abida qunar zuciya ta hanata fitowa,abdallah yayi sammakon zuwa ofgice saboda wani taron gaggawa da zasuyo wanda shi kansa bai san da shi ba sai da asubahin ranar his excellency mr presdent ya sanar mishi,saboda haka kiegin qarfe shida yabi zuwa abuja
maryama kuwa tsoro da fargabar haduwa da abdallan ne ya hanata fitowa bayan ta samu ta kammala aikin ba tare da sun hadu ba
''shi kam abdallah ai ya jima yanzun a abuja,jeki kiramin abidar dai ta karya,ya zatayita zama bata ci komai ba''
kamar tace da mami ba zata iya zuwa ba don tana fargabar halin da zata je ta taradda abidar,bata da amsar tambayar da mami zata yi mata game da abunda zata ga ya samu abidan
ba zata iya qin zuwan ba don haka ta miqe jiki a sanyaye ta nufi dakin,sai da tayi knocking sau biyar kafin a bada izinin shiga cikin qaqqarfa kuma kausa sashiyar muryar abidar
ga mamakinta sai ta tadda abidar ta fito daga wanka ras da ita,babu wasu alamu dake nuna wani mummunan abu ya faru da ita
''meye kika tsaya kikatsaya kika zuba min idanun kin nan masu zubi da na mage?''
sai a lokacin ta ankara da tsayawa tayi kallon abidar
''mami ke kiranki''tana jinta tana tambayarya ta dawo ne tayi mata banza ta wuce
da daren ranar ta sake shiga wani rudanin,a hanyarta ta dawowa daga sashen baba uwani zahariyya ta sha gabanta ,tace taje nene na kiranta
zaune take gaban nenen cikin falonta na can sama,daga ita sai nenen sai zahariyyar
''maryamu kike ko?,nasan zakiyi mamakin irin wannan kira na bazata,ba komai bane yasa na kira ki wata buqace da ni wadda nake neman taimakonki gurin cikarta,ina fata kuma zan samu hadin kanki gun cikar buri na''
''zan iya taimaka mikin indai bai kauce addini na na ba''
wata dariya nenen ta kece da ita
''idan banda quruciya irin taki ai yanzu kowa ma ba bin qa'idar addinin yake ba,biyan buqata kawai ake nema''nene ta sake qasa da murya kana ta kuma matsowa kusa da maryam
''ba wani abu nake nema agunki illa poising da nake buqata kawai ki diga a abincin abdullahi''
a firgice ta miqe har jiri na shirin kayar da ita lokacin da nenen ta gama zayyana mata buqatarta,bari kawai jikinta yake,addu'a duk wadda tazo bakinta yi take
halin da ta shiga kawai ya ishi nene amsa
''kinga zauna ki nutsu,sai kace wadda aka ce ta diga a abincin ubanta,aikin nan fa ba a kyauta zakimin ba,biyanki zanyi kudi masu yawa da nauyi,zan dauke miki dukkan wani quncin talauci da kike ciki,zan wadata ki zan yalwataki''
hawaye ne ya shiga bin kuncinta,girgiza kai kawai take cikin takaici
takaicin ha'intar managarciyar mace kamar mami
takaicin cin aman ada yaudara da sukewa mamin
takaicin son dasa baqincikin da qunci na har abada da mutanen keson dasawa a zuciyar mamin
wannan cin amana da me tayi kama?,haka mutanen duniya suke
''bazan iya ba,bazan iya cin amanar mami ba ko duniua da abunda yake cikinta zaki bani''abunda ta iya fada kenan ta juya a guje zata bar sashen
''ke,dakata''mamin ta tsaidata,har ta iso gabanta ta kasa motsawa,cikin huci take dubanta
''rashin karbar tayi na yarinya daidai yake da tangal tangal da rayuwarki,arziqi na binki tsiya ta hanaki ki ganewa,kije....ko babu ke sai na cika burina,hanyoyin nada yawa,amma ki tabbata rayuwarki na cikin hadari,kuma wallahil azeem kika bari maganar nan ta fita sai na batar dake''
a sukwane ta bar sashen,da qyar ta kai kanta dakinta cikin mawuyacin hali,fadar irin halin data tsinci kanta bata baki ne
tabbas ta kuma gasgata cewa nene na iya aiwatar da duk abinda ta fada din,ta gani,cikin qwayar idonta
mafita daya take hangowa a gareta shine ta nemi miji tayi aure,ba zata iya kallon qwayar idanun mami ba tace tabar aiki,wata fuskar tafi gaban mari,aure shine zai rabasu salin alin
*_dukkan godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki_*
*_ina taya daukacin al'ummar annabi murnar zagayowar babbar sallah da fatan za'a gudanar da bukukuwan sallah lafiya_*
*_insha Allahu daga yau zamu je hutun sallah,littafin abadan zaici gaba da izinin Allah bayan qare hidindimun sallah_*
*_subhanakallahumma wabi hamdika,ashhadu an la'ilaha illa anta,astagfiruka wa'a tubu ilaika_*
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:53 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺 ▶2⃣8⃣
*_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*💡
*_wannan page din naku ne,wato mata iyayen gida,ku huce gajiyar sallah,Allah ya qara mana himma da lafiya,ya bamu ladan kula da iyali_*
material ne a jikinta mai baqi da fari,skert din baqine sol babu digon komai,rigar kuma fara ce mai adon baqaqen fulawoyi,irin dinkin nan ne da muke kira three quater iya gwiwa,skert din simple ne mai tsaga a baya,baqin mayafi ne tayi rolling da shi sai farin plate shoes mai igiya data sanya
a kasalance take nunawa ma'aikatan irin kayan da suke so su kuma suna cirowa suna sanyawa cikin keken tura kayan,qarfin hali kawai take,batason nunawa mami wani abun na damunta,duk da tana jin kamar zazzabi na shirin kamata
sannu a hankali suka qurewa bangarwn electronics dake cikin makeken shagon zamanin nan na shoprite dake ado bayero mall,suka juya bangaren warmers da plates cups da sauransu,daya bayan daya take bi tana zaban sababbin design
''subhanallah''suka fadi a kusan tare suka kuma ja da baya,tuni cups din da ta dauko sukayi nasu guri a qasa sakamakon karon da sukayi,a tare suka duqa suka soma kwashewa
''kiyi haquri madam don Allah ban kula bane''ya fada yana miqa mata guda ukun da yayi nasarar kwashewa,sai a lokacin ta dubeshi,baqi ne ba can ba zaka iya kiranshi da chaculet,dogo ne maras qiba,ya mata kama sosai da mutanen qasar habasha ko kuma baqaqen fulani
''ba komai'' ta fada tana amsar kofunan,kana ta rabeshi ta wuce
''ko am min izini na taya madam din zabar kayan duk da ba bangare na bane?''taji an fada daga bayanta,da sauri ta waigo mutumin dazun ne,tamkar tace a'a sai kuma taga babu buqatar ta fadi hakan
''bismillah''tace da shi
cikin hikima da dabara yake bayyana mata ko shi waye
''ni sunana abdur rahim tasi'u alhasan,ina zaune a unguwar qoqi dake tsakiyan birnin,ni dan kasuwa ne kamar yadda mahaifina yake,ina fata kin gamsu da dan taqaitaccen bayanin da na miki''ya qarashe magana lokacin da yake tura kwandon yana kuma kallon fuskarta
dan qaramin murmushi ne ya subuce mata
''to ni kuma meye nawa da sanin kai waye,daga taya ni siyayya?''
murmushin shima yayi bayan ya tsaida basket din
''ke kuwa kike da ruwa,saboda ina sa ran zamowarki uwar gida na,bazan boye miki ba tunda na ganki naji kin kwanta min,da gaske nake sonki *maryam*aurenki kuma nake so inyi anan kusa''
a mamakance take kallonshi,to ko addu'ar da ta kwana yi jiya ne Allah ya amshi roqonta?,babu shakka Alkah maji roqon bayinshi a kurkusa ko a nesa
''yaya akayi kasan sunana,bayan a iya sanina ban gaya maka ba baka kuma ji wani ya ambata ba?''
murmushi ya sakeyi
''maso dan tsuntsu shike binsq da jifa,sonki nake bada wasa ba hakan yasa nasan komai game dake kafin na iso gareki''
cikin wani mamakin ta kuma dubanshi
''kana nufin ba yau ka fara sani na ba?''
ya dage girarsa sama
''eh,kusan haka dinne''cike da mamakin shigowar abdur rahim cikin rayuwarta lokaci guda suka kammala dukkan siyayyrsu ita da abokan tafiyar tata,har lokacin abdur rahim din na biye da su hqr suka kammala,a bakin motarsu ya dubeta
''yaushe zanzo mu tattuna a nutse''ya tambayeta yana murmushi,dan jim tayi tana tunani a lokacin taji wayarta na ringin,da sauri ta cirota,ta duba,atsammaninta hindatu ce don tace zasuyi waya sai kuma taga baquwar number
''ga number dina nan kiyi serving zan kiraki naji lokacin da zanzo din''
da mamakin karona uku ta sake dubanshi,mamakin ina ya samu num dinta,kamar yasan me take tunani yace
''nasan mamkin inda na sami number dinki nake ko,kada ki manta na gaya miki dazu,na shigo sonki ne bada wasa ba hakan ya sanyani sanin komai game da ke tun kafin na iso gareki''murmushi ta sakar masa,sai taji abdur rahim din ya burgeta karo na farko,wannan wane irin so ne haka?
ko cikin motarma tunani abdur rahim din ta fada,tana gaya wa kanta ta samu mijin aure tabbas,tana kuma qarfafawa kanta gwiwar wannan karon zata shiga dakin aure kamar kowacce mace
bayan mami ta gama ganin kayan ta yaba sosai,don tace basu taba siyan kaya new fashioned and durable haka ba kamar wannan shekarar,kai tsaye dakinta ta wuce don tayi sallar la'asar su fara rage koda gyaran kitchen ne tunda taga da time,biyu daga cikin daki hudun dake rufe ta sake gani a bude,bata ce komai ba don ga tsammaninta baqi mamin ta sakeyi
da taimakon ma'aikatan harda baaba uwani cikin qanqanin lokaci suka fidda tsoffin kayan kitchen din suka fara shirya sababbi,aiki na yiwa maryam dadi sakamakon yadda yake tqfiya cikin tsari,sunayi kuna suna hiransu abinsu,kada ma baaba uwani taji labari,akwai abun dariya
''lamarinku na yaran zamani na bani mamaki''baba uwani ke fadawa maryam qasa qasa
''me mukayi baaba uwani?''maryam ta tambayeta tana fiddo da wani foodflask daga cikin kwalinshi
''mata su dinga biyo maza gida suna neman aurensu?''
''kamar yaya baaba?''
''hmmm,yaran nan mana dake son yaron gurin hajiya abdullahi,dazu daya yarinyar nan itama tazo da kayanta na satittika,ummm.......salamatu,mu a da ba sai an kaiki daki ba ma kike sanin waye mijin?,idan ma kuwa har kinsan waye shi din kafin a daura aurenku to ko hanyar da yabi baki iya bi saboda kunya,idan kuwa tsautsayi ysda kuka hada hanya to sai kinkusa qamewa a tsaye vaki iya motsi har sai ya wuce''
dariya ce ta kubcewa maryam
''baaba kin iya bata suna,salma ake cewa ba salamatu ba''
''kome me take ne barta,abun nasu sai addu'a,ko kunyar hajiya basa ji,ko fada ne ya kama yi suke a gabanta,abunda mu ko abinci baka iya ci gaban suruka,wannan zamani wannan zamani yazo qarshe,fatan Allah yasa mu gama lafiya''
''ameen''maryam din ta amsa mata da shi,daga haka bata ce komai ba,ita kanta mamaki take,saidai babu ruwanta don bata shiga shirgin da ba nata ba
ana kiran sallar magariba suka kammala aikin duk girman kitchen din yayi kyau ya sake haske,lallai sabon abu akwai kyau inji baaba uwani,ita kanta mamin ba qaramin mamaki tayi ba,ta sallami sauran ma'aikatan tana yabawa qoqarinsu
dakinta ta kuma komawa sanda tafito daga kitchen din abida ce zaune gaban makekiyar t.v plasma tana kallo sanye da matsattsun riga da wando,kusan duka shigarta kenan ta fidda tiraici ko doguwar riga zata sanya sai ta samu mai tighting jiki,wanka tayi ta sauya kayan jikinta,ta daura alwala tayi sallah,tana saman dadsuma tana lazumi ta tuna zata kira fa hindatu,ta laluba wayar bata jita ba hakan ya bata tabbacin ta manto ta a kitchen,ta gyara zaman ijabin jikinta ta fice ta nufi kitchen
su uku ta tadda yanzu a falon abida salma da abdallah da suka saka atsakiya,kallo daya zaka musu ka tabbatar daga abidan har salman ba jin dadin zaman suke ba,shi kuwa hakimin na tsakiya zaune yana ta aikin amsa waya,bisa dukan alamu wani aiki yake shiryawa don taji bada order din yayi yawa cikin fada da fushi
ilai kuwa cikin sabuwan kitchen wear din ta ganta,missed call goma ta taras,hudu na hindatu hudu na abdur rahim daya na raliya,murmushi tayi don dama ta sani bata da masu kiran nata sai su,sai ta rasa wanda zata soma kira a cikinsun,cikin haka kiran mami ya shigo
''kina ina ne maryamu,na shiga dakinki ban tadda ki ba''
''mami ina kitchen''
''baki gajiya ne maryam aiki sai kace inji,already baaba uwani tayi abinci ki huta haka nan don Allah''
tana jin dadin qaunar da mami ke nuna mata qwarai da gaske
''wayata na manta ma nazo in dauka''
''ok,ki sameni a parlour na''
''to''ta amsa mata ta cire wayar daga kunnenta ta fita daga kitchin din
''ke mero''taji an fada lokacin da take qoqarin hawa matattakalar benan
kamar kada ta juyo sai kuma ta waiwayo din don ganin mai mata kiran,abida ce
''meye kika tsatstsareni da idanuwankin nan kamar na?,shawarma nake sonci,ki shiga kitchen yanzun kimin idan kin iya''
rausayar da kai maryam tayi
''batun iyawa na dade da wuce babinshi,saidai lokacin aiki ya qare,zaki iya barwa gobw idan Allah ya kaimu,tunda majority utensils din duka sabbi ne bamu bude su ba''
cikin izza isa da gadara tace
''ke,wai mai kike taqama da shi ne,ki fadi nawa ne albashinki duka a nunka miki bama iya kudin aikin yau ba,ban mance ba rannan haka kika mana wani abu tuwo sunanshi ko me?nace kimin wani kalar girkin kika ban banzan answear irin wannan,kinsan wace ni kuwa?''
sakin makarin silver din da maryam din ta riqe tayi ta juyo ga abidan sosai
''ni ba kowa bace kuma bana taqama da kowa face Allah,kudi kuma ba zaki bani yanke talauci ba har abada,matsayin da Allah ya ajjiyeni ya gamsar da ni sosai na kuma gode masa,gaskiyata na fada tsarin siki na kenan cikin gidan nan,baquwa ce ke ina zato shi yssa kike mantawa,sannan ke din ma ba kowa bace face baiwar ubangiji kamar yadda nike kowa kuma yake''
a hankali abdallah ya dago kanshi daga kallon wrestling a tashar mbc action da yake ya dubeta,sai yaji amsarta ta burgeshi,babu hayaniya cikin raddinta,cikin calmnesses and cool voice,sai ya dan tsaida abunda yake yaga yadda za'a qare
tuni fuskar abida ta canza,cikin bacin rai ta dubi abdallah
''mu sugar kana gani da jin abunda yarinyar nan ke gaya min ko''ta fadatana nuna maryam wadda tuni har ta kusa kaiwa qarshen benan
murmushi ya saki mai hade da yar dariya
''duk bakery din dake garin kano kin raina,kin rasa inda zaki ci shawarma ne?''
''zaka iya kaini ne?'
''a lissafin lukuta na babu wannan,idan kina so akwai direbobi sai wani daga ciki ya kaiki ya dauko''sai ta sake tunzura,ya yrfata gaban salma kenan?,abunda madyam din ta mata ya hadu da wanda abdallah ya mata ya zamar mata zafi biyu
a zafafe ta miqe tana cewa
''tunda kai bazaka iya daukan matakin komai ba to ni zan daukarwa kaina,bazan zauna talaka 'yar talaka wulaqantacciya ta dinga taba mutuncina ba''
wani murmushin ya kuma saki ya kima kashingida
''eh kuma fa,gaskiyarki nima na goyi bayanki,kamarki diyar ambassador guda bai kamata a dinga samun iein haka ba,jeki dauki mataki''
sai ya kuma tunzurata don ta fuskanci kamar gatse yake mata ko kuma jirwaye mai kamar wanka,a haukace ta haye saman
kujera ta samu ta zauna tana fadin
''gani mami''
''yauwa maryam....cewa nayi''maganar mamin ta katse sakamon kiran da ya shigo wayar maryam din,screen din ta duba,sunan abdur rahim ya bayyana,sai ta maidata silent taqi dagawa
''ki daga mana maryamu''inji mami
murmushi tayi ta dan sadda kanta
''um um mami,ina jinki''
cikin murmushin da salon zolaya tace
''kodai suruki na ne maryam?''
sai kunya duk ta kamata tayi qasa da kanta tana murmushi
,ganin tayi shiru yasa mami cewa
''Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa,shawarata gareki ki riqe mutuncinki,ka kame kanki,mutuncin mace kunya da kamun kai,duk da nasan duka halayenki ne,idan na samu lokaci zan miki magana yazo inganshi mu gaisa''cikin jin dadi da gamsuwa da maganganun mamin take gyada kai,sai ta kuma tsokanarta
''bari nayi sauri na sallameki kada surukin nawa ya qosa da jirankin ko''sai ta sake bawa maryam din kunya
''kaya ne wadanda aka fitar da kayan firniture da za'a fitar gobe nake son ki zazzabi dukka abunda kike so ki kaiwa mamnki ko zatayi amfani da wasu wadanda bata so ta bada''
tayi mamakin yadda mamin ta bada kayqn,don kaya ne da babu abunda aukayi tamkar yau aka zuba su espicially kayan furniture din,ta wani fannin kuma ba abun mamaki bane saboda halayen mamin ne *karamci* da *kyauta*
sabanin wasu masu hannu da shunin da sun gwammace su saida kayan maimakon 'yan uwanau su amfana furniture ne ko kayan sawa,ko me zasuyi da kudin oho,bayan Allah ya wadata su ya basu arziqin amma suna maida kansu baya
''na gode mami qwarai,Allah ya qara girma''
murmushi mamin tayi
''bakin maryamu ya saba da godiya,nasha fadi miki ba haka tsakani na da ke''
kafin tace wani abu an banko qofar an shigo,abida ce kanta tsaye ta tafi gurin mami
''mami,ki shiga tsakanina da house girl din nan,hala bata san koni wace ba,ta raina ni matuqa,wallahi idan bata kama kanta ba zanyi sanadiyyar qulle danginta kaf babu wanda ya isa ya fito da su,batasan ba'a raina ni ba,bana daukar raini?''
kama kai mami tayi tana kallon abida
''qara kika kawomin ko mataki kika zo dauka?''cikin rashin iya magana tace
''duka mami''
ta riga da tasan abida rainon tabara ce,ta san ita har zuciyarta magana ta fada mai kyau,ta bar ta tata ta juya ga maryam ta tambayeta mai ya faru,a nutse ta gaya mata
''tashi kije maryam,sai da safe Allah ya bamu alkahairi''
''ameen mami''ta fada tana ficewa,yunqurowa abida tayi gurin maryam mami ta dakatar da ita
mamaki ne ya ishi maryam,tana shiga daki kiran abdur rahim ya shigo wayarta,murmushi ta saki ta isa gefan gadonta ta zauna sannan ta daga
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:53 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺 ▶2⃣9⃣
*_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*💡
*_home of expert and perfect writers_*
Kimanin awanni biyu suka shafe kan layi ita da abdur rahim din,ta fuskanci ya dan san wasu abubuwa game da ita wanda hakan ke qara mata amanna da qaunar da yake iqirarin yana mata din,tuni ta yanke ma ranta abdur rahim na daya daga cikin batutuwan da zasu tattauna a gobe ita da mamanta,bai barta ba har sai da ya fuskanci ta soma jin bacci tukunna ya mata sallama cike da qauna da bege mai yawa
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Abu na farko da ta fara cin karo da ahi cikin gidan nasu bayan yin sallamarta shine dambe tsakanin huwaila da haduza abinda zata iya cewa bata taba gani ba,daga gefan huwaila lubabatu ce da binta ke zuga uwarsu,yayin da kuna gefan hadizar kuma shamsiyya da yasira ne suma ke nasu aikin sai jamila dake zaune bisa dakalin qofar dakin mahaifiyar tata da uban akwati a gaba,idanu jajir wanda ke nuna bisa dukkan alamu kuka take sharba ko kuma take kan sharba din,mamanta ta hango na shirin fitowa daga dakinta hannunta ruqe da dankwalinta tana mai qoqarin daurawa hindatu na biye da ita tana fadin
''don Allah mama ki barsu''
Da sauri maryam ta taya hindatu tarar maman nata
''mama wanna ba sabgarki bace,kin taba ganin suna dambe?,to ki qyalesun kamar yadda hindatu tace Allah ne yasan me ya hadosu,babu ruwanki mamana tunda koma mene lokacin da zasu qulla basu nemi shawararki ba,kiyi addu'a kawai Allah ya warware musu ita ta ruwan sanyi''
da dadin baki suka sanyata a tsakiya suka koma cikin dakin abinsu,har aka gama shigowa da kayan suna bala'i basu sani ba
''amma maryama gini irin wannan namun ai bai cancanci kayan gado na alfarma irin wannan ba''
dariya ma maman ta baiwa maryam
''haba mama,tunda Allah ya baki sun cancanta din kenan,yanzu aikin kawai zamu shiga yi har kitchen din''
hindatu dake tsaye wadda farinciki duka yabi ya cikata tace
''yauwa adda maryam,kinga zuwa gobe mun gama zama 'yan gayu,babu raini wallahi,don duk cikin gidannan babu mai arziqin siyan irin wadan nsn kayan''
dadiya duka ta basu don har yau hindatu shirmen auta bai saketa ba
sai da suka soma fidda na dakin maman suna shigar da wadancan sannan suka ankara,lubabatu ce ta fara gani ta zunguri uwarta dake riqe da habar zaninta daketa kwancewa saboda azabar bala'i tana qoqarin daurawa
''huwaila tayani gani,kinga su kuma wadan nan ina suka samo kayan alfarma haka''
da sauri ta juyo don ganin abunda lubabatun ke nuna mata,idanunta suka sauka kan kayan fadon da buhun shinkafa catoon na taliya mscaroni da couse couse wabda mami ta hada mata da su irin kayan da Abdallah ke rabo na musamman duk azumi sadaka ga mahaifinsa mafigayi alh abdul kareem mai nasara
''kinga inda ake abu,kare ya san ana abu a gidansu,tunda gashi yana gani a qasa''
wannna zancan ne ya dauko hankalin hadiza kan kayan
''mtswew,aikin banza aikin wofi,kayam haram din da aka samu ta hanyar haram har wani abun fariya da alfahari ne?,kwadayi dai ai mabudin wahala ne Allah na tuba nawa akayi''
''kamar ku kenan da ruwan ya qarewa dan kada ko?'' wani irin ashar hadiza ta lailayo ta narkawa huwaila
''ai wallahi qaryarki tasha qarya,tuni na gama fahimtarki dama huwaila,sai kima kinsan cewa ba'a ja da masu kudi''
tsaki ta ja kana ta turo daurin dankwalinta gaba
''yo Allah na tuba ina abun yake,ina qudan yake ballantana romonsa?,game ce anyita kuma yau anzo game over din,sai kusa haquri masu rano su dara daga inda kuka tsaya'ta antaya qeyar yaranta daki ta bar hadiza abakin qofar tana ci gaba da zage zage kamar zata tada jinnu,ta gama da huwaila ta kalli qofar dakin mama ta yi nata,ita kadai ita da yaran nata tamkar wasu sababbun tabi
hindatu kam babu abunda take sai sheqa dariya cikin dakin suna aikinsu maryam ta dan dubeta kana ta kau da kai ta ci gaba da ahimfida zanin gadon dake hannunta kan sabon gadon maman
''ko kema shirin bin sahun nasu kike irin wannan dariya haka''dariyar na ci gaba da cinta tace
''ai wallahi adda maryam ki gode Allah,kinsan wannan bala'in tun jiya ake zuba shi cikin gidan nan''
''amma ina baaba,bai tsawatar ba?''
''ya tafi gaya duba inna gwaggon baba,kuma ko yana nan ma ma zai tsawatar din akai?,mowarshi aka taba fa,jamila ce ta dawo gida jiya wujiga wujiga''
sai da gaban maryam ya fadi,a hanzarce cikin fuskar mamaki ta kalli hindatu
''garin yaya?''
''to yaya jabir yace baya yi ta taho gida har dactakardar sakinta kyawawa guda uku,a kuma karbe duka wani abu na dukiya ko kadara da ya mallaka mata,amma in fada miki baaba hadiza da yake jahila ce ba ilimi a take suka hau dan sahu ta maidata wai zata bashi haquri a daidaita,wallahi in taqaice miki ko zama bata yi ba bayan dawowarta sai ga jamilar ta biyo sahunta,da duka ya koro ta daga cikin gidan da qyar ta qwaci kanta,to kuma bala'i sai ya koma kan inna huwaila wai itace sila tunda dama ta taba cin alwashin sai ta wargaza komai''
hindatu ta sake qasa qasa da muryarta kada mama ta jiyota
''in taqaice miki adda maryam jiya dai har gun bokan da sukaje ya raba tsakaninsku da ya jabir sai da suka tona abinsu,cikin hargagin fadansu''
sai jikin maryam yayi sanyi,ta bar abinda take yin din tayi zaune gefan gadon,tabbas tasan ba'a yi mata adalci ba,saidai rabuwar aure ai ba dadi gareta ba,espicially yaran gidansu da dukkaninsu babu wani mai qwarin gwiwa kan aurenshi kullum cikin jeka ka dawo suke,to ga wata kuma sabuwata samu
''kinga ya maryam,kada kice fa zqki wani damu,sakayya ce Allah ya miki ita da gaggawa haka''ta fadi ita tana ci gaba da dame gadon aikin da maryam din ta saki
''a'ah,maryamu kin gaji ne,idan ba dama sai na aika hindatu ta kiramin laure ta tayamu''
girgiza kanta tayi alamun a'a
''mama haka abu ya faru da jamila kuma dai?''
''uwar asugwi din ta fesa miki din kenan ko''maman ta fada tana qarasowa cikin dakin,ta kama kunnen hindatu ta dan murde har sai da ta saki aiririyar qara tana dafe hannun maman
''don Allah mama kunne na,zaki tsinke kunnen autar taki fa ki rage mata kudin sadaki''
''ai gwara in tsinke kunnen tunda ya iya jiyo gulma ya fadawa addarshi''
da qyar hindatu ta zame a hannun maman
jikinta babu qwari haka suka dinga aikin,har ga Allah bata ji dadin mutuwar auren ba,tunda yau babu wanda,zaiso ace nashi ne kullum a bazawara,sai magariba uka kammala aikin komai yayi neat da shi,ta cire kaya jikinta ta daura zani da hijabi tq fito bandakin tsakar gidansu tayi wanka,tsakar gidan shuru da shi qwal kowa yana daka da mugun abinshi a zuciya,girgiza kai kawai tayi cikin zuciyarta tana fadin Allah ya gyara,sam rayuwar gidan nasu a karkace take kowa da inda ya dasa tasa alqiblar
tana cikin sallar isha'i kiran abdur rahim ya dinga shigowa wayarta,hindatu ce zqune kan kujerar dq wayar ke kai don haka ta daga,bata ankare ba taji sun shiga hira da hindatu,dama gata gwanar surutu,sai da ta idar sannan ta miqa mata wayar,kasa dagawa tqyi saboda kunyar ama dake gurin,itama maman na ankare da ita amma tayi kamar batq gani ba,dn tasan maryq din ba boye mata zata yi ba,cikin zuciyarta take addu'ar Allah yasa mijin aure ne diyartata ta samu
su ukun cikin kwano daya kamar ko yaushe suka ci tuwonsu na masara miyar busashshiyar kubewa,santi kawai maryam ke ti wa mama don tayi missing girkin maman sosai,mama gwana ce ba baya bace gun tsara girki musamman namu na gargajiya
zumudi yasa hindatu ta kasa shiru jin addar tata taqi tada zancan mutumin da ya kira din dazun
''wai adda maryam abdur rahim din dazun fa yace saurqyinki ne,kuma naji shiru baki ce komai ba''
hara rarta tayi
''wannan baki naki hindatu kamar ba'a gasa miki shi ba?''
dariya suka sa su dukka ukun,tilas yanzun ta yiwa mama maganarshin tunda tun ajiyan yake jadda da mata aure yake son yayi bada wasa ya zo ba,a kunyace ta yiwa maman bayani,farinciki fal zuciyar maman
''Allah ya tabbatar mana da alkhairinsa,ya kade dukkan sharri da fitintinu,addu'a ce yanzu kawai abunyi gareki maryam''
''insha Allahu mama,sai a tayamu muma da ddu'ar''ta fada cikin karyewar murya wanda ke nuna raunin zuciyarta,tausayinta ya kama maman
''addu'a ta zama dole akan musulmi,ballantana uwa ga 'ya'yanta,wacce garkuwa kike da ita da zaki basu wadda ta zarce addu'ar,uwar ma irina mai yara mata da take musu fatan samu mazaje na gari nagartattu,babu sallar da zan idar da ita maryama ban muku addu'a ba,ku kadai nake da su fa''
wata iriyar qauna hade da tausayin mahaifiyar tasu suka lullubeta,haqiqa uwa ba wasa bace,wata ni'ima ce daga ubangiji,cikin zuciyarta take fata insha Allahu wannan karon zuciyar mqhqifiyar tasu zata wanke daga dukan wani quncin rashin auren nata,hawayen da suka tqru suka fara sauka a idanunt cikin dabara take sharewa don kada maman ta gqni hankalinta ya tashi
kiran abdur rahim ne ya sake shigowa,wannan karon ba tare da jinkiri ba ta daga don so take ta kaucewa idon amman kada tqyo tozali da hawayen da takeyi
''ranki ya dade lafiya kike kuwa?''ya tambaya a sanyaye
''lafiya nake me kaji?''
''muryarki ce naji tamin kama da ta masu kuka''
duk da yanayi da take ciki sai da murmuahi ya subuce mata
''idan banda abun abdul har yaushe kasan muryata da zaka tantance kuka nake yi?''
murmushi ya saki har tana iya jiyo sautinshi
''na dade da sanin muyarki maryam,ke dince baki sani ba,kina gidanku ko?''ya qarashe maganar da tambaya,cikin mamaki da sigar tambaya itama ta maida masa amsa
''wa ya gaya maka?''maryam,kina shakka cikin son da nake miki ko.....any way....naje gidanku ance min baki nan kina gun mamanki''
a wani mamakin ya kuma sakata,son iya saninta babu mai shigowa gidan su mamin ta sauqi
''ya akayi kasan gidan da nake zama taya kuma ka iya shiga da sauqi irin haka?''
''maryam,duka abdul ba mai daukar abunda yake so da sauqi bane,yana bashi muhimmanci ne afili da boye,ina fata kin fahimceni?''
''jinjina ga irin wanna son da abdul yake min''
''jinjina ga zuciyar data sadaukar min da kanta''sai duka suka yi murmushi
''ina fata zuwa yanzu mutanen gida sun san da zama na?''
''tun yanzu abdul,duka duka jiya fa muka hadu''
''ke kika hadu da ni jiya,nikam ba tun jiya ba kika zama wani bangare daga jikin zuciya ta,so inason asan da ni maryam,aure nake so nayi da,wuri idan da ina da iko ma cikin watan nan banqi ki zama tawa ba''
tilas abdur rahim ya bawa maryam dariya
''gaskiya na baka sarkin zumudi na duk duniya''
''na amsa tunda sonki ne ya ja min''
cikin qanqanin lokaci ya cika zuciyarya da farinciki ta mance duka abinda take ciki,ba dadewa da gama wayar tasu bacci yayi awon gaba da ita don tuni mami ta yarje mata tayi kwananta a gida washegari taa dawo
🎄🌲🎄🌲🎄
qarfe tara na safe ta gama shirinta tas,a falo ta taradda hindatu na shirya musu abun kari kan center table daya daga cikin abunda jiya ya zama mallakinsu
cikin girmamawa hindatun ta gaidata ta amsa mata tana tambayarta mama
''mama na gurin baaba''
''ya dawo ne?''
''eh ya dawo dazu da sassafe,kin sanshi da tafiyar asubanci,yauwa tace idan kin tashi ki shiga ku gaisa''
''yanzu kuwa''ta fada tana ciro wayarta dake tsuwwar shigowar saqo tana dubawa
saqon barka da asuba ne aga abdur rahim,zaqaqan kalmomi da suka sanyata mirmushi ita daya tamkar wata zautacciya,tana mamakin yadda zuciyarta ta nutsu wa abdur rahim lokaci guda,sai da ta kammala karantawa ta masa reply sannan ta koma bedroom ta ciro dubu goma cikin kudin da mami ta bita kyautasu jiya dubu goma sha biyar
mamanta inna haule baaba hadiza sai lubabatu jamila da shamsiyya su ta tarar cikin dakin,kallo banza uka suka bita da shi,gefan binta ta matsa zata zauna,cikin rashin mutunci bintan ta janye jikinta tana wani harare harare da kumbure kumbure
gaida su ,bata da isar da zasu amsa mata har gara inna haule ta ama din sama sama,cikin girmamawa ta gaida baaban nata,ba laifi a sake ya amsa mata har yana tambayarta gun aikin nata,shiru ne ya biyo baya na wasu mintina sanan baaban ya dubi jamila
''inatambayarki tun dazu kun min shiru,yaro yace shi baisan lokacin da ya aureki ba,to inason in san ta yaya akayi ya aurekin,tunda shi ya rantse ya mayq bai san ke matarsa bace kuma bazai dawo dake ba''
cikin fitsara da rashin tarbiyya ta zumburo baki
''toni baba....ka tamvayi hadiza mana''
ya juya ga inna hadizan
''to kimin bayani tunda tace a tambayeki''
cikin borin kunya da haqiqancewa tace
''haba malam,wannan wane irin abu ne,ya zaka zo kasuwa ka dinga kwance min zani,sai da ka tara min idon duniya ni da diyata zaka hau bin qwaqwafinmu''
''ke hadiza dubanni nan da kyau,na gaji da iskanci da rashin mutuncin yaran nan,jiya tunda naje qauye fita ta daya na gaza fita,zance na ake ko ina,ance na kasa kula da yaya matan da Allah ya bani,dukkansu babu mai zaman aure ko wacce rabi aure rabi zaman gida,ga wasu kuma sun kasa auruwa''
zuciyar mafuam ta kada don tasan maganar qarshen tata ce
''to wallahi ya isheni haka,kun gama mai da ni mutumin banza ko,baku isa ba wanna karon na gaji ko masu auri suyo zaman auresu marasa aure suyi aure ko inci uban yarinya wallahi''
ba inna hadiza kawai ba hatta da su maama sunyi mamaki,yau baane ke ja in ja da inna hadizar?,lallai a dade anayi sai gaskiya,komai yayi farko qarahensa na zuwa babu shakka,a bangaren inna hadiza kuwa ta gama qullatar huwaila ne dadi bisa dari kan dukkan bala'in da taga ya afko,mata babu shakka ita ta qulla zuwanshi
qasa mama tayi da kanta tana fadin
''Allah ya huci zuciuarka malam,a yi mana afuwa''
sai yaji zuciyarahi ta dan rage zqfihar ya juya ya dan dubi maman,sannan ya maida idonsa gasu hadiza wadanda sjka zuba masa iddo qir babu mai cewa komai,baba hadiza na huci tana jiran ya gaya mata cuta ta fada masa mutuwa
''ke jamila ki tsaida hankqlinki,mahaifinki ne wanna,ki fada masa ya aayi hakan ta kasane don,samun bakin zaren,so ake a gyara lamarin ki koma gidanki kuci gaba da zama,mutuwar aure gun diya mace ai faduwar daraja ne,saidai kuma idan na qaddara ne''cewar mama
jin an sako maganar komawarta gidan jabir ya,sanyata cikin rawar jiki ta bude baki zata yi bayani a wautarta da jahilcinta za'a maidata din,don a yadda ta dandana zaman daula bata jin zata iya zaman gidan nasu kona wata daya ne bare na dindin din
tuni inna hadiza ta katsi numfashin jamilar
''uban me zaki gaya musu,cin fuska yaso yi miki kawai,ya aureki da kansa sanna yace baisan ya aureki ba,kujimin da,ke kuma aminatu banason munafurci da gilma,ina ruwanki?,ina cewa dai jamila bake kika haifa min ita ba,ai na dade da sanin cewa abunda kike nema kenan saboda har yau baqincikin qin aurar diyarki da baiyi ba yana nan cikin zuciyarki,to ahir dinki ki fita sabgata data yara na''
tsawa baban ya daka mata ya kuma ce ta ta shi ta fice masa adaki,koda ta ficen da yake ta riga da ta rainashi sai tayi tsaye abakin window tana eqa dakin tare da kallon jamila tana mata gargadi
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:53 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺🌺
🌺💖🌺💖🌺
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
🌺💖
💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖💖💖💖💖💖💖
*WRITTEN BY*
*SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
💖🌺💖🌺💖🌺
💖🌺💖🌺💖
💖🌺💖🌺
🌺💖🌺
🌺💖
🌺 ▶3⃣0⃣
*_HASKE WRITERS ASSOCIATION_*💡
*_home of expert and perfect writers_*
dauke kanta tayi tamkar bata ga gargadin nata ba,domin burinta kawai a maidata ga gidan jabir,don ba jabir dinne ma yafi damunta ba tunda bashi daman take aure ba dukiyarshi take aure,tana da abokanan holewarta a waje
a take ta warware musu yadda tayi amfani da sihirtaccen kwalli da turare har sau biyu ta dauke hankalin jabir ya aureta cikin gushewar hayyaci
gumi ne kawai ke ketsatstsafowa maryam,bata sake jin tsananin tausayin jabir ba sai a lokacin,shikam baban nasu shiru yayi ya kasa furta komai,kimanin mintina biyar sanna ya dubi su binta yace su fita adakin,sumi sumi suka fice ya dubi huwaila da tayi tsamo tsamo
''duk abinda kukayi huwaila don kanku,amma ku sani dole ne ku nemi yafiyar maryama don an zalunceta''
ya waiwaya ga inna hadiza dake labe yace
''kije Allah ya isa tsakani na dake,tarbiyyar yara da kika bata min,haqqin maryam kuma ke da ita,kya sake samowa jamilar wani mijin,ku taahi dukkanku ku bani guri''
dama a qagauce suke saboda kunya da nauyi tuni suka fice,saura maryam da mama,miqewa itama maryam din tayi ta ajjiye masa kudin hannunta
''ba wanna babu yawa amana addu'a,kuma kayi haquri Allah ya huci zuciyarka,insha Allahu zamu gyara dukkan abinda baka so''
''na gode,Allah yayi miki albarka,baki gaji ba maryam baki dade da yi mana hidima ba,har yanzu abincinki ake ci a gidan nan''
''ba komai baba,kunfi qarfin haka ai''
tana shirin ficewa mama tace
''dawo ki zauna ayo maganar yaron nan a qareta''
cikin rashin fahimta baban ya dubeta
''au ta samu wani mijin ne?''
''eh,gata nan ta maka bayani''inji mama bayan ta miqe tana tattare kwanukan da ya karya
kanta a duqe ta gaya mishi iya abinda ta sani game da abdur rahim din
''to,madalla,sai a sanar masa ya turo kawai,ai babu wani bincike da za'a tsananta tunda kina sonshi kuma ma kada muje ya subuce mana garin binike,kinsan wani baya son tone tone''
sai taji,maganar ta mata wani iri taya za'a dauketa adanqata ga mutumin da ba'a binciki wayeshi ba,sanna kuma uwa uba daga haduwarsu jiya sai tace ya turo magabatansa,tilas sai an nuna masa an gaji da zamanta dama
sai ta lanqwashe murya tace
''baaba,ina ganin an dan badakamar wata guda ko fiye kafin ayi masa maganar turowar,sanna baba ka gafarceni ayi binciken inaga haka sai yafi kyau''
''hmmm,karatun boko ya bude miki ido mero''ya fada yana murmushi
bata ji dadin yadda ya fassarata ba,don ita tayi ne da zuciya daya,tayi ne don gujewa auren jeka nayika
''shikenan tunda kin zabi hakam,amma kada kiyo kuka dakowa idan shima ya kama gabansa kafi wata gudan,maganar bincike kuma tunda ya gaya miki unguwarsu na baki wuqa da nama kiyo kinga kin hutashaheni ma''
hawaye ni ya silalo mata,bata taba jin inda 'ya takewa kanta binciken ma'aurinta ba,amma yata iya jaka tata *qaddarar rayuwar* take,ta kuma godewa Allah da bai sata ta kauce hanya ba duk da yadda ta tsinci rayuwar tata cikin tsangwama
''na gode baba,Allah ya gara gima''ta fada aladabce
''ameen ameen,idan kin fita ki turo min iwar taki''
tare suka karya da lafiyayyen qosai da kunun tsamiya wanda yasha lemon tsami,sosai tayi namijin qoqarin fidda dukkan damuwa daga zuciyarta suka karya din cikin wawala
sun tattauna da mama kan atamfofi da take so ta dinga sarowa maman idan tadauki albashinta na wannan watan ko falle bibbiyu ne ta fara saidawa agani idan zasu karbu,albarka maman kawai ta shi mata tare da mata kyakkyawan fata
sai la'asar ta fara shiri tafiya,hindatu tace
''ki jirani adda maryam mu fita tare zanje duba jamb dina,tun jiya naji sanarwa ta fito''
''to kiyi,maza ki shirya don so nake naje nayi abincin dare,jiya duka baaba uwani na dorawa aikin''
''gaskiya kam,don ma muta nene masu karamci da mutunci''
inji mama dake ta hadawa mami su kuka daddawa kubewa man shanu da sauransu
qarfe biyar sukayo sallama da mama ta fito don raka su,jamila ce tsaye a tsakar gidan sanye take dai da swiss lace dinta tun na shekran jiyan,mai tsada ne amma gaba daya ya yamutse yasha squeezing,fuskar nan ta hqutsine kamar dakalin kashi sqboda tsabar bqcin ran da take,ciki da baqinciki uwa uba kwana biyun nan bata saurari wanka ba,gabanta hadiza ce riqe da kwanon da yasha uwar lamba shinkafa da wake da manquli ce aciki da barbaden yaji
''haquri fa zakiyi kici tunda dai na ba gidanki bane,mu bamu da wani miyar nama da zamu zuba miki,kina kallo haka suma qanna naki suka ci''
''idan naci wannam abun Allah ya tsinen hadiza,wai ma meye amfamin kudaden da na ringa satowa ina kawo miki duk ina kika kaisu?,kinje kin rabawa garadan soro sun cinye kuma gashi nan auren da ake ta tattali din ya tsinke....''
da sauri hadizan ta kaiwa bakin kamilar dula kin zata mata tonon silili cikin jama'a
''don ubwnki sharri zakimin''
''ba wani sharri wlh gaskiya ce da bakina sai a hanani fadan gaskiya ta...''
binta ce ta atse cece kucen ta fito dakin,inna hadizan hannunta dauke da wayar jamilan wadda ta tasamma dubu dari biyu da hamsin tana ta digar ruwa
''kinga aikin da kulu ta miki''ta fada tana miqa mata wayar
hannu jamia ta dora aka ta kurma ihu tana fadin kulu ta kasheta,ita kadai ce ta rage mata kadara shine don baqar zuciya zata tsoma mata ita a ruwa wallahi to ba zata yarda ba
kukan kura tayi ta banka dakin nasu da gugu inna hadizar tabi bayanta tana fadib kada ta nakasta mata yarinya amma ina kota kan uwar bata bi ba
tsaki hindatu taja tana fadin
''jarababbu,ku kashe kanku dai''
naira talatin talatin suka biya zuwa caffe din dake qasansu,su taradda gun cike da dalibai masu duba jarabawarsu,hakan ne ya dan janyo musu jinkiri,sai da suka jira har kusan shida sannan suka samu sarari,babu jimawa aka gano result din hindatu,ba ita mai jarrabawar ba hatta maryam tayi farinciki ainun,don makin hindatun ya kai dari biyu da biyar,sai da ta rakata ta samu ota sanna itama ta tari tata ta wuce gidan
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
kamar yadda layukan suke shiru gidan shima yake shiru lokacin da ta isa
tana shirin shiga ita kuma na shirin fita kunnenta maqale da waya,cikin dinkin fitted gown take na material ruwan zuma,dan siririn dankwalin kawai ta nade wuyanta da shi,ganin ta nufota gadan gadan yasa tayi hanzarin matsawa gefe dob ta lura idab batayi hakan ba tsaf zata bangajeta ne ta wuce,saddiqa ce uwar girman kai da dagawa,duk da hakan bata tsira ba sai data yi mata kallon biyi babu taja tsaki bayan ta cire wayar a kunnenta sanna ta wuce
su biyun kuma na kwance cikin kujerun falon wato abida da salma kowa na sabgar gabanshi,abida na charting salma na danne dannen laptop da bata san me tak yi ba,sai t v plasma din falon dake ta zuba aiki babu mai kallonta,babu wadda ta amsa sallamarta cikinsu,bata damu ba sam don ba yau ta soma ganin hakan ba,har zata wuce daki sai ta jiyo motsi cikin kitchen din haka ta sauya akalar tafiyar tata can,baba uwani ce ke wanke kwanuka,ta qaraso kitchen din dafe da bakinta
''ayyah,baaba uwani ayimin afuwa na barki da wahala jiya da yau''murmushi tayi tana taunar goro
''haba 'yar nan ai an zam daya babu komai,ke dai ya kika barosu?''
''lafiya baaba suna gaidake''ta amsa mata tana karbe soson wanke wanken
''to madala muna amsawa,inace yanzu kika shigo gidan?''
''eh baaba''
''to amma shine zaki wani,karbi wanke wabke,bani in qarasa kije ki huta ga kiran sallar magariba can anayi''
''a'ah baaba,haba gaskiya bazan baki ba,ki huta kema nasan tun jiya kike dawainiya''
''hmmm,wallahi ke dai bari 'yar nan,inda ace abdullahi ne sai ni sai hajiya aikin da sauqi,tofa ina wadan can marasa kunyar yaran kawai sun isa su saka ka gaji,ga daya ta dadu,wancan tace ita kaza za'a dafa min waccan tace kaza''
wani takaici ya kama marya
''kuma kika dafa baaba?''
''to ya za'ayi meramu sai haquri''
ta ajjiye kwanon hannunta
''bana jurar raina babba baaba,babu wadda zaki sake dafawa komai saidai idan maami ta saka ki,duk mai buqatar wani abu ta shigo ta dafa ai itama tana da hannu''
sai da suka qarasa komai sannan suka bar kitchen din tare bayan baaban ta gaya mata mami na asibiti da azahar ta fita zuwa bayan isha'i zata dawo,yadda ta barsu a falin haka ta dawo ta taradda su babu wadda ta motsa don tayi salla
tara saura ta fito din ta debi abincinta,zaunen dai suke duka su uku wannan karon kowacce taci ado,abida cikin matsatstsun riga da wando,salma cikin fitted gown,saddiqa kuwawata gown ce wadda bata da hannu duka saman qirjin a waje,mamaki ya cikata tamkar irin matan gidan nan dake tsammin dawowar mai gidansu a lokacib,babu tababa zaman jiran dawowar abdallah suke,takaici ya isheta kamar ta rufesu da duka,duk su suke jawowa abdallan ke daukar kansa on top,yake rage qimar mata,koma meye sune sila
tasa kanta gaba zata wucesu dauke da plate din abincinta
''ke malama a bawa mutane abinci ko su zasuyi serving kansu?''
a nutse ta waiwayo
''su waye mutanen?''ta tambayi salma cikin gatse,amma da yake sam ba ganewa take ba sai tace
''mtseeww,gani kuwa kina kallona''
''ayyah,to ai na dauka a qoshe kuke ko''
ta shige dining area din ta zuba mata ta ajjiye mata
''ni da kika raina sai nayi magana zaki zuban?''inji abida
maryam ta dubi plate din hannunta
''sai kayi magana zansan kana so ai,ga wannan kici na zuba wani''ta fadi bayan ta ajjiye mata shi a gabanta,ba bata lokaci tasa qafarta ta shure shi take yayi dai dai a gun,wanda ba don tayi saurin ja da baya ba har a jikinta zai samu masauki
''lallai ne ba qaramun raini ne tsakanina da baqauyar yarinyar nan ba''cikin qanqanin lokaci ta yar da wayar hannun ta ta miqe tayo kanta,qyam ta tsaya hannayenta harde da qirjinta tana kallon abidan,qarasowarta dab da ita ta daga hannunta saidai kafin ta aiwatar da komai muryar mami ta karade falob
''kai,meye haka abida?''dolenta ta sauke hannun nta cikin hayaniya take fadin
''wallahi mami sai na hora yarinyar nan''
''me ya hadaku kuma yau maryamu?,ban sanki da fad ba fa''hankali kwance ta gaya mata abinda ya faru,girgiza kai kawai mamin tayocikin takaici tace wuce amaryamu''
cike da takaici ta isa dakinta,tayi imani a lokacin da abidan ta taba jikinta ko siyar wace ce ita ba zata daga mata qafa ba,bata ga amfanin alkunya ga mutumin da baisan darajar dan adam ba,cikin ikon Allah abdul ya kirata,shi ya ebe mata kewa har bacci yayi awo gaba da ita
🍃🍂🍃🍂🍃
cikin bacci ta dinga jin yunwa na rage mata dadin baccin wadda ta tilastata farkawa,wayarta da ke gefan pillow dinta ta dauka ta duba lokaci,shabiyu da arba'in da takwas na dare,cikin mutuwar jiki da kasala ta sauko daga adon ta shiga toiket ta dauraye bakinta ta daura alwala ta fito ta tayar a sallah,raka'a hudu ta samu tayi tayi addu'oo'inta ta shafa
a hankali ta bude qofar dakin nata ta fito don samawa kanta abinci a dining,tayi mamakin ganin qwayayen falon duka akunne,ganin laptop da waya kusa da ita yasa ta bayar salma ce qarshen tashi tabar falo a haka
jingine yake da bango falon hannayenshi harde a qirjinshi,idanu kawai ya zuba mata fuskarsa qunshe da qaramin murmushi,yayin ita kuma take gaf da ahi har tana iya sheqar hucin nashi numfashin,hannayenta dafe da bangon kusa da kafadarshi
''fyaden kema zakimin?''ya tambayi salma kanshi tsaye,cikin lumshe idanu ta kada kai
''ko kadan,kawai ina da buqatar inji dumin jikinka ne,dubi kwalliyarnan duk kai na yiwa amma tun dazun nake jiran dawowarka,na hana idanuna bacci don kada ta tashi a tutar babu''
murmushinsa ya qaru fiye da na dazu,yasan kalma daya zaiyi amfani da ita wadda zata sata taji haushi
''sai ance mutum kaska ne yace shi bashi bane''
a maimakon yaga taji haushi kamar kullum sai yaga ko a jikinta,murmushi ta kuma yi
''to meye idan ma kaskar ce,duk akan sonka ne,nidai ko hugging dina ayi kawai na wuce dumin da naji da qamshin turarenka ya isheni''
ya janyeta ya bada nisa tsakaninsu yana fadin
''saboda tsabar raini ma naga sai da kika nemo irin turarena da shi kike amfani ko''
''idan zan kwanta na fesa jina nake kamara qirjinka nake kwance''ta fada tana sake matsowa daf da shi,hannunta ta dauke daga kan makunnin da takeson kashewa wanda hakan ya haddasa motsin awarwarayenta da suka jawo hankalin abdallah,jiki na rawa ta juya zata bar gurin,tuni ya saki briefcase dinshi da ya dawo da ita daga office ya biyo bayanta da sauri,ganin tana niyyar takawa a aguje yasanya shi dada hanzarinsa don ya fuskanci idan ya qyaleta zatq sake masa irin fassarar da tayi masa kwanaki,taku uku ya cimmata tare,da fusgota baya,tayi taga taga ta fadi jikinsa cikin tsoro da daukewar numfashi
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻
[9/17, 12:53 PM] 80k: *ABADAN*31
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*_home of expert and perfect writers_*
jikinsa ta fada qeyarta ta samu masauki a tsintsiyar hannunshi fuskarta na facing tashi fuskar,yabi oily eyes and golden eyes dinta da kallo wadanda suka dada sheqi saboda hasken farin qwai daya mamaye falon ya haska cikinsu,ya kalli dan qaramin bakinta da yake motsi yana tattara kalmomin kayi haquri cikin rudewa
Ranshi ya baci,wai me yarinyar ta maida shi ne?,dan iska?,haka wancan karon tayi masa fa?,tana so tace masa a age dinta bata taba ganin romance tsakanin mutum biyu ba saboda tsabar rainin hankali?idan ma hakanne yau zai koya mata hankali,a hankali ya soma kusantar da bakinsa zuwa nata,numfashinsu ya soma gauraya,tsoro da rawar jikin maryam ya dadu,don tuni zuciyarta ta gama ayyana mata abinda abdallahn ke shirin yi
karon farko tattausan lips dinsa suka taba haduwa da na wata diya mace kamad yadda yake haka a gurinta,baisan yadda akayi ya tsinci kanshi da tsotson lausasan lebunan nata ba cikin rashin sani
''hasbunallahu wani'imal wakeel''kadai take ambata cikin zuciyarta,gudun zuciyarta ya dadu har numfashinta na qoqarin janyewa,hawayen dake malala kan fuskarta ne ya soma taba fuskarshi da sajen bakinsa na quater millon
''abdallah!,meye haka kake yi?''salma ta fada cikin qaraji da wani irin yanayin baqin kishi da bata taba shiga irinshi ba,a nutse ya saki bakin maryamun ya juya yana kallon salmar wanda hakn ne ya bawa maryam qwarin gwiwar hada ragowar qarfinta don ta tsere masa,saidai tana tashi taji ya cafko dantsenta idanunsa na kan salma,kallon 'yan sakanni ya mata ya maida idonsa ga maryam
cikin fada da tsawa yaso yi mata maganar amma sai ya gaza,kasala ce ta saukar masa lokaci guda tamkar mai jin tsananin barci
''gobe ma idan kinganni tsaye da wata kimin kallon dan isaka,zaki ga yadda ake iskanci ra'ayil ain''ya fada yana kallo tsakiyar qwayar idonta da hawaye ya cika yake zuba kana ya cikata,da gudu kuwa ta bar gurin sai ya bita da kallo yayin da salma ita kuma ta tsare shi da idanunta wadanda suma tuni suka kawo qwalla
''haba,haba abdallah,irin wannna cin fuska haka da me yayi kama?cook dinka?''ta fada tana nuna hanyar da maryam din tabi da yatsa ''abdallah ka rasa bakin da zaka tsotsa sai nata,ni me na gaza da shi?just hugging dina kawai nace kayai ka kasa sai gashi ka buge da kissing house girl''
''hey!stop''ya tsaidata cikin hade girar sama data qasa,ya qara taku biyu ya iso gareta ya tsaya agabanta
''kada ki sake ambatar nayi kissing yarinyar can,kaifi tayimin nayi punishing dinta,ina fata kun fahimta''
murmushin takaici ta saki sannan takama qugunta da hannu daya tana girgiza kai
''kada ka maidani jahila mana abdallah,sau nawa ina maka laifi ka taba punishing dina ta wannan hanyar''
har ya juya vaya taba dauke briefcase dinsa sai ya waiwayo
''ita tana showing kanta a matsayin kanta a matsayin mai nutsuwa tana min kallon abinda ban taba aiwatar da shi ba,kinga gwara nayi mai dalili ko?''
girgiza kanta ta sake
''ko jikina kunne ne bazan yadda ba,kayi ne da manufar wulaqantani da nunama duniya iyakata''
''well,idan hakan kika zaba shikenan daidai ne''ya fadi yana kewayeta ya fice daga sashen bayan yasa key dinshi ya kullesu ta baya kamar yadda yazo ya tarar da su,dama abincinshi ya shigo yaci ya sameta zaune ita daya afalon
kamar ta dora hannu aka tayita rusa ihu haka ta ji,hawaye shabe shabe ta shige dakibta bayan ta qudiri abinda zata aiwatar musu a gobe
Qarfe goma ta gama breakfaat di gidan ta shiryashi a dining,Allah Allah take ta kammala komai ta shige dakinta don bata son haduwa da kowa uwa uba abdallah da take masifar jin haushi tsoro da tsanarsa,ta yanke ma zuciyarta abdallan yana layin 'yan iskan maza ne kawai,tuni ta bashi wannan sunan
tana gefan gadobta tana shafa mai bayan sanya doguwar rigar atamfa da tayi mai dogon hannu taji wayarta na b'urari,sunan mami ya soma yawo saman screen din,haka kawai gabanta ya fadi,cikin rashin kuzari ta sanya robar lotion din dake hannunta a gefanta kana ta daga wayar,tana qoqarin gaidata taji tace
''ki sameni yanzun a sama''
''to mami''ta fada cikin rawar murya,kasa ci gaba da shiryawar tayi sai ta zaro blueblack din hijabibta ta ware shi daga gugarsa ta sanya ta miqe ta fice a dakin
kallo daya ta yiwa mamin gabanta ya fadi don zata iya cewa a iya saninta da ita bata taba ganin yanayin fuskarta haka ba,gefanta salma ce zaune fuskarta jazur idonta a tashe,a salube ta qaraso,qasa ta zauna daga can gefe tana fadin
''barka da safiya mami''
''matsonan''tace da ita tana nuna mata gabanta ba tare da ta amsa gaisuwar tata ba
''maryam,me ya faru jiya da misalin daya da wani abu na dare tsakaninki da abdallah?''wata mummunar faduwar gaba ta ziyarce,tsoro da fargaba suka mamayeta ,bata raba dayan biyu wani abun salman ta gayawa mami mai muni a kanta
kimanin minti uku mamin na saurarenta babu amsa,don bata da bunda zata ce din
ta fadi gaskiya?,bazata iya ba,tasan mamin mai yarda ce da gaskiyar abunda ta fada din amma bata burin shiga tsakanin soyayyar da da mahaifiyarsa don ta dan dana hakan ba lamari ne mai dadi ba kona second guda
ta musanta kuma ya zamo mata zunubin qarya,idanun mamin na kanta tana jin babu dadi cikin zuciyarta,don har ga Allah 'yar cikinta take kallib maryam,dan yanzu ba'a shaidarsa duk da ta shqida da nagartattun halayen abdallah,amma yaran zamani koda yaushe yana iya sauya halayyarsa,tsoronta daya kada ya yaudari maryam din ya bata rayuwarta,hakan idan ta tuna shike qara hasalata da sa mata suya cikin zuciya
''dake nake magana kinhi shiru''
shirunne ya sake biyo baya,tuni hawaye ya soma ambaliya cikin idanunta tana sa gefan hijabinta tana sharewa
''to tunda kinqi magana bari na kira ahi shi mai gayya mai aikin yayi bayani''
''a'ah mami,tun farki na gaya miki ba laifinshi bane''
salma ta fada da sauri har tana kamar zata dafe hannun mamin da ya dauko waya don kiran abdallah
wani kallo mamin tayi mata
''bana hukunci da ji daga bakin bangare daya ba tare da dayan ba,koma mene da nashi laifin kuma tilas ya bayyana nan,''
mami ta qare maganar tana kara wayar a kunnenta
shiru ne ya biyo baya har ahigowar abdallah,sanye yake da kayan training ajikinsgi wanda da alama yana filin motsa jiki ne,hannunahi daya handkhercief ne yana tsane gumin suma da fuskarshi,daya hannun kuma gorar ruwan swan ce dake fidda gumin sanyi bisa dukkan alamu a falon qasa ya daukota
da zolayar mamin ya shigo falon saidai yanayin fuskarta kawai ya bayyana mishi ba lafiya,shi sam bai kula da su ba cikin falon ba sai da mami ta jeho masa irib tambayar data yiwa maryam sannan ya kuka da salma
cikin ko in kula yace
''nothing happened,nasan dai sha biyu da rabi na dawo gida,so ina jin yunwa sai na bude nan na shigo naci abincina,sai waccan da na hadu da ita zaune a falo tana game''
''ita kuma maryamu a ina kuka hadu da ita?''ta fada tana nuna masa ita wadda kanta ke duqe
yatsan bata yabi da kallo har zuwa gun maryam,sai ya yamutse fuska
''wace kuma maryamu?''ya fada yana shanye ragiwar ruwanshi,sai ran mamin ya baci,ita zai bunne,tasan waskewar abdallah sarai tunda ita ta haifeahi,kadan daga aikinshi ma yace bai tabajin sunan ba sai yau
''ni zaka ninke a baibai?,ko ka manta cewa ni na haifeka na raineka?, a hannuna kayi wayo?,naci kashinka da fitsarinka?,yaushe abdallah ka sauya hali?,ita da na tambayeta ai tasan baku da gaskiya shi ya sanya tayi shiru bata ce komai ba,amma kai da yake madainiyar wayonka ta tambayeta sai ka nemi raina mata wayo ko?''
ya danyi qasa da ido dob sam kalaman mamin basu yimishi dadi ba,bazai iya yaushene na qarshe da rayi masa irin wanna fadan ba
muryarshi a sanyaye yace
''idan ita ta gayamiki ai sai ta bude baki mami ta fadi abunda na mata ko?''
''ta gaya min ne tunda tare kuka aiwatar,mai kishina binda ya faru ne ta fada salma,har yaushe ka farq neman yaran jama'a,ko kunyar ina cikib gidan bakayi ba?,kasan illar da girman zunubin abinda kuka so aikatawa badan Allah ya kawota ta hana afkuwar lamarin ba,mai makon kuma ka gode mata sai cin mutunci ya biyo baya?''
sumewa ne kadai maryam bata yi ba a zaune kukan da take aboye sai ya koma na fili,ran 'yan maza yq baci take idanunshi suka sauya kala,ya zubawa salma ido wadda runi dana sanin abinda ta aikata ya mamayeta,ita so tayi aci mutuncin maryam ita kadai a kuma koreta ta bar gidan,kasa daukar irin kallon da yake matq tqyi tqyi qasa da idanunta
muryarsa a kausaahe cike da sautin fushi yace''wanne la'a nannen Allahn ne ya mana wanna qazafin,ko da yake mami kince salma ce,amma nayi mamki mami,kin san halina ciki da bai,kinsan abunda zan iya aikatawa da wanda bazan iya ba,me yasa lokaci guda wata can zato ta rushe kyakkyawar fahimtar da mukayi shekara da shekaru da gina ta,kai cina da har yau,ban kubuta daga zarin zan aikata zina ba daga gun mahaifiyata''ya fada yqnq girgiza kai jijiyoyin kansa na tashi,sai jikin mqminyayi sanyi,tabbas babu kyau gaggawar yarda da abunda baka da yaqini,balle abdallah da maryam,babu wana bata san halinsa ba,dukkansu tasan ne zasu aikata da wanda,ba zasu aikata din ba
ganin da salma tayi mami na shirin yarda da abdallan ita ta tashi a tutar kunya ya sanyata sake,zaqalqalewa
''ni ba la'a nanniyar Allah bace,kuma na gani din ne da ban gqni ba ai da bazan......''
bata qaraahe maganar ba taji quma abakinta,abdallah ya jefeta da ruwan robar dake hanjunahi wanda ko rabi bai sha ba,aka kuma yi sa'a ya sauka a bakin nata,ta dafe lebunan nata wani azabar zugi na ratsata,take lebunan suka fashe,bayan sun kumbura sunyi suntum cikin daqiqar da bata wuce talatin ba
hakan baiwa Abdalla ba ciki fushi ya yo gunta,da sauri mami ta shiga tsakaninsu tasa hannunta tana tokare qirjinsa don iya inda tsawonta yake kenan tana turashi da baya
''ki barni mami na lalata shashan bakin da bai iya komai ba face sharri da qazafi wa mutane''
''ka dakata abdallah,nutsu don Alla banason shashanci''mamin ke cewa,tasan halinshi sarai,bai fiya sairin fuahi ba amma idan ya fusata din komawa yake kamar mahaukacin zaki
kusan minti biyar mamin na artabu da shi
''na nutsu mami,amma na bata minti goma ta tattara dukkan wani abu nata tabar gidan nan,wallahi wallahi ta sake muka sake haduwa da ita sai na nakasta ta,banza shasha sha kawai,don ina rufa asirinki,sau nawa nake kamaki da syrup da capsule cikin jaka,shine har kike da bakin yiwa wani qazafin zina,to idan baki bar gidan nan ba nan da minti goma ba nine zan zamo mutum na qarahe da zaki tiwa qazafi a rayuwarki,bindigata zansa na harbeki ki mutu kowa ya huta''
cikin huci ya juya a sukwane ya fice,da sauri maryam tayi gaggawar jaye qafafunta badon tayi hakan ba kadan ya rage ya take mata dogayen yatsunta
bibbiyu ya dinga hada matattakalar har ya gama sauka daga benan,abida ce da saddiqa tsaye kowacce cikin sleeping dress tayi tsuru tana sauraron abinda ke wakana a saman,zuciyar kowaccensu tayi fari jin an kori salma suna ganin tamkar aiki aka rage musu
wani banzan kallo ya bisu da shi ba tare da ya furta komai ba ma suka watse
cikin mintina qasa da goma salma ta hada komatsanta tana kuka wiwi mami na lalkabrta ta shiga motarta ta fice agidan,ranar sai gidan ya wuni shiru kowa na dakinsa,mamin ma haqura tayi da fita asibitin ranar don tsoron kada ta tafi wata fitinar ta taso,jin shirun yayi yawa abdallah bai sake shigowa ba ya sanyata tattaki da kanta zuwa bangatenshi,don ta san cewa ba lafiya,don komqi akayi bazai iya fita bai gqyq mtq ba,to tabbas yana cikin dakinshi ne
A qurya ta sameahi kwance daidai yayi rigingine kan gadonshi,shigowartaya sanya shi miqewa ya zauna
''me kake haka har yanzu baka fito ba ko karyawa baka yi ba ga azahar ta gota biyu da rabi fa yanzu''
''bana jin yunwa mami''ya fada cikin rashin walwala,sai kuna ya dago ya dubeta
''mami ina fatan bakiyi fushi da ni ba,na kasa sukuni tun dazun''
dama ta sani a runa,yanzun haka bacin ran da ya gqni kan fuskarta ne ya sashi kasa fita,tun yana qarami haka yake,baya juriyar ganin bacin ranta
''zan iya yin fushin da kai dai na haqiqa matuqar baka gayan gaskiyar abunda ke faruwa ba''
''zan gaya miki mana mami,mami kiss ne kawai,wallahi bayan haka babu komai,kuma ko shi din ma haushi ta bani,kallon dan iska take min''ya fada bayan ya riqe hannayen ta cikin marairaicewa
dariya yaso bawa mamin amma sai ta gimtse don ba muhallinta bane
''don tana maka wanna kallon idan banda rashin dabara da wayo ta hakan zaka wanke kanka ta fahimci na gari ne kai?''
''am sorry may mami,nayi kuskure''
a nutse ta dinga masa fada sanna ta rufe da fadin
''idan irin hakan ta sake faruwa raina zai baci fiye da bacin ran daka gani yanzu,don ban yarda asabi Allah ba,duk son da nake maka zan iya ajjiyeshi gefe na hukuntaka hukunci mai tsanani,kada makamancin hakan ya sake faruwa akan ko wace ma indai ba matarka bace''sai maganarta ta qarshe ta bashi kunya ya dan sunne kai
dariya ta danyi
''da nema yau kuma nice akejin kunya''dariyar shima ya tayata
sai kuma ta hade cikin seriouse tone
''sannan abdallah,lallai lallai ya kamata kayi aure indai kana son hankali na ya kwanta yadda ya kamata,ka fidda mata cikin masu qaunarka''
qasaitaccen murmushin nan nashi ya saki
''relax mami na,insha Allahu kwanan nan zan sanyaki farincikin da kika dade kina fata,zan kawo miki mata ta har gida nan kusa,amma fa abida da saddiqa kowacce ta wuce gidansu,don wlh mami bazan iya auran kowaccansu ba''
''naji,saddiqa dama gobe tace zata tafi,abida kuwa dole ayi haquri sai an samu visa,zata sake ko sati uku ne tare da mu''
''shikenan mami,zan wa abokina magana harkarsu ce''
qememe yaqi fita yace zai je ko ina ba sai ya tabbatar ta gama hucewa haka suka wuni a gida gaba dayansu
*mrs muhammad ce*
[9/17, 12:53 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣2⃣
*Allahumma ya imada man la imada lahu,ya sanada man la sanada lahu,ya giyasa man la giyasa lah,ya karimal afwu,ya hasanat tajawuz,ya khaahifal bala'a,ya azimar raja'a,ya aunaddu'afa'ah,ya munqizal garqa,ya munjiyal halka,ya muhsin,ya mujmil ya mun'im,ya mifdil,antal lazi sajada laka sawadul laili wa nurun nahaar,wa dau'ul qamar wa shu'a ushshams,wa da wiyyul ma'i wa hafifushshajar,ya Allahu la sharika lak,ya rabbi ya rabbi ya rabbi,Allah ka shiga lamarin mutanen qasar burma,Allah ka shiga lamarin jama'ar musulmin duniya baki daya don sayyadis saqalain*👏🏽👏🏽😔😔
Qarfe goma saura na dare mami ta shiga dakin nata,har ta gama shirin bacci tana kwance tana jiran wayar abdur rahim da yace ta jirashi kada tayi bacci zai kira ta,da sauri ta miqe tana maida hularta da santsin gashinta ya sa ta sabule,mamin ta dan bita da kallo qauna da tausat
yinta suka lullubeta ganin ta takure ta kasa hada ido da ita
gefan gadon ta qaraso ta zauna kusa damaryam don ta dafa gadon bayanta
'.dago ki kalleni maryamu,mamanki ce fa''sai taji qwalla na shirin zubo mata nauyi da kunyar mamin takeji,gefe daya hauhi da tsanar abdallah na takura zuciyarta
''ki kwantar da hankalinki abdallah ya yimin bayanin gaskiya,ba laifinki bane laifinsa ne,kuma nayi masa gargadi insha Allah bazai sake faruwa ba kinji,ki i gaba da kame kanki maryam kamar yadda kike,daraja mace da mutuncinta yana tqfin hannunta,ruwanta ne ta riqesu su zame mata abun alfahar ruwanta ne ta wargaza,bazan so wani abu ya shafi mutuncinki ba maryamu don tamkar amana kike a hannu na,ko bayan haka ma unajinki har cikin zuciyata,haka za bazan iya yafewa abdallah ba idan ya maki wani abu da ya sabawa shari'a da mutuncinki,duk abinda kuma nayi nayi ne saboda kare martabarki,ina fata kin fahimce ni?''
gayada kai tayi tana share hawaye
''na gane mami,na kuma gode Allah ya qyara girma da lafiya''
wayar abdur rahim ta katse 'yar hirar da mamin ta fara janta da shi don ta saki jikinta,ganin maryam din taqi dauka yasa mamin ta dago wanda ke kiran
''bari in abku waje kinga ma shikenan ya fanshe ni sai ya qarasa lallashin,ki gaisheshi sai da safe''ta fadi tana miqewa cikin dariyar zolaya,kasa amsawa tayi ta sunne kanta saboda kunya mamin na dariya ta fice
hira suke abinsu sosai irn ta masoya kamar sun shekara da sanin juna
''maryam ya kukayi da abban,nasan dai an bani dama ko?''
ta dan zaro ido tana fadin
''wa ya gaya maka,abdul irin wannan zumudi haka''ya marairaice murya
''maryam bani so in rasaki ne inaso a bani dama koda kudine a kawo''
ajiyar zuciya ta saki
''abdul dole dai ai mu danyi haquri ko,tunda yanzun dai kaga azumi saura kwana bakwai,mu bari bayan sallah idan Allah ya kaimu sai ayi dukka abinda za'ayi''
''wa ya gaya miki azumi na hana kai kudi,akwai cousing dina safiyya hudu ga azumi aka kai kudin aurenta,so pls maryam ki barni na kawo kudin idan yaso bayan azumi asa mana ranar aure na qagu ki zama tawa,baki san ya nake ji ba duk lokacin da na kalleki ko naga kin fita a matsayin budurwa ba mata ta ba,bani da wani iko a kanki''
dariya ta saka
''yaushe ma kake ganin nawa ne abdul''
''ina iya ganinki mana da idon zuciya''
''shikenan yanzu mu bari zan sanar da mami na,duk yadda ta kama zaka ji''
da qyar abdur rahim ya barta bayan ya cikata da dad'ad'an kalmomin qauna
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Su hudu ne cikin lafiyayyar motar da idan ka shiga ba zakayi tsammani tafiya akeyi ba sai idan kaga kuna wulga gurare,mami ce da maryam a baya sai Abdallah da driver a gaba
mami cikin shigar leshi dinkin buba orange wanda yasha adon lemin hreen,takalmi jaka da mayafi dukka toomatch masu dan karen tsada da kyau,ba qarya mami gwanar iya ado ce,ko cikin mata masu shekarunta da wuya ka samu irinta goma,shi yasa sam sai ka rantse bata haifi abdallah ba,zakayi tsammani yayarsa ce kawai
maryam ma cikin cikin kwalliyar take amma zamu iya cea kwalliyar jiki don babu wani make up a fuskarta,material ne pich da kwalliyar sea green,tayi adon takalmi mayafi da fashion na dan kunne duka kalan sea green,ba gwanar jaka bace hakan ya sa wayarta ce kawai riqe a hannunta,abdallah dake gaban mota yake ta faman zuba mitar shi kam da an barshi bazaya je ba,ba gun zuwanshi bane idan ba kamawa tayi ba,sanye yake da shadda light blue dinkin tazarce da yaji aikin hannu na maza dan ubansu da baqar hula,takalmi sau ciki baqi da agogo,kallo daya zaka masa ka tabbatar kudin da jikin nashi ya lanqwame ya ishi mai qaramin qarfi jari
''ayita aure gab da azimi barna tayi ta afkuwa''ya fada yana yarfar da hannunshi wanda ke daure da agogon ruwan gold''nikam dai wallahi kam duk wanda yamin aure a irin wannan lokacin alhakin a kansa''
''baka da kunya ka maidani kakarka,yaro duka ka gama mitarka,dinner ce dai si kaje,minti nawa anyi an gama,hajiya mai gado idan da halacci ba zaka mata haka ba,ita tayi yayenka abdallah,ba qaramib sonka take ba''
ya dan waigo yq dubi mamin
''ayyah mami me ya kawo maganar yaye na''ta dago shi qwarai wai shi baya son raini,dariya ta saka
''to meye kowa ma an masa yaye har ni kaina''kadan kadan take bashi labarin quriciyarsa gidan hajiya mai gadon,yana son ji amma baiso wani ya ji masa ya raina shi don haka ya canza topic din
''mami,cikin kwankin nan nake son kawo miki dear ta gaidaki,so kuma bata nan sunje umarar azumi,ni kuma na qagu mami in yi wani motsi''
murmushi ne ya subucewa mami
''ummm,abdallahhh......,yaushe ka zama haka?yaushe sonta ya maka irin wannan kamun?kai har naji ina sonta data iya sato zuciyar birkitaccen yarona haka ta farat daya''
murmushi yayi hadi da lumshe idonsa,ya jinginar da kansa jikin seat din motar yana tunata yana jin wani yanayi na shigarsa,mami ta sosa masa inda yake masa qaiqayi
''dis luv inside of me is strong mami,there ar no boundaries that it can hide''
Kasa daurewa mamin tayi har sai da ta dan daki kafadanshi ta baya dariya ta kamata,ringin din wayar maryam ya katsesu,abdur rahim ne,kamar ko yausheta kasa dagawa saboda kunyar mami shi kuma bai fasa kira
tsaki abdallah yaja yana fadin
''du Alla a kaahe wannan culculator din ya damemu haka nan''
mami ta kalli maryam
''daga kiranki maryam,ba mai jinki hirar mu muke''
tsaki ya kuma j''idan ba zata daga ba asauketa ta kammala wayar ta biyo mu daga baya kota koma gida''
''shut ur mouth,oya ina jinka,muyi maganar dake gaban mu''cewar mami
Minti ashirin tsakani suk iso gun dinner din,ita dai maryam rava idanu kawai take don bata saba zuwa ire iren guraren ba,bata da wannan rawar qafar sam,da dai su jamila ne su lubabatu tof babu na biyunsu
uwar taron dakanta ta fito ta taresu
''masha Allah hajja bintu ina kika samu kyakkyawar diya haka,ko surukar taki ce''
murmushi tayi ta wauwaya ta kalli maryam da abdallah dake bayanta,sai taga sun mata kyau din kuwa tamkar wasu couples,abinda bata taba kawowa a ranta ba ta jishi lokacin,sai taji tana fadi cikin zuciyarta ina ma da gaske ne haka dinne,ya waiwaya ya danqarawa maryam harara sai akayi sa'a suka hada ido,ya dan matso gab da ita har tana sheqar qamshinsa kana yayi qasa da murya kamar mai fada mata abun arziqi
''yi gaba mamalama,kin wani jera da muta ne kamar sa'anninki,salon 'yan jarida su ganmu tare ki samu daukaka ni kuna ki bani kunya'',itakam tsoronshi take don neman tsari take da shi hakan ya sanya batare ce masa komai ba tadan ja da baya da yake ya fita sauri tuni ya dan zar tata
mami ta kalli hajiya mai gado
''diyata ce ita din ma,amma surukar naku na zuwa insha Allahu,don shekaran jiya yaron naki ya min albishir,ya gama ruwan idon nashi da bani kunyar gun iyayen yara''
''a'ah,a qyale yaro na,ai lokacinshi ne a barshi ya zaba ya darje,ai ya cancanci yin hakan''
''um um kada ka ki fasa masa kai''
''ba zancan fasa kai sai tsabar gaskiya''da daddan hirarsu irinta qawaye suka iso gurin da ka tanada don baqi na musamman irinsu
anyi kiran iyayen amarya suzo su nuna tasu karar don haka mami ta miqe,ta dubi abdallah dake ta faman shan qamshi idanunshi na kan waya tunda sukazo
''bari muje nida martmyam liqi yanzun zamu dawo,kaima ya kamata ka qarasa ku gaisa da amaryar''
''ina zan iya tashi an cika guri da sakarkarun 'yammata marasa kamun kai,duk inda ka motsa suna kallinka kamar wasu mayu''
''kaji da shi dai,kallo kuma kayi abun kallin ne dole a kalleka,dukka abokan ango na gun stage suna liqi kaja ka zauna bayan kaima abokinka ne''mamaki ya cika maryam,yadda taji ana tababa da shi kan bazai je ba tayi zaton ma bai sanshi bane
''mami ni bazanje in kalli matar wani ba don nima babu mai kallarmin tawa''
''haka za'ayi naka bikin kenan kana nufin''
''ko za'ayi mami ba zata zo min da irin shigar da amaren yanzun suke ba,sai babballata in zubar''
hade rai mami tayi
''to ni kuwa bazaka balla 'yar muta ne ba ka barmu da jidali ba ka canza tunani''
murmushi ya subuce masa ganin yadda mamin ta hade rai kamr ma ya riga da ya aikata
miqewa yayi ya karbi jakar hannunta yana dariya
''Allah ya barmin ke mamata ni daya,muje in rakaki,Allah ya huci zuciyar hajiyata''
''hutsu ne abdallah''maryama ta fada cikin zuciyarta,suna hada ido ya daka mata harara ya kuma hade rai qyam tamkar bashi yake murmushi yanzun ba
a baya suke binta har suka isa atge din,ya miqawa mami jakar yana fadin
''gashi mami,ayi liqi a hankali''
''haba handsome,girman mami ne ai ta liqa ko nawa take so,babu ji tunda tana da kai''maryam da abdallah suka kalleta lokaci guda don mami bata ji ba tuni da kutsa ciki,wani sakaran kallo yayi mata gami da jan tsaki,ita dai maryam gaba tayi tana qoqarin bin sahun mami tana fadin cikin zuciyarta
''kin debo ruwan dafa kanki''
ji tayi an riqo tsintsiyar hannunta gam ana janta,babu shiri ta waiwayo abdallah ne tuni har ya fara tafiya,tilas ta saita wa kanta hanya ta bishi a baya tamkar raqumi da kala,don idan tayi tirjiyar bin nasa zata iya zubewa a qasa don da sauri yake jan nata
bai saketa ba sai da suka iao teburin na su kana ya sakar mata hannu hadi da yi mata nuni da kujerar data tashi dazu a kai,tsareta yayi da idanunshin nan masu kaifi
''sit,dake aka hada kutingwilar zuwa na nan,shine kuma duka zaku fashe ku barni zaune ji daya kamar yaron mayu,ki zauna ki kula da ni har mamin ta dawo ta karbeki,daga nan ma idan club zaki wuce ke ya shafa''
Tuni hawaye sun cika idanunta,bata ce masa komi ba ta zame ta zauna,shi kuma yayi tsaye hannayenshi harde bisa qirjinsa yana qarewa gun kallo tamkar mai neman wani
matashin saurayi ne yake dosowa gurin,kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewa ya gogu cikin duniyanci,sannu a hankali yake qarasowa har inda maryam din take,shigowarsa gurin kenan idanunahi sukayi tozali da ita,totally ta gama yi masa fatanshi daya 'yar hannu ce,zai iya kashe mata ko nawa ne matuqar zai samu hadin kanta,ta bayan kujerarta ya zagayo yasa dukka hannayenshi ya dafe makarin kujerar
''hello babe...''
gabanta ne ya yanke ya fadi,har ta kasa jiyowa taga ko waye,ga zatonshi bata ji ba don haka ya ranqwafo bayan nata yana shirin sanya hannunshi ya dafa kafadunta
cafkar da yaji an yiwa hannunshi yasan bata wasa bace,tamkar tarko ya kama bera haka abdallah ya riqe hanun nashi tsam,bai gama qarewa abdallan kallo ba yaji saukar lafiyayyun mari guda biyu da suka gigita shi,
hannu abdallah yasa ya yaye dogon hannun rigar t shirt din dake jikin saurayin,take wasu yan qanan rubutu da suka fi kama da na 'yan china suka bayyana a saman tsintsiyar hannunshi,a tare suka kakki juna ahi da mataahin tashin farko tsoro qarar ya bayyana idanun matashin,motsin da matashin ya fara yi da daya hannun nasa da abdallan bai riqe ba yana qoqarin cusa hannunshi aljihun bayan wandonshi ya ankarar da abdallan,cikin hanzari ya dunqule hannunshi ya daki hannun matashin take ya sagar masa da duk wata jijiya da zata taimaka masa ya iya motsa hannun,ya zura hannunshi aljihun matashin ya ciro 'yar qaramar bindiga ya cillata cikin nashi aljihun,qarar da ya saki ita ta janyo,hankalin mutanen dake kurkusa da su,cikin zafin nama da qwarewa da hannu daya ya tsinke duk wani maballi dake jikin t shirt din matashin ya finciketa daga jikinsa hade da juyo da bayan matashin ya kalla,zane ne kala kala a jiki wanda ba lallai kai ka iya ganewa ba
''anaconda isnt it?um?yaron alhj hamza mai qusa''
Abdallah ya fada bayan ya zagayo gaban matashin sunyi face to face,hannunshi daya ya sanya a aljihub rigarshi ya ciro qaramar wayarahi keypad qirar samsung,cikin qanqanin lokaci ya bada order turo ma'aikata inda suke din kana ya maida wayar aljihunsa,idanunshi qyar cikin na matashin yake tambayarsa
''ku nawa ne agurin nan?''shiru ya masa babu alamun zai amsa masa,hakan ya bawa abdallah damar yin tsai yana karantarshi,ba tare da matashin ya masa nuni ba ya karanci tabbas akwai abokin tafiyarsa ahannun daman abdallah,sai kuwa akayi dace shima ya yunquro da niyyar kubutar da dan uwanshi,duka daya abdallah ya waiwaya ya masa a dokin wuyanahi ya zube a qasa yana malelekuwa.
minti goma kyawawa basu cika ba jami'an ss suka iso gurin ya damqa musu su yace su kira jamal hussain ya fara aiki a kansu kafin gobe ya iso office din,mutanen dake gurin kam kowa godiya yake ma Allah suna fadin Allah ne kadai yasan me zai faru badon zuwanshi ba,sai da koma cikin mota ya kira mami yace suzo su taci don baya son,jama'suci gaba da shaida fuskarshi
ko cikin motar tamkar kace ket maryam ta zura a guje take ji,tsoron abdallah ya kuma cikata,ya dubeta da madubin motar lokacin da yake goge hannunshi da handkherchief suka hada ido,hade rai yayi yaja tsaki
''mutum sai shegen tsoro,komai ma tsorataka yake''mami tayi zaton da jama'ar inda suka baro yake
''a'ah wannan lamari fa da tsoro,wannan aikin ai saiku,kawai dai Allah ya tsare mana ku daga dukkan sharri''
murmushi ya saki
''haba mami na,kema fa jaruma ce,kin manta ke ke fede mutum ki ciro abun cirowa ki,mai da na mai dawa ki hadeshi ki dinke ya tashi tsaf yaci gaba da rayuwa cikin ikon ubangiji'
''um um,wannna daban da naku abdallah,a'uzubika bi kalmaatillahit taammaat min kullu ainin lammah wamin kulli shaidanin wa hamma''ta mishi irin addu'ar neman tsari da annabi s a w kewa hassan da usaini r.a
''ameen mami''ya fada don kusan a bakinta ya haddace wanna addu'ar tsabar yi masan da take yi,kuma yasha ganin riba da fa'idar ta
🌲🎄🌲🎄🌲🎄
ana jibi za'a dauki azumi ta tafi gidan raliya don su tattauna,ba qaramin dadi raliyan taji ba dq jin fitowar abdur rahim da dukkan qarfinshi neman auren aminiyar tata,ta jira har nasir ya dawo tayi mishi bayanin abdurrahim da kwantancan anguwarsu,ya dauka mata alqawarin xaiyi tattaki da kanshi har unguwar ta qoqi don ya mata bincike a kanshi,sosai taji dadin kara da karamcin da hayi mata,sun rabu kan duk yadda ake ciki nan da sati zaya sanar mata,ta mishi godiya sosai,yace babu komai ai an zama daya ya zolayeta da don ma ta qishi ne,dukkansu dariya suka saka da tuno baya da sukayi
kwanki shida kacal ba'a cika na bakwai din ba nasir ya kirata ya mata bayanin abdur rahim bashi da matsala,dukkan abunda ya fadi din haka yake,saidai abu guda bayan kasuwanci da yakeyi din yana da damara wato ma'aikacin tsaro ne,ta masa godiya mai qima sannan suka rabu,data tambayi abdur rahim din dariya kawai yayi yace yana tsammanin bata son auren mai unifoarm ne ya boye mata,bata dauki abun wani seriousd ba duk da ta nuna masa rashin jin dadinta ya kuma nemi afuwarta maganar ta wuce
azumi na da kwana goma ta sanar da abdur rahim ya shirya yazo ya gaida mami,bai musa ba ya amince,ta shirya masa girki na musamman,cikin wani dan kebantaccen gu dake harabar gidan ta ahirya komai,guri ne mai kyau davtsari cike da shuke shuke tamkar qaramin lamvu,duk da cewa daga can bayan gida akwai lambun amma wanna hakanan aka yishi darumfar bunu qwaya daya,qasanta shirye da fararen kujerun roba
mintina goma sha hudu ya rage akira magariba ta shiga wanka,ta ahirya tsaf cikin baqar doguwar riga mai sulbi data wadatu da dutsuna masu sheqi saqar qasar oman,mai kawavta shafa hoda ta zizara kwalli da man lebe,ta taje gashinta tayi acuci da shi daidai lokacin da masallatan garin kano suka soma kwarar kiran sallar magariba dabinonta dan madina dake cikin qaramin fridge din dakin ta ciro ta ciri uku taci ta ciro ruwa tasha sanna tayi add'ar buda baki,bandakinta ta koma tayi brush hadi da alwala ta yi sallar magaribar,kusan tunda aka fara azumi tare suke yin buda baki gaba dayansu,don haka bakwai na qarasa cika ta sauko qasan
tuni har mami da abida sun hallara don haka ta gaida mamin da yi mata sannu da shan ruwa ta soma sarving dinsu,ta kammala ta ja nata ta zauan,bata kai ga fara ci ba abdallah ya shigo ya ja kujera kusa da mamin yana fadin
''mami ke daya zaki ci ki bar autan naki''
''hmmm su auta manya''abida ta cafe zancan,harararta ya danyi
''kinga bansa da ke ba,wanna magana ce tsakanin d'a da mahaifiya''
hannu yasa cikin plate din chips dinta ya soma kaiwa baki dadin na ratsashi,bai ko kalli farantinsa guda biyu da cup da maryam ta shirya masa ba
sai teburin yayi shiru kowa na harkar gabanshi,cakula kawai maryam keyi don bata qaunar zaman cin abincin nan tare,sam bata sakewa
mami ta dubeta tana goge hannunta da ya dan baci da maiqo da tissue
''amma dai maryam ba wanna ce shigar fita zancan ba ko''
tayi murmushi har dimple dinta na lobawa kanta aduqe
''itace''ta fada kanta asunkuye,kallonta abida tayi ta sheqe da dariya kana tace tab,kallonta take kwaia wadda kanta yake cikin tukunya
''ban me yasa baki wa fuskarki makeup ba ko don kinsan ke din mai kyau ce,kyanki yana qara......''
bata iya qarasa zancan ba sakamon ciko pork da abdallah yayi da chips ya cusa ma mamin a baki
tilas ta karba sai davta fara taunawa ta dubeshi
''meye haka abdallah,dure zaka min''
ya marairaice
''mami baki qoshi ba fa,kuma idan ana cin abinci ba'a magana,ki qyale koma mene sai kin qoshi''
dauke kanta tayo ta dubi maryam
''ki duba kan mirrow dina akwai makevup kit ki dauko min yau da kaina zan miki kwalliyar
raka'a shida kacal ta samuyi sallar tarawih a maimakon raka'a goma sha uku davtakeyi,cikin awa daya saiga fuskar maryam din ta canza,zama mamin tayi sosai ta mata make up,abida kanta mamaki ta dinga yi,haka mami ta iya make up mai ma'ana?haka maryam ke da kyau,tun usuli ita din ba maison cika tarkace bace ta makevup a fuska,wannan kaye kayen sai hindatu,kyan da ta yiwa mamin yasa ta ta gaza barinta sai data mata hotuna,ta yi azabqr fita kuwa ahoton
aka gama kuwa a daidai,don gamawar tasu bai wuce da minti uku ba abdur rahim ya kirata gashi a compound din gidan ya samu shigowa bayan tarin tambayoyi da waya da mami ta yiwa securities din kan su barshi ya shigo
''jeki maza diyata ki shigo da shi''mami ta fada tana maida hijabinta data idar da sallar asham
tana qoqarin fita saqo ya shigo wayarta ta zaro tana dubawa,number din abdur rahim ta gani wanda hakan ya sanyata sakin murmushi ta soma qoqarin duba abinda ya turo mata
''ya subhanallah''taji ance bayan taga inuwar mutum a gabanta,da sauri ta daga kanta kana ta duba abinda taji ta taka
qafafan abdallah ne,taja baya kadan da sauri a tsorace,dawowarshi kenan daga sallar asham,sanye da jallabiya fara sol mai gajeran hannu wadda hakan ya sanya dukka gargasar hannunshi bayyana da hular tashi ka fiya naci itama fara,sai ya koma tamkar wani balarabe,kallonta yake kawai wanda har hakan ya bata tsoro,sexy eyes dinshi ya lumshe bisa fuskarta na aecond biyu ya bude
murya qasa qasa yace
''wacce iriyar makauniya ce ke,ki hau qafafun mutum ki taka saboda rashin kunya,idan baki wasa ba zan targada qafafun''tuni idanunta suka kawo qwalla
''kayi haquri ban kula bane''
ya janye shanyayyun idanunshi ya motsa zai wuce,har ta gifta shi yace
''wannan wane irin sakarci ne kwalliya cikin ramadan a irin wannan time din''cak ta tsaya zuciyarta na bugu
''ina zaki?''
''waje zanje.....baqo......''
bai bata damar qarasawa ba ya daka mata tsawa
''oya,wuce ki koma wannan iskancin ba'a gidan nan ba,idan zaki tara mazan ki bari sai a naku gidan''
jikinta na rawa ta wuce ya take mata baya
mami data hangota tace
''a'ah,ina baqon?''kasa cewa komai tayi sai satar kallon abdallah da yayi kicin kicin da fuska ya kuma basar kamar bashi ya korota ba,ya samu gefan mamin yayi zamanshi yana shan ruwan bunun da yasha kayan qamshi wanda mamin ta zuba tana jira ya huce ta sha
''kai abdallah,kai ka dawo da ita ko?''
''eh mami dare yayi me zata fita waje tayi taje ta dauko mana magana?''
''kaga malam baqo tayi yana nan compound ba wani gu zata ba''
''ok,wannan stupid din ita yake jira?,to ki fita mu gani,mami baza a ja mana magana ba agia,ta kwatanta mishi gidansu suje can su hadu''
''kai dakata!banason iskancin banza iskancin wofi,uwarta ne kai ko ubanta da zaka hanata fita ga mutumin da zai aureta,ina cewa jiya kasa bacci kayi sai da ka tasheni ka gayamin rana ita yau akai maka kudin aure?shine zaka hana wasu saboda tsabar son kai,to wallhi ahir dinka ka fita daga sabgar maryamu indai kanason zaman lpy''
saukowa yayi qasa ya sanya gwiwoyinshi a qasa ya kama hannayen mamin
''kiyi haquri mami,wannna ne karo na qarshe insha Allahu da zaki sake samuna da irin wannan laifin,ki yafe min banason shiga fushinki,cikin wata muke mai alfarma''
Sai da ta juya tace da maryam taje ta ahigo da baqon sannan ta kalleshi
''idan kana haka abdallah sai ta dinga jinta daban acikin mu,yin hakan tamkar takura ne agareta,ka gyra pls my son''
''insha Allahu mami''ya fada sannan yayi kissing bayan hannunta
shigowar abdur rahim ya sanya abdallah fita,a nutse suka gaisa da mamin,sosai ta yaba da hankalinshi,shi yake sanar mata maryam tace ita zata fadi ranar da za'a kai kudin aurenta gidansu,ya zabi kwana bakwai tace yayi kusa
murmushi mamin tayi
''maryam manya,kwana bakwai din yayi,Allah ya nuna mana''cikin farinciki walwala da mutuntuna juna suka rabu da mamin ya nufi inda maryam tayi masa masauki
''me yasa abdul kaqi cin komai ne''murmushi ya saki kana ya miqe tsaye yana duba agogon hannunshi,ya dauke idonshi daga agogon ya dan kalli bayanta kadan yasake dauke idonsa
''zan wuce ne maryam,lokaci yayi sai wani jiqon''ya fada agaggauce,a hankali ta waiwaya ta maida idanunta inda taga yana kalla din,abdallah ne tsaye saidai sam ba sashen da suke yake kallo,tuni har abdur rahim ya soma tattakin barin gurin,ta bishi a baya don masa rakiya,ya tsaya cak kana yace
''na gide,bana buqatar ki wahalar min da kanki ki koma ciki,sai haduwa ta gaba?''ya fada cikin sigar tambaya yana daga gira,kafadarta itama ta daga sukayi sallama ta juya don komawa mazauninsu na dazu ta kwashe kayan data shirya masa duk da bai taba komai ba face ruwan,duk da ya bata uzirin cikinshi a cushe yake baya iya cin komai sai da sahur amma bata ji dadi ba
abdallah ta taras yayi daidai yana kwasar garar abinshi,bata ce komai ba ta juya ta bar gurin ta shige bangaren mamin
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[9/17, 12:54 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣3⃣
💞😍💞😍💞😍
*_godiya ga masoya na_*🙏🏽👩❤👩
*_masu qaunar rubutuna_*💞✍🏽
*_qaunar da kuke min bazaiyu na manta da ku ba,na yaba qwarai da gaske_*😃😍
*_gaisuwa ban girma da jinjina mai qima ga_*
*huguma novels room and huguma conversation room*
*maman aysha novels group*
*hausa novel group by umar dalha 1&2*
*zama na amana group facebook*
*khafinga group 2012 class*
*gaisuwa kai tsaye zuwa ga GARKUWAR ABADAN SISTER RABI'ATU HARUNA*😄😄
*Allah ya barmu tare ya samu cikin masu son juna saboda shi da zuciya guda ameen*
*_rabbanag fir lana wa li ikwaninallazina sabaquna bil eman wala taj'al fi qulubina gillal lil lazina amanu rabbana innaka ra'ufur rahim_*🙏🏽
Sau biyi tana zuwa dubawa taga ko ya kammala sai tazo ta tarar bai gama ba,sai a zuwa na ukun ya sameshi ya ture kwanonin gefe alamun ya kammala kenan,bata ce da shi komai ba ta soma hada plates din guri guda tq zuba cikin kwandon
''ji mana''taji yace da ita,a hankali ta dago kai suka jada ido,ya kafeta da zaratan idanunshi sai ta kau da kanta gefe
''idan kin koma kuma ki sake hada ni da mami na kice ni naci abincin,ko da yake ko kin fada din dama ai aikina aka dauko ki yi ba wai ki dafawa wani qato ba,a qa'ida ma idan kika kuma gigin yiwa wani girki ba da izini na ba ma a albashinki''
ya ture kujerar da yake kai baya ya miqe ya kewayeta ya wuce,ta biahi da kallo tsanarsa da tsanar halyenhi na takura matsi da girman kai na addabar zuciyarta,sai da ta tabbatar ya ahige bangarenshi sannan ta shiga nasu bangaren
🎄🌲🎄🌲🎄🌲
da yake azumi ne qarfe tara ta shirya taje gida,ita da hindatu suka tattauna abinda za'a shirya don 'yan kawo kudi da zasu zo jibi da safe,ruwan roba ta siya carton biyar na lemo ma haka,sai maltina itama carton uku,kujerun da aka fidda dakin mama su aka maida sitroom dinsu wanda rashin wadata yasa yake fanko babu komai a ciki,babu abinda kujerun sukayi tunda ba'a dade da yi musu kwaskwarima ba ta qarin katifa da canza yadin kujerar kuma ba yara gareta ba balke su lala ce da wuri,ko dama can ita mamsn mai tsumi tattaku da tanadi ce,ta siyi leda da labulaye duka aka sanya,sai sitroom din yayi kyau daidai talaka,tuni dama kayan gadon maman aka shiryashi bedroom din baban sun zama nashi
muqullin ta danqa hannun hindatu don tana jin su kula na rawar kan yau a ciki zasuyi zance don duka babu wanda yasan me za'ayi da dakin aka gyara shi haka,wannan rufewa fa da tayi sai taso zama dan zani sukayi dafifi a tsakar gidan suna basu amince ba ai gida dai na ubansu ne babu wanda ya isa ya musu shamakivda wani bangare na gidan,shigowar baban ya tambayi ba'asi wannan karon hindatu ce tayi uwa tayi makarbiya ta masa bayani
to shi din ma wannan karon bai basu goyon baya ba yadda suka saba samu,hakab ba qaramin qullacinsu maryam ya sake sa musu ba,da azahar sukayi sallama don tana so ta leqa raliya,mama ta dakatar da ita tana fiddo da dararen borikan fenti uku daga uwar dakanta
''me wannan a ciki mama?''ta fada tana budewa
botikin farko alkaki ne a ciki
na biyu dubulan
na uku nakiya ce
ta dago ta dubi maman
''duka na meye wannan?''
''saboda 'yan kawo kudin nsn nasa akayi,kinga za'a kuma fita kunya ko''qauna da tausayin mamanta ya sake shigarta,Allah sarki mama,farincikin dake zuciyarta Allah kadai ne ya sani,a haka ma tana alkunya tana danne farincikin nata sabida kara irin ta dan fari
''Allah ya saka da alkhairi mama sunyi,Allah ta qara arziqi,amma mama banason ki dinga tatse kudin hannunki haka,yanzu wannan kayan ai sunci kudi da yawa''
''ai aikina ne maryamu,idan da da akwai cikakkiyar wadata ma baki cancanci ki kiyi komai ba''
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
qarfe biyu da rqbi suna falon raliyan su biyu sai fadil dake kwance kujerar geansu yana baccinshi hankali kwance,cikin farinciki raliyan take tamkar ma itace maryam din
''wani hanin ga Allah baiwa ne maryam,yau gashi Allah ya musanya miki da jabir,sun sanya bawan Allah a tsaka mai wuya har yau yana cikin damuwa,shekaran jiya yazo gidan nan yake tambayar abban fadil ke,yana son ya nemeki amma wai kunyarki yake ji,shegiyar yarinya marasa tsoron Allah itavda uwarta,duk jabir ya fita hayyacinshi kmar bashi ba,roqon Allah ne masa ya dawo cikin tuna ninshi cikin lokaci qanqani haka''
ajiyar zuciya ta saki
''duk wanda ya debo da zafi ai bakinsa raliya,nikam wanna ya riga ya wuce tamkar wani mafarki na daukeshi''
ta zura hannunta cikin jaka ta soma laluben wayarta dake ringing hade vibration ta cirota,kiran abdur rahim ne tasan shi dinne tun kafin ta ciro saboda special tune da ta sa masa
''ranki ya dade duka yau ban jiki ba ko cigiya ta baki yi anya kuwa''ya fada cikin salin zolaya bayan sun gama gaisawa
murmushi ta saki
''yau na tashi ne cikin sabgogi amin afuwa''
''ayyah,da kinyi magana ai da nazo na tayaki,ina fata basu wahalmin da ke ba''
''alhmdlh tunda tuni na kammala yanzun nake shirin in koma gida''
sai ya danyi duf kana yace
''me yasa baki tambayeni ba da zaki fita,saiki dinga fita kanki tsaye maryam ana ganemin ke''
murmushi ta saki
''mantuwa nayi ashe fa yanzun ina da miji,baza'a sake ba''
''matsalar ban iya fushi dake maryam,yanzun dai sgikenan kimin kwatancen gidan da kike zanzo yanzun nan na maidake gida,naga hadari na haduwa kada ruwa ya dakarmin ke ya barni da zazzabi''
ba qaramin nishadi maganar ta saka ta ba ,take ta masa kwatancen inda take din sukayi sallama ta ajjiye wayar
suka hada ido da raliya tare suka saki murmushi
''gaskiya na fuskanci ba qaramin ji dake abdul din nan yake yi ba,Allah ka nuna mana wannan rana''
dariya tayi gami da dukan gefan cinyar raliyan tace
''har ya kama qafar nasir abban fadil''suka sake sa wata dariyar raliyan na fadin haba wane mutum
minti goma wayar ta sake kadawa,abdur rahim tayi tsammani shi dinne kuwa
''kiyi min afuwa maryam zuwa na bazai samu ba wani aiki ne na gaggawa yanzu aka turamu dole kuma na kasance aciki idan ba haka ba akwai matsala,amma kiyi sauri don Allah ki koma gida hadari ne sosai a garin kada ruwa ya tabaki''
macace mai sauqin kai da fahimta don haka tace masa
''babu damuwa Allah ya bada sa'a''
ya saki ajiyar zuciya
''na gode da kika fahimceni sai munyi waya''
ta dubi raliya bayan ta miqe tana hada jakarta,ta tavbata hadarin ne don tuni garin ya lumshe har ta soma jin quginsa
''wucewa zanyi raliya an samu matsala abdul bazai samu zuwa ba aikin gaggawa nebya taso muau yanzu a office''
''a'ah,yanzu da uban hadarin nan zaki tafi?ki jira abban fadil ya dawo sai ya kaiki''kama baki tayi bayan ta gama rolling mayafinta
''girkin kuma na barwa wa?,so kike kenan yau abdallah ya samu nayi ko,cikin watan nan ya tairi wani abu ko kunu ne idan bani nayiba sai ya gane,yanzun sai yace a salary dina''
ta dage girarta sama
''haka ne fa,muje in taka miki,amma jirani in shiga in fito''cewar raliyan tana shigewa bedroom dinta na qasa
kwalbar turare ta fito da shi hade da baqar leda qarama ta miqa mata
''turaren da kike ce min kina son irinsa nasa abbn fadil ya aiyo manaamma kiriqe da kyau saboda yana leeking,sai bra din nan qualitative one da mukayi maganarta jiua da muka fita na siyo mana''
''kai qawata,bani da bakin magana,Allah ya raya mana fadil ya bar mana zumuncinmu,ya tsone idon maqiya''
''ameen raliyan ta fada tana bin bayanta,haduwar jadarin ya sake rudata har ta kasa saka kayan cikin jaka,a bakin get suka rabu ta soma sauri gashi ita ba gwanar saurin bace
har ta kai bakin titin su raliyan bata ga abun hawa na haya ba,kusan dama haka yanayin unguwar tasu yake ko jama'a baka fiya gani ba,bare yanzu yanayi na azumi kowa yayi likimo cikin gida,hankalinta bai daga ba sai data tsaya atitin,taga motoci dake karakaina ma baifi ka irga au ba,adaidaita uku ne suka wuce biyu daga cikinsu duk cike take da mata dayarkuma maza ne cike har gaba kusa da mai tuqin,a hankali iska ta soma kadawa mai qura alamun dake nuna hadarin ya gama nuna a sama sauka kawai yake da buqatar yi,addu'a kawai takeyi cikin zuciyarta a haka ruwan saman ya soma sauka
tsamo tsamo tayi don ya fara jiqata ta soma hade jikinta guri daya,motoci uku ne qirar land cruisser baqaqe wul hatta da glass dinsu suka tsaya a gabanta,gabanta yayi mummunan faduwa,tuni ta somacwaige waigen neman inda zata fake idan gudun ceton rai ya kama
glasan motar farko nagaba mazaunin mai tuqi suka sauka qasa,hassan ta gani daya daga cikin direbobin abdallah,sai a likacin taji ta samu nutsuwa,murmush yayi nata itama ta maida masa
''madam yi sauri ki shigo kina ta jiqewa''
taji dadi sosai kuwa,da saurinta ta qaraso ta bude mazaunin gaba ta shiga tana fadin
''na gode qwarai,amma ba tare kuke da og.....''
''me muka tsaya yine hassan?''
muryar data fito daga sit din baya ta katsse mata sauran magan
''nun dauko madam ne''ya fadi yana qoqarin tayar da motar
''waya baka izini ko tsabar iya sayawa mutum raini ne?''
''sorry sir,naga gida zamu ne,kuma itama gidan zata.....''
''ni na gaya maka haka?''ya tambaya murya a kaurare
''am sorry sir naga madam nada kirk.......''
abdallah ya katseshi ta hanyar fadin
''mtswee,shutup malam sauka ka barmin mota ka koma motarsu auwal''
da saur maryam ta kuma riqe jakarta wadda garin saurin ledar hannun ta har ta subuce ta fadi qasan motar bata sani ba
''kayi haquri,ni ya kamata na fita ba hassan b.....''
''hey,bana son iyayi shi nace ya fita din bake ba''
tuni hassan ya bude motar ya fice ganin hakan ya sanya itama ude na bangarenta tana qoqarin fita
''idan kija sake kika fita sai na karya sillar qafar taki inga ta rashin kunya''
tilas tana ji tana gani ta koma ta zauna
''rufemin mota malama don idan ruwa ya jiqata sai kin busar da ita tas a yanzu yanzu''taja qofar garam ta rufe cikin haushi,tana iya gano ragowar motocin suka zagayesu suka wuce
mujallar da yake research kanta tun dazun ya sake janyowa ya bude yaci gabavda karuntunshi hankalinshi kwance tamkar yana cikin dakinshi ne,sanyin a c din motar ya soma takurata gashi tayi mata kusa da yawa,tuni kanta ya fara sarawa ta qudunduna gu guda tarw da jingina jikin makarin motar ta lumshe idanunta tana ci gaba da jin yadda ciwon kan ke dada yin gaba
'yar qaramar qara taji tamkar ta waya ''siiit''a hankali sai dumi ya maye gurbin sanyin ac din,bata tantama maidashi akayi banaren dake bada dumi,duk da taji dadin hakan amma babu abinda ya rage mata daga ciwon kanta
mintina kusan arba'in basu tafi ba kamar yadda ruwan bai tsagaita ba,ta bude idanunta a hankali ta miqe ta zauna daidai,a karo na biyu ta kuma sanya hannunta kan mabudin qofar don ta qudiri aniyar ficewarta zatayi kome zaiyi mata saidai yayi,saidai taqi buduwa da alamu an saka lock,ya ajjiye mujallar hanun nashi ya jawo baqin space ya mannawa idanunshi sannan ya bude 'yar qaramar kyakkyawar baqar lemar dake kusa dasji ya fito ya dawo mazaunin driver
amadadin ysyi hanyar gida sai taga sun csnza titi,batason kulashi amma ya zama mata dole
''ina cewa gida zammu ko''
banza yayi da ita,ta qufula amma bata fasa sake fadin
''girki fa na can na jira na gashi yanzu hudu harda rabi''
''karki cika ni da hayaniya,baki da zance sai na girki kamar dinshi aka halicceki,ai bake daya kika iya girku cikin gian ba ko''
ya fada udanunshi na bisa kwalta,bata sake tofawa ba ta maida kanta gefe daya
cikin wata unguwar taga sun shiga wadda take kama da tasu mamun wajen kyau da tsari,qofar wani katafaren gida taga ya tsaya,ita kanta sai da ta bi gidan da kallo,duk kyau na gidansu mamin wanna ya dokeshi,bude motar yayi yay ficewarsa ba tare da da yace mata komai ba
zaman kusan awa guda da rabi tayi kafin ta sake ganin fitowarsa,a dan bakin qofar ya tsaya kafin ya qaraso tana iya hango jikin wanda suke magana tare,da alama macece don ga gefan mayafi nan,ba qaramar qufula tayi,ba cikin zuciyarta
''zance yazo kenan ya barni a mota ko yaya?''ranta sai ta kuma ji ya baci,ya bude motar ya shigo
''zance da ranar Allah cikin watan azimi,wanne wane irin tsari ne''ta ja tsaki,saidai cikin subutar baki tsakin ya fito
juyowa yayi kalleta
''wa kike ma tsaki?''sai ta juyo tana kallonshi itama
''idan kika sakemin tsaki sai kin fita min a mota tunda bada kudinki aka siya ba''sai idanunta suka wal
''daina kallona''ya fada bayan ya dauke kanshi da sauri daga cikin idanunta
''kada ki cuceni''ya fadi can qasa yana lumshe idanu tarw da yiwa motar key,bata kawo komai cikin ran ta ba ta dauke idonta cike da jin haushinsa
🎄🌲🎄🌲🎄🌲
Ashirin ga azumi mami ta bata kayan sallarta,a dinke suke dinki ne na gayu wadanda suka mata cif a jiki,atamfofi uku lace daya material daya,sai codelace shima daya,duka atamfofin dogayeb riguna aka mata don mamin ta fuskanci tana sonsu,jaka biyu takalmi biyu sai mayafi biyu hijabi daya,sannan tace ashirin da biyar ga azumi zasu fita sai ta zabi fashion da zatayi amfani da su,bata fasa yiwa mami gidiya ba duk da ta gaya mata diyarta ta yiwa no need tace sai ta gode mata,godiya kuwa ai tamkat wajibi ne tayi mata don ko daga gurin mahaifinta bata taba samun makamancin irin wannan gatan ba
abida kam akwati guda medium abdallan ya hada mata bayan takurawar da mami tayi masa kan ya hada matan,don shi totally baiyi niyyar mata komai ba
cikin irin kyautar da mamin ke yawan yi mata ta fidda atamfa biyu ta baiwa tela ya dinkawa mamanta,ta siya mata mayafi takalmi da jaka,albashinta na watan ciki ta cira ta baiwa hibdatu tayi siyayyar salkarta babanra ma shadda ta siya masa kala biyu ta hada mishi da kudin dinki da takalmi da hula daidai,kai kada ksso kaga baqinciki,ina wuta a saka maman da iyalsnta,godiya kam gun baban ba'a magana
''sai yanzu nasan na haifa,yanzu ne na fara cin albarkar haihuwa''baban ya fada lokacin da yake gwada hular da ta kawo masan
''oho dai,wlh malsm ka guji ranar da zaka karbi shegen jika cikin gidan nan,ka gama cin dadin dai wuyar na tafe,shi yasa gata nan har yau babu mashinshini yo kowa yasan aikin tsiyar da take aikatawa''
inji baba hadizar don daga ita har huwailsn babu wanda yasan da zancan kawo kudinta,ranar kamar Allah ya kadasu duk suka fice unguwa suda qananun 'ya'yansu,huwaila tayi gurin boksn boginta ita da uwale hadiza ma ta bazama ga nata bokan,sunacan yawon asara har yan kawowar suka tafi,'yammatan da zawarawan kuma na nade a gado suna bacci don wadan nan sukan kai sha biyu da rabi zuwa daya basu tashi ba
huwaila kuwa cewa tayi''mu namu ai shegensu mukayi muka shigo dasu gidan ko,ko ince tsinannu ne''shidai babu wadda ya kula cikinsu ya kwashe kayanshi ya shige dakinsa
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Qarfe goma suka dawo daga siyan kayan kwalliya da suka fita harda mami da abida,tayi sallama da mamin ta shige dakinta don da wuri take son yin bacci ta tashi akan lokaci sallar dare saboda yau an kai azimi ashirin da shida zuwa anjima daren ashirin da bakwai zai shi daren da akesa ran dacewa acikinsa
zuwa sha daya na dare takammala komai ta haye gado bayan ta gama addu'o'in kwanciya ta karanta saqon abdur rahim fuskarta fal da murmushi,kusan cikin watn gaba daya wayarsu bata fi aqirga ba sai tex akai akai,yace shikam bazai iya jurar jin muryarta ba,tana shirin kashe wayar kira ya shigo,ta zubawa lambobin ido tana kallonsu,tana tunanin inda ta taba saninsu
tabbas ta taba sanin numbers din,har wayar ta tsinke ta kasa dagawa,second biyar tsakani wani kiran ya kuma shigowa,jiki babu qwari ta sanya hannunta ta daga ta kara akunnenta
''assalamu alaikum wa rahmatullah''itace abinda yavdaki sodon kunnenta,mummunar faduwa gabanta yayi,babu inda zata ji muryar ta kasa ganeta,amma tan tama take kiran nata ne ko batan kaine,ta sake cire wayar akunnen ta tayi ta kuma duba screen din wayar mai kiran dai na bisa layi kuma ita din aka kirar
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[9/17, 12:54 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣4⃣
*_daga abu hurairah Allah ya qara yarda da shi yace:an tambayi manzan Allah s a w wanne musulmi ne yafi falala?,sai yace:wanda musulmi suka kubuta daga sharrin harshensa da sharrin hannunshi(ma'ana bai cutar da kowa da harshensa ta hanyar magana,ko kuma da hannunshi ta hanyar ayyukansa,daure ka/ki zama daga cikin musulmin da suka fi falala,abun ba wuya 👌🏽matuqar ka jajirce kafi qarfin zuciyarka,Allah ta bamu iko ameen)_*
''wa alaikumus salam''ta fada asanyaye
shiru ya dan ratsa tsakani kadan
''da alamu baki ji dadin jina da kika yi ba ko maryamu?,hala ma kin manta da ni?''
''ko daya,ban kuma mance da kai ba''
''da fari kafin nace momai maryam,nasan bani da kalmomin da zasu gamsar da ke gurin ban haquri,amma duk da haka ina roqarki don Allah don annabi ki yafemin,ba da gangan abinda ya faru tsakaninmu ya faru ba,bada sani na bane maryam,ki yafewa jabir masoyinki''
tausayinshi ya kamata ta dan kumshe idonta kadan ta bude
''kada ka bata bakinka gurin bani haquri jabir,tuntuni gaskiya ta dade da yin halinta,anyi walqiya komai ya bayyana''
yaja dogin numfashi kana ya sauke ajiyar zuciya
''alhamdulillahi rabbil aalamin,dukkan godiya ta tabbata ga Allah,babu shakka ke din jaruma kuma nagartacciyar masoyiya ce,bana tantama zaki zama mace ta gari uwa ta gari gurin 'ya'yanta,bazanyi nauyin baki ba ba kuma zanyi qauro ba maryam inason ki bani damar fitowa neman aurenki karo na biyu,tare da cikakken fatsn babu wani da ya sha gabana''
sai da gabanta ya fadi,tayi shiru tana son daidaita bugun zuciyarta sannan daga bisani tace
''qaddara ta riga fata jabir,Allah ya qaddara run da dama ni ba matarka bace,hakaza matar mutum kabarinsa,bai wuce sati biyu da kawo kudin aure na da wani ba''
''la haula wala quwwata illah billah''ita ya dinga maimaitawa tsawon mintina biyar
''yanzu kina nufi maryam na rasa ki kenan,zaki auri wani na?,ki bani dama maryam mai rabo shi zaya samu tunda har yanzu ba'a daura aurenku ba balle kice kin haramta a waje na''
''kai mai sani ne jabir bakin gwargwado,ka sani cewa nema akan nema haramunne,baya ga haka ma daga ni har kai babu wanda aka bawa qudirar rubuta kundin qaddararsa da kansa,kuma buwayin sarkin dake rubuta msna din mai dumbin adalci ne,babu yadda za'ayi ya rubuta mana abinda zai zama zalunci ne a garemu''
''haka ne maryam,alhndlh Ala kulli hal,na gode maryam,na gode matuqa da gaske,bazan taba iya mantawa dake cikin kundin rayuwata ba,na barki lafiya''
tafi minti biyar riqe da wayar ra kasa ajjiyeta,tausayin jabir dinne kadai ke dawainiya da ita,babu shakka bazata iya manta dumbin alkhairansa gareta ba,koda ta tashi sallar dare bata mantashi cikin addu'o'inta ba,ta roqa masa alkhairi mai yawa kamar yadda a baya yayi nufinta da shi
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
Washegari mai lalle tazo yi musu,babu yadda mami batayi da abida ba amma qememe taqiya,tabe baki tayi
''nifa mami ba za'a batan hannu ba hakakawai da wannan abun''
''banda abinki ai shi jan lalle ga mace sunna ce baya ga haka ma ado ne''inji mami
ta sake ya mutsa fuska
''um um,a muku dai,mukam a turkey bamu irin wannan abun''ba wanda ya kuma tanka mata cikinsu nanta kwanta tun tana kallin qunshin har bacci yayi awon gaba da ita
kamar ko yaushe suna table don cin abincin buda baki u ukun maryam mami da abdallah,ta zubawa mami da abida ta soma zuba na abdallah,ya dago da sauri don yaga iya wanda zata zuba din don vaiso ta cika masa plate kamar na jiya,idanunshi suka sauka kan zara zaran fararen yatsunta da qunshin yayi kwanciyarshi kai ya sake fidda kyawun hannunta,farar fatarta ta sake shar
Zanen ya burgeshi duk da ya saba gani lokaci lokaci gun maminshi,duk kuwa sanda tayi din tun yana yaro ya dinga cewa tayi kyau kenan,maryam ta janye hannunta bayan ta ajjiye nasa plate din ta koma mazauninta,sam babu wanda ta lura sai abida,kishi ya cikata har taji kamar ta guntike hannun maryam din,ya janye idanunshi daga kan lalken suka hada udanu da abidan
''ke ina naki kwalliyar?''
''abida kam ai ta manta gargajiyar al'adarta,tace bataso bata mata hannu za'ayi,bayan shi kanshi ma ganine''
caraf abidan tace
''naga kamar ya burgeka ko,ba damuwa sai amun gobe''
tabe baki yayi ta daga kafadarshi hade da ware ya tsunshi
''no,idan ta nine kada ki sauya ra'ayinki ki bata hannunki''ya qarashe zancan yana jan plate dinshi ta soma cin abincin
zahariyya ce tayi sallama hannunta duka biyun dauke da foodflask masu azabar kyau da tsada,fuskarta a washe da faea'ar data qiqirarwa kanta ta qaraso gun,ta fara da dora flask din duka saman teburin wadanda tunda aka shigo dasu maryam take jin matsananciyar faduwar gaba ta kuma kasa daina kallonsu,mami ta gaida kana abdallah,tsakanin ita da abida kuwa babu wanda ya kula wani kowa na ji da danbanzan girman kanshi rawanin tsiya
''favourite food na ya abdallah nene ra tashemu sai da mukayi masa wai yadda ta saba sanda alhj baaba(alh abdulkareem mai nasara kenan mahaifin abdallah)yana raye wai yanzun ma ba zata fasa ba''
murmushi mami tayi tana janyosu gabanta tare da fadin
''kai kice mata kam mun gode qwarai,kamar kuwa tasan yau bamuyi girki ba nace maryan ta bari sai sahur aikin yayi yawa''inji mami sanda take hude flask din,rake kuwa qamshi ya cika gurin
''ki mata godiya''inji mami sanda zahariyyan ke nufin fita
''zata ji kam''ta amsa mata lokacin da take qoqarin sanya qwayar idanunta cikin ta maryam a fakaice,cikin sa'a kuwa suka hada idon,wanu mummuna kallo mai cike da gargadi da jan kunne tayi mata kana ta fice
Gaba daya ta saki cin abincin ta zurfafa cikin tunanin yadda zata salwantar da abincin ba tare da tabar kowa ya dandana ba,tayi imani komai zasu mata ba zata iya bari tana gani gaban idonta wannan ahli su salwanta ba,qarshen butulcin da zata musu kenan wanda ba zata iya yafewa kanta ba har abada,cikin haka taga mami na kiciniyar bude food flask din zata zuba,da sauri ta miqe tana fadin
''mami barshi in zuba miki mana ''tuni har ta isa gabanta ta karba don kada ta yanke mata hanzari tace ta barshi,ta jawo flask din miyar gaban table din sosai ya zama rabi kan tebur din yake zaune rabi kuma free ba matokari,sai ta jawo na abinci ta bude,da plate a gabanta amma sau tayi dabarar miqa hannunta tavdauko na can sashen da abida ke zaune
Tana daukar plate din ta sakeshi kan flask din miyar take nautin tangaran din ya rinjayeshi sukayi qasan table din suka tarwatse kan tiles,tangaran din ya koma piece,taja baya da sauri tana salati tate da kallon gun da abincin suka kife
''subhanallahi ya haka maryam?''
''for god sake mami yanzu wannan wane irin kidahumanci,ita din qaraman yarinyace da zata kifar da abinci flask biyu,kayi magana kuma yanzun mami ta ji haushinka ta saka a black list''ya qarashe maganar cikin bacin rai yana yayyarfa hannu da jujjuyawa hagu da dama kan kujerar da yake zaune
harara ta balla masa sannan ta kalli maryam
''ina fata baki ji ciwo ba maryamu''
kai ta gyada zuciyanta na wani irin gudu gefe daya kuma tana hamdala ga madaukakin sarki da ya bata nasara a sauqaqe ta rabasu da abinda zaya hallakasu,ita ta tsaya ta gyara gurin duk da momi tace ta bari sai ta huta tukyn amma sam ta qiya,bazata iya ba don ko quda bata fata ya dandana abincin,balle ma ta tabbata ban da awa biyu ko uku indai da gubar abincin zai fara ratattakewa
ta gyara gurin tsaf ta kwashe bayan ta rage kadan ta samu yar roba ta zuba hade da miyarshi ta shige da shi dakin gadonta ta tura ahi qasan gado,sai da ta gama komai kafin ta kwanta ta jawo robar don dubawa,cikin awa uku abincin ya fita kamanninsa kamar wancan,batasan lokacin da hawaye suka soma zuba daga idonta ba
mutum abun tsoro Allah abun tsoro
yanzu dan uwanka bil'adama kake da buri yaci wannan abun?
waishin wanne rin laifi ne abdallqh ya yiwa mutanen nan ne haka da zafi da suke da burin rabashi da soron duniya?
sai kace mudin an mana wahayin tabbata acikinta?
kwana nawa ne kaima ka hada ya naka ya naka ka qara gaba?
koda shekara miliyan zakayi wataran dai sai sun qare din ka tafi.
itakam ko kadan batq ga abun morewa ba wajen cutar da wani bayan ka san cewa Allah bazai taba qyaleka ba sai yabi kadi,duk wanda yaci nanin nanin dole ta cishi
cike da kasala da mutuwar jiki ta shige toilet dinta tayi plushing din duka abincin ta wanke robar ta wullar a dust bin
🍃🍂🍃🍂🍃🍂
Sallah bikin daya rana,cike da walwala farinciki bikin sallah ya soma gudana cikin duniyar musulmi baki dayanta,sai a lomacin mayama ta dinga ganin dangin su mami da na mahaifin Abdallah,don kusan kullum ne sai sunyi baqi,saboda haka bata samun zama aosai,damuwarta daya ma kada abdur rahim yace zaya zo ya samu bata da lokaci sai gashi bai ma nemi zuwanba iyakaci waya sai saqon,barka da sallah daya turo mata na credit din dubu goma yace kuma ta jirayi kayan salarta duk ranar da zaya zo
Ta fuskanci ba kadan bane maso sun abdallah cikin danginsa daga na mamin har na abbaanshi,kishi ke hana abida zama ciin gidan tayi ficewarta yawo sai dare
''rashin sani yafi dare duhu''maryam kan fadi hakan cikin zuciyarta ko kuma tace
''bonono rufin qofa da barawo''a duk sanda taga abida na wannna haukar kishin nata don bata da masaniyar kai kudi abdallah daga ita har zubaidan bare salma da saddiqa da bama ganinsu ake ba,har ga Allah tausayinta takeji kan fadawa son botsatstsen mutum irin abdallah,wanda koda yana sonki zaki sha wuya da shi bare kuma baiyi da ke a ganinta
hudu ga salla suka fara samun sararawar baqin duk da ana cikin dai hidimar sallah da shagulgulanta
da la'asar ne babu dadewa da gama salla wayarta ta fara ringing,tana kan cinyarta din haka ba jinkiri ta daga,muryar jabir ta tsinta yana mata sallama,ta amsa masa kana suka gaisa amutunce
''mai yayi zafi haka ido zaici wuta maryam,a qalla dai ai ko barka da salla a kirani ayimin''
ta dan saki murmushi
''kayi haquri,na ahiga sabgogi ne da yawa,ayyuka sun kacame min kusan yaune ma kadai na dan samu kaina''
''gaskiya ne,ai manya dama sai da uziri''dariyar zolayan da yayi mata tayi,kafin tace komai ya dora da fadin
''ko zan iya ganinki,maryam?''tavdan fiddo ido waje kamar yana ganinta
''yanzu?''
''eh idan da zan samu yau din da nace miki na gode,amma da zakimin alfarma da sai mace miki mu hadu gobe''
tunaninta daya ina zata ce mishi su hadun?,sam bata da sha'awar kawoshi nan gidan kamar yadda ko kusa ba zata yarda su hadu gidansu ba
ajiyar zuciya ta saki
''babu damuwa,muna iya haduwa gobe kamar hudu na yamma a gidan zoo ko?''
''kin ko san a itin kwanakin nan cika yake,anya zamuyi magana anutse kuwa?''
''eh nafison gurin jama'a din ai,kuma akwai bangaren da zamu iya zama da babu cikowar''
''shikenan babu damuwa na gode,amma baki tambayeni,mai yasa nake da buqatar mu hadun ba''
murmushin ta kuma yi
''a tun sani na da kai da alkhairi,na sanka,don haka yanzu bazan canza in maka zaton sharri ba,kaga kenan ina tsammatar jin alkhairi ne daga bakinka''sosai yaji dadin irin shaidar da tayi masa,har yau bai fasa yaba kyawawan halayen maryamu ba,kowa tana masa kallon mutumin krki ne kamarta,hakanan tana kowa kallin mai kyakkyawar zuciya kamar yadda ita din take
🎄🌲🎄🌲🎄🌲
Qarfe hudu suka fita daga gidan zuwa gidan zoo din ita da hindatu,dukkaninsu cikin kwalliyar atamfa suke riga da skert,sunyi kyau kam masha Allah
a can suka taddashi har yana zolayarsu sai yaci tararsu sun mishi african time,yayi kyau abinshi cikin dinkin kufta ya dswo jabir dinshi na ainihi,kyakkyawan matashin saurayin nan mai yawan ado da fara'a jabiru
gurine kebantacce dake can cikin ainihin gidan ajiyar namun dajin na garin kano,tamkar lambune ska yishi na musamman kudin shigarshi ma daban yske kusan ba kowa ne ma yasan da gurin ba,kujera ce irin ta siminti suka zauna a dayan shima ya zauna a dayan,sabuwar gaisuwa suka sake,maryam ta dubi jindatu tace dan bamu guri kadan to tace kana ta miqe,jabir din yace
''ai da kin qyaleta ma don maganan ya shafeta''ta yi gaba amma ta jiyo abinda yace din sai gabanta ya fadi hakanan
''maryam,haqiqanin gaskiya na yaba da kyakkyawar tarbiyyar da kuka samu,sannan nayi baqinciki qwarai da gaske da rasa ki da nayi duk da nasan cewa komai qaddara ce daga ubangiji,saidai ina kwadayin hada iri da ku maryam,ina neman wata alfarma guda daya,Allah yasa wannan karon bazanyi failing ba''
cikin tattara dukkan hankalinta a kanshi tace
''babu wata alfarma da bazan iya maka ba indai ina da iko kima bata keta haddin shari'a''
''be keta ba maryam''ya fada yana murmushi wanda ya qara masa kyau da kamala
''so nake ku bani hindatu''
idanu ta zazzaro tamkar taga wani abun tsoro idanunta kan jabir din
''jabir........shin ka manta alaqar dake tsakanin hindtu da jamila ne?,ya da qanwa ne fa?''
''koda na taba sanin jamila a matsayin diya mace hindatu bata haramta gareni ba tunda igiyar saki ta raba tsakaninmu balle babu abinda ya taba shiga tsakanina da ita na auratayya,yadda aka kaimin ita haka na dawo musu da ita,so kika babu maganar janamin auren hindatu kenan''
kai ta girgiza''haba jabir,yau ko maqota muke mu da su jamila ai duniya ta zagemu balle iba daya''
''ya kamata kiyi amfani da ilimin da Allah ya huwace miki,ki dinga saka addininki gaba da al'adarki,babu wani abu da ya jaramta min auren hindatu koda kuwa ke na aura matuqar mun riga da mun rabu''
cikin girgiza kai tace
''haba jabir,amma dai ai ana barin halas don kunya''
take yanayin fuskarsa ta sauya
''gwara maryamu ki fito kanki tsaye kice min ba kyason tarayyata da hindatu,gwara ki cemin jabir ba zamu baka hindatu na tafi qarfinka
wace iriyar kunya kike magan akanta ne maryam?
su waye kima wadan da za'aji kunyar?
ko kin manta jin kunyar mara kunya asara ce?
har kin manta da abunda suka miki ne,shin a lokacin da suka aikata din ba'a halicci kunya ba ne ko kiwa akwaita sune basu da ita?''ya qarashe maganar cikin bacin rai,ta bude bakinta zata yi magana ya dakatar da ita da hannunshi kana yace
''dakata maryam,bana buqatar kice komai,tun yanzun na cireki daga batun nan,ban neman kimin komai,zan yiwa kaina yaqin samun hindatu,naki kawai ido addu'a da fatan alkhairi''bai bata damar cewa komai ba ya tashi ya nar gin yabi hanyar da hindati tayi
kimanin minti talatin ta gaza tashi a gun,wani bangaren na zuciyarka na gaya mata bata kgautawa jabir ba,mai son naka ai ya gama maka komai,yayin da wani,bangaren kuma ke ganin dai dai tayi,don rigima ce zata riri ba qarama ba cikin gidan,daya barin uace mata,to sai me?,da ba naki bane jabir din suka aikata abinda suka aikata suka maidashi nasu?to ai dama idan mai guri yazo mai tabarma nade kayarshi yake
shiru shiru hindatun ma bata dawo ba,ta ciro wayarta tayi kiranta,abun mamaki sai taji jabir ne ya daga,kafin tace wani abu ya rigata
''kada ki cikata da fada gamu nan zuwa''hangame baki tayi tana kallon wayar,bata qarasa daskarewa ba sai da ta jangosu sun jero suna tafe suna qyalqyala dariya hannun jabir din riqe da fararen ledoji masu dauke da tambarin sahad store
duban hindatun tayi saivtaga yarinyar ta waske mata tamkar babu wani abu da tayi,kabir me ya katse kallon da take mata ta hanyar ajjiye mata leda daya kusa da ita
''kada ki cinye min gimbiyata ki barta hala,s
duka sauran tuhumarki ki hadiyeta na karbi tutar hindatu''
bata data cewa kallinsu kawai take,haqiqa ta san cewa indai hindatu tayo,nasarar auren jabir bata da sauran matsalar rayuwa,miji na gari kam ta gama samunshi,suka qaraci mata shaqiyancinsu suka miqe don tafiya,nan ma ya kasa ya tsare kan shi zai kaisu,hindatu ta takura tolas suka bishin ya ajjiyau har qofar gida
suna shiga soron gidan maryam tayi saurin janyo hindatu da har tayi gaba
''hindatu ashe baki da tunani?''
ta zumburo baki
''me kuma nayi adda?''
''kin manta waye jabir tsohon mijin yayarki jamila?''
sai ta kwashe da dariya har maryam na toshe mata baki kada ta dauko hankalin mutanen gidan
''nice ta biyu wajen sanin waye jabir bayan ke ta farko,to wai ma anty don autukina yaje aikin hajji sai in kasa zuwa in sauke farali nima saboda kunya?,jabir yayi min adda don na tabbatar yana da nagarta tunda har kika amince da shi a baya''
sai ta kuma yin qasa da murya
''baya ga haka adda wannan wata qatotuwar dama ce garemu ta rama duka cin kashin da aka mana,wallahi sai na dauki fansar duk baqincikin da suka cusa mana''
ta fuskanci da gaske hindatun take
''Allah ya taimaka''ta fada kana ta shigeta cikin zuciyarta tana musu addu'ar tabbatar lamarin cikin nasara da farinciki
🎄🌲🎄🌲🎄
Batasan ya akayi ba itadai taji an kawo kudin hindatun har da kudin sa rana jimillar naira dubu dubu dari uku dubu dari kudin aure dubu dari biyu kuma kudin sa rana,hakan ya sanya baba yace ta shaidawa abdur rahim ya turo a saka rana,su din ma kudin sa ranar suka bada naira dubu dari biyar,kudin sun bawa maryam din mamaki,murmushi abdur rahim din yayo yace
''ko nawa na bada kudin aurenki yayi kadan maryam,kinfi qarfin haka,me din mai tsada ce''murmishi kawai tayi tana sake ganin qima da darajar son da yake mata
duk abin nan da ake jama'ar gidan basu da masaniya,kusan duk ranar da za'azo din basu gidan suna yawon asara yawon bidar asiri,asara goma da ashirin babu kudinsu ba imani
*mrs muhammad ce*👑
📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[9/17, 12:54 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*
▶3⃣5⃣
👇🏾 *wannan page naku ne*
👉🏾 *_haske writers asso_*
👉🏾 *huguma conversation and novels rooms_*
👇🏾 *da kuma*
👉🏾 *Zauren biebie isah*
*Allah ya bar qauna*👍🏽❤🤘🏽
*_Ankarbo daga imam bukhari r.a,manzan Allah s.a.w yace_*
*_(qarami ya yiwa babba sallama,matafiyi ya yiwa wanda ya taras,jama'a 'yan kadan su za suyi yawa masu yawa)_*
*_a wani hadisin da imamu muslim ya rawaito daga annabin rahama s a w yace(wanda a zuciyarshi akwai girman kai daidai da qwayar zarra bazai shiga aljanna ba)_*
*Allah kayi mana tsari kada ka haramta mana aljannarka,ka hanamu dukkan wata baiwa ko ni'ima taka da zata yi sanadin zamowa masu girman kai*
Fadar irin farincikin da mama da iyalinta ke ciki ma bata baki ne,sunyi amanna cewa wannan ce shekarar farincikinsu,addu'o'in da suka dade suna qwanqwasawa qofa yau kam an bude musu dukkan qofofin,duk wani tsohuwar ajiya ta mama data jibanci kadara ta daga ta saida,ta yiwa bikin shiri matuqa da gaske,ga dangi masu zuciyar yi mata da Allah ya hadata da su
takanas suka ziyarci gaya ta saida manyan gonakinta na gado guda biyu,ba qaramin kudi ta samu da su ba kasancewar yadda a yanzu kowa ya koma noma gonakin daraja suke,tuni ta fidda kudin kayan gado kayan kitchen da sauran tarkace na hindatu,maryam kam dama da yan kudadenta da take sa ka ran zasu isheta sayan kayan gado,ga mamakinsu saiga kudade baban su ya damqa masu a boye yace sukaje su zabi kayan gadon da suke so,shi din ma gonakinsa biyu ya siyar dake gayan,dama bashi yake amfana da su ba yan uwansa ne,cikin rufin aairi, Allah sai gasu sun tashi da kayan gado na kere sa'a masu kyau tsada da aminci
bata sake shiga farinciki matsananci ba sai da mami ta damqa mata passport dauke da visa ta qasashe biyu saudiyya da china
''maryam,inason inje siyayyar lefen abdallah ne,sannan ke kanki ina son in miki siyayya irin wadda uwa take wa diyarta,naso 'ya mace amma Allah bai bani ba,to a yanzun kuma sai Allah ya bani ke,naso ace lokacin bikinki da abdallah bai hade ba da ina mai tabbatar miki anan gidan zaki zauna har akammala taro a miqa ki gidanki,saidai duk da haka bikin magaji ai bazai hana na magajiya ba,zamu fara zuwa china muyi siyayya sanan mu dawo saudiyya muyi umara,kuyi addu'a kowannanku ya roqawa kanshi alkhairi kan sabuwar rayuwar da zaya shiga,ni da ke ne da abdallah''
rasa bakin da zata gode mata tayi saidai ta tsinci kanta cikin zubda qwallar farinciki,tabbas uwa ce,mami uwa ce wadda tasan ciwo da darajar 'ya'ya,babu shakka ko ita ta tsugunna ta haifeta iyakacina binda zata mata kenan,haduwars ta tabbatar daga Allah yake,bata manta yadda taqi taji batason aikin gidan mamin ashe alkhairi ne Allah yake nufinta da shi,gaskiya ne maganar Allah haka take da yake cewa cikin alqur'a ninshi mai girma
(zaku iya qin abu kuma alkhairi ne agareku,sannan zaku iya son abu kuma sharri ne a gareku,Allah shine ya sani ku baku sani ba)
mama kam rasa mai zata fada tayi,babu shakka duk yadda kaga Allah yayi da rayuwarka baiyi don zalunci a gareka ba,yayi ne saboda shi ne mafi sani ga abinda ya dace ga bawansa
raliya har da hawayen farinciki
''damuwarki tazo qarshe diyana,Allah ya yanke miki,maqiya kuma sai su kashe kansu don baqinciki''abinda ta dinga fadi kenan fuskarta qunshe da murmushi
hindatu kam buri ya cika,don tace ko iya haka Allah ya barsu sun gode masa,Allah ya nuna isa da buwayarshi,itama tata visa din umarar na nan jabir ya tanadar mata bayan sun angwance da wata daya
🍂🍃🍂🍃🍂🍃
qarfe biyu na azahar jirgin ethopian airline zai debe su zuwa ethopia inda anan zasu fara yada zango kafin su isa qasar sin,cikin masu rakiyar tasu harda jabir da hindatunshi,abdulrahim sai zubaida,raliya da yaronta fadil,
ranan ne abdulrahim suka fara haduwa da jabir,tuni ya dade da sanin waye jabir din da kuma matsayin da yake kai a yanzu a gun maryam din,don haka gaisuwar mutunci sukayi tamkar sun jima da sanin juna,kusan dukkansu sama sama suka gaisa da abdallah yaja gefe yana faman cin magani tamkar wanda aka yiwa dolen tafiyar,ita kuwa zubaidan bata damu da ta qyaleshi ba ganin yadda yake faman fuskewa ba tana liqe da shi tana zuba rawar kai yayin da shi kuma yayi mata dif ko kanzil yaqi tanka mata da ita cikin hirarta
cike da bege da qaunar juna suka yi sallama lokacin da aka soma neman matafiyan
maryam ce qarshe saboda tsayawan da sukayi da abdulrahim
''abun mamaki banga irin sallmar nan da masoua kanyi ba yayin rabuwa da juna abdulrahim meke faruwa?''
murmushi ya saki yace
''me kika gani maryam?,kina tuhumata ne kan rashin damuwa da tafiyar da zakigi ki barni?''
''dole in tuhumeka mana abdulrahim,ba sau daya ba basau biyu nasha kamaka da laifin qin sakin jikinka idan muna tare matuqar abdallah na agun,wai shin tsoronshi kake ne ko meye?,aure fa zamuyi nan da sati uku kowa yasan da zamanka,ko wata barazana yake maka aboue wadda mu bamu san da ita ba''
sai taga ya tuntsire da dariyar har yana dan duqawa
''babu tsoro balle barazana tsakanina da shi,ke kika dai fuskanci hakan,hasalima abinda kike zaton ba haka bane,Allah shine mafi sani ga abinda yake cikin zukatan bayinshi,Allah ya kaimun ke lpy ya dawo min da me lpy,ki kula min da kanki matuqa,ki yiwa kanki addu'a mai yawa maryam,kada ki kashe wayarki da wuri zan kiraki kafin ku tashi''sallamar da sukayi kenan
koda ta shiga gurin tayi tsammanin ya dade da wucewa tunda sun rigata shigowa da wajen minti goma sha biyar,sai gashi tana gaba gun screening shi kuma yana tsaye a bayanta,gaba daya sai ta takura,tana ji a jikinta tamkar yana qare mata kallo ne kawai,gashi doguwar riga ta saka sai rolling da tayi wanda iyakacinsa kafada,hill shoes ta saka wanda sanadiyyar hakan yasa ta kusa kama abdallan a tsawon
ko cikin jirgi ma number din sit din nasu daga shi sai ita,mami na a sit din bayansu,tamkar ta zura a guje ta bar sit din haka ta dinga ji,tunda take basu taba zaman kusanci na tsawon lokacin da zasuyi yanzu ba,ta njtsu tsaf tamkar ace ket!ta zura aguje
wayarta tayi tsuwwa ta duba saiga kiran abdur rahim,tamkar ance mata ta kalli gefanshi sai ta tsinci idanunshi a kanta,wani irin kallo yake mata da ta kasa fassara ma'anarsa,shi ba harara ba ba kuma normal kallo ba,ya kafeta da mayun idanunshi masu cike da kwarjini,sai ta tainci kanta da kasa dagawa har wayar ta tsinke,gani tayi ya ciro tashi wayar ya fara danne danne hakan ne yasa tayi saurin jan tata wayar ta soma dubutawa abdulrahim din saqon karta kwana kan bazata iya amsa waya ba a yanzun cikin yi masa sallama da bankwana,saida kamfanin layin sadarwa suka tabbatar mata da yake sanna ta sauke idanunta daga kan wayar,ta sauke siririyar ajiyar zuciya daidai kokacin da taji shi kuma anasan bangaren yaja tsaki qasa qasa ya furta
''fool''
dayar wayarshi data fara ringin taga ya janyo ya zura earpiece
''hello baby......muna jirgi yanzu zamu tashi.....ok...ok bye take care,i will missed you too''ya kashe wayar gaba daya ya ajjiyeta guri daya
''janye cat eyes dinkin nan daga kaina,yanzun zansa a canza miki gurin zama indai kika ci gaba kallona,bansin kallo kin gane?''
ji tayi kanar ta hukunta idon nata da har yayi kuskuren kallonshi
''me zan kalla wanda babu shi jikin abdul dina?''ta fada cikin dakiya kamar ma bada shi take ba,kanta na kallon wani sashin
''there ar many,ko skin dina kawai batayi kama data baqin mijinki ba mai zubin ta 'yan garuwa,after all ma kinsan da hakan kike qarewa mijin wata kallo,kinsan kina so tun farko bakiyi magana a taimakeki ko a qwarqwara kixo,yanzun kam its too late qwalelanki''
maganan ta mata baqi da yawa,tayi qoqarin control din bacin ranta don ta samu maida masa amsa yadda ya kamata
''shi dan garuwan ai Allah ne ya halicceshi......''
''eh mana,da ke kika halicceshi''ya katsi numfashinta ba tare data idar ba
da sauri ta dora don kada yaci da rabonta ba tare data samu ta rama ba
''ba kyau ko kudi nakeso ba mutunci nake bida da daraja,kai din kuma ai inama kallon mace ne 'yar uwata kaga babu yadda za'ayi ince inason jinsina,abdul dina yafimin kowanne namiji cikin jinsin maza,ko a mai min shara bazan iya daukarka ba da dai mai wankin toile......''
''qarya kike wlh ya fada cikin fushi da dan daga sautinshi,ita kanta ta dan tsorata don qasa qasa suke maganar lokaci daya ya daga muryarshi,idanunshi data kalla kawai suka sake sata a zulumi,sai a lokacin ta tuna waye fa,abdallah ne,ta runtse ido tana jin zafin matsar da ya yiwa yatsunta kamar zai karya su ya kuma qi saki
''meye ne abdallah''mami ta fada tana dan leqo da kanta
''babu komai''yace
''ko baka jin dadi ne?''
mami ta tambayeshi cikin yar damuwa jin sautin muryarshi ya canza lokaci guda
''am fyn''ya fada a taqaice
''ok,to ku kashe wayoyinku''tace mishi bayan ta koma ta zauna daidai ksn sit dinta
sai da ya fara hucewa da kanshi sannan ya sakar mata hannu,zuwa lokacin tuni ta fara share qwalla don azaba,jin hannun take kamar ba'a jikinta ba sanadiyyar taruwar jinin da taji ya mata,tuni har jirgin ya daidata a sama,da qyar ta janye hannun tana yarfar da shi tare da fatan jin ya sake daga daurewa da zugin da yaje mata,ko da aka tamvayesu abinda zasu ci cikin jirgin kasa ma mafa na tayi,tanaji yasa aka kawo baqin coffe aka ajjiye musu,itakam ko kallo ma bai isheta ba
a hankali suke sauka daga jirgin daya bayan daya,gaba daya qafafunta sun mata tsami ga hannunta na damunta,itace a gaba abdallah a bayanta mami a bayanshi,rashin qwarin jiki ya sanya qafarta hardewa ta tafi luu zara gangara daga matattakalar
a tsorace mami tace
''subhanallahi,abdallah tarota''
tuni ya tallafota ta dawo jikinsa
''kin zame mana kaya wallahi,dama so kike a rungumeki din an miki hankalinki ya kwanta,amma net tine kika qara sai nayi maganinki''ya fadi yana tureta daga jikinsa
''sannu'' mami ke ta mata har suka sauka,duk da yanayin rashin dadin jikinta baihanata ganin qawatuwar garin ba
gida ne mai hawa ashirin cikin unguwar,gini ne qawatacce mai kyawu matuqa da gaske,cikin hawa na takwas nasu gidan yake,gida ne mallakinsu abdallan da suka siya da kudinsu,da fari falone madaidaici sai corridor daga damanka wanda idan ka shiga zaka tadda kitchen wani corridor dinne yake kallan kitchen din shi kuma dakunan bacci ne guda uku kowanne dactoilet cikinsa,sai valcony 'yar qarana mai kyau daga fuskar kowanne hawa na gidan wanda ta nan kana iya gano ainihin cikin unguwar da layinku da kuke an qawatashi da kyawawan kujeru guda hudu da yan shuke shuke
daki daidai kowa ya dauka,tunda ta shiga dakin tayi wanka tayi akwala tayi sallah ta nade a gado sai bacci,tun la'asar dinsu sai da aka kusa idar da sallar magariba sannan mami ta tadata tayi sallah,tuni sunyi order din abinci an kawo musu har gida don haka shi kowa yaci,ba damar girki an dai siyo dan abinda zasu buqata kafin su gama kwanakinsu kamar ruwan roba qwai suger da sauran abinda zasu iya buqata,tana shirin basu guri don taji sun fara lissafe lissafen siyayyarsu mami ta tsaidata.
''maryam gaya min dame dame kike so,don gobe insha Allahu zamu fita bana son mu wuce kwana hudu,muje muyi kwana goma ko sha biyu a makka mu wuce gida lokaci na qurewa''
a kunyace tace
''bani da zabi mami,duk abinda kika zabarmin yayi''
bata ce mata komai ba ta miqa mata takarda da biro tace taje tayi mata list din duka abinda takeso nan da goma ko sha daya tazo ta kawo mata,hannu biyu tasa ta amsa ta koma daki
sai ta rasa ma me zata rubuta,bata da layin qasar balle ta kiraliya ko hindatu suyi shawara,wani tunani tayi ta koma falon,nan ta samesu yadda ta barsu,saidai wannna karo sunyi kace kace cikin takardu,rubutu kawai kowannansu ya duqufa yana yi
''hmmm,gaskiya ne,ai dole ayi bikin da babu kamarsa,da daya tilo''maryam tace cikin zuciyarta
''ya akayi maryama,har kin gama?''mami ta tambayeta bayan ta dago kanta ta maida kan rubutun da takeyi
''ummm...mami cewa nayi don Allah ko zaki aramin wayarki in dan kira gida?''
''ayya nima kuwa bani da layin qasar nan duk sanda muka zo sabo nake siya wancan faduwa yake,sai gobe idan Allah ya kaimu zan siyi wani''
har ta juya zata koma dakin mamin ta sake kiranta
''maryama zo....abdallah naga kai har ka hada naka layin ara mata tayi wayan''
yayi wani kicin kicin da rai ya saci idon mamin ya harareta kana ya ciro wayar daga aljihun trouser dinashi ya miqo mata
ta miqo hannu zata karba
''idan kinsan wannna baqin basamuden zaki kira da wayata ma gwara kiyi tafiyarki ki barmun abata,don wlh kika sake kika cinyemin credit sai na zara asalary dinki,don shi na fuskanci baya da arziqin da zai iya biya na''ya fada qasa qasa yana kallon paper din hannunshi da yayi rubutu,sai ka rantse ba da ita yake ba,murguda mishi baki tayi bayan itama ta harareshi kana ta karba duk da cewa bai ganinta,shi baisan yadda ta tsaneshi bane,idan banda lalra babu abinda zai hadata da wayarshi ma.
Ta loda numbers din raliyan ta kirata,sosai taji dadin shawarar data samu na abinda ya dace ta siya dim,ta kira hindatu ta zabi abinda itama takeso sai ta rage nata ta hada da na hindatun,kasa jurewa tayi don haka ta saka numbers din abdulrahim ta kirashi,sun taba hira sanna ta kashe,tana shirin ajjiyewa wani kiran ya shigo
*my suger* ta gani a rubuce,ta zubawa numbers din ido tana kallo,sai ta tabe baki sanna tayi rejecting.