Complete Hausa Novels

Abadan Daiman Complete Hausa Novel

Reading file: Abadan_Daiman_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 3 of 4

ci gaba akayi da kira ita kam bazqta taahi ba sai ta gama rubuta duka abinda zata rubuta din ta fita gaba daya,kiran yaci gaba da shigowa ba qaqqautawa,tsaki ta ja ta janyo wayar ta daga kana ta kara akunnenta
''kada a cika mana kunne mai wayar bayi kusa''dum akayi kana taji ance
''ok''can qasa qasa

wayarta mata kyau ta dan juyata a hannunta,garin cire lock ta taba gurin pictures,daya bayan daya ta dinga bin folders din tana kalla,abinda ya daure mata kai ganin hounan abdallah da yammata kala kala,tana kalla tana tabe baki,wannnan guy din dan garari ne,waishin ma a ina yake haduwa da yammata haka zuqa zuqa yadda yake nuna he was always busy,ta shafe aqalla awa guda har taso shagala,duka hotunan babu na yarwa ya iya wanka kam babu ja a wannna tana iya bashi maki hundred parcent cif

larm din da agogon dakin yayi na qarfe goman dare ya tunasar da ita,garin sauro ta manta bata sauka daga folder din pics din ba ta kashi takardar ta fita falon,shi kadaine yanzun sai gun da mamin ta zauna,da alama yanzu ta tashi kuma ba dadewa zata yi ba,jin fitowarta bai sanyaahi daga kanshi ba,wayar ta miqa masa kana cikin cool voice dinta tace
''na gode''ya amshi wayar baiko dubeta ba,sai da ya bude screen din yaga inda ta shiga sanna yace
''awa ukun da kika kwashe wayar na gurinki hoton mitum daya dama kika tsaya kalla?''ya tambayeta idonsa cikin nata

ta dan zaro ido tana duban wayar,sai lokacin takula hotonshi ne a kai,yayi kyau cikin shigar suit yana murmushi,da alama ba'a qasar aka dauki hoton ba,bata kai ga cewa komai ba mami ta shigo falon
''kin gama maryamu''
''eh mami''ta fada tana miqa mata takardar,ta karba tana dubawa kuma tana qoqarin zama kan kujerar
''an gaisheki maryam,duk tsawon awoyin man iya ka kadai wadan nan abubuwan kika rubuta?,sunyi kadan''tace tana sake qarewa takardar kallo tana girgiza kai''
kararki tayi yawa dama nasan ba iyawa zakiyi ba,jeki kawai,zanyi amfani da wannan din da kuma wadanda na rubuta''
tana murmushi ta juya ya shige dakin ta barsu nan suna ci gaba da lissafe lissafensu

🌲🎄🌲🎄🌲🎄

ta riga su tashi kamar yadda ta rigasu kwanciya su sai yanzu suke nasu baccin gajiyar,kafin su farka harta kammala breakfast taci nata,sai tayi zaune a parlour tana kallo abinta cikin riga da wando na pakistan orange da baqi,ya mata kyau kuwa sosai

takun da taji shi ya ja hankallinta abdallah ne ke fitowa sanye da riga armless da wando three quater,fuskar an ahade kirtif ya qarasa gaban freezer ha ciro fresh milk da ta hada sanyi ya balle robar ya soma sha,baifi rabi ba ya ajiye saman freezer din ya nufi kitchen sai gashi da plate da cup,mamaki tayi yau da kanshi ya zuba baiko nemi ta zuba masa ba lallai da alamu tunwa ce ta koroshi ma,zaya zo yana wani ciccin magani kamar wanda wani ya zageshi

can gefe guda ya samu ya zauna kan ya fara break din,duk sai taji kamar ya cika falon,zaman ya daina mata dadi,neman dalilin da zaisa ta tabar falon kawai takeyi,don bata buqatar ko qanqani zama inuwa daya ya dinga hadata da shi ko naminti dayane idan ba lalura ba
''ke''taji yace sai tayi banza da shi kamar bata jishi ba,ta fuskanci wani jan bala'i gake nema da ita tunda suka taho,ita kuwa kodan daraja da kunyar mami bazata bari su raba abun fada ba

''bakiji kashein da na miki jiya ba kenan sai da kika kira wani da phone dina ko,to ki gayawa rubabben saurayinkin kada ya kuma kiran numberta don ba sa'anshi bane ni''ya miqe yana dauke cup din tea tare da bari plate din a gun,bai kai ga shiga corridor din ba sukayi kacibus da mami tana fitowa da hijabi jikinta qafarta sanye da silifas
''mami ina zaki?''
''zan sauka ne floor na qasa mu gaisa da maman farida,jiya kaga ban samu na ahiga ba saboda gajiya''
''pls mami ki taimakeni kada ki cewa zeenah tare muke,wallahi kika bari ta sani tofa na banu kafin mubar qasar nan nacinta sai yasa na rame,ango kuma da rama ami ai babu kanta kada ta koro miki ni tace na mata rama da yawa''
dariya ma ya bata gani irin marairaicewar da yayi
''ka maida ni kakarka Allah abdallah,kakannin naka ma ka shafa musu lpy a kaina abun yake qarewa,ni dai Allah ya kusa rabani da alaqaqai gwara kayi auren ko kunnuwa da idanuna zasu huta da ganin yammata,ka shirya kafin na dawo mu fita da wuri so nake a yau a gama siyayyar baki daya''

tayi gaba suka gaisa da maryam ta fita,tayi zaton ya shige dakinsa tana zuwa sukayi kacibus bakib qofa,tana mura handle din dakin da qoqarin shigewa ciki taji yace
''kika sake mami ta miki tayin fita kika ce zaki bimu wata siyayya sai na qarasa targaden da na miki jiya''wuf ta shig dakin ta saka maqulli tadan daga murya
''to baaba na'' sanna taja tsaki,gado ta fada cikin jin haushinsa,dama ita bata sha'awar zuwan ma sam,dadai ba da si din zasu je ba shine,amma indai da shine zamanta a gida ya fiye mata dadi,qofar ya tsaya yana kallo,dan qaramin murmushi irin na gefan baki ya subuce masa ya cije lebansa na qasa kadan kana ya tura qofar nashi dakin ya shige ya cire kayan jikinshi ya fada wanka

*Mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
[9/17, 12:54 PM] 80k: *ABADAN*36
*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*
*_home of expert and perfect writers_*
*_annabi muhammad s a w ya tambayi sahabbansa_*
*_''shin ko kunsan waye matsiyaci?''_*
*_sai sahabbai suka ce''matsiyaci shine wanda bashi sa dirhami ko dirane''ma'ana bashi da cin yau bare na gobe_*
*_sai annabi yace musu''matsiyaci shine wanda zaizo ranar qiyama,yayi azumi yayi sallah yayi sadaka yayi zakka yayi hajji saidai kuma ya cuci wancan ya zalunci wancan ya zagi wancan yaci dukiyar wancan,sai Allah ya dinga dibanadan wadancan ayyuka na alkhairin da yayi ya dinga rabawa yana biyan wadanda ya zaluntar har sai ya tashi bashi da komai cikin aikin ladansa,ga ragowar wadanda ya zalunta ba'a gama biyansu ba,sai Allah ya dinga diban zunubinsu yana bashi da haka da haka har sai ya tashi bashi da komai face kayan zunubi sai Allah ya jefa shi a wuta''_*
*ya ubangiji kayi mana tsari don isarka*
Har mami ta dawo daga gidan maman farida ta shirya bai gama nashi shirin ba,sai da ta leqa ta masa magana,ta leqa dakin maryam ta taddatakwance
''ya kike a kwance mu da zamu fita?''
sai ta miqe zaune
''bana jin dadi sosai mami''
''ashsha,Allah ya sawwaqe,ki kwanta ki huta qila gajiyar tafiyar ce bata sake ki ba,Allah ya qara sauqi ma fita gobe ba damuwa,ungo wannan ajjiye min''ta miqa mata baqar leda,kayan bacci ne masu azabar kyau guda hudu
''maman farida ce ta bani su,nikam ina ni ina saka wadan nan qannnan tsirarar ai sai ku''
kunya ce ta kama maryam ta karbi kayan fana sunne kai,sanann ta tashi tayiwa mamin rakiya zuwa falo,sgi din ma ya fito sanye da qananun kaya,t shirt ce mai gajeran hannu baqa wanda a gaban rigar akayi rubutu gwara gwara kamara haka *we all have story to tell*,sai baqin trouser da ya saka,sun masa kyau aoaai kasancewarsa fari sai suka haskashi,qofan ta maida ta rufe ami tace sai sun dawo
kusan wuni sukayi ranar a waje har maryam ta qosa da zaman kadaitakar,duk da cewa ko a gida ma idan duka suka fice kusan haka ne amma acan wani okaci takan fice gidan baaba uwani susha hirarsu,da zaman shirun ya isheta sai ta fito valcony din gaban floor dinsu tayi zamanta tana qarewa unguwar tasu kallo
basu suka dawo gida ba sai da suka kammala siyayyar lefe kaf baki daya,hatta da akwatunan basu bari ba,daga can kuwa gurin da zasu dora kayansu a jirgi suka zarce basu ko dawo gidan ba,sun zabi zuwan kayan ta iska wato ta jirgin sama don shine mafi sauri,tunda kafin su koma za'a kai kayan suna sa ran kuma idan ta jirgin saman ne bazaya wuce kwana hudu zuwa biyar ba yaje sabanin ta jirgin ruwa da,zaya dauki watanni
sai da mami ta tabbatar komai ya kammala sannan ta karbi wayar abdallah ta kira qanwarta hajiya ruqayya ta mata bayanin kaya sun taho,tayi qoqari don Allah da sunzo a shirya komai yadda ya kamata aje a kai lokaci yana qurewa
a mugun gajiye suka dawo don haka suna dawowa wanka sallah da cin abinci kawai sukayi,cikin qanqanin lokaci gidan ya sake zamowa shiru saboda yau babu zaman hirar daki kowa ya shiga ya kwanta
Washegari dukkansu su ukun suka fita kai tsaye kamfanin sarrafa kayan gado suka shiga,katafaren kamfani ne da suka qware wajen qera da sarrafa kayan daki da suka hada da gadaje sif madubi zuwaafiyayyun kujeru iri iri,inda suke ajjiyesun bayan sun gama sarafa su aka shiga da su,mami ta bawa maruam dama ta zabi irin wanda takeao,duk sai ta duburbuce ta kasa zabar kowanne daga ciki
sun kusa shafe awa guda saboda girman gun ba tare sa ta iya zabar koda kala daya ba daga ciki
abdallah ne ya ja tsaki
''yarinyar nan fa wahal da mu kawai take yi mqmi,kawai ki fidda mata wanda kika ga ke ya miki''
''meye naka a ciki dakina ko naka ko kuma dakinta ita zata zabi abinta''
''Allah ya baku haquri''ya fadi yana kewayesu ya barsu a gun ya nufi inda ma'aikatan ke zaune
ma'aikata biyu da leburorin gurin guda biyar suka qaraso inda suke tsaye ita da mamin,daya daa cikin su yace da mami cikin harshen nasara
''madam,ku zaku yi signing a nan za'a fitar da kayan,motocin kamfaninmu zasu kaimuku har inda kuke buqata suna wajen kamfanin suna jira''ya fada yana miqa mata wata yar matsakaiciyar takarda,ta amsa ta duba kana ta kalleshi cikin arahen nasaran itama ta maida masa
''ai bamu kai ga zabar wadanda mukeso din ba ai''
''yallabai ya riga ya zaba har ma ya biya kudaden''yayi maganar yana nuna wasu tsadaddu kuma tsararrun kayan gado dake gefan hannun damansu,kala biyu ne kujeru sif gado da madubi curtains,dressing chair da bedside sai abun maqale jakankuna dukkan kalolinsu light and dark purple ne sai wasu set din kamar haka amma su blue black ne da light blue
ba qaramin burge mami kalolin sukayi ba har ta tsaya kallinsu saboda kyawun da sukayi mata,abdallah ya iya zabe kamar mace,ta daga kai sai ta hangoshi can sama wata kujera mai siffar kwano mai azabar tsawo a zaune hannunshi riqe da cup din glass yana shan lemo,kashe mata ido yayi ya langwabar da kai alamun bada haquri tare da nuna mata agogo lokaci na tafiya kenan kana ya mata alama da hannu na kayan sunyi?,dariya ma ya bata sai ta daga masa girarta alamar eh,hannunshi ya sake dagawa ya mata alamar i love u,murmushi ta kuma yi ta girgiza kai kana ta samu gefe ta zauna tana fara signing din paper din zuciyarta cike da tunanin mahaifin abdallah,wani lokaci idan hayi wani abun sai taga ya koma mata alh abdulkareem sak,barewa batayi gusu danta ya rarrafa ba ta fada cikin zuciyarta
duka cikin kamfanin suka nufi bangaren kayan kitchen anan kam dama kawai ta basu nasu hada mata duk wani abu da yake,da amfani cikin kitchen,cikin lokaci qanqani sai gasu da,kaya bila adadin sukayi total ta biya,yawan kudin da maryam taga mamin ta kashe mata shi ya sake raunata mata zuciya sanyata kuka,kuka sosai ta saka har ta kasa magana ma,hatta da abdallahn dan garari tsayawa yayi yana kallonta,karo na farko da ta bashi tausayi,jawota mamin tayi jikinta sai ta ora kanta a kafadarta,hawaye naci gaba da zuba,itama mamin kasa magna tayi sai bayan maryam din da take dan bubbugawa a hankali cikin sigar lallashi,har cikin zuciyarta tanq jin ciwon rabuwa da maryam din,idan banda aure batq jin akwai abinda zata lamunce ya tsinke zamansu mai dadi da suka fara
washe gari ma baccinsu suka sha sai yamma sanan mamin tace su shirya su fita maryam ta danga gari,kada tazo ta kuma koma bata san ya garin yake ba
babu musu ta shirya cikin doguwar riga dark blue da adon golden din duwatsu saqar india ce,ta haskata qwarai,saidai kasala da rashin dadin zuciya da take ji ya rage walwalarta qwarai,wanna fargabar ta aure sai yqnzu taji ta fara shigarta daga lokacin da tayi tozali da kayan dakin aurenta,Allah ya sani ba zata yiwa Allah butulci ba amma tilas amatsayinta na budurwa taji fargabar aure kamar yadda kusan kowacce soya mace take ji a auren farinta a rayuwa
da qafa suka dinga tattakin suna taba hira kadan kadan cikin sassanyar la'asar din,yanayin garin ami kyau ne,babu ruwan wani da harkar wani,kusan hirar dake gudana jefi jefi tsakanin mami ne da abdallah,bata ankara ba sai da taji shirun na maryam yayi yawa,a hankali ta juyo ta dubi maryama dake hannun hagunta
''maryam''
da sauri ta juyo tamkar mutumin dake cikin tunani aka katse masa,nazarinta tayi na yan sakanni kafin tace
''lafiya kike kuwa,daga jiya zuwa yau naga duka kin canza,ko bakijin dadi ne?''kai kawai ta iya girgizawa tayi qas da kan nata tana qoqarin mayar da qwallar data cika mata idanu,hannunta mamin ta kama ta jata kan kujerar dake girke daura da su yayin da abdallah yayi tsaye hannayenshi harde a qirjinsa yana kallonsu,bai iya jin me suke fada amma yana iya ganin me ke gudana,motsawar bakin mami da gyada kan maryam,a hankali ta dinga share hawayen idanunta qarshe ta buge da murmushi kana suka taso suka iske shi
mami ta dubeshi ya wani hade rai yayi kitchen kitchen,ta dan ranqwashi qeyarsa
''kai kuma da wa mai aljanun sauyin yanayi''dariya taso qwacewa maryam har sautinta ya dan fita,tayi gaggawar gumtse bakinta ganin yadda ya zuba mata harara cikin shan mur
''nifa mami gaskiya ina da kishi,don me za'a tafi ni a barni ni kadai a tsaye kamar maye bayan da can ba haka kike min ba,kawai don an samu wasu''
''maganarmu ce ra mata bai kuma cancan ci kaji ba ehe,ciwon 'ya mace na 'ya mace ne,sannan wasun ma da ka kafawa qahon zuqa suka tsole maka idanu sun kusa tafiya su baka sararin gurin kaga qarewarta sai ka koma shan nono kace ma ko yaye ka banyi ba''sosai mami ta bashi dariya har sai da ya dara yana fadin
''ni na isa,amma dai nasan tattalin da ake min irin na da zai dawo,kinga na zama dab lelen murum biyu,ga na my dear ga naki,thank god''
Da daddare suka hada dukkan wasu kayayyakinsu washegari jirgi ya debesu sai qasa mai tsarki,washegarin ranar da suka je suka sauke faralin ibadarsu ta umara,hakan bai sanyasu shiga wasu sabgogin ba sai da suka kwashe kwana biyar basu rabo da masallaci wanka ko cin abinci ke fiddasu,har gwara mami wani lokacin ta dan koma ta runtsa,maryam kuwa bata bawa kanta wannan hutun ba,tun mami na mata mita kan ta huta harta gaji ta barta,cikin kwana biyar din nan sai da tayi saukar alqur'ani biyu,dukkan alkhairi babu wanda bata roqawa mami mamanta raliya hindatu da ita kanta ba
kwana uku sukayi a madina ziyara,daga nan suka hada ya nasu ya nasu,mami tace itafa sai ta sauka a sudan tukun,cikin alamun tuburewa yace
''me zamuyi kuma a sudan mami,dear fa ta matsanta tana da buqatar gani na,i have alort to do mami a gida,inaga tafiya zanyi nikam sai kin taho''
''wa salaam wa kitabi,nima na huta da qorafi kama gabanka Allah ya miyaye hanya sai mun taho''anan suka raba jaha da shi,maryam batasan me zasuyi a sudan ba sai da suka je,unguwar tamkar tana cikin qasarta haka ta gani,sai dai 'yan bambance banbance da ba'a rasa ba na suturu abinci da al'adu.
kallo daya zaka yiwa matar ka tabbatar da 'yar sudance gabanta da bayanta,saidai mamakin da maryam tayi yadda hausa radam ta kama bakinta yanayin karyewar hatshen bw kawai zai nuba maka ba yarenta bane ara tayi ta yafa,ba abun mamaki bane jin yaren gausa bisa harsukan wasu al'umma ko qabilun da ba ahalin hausa ba,saboda yaren hausa yare ne sha kundum da ya fantsama lungu da saqo na fadin duniya,kusan a yanzu shine yare na biyu ko na uku da akafi amfani da shi,babu inda zaka tsoma qafarka a duniya ka rasa wanda ya iya ko yakejin yaren
gida ne babba mai bangare biyu bangare daya na matar ne daya bangaren kuwa harkar sana'arta kawai take gudanarwa,gyaran jiki gyaran gashi lalle ne kayan gyaran jikin na mata turaruka na ruwa dana ice da humra na tsuguno harda na wanka,kai hatta da kitso idan kana da buqata akwai mai yi maka,yadda maryam taji suna hira da matar tana tambayar mamin bayan saduwa ya fahimtar da ita lallai sun san juna dama can da mami,tunda har taji tana tambayar matar wata najwa tace taje daarfur sai gobe zata dawo,hajiya laila ita kewa mami irin wadan nan gyararrki zamanin alh abdulkareem mai nasara nada rai,gayu kam da gyaran kai mami ta yishi lokacin da mijin nata ke raye shi yasa ta zama ta gaban goshinsa,duk da a yanzun ma bata saki gayunta ba saidai ta daina wasu abubuwan tunda babu mijin
cikin kwana uku matar ta fara tsuma maryam,gyara take mata bana wasa ba tunda ta san haj bintu akwai sakin hannu idan harka ta hadaku,wani irin daddadan qamshi ta zaunar a jikinta wanda ko zama tayi a gu sai qamshin ya nasheka,farar fatarta ta canza yanayi farin nata ya saje armashi kyau gami da daukan hankali,sati guda ana mata gyararrkun taki wanne b'angare kafin suyo gida nijeria bayan haj laila ta hada muta wasu hade haden da zata ci gaba da amfani da su koda bayan bikin ne
bayan sun koma boyonta mami ta dinga yi,tuni ta daina komai a cewarta bataso nan da kwanakin da suka rage biki wani abu na gyaran da akayi mata ya samu naqasu,baaba uwani ita ta goyi bayan mami tayi uwa tayi makarbiya take komai
sunyi waya da mama da hindatu,mama cewa tayi sai tazo godiya don sam bai canci ta yiwa mami godiya iya ta waya kadai ba,amma da maryam ta sanar da mamin sai tace sam wallahi kada tazo,idan kuwa tazo din to ta nuna ba ita ta haifi,maryam ba,karamci da mutuncin mamin sunyi yawa har suka sa mama ta rasa ma me zata ce ko ta saka mata da shi?,hindatu amarya kam babu zama,ita da qawayenta ke gudanar da komai,don hatta da rabon kati su suka dinga yi,saboda mami ta riqe maryam tace babu yawon rabon iv da zata ta bata jikinta,ganin komai take tamkar a mafarki,wai tau ita maryam ce ake kira da sunan *amarya*,lallai babu wani abu da yake tabbatace sai mulkin ubangiji
bata fidda ran ganin irin wanan lokacin ba saidai koda wasa bata taba kawoshi nan kusa ba haka,dukka kayan da zata saka raliya ta fidda takai dinki,duk wata sabga da ya zamto ita zatayi raliya ta tsaya kan komai ita keyi kan jiki kan qarfi kamar a itace maryam din,kyakkyawan amincin da aka gina shi bisa turbar gaskiya da amana kenan,yakan iya kai ku zama qasan inuwar al'arshin ubangiji ranar da babu wata inuwa sai taahi
Biki ya rage saura kwana uku da daddare tana gurin baba uwani ta kai mata wasu kaya da take son bata ita da yan jikokinta kiran hindatu ya shigo wayarta
''kinyi tsada adda maryam,mami ta tsaya miki''inji hindatu cikin salon tsokana
''kema mama ta tsaya miki ai ya akayi ya gidan''
ajiyar zuciya tayi
''lpy lau,gida alhmdlh don har wasu daga 'yan gaya sun fara sauka,saidai ta wani bangaren ba lafiya lu ake ba''sai da gaban maryam din ua tsinke ya fadi,cikin sakonni zuciyarta ta fara raya mata faruwar abubuwa marasa dadi masu yawan gaske kuma duka akanta,muryarta na rawa t tambayeta mai ya faru
dariya hindatun ta qyalqyale da ita
''kwantar da hankalinki adda mana,na gaya miki mu lpy muke alhmdlh,bangaren da babu lafiyar su inna huwaila ne da baaba hadiza,kinsan watan baqincikinsu ya kama,yanzu haka jamila na daki ita da sauran yan uwanta anata mata ruqiyyar banza da wofi ta tada aljanun qarya,wai wlh indai na auri jabir sai ta kashe kanta,ni kuwa nace shashasha ki kashe kan naki mana kanki da uwarki kika yiwa asara,ita kuwa inna huwaila sai zirga zirga take ta fita aje ta dawo ta kasa zaune ta kasa tsaye,zuwa dare saiga aminiyarta uwani sai ji mukayi tsakiyar tsakar gida tana cewa,ke kika kawo kanki kikace na kaiki gun bokan nan bani na jawoki ba,don aiki bai ci ba kuma zak nemi tijara ni gaban kishiya?,to ai ramuwar gayya tafi ta gayya zafi shi yasa na biyoki ayita mai kankat kema kowa yaji,mugun qullin da kika so qullawa,ta fayyace duk abinda suka qulla din sannan ta dora da fadin,bola kuma na bogi ne kudi kuma muni babu yadda kika iya,aminad da kuke baqinciki da ita daga ke har hadizan ai ta fiku,yanzu gashi data miqawa Allah kukanta ta jadiye baqicikinta na shekara da shekaru Allah ya yaye mata damuwarta ba tare da tayi hasarar sisin kwabonta ba,ku kuwa haihuwar asara babu kudi babu biyan buqata ga asarar imani,sallolin kwana arba'in a ajejere kun rasa ta kusan kwana dari bakwai,amina Allah ya sanya alkhairi ya tsone idon maqiya,kuma wallahi ni da ku dukanku ke da hadizar shege ka fasa,naci uwar mace a iya tijara da ramuwar gayya,duk kuma wadda take jin ta haifu da jini uwarta ta haifeta ta fito ta tanka
wai in gaya miki adda saiga inna huwaila ta fito da borin kunyarta waisai sun daky wallahi bugu daya uwale rayi mata sai gata tayi plate a qasa''hindatu ta fada tana sheqa dariya
''wai kuma ta sumewa mutane jadiza tayo kanta wai huwaila kinci amanata ta hau dukanta,lubabat
u kuwa itama tayo kan,hadizar ke in taqaice miki labari kowa sai ya ahigarwa uwarsa gida ya zama na wrestling,ina ta laluben wayata in miki vedieo don,kada ayi babu ke saiga babamu nan ya shigo shi ya raba cakwakiyar,kowacce da dogon bakinta ta taho zungi zungi zata yi masa bayani don ya bata gaskiya yadda suka saba yace babu wadda zai saurara,wanna ya ishesu ishara,mama ce......''
''haba aku mai vakin magana,sai kace na kunna freedom?''inji maryam tana murmushi bayan ta katse hindatu
''kefa adda ba'a miki abun arziqi''
''to ai wanna ba baun arziqi bane''
''wallahi nikam abun arziqi ne tunda na gano tashin hankalinsu ranar kawo lefenki,da farko da suka ga anfara shigowa da qananun akwatuna har sun fara yada habaici,da suka ga dai shigowara ke sai suka fara lissafi suna tabe baki,qarshe da suka lissafi akwati ashirin da hudu cif manya da qananu sai aka nemesu aka rasa,inna hadiza na quryar daki suna safa da marwa huwaila kuwa anyi tsamo tsamo an rasa na kamawa,ana cikin haka saiga nawa lefen akwati sha uku,qarshe saiga inna hadiza na dora hannu aka tana xunduma ihu huwaila a taya ta da sharbe hawaye da fyace majina,a gaban idon mutane fa abin mamaki da dariya,ko kunya babu''ta sake qyalqyalewa da daria don tuna abun da tayi
''Allah ya rufa asiri,yanzu ya abubuwa suke tafiya?''
''komai na tafiya daidai,amma wlh adda kizo ki kalli lefanki''
''kai hindatu,me kike ci na baka na zuba,abinda za a ajjiye maka su a dakinka wataran har sai ka gaji da su''
''to ai shikenan,dazu yaya abdur rahim yazo ya kawo kudin dinkunanki,dazu naje gidan adda raliyan na kai mata,har ta fara karbo wasu ma ta bayar an goge miki,gaskiya adda raliya tayi wallahi,akwai zumunci tayi qoqari''
''gaskiya ne Allah ya bar zumunci ya saka mata alkhairi''
''ameen''
nan take aya mata kayan gadonsu da aka siya duka an hada mata sun zama biyu kenan har kayan kitchen dinsu,madyam din tace yayi babu laiciya zama dakin baqi kenan da naki dakin tunda kince shima jabir din ya zuba naahi furniture din,jibi insha Allah nima zan taho gidan gaba daya ai,ki gaida mama''
''Allah ya kaimu,zata ji insha Allah''
daga haka dukkaninsu suka katse wayar
*mrs muhammad ce*
[9/17, 12:54 PM] 80k: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶3⃣7⃣

*_ina so nayi amfani da wannan 'yar damar wajen miqa jinjinar ban girma tare da ddu'o'i na fatan alkahairi wajen jajirtaccen dan kishin qasa da al'ummarsa BARRISTER ABDU BULAMA BAKARTI duk da cewa ban masa sanin ido da ido ba saidai tarin gaskiya amana taimakonsa da jajircewa kan qasarshi da garinsa ya kewaye kunnuwanmu,ina tare da duk wani jajirtacce mai gaskiya da amana dan kishin qasa da al'ummarsa,ubangiji yayi maka jagora ya tsare gabanka da bayanka,ya qara yawaita mana irinku cikin wannan alumma tamu dake fagamniya cikin wani irin hali,Allah yayi ruqo da hannayenka ya dorar da kai kan gaskiya har abada ameen suma ameen_*

Kanta bisa kafadar mamin tana rabza kuka tamkar wadda zasuyi rabuwar har *ABADA*,sai yanzu take kuma jin zugin rabuwa da mamin,tabbas sabo turken wawa ne,ita kata mamin zuciyarta a karye take ta kasa cewa komai,tanajin zatayi asarar diyarta ne guda zata rabu da ita,da qyar tayi,conrtolling kanta kafin,su tsaya suyi sallama
''naso a gudanar da komai da ni maryam,saidai ga yadda lamarin Allah ya kasance,date din bikinku da abdallah yazo daya,kinga ma ko a yanzun gidan ya fara cika da mutane wasu ma rabonsu da gidan nan an jima,kinga bazan iya tsallakesu ba na fita wani guri ba,amma nayi miki alqawarin bayan komai ya lafa wuni guda zanzo nayi a gidanki,hakanan zan dinga dubaki akai akai da yardar Allah''

kafin tace komai muryar abdallah ta ratso falon yana kiran mamin
''gani nan abdallah''
da azamarsa ya shigo hannunshi daya riqe da leda baqa mai kauri mai dauke da tambarin wani gurin saida kayan maza na ado,daya hannun kuma rafar yan dubu dubu ce dauri biyu,cikin shigar qana nan kaya yake,sai ya sake wani dan banzan kyau,farar fatar nan tayi luf da ita tamkar rainon larabawa,ko dama can yafi yanayi da su din sam sai ka rantse babu abinda ya hadashi da nijeria ,sai ya danyi turus yna dubansu
''qaraso mana abdallah,ya ake ciki?''
ya qaraso ya zauna gefanta
''mami duka guest house din guda biyu sunyi kadan,yanzun dai hisham ya samar ma ragowar mutanen hotel''
''yayi kyau hakan,sai ayi total abiya kudin kwanakin da zasuyi da abincin da zasu ci basai an yi jigilar kai musu daga nan ba''
'to''yace yana dora mata daurin kudaden kan cinyarta
''wannan fa na meye?''
''wani abokin aikina ne ya bani gudun mawarshi.......''yayi maganar yana qiqarin zaro wayarshi daga aljihu wadda keta faman ringing,ya kara a kunnenshi kana ya niqe tsaye yana fadin
''gani nan zuwa''yadan dubi nami yana yin gaba
''mami ina zuwa''
''uhm,yanzu haka abincin na da nasa aka kaima baka ciba,kadai kula da cikinka abdallah''
''ok mami''ya fada yana mata murmushi gami da qarasa ficewa a gurguje

nasiha ta mata sosai irin ta 'ya da mahaifiya kafin ta saka driver ya kaita zuwa gidan cikin kuka da kewar rabuwa da juna
ita ta ruqota suka dinga tsallake mutanen da suka fara cika gidan ta rakata har bakin motar sai da suka fice kana ta juya ta koma ciki

🍃🍂🍃🍂🍃🍂

Tun lokacin da idanunsu sukayi tozali da katin daurin auren abdallan hankalinsu yayi qololuwar tashi
''wacce irin hasara nuke shirin tafkawa haka,me kuke tunanin zai faru matuqar muka bar abdallah yayi auren nan,cikin watanni tara ko goma da yin surensu matarshi kan iya haihuwa,zata iya kasancewa ta haifi namiji ma,wannan shike nuna munyi bankwana da cikae burinmu?''

cewar nene dake faman safa da marwa,can cikin dakinsu zahariyya da zubaida kuwa kowa da abinda ya dameshi,zahariyya irin tunanin nene take,ba qaramin tashin hankali take ciki ba,burin da take da shi ya girme mata,yau idan abdallah yayi aure daidai yake da nisanta da dukiyar da suke kwadayin zareta daga hannun mamallakanta su su amfana da roman nata.

Afusace ta kalli zubaida dake zaune a cure can quryar gadon tana ta faman surfafa kuka wanda tunda labarin auren ya isa kunnenta itama ta hana kanta sukuni,kuka take tuquru kamar ba gobe,udanunta duka akumbure suke sun ui luhu luhu sosai daga jiya zuwa yau
''dalla malama ki wa mutane shiru,banza shashasha mara kishin kanta bare yan uwanta,yasan dake din ai ya zabi ya auri wata ba'a gabanshi kike amma ke kin quntata rayuwarki saboda shi''

dama a fusace take maganar zahariyyan sai ta qara tunzurata
''anqi ayi shirun bazanyi shiru ba,kece babbar shashsha da bakison so na haqiqa ba,babu ruwanki da sha'ani na ehe''sai kuwa zahariyyan tayo kanta a zqbure tana cewa
''ni kike gayawa haka,yau zan nuna miki baya ga shekaru da na fiki na fiki iya rashin mutunci''dambe ne ya sarqe tsakaninsu har nene dak samanta ta jiyo hayaniyarsu ta sauko,da qyar ta iya rabasu tana fadin
''sai ku kashe kanku ai,yan iskan yara marasa hankali da tumani,mazq ku raba abun fada cikin taron mutane''

sai sukayi tsit suna maida numfashi kowacce zuciya iya wuya,nene ta kalli zahariyya tace ''ki sameni a sama''ta juya ta fice ita kuma ta rufa mata baya,gware suka kusa yi da adnan wanda ke qoqarin hawa saman da gaggawa
''lafiyanka kuwa?''nenen ta tambayeshi bayan ta danja baya tana qare masa kallo
''muje sama nene akwai magana''ba tare da kowa ya sake tankawa ba suka duru saman gaba daya

''barin yarinyar gidan nan babban abun farinciki ne a garemu,mun riga da mun gama magana da malam na hayi ya tabbatar min da cewa zai mana aiki ammafa matuqar tana cikin gidan nan babu lallai yayi tasiri,tana da wani irin dafa'i a jikinta tun na kakanni da iyayen kakanninta,tunanin da nake yanzu kenan ta yadda zamu gabatar da aikinmu don auren abdallah ba qaramar barazana bace da faduwa garemu sai ga kuma kyakkyawan labarin da na jima banji irinsa ba,mun gode Allah faduwa tazo mana daidai da zama,yau din nan ba sai gobe ba zamu isa vurin,malam na hayi,kwana daya zamuyi a hanya zuwa jibi zamu dawo ya kama ranar daurin aure kenan ko ana gobe daurin aure?''
ta tambayi,adman,sai da ya danyi tunani kadan sannan yace
''ana gobe daurin aure ne''
''to yayi,kai adnan ka zauna muje da,zahariyya,ka shiga ayi duk wata hidima da kai,banason a fahimci komai,zan sanar da haj bintu qanwar ubanku ce ba lafiya zamuje dubota''

a nan suka gama dukkan wani shiri da tsarinsu kana suka shirya ta gayawa mami abinda ta shirya gaya matan,cikin tausayawa mami tace ayi mata sannu Allah ya qara sauqi,idan sun isa zata kira su sai ta bata ta mata sannu

🍃🍂🍃🍂🍃🍂

tun daga qofar gidan ta soma ganin alamun cika,mutanene maza da mata keta kai kawo,a haka ma ba'afara gudanar da bikin ba kenan ina ga kuma an fara,gefe driver din ya samu yayi parking,akwai sabo tsakaninsu da mutunci da girmama juna duk dacewa ya kusa shekaru hamsin dattijon mutum ne mai hankali da nutsuwa,malam baaba direba ya kalleta bayan ya fito
''to malama meramu(haka yake kiranta sunan diyarahi ce ta fari data rasu),Allah ya sanya alkahairi yasa ayi a sa'a,ayita haquri da rayuwa,mu sai ranar daurin aure idan mun dawo daga na mai gida abdullahi''
kanta a sunkuye tace''na gode sosai baaba,Allah ya nuna mana''ya bude boot din motqr yana cewa
''bari in shigar miki da kayan ko''da sauri ta amshi jakar da ya fara fitowa da ita
''a'ah baaba,ka barshi ga yara zansa su shigar min da su''tayi kirqn yaran maqotan dake zaune can gefe da su wadanda da wasan qasa suke tayi da yan guje gje ganinta yasa suka bar abinda suke suka tsaya kallonta,kiransu tayi kunsan amarya da farinjini a guje suka taho dukkansu har ana rige rigen zuwa,kqn ta qarasa mqganar ma sun fara zundumar kqyqn,nata suna shige mata da su cikin gida,dubu biyar ta qirgo cikin dubu dari biyun da mami ta bata tace ta riqe a hannunta tasan amarya kudi basa zama a hannunta,da fqri qin karba malam baaba yayi

''idan da ni mai wadata ne meramu ai nine mai baki ma a matsayin gudun mawa,ke yarinya ce ta gari merama,babu komai tsakaninmu dake saidai muyi miki sai fatan alkhairi''
sai ya kuma karya maya zuciya
''indai ka daukeni 'ya baaba ka karbi kudin nan,ayi min addu'a''da qyar ta shawo kansa ya karba yana sa mata albarka,sukayi bankwana ta shige gidan ta juya don shiga gidan,tun daga qofar gidan ta fara ganin canji,yasha fenti radau ruwan madara tun daga waje har cikin gidan

mutanene da suka kusa dosan ashirin a tsakar gidan,hira ce kawai ke tashi cike da farinciki,dangin mamanta ne da na babanta na nesa,na garin gaya da sauran garuruwa,sallamarta ya sanya su saka guda atare kowa na fadin albarkacin bakinsa ganin yadda tayi kyau ta canza tamkar ba maryam din ba ,kunya ta kamata ta qarasa gurinsu suka gaggaisa,maryam mai alkahiri,ce duk da yanayin gidansun hakan bai hanata idan ta dauki albashinta ta duba mabuqata sosai cikin dangin nasu ta taimaka musu da dan abinda ba'a rasa ba iya abinda zata iya

daga nan dakin mamanta ta wuce,nan din ma da mutane dakin yayi kaca kaca da kayyaki samiru da kayan robobi wadana aketa kwashewa za'a tafi jere,suka gagggaisa ta shige dakin gadon mama,ita da hindatu ne a dakin kayan sawa ne zube saman gadon sunata aiki,gefan gadon ta samu ta zauna ta soma gaida maman,dafe bakinta hindatu tayi
''la la la adda maryam,tabdijan irin wannan canzawa haka gaskiya mami ta iya kiwo,za'a gigita ya abdur rahim kenan''alamu tayi mata da ido tayi shiru don Allah

''qaraso maryamu ki fidda kayan da kike so za'a bada na bayarwa''
''um um mama kawai a bawa wadanda za'a bawa dim babu komai''hindatu ta janyo jakar bakko gaban maryam din tana fadin
''duba kayan nan adda maryam dinkunanki ne jiya adda raliya aiko idris direba ya kawosu gobe zata amso miki sauran''
da daidaya ta dinga daga kayan,ba qaramin burgeta dinkunan sukayi ba duk ciki babu na kushewa
''Allah ya saka mata da alkhairi''ta fada bayan ta kammala dubawar

A bakin fanfo ta fito yin sallar la'asar ta tadda jamila ta fito ita kuma daga bandaki,gaba dqya ta fige ta lalace kamar mai cutar qanjamau,wani banzan kallo ta yiwa maryam din tare da jan tsaki,bata kulata ba ta bude fanfon ta kunnashi ta fara alwala,bata kai ga gamawa ba taji an bangajeta tayi taga taga kamar zata fadi sauran qiris ta qume goshinta Allah ya taqaita mata ta dafe kan fanfon,miqewa tayi tana duban bayanta,binta ce a tsaye cike da tsabar rashin kunay tana girgiza,ta arkade jikinta da ya debi qura kana ta kalleta
''baki gani ne binta kika bugeni?''
''ina gani mana sai me?,dama jiran dawowarki nake cikin gidan nan,tsofaffin munafukai maciya amana masu aure mijin yar uwarsu''
duk da kalamanta sun mata ciwo amma sai da ta bata dariya,tsayawa tayi kallonta kawai,cikin yaran gidan susu goma sha bakwai binta ita ce qanwarta ta tara,aqalla ta bata ahekaru kusan goma,sai taga ada ma ba ni ta kanta take ba sai ayanzu,ranar tqrihi a rayuwarsu,kada kai tayi tana sake yin murmushi ta juya don ci gaba da alwalarta kafin tace
''duk wadanda kika kira da wadan nan sunayen ai aun riga da sunsan kansu,kinga kenan bada ni kike ba''
''dake nake mana,kuma idan kin isa ki tanka kiga yadda ake ruwan bala'i cikin gidan nan''
ta zubar da ruwan dake bakinta ta gyara daurin dankwalinta kana ta dafa kafadar bintan
''mai abun fada baya fada,harkar girma muke da mutunci bata bala'i da masifa,ina da damar da zan miki dukan tsiya binta hakan ba gagarata zaiyi ba,amma bazanyi hakan ba abinda kuka shuka kuke girba ma kadai ya isheku duka mai taba qololuwar zuciya''ta sake mata kafada tayi dakinsu

''ki dakeni mana kinji ko karuwa kawai''
''ke kuwa tunda bata kulaki ba ai sai ki shafa mata lafiya''inji kulu dake diban ruwan wanka
''babu ruwanki munafukai,dama tun jiya naga kunatavrawar kai ke da uwarki a kansu''kulu ba haquri kamar yadda bintan keji da kanga,take suka hau dambatawa,ragowar dangin babansu da basu je jere ba ne suka rabasu

Dawowar yan jere suka hau hirar gidanjan su maryam din yadda Allah ya musu baiwar samun mazauni mai kyau da qayatarwa ta,maganar ta qara hasala hadiza da yaranta wadanda suka zame mata qawaye,suke kuma tayata haukan da take ta faman yi,don tuni jikin huwaila yayi sanyi,saidai atafau hindatu ta hanata shiga jikinsu,tace sam baza'a maimaita abinda ya faru shekarar bara ba,an dai fidda kayan sawa jakanku na da takalma cikin kayan maryam din an bawa yaranta kuku lubabatu da batulu,da murnarsu kuwa suka arba koba komai sun samu na fitar biki,wannan karbar ma da sukayi saida ya zama bala'i,hadiza da yayanta suka fito suna zubda ruwan rashin mutunci cikin dangin ubansu,hali kam sun saidashi,wanda baisan halisu ma ba ada ayanzun ya sani,kowa ya budi baki tir yake da halayensu

🎄🎍🌲🎍🎄🌲

Tara ga wata ya kama ranar talata ranar sukayi kamu,washegari laraba sukayi budan kai duk shigar da sukayi iri daya ne komai da komai ita da hindatu hatta da yari,alhamis aka musu wani wani dan reception na fulani wanda shiga ce ta fulani kowa da kowa yayi,ba qaramin qayatarwa tsarin nasu yayi ba,komai a tsare cikin nutsuwa da kwanciyar hankali

Ranar juma'a ya kama daurin aure,a gaya aka tsara za'a daura auren wannan karon,dalili da yasa kenan gidan ya zamto sai mata kawai mazan duka sun tafi gaya

Da yammacin gidan maman zahra suke zaune maqotansu,tana tsakiyar qawaye da 'yan uwa,tayi kyau cikin shadda 'yar ubansu lemon green da akayiwa adon light blue,rigace da zani dinkin ba qaramin mata kyau yayi ba,tamkar wata fure haka ta koma,raliya na gefanta tana zuba mata abinci cikin plate kana ta miqa mata
''maryam,karbi kici,tunda aka fara sabgogin nan baki ci abincin kirki ba fa''
ya mutsa fuska
''banajin dadin bakina raliya,faduwar gaba nake fama da ita tun da safe''
murmushi tayi
''fargabar shiga sabuwar rayuwa ce,kowacce mace najin hakan har da bacin rai ranar daurin aurenta,wasu ma har kuka suke kafin suji sanyi cikin zuciyarau,kiyita ambaton Allah''

kafin tace komai waurta ta fara kuwwa,a kasalance ta ciro mami ke kiranta,mirmushi tayi sanan tace
''Allah sarki mami na''
''tun da safe naso kiranki maryam,nasan tuni an daura tun safe ko diyata girma ya hau kanta an zama manya''murmushi ta sake yi tace
''na yamma ne mami,suna can dai''
''to Allah yasa ayi a sa'a a gaida maman kice ina mata Allah ya sanya alkhairi''
''ameen mami,na gode''

batulu tayi sallama falon sanye da daya daga cikin kayan da maryam ta bata an gyara mata daidai ita,sun mata kyau kuwa don duka yaran gidan nasu babu laifi akwai kyau irin na fulanin usuli
''adda maryam kizo kinyi baqi suna falon mama''cike da mamaki ta kalleta,gau ta zama adda,sunan da koda wasa bata taba jin wani daga cikin uaran gidan ya kirata da shi ba idan ka dauke hindatu,hatta da isyaku autan gidan
''kice ina zuwa''ta bata amsa tana janyo mayafonta ta lullube jikinta,ta dubi suwaiba dake zaune gefe tace tazo ta rakata
da qyar ta samu ta kutsa ta ahiga gidan nasu saboda yawan jama'a musamman da masu kidan qwarya suka baje hajarsu cikin qwarewa don daga cikin gidan sarki aka daukosu

qannenta shamsiyya,azara,balaraba da yasira na zaune daga gu guda an samu abinci suda yaransu anata kwasa,sannu tayi,musu kafin ta shigesu,yasira da shamsiyya suka danyi qus qus kana suka tabe baki
''an samu duniya''inji azara
tayi sallama falon,maman ma zaune tayi kyau cikin dinkin atamfarya,sai ta koma kamar yarinya mai qananan shekaru,Allah ne kadai yasan farincikin da take ciki,babu shakka komai yayi farko zaiyi qarshe,aure kuwa lokaci ne idan yazo ko ba'a shirya ba sai anyi shi,fata dai kada gaggawar anason ayi auren tasa aje ayi zaben tumun dare
abokan aikinta na na gurin haj atika,taji dadin zuwansu kuwa qwarai da gaske

qarfe shida suka fita meena event center suka gabatar da wata qwarya qwaryar dinner,ta maryam ce ita da qawaye da iyayenta,su hindatu kuwa tuni jabir yazo ya dauke matarshi suka wuce dinner,fir maryam tace ma abdur rahim bata buqatar wata dinner,su din ma da zasuyi sai sun dawo,hindatu da jabir na mata dariya sukayi tafiyarsu,bashi kuwa ya dawo da ita gida ba sai daya saura na dare,maryam din zata soma mata fada tayi shigewarta bargo tayi kwanciyarta
''hindatu rawan kan amarci ya fara tabaki kenan''cewar raliya wadda ke gyara kwanciyar fadil,suna jinta tana musu dariya

🎄🎍🌲🎍🎄🎍🌲

tun qarfe biyar da rabi na yammacin ranar asabar motoci suka cika layin har suka musu kadan,tilas ya sanya wasu motocin suka dinga parking a bakin titin unguwar,moto cine na kere sa'a waccan tana wace wannan haka wannan ma haka,a nutse kowa ke zaban wadda zai shiga kasancewar tare za'a tafi,sai hindatu ta raka maryam din tukunna.

''da Allah malama kihi ki foto,kunzo kun sanya uwarku a tsakiya kuna neman sata kuka,ina cewa ba'a kanku aka fara aure ba,haba da Allah''inji yayar mama hajiya aysha,hindatu da maryam dinne duqe gaban maman,maryam ta soma qoqarin taahi amma kuka yaci qarfinta ya hanata,sanye take da atamfa riga da simple zani an lullubeta ruf da wadataccen mayafi,hajiya aushan ce ta taimaka mata ta miqe ganim da gasken ta kasa miqewar,addu'o'in fatan alkhakri ta biyo yayan nata da shi.

caraf sukaji an damqe hindatu,jamila ce a zabure kamar mahaukaciya sabon kamu surutai take zage zage da sumbatu kala kala
''shegiya tsinanniya,wallahi babu inda kika isa kije,gidan mijina nawa ne ni kadai,wallahi bazan baki damar cin irin daular da naci ba don uwar ubanki''ganin abin na gaske ne daya daga cikin qannen malam amadu sailuba ta qaraso ta daga hannu ta zabgawa jamilan mari
''saketa 'yar iskar yarinya mai kama da 'yar Allah bani,dul abinda kika aikata akayi muku shuru ba'ace muku komai ba bai isheku basai yau ranar da Allah ya tashi nina muku kuskurenku,shekara nawa kuna cutar amina baiwar Allah ta taba tadakai ta kalli waninku,tunda aka fara bikin nan baku,bar mutane an zauma lafiya ba,uwarku dai ta cuceku wallahi,kuma ki saketa tun kafin ki debi haqoranki a hannu,idan tsiyace kowa ma ya iyata''ba shiri ta saki hindatun taja da baya sai gata yaraf a qasa.

da gudu inna hadiza ta qaraso gurin,hannu ta dora a ka cikin qaraji tana fadin
''huwaila amina dake kanki sailuba,zaku kashemin 'ya,munafukai tsinannu,dama ai na dade da sanin kun fi son amina saboda 'yar garinku ce,to Allah ya fiku kina ranar daukan fansa na tafe''
babu wanda yabi ta kanta,hssalima zamewa kowa ya dinga yi ko ruwan da za'a kwarawa jamilar an rasa me miqowa,su kansu sauran 'ya'yan nata na qofar gida suna jallin yadda motocin sukayi farin dangon daukar amare,kwalliya kowaccensu taci tare da fatan daya daga cikin mamallakan motar ya taya

ta dubi sailuba sata zo wucewa tana sauri don kada ta rasa motar tafiya
''da Allah sailuba miqo min ruwa na kwarawa jamila kinga bata numfashi''kallon banza tayi mata
''kici mutuncinmu kici na uwarmu kice zaki moremu,saidai ki nemi wata ta baki wallahi badai ni ba''ta buga qafa tayi ficewarta,tilas ta saki jamilan ta debo ruwan ta sheqa mata kana ta jata zuwa cikin daki tana fyace majina.

Gwanin sha'awa motocin ke tafiya cikin tsari da nutsuwa,sam babu irin mahaukscin gudun nan da 'yan kai amarya keyi,mitoci ne kimanin guda arb'in banda na security guda goma

wani matsananciyar faduwar gaba take fama da shi idan ta tuna izuwa gidan aurenta fa take tafiya,addu'o'i ne fal cikin zuciyarta na samun sa'a da nasarar sabuwar rayuwar da zata fuskanta

🍃🍂🍃🍂🍃

sau uku tana sako qafarta waje da niyyar fita saidsi ta kasa,sakamakon mutanen dake giftawa bata da buqatar kowa ya ganta,aiki ne na sirri wanda bata da buqatar haduwarta da wani,wayarta ta fara vibration jikinta na rawa ta daga,muryar nene ta cika dodon kunnenta
''kada fa kiyi kuskuren da zaki jawo mana bacin aiki,wannan ce damarmu ta qarshe''murya can qasa take fadin
''na gama aiwatar da komai nene,fitowata ce ke neman gagara mutane na kai kawo a gun''
''kada ki kuskura ki wuce mintina talatin baki baro area din ba,wuce hakan na nufin bacin komai''din din din wayar ta katse,hankalinta ta msida sosai kan hanyar ficewarta,wuf ta faki idanu ta fice ta nufi bangaren nasu cike da farincikin nasarar aikinsu

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

Qarfe goma da rabi ne na dare,gefan lallausan gadon dakin nata take a cure guri guda,tafiyar yan kawota da mintina ashirin yayyafi ya fara sauka wanda ya haddasa sanyi da garin yayi hade da qamshin qasa,bai kankama ba ruwan hakanan yayyafin bai tsaya ba,kusan tunda suka tafi suka barta anan take zaune bata ko motsa ba

hayaniyan data soma ji cikin paflour na muryoyin maza daban daban suka qara mata fatgaba,ta runtse idonta tana jin yadda zuciyarta ke dukan uku uku kamar zata yi tsalle ta fito

''ko baka fadi ba ba shiga muma za muyi ba don an dade da daina wannan''ta jiyo muyar wani daga cikinsu,tun tana jin hayaniyar tasu sama sama har taji dif alamun basu cikin sun fice kenan

da gudu gudu sauri sauri ya qaraso cikin parlojt din saboda ruwan da ya sake danyin qarfi,duk da haka ya jiqa masa fararen kayanshi,ya tsaya ya kulle ko ina ya rage yawan qwayayen dake kunne kana ya doshi dakin kai tsaye

a hankali ya tura qofar dakin kana ajjiye tarin ledojin dake hannunshi,qamshin dake dakin kawai ya isa ya tabbatar maka rana ce ta musamman,tsaye gayi hannunshi harde a bayanshi,sai ya lumshe idonshi yana zuqar qamshin qasa hade da turaren jikinsa da na dakin baki daya yadda suka hadu suka fidda wani qamshi na musamman kuma na daban,gwagwarmayar da ya fada kacin samunta ta zama mallakinsa ya dinga dan tunawa,a hankali ya bude idanun nashi ya tsaya yana qarewa shigar tata kallo

gaba daya jikinsa ya saki lokacin da wani tunani ya darsu a ransa wanda ya qada maaa qwarin gwiwa da azamar isa gareta,tamkar mai tausayin gadon haka ya hau ya dinga rarrafawa har ya isa gareta kana yayi zaman dirshan a gabanta

sannu a hankali ya dinga yaye mayafin dake kanta har ya cimma nasarar cireshi duka fuskarta ta bayyana,saidai ya cimma idanunta aruntse ne,ya karyar da kai yana ci gaba da kallon fukartata irin kallon da bai taba samun dama ya tsaya yayi mata shi ba,kyawunta yaci gaba da fito masa muraran,sosai ya shagala har baison abinda zai shiga tsakaninsa da yanayin

Qememe zuciuarta taqi amincewa da daina mugun tseran gudun da take,gashi ya sata agaba,nauyi da kunyarshi sun hanata bude ido,jin shirun yayi yawa ya sanyata yanke shawarar bude idanun nata ko yama fita adakinne ma bata sani ba

da kadan da kadan ta dinga budesu har sai da suka kammala buduwa tar,da qafafunshi ta soma tozali a hankali ta dinga daga kan nata har ya sauka bisa fuskarshi da ruwan sama ya jiqa har ruwan da ya soma taba kanshi ke diga kadan kadan,batasan lokacin data ta wuntsila gefe ba cike da *TSORO RAZANI DA FIRGITA BA* sakamakon wanda ta gani

*ABDALLAH* ne cikin daren nan cikin gidanta kan gadon aurenta?,idanunta ke mata gizo koko meye?,me yake faruwa ne?,hauka ce ta samu qwaqwalwar abdallah ko bashi bane bama gaba daya aljanu kesan mata wasa da qwaqwalwarta da tunaninta,ina abdur rahim da ya bar abdallah ya keto dakinsu na sunnah?
dimbin tambayoyin da suka nemi jirkita mata qwaqwalwa kenan tashi guda ba tare da tasan duka amsoshinsu ba

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽

💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶3⃣8⃣

*_JIRGINSO ZAYA TASHI KE DAI AKE JIRA ...'YAR GATA DUNIYAR SO.... KECE DA SARAUTA_*🎶🎶

*_na dawo gunki nazo baqo da sallama....kai kawo nayi qarshe...a qauna na tsunduma....kin jawo nayi roqo nazo ki ban zuma....na sawo dubi tufata mai kyau da karrama....ke naiwa kwalliyata shiga ta alfarma....._*🎶🎶
*_soyayya gaskiya ce ya zanyi in raina....wanda yake aac cikintaaa nima don na zauna.......nayi dare ban masauki gidanki in kwana....zo ka shige har abinci zan maka kwadon rama....._*🎶🎶

*_riqe sirri sai mai sirriiii....da fari a cikin taurariiiiii...._*

*wannan waqar na sadaukarwa da readers don jin dadinsu kana iya sauraronta bayan kammala karanta wagga shafi*
😜😜😂😂

Matsowa kusa da ita ya sakeyi tattausan murmu kwance bisa kyakkyawan fuskarshi,duka hannayenshi ya ware da nufin ta iso gareshi,take jikinta ya soma bari,qwaqwalwarta so take ta tsaya cik da aiki saidai ta ware qwanjinta wajen hana hakan faruwa,bata da buqatar tsayawar tunaninta a yanzu,tama fi buqatarshi fiye da ko yaushe,ya sake matsowa gareta yana nufin janyo ta jikinshi

wata hadaddiyar tsawa ta sakar masa bayan ta dira daga kan gadon jikinta na qyarma,tuni zuciyarta ta karye hawaye ya soma sintiri bisa fuskarta,dukkan tunaninta sun gama vata fyade abdallah yazo yi mata,tunda ba wannan ne karo na farko data taba ganinshi kebe da diya mace ba,amma wanne irin tsoro abdur rahim kewa abdallah da ua bashi irin wannan damar?,ko wani abu yayiwa abdur rahim din nsta har ya kai ga shigowa dakinta shi daya ba tare da wani qwaqqwaran motsi ko hayaniya ba.

Abdallan ya sake motsawa don biyota qasan,cikin daga sauti hargagi fushi bacin rai da tashin hankali ta dakatar da shi
''dakata marar tsoron Allah,me kake nema da ni?,me ya shigo da kai dakina?,kana shirin tozarta sunnar ma'aiki?,kana shirin cin mutuncin matar da bata yi maka komai ba?,to Allah ya fika''
jikinta na rawa ra fara daddan na wayar dake hannuna tun dazun da aka kawota lubabatu ta danqa mata a hannunta

Numbers din abdur rahim ne guda uku,saidai duka wadda ta kira sai taji ringin dinta cikin aljihun abdallah,cike da wani tsoron ta dago ta dubeshi,hawaye ne kawai ke kwaranya da sintiri kan fuskarta
''abdallah!,ina abdur rahim?,me kayi mishi?me ka yiwa mijina!?''ta qarasa maganar cikin qaaraaji

baisan sanda yayi alkafura ya diro daga gadon ba,gadan gadan ya nufeta don ya riqeta ganin yadda take kuka tuquru tana dafe bango,saidai kafin ya kai ga riqeta ta goce
''kada ka tabani,kaji tsoron Alkah kasan cewa ni matar wani ce''cikin cool voice dinsa mai cike da jarumta da mazantaka wadda a yau rauni ya cikata ya saje maidata sassanya yace
''pls cool down mana,ki natsu in miki bayani kinji,ki saurareni''

''bazan nutsu ba,in nutsu ka cucu ne,me kake nufi abdallah,me nayi maka,ka shigo dakin aure na,banga mijina ba,na kira wayoyinshi suna jikinka,ka gaya min me ka masa!!me kayi masa!!!''
duk yadda yaso tayi shiru ta saurareshi abun ya faskara,idanunta sun rufe bisa dukkan zatonta ko abdallah ya kashe abdur rahim ne
''ki zauna ki fahimceni...'''
''bazan fahimceka ba.....ina mijina.....ina ka kaimin mijina abdu........''

''maryam!ni ne nan mijinki,ni ne mijinki ba abdur rahim ba,ni abdallah da ni aka daura miki aure!''ya fada yana nuna kanshi shima cikin daga murya har jijiyar wuyanshi na tashi
sai kukan nata ya tsaya cak,ta tsaya tana kallonshi tamkar doluwa ko sakarya,jin maganar tayi tamkar cikin mafarki,da saufi ta kama hanunta ta mintsina sai ta tabbatar cewa gaske ne,girgizq kantq ta shiga yi tana fadin
''ba kaine mijina ba,bakai ka aureni ba ni zaka yaudara?''

''bari in baki shaida don ki tabbatar''ciro wayarsa yayi ya kira wasu nimbers,ga mamakinta sai ga muryar abdur rahim radau
''kai,bakasan ganganci bane kiran ango daidai wannan lokacin ba?,ko baka shiga dakin marya bane?''yake tambaya cikin sigar zolaya
''hmmm,abdul maryam zata amince nine mijinta kuwa?''
dariya yayi
''a'ah,mai zai hana,idan ma taqi ta amince ka dauketa kuje gidansu tunda su sun sani kaine ka aureta din,ko ni inzo gobe sai in dauko gimbiya muzo in mata bayani''

baiga qarasowarta ba sai waftar wayar da tayi,cikin rawar jiki ta kara wayar a kunnenta
''abdur rahim,ka cemin kaine mijina ba abdallah ba,ka gaya masa don Allah''
''kiyi haquri maryam bani na bada sadakinki ba bani ke neman aurenki ba,duniya bani ta shaida a matsayin mijinki ba duka wannan abdallah ne,nine *abdurrahim a fili a boye kuma abdallah,nike neman aurenki a gaban idonki a bayan idonki abdallah ne*,banyi hakan ba don komai sai don *DACE DA JUNA* da kukayi ke da shi,babu wadda ta dace ta zauna da abdallah saike......''

bata bari kunnuwanta sun qarasa ji mata kalmomin da ta yiwa laqabi da munanan kalmomi ba ta saki wayar ta tarwatse agun,taji daga baki mai tushe to shin kuma wa take jira?me take jira da zai tabbatar mata fiye da abinda taji yanzun?babu,babu shi,take taji garkuwar jikinta na raguwa,qarfinta yana yin qasa,sai ta soma sulalewa agun

da gudu abdallah ya isa gareta ya tallafota,tabbas da tana da isashen qarfi bazata yarda ta sauka ajikinshi ba,rungumeta yayi yana jijjigata,numfashinta na fita hakanan idanunta akansa suke hawaye na bin gefan kunnenta saidai numfashin na gware ne gurin fita,rungumeta yayi tsam cikin jikinsa cikin wani tashin hankalin,daukarta yayi tsam tamkqr wata 'yar tsana ya komar da ita kan gadon ya shimfideta.

mahaukacin bugu yaji ana yiwa qofar bangaren nasa ,sai ya sake diriricewa,cikin qanqanin lokaci kuma ya gayyatowa kansa dakiya da jarumta yana tafiya yana waiwayen maryam din tamkar wanda aka ce masa kafin yaje ya dawo zata bace ya sauko ziwa bakin qofar ya saka key din ya bude

jikinsa ta fado tamkar wadda aka hankado,cikin hanzari yasa hannunsa daya ya cireta daga jikinsa yayi gefe da ita saidai ita qoqarin dawowa take zuwa jikin nasa tana gunjin kuka duk ta wani burkice kamar mahaukaciya
''wai meye haka zubaidq!bana son hauka fa!''ya fada cikin hargagi
''bazan iya ba abdallah,wallahi bazan iya jure rashinka ba,ka tausaya min abdallah,ta yaya muna cikin gida daya zaka kwana da wata abdallah?''
ya tabbata idan yace ma zaya tsaya bata baki ne wahal da kansq kawai zaiyi don ba zata taba fahimtarsa ba,kai infact ma a yanzu bai da time baijin yana da time din wani a yanzu a duniya koma bayan maryam,ya tabbata idan yayi sake kwabarsa zatayi ruwa ne tsululu kuwa,a nashi zaton da hasashen abun bazai kai bacn haka ba,yayi zaton cewa duk randa maryam din ta samu labarin shine miji a gareta zatayi farin ciki ne fiye da kowa kodon,dimbin dukiya da Allah ya mallaka masa

ganin yadda take faman ahigewa jikinsa kamar hauka yasa yq cira hannu hankadata baya tayi taga taga kamar zata fadi
''ki shiga hqnkalinki zubaida,bana cike da iskanci da hauka kina jina ko,bace min da gani''
maimakon tayi kamar yadda yace din sai ta qara tasowa kansa,cikin zafin nama yaja qofqr ya rufe ya maida muqullin,ta kuwa fada jikin qofar ta saki wani kukan tana bubbugawa iya qarfinta
''ka bude min don Allah abdallah,wallahi na kasa barci,na kasa cin abinci,na gaza jurewa,ka bude min abdallah''haka ta dinga fada tqnq bubbuga qofar,yana jinta hqr ya haura sama ya barta anan
ruwan roba mai azabar sanyi yq ciro ya hado da cup ya koma dakin,yadda ya barya haka ua sameta sai qaruwa da ruwan hawayen fuskarta sukayi

ajjiye cup din yayi a side drower ya haura gadon,ya zame mayafin dake jikinta ya wulla shi gefe,ya janyo cup din ya tsiyaya ruwan yana tsoma hannunshi cikin ruwan yana shafa mata a fuskarta zuwa wuyanta,duk da yanayin da yake ciki hakan bai hanashi kin laushi da santsin fatarta ba,duk lokacin da hannunshi ya taba fuskarta ji take tamkar yana dora mata wuta ne a jikinta,zuciyarta,cike fal da tsanarshi,sannu a hankali numfashinta ya soma daidaita,qwarin jikinta ya soma dawowa,da sauri tasa hannunta tayi wurgi da hannunshi dake ci gaba da shafa mata ruwan,ta miqe dqga kan gadon tana shirin sauka,da sauri ya tareta
''ina zaki maryam?''
''ina ruwanka da inda zani?,ka rabu da ni!''tayi maganar cikin tsawa,ganin da gasken fita zatayi yasa ya tareta ya riqe dukkan kafadunta,ta soma zile zille da qoqarin qwacewa tana fadin ya rabu da ita ya saketa,ci gaba yayi da qoqarin tsaidata

''ina buqatar hankalinki maryam,ina buqatar nutsuwarki,ki zauna ki bani dama muyi magana,ki nutsu ki fahimceni,me kike so ne maryam,me kike buqata''
sak ta sakeyi tama kallonshi
''sai yanzu kake da buqatar hankali na?,sai yanzu kake d buqatar nutsuwata?me kake son gaya min,ka aureni ba da sani na ba kuma kace nutsuwata kake buqata?wacce nutsuwa kake sa ran samu daga gareni?,haka ake aure?,ok saboda kana tsammani kana da dukiyar da zata iya kawo maka duk macen da kake so kamar yadda naji kana alfahari kana gayawa abokanka?,koda dukiya zata iya kawo maka kowacce mace da kake miradi yes na yarda zata iya amma banda ni maryamu aciki,koda ina da muradin dukiyarka ina cewa saida izini na zaka aure ni?,after all ma bana aonka abdallah bana qaunarka,bani da burin auren ire irenka ma,abu guda nake da buqata daga gareka shine ka rubuta min sakina guda uku a yanzu ka bani,ni kuma na maka alqawarin bazan kwana maka cikin gida ba,ka sakeni abdallah ka sakeni!''
ta qare maganar cikin hargowa

hannayensa ya harde aqirji yana kallonta,ba qaramin duka kalamanta sukayi masa ba,tunda ya tashi mace bata taba kallon qwayar idanunshi tace bata sonshi ba,akoda yaushe kalmomin so yake samu da karba daga garesu,kalmomin da bai taba samin suna da dataja ba sai yanzun akan maryamun,ya fuskanci ba qaramin fita tayi daga controll dinta ba,kome zaya fada bai da tasiri yanzun cikin kunne da ziciyarta don hakq ya dan jada baya,ya zame rigar jikinshi ya rage daga shi sai farar vest da dogon wandon shaddarsa,ya nufo inda take gadan gadan sai ta juya zata sa gudu caraf ya kamota,duk iya yada taso qwacewa abu ya faskara,qyaleta yayi taci gaba da qoqarin qwatar kan nata har jikinta yayi tubus qarfinta ya qare

''haka kurum zaki bata mana farin darenmu kan dalilin ki wanda kika qi tsayawa kiji nawa dalilin,dare ya tsala lokqcin da ya kamata mu samu hutu amma kin hana mana''ya fada yana mirginata tare da zuge mata zif din rigarta,ganin yana qoqarin cire mata rigar jikinta ya sanya ta sake sakin wani kukan cikin dausashshiyar muryarta da kuka ya dasheta tana ci gaba da qoqarin ture hannauenshi wanda saboda tsabar rashin qwarin jikinta ko motsi hannun nashi baiyi ba
''ka qyaleni abdallah,wallahi idan ka taba mutuncina zan maka Allah ya isa kuma bazan taba yafe maka ba''
duk da yana cikin rashin nutsuwa sai da ta bashi dariya
''kome zan miki ma ai nawa ne,dukkaninki halas dina ce,so ko kin min Allah ya isan ma ba bina zata yi ba''ya qarasa sabule rigar tata,hannayenta tasa ta fara kare qirjinta tana cewa
''ka zalunci rayuwata abdallah,zamu tsaya fa hisabi gaban Allah''
hannu daya yasa ya kawar da hannayen nata wanda ita iya ganinta duka qarfinta tasa gun kare su,ya balle bra din ya zameta daga jikinta,take numfashinsa ya dauke da sauri ya lumshe idanunsa kana ya squka agadon ya isa bakin wardove dinsu ya zabo rigar bacci mai adon fari da pink mai sulbi da taushi ,saidai kafin ya qaraso har ta isa bakin qofa cak ya sake daukota kamar wani kara ya maidota kan gadon ya danneta da rabin jikinsa ya sanya mata kayan baccin

fillow guda ya ajjiye musu bayan ya duba lokaci qarfe biyu da rabi na dare,cikin jikinsa ya jata ya matseta gam suka kwanta ba tare da ya damu da sauya nasa kayan ba,yana jinta tana wutsil wutsil dinta da dan ragowar qarfinta hade da hawaye don tuni muryarta ta gama dakushewa koda tayi maganar ma ba fita take ba,gashinta mai sulbi da taushi kawai yake shafawa yana jin digar hawayen nata tamkar na dalma kan tsokar zuciyarsa.

a hankali ya zagaya da kansa kan kunnenta ya rada mata
''kiyi haquri,na yarda na cutar da ke amma relax pls mu barwa gobe,kome kikeso zan maki,kiyi bacci zuciyarki tayi sanyi''
''ka sakeni bazqn kwana daki daya da kai ba bare jikinka,ka sakeni abdallah''abinda take ta fadi kenan saidai ina muryarta bata fita bare yaji abinda take fada,gaba daya ma taga ya maia abun kamar wani wasa saboda tsabar qarfin hali irin na abdallahn.......

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶3⃣9⃣

🎶🎶🎶🎶

*_alqawari ki riqeeee..komai wuya karmu rabu kinji..._*
*m sharif song for dis page*
😜😂

A hankali ta dinga bude idonta da taji ya mata nauyi sakamakon kumburar da sukayi,tana gama budesu tarwai komai ya dawo kanta,abu na farko hawaye ne ya fara bin idanunta kamar yadda ya ta kwanta da shi,jin alamun motsi daga qasa ya sanyata wurga idanunta can,abdallah ne zaune kan sallaya,ta dubi agogon dakin qarfe bakwai saura na safe,da sauri ta miqe cikin zuciuarta tana istigfarin rashin yin sallar asubahi akan kari,jiki babu qwari ta zuro qafafunta qasa motsin wannan ne ya juyo da hankalin abdallah kanta

sai ta kasa tashi don batasan ina toilet yake ba,da suka hada idanu kuma sai ta dauke kanta gefe guda
''ga toilet din can''ya fada yana kada yatsunsa tare da yi mata nuni,ta jishi sarai saidai ba zata oya tashi ba saboda rigar baccin jikinta gajeriya ce,gashi ta wuwwurga idanunta ko ina bata hango kayanta ba,zanin gadon ta yayaye kawai gaba daya duk da girmansa ta lullube jikinta da shi kana ta samu sukunin shigewa bandakin

kuka ta zauna yi riris kan daddumar,tana ji har cikin zuciyarta abdur rahim ya zalunce ta abdallah ya cuceta,don ko kadan bata da plan din airen abdallah akundin rayiwarta,sai gashi dare daya wata qatotiwar qaddara mai wuyar afassara ta fada mata,abdallah mai girmankai,mai izgili mai taqama da dukiyarsho,mai titiya da kyawun surar da Allah ya bashi,abdallah mai tarin 'yammata,ko baya ga haka ma sama ai ta yiwa yaro nisa,ina zata kai abdallahn,batajin cikin yarin masoyansa ita din karanta ya kai tsaikon da zata daga hannu,me take da shi da zata nunawa duniya amatsayin matar abdallah abdulkarem mai nasara?,yaro dan gata gaba da baya da daya tilo tamkar taoka daya cikin miya,mai tarin kyau asali dukiya da arziqin ma baki daya,ta ina tarayyarsa da maryam diya ga malam amadu zatqyi daidai,masu nema da qyar suci da kansu da qyar,diyar da ta taso cikin qunci hantara da takurar rayuwa?,rufin asiri take nema da girma ba bankada da tonon sililin asirinta va,ta iya talaucinta haka zalika ta iya tsayawa iya matsayinta,to akan me yanzu zata yadda ta sarayar da dulka wadan nan abubuwa?,ko ta zuba ido abdallan ua sarayar mata da au lokaci guda

tasha ji daga bakunan wasu matan yadda auren mai dukiya quruciya da kyau yake zamewa mace qarfan qafa alaqaqai,don me zata zira kanta rijiya mai gaba dubu?bata taba sha'awar auren mai tarin dukiya irin abdallah ba,balle shi din da tasha jin kalmomin nuna ko ahi waye da matsayin da yake ji ua taka daga bakinsa,idanuwanta sunsha nuna mata kal kalan 'yammata dake hauka akanshi,tana cikin wanna tunanin ta tsinci tafin hannunshi dafe da saman qafafunta,da sauri ta janyesu ba tare data daga kai ta dubeshi ba
''maryam''ya kirata asanyaye
''ko baki fada ba kuka kike''
''kuka na ya zama dole,auren dole qiriqiri?,irin auren dolen da ko a fina finai ban taba cin karo da ahi ba sai gashi yau ya faru a kaina?,ka fada min wanne mataki ka dauka game da zaman mu,zaman mu ba mai yiwu bane''
''ki bani dama mafyam ni zan mai da ahi mai yiwuwa,indai matsalar taki ta zuciya ce,zuciyarki bata san abdallah,ta bawa abdallah dama na kwana talatin cif na rantse miki sai taso abdallah fiye da yadda take son kanta''
''ka taba ganin inda ruwa da wuta suka cakudu suka zauna guri guda lafiya lau?''
ya fuskanci mai take nufi da maganarta don haka bata buqatar amsa

kusan mintina goma ahiru ya ratsa tsakaninsu,ta qagauta ya janye jiminahi daga inda take,ganin babu niuya tasa ta bude bakinta murya can qasa
''ka matsa daga kusa da mi,kuma ka cika min alqawarin da ka dauka min daren jiya yanzu ba sai anjima ba''
gayara zamanshi ya kuma tamkar ma basa ahi take maganarta ba
''naji,zan sakeki.....amma bisa wani sharadi guda''
tunda suka fara maganar bata dago ta kalleshi ba sai a yanzu
''ba buqatar wani sharado daga gareka ko wanne iei ne saki nake so,kuma dole ka sakeni''
ya sanya fitinannun qwayoyin idanunshi cikin nata kana ya tabe baki
''babu dole fa maryam,abdallah ne mijin ba wai maryam ba,idan kin amince zan gaya miki sharadina daya ne zuwa biyu da zarar kin cika sharadina ba tare da bata lokaci ba agobe ma kina iya tafiya da takardarki''idanunta ta lumshe saboda yadda ya nutsa qwayoyin idanunshi cikin nata yake mata magana haka kanshi tsaye kamar ba mai laifi ba

shiru tayi,cikin dan taqaitaccen nazari zuciyarta ta bata shawarar sauraranshi kanta kawai ta gyada masa,ya sake sanyaya murya tamkar mai jin bacci tare da sake matsowa kusa da ita,tayi yinqurin matsawa da sauri yace
''babu buqatar ki kuma matsawa baya,kin manta sirri zamuyi,ko kina nayita daga sauti na bayan jiya kinsa maqogarona nata zafi har yau?''tilas ta zauna a hakan qamshin turaren da tun jiya ya fesa shi amma har yanzu yana tashi a jikinshi

''tambayoyi ne zan miki su da farlo wadanda nake buqatar amsarsu daga yau zuwa gobe da safe kafin ki bar gidan nan,kada kiyi tsammanin samun takardar sakinki daga gareni matuqar kika gaza amsa min tambayoyina cikin gamsashshiyar amsa,na farko mai yasa kika damu da abdallah da yawa,kika gaza barinshi yaci guba da aka zuba cikin abincinshi har sau biyu?''da hanzari ta dago cikin mamaki da tsoro ta dubeshi,yaushe abdallah yasan da maganar gubar data hanashi ci?
gira ya daga mata yana mata killing smile dinshi
''hey,meye na tsorata haka,bayan tambayoyin basu qare ba,daya cikin wadanda zasu biyo baya fa''
sai ta duqar da kanta zuciyarta na dukan uku uku
''me yasa kika damu da sanin irin gubar da ake ahirin kasheni da ita sai da kika dangana da asibiti a washegari aka tabbatar miki da irin qarfi da illarta ga duk mutumin da yaci?,me yasa kika gaza barin gidansu abdallah duk da irin takura raini da abdalla ke miki?,me yake saki rudewa harda kuka duk lokacin da kika ganni kebe da wata cikin tsakiyar dare?suke nan tambayoyina''

gaza daurewa tayi a wannan karon ma sai data dago ta dubeshi cikin mamaki shin abdallah yasan akwai masu farautarsa ua qyale ya zuba musu ido?,tamkar yaji abinda take zantawa cikin zuciyarta yace
''kada kiyi tsammanin abdallah wawa ne bansana ana farauar rayiwanshi cikin gidan ubanshi ba,i know kuma zuwa gobe zaki ga abinda zaya faru,naki kawai answer din question dina.....gaba ta gaba,are you ready madam?''
kai ta sake gyada masa kamar qadangaruwa
''ok,mami is unaware game da wadda na aura,nayi haka ne saboda ina son inyi suorising dinta,ta bani komai a rayuwa bansan me zan bata ba,na sani baya ga ni kece ta biyu cikin diyoyin da take so,bata san diyarta na dawo mata da ita ba,na tabbata zatayi matuqar farinciki da mamaki da ganinki...saidai kinsan me?,farincikinta da mamakinta zai dore ne matuqar taji cewa auren so da qauna ne tsakaninmu,kinsan abun duba?duk wani motion da act namu zai zama irin na masoya a gabanta daga wunin yau zuwa goben tafiyarki babu musu tsakaninmu,yi nayi bari na bari wannan shine abubuwan da zasu sana miki takardar rabuwa da ni thats all''

gaba daya ji tayi ya daurera da duka jijiyoyin jikinta,wadan nan tsauraran sharuda har ina?,har gwara ya samu bulala ya bugeta yadda yakeso kana ya sallameta yafi nata sauqi,ina zata sami tulin amsoshin tambayoyinsa wadanda bata tab tunanin ma a kansu ba?me yake nufi yace da ita?,ama ture ta wannan baki daya,ya zata iya tanqwara zuciyarta ta nuna alamu na soyayya ga mutumin da babu so ko qwauar zarra tasa cikin zuciyarta.....

''idan kuma baki iya tsallake wadan nan abubuwa.....fine....sai ki shimfida ta barma da daura damarar zama da abdallah kiga idan bazai saceki gaba dayanki ma ba zuciyarki ba cikin kwanaki talatin kacal,hakan kuwa kinga bazaya miki dadi ba tunda kince wai baki sonshi bayan tsayin daka da kikayi wajen kare mishi ranshi da lafiyarshi don kina da buqatar ra......''
''naji....naji na amince''ta fada da sauri don katse soki burutsun da tace yana shirin yi mata
''good job,shikenan Allah ya bada sa'a''ya miqe daga inda yake,har yayi taku biyu ya kalleta still tana duqe
''kada ki manta da answer din tambayoyi na,don sune bqngare na farko na yarjejiniyar mu''

Sakaliyar la'asar ce data gama hada hadari wanda ya tilastawa garin lumshewa,sannu a hankali suke taku wanda idan ka gansu sai ka rantse shaqiqan masoya ne guda biyu hannayensu sarqafe cikin na juna,sanye suke da kaya kala daya saidai bambancin sunan yadikan,nata material ne na mata yayin da nashi ya kasance na maza,dukkansu sea green colour ne,abu daya zai saka duhu yadda fuskanshi ke qunshe da wani irin haske da annuri,yayin da nata fuskar ke duqunqune cunkushe da bacin rai duk da hakan bai hanata yin kyawu ba,maryam ne da abdalla kan hanyarsu ta zuwa gaida mami bayan ya tabbata da jama'ar gidan kowa ya koma inda ya fito

sunfi minti talatin cikin bangarensa yana nuna mata salon kallo magana da ladabin da yakeso tayi masa gaban mamin wanda hakan shi ya kusan janyo rikici
ya sake waiwaya ya dubeta suna gab da ahiga bangaren mamin kana ya dakatar da tafoyar tasu,tsatstsareta yayi da kallo,ta kauda kanta tana qoqarin sabule hannayenta dddaga cikin nashi
''malam bamuyi da kai zaka dinga min akallon mayi ba ko,idan kuwa kaci gaba daidai nake da na koma inda na foto na hada ya nawa ya nawa na koma inda nafi wayo''
''kya sha tsinuwar Allah data mala'iku,runda ko banza miji nake agareki koda qarshen duniya zaki gudu,nike ma da magana dake,kinfara karya wasu dokokin tun yanzu,wanda hakan na nufin tangal tangal da muradinki ne,haka koka ga fuskar amarya na kasancewa washegarin ranar da aka kanta,look at ur self don Allah,jiya kin kwana kuka idanunki sun koma kamar kumburarren qullin qosai,an samu da qyar sun daidaita kafin yamma,sanna kina son ki sake wargaza mana shiri,to wlh u hv to make sure idan kika bari mami ta dago wani abu babu ke ba samun takardar sallama''

wani tafarfasa zuciyarya ke mata,ta debi a qalla mintina biyar kafin ta iya controlling kanta ta sauyawa fuskarta mood sabanin na dazu,cikin tafasar zuciyq ta miqa masa hannunta shkuwa yasa nashi hannu ya riqe suka ci gana da tafiyarsu daga nesa tamkar ka sacesu don kyai tsaro da marching da sukayi

A guje ta juya kamar zata ci da baka ta koma bangaren nasu tana zabgawa nene kira,saura kadan ta take zubaida dake kwance agashiyyan wanda cikin nene adnan da zahariyya an rasa wanda zai ce da ita yi haquri ba don komai ba sai don tsananin haushinta da sukeji kan wanda ta shiga halin sabo da shi
da sauri nenen itama ra iskota don dana a tsaye take cikin safa da marwa
''yaya?,ya ake ciki?''
cike da tsananin tashin hankali kamar wadda aka gaya mata uwa da uba duka sun mutu tace
''wallahi nene yana nan bai mutu ba,tas na ganshi babu abinda ya tabashi wallahi,tare suke da yarinyar nan nene bata bar gidan nan ba,hannayensu riqe da juna,mun shiga uku nene kada dai ace ita ya aura?''maganar ba qaranin sa nenen tayi a tashin hankali ba,a aukwane ta juya kan kujerar data tashi zata dauki wayarta,garin rarumar wayar ta dauki remote,sai data fara dannawa ta lura ahine,wurgar da shi tayi ta suri wayar kai tsaye ta kira malam na hayi

Mgunyar dariya ya dinga kwarawa kafin yace
''sanda muka gudanar da aikin bata cikin gidan,don haka ki kwantar da hankalinki ki zuba ido kiga abinda zai faru,saidai babu lallai abunda zai farun ya zama abunda mukai nufi da shine,kasantuwar yarinyar na tare da shi''yana gama fada ya katse wayar,nene ta dubi wayar tana jadda maganar daya gaya mata,saidai ta samu relief jin cewa wani abu na iya faruwa da abdallan,nasu kenan yanzu zuba ido suga mai zai faru kenan?

cikin falon mamin babu kowa sai yan surutai da yake iya jiyowa cikin kitchen,hanyar saman mamin yai direct da ita,bai saki hannunta ba sai da suka dangana da bedroom din mamin yace zquna ina zuwa,cikin sassarfa ya sauko qasa ya dawo kitchen din

Tun daga falon ya soma qwala mata kira,ita da wasu mata ne su uku ta hudunsu baaba uwani da alama gyara kitchen din ake sakeyi da wanke abubuwan da suka babbaci
''omg,abdallah taushe zai girma ne jama'a''ta lumshe idonta tana fada jin irin kiran da yake mata
ya qaraso kitchen din cikin hanzarinsa ya kama hannayenta
''suprise mami suprise''yake fada cike da murmushi yana dubanta,sai ta dan hade rqi
''suprise wanne iri?wai shin ma wanne abu ne ya fito da kai daga gidanka?,salon kaci gaba da takuramin ya sanya kaqi tarewa gidanka kace sai bayan sati biyu''
''mami nidai kizo muje ols mami,nasan zan sanyaki fafincikin da kika jima baki irinsa ba''
''abdallah barni in gama da aikin nan tukun kahe zan sameka ko wanne irin suprise ne sai in gani''
ya langwabe mata kamar qanqanin yaro
''mami bana ao ya huce fa don Allah kizo muje''
baaba uwani ce ta sanya baki dole ta ajjiye plates din hannunta ta bishi tana mita shikam yana qyalqyala dariyanshin nan dake fidda sigar kyawunshi

*_kuyi manage da wannan pls_*

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶4⃣0⃣

*_An karbo daga Abu Hurairah Allah ya qara yarda da shi,Manzon Allah S A W yace''ana bude qofofin aljanna duk ranar litinin da alhamis,sai Allah ya gafartawa ko wanne bawa musulmi indai ya kasance baya shirka baya hada Allah da abokin tarayya,sai dai wani mutum wanda ya kasance akwai qulli ko gaba tsakaninshi da dan uwanshi musulmi,sai ace''ku qyale wadan nan har sai sun shirya,ku qyale wadannan har sai sun shirya_*

mami na gaba yana take mata baya,sai mita take masa na ya tasota tana cikin mutane,shidai baice uffan ba in banda murmushi da yakeyi,suka ahiga falo tana qoqarin zama yace
''a'ah mami mu qarasa daki''
''kai abdallah.....abdallah trouble maker,muje dai inga suprise din nan da aka hanani sakat,amma ka tabbata indai bai kai ya kawo ba to zan ck tararka''
''na amince,amma mami idan ya kai ya kawo din fa,me ni kuma za?a bani?''
''sai abinda naga ya dace....''
''zoben daddyn dake gunki kadai nike so''
hara rarshi tayi lokacin da take tura qofan bedroom din nata
''kayi kadan yaro,gwara ka fadi amount na kudi in baka da na baka wannan zoben,bakasan tarihinshi bane har yau.....''

maganar ta maqale mata saboda ido hudu da sukayi da maryam,jikinta a sanyaye hankalinta a tashe ta nufeta ta kama kafadunta bayan ta zauna kusa da ita
''maryam,lafiya?daga ina?,ya akayi ika baro gidanki a idin wannan lokacin?,ina fata ba matsala bace ta faru?,ina maigidan naki?''
''gani...''taji ance,ta waiga da sauri don tabbatarwa,shaf ta mance ma tare da abdallan suka shigo sai da yayi magana
harararshi tayi
''kaga malam bana aon wasa,fice min a daki zamuyi magana''

idonshi ya kanne guda daya h
gami da daga girarshi
''wannu batu kam ai mu ya shafa mami,nima diyankin ne,nine kuma mijin diyar taki dai,tuwonki manki''yayi maganar yana zama kusa da mami hade da dora kanshi saman kafadarta suka sanyata a tsakiya

Ba don murmushin dolen da maryam ta qirqira ta dorawa allon fuskarta ba da babu shakka mami qaryata abdallah zata yi,duk da hakan sai da ta dubi maryam din
''bana son shashanci,maryamu gayan meke faruwa?''
da sauri ya karbi zancan
''ko zan miki wasa kan komai mami bazan miki kan wannan ba,idan maryam bani ta aura ba ina zan ganta ma a irin wannan lokacin naje na daukota''sai ya dawo gaban mamin yayi zaman dirshan harda lanqwashe qafafuwa,ganin haka yasa maryam itama zamowa tayi irkn zaman da yayi gabam mamin,saidai ita zuciyarta cike take da rauni,badon namijin qoqarin da take ba wajen danne zuciyar tata ba da tuni hawaye ya fallasa fa,cike da salo na iya sarrafa harshe cikin nutsatstsiyar muryarshi yace
''mami,zai iya yiwuwa kiga na miki qaton laifi,zai iya yiwuwa ma daga qarshe kice sai kin hukuntani kan maganar da zan gaya mikin yanzu,maryam bata da laifi ko daya don ni na nemi a boye abun,mun fara son juna har ta kaimu ga buqatar muyi aure,na boye miki ne mami saboda ina sane da dimbin so da qauna da kike wa tilon danki,farinciki bazaya bari idan na sanar miki ba ki kasa sanarwa da wasu mutanen ba musamman wadanda muke zqune gida daya da su wadanda bana buqatar kowa ya sani cewa maryam nake da muradin aura saboda tsaro,mami kinfi kowa sanin irin traps din da na shiga,an farauci dayuwata ba sau daua ba ba sau biyu ba kuma sau uku ba,wadansu trap din sun yi aiki wasu kuma Allah ya kareni basuyi tasiri ba,na tabbata da ansan maryam ce wadda zan aura ba abun mamaki bane wani mummunan abu ya faru da ita''

''mami...ga maryam nan ta sake dawo miki a karo na biyu,saidai wannan karon uasha banban da sauran lokutta,wannan karon ta dawo gareki da matsayi guda biyu,diyarki kuma aurukarki,nayi kwadayin ganin irin farincikin da zako shiga ta sanadiyyata ne mami shi yasa na sake dawowa da maryam cikin rayuwarmu,sanin maryam kikayi mami a fili amma a badini nafiki saninta kuma zuwa gobe zan warware miki ita don wace a sarari ki gani,ina fatan samu sassauci cikin hikunci boye miki wadda zan aura da nayi mami na''

ga mamakinsu saiga mamin itama ta sauko gabansu,hawaye ne bisa fuskarta wani na nin wani,a rude abdallah yasa hanninshi yana shate mata hawayen
''idan na bata miki mami kiyi haquri,hawayenki bala'i ne mami a gurina''
sai ta kasa cewa komai,jikinta ta janyosu gaba daya ta rungumesu
''barni abdallah na nayi kuka,kuka ne na tsantsar farin ciki ba baqinciki ba,tabbas addu'a bata faduwa qasa banza,na jima ina addu'ar Allah ya baka mace ta gari,lokacin da maryam ta shigo rayuwarmu na fuskanci dukkan halayenta na gari sai maji ina maka sha'awarta,domin hasken alkhairai da nake iya hangowa qunshe da ita,ganin hankulanku bai gamu guri guda ba yasa na fidda burin daga daina na dungumi yi muku addu'a gaba dayanku,kai har wayewar garin yau maryam ce a raina da ita na tashi har ka cimmani a kitchen tunanin maryam nake''

ta janye daga jikinsu bayan ta dauke qwallar idonta,kama hannun abdallah tayi da na maryam ta hade guri guda bayan ta dora nata a saman nasu
''na godewa Allah da irin wannan zabi da ya mana baki daya,naji dadi matuqa da kasancewarki maryam cikin zuri'ata,maryam,ga abdallah nan amana ce na baki ita har bayan raina,na baki amanar abdallah har abada,bani da kowa sai shi,ki zauna da abdallah cikin amana da aminci,abdallah kaima na baka amanar maryam,matuqar ka cuceta bayan zamowarka miji a gareta ban yafe maka ba,ku kula da junaku''abinda ta fada kenan tana jijjiga hannunsu

Duk yadda yaso ya daure sai da ya kasa,qaunar shi da maryam qarara yake ganowa cikin idanun mamin,baiso maryam din taga kasawarshi saboda haka ya kifa kanahi saman hannun mamin ya sumbata cikin dabara ya goge qwallar idonshi
''nikam na dauka mami,na dauka,Allah ya tayani riqo''
''kefa maryamu na?''ta fada tana kalllob maryam wanda kanta ke duqe take cure guri guda,abune goma da shirin suka cunkushe a qwaqwalwarta,zuciyarta na gaya mata wayo kawai abdallah yayi mata,mai yasa bata bar gidan salin alin ba tare da mami ma tasan wadda abdallah ya aura ba bare ta mata wanna kandagrakin mai daddaure jijiyoyin jiki?,zata iya watsawa mami mai dimbin alkhairai da karamck qasa a ido koko zata yarda ta zauna da abdallan ta sarayar da dukkan wani haqqi da 'yancinta da ya take,ya aureta ta sigar 'yar burum burum,zata barshi yaci nasara a kanta ya sameta a bulus ya sameta ta sigar qarfa qarfa da banga banga?,wani sashen na zuciyarta ke mata qarfafa ata gwiwar alqawari ya daukar mata,kuma ta riga da ta cika masa gabar farko na yarjejeniyarsu,bata jin kuma zai karya alqawarin

daga qasa kuma hannunta yaketa yamutsa mata cikin wani irib salo da yake sa taigar jikinta tashi saboda nata hannun na kife ne cikin nashi tafin hannun,dob samun hanyqr tsira do son cire hannunta daga nashi tayi saurin cewa
''na karba mami,insha Allahu''cikin zuciyarta tana sauya qudirin ma'anar na karba in don kada Allah ya tuhumeta

Mami dake sauri ta koma gun mutane sai gata ta rashe a cikinsu,hira sabuwa ta barke duk da maryam na rakube gefe guda,ga zaton mami surukuta ce da kunya irin wadda tasan maryam din ko da can baya da ita bare yanzun,saidai ga maryam kuwa takura ce data sanyawa zuciyarta na nemo amsoshin tambayoyin abdallah,sai ta hada amsar sai taji duka sun wargaje,idan ta kamo nan ta qulla da can sai ya tsinke,ita kanta ta rasa dalilin da ya sanyata kasa barin gidan a lokacin da ta fahimci abunda ke faruwa,dik da tana ta bawa kanta amsar cewa girma da darajar mami ne saidai ita a karan kanta take jin amsar ba gamsashshiya bace bare ta doshi abdallah da ita

''ina zuqa,bari naje kitchen indauko wayat na kira mr stephien,dinner nakeso a shirya mib sabuwa daga nan zuwa takwas na dare a compound din gidan nan''mamin ta fada ikin zumudi da farinciki tana fita daga dakin

bayan fitarta shiru ne ya biyo baya,abdalla nata qate mata kallo ba tare data sani ba don kanta na duqe ne
''sai faman duqar da kai kike kamar wata mai gajeran wuya,amma dai ba haka mukayi da ke ba ko?,sauran qiris ki wargaza wannan matakin da kika kusa kammalashi,ki tashi ki dauko drink cikin fridge ki zuba kin,ki kuma zauna agaba na har sai maki tazo ta ganmu a haka dn mu sake wanke zuciyarta''

batasan lokacin da ta dago ba ta kalleshi da oily eyes dinta ba ta balla masa harara,idanu ya lumshe yana jin wani abu na tsirga masa,ko banza buqatarsa ta biya,burinshin dama ya kalli oily and brown ayes nata wanda tun jiya rabonshi da su
''ka isa ma?''
''haka kika ce?''
''eh''ta bashi amsa kanta tsaye tana kawar da kanta daa kanshi,gyada kansa yayi cike da mamakin tsiwarta
''za kuwa kiga kalar tawa isad,ki bar gani na kodaki gaban mami na baki muhimmanci,ina iya qin sakin naki naga wanda ya isa ya sani in sake ki''

bata san lokacin da kuka ya qwace mata ba
''tabbas abdallah ya gama raina mata hankali,a daki mutum a hanashi kuka haka ake,ita da ya kamata a lallaba ita ake raina ma wayo
dauke kanshi yayi gefe guda tamkar bsi damu bs,saidai shi kadai yasan zugin fitar hawayenta da yakeji,hakan ya sashi gaggawar fadin
''Allah ya baki sa'a kici gaba sa kukan har mami tazo ta ruskeki a haka,idan tabi ba'asi kuma na warware mata zare da abawa kinga daga haka ta daina ganin girma da mutuncin mu baki daya,ni kuma naqi sakinki tunda igiyar na hannu na,qarshe kiyi biyu babu''

Jin hakan ya sanyata miqewa da hanzari kuma cikun nutsuwa ta durfafi fridge din,binta tayi da kallo a sace sakamakon yadda rigar tabi jikinta ta fidda surarta,ta ciro lemon ta dauki glass cup saman fridge,gabanshi tazo ta tsaya ta tsiyaya mishi ta miqa masa,qi karba yayi sai harara ma da ya gallamata
''kina tsammani idan mami ta shigo ta taddaki a haka kina bani abu ba zata zargi komai ba?kin min tsaye a ka kamar zamu shiga filin yaqi''
cikin qufula da hasala tace da shi wasu hawayen sabbi na bullowa
''ya isheni ya isheni fa,don me zaka dinga juya ni kamar wata waina,wannan wanne irin abu ne?''

sake dauke kanshi yayi
''har yanzu ke din a matsayin matata kike,ko babu yarjejiya tsakaninmu dole kiyimin dukka abinda nace tunda ban sakekin ba,ruwanki ne ki rusuna ki bani ruwanki ne ki bar leminki nima na riqe aure na''
ba maganar da taqi jinin ya fadeta kamar wannan,tilas ta rusuna ta miqa masa,sai da ya wani sha qamshi kafin ya karba,bayan zuciyarshi cike take fal da tausayi da qaunarta,daga shi sai Allah sukasan abinda yake ji cikin zuciyarsa

Ai kam a hakan mamin ta samesu
''a'ah me ya sameki maryam?''caraf ya karbe
''don nace ta miqon drink''girgiza kanta mami tayi tana miqar da ita tsaye
''a'sh banson sharri,bansan maryamu da qiwa ko ganda ba bare kan mijinta,halan bata da lafiya tafiyanne batasonyi ko?''ta fada tana kallon maryam,sam ita bata fahimci ma'anarta ba rashin sanin me zata ce yasanyata saurin gyada kai don shine kadai mafita
''ayya sannu,hau gado ki kwanta bari in lalubo miki magani,kai kuma banason takura ka qyaleta ta huta har ta warke,ko kuma na riqeta anan idan bakayi wasa tayi sati''

Wayyo Allah,ai duka sai a lokacin suka fahimci inda ta dosa,a tare suka hada ido ita da abdallah,wata iriyan kunyanshi da bata taba jin irinta ba ta saukar mata,da sauri taja idonta ta qulke gam,shi din na da sauri yaja qafafunshi ya fice a dakin don bazai iya hada ido da mamin ba tunda kallon da take masa kenan,ita kam ko a jikinta,cikin gurin da take ajiyar magungunanta ta duba ta fito da pain killer da paracetamol ta hado da ruwa ta kwowa maryam din
''tashi kisha kinjk marya,kada ki biyewa abdallah ya cutar da ke ba tare da kin warke ba,idan kinga ma da takura kimin magana zan maganinsh don nasan halinshi da rawar kai sarai,idan kinki jikin bai miki daidai ba ki sanar min sai a haqura da dinner din''ita dai kamar qasa ta tsage ta shige haka ta dinga ji,wannan abun kunya har ina,sai da taga ta sha ta kwanta taja mata bargo sannan ta fice a dakin

Tayi nisa sosai cikin saqe saqe da tunani taji dumin mutum a bayanta wanda sam bata san lokacin da ya shigo din ba,a zabure ta miqe zata sauka ya damqeta da hannu daya
''kiyi a hankali kada ki fama ciwon naki''ya fada cikin salon rainin wayo,kasa motsi tayo abdallah zai kasheta kam wallahi,sai kuma ya hade rai
''kikaci gaba da kuka zuwa anjima idanunku zasu kumbura,kinga idan anzo dinner sai ki tanadi amsar basu''ya miqe tsam daga gadon ya fice abinsa adakin bako waiwaye,ajiyar zuciya ta saki,sai da ya fita din sannan taji kamar ta bishi ta rufe da duka,gaba daya ma shi babu abunda ya shalleshi,babban isue da ya kamata ace yana cikin rashin nutsuwa amma ko a jikinshi.

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

Bayan ta kammala sallar magariba mami ta shigo
''yaya maryamu jikin,dinner din zai yiwu kuwa?''
kanta a duqe ta amsa mata da eh don kawar da zargin da mamin keyi na wani abu ya faru da ita,amma a zahiri ba don wannan zargin da mamin keyi ba da cewa zata yi bazata iya zuwan ba,saboda har yanzu zuciyarta cikin qunci take,nan mamin ta sakata ta shiga tayi wanka duk cikin dakin,mai makeup ta tadda na jiranta,hakanan tanaji tana gani ta zauna aka zuba mata kwalliya ta gani ta fada aka sata ta shirya cikin wedding gown irin ta larabawa fara tas mai dige digen adon zaiba kadan kadan,rolling aka mata sak irin na larabawan wanda iyakarsa saman qirjinta,hill shoes shima da earings sarqar hannu data qafa duka ruwan zaiba ne.

Kada kaso kaga kyawun da maryam din tayi,kusan duka cikin event din bikin da suka gabatar wannan itace shiga mafi kyau da tayi.

Tana zaune nan cikin bedroom din shiru kamar yadda mami ta umarceta,qofar taji an turo wanda kafin ma ta daga kanta taga waye qamshin turaren data jiyo ya sanar mata,saboda haka taci gaba da dauke ganinta daga bakin qofar,tsayawa yayi kawai ya zuba mata ido cike da sha'awa da burgewa,tayi masa kyawu fiye da tunani,bai qara amanna da kyawun da Allah ya bata ba irin yau,kasa controlling din kanshi yayi ya miqa hannunshi da nufin shafa lebenta da yaci jambaki maroon colour,har ya kusa da ita kome ya tuna kuma sai yayi saurin janye hannunsa ya daidaita nutsuwarsa hadi da cunkushe fuska
''ki tashi muje mu ake jira''
sai a sannna ta daga kai ta kalleahi cikin sakannin da basu wuce uku ba ta qare mishi kallo
eh yes ta yadda abdallah mai kyau ne,sanye yake cikin jacket mai bala'in tsada da kyau fara tas da ita komai nashi farine idan ka cire necktied dinshi takalmi da agogonshi duka ruwan zaiba kalar nata shigar sak,kau da kanta gefe tayi don bata son fiya hada inuwa da mutumin da ya yiwa rayuwarta karan tsaye
''kayi naka wuri nima nayi nawa''sunkuyowa yayi saitin fuskarta har numfashinsu na gware
''kin manta a idanun duniya mu masoya ne da mukayi auren qauna,qwarai ni airen qauna nayi amma ke da aka yiwa auren dole na fada miki dole ki ari acting na ma'abota so ki dorama kanki matuqar kina buqatar cikar burinki,wannan ne magana ta da ke na qarahe,harshe na ya gaji da yi miki tuni''

Kanta ta sake kaudawa ta yadda babu yadda zai iya ganin hawayen dake qoqarin fita a idanunta,cike da zafin rai tace
''saidai kayi dukkan abinda kaga zakayi,kaga,nifa na gaji da wanna game din naka,kawai ka sallameni a yanzu na san inda dare yayi min''
''idan anqi fa?''
ya fada bayan ya miqe tsaue ya goye hannauenshi a qirjinsa yana leqa dan qaramin bakinta dake raahin kunya
''tilas ma ka sakeni tinda nace bana so bana yi akai gaba wataqila asamu mai tayawa''

Yaji zafin maganarta amma son biye mata balle a gamu da matsalar da tafi ta baya
''lallai kam yarinya wuyanki yayi kauri,naga alama kinga makwancina da yawa,don kin samu kamar ni abdallah na nuna sonki har na aureki kikeda bakin fadin haka,kinsan kalan 'yammatan dake rububi da fatan na zame musu miji ba tare da aisin kwabo na ba ma?''
A sukwane ta juyo tamkar mai jiran ya gama fada,ido cikin ido tace masa
''ni ba irinsu bace,na sha ban ban dasu nesa ba kusa ba,baka yimin ba sam ko kusa ko alama,kuma na fada na gaya maka bana sonka bana buqatar igiyar aurenka a kaina,ka ssakeni mana dole ne,kaje ka auri masu rububin naka,idan ka taya akace ba'ayi ai sai ka matsa ga masu yi inda kake da muhalli,bawai ka tsaya ka nace a inda babu muhallinka ba''

Mamaki kam kusan kasheshi yayi a tsaye,gadan gadan ya nufota yana fadin
''ba irin mu mace ke kalla kai tsaye tace bata son mu ba duk isarta da tsadarta,bamu cewa muna so ace ba'a son mu,ni abdallah na miki alqawari sai na azabtar da zuciyarki da kalar soyayyar da baki taba yiwa wani da namiji irinta ba''bai bata damar furta komai ba ua sirute gaba daya ita da wedding gown din nata harda 'yar purse dinta marching na kayan,dike doke da zille zille ta fara tana fadin ya saketa ita ba 'yar iska bace yana sauka daga step din benen zuwa falon mami na qasa yana fain shi kuma tantirin dan iska ne sai yaya kenan?

kafin su qaraso falon tuni ta soma jiqa fuskarta da hawaye,ajjiyeta yayi saman kujera ya dora qafansji daya saman kujerar kusa da cinyarta yana huci kadan kadan,sai da ya gama qare mata kallo kana ya bude 'yar jakarta dake hannunshi yaci sa'a kuwa ya samy tissue turare da powder,cirosu yayi ua cilla mata
''ki gyara fuskanki nan da minti biyu''
cikin muryar kuka tace
''idan naqi fa?''
wani dan gajeran qayataccen murmushi irin na gefan baki yayi idanunahi sun kada sunyi ja don ta soma bashi headach bai taba fuskantar irin wanna trouble ba daga gun mace,idan suka botsare basu da dadin sha'ani saidai ka bisu ta yadda suke so ka ka musu jan ido.

''meyi baya fada,kiqi yin kiga mai zai faru a aikace kinga ai yafi dadi akan na fada miki da baki''ya sauke qafanshi ya nufi fridhe ya ciro sassanyar ruwan swan na madaidaiciyar roba ya soma daddaka,sai da ya shanye tas ya juyo inda take,tuni har ta gyara atsoronta na kada ya hanata takardarta,tamkar ya qyalqyale da dariya sai kuma ya maze yasha mur
tana shirin miqewa ya hangi igiyar takalminta ta kwance da sauri ya duqa don daure mata zata ja baya ya riqe qafan gam ya soma daure mata,lokacin mami ta ahigo tana fadin har yanzu basi fito ba me suka tsaya yi ne?,yanayin data gansu ya matuqar burgeta ta sake amanna da soyayyar dake tsakaninsu,tayi murmushi tana tunanin tana tsakiyarsu basu taba nuna mata soyayya suke ba saima fada kullum ashe ninketa suke baibai.

Compound di ya cika babu laifi da jama'a,wanda kusan rabinsu duka 'yan uwane irin mugun na jikin nan sai daidaikin maqota da abokai,tayi mamkin yadda adan taqaitaccen lokaci irin haka ma aka tara jama'a mai dan dama har haka,ko ina ka duba gurin walwali yake da decoratiom na farin yadi da wasu fararen fitilu,komai na gurin fari ne hatta da kayan mahalarta taron farine
tayi mamaki da ganin raliya da nasir lubabatu qanwarta batulu harda hindatu da jabir,to wama ya gaya musu wa ya gayyacesu?,daga sashi guda kuma nene ce da adnan sai zahariyya,idanun zahariyya da nene na kan abdallah duk wani motsi nashi suna ankare da shi,fatansu daya suga mummunan sauyi tattar da shi,yayin da adnan ya tattara nashi ma mujiyar kan maryam wanda babu abinda yake sai aukin hadiyar yawu,cikin zuciyarsa yana yiwa nene Allah ya isa da ta hanashi mallakar maryam din har abdallah ya sameta,gefe guda kuma yana tainewa abdallahn yana fadin duk taurin ranshi ne ya jawo,amma yaci alwashin da zarar burinsu ya gama cika kota tsiya kota arziqi sai ya mallaki maryam din,ko nenen na so ko bata so,kai baiqi ya kawar ma da duk wanda zaice zai kawo masa cikas ba,zubaida na gida nene ta qulleta cikin dakinsu kana ta qullen bangaren ma baki daya,ta rantse ta maya babu inda zata fito har a watse.

cikin wani irin salo mai qayatarwa dinner din ta dinga gudana,kowa ranshi fari tas cikin burgewa,tana zaune a muhallinta suka mutane suka dinga zuwa suna gaisawa da taya su murna,saidai babu daya cikin yammatan da suke son Abdallah data gani a gun,da alamu kuwa hansu zuwa gun akayi,kodai iyaye ko yan uwansu,qarfe aha daya aka taahi kai tsaye mami tace su quce bangarensu maryam taje ta kwanta ta huta.

Yana iya hangota cikin dan qaramin hasken fitilar barci takure saman gadon yayin da shi kuma ke kwance saman sofa din dake cikin bedroom din,a haka sai kayi tsammanin bacci suke saidai ko kadan kowannansu da duniyar daya shiga ita nata tunanin har yau kan amsar tambayoyinne da takeson bada su a gobe batasan ta samu failure,ya miqe ya ciro paper cikin ma'ajiyar da yake ajjiye takardu yar qarama dake can qasan gadon wanda sai ka danna wani abu take iya bullowa ya hada da biro ya dawo yayi kwanciyar rigin gine ya soma rubutu ajiki.

a qalla mintina goma ya samu kyawawa yana ruutun,a hankali yaji jikinsa ya soma masa nauyi tamkar an dora masa dutsen dala,ya sake yunqurawa da nufin daga hannun nashi a karo na biyar saidai ko alamar motsawa baiyi ba,wasa wasa sai magana ta zama babba,ya bude bakinsa da niyyar yin magan amma sai yaji kamar super glue aka saka aka manne fatar lebansa ta sama da qasa saidai.

Cikin mintina da basu gaza ashirin ba komai nasa ya daina motsi face idanunshi da kunnuwansa dake iya jin abinda ke motsi da qara baya ga haka babu wani abu dake moruwa,tuni takarda da biron hannunshi suka sulale suka fadi qasa,hannayen suka zube gefe guda,gasu a jikinsa amma ji yake kamar an cire masa su su da qafafunsa.

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶4⃣1⃣

👂🏾👂🏾👂🏾👂🏾

*shin ka/kina da labarin mutune guda bakwai da zasu shiga inuwar al'arshin ubangiji ranar da babu wata inuwa sai tasa?,ranar da rana zata matso daf da kawunun al'umma ta dinga tafasa qwaqwalwansu?,to ku matso kuji daga bakin da baya qarya*

*_An karbo hadisi daga abu hurairah R A yace:Manzan Allah S A W yace: mutane guda bakwai Allah zai saka su cikin inuwarshi,ranar da babu wata inuwa sai tasa_*
1⃣ *_shugaba adali_*
2⃣ *_da saurayi matashi ko matashiya da suka rayu cikin bautawa Allah mai girma da daukaka_*
3⃣ *_da mutumin da zuciyarsa ke rataye da masallaci,ma'ana wanda ko yaushe jira yake yaji anyi kira zuwa sallah ya tafi masallaci_*
4⃣ *_da mutane guda biyu da suka so junansu saboda Allah,don Allah suka hadu kuma suka rabu donshi ma'ana badon wani harkar banza ba ko duniya_*
5⃣ *_da mutumin da mace ma'abociyar kyawun sura tayi kiransa zuwa yin zina ko aikata wani fasiqanci yaqi yace mata ni ina tsoron Allah_*
6⃣ *_da mutumin da yayi sadaka ya boye yin sadakar da yayi har hannun hagunsa baisan me damansa ta ciyad kota bayar ba_*
7⃣ *_da mutumin da ya tunq girma Allah a kebe shi kadai idanunsa suka zubda hawaye saboda tsananin girma da tsoro Allahn_*

Duk yadda abdallah ya kai ga son motsa sassan jikin nasa bun ya faskara,ya yarda ya kima saddaqar da cewa wani mummunan abu ya gama faruwa da shi,tamkar wanda dannu ya danneshi haka yake ji
babu tsumi babu dabara sai Allah haka yake ta faman ambata

sam bata san halin da ake ciki ba,saidai gaba daya ta nemi bacci a idonta ta rasa wanda ta alaqanta hakan da damuwar dake cunkushe cikin ranta,tayi juyi kan gadon yafi a qirga,ba zata iya tantance lokacin da bacci yayi gaba da ita ba

🍃🍂🍃🍂🍃🍂

qarfe biyar da rabi na asuba ta farka daidai lokacin da wasu masallatan suka kai tsakiya a sallarasu,da ddu'ar tashi a bacci ta farka a bakinta kamar yadda ta saba sannan ta lalubi wayarta don jaska dakin da babu wadatar haske a ckinsa sakamakon kashe qawayen da akayi,sai data lalubi makunnin ta kunna sanna ta sauko daga gadon,a hankali idanunta suka sauka kan abdallah wanda zuwa lokacin ya rufe idanunsa gam zuciyarshi kawai ke aiki,ya gama amanna cewa tashi ce ta zo qarshe abinda yake jira kadai shine fitar ruhinsa daga gangar jikinsa,kamar ta wuceshi sai kuma taga bai kamata ba tunda dole dai ya tashi yayi sallah.

ta tsaya saitin kanahi cikin muryar dake nuna alamun yanzu aka tashi daga barci tace
''ka tashi kayi sallah lokacin sallah yayi,anyi asuba''jin ahiru ya sanya tayi zaton ko bai farka bane,amma wannan wace idiyar kwanciya ce haka yayi ya yada hannun?,sai ta dan duqa tana bubbugar filon da ya dora kanshi tana sake fadin
''anyi sallar asuba an kusa idarwa''

jin muryarta ya sanyashi bude idabun nashi a hankali tamkar mai tsoron ganin wani abun,sai ta dan zuba masa ido ganin yadda qwayar idanun tayi jazur,a sanyaye ta juya ta ahige toilet ta daura alwala ta fito ta tada sallah,ganin har ta idar bai tashi ba ya sanyata tayi zatob ko komawa ya sakeyi ne

kanshin ta kuma komawa ga mamakinta sai taga idanuwanshi biyu
''lokacin ta zaya fita alfijir na ahirin ketowa''
''bazan iya taahi ba maryam duk yadda naso hakan,ji nake kamar an daddaureni,ki taimakamin in tashi''abinda yake aon fada kenan saidai ina bakin yayi nauyi,ci gaba kawai yayi da kallonta,saita tsinci kanta itama da kallon nashi,lokaci guda kuma taji jikinta ya mutu murus,komawa tayi bakin gadon ta zauna ta inda take iya fuskantarsa suna ci gaba da kallon juna

kusan mintina talatin suna a haka har shida da rabi
''rana fa ta fito ba zakayi sallar bane?''sai taga ya maida idanun nashi ya lumshe,hakanan gabanta taji yayi wata mummunan faduwa,sai ta kasa zaman ta qarasa inda yake,abu na farko data fara lura da shi shine hannunshi da ya zamo qasa tunda ya farka bata ga ya gyara kwanciyarshi,ta sanya hannunta tadaga hannun taga ko zai gyara saidai tan sakinshi ya biyo ta,ta sake gwadawa har sau biyu babu banbanci
batasan lokacin data furta
''abdallah lafiya kuwa kake!''cikin tsorata da rudani
idanun nasa dai taga ya kuma zuba mata tamkar zai hadiyeta,sai ta shiga kiran sunansa a jejjere saidai ko guda bai amsa mata da shi ba

Lokacin da zuciyarta tayi mata hasashen abinda ya samu abdallahn jiri ne ya debeta ta zube a nan tana fadin
''me ya sameka?,me ya sameka don Allah abdalkah,ka bude baki ka gaya min''
inda zai iya da ya mata maganar amma babu iko

sai kuma ta zabura ta miqe da gudu ta fice a sashen nasu tayi bangaren mami

da sauri nene ta toshe bakin zahariyya da ta dan saki ihun farinciki ganin shigewae maryam bangaren mamin a hargitse
''nene Allah yasa ya sambade lahira''
''ko bai mutu ba to yana kan hanyarshi ta mutuwar''ta fada tana duban zahariyya
''don da ya kammla wucewar da ihun kururuwatsu kadai ta ishemu albishir''

saman mamin ta haura kai tsaye ta fara bubbuga qofar dakin nata ba qaqqautawa,tunda taji bugun ta tabbatar ba lafiya ba,ga zatonta ma abdallah dinne,tunda ta tashi dama takejin jikinta ba normal ba yadda ta saba jinsa,da hanzarinta ta murza muqullin ta bude qofan,kama hannun maryam tayi wadda taga tsagwaron rashin hankali kwance kan fuskarta
''lafiya maryam ne ya faru?''
fara jan mamin tayi
''mami zo kiga abdalkah,zo ki ganshi mami...''ta qarashe cikin rushewa da kuka

''Allahumma la sahla illa ma ja'altahu sahla,wa anta taj'alil hazna iza shi'it sahla''addu'ar da mami keta maimaitawa kenan fili da zuciyarya cikin sassarfa take biye da maryam suka gifta su nene dake labe jikin window dinsu suna jiran jin abinda zai biyo baya

Yadda ta barshib hakan suka sameshi,a raunace mamin ta isa gaban kujerar ta zube,gaba daya rungumoshi tayo tana kiran sunanshi,ita din ma saidai kallo da ido daga bisani ne hawaye ya gangaro daga ianunshi saboda ganin mamin nashi na kuka haiqan babu kuma baki ko hannun lallashinta,kjran sunan Allah kawai sike daidai lokacin da nene ta shigo dakin a rude kamar gaske

kallon da abdallahn yake mata ya sata tasha jinin jikinta,saidai ta nasar kawai don babu baki ko qarfin yin wani abu a kanta,tana ma sa masa tsammanin wuta zai qara zuwa lahira,
wani kallo ta jefi maryam da shi tare da zabura ta kai mata duka''me kika yi masa muguwa azzaluma''
mami ce ta tare dukan
''haba nene''cike da haqiqancewa tace
''wlh ban yarda da yarinyar nan ba bintu,daga aure jiya jiyan nan ace mutum ya kamu da irin wanna lalurar?,anya ba mayya ya aura ba bintu?''
''me ya kawo duka wannan zancan nene,muyi ta lafiyarsa ma mana''
kuka ta dinga yi haiqan tana fadin duk daren dadewa asirinki sai ya tonu shegiya mayya daga jiya zuwa yau kin lashe kurwar yaro saboda tsabar shahara a maitadaga bisani saiga zahariya da adnan,abun nasu ma sai ya zama over acting,don mamin ce ke masu suyi shiru

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

Ranar basu kwana gidan ba cikin asibitin amalam aminu kano suka kwana,cikin kwana biyar babu irin gwajin da basuyi masa ba,saidai komai ya nuna normal yake qwaqwalwarsa spinal code dinsa da zuciyarsa kai har hanta da qoda duka sai da suka duba saidai result sai yazo komai normal

A lokacin zaka tausaya wamami da maryam idan kaga yadda suka koma,duk da qoqarin boye cutan da ake saboda yanayin aikin abdallan,shi kanshi ya rame saboda tashin hankalin da yake gani cikin qwayar idanun maminshi da maryamu

cikar shi sati guda suka koma gida mami ta bada umarni ayi musu visa cikin satin zata fita da shi,kafin nan daya daga cikin manyan security dinsa mubarak wanda yake babba ne cikin masu tsaron lafiyanshi da hisham amininshi ke taimaka su mamin gun kula da abdallah,kamar daga shi zuwa toilet da sauransu,mutum ne mai matuqar kirki mubarak kamar hisham,har albashinmubarak din mami tace zata dada yace baya buqata,babu irin alkahirin da abdallah baya musu don haka bashi da abunda zai sakq masa da shi sai ta wannan hanyar,haka hisham babu komai tsakaninsa da mamin sai fatan alkhairi da sa masa albarka.

Batun fitar da abdallahn da za'ayi yayi masifar daga hankalin nene ta soma zaton kada fa a kaishi wajen ya samu sauqi haj bintu ta dawo musu da hannun agogo baya,don nene ta gama tsorata da irin kallon da abdallan ke binsu da shi duk lokacin da suka shigo duba shi
bata bata lokaci ba ta koma gun malam na hayi ta zazzage masa bakin jaka tare da qarin buqatunta

🌲🎄🌲🎄🌲🎄

Misalin qarfe sha daya ne na safiya suka gama waya da mama ta kirata don jin jikin abdallahn,tana shirin ajjiye wayar taga har sha daya da minti goma,mamaki da fatan Allah ya sa lafiya maryam din ke tayi jin shiruchar yanzu mami bata leqosu ba

mawuya cine qarfe takwas ta gita bata shigo ta dubasu ba,haka nan ba zata tafi ba sai mubarak da hisha amininshi sunzo sun gyara abdallah ita kuma maryam din ta shirya breakfasy ta gyara bangaren nasu ta miqawa mamin break din ta bawa abdallan da kanta sannan taje tayi wanka,to yau kam duka mubarak ne yayi hidimomin shi kadai ita kuma tayi saura,da taga shabiyun rana ta kusa sai ta sanya hijabinta taga gwara taje ta duba mamin,don ta tabata ko bata da lafiya ba zata iya zama ba sai tazo ta gansu

sai da ta sake leqawa bedroom din abdallah ta taddashi har yanzun baccinsa yake don ko break baiyi ba,a haka fes da shi sakamakon kyakkyawar kulawa da yake samu,sai ka rantse lafiyanshi lau,kyau dac kwarjininsa duk suna nan sai 'yar rama da yayi,tausayi yake bata sosai,ta sake girmama kadaitar zatin Allah,dan adam ba'a bakin komai yake ba,yanzu kake mutum yanzu kake ba mutum ba,duk kuwa kyau asali dukiya da kake da shi idan yaso sai ya maidaka abun Allah sarki
ta share hawayenta sannan ta fito daga sashen,sai data tsaya ta tabbatar ta qulle ko ina don yanzun bata yadda da kowa ta barshi daga shi sai abdallah idan ba mami ko mubarak ba

Ba zato taji ansha gabanta,da sauri taci burki tana dubanshi,adnan ne ya tsaya yana qare mata kallo kamar wani tsohon maye
''babe ina zaki haka?''duk wanda ya fito daga tsatson nene yanzu haka ta tsaneshi bata qaunar ganinsa,hakanan taji bata qaunar koda hada inuwa guda da su,tsaki ta ja kana tabi ta gefansa da niyyar rabeshi ta shige,sai ya sake binta ya tare hanyar yana fadin
''haba baby ki tsaya ki saurareni mana,nifq sonki wallahi nake ki bani dama mu huta abinmu,da kyaunki da komai kin tattare kanki guri daya kin batawa kanki lokaci wajen jiyyar wancan nakasashen,kada ki cuci quruciyarki mana baby,ki bani hadin kai ni kuma na miki alqawarin biya miki kowacce iriyar buqata kike da ita''.

dan ya tsanta ta nuna shi da shi
''ka bani hanya na wuce malam ko baka ji ba''
''common baby ki.....''
batasan lokacin da ta daga hannu ta tsinka masa mari ba cikin zafi da huci tace
''ni ba irin matan da kake tnani bace,hakanqn ni ba butulu bace irinku,nakasashen mijina ya fiye min kai da yan uwanka kai da duka ma danginka,daga rana irin ta yau kada ka kuma kuskuren tarata da banzayen magnganu irin wadan nan,banza shashaaha bani hanya na wuce''
''ni kika mara,wallahi zaki san ba'a ja da ire irenmu,zaki san kin sanya hannunki kin mari adnan''
''na marekan,sai me,na mari banza na mari wofi?''ta fada bayan ta masa wani kallon banza ta kewayeshi ta shige gun mamin

Baaba uwani kawai ta taras itama tana qoqarin fitowa akitchen da alamu wanke wanke ta gama,suka gaisa a mutunce tana tambayarta mai jiki,ta amsa mata da sauqi kana ta tambayeta mamin
''hajiya tana sama,nima tun jiya da yamma rabina da ganinta,tace dqi da yammacin jiya kanra na mata ciwo zata ta kwanta,to tunda ta hau kuma har yanzu bata sauko ba''
''bari na dubata to,Allah yasa lafiya''inji maryam wadda ta fara taka benan
''ameen,kice ina mata sannu''inji baaba uwani dake ficewa daga sashen
''zata ji''

knocking tayi ya kusa goma kafin taji cikin murya kamar ta fada fada ance waye ne?''a sanyaye tace maryam ce''
ta kusa minti talatin kafin ta bude qofar bedroom din
mamin ce fes da ita ikin lace da alama bata dade da gama wanka ba saidai babu make up a fuskarta kamar yadda taje a hade kamar wadda aka aikowa da labarin mutuwa ,kusan zata iya cewa bata taba ganin kwatankwaci yanayin a gun mami ba,kullum cikin fara'a take.
fuskar maryam qunshe da murmushi ta dan rusuna tana gaida mamin,duk da adaqile take amsa mata bata kawo komai cikin ranta ba,tayi tsammanin ciwon kan ne ke damunta

Shiru ne ya ratsa tsakani bayan ta gama gaishetan
''wai lafiya malam kin min tseye a gaba na?''ta fada cikin sautin fushi
a tausashe tace
''ah.....dama ji nayi shiru baki shigo ba,shine nae bari inzo in duba ko lafiya,ga abdallah ma baici abinci ba saboda rashin shigowarkin''
''banga damar shigowar bane,ni baiwar idan ubanku ce,siyata kukayi da zanta muku bauta,ok....na ganoki ma,wato bani da lokaci sai naku ko?,to kada Allah yasa ahima yaci abincin kinibabbe,ruwansa ne daga yau kada ya kuma cin abinci a duniya,ni da zaya mutu ma da bai hutar da muta ne ba,mtswee aikin banza shine kika zo kika taahi mutane suna cikin hutawatsu,to wannna ya zame miki na qarshe da zaki sake takomin saman ma,duk abinda kuke buqata ki tsaya daga qasa har sai na sauko,kinji na gaya miki''
daga haka ta ja qofarta ta bame ta bar ta anan

tamkar gini haka maryam ta koma,mafarki ne koko gaske,almara ce ko tatsuniya ce,ji tayi wasu hawaye masu dumi na sauko mata,batasan sanda ta tsinci bakinta na furta
''ya Allah kada ka jarrabemu da wata jarabtar ta daban bayan wadda muke ciki,ubangiji idan ka saka mana wannan cikin sabuwar karrabar da zaka mana ba zamu iya jurewa ba nida abdallah,ya Allah sassaucinka muke nema''bibbiyu ta dinga gani a haka ta bar bangaren zuwa nasu,tafi qarfin minti talatin zaune afalonsu tana rasgar kuka
wanna wace iriyar jarrabar rayuwa ce da suka wayi gari da ita da safen nan,anya ma kuwa da mami tayi magana?,mamin abdallah fa,mai tattali da qaunarshi akoda yaushe,mai son ganin farinciki da walwalarsa,mamin da tasha bata amanar abdallah,tasha gaya mata bata da kowa sai shi ta kula mata da shi bata so ta rasashi yadda ta rasa mahaifinsa

cike da tantamar ba mamin bace ta dauki wayarta ta kira number dinta don ta tabbatar,saidai dagawar farko ta kuma cin karo da muryarta tana fadin
''wai nikam sa'arki ce maryam?,lallai na sakar miki da yawa kinga gadon barcina,sai na dauki tsatstsauran mataki a kanki kamar yadda nene tace''jin sunan nene kawai data ambata ya sata dauke wayar daga kunnenta tana kiran sunan Allah,tabbas akwai wani abu na daban dakeaon kunmo kai
''Allah na roqekakoma meye ka kawoshi da sauqi ya arhamar rahimeen''ta qarasa fada tana rufe fuskarta da tafin hanunta hadi da rushewa da kuka

kiran sallar la'asar ya fargar da ita abdallah data bari,da sauri ta miqe a rude ta tura qofar dakin ta shiga,yanayin fuskarsa kawai ta kalla ya tabbatar mata ya gaji da kwanciyar,sai tausayinsa ya kamata,da sauri ta qarasa kan hadon cikin rawar murya
''kayi haquri don Allah,mun barka kai kadai wallahi ma.....''
maganr tata ta katse saboda yadda taga ya zubawa fuskarta ido,tamkar mai son tambayarta abinda ya sanyata kuka,sai a lokacin ta tuna da hawayen fuskarta,kawar da kanta tayi gefe tana qoqarin boye damuwarta,kusan minti biyar kafin ta dawo da kallonshi saiai har yanzu ita din yake kallo,data fuskanci tambaya ce yake mata sai ta girgiza kai
''ba kuka bane abu ne ya fada min io kuma daga nan sai ma dauro alwala da yaqi fita....bari na kawo maa abincinka''ta fada tana miqrwa da saudi ta fice adakin yayin da ya bita da kallo zuciyarshi cike da wani abu dake masa yawo ko ina cikin jininshi

Da qyar ta iya jingina ahi da fuskar hadon ta tattare si da filota zauna dab da shi har cinyarta na gogar tasa,ya lumshe ido cikin zuciyarshi data zame masa abokiyar tadi yake fadin
''so bala'ne,duk cikin yanayin da kake baya barinka ka huta?''
''bismillah karbi''yaji tana fada saitin kunnenshi,tsigar jikinsa ta tashi,a hankali ya bude idonshi ya sake zubasu a kanta,yana hango bacin rai da tashin hankali qarara kan fuskarta,da yana da baki zaiso ya tambayeta yaji me ya sameta?,bai taba tunanin zata ci gaba da zama da ahi a yadda yake ba,yayizaton a washegarin randa lalurar ta sameshi zata hada yanata yanata ta qara gaba ko babu takardar saki,kwatankwcin yadda yaji wasu matan nayi ga mazajensu idan lalura ta samesu,wasun su kun hayayyafa ma tare amma basu iya zama da kai da,bare su da kwana bihu kacal sukayi a matsayin ma'aurata.

kallon taga yayi yawa
''ka karbi abincin''a maimakon taga ya karba sai ya juyar da kanshi yana duban bakin qofa,hakan ya nuna mata mami yake son gani,hakan sai ya sake karyar mata da zuciya,ta sani mawuyaci ne ya karbi abinci idan bai ga mamin ba,saboda haka ta ajjiye cokali ta kuma daukar wayarta cike da fatan ta samu sauyawar yanayin mamin
''mami ya farka yaqi ya karbi abincin keyake jira''
''ke!ke fita daga idona,wai shin komayyar ce ke da gaske?,to wallahi zan ci iki mutunci fiye da zatonki,ko rayuwarku wajibi na ce,kuje kuji da kanku kada ki kuma kira na na gaya miki''daga haka ta katse wayar,hada idanu sukayi da abdallan da alamu yaji wani abu cikin abina mamin ta fada,mutum ne mai kaifin ji,hadiye kukan da yake taso mata tayi ta kuma diban abincin a cokali ta miqa masa tana fadin
''kayi haquri ka karba,anjima mamin zata zo kaji''

🎄🌲🎄🌲🎄

wasa wasa abun sai ya zama gaake,tun ranar data yi shigowar qarshe mami bata sake waiwayarsu ba,sam ta mance da su ma baki daya,gaba daya an canza mata alqiblar rayuwa,kusan gidan ma baki daya ya koma hannun nene sai abinda ta shimfida wa jama'ar gidan ciki harda mamin,a hankali a hankali suka dinga karbar takardun lamfanoni filaye gidaje da duk wata plaza na abdallahn daga hannun mamin,ba tare da musu ba haka zata dauka ta damqa musu

hisham baisan halin da ake ciki ba,bai an kara ba sai da yake duba kamfanin yin flower na abdallahn ya tadda adnan dare dare kan kujerarshi kamar wanda ya gada daga gurin ubanshi,da ya sami mamin ya mata maanar ranar ya ga bala'in da bai taba gani ba gurinta,har da ja mishi kunnen matiqar bai dauke idonhi daga lamuransu ba zata sa ahanaahi shigowa gidan kamar yadda tasa aka hana duk wani dan uwanta ko na maryam zuwa gidan,tilas ya ka bakinshi on ya san daina zuwanshi gidan ba qaramin tagayyra zai haifarwa abdallah da maryam ba,ya dai cika da mamakin canzawar mamin lokaci guda,tsana nin biyayya da bi sau da qafa da takewa nene

🎄🌲🎄🌲🎄

Sau biyu tana leqowa taga ko bacci ya daukeshi?wanka take son tayi ta sauya kayan bacci ta kwanta,a karo na uku ta tadda idanunshi ruf alamun ya samu bacci kenan,ta jima tsaye akansa tana qare masa kallo,a hankali ta sanya hannunta cikin tattausan sumarshi,yana buqatar a rage masa ita saidai bazai iya magana ba,cikin ranta ta qudirci gayawa hisham gobe ko zai iya masa yana da clipper tunda ita bata iya ba,jin ya motsa ya sanyata saurin janye hannunta tsoronta kada ya farka,sai da taga ya bar motsin kana ta tofa masa fatiha da yatul kursiyyun da take yawan tofa mishi akai akai ta juya ta isa bakin cupboard dinsu ta soma cire doguwan rigan jikinta

a hankali ya bude idanunshi ya zuba mata ido duka batasan me akeyi ba,ta janyo towel ta daura tayi banaki,ya lumshe idona wani dan murmushi ya subuce masa,maryam maryam bai san maryam ba sai yanzun,yanzun ne yasan maryam,cikin tunaninshi yaji tana qoqarin itowa ya maza ya maida idanunshi ya lumshe,yana iua hagota tana shiryawa tsigar jikinhi na tashi,ji yake ina ma yana da lafiyar da zai nuna mata irin soyayyarta dake danqare ciki zuciyarshi,har ta kammala ta zura rigar baccinta ta dora dan hijabinta a kai

Bata taba yarda ta kwanta kan gadon matuqar idonshi biyu,sai bacci ya daukeshi take lallabowa ta kwanta ga tsammaninta duk bai sani ba,saidai data kwanta din ko cikin bacci yake zai farka saboda wani dumi na musamman yake ji daga garta,yau din ma lallabowa tayi ta kwanta gefanshi bayan ta gama qare masa kllo kamar yadda ta saba,a hankali gajiya ta mamayeta,bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita,a irin wannan lokacinne shima yake samun damar qare mata nashi kallon,yakan tsinci kansh ciki wani irin nishadi a lokacin
ya daga hannunshi da niyyar janyota cikin jikinshi ya kusa sau goma amma ya kasa,ya saki nannuyan ajiuyar zuciya yanajin radadin hakan cikin ranshi.

cikin sa'a tayi wani juyi tashin farko sai gata cikin jikinshi,murmushi yayi yana godewa Allah tare da dora kanshi saman kanta,duk da hijabin jikinta hakan bai hanashi jin dumi da qamshinta ba
sannu a hankali sai kuma ya dinga jin motsi kamar ana hawowa saman da suke,yaci gaba da kallon bakin qofar don ya tabbatar yau maryam tayi mantuwa bata rufe qofofin ba,idanunshi fes kan qofar yaji an turo an shigo,tashin farko aka dallare dakin da fitila mai tsananin haske kai tsaye hasken ya iso har inda suke
''wal masakinu bakayi bacci ba?''yaji an fada kana aka kunna duka qwayayen dakin,fuskar adnan ta bayyana
''gwara ma da bakayi baccin ba ai kaga ka gani da idonka tunda gani ya kori ji ko?,yau zan cika burina,zan kwanta da matarka agabanka,zan cusa maka baqinciki abdallah irin wanda na dade ina sha akanka,ka fini kyau,ka fini matsayi ka fini kudi ka fini nasaba hakanqn ka fini farinjini,yau zan kuma nakastaka kafin lokain da muka diba maka na mutuwarka ya cika,kabi bayan tsohonka ku hade acan kafin tsohuwarka ta biyoku''

gadan gadan ya hauro gadon yasa hannunshi ya janyo maryam dake jikinshi wanda hakan ya sanyata farkawa afirgice,ba qaramin kaduwa tayi da ganinshi cikin dakinsu ba cikin takiyar dare,bata ankara ba ya sabule hijabnta ya wurgar take gashinta mai tsaho da santsi ya warwatsu,runtse idonshi abdalah yayi yana jin tamkar an ciro zuciyarsa ana tststsagata,kamar an karata kusa da tukuba turiri kawai take maa,ya bude idonshi yaga yadda ake dambe tsakanin adnan da maryam,gashi kwance bashi da ikon tsinana komai,qoqari yake na daga hannunshi saidai hakan ya faskar,ihi yakeso ya kurama na baqinciki da takaici amma ko bakin ya kasa motsawa,sai ya koma kiran sunayn Allah ciin zuciyarshi tare da yunqurin motsa hannun nashi

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶4⃣2⃣

*assalamu alaikum warahmatullah,zuwa ga masoyan ABADAN,kamar yadda aka saba 😄 duk lokacin da littafi ke tafiya readers kanyi qorafi kan wani abu da ya shafi jaruman cikin littafin,wannan karon ma hakan ta faru,abinda nakeso ku sani shine bangaren rayuwar maryama true life story ne banbanci shine ita wadda abun ya faru a kanta kishiyar uwa ce ta mata hakan ba kishiyar suruka ba,hakanan na samu saqo daga gurin daya daga cikin makaranta ita kuma bangaren abdallah ne ta sani a gaske ya faru da wani da ta sani,kada ku manta babu yadda Allah baya iya jarrabtar bayinsa,gwargwadon imaninka da Allah gwargwadon girman jarrabawarka,na yarda da addu'a fiye da zaton mai zato☝🏽don ta yimin rana ta bani kariyar da har a nade duniya babu wani abu daya isa yamin kwatankwacin abinda ta yimin,na gani a zahiri na gani a mafarki,a rayuwa babu dole a lokacin da ka roqa Allah ya baka a take,yana iya jinkirta maka gwargwadon yadda yaso,kuyi haquri kuci gaba da bin littafin a duk yadda yazo muku don mu samu cimma manufofi da alfanu da gaci da nake son kaiku,idan kuma abun na damunka 😂,a shawarce ka tara littafin har sai an wuce inda baka son ji sai ka ci gaba da karatunka hankali kwance,na gode matuqa da gaske don nasan duka qauna ce,nima ina qaunarku a duk inda kuke,MRS MUHAMMAD DINKU CE*👑

Ji yake tamkar ya kashe adnan,bai kuma jin ciwon lalurar data sameshi ba irin yau,saboda ya riga da yayi amanna dukkan wani abu da zaya samu bawa da sanin ubangijinsa,hakanan bazai jarrabceka ba tare da wata manufa da take alkhairi ce a tattare da kai
bai gaza ba ci gaba yayi da ambaton sunan Allah cike da neman agaji don yana jin cikin zuciya da gangar jikinsa matuqar wani abu ya faru da maryam mutuwa zaiyi

a gigice ta sake dawowa jikin abdallan ta maqale shi tana neman agaji ta cukuikuye jikinta ta dunqule guri guda,tsabar gigita ta mance da halin da abdallan yake ciki,cikin dariyar mugunta ya biyota,ya tsaua a gabansu dukkansu ya qare musu kallo kana yace
''kin daga hannu kin mare ni ga zatonki kin ci bulus?,bakisan dama na jima ina sha'awarki ba hanyar kawar da ita kawai nake nema?,sai gashi yau Allah ya ara min dama ta yaya zan yi sake ta kufcemin''
ya kalli abdallah da idanunshi suka kada suka koma jazur,dukkan wata jijiya ta kanshi ta gama fitowa rada rada
''hmmm,sarkin zuciya,ka qaraci quncin zuciyarka amma babu abinda zaka iya yau sai na cika buri na''ya sake yin kanta gadan gadan,ya miqa hannu da niyyar damqota
cikin qaraji da kuka mai quna tace
''kaji tsoron Allah,yana kallonka,yana kallin duka abinda kake aikatawa''

ga tarin mamakinta sai taga ya qyalqyale da dariya
''ki bari idan na kammala sai ki gaya min duk abinda kike son gayamin,amma a yanzu babu abinda nake ganewa kinji ko''
ya sake yunqura zai fincikota yayib da take sake lacewa jikin abdallah kamar zata koma cikinsa
cikin hikima ta ubangiji hannun sa bai qarasa kanta ba yaji saukar wani abu mai azaba a qeyarshi,ga mamakinsa ya juya don yaga wanda ya masa wannan aika aika,abdallah ne yana daga kwance yaji tamkar an kakkatse duk wani abu daya hana hannayenshi biyun motsi,cikin hikimar Allah ya bashi sa'ar janyo plate din tangaran da maryam ta zuba abinci dazu Allah ya sa mata mantuwa bata dauke shi ba,don bata barin kwano ko daya ba'a muhallinsa ba ko ba'a wanke ba

sai kuma ya juyo yayo kan abdallah,saidai ina tuni jini ya fara dibarsa ya sona tangal tangal,ganin gaka ya sa maryan saurin maida hijabinta,qofa taje ta bude ta dakin kana ta dawo ta dinga tura adnan da ragowar qarfinta tana hankadashi yana dawowa amma da yake jini yaci qarfin sa sai ta samu nasarar tunkudashi har qasan benan yana qoqarin biyota ta dawo benan a guje ta datse qofar falon kana ta shige bedroom din ma ta saka muqulli tana maida numfashi

babu abinda qirjinta yake sai dagawa sama da qasa kamar numfashinta zai dauke,har yazu tsoron bai saketa ba,ji take kamar adnan din zai dawo,hannu ta ga abdallah na dago mata da alamun ta taho,mafaka take nema ibda zata sanya kanta taji sanyi,inda zata sanya fuskarta tayi kuka,babu musa ta isa gadon cikin sassarfa ta hada jikinsa da nata,cusa kanta tayi cikin qirjinsa wani kuka ya qwace mata

shafa kanta kawai abdallah yake yana hadiyar zuciya,godiya yake ma Allah maras adadi da ya bashi damar tserar da mutuncin iyalinshi,maryam ta riga da ta zama jinin jikinshi,sukan qirjinshi kukanta yake,saidai babu bakin hanawan babu kuma cikakkiyar lafiyar rarrashi,a hankali ta dinga jin nutsuwarta na dawowa,ta dinga sauke ajiyar zuciya kadan kadan
hannun abdallah ta tuna taga yana motsi dazun,a hankali ta zagaya hannunta ta saman cikinsa ta laluba dayan hannun abdallahn,tafin hannunta ta zura cikin nasa ga mamakinta sai taji ya sanya yatsunsa cikin nata ya hade hannayan nasu gam,wata sassanyar ajiyar zuciya ta saki
''alhamdulillahil lazi bini'imatihi tatimmus saalihaat''ta fada cikin zuciyarta tare da rufe idanunta,wani farinciki taji yana ratsata,atleast tasan cewa wani ci gaba ya fara samuwa game da lafiyar abdallahn
dukkaninsu a daren babu wanda ya iya runtsawa,zuciyoyinsu tamkar anyi gobara kada ma abdallah yaji labari,ita kam takan samu sassauci kadan duk yayin data motsa yatsunta dake cikin nasa wanda yaqi sakinsu taji nashi hannun ya motsa

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

zaune yake gabanta qasan carfet din dakin kansa nannade da farin bandeji,zahariyya na agefansa saman kujera nene na kusa da ita ta zubawa danan ido
''adnan,wanne irin mahaukacin yaro ne wai akau,sau nawa ina gaya maka ka fita hanyar yarinyar akwai lokaci ka bafi idan yazo sai kayi duk abinda kake buqata?,yanzun inda ta samu dama kasheka fa zatqyi?,baka lura da irkn yadda take mana wani irin kallo ne,dukkan zarginta ina mai tabbatar maka ita da abdallan a kanmy yake don babu bakin magana ne''

cikin fushi ya dago ya dubi nene
''to wai nene ke wanne mataki kika dauka yanzu,na rantse da Allah ba za'a zubar min da jini a banza ba''wani shu'umin murmushi ta saki
''ni yanzu duk wani mataki nawa nafison abdullahi ya wuce tukun shine babbar matsalarmu,yaron ne shegen taurin ran tsiya kamar kyankyaso.....amma yanzun bamu da nutsuwar da zamu tattauna wanna batu ku tashi kuje jibi zamu zauna,na kira malam na hayi yace baya nan sai jibi zan kira shi naji mataki na gaba,zan sanar da bintu abinda yarinyar tayi don bani da burin da ya wuce ta sata ta bar gidan saidai abun mamaki duk irin aikina bata kudina da nake taqi sallamarta hakanan ko ma samu sauqin tafiyar da aikin....''

itakam zahariyya ma kasa cewa komai tayi
''amma fa nene,naga hannun abdallah ya dawo aiki''ya fada yana kallon nene,da sauri zahariyya ta tashi zaune daga kashingidar da adazu tayi tana kallon fuskar nenen tana zazzare idanu
wani murmushin ta kuma saki tana girgiza qafa
''ko duka jikin abdallah ne ya dawo aiki wanna karon naci alwashin abdallah bazai qara sati guda araye ba,don nima......''
tilas suka katse maganar kowa ya watse sakamakon shigowar zubaida dakin
nenen ta bita da kallon mamaki don tayi zaton ciwon ABDALLAH zai sata a wani hali sai ta lura ma sam tunda ya fara cutar ko hanyar part din bata yi,hankalinta kwance kamar bata da wata damuwa da shi,hakan ba qaramin dadi ya yiwa nenen ba

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

Su uku ne cikin bedroom din,hisham da abdallah sai maryam dake zaune kan ressing chair data janyota bakin gadon inda abdallah da hisham ke kai hisham na bawa abdallan kunun gyada bayan masa wanka da canza kaya da aka masa ckkin baqin t shirt da trouser da suka sake haska shi

farinciki ne fal zicjyar hisham sakamakon ci gaban motsa hannun da abdallah ke iyayi yanzun,yana bashi kunun suna hirar da maryam duk da nata bai wuce eh ko a'a,ba gwanar magana bace ama sanann bugu da qari kallon da abdallan keta tsareta da shi ke dada takura ta,wani kallo ya koya daga wayewar gari zuwa yanzun,duk wani motsinta na kan idanunshi,lafiyarta yakeson ji amma babu bakin tambaya
''kai man,irin wannan kallo haka ko na baku guri ne?''inji hisham yace da abdallah cikin zolaya,kallonshi kawai abdallan yayi ya saki murmushi,duk sai suka zuba masa ido don tunda ya fara ciwon wannna ne karon farko da suka ga murmushi kan fuskarshi

cikin dariya hisham yace
''kai mutumina,anya daren jiya ba soyayya aka sha ba kuwa?''kunya ta kama maryam ta duqar da kanta ,yayin da abdallah ya sake wani murmushin yana duban fiskar hisham bisa dukkan alamu akwai abinda yake son fada wanda ya kasa fada
''Allah ya baka lafiya abdallah''inji hisham yana dafa kafadanshi,ya dubi maryam
''me kikace dazu yana buqata?''
kanta na sunkuye tace
''shaving za'a masa,naga kanshi yayi suma da yawa''
ya dan duba agogonshi ''eh gaskiya ya kamata,bari na masa na kai ke sqi kiyi masa na fuskanshi''
''ai ban iya ba''
''eh,ya kamata ki koya madam,zan nuna miki,akwai meeting da zamu shigavda ma'aikatan kamfanin suger na abdallah,don ina tsammanin gwara kawai a rufe kamfanin har zuwa lokacin da zai samu alfiya,saboda barnar da ake cikin kamfanin tayi yawa''

''Allah ya taimaka'' ta ce bayan ta miqevta dauko masa kayan askin,ya kammala kana ya nuna mata yadda zata masa na fuskar ya musu sallama ya wuce ta bishi da godiya

gefanshi ta dawo ta zauna ta fara matso cream din,a hankali take shafa masa a gefe da gefan fuskarshi,idanunahi qyar cikin nata,nauyi takeji da kunyarsa duk lokacin da ya zuba mata idanunshi,a hankali ta janye qwayar idonta tana ci gaba da shafa masa din,ta kammala ta dauko shever ta fara masa askin,ajiyar zuciyan da ya saki ya sata saurin kallonshi cikin tsoro,cikin sassanyar muryarta tace
''ko na yanke ka?''murmushi ya mata ba tare da ya nuna alamun a'a ba,kusan sakanni uku sannan taci gaba,a hankali taji ya riqe hannun nata da take shaving di dashi,ta sake waiwayo ta kalleshi shima din ita yake kallo
ta langabe kai
''da zafi ko?,dama na ce masa ban iya ba.....''bata qarasa ba taji ta kan qirjinsa sakamkon janyota da yayi ya rungumeta tsam

dukan uku uku qirjinta ya shiga yi,tayi yunqurin tashi taji ya sake maidata,idanunshi a lumshe kamar yadda nata yake,dukkansu suna jin bugun zuciyar junansu da ta qara gudu fiyeda yada take bugawa,sannu a hankali taji kasala na kashe mata duk wata gaba ta jikinta,jikinta ta saki batasan yadda akayi bacci yayi awon gaba da ita kan qirjin nasa ba,shi din ma yanayin ya masa,ji yake amar ya tsaida lokaci don su dawwama a haka,tun yana jin saukar numfashinta har shima baccin yayi gaba da shi

🍃🍂🍃🍂🍃

kusan lokaci daya suka farka,da hanzarita ta miqe daga jikinsa don tunawa da cream da ta bar masa a fuska,idanunshi a lumshe yake kallonta,sai taga ya kai hannunshi gefan kunnenta ya ciro wani abu ya nuna mata,cream dinne da sauri ta dauki madubin dake hade set da shaver din ta haska,ai kuwa gashi nan ta kwaaheshi ya bata mata fuska ta dubeshi suka hada ido sai suka saki murmushi tare,dan towel din askin a janyo ta goge fuskarta ta matsa ta dauki shaver zata ci gaba da askin,dora hannunshi yayi saman nata hannun da sauri ta janye hannun nata saboda tsigar jikinta da taji ta tashi,ya karbe abun askin ta fuskanci me yake nufi don haka ta dinga haska masa yana askin da kansa,idan ya gaji ya tsaida hannun nashi ya huta tunda har yanzun ba wani qwari ne da shi ba
towel tasa mai mai kyau ta goge masa fuskan bayan ya gama,tana shirin miqewa taji ya riqo hannun nata ya sanya tafin hannunshi cikin natan ya matsa su sannna ya gyada kai ta fuskanci godiya yake mata,murmushi kawai ta saki ta sunkuyar da kanta kana ta zame hannun nata ta sauka daga kan gadon tana tattara kayayyakin da sukayi amfanin da su har yanzu idonshi a kanta yake,yanayinta kadai burgeshi yake,kominta anutse cike da tsafta tausayi da kulawa,ya maida idonsa ya lumshe bayan yaga fitarsa yana addu'ar Allah ya bashi damar da zai nuna mata nashi kalan halaccin koda bata sonshi

da uammain mubarak ya kawo wheelchair da hisham yace ya kamata a fara dora abdalla atleast zai dinga jin dadi idan an fita dashi daga bedroom zuwa parlour zuwa balcony din saman tunda ba zata iya saukowa da shi ba falon qasa,yaji dadi kuwa don alamu sun nuna afuskarshi,yawanci idan la'asar tayi aka dorashi zata yita shawagai da ahi daga parlou zuwa kitchen zuwa balcony din wani sa'ilin ma ya mata alaman su zauna cikin kitchen musamman idan tana girki,ganin zaman shiru suke yi yasa tana girkin tana bashi labaraimasu debe kewa,hakan kuwa na matuqar sa farinciki a zuciyarshi,don zata ga fuskarsa ta fadada sosai da murmushi alamun yana jin dadi

saidai kallon qurillar da abdallah ya koya tilas yasa take zama da hijabi,don ba qaramin kunya yake bata ba,ko ina yaso kalla kallonsa yake kanshi tsaye,da sun hada ido kuma ya wani lumshe ido ya basar kamar bashi ba,wani lokacin murmushi take cikin zuciyarta tace
''hali zanen dutse,babu abinda ke saiyawa dan adam halinshi,har yau halin abdallah na basarwa da waskewa na nan cikin jininshi''

*mrs muhammad ce*

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶4⃣3⃣

*_An karbo daga nana Aisha Allah ya qara yarda a gareta tace:naji manzan Allah S A W yana cewa ''ya Ubangiji duk wanda aka dora mishi wani shugabancin na al'umata,ya tsananta musu Allah ka tsananta masa shima,wanda aka dora mishi wani shugabanci na al'ummata ya tausasa ya sassauta musu Alla ka tausasa masa ka sassauta masa shima_*

Qarfe biyar da rabi ne na yammaci mai cike da ni'ima da dadi kasancewar ko kusa garin babu rana sai lullumin hadari da ya lullube sama,su biyu ne zaune cikin falon yana kan wheel chair tana kan kan kujera saidai suna facing juna ne
novel ne a hannunta take karanta mishi sannu sannu cikin daddadar muryarta,tunda ta kifa fuskarta alittafin data kare fuskarta da shi bata dago ba saboda nauyin da kunyar kallon da abdallahn yake mata,gashi hakanan yaqi yarda yau a saka mashi kaya complete,duk wanda hisham ya ciro sai ya wurgar shi daminshi suke,wando three quater ne ajikinshi da riga armless duk wata qirar jikinsa ta bayyana

A hankali yasa hannunshi ya riqe littafin yayi qasa da shi tavdago kanta suka hada idanu,ido daya ya kashe mata yana murmushi don ya fuskanci abinda ya sata qin sakewar,littafin ta sakar mishi ta dora fuskarta saman cinyarta cike da jin kunya,taba kanta taki yayi sai taqi dagowa,ya daga littafin ya dan buga mata kadana akanta tare da cusa mata shi.

A hankali ta dago da zummar dauke littafin taci gaba da kare fuskarta,rubutu ne baro baro a bangon littafin I LOVE U,wani feeling ta dinga ji tana sake maimaita rubutun tamkar yau ta fara ganin kalmar,a dan sace ta rage tsawon littafin idanunta suka fito,karaf suka hada idanu da abdallahn daya zubawa cover littafin ido,tayi azamar maida littafin saidai tuni ha riqe da hannunshi daya yana ci gaba da kallonta,ji tayi bazata iya hada qwayar idanunsu ba saita sauke qwayar idanun nata kan cinyarta tana kallon yatsun hannayenta.

Qarar bugun da akayiwa qofar dukkansu sai data basu tsoro,kusan a tare suka kalli qofan,mami ce ke shigowa a burkice idanunta a kansu, qaraso gabansu ta ja burki
''sannunku qananun 'yan ta'adda,wato har kisa kuka so yimin cikin gida na ko?,to wallahi baku isa ba matuqar kuka ci gaba da yunqurin taba lafiyar wani cikin gidan nan zan iya tattarku kubar min gida tunda dai ba naku bane,kada ku kiskura ku sake aikata wani abu mai kama da haka don ba gidan 'yan ta'adda bane nan''duk maganar da take kan maruam na duqe a qasa,yayin da abdallah ya zuba mata ido cikin qunar zuciya da tashin hankali,me ya sami maminshi haka?me ya canza masa mami?,mamin da bata qaunar taa ko sauyawa fuskarshi tayi,mami mai tattali da qaunar farincikinsa,mami dake qauqnr maryam ta dauketa tamkar diyarta ta cikinta

ta kalli maryam''kuma ki gaggauta zuwa ki nemi yafiyar nene da danan idan ba haka ba wallahi sai na wulaqantaki,idan banda ma ke butu ce shegiya mara mutunci daga zuwa ya duba lafiyar mijinki sai ki masa irin wann mummunar sakayyar,na baki nan da minti talatin kije ki basu haquri''ta juya zata fota suka hada ido da abdallqh,hara ra ta wurga masa saboda jin wani abu na son taba zuciyarta,sai kuma wani abu daga can daban ya taso ya danneshi

shiru ne ya ratsa falon bayan fitarta,dukkansu kansu na sunkuye zuciyoyinsu na saqa musu abubuwa mabanbanta,ganin ya kusa gota mibti talatin din da mami ta bata ya sanyata miqewa da sauri,hannunta taji an damqo,ta waiwayo sai taga abdallah ne,a hankali ya dao idonsa suka hada ido,da sauri ta kawar da kanta saboda tashin hankalin da ta gani cikin qwayar idanunshi basu musaltuwa,fararen qwayar idanunshi sun juye sun koma ja baya ga jijiyar kanshi da ke tashi,kai ya girgiza mata alamar ba zata je ba,itama kan ta girgiza kana ta dawo gabanshi ta durqusa tace
''kayi haquri ka bari inje din,umarnin mami nake qoqarin cikawa ba donsu zani ba,kada ka manta har yau mami na matsayin uwa ne a garemu kaga ya zama dole mu bi umarninta don gamawa da duniya lafiya indai ba ya sabawa addini ba''

shiru yayi ma wasu 'yan daqiqu kana ya daga mata yatsunshi guda biyar alamun minti biyar ya bata,guada kanta tayi sanan ra miqe ya bita da kallo har da fice

tana gab da shiga waitin falo inda anan qofofin bangaren nau yake ta hango adnan,muta ne uku ne zabga zabga baqaqe,cikin baqin kaya masu qirar samudawa biye da shi,kallo daya zaka musu ka tabbatar cewa babu masaukin imani cikin zuciyarsu,mamaki ya cikata duk da tasan cewa lokaci lokaci zaka ganahi da ire iren mutanen a matsayin abokanshi,sai ta kasa wucewa ta rakube har suka wuce,tazarar minti biyar ta bada tasan zywa lokacin sun shiga koma ina zasu ahiga sannn tabi bayansu,a qofar waiting parlour din suka kusa karo da mami wadda ke sanye da kayan aiki da alama asibiti zata fita taja da baya ta bata hanya,harara ta watsa mata mamin kana ta fice,girgiza kanta tayi kawai tabi ta da kallo,kallo daya zaka mata ga wanda ya santa yasan cewa ta canza,tsaftarta har yanzu tana nan saidai duka gayun nan babu shi,bata mantawa shekaran kiya doctor safara'u abokiyar aikin mamin ta kira maryam take tambayarta me yake damin mamin ne,kullum tazo office bata da aiki sai kuka,tambayar duniya kuma ba zara gaya maka abinda ke damunta ba,magana daya zata gaya maka shine babu komai

Ganin babu kowa cikin falon qasan ya sanyata nufar sama,tana atep din qarahe na matattakalar ta soma jiyo maganganu,tamkar an dasata agun ta kasa gaba ta kasa baya
''yace saidai mu mu qarasa aikinmu,dalili kenan da yasa nace ka nemo min su mugu,wanna karon zamuyi aikin qarshe kan abdullahi,jibi da daddare nake so ku kashemin abdullahi,kafin ranar zansan duk abinda zanyi na kori yarinyar daga gidan nan,idan kuma tayi taurin kan qin tafiya na baku dama ku hada harda ita....''
''haba nene haba nene,ya zaki ce a kasheta bayan kinsan qudirina akanta...''adnan ya katseta
''dakata min adnan,wanna karon bana son matsala kowacce iri ce,mata gasunan bila haddin,koda an kasheta da zarar ka samu 'ya'yan banki kana iya samun dubunta ka huta da su ko ka auresu,mubar wannan maganar''

bibbiyi ta dinga hada matattakalar benan tana saukowa,badon nutsawa da sukayi kan maganr ba da babu abinda zai sanyasu jin takun saukarta,saidai ina dukkansu hankalin yayi gaba,a inda ta bar abdallah ta tarar da shi,a hankali ya dago kai yana dubanta,gqnin irin birkicewar da tay ya zuba mata ido kamar mai tambayarta,cikin rawar jiki ta tura whewl chair din suka ahige brdroom ta maida muqulli ta rufesu,jikinta na rawa ta dauki wayarta,ta fara qoqarin neman numbers dib hisham saidai bata yi sa'a ba ta samesu a kashe,bakin gadon ta koma ta dafe kanta ta fashe da matsanancin kuka,tana kallon abdallah na daga mata hannu saidai ta kasa ce masaa komai,tausayinsu su duka biyin ya lullubeta

Misalin goma na dare ta samu wayar tashi ta shiga,da sauri ta fita adakin ta canza daki don bata son abdallah yaji komai,shi,kansa da baisan meke faruwa ba hankalinshi a tashe yake tun dazun fuskarsa ta nuna,bata jira jin komai daga bakinsa ta fara fada masa abinda ke faruwa
innalillahi wa inna ilaihi raji'un kawai yake furtawa,tabbas zarginsa ya zama gaskiya
''ki saka nutsuwa afuskarki maruqm,kada ki sake ki nuna musu kiji wani abu,yanzun haka ina kaduna amma gobe qarfe biyar da rabi na asuba zan taho,insha Allahu duk inda goma na safe yake ko tara na iso kano,na miki alqawarin babu abinda zai sameku,a gobe zan fiddaku daga cikin gidan insha Allahu''

Yadda ta kwana tana sallah haka ya kwana akan whellchair yana kallonta,cikin jikinshi yake jin wani mummunan abu na tunkaro su,yanayin data shiga kadai ya isheshi amsa,sam yaqi yarda ma akwantar dashi,da safe saiga nenwn zahariyya harda danna wai sunzo duba abdallahn,yanayin fuskarta idan ka kalleta dik qwaqwarka ba zaka tsammaci gana cikin mummunan tashin hankali ba,ba qaramar jarumta ta nuna ba,haka suka qaraci kallonau suka fice maryam ta bisu da ido cike da mamakin qarfin hali irin nasu

mubarak ma da yazo sam qin yadda abdallah yaui ayi masa wanka,abincin ma da qyar ta samu yaci,ya fahimci manufarsa yana son jin abinda ke faruwa ne a ganinta kuma bai kamata yaji din yanzu ba

🍃🍂🍃🍂🍃🍂

yana kan wheelchair din yatsunsa soke cikin na juna yana kallon su
tsaf hisham ya gama hada duka wani atm card takardun companies filaye gidan gonaki da na duk wani estate da plaza na abdallan ya sanya cikin wata jaka baqa ua zuge zif din,maryam yasa ta ciro babban bargunan dake ninke gefe daya kan gadon,ya jera dukkan filallukan dake kan gadob ya lullubesu da bargon take suka tashi kamar mutum kana ya qarasa inda abdallah yake da niyyar sauko da shi daga kan wheel chair din

qememe abdallah yaqi yarda ya sauko da shi din,idanunahi sun kada sun koma tamkar gauta saboda tsananin fushi da masifa,jijiyoyin kanshi dana wuyanshi sin fito rada rada,ua fahimci abinda abdallan ke nufi saidai bazaiyiwu suyi masa abinda yake so ba,a tausaahe ya dubeshi
''abdallah na sani sarai tun ba yau ba kai din jarumin namiji ne ba rago ba,kaga abubuwan masu hadarin gasje ka shiga wasu da dama daga cikinsu,amma a yanzun abdallah bazai yiwu mubarka ba rayuwarka na cikin hadari,da ace yau lafiya qalau kake abdallah bazqn maka ahishshigo ba saisai na taya ka da ddu'a ko kima idan ka buqaci taimakona,nayi imanin da lafiyarka qalau ka fini experience na yadda zakqyi aolving case din,amma ayanzun haquri zakayi abdqllah dole kana buqatar taimako''

A nutse kuma ahankali ta tako gabanshi ta taugunna,hannunta ta sanya cikin tafin hannunshi ta mannesu tare hisham na gefe yana kallonsu,lumshe idonsa yayi,kimanin minti goma suna a haka sanna tace cikin tattausan muryarta
''kabi hisham mu fita daga gidan nan abdallah,ni maminka hisham dama qasarka baki daya duka muna buqatar rayuwarka,bama so mu tasa ka bamason muyi asararka abdallah don Allah''

cikin jikinshi babu inda maganarta bata shiga ta tsinka masa jijiya ba,ina ma ace zaya iya hude baki yayi magana,da banu shakka zai tambayeta ne daga zuciyarta kalaman suka fito ko ko iya labbanta ne,koma dai yaya ne ta sanya zuciyarsa cikin wani kundi mai wuyar karantawa lokaci guda,bai taba jin kalamai makamanta wadannan daga bakinta sai a wannan karon,a nutse hisham ya sauke abdallah daga kujerar ua ahimfidar da shi cikin bargon har a lokacin idanunshi na kan maryam dake tsaye tana kallonsu cikin raunin zuciya,yana shirin nanndeahi ya kanye idanunshi daga kanta ya maida kan hisham,alama yayi masa da maryam,ya fuskanci me yake nufi duk da yanayin da suke ciki sai da murmushi ya subucewa hisham din.

''ka kwantar da hankainka ba'a gidan zamu barta ba itama zata fice amma ba lokaci daya tare da mu ba don kada afuskanci me muke ciki alright?''kai ya gyada masa sanan ya lumshe idanunahi kamar mai bacci
tsaf ya gama nade abdallan kamqr kayan wanki cikin bargon,qofar shan numfaahi kawai ya bar miahi,yana nishi da qyar ya saba shi kan kafadarshi

maryam ce ta fara yin gaba,ta fita tana dube dube kamar mai neman wani abu,saida ta tabbata babu idon kowa sannata dawo ta yiwa hisham magana,ya qaraso bakin motarahi ya bude gidan baya ya shimfidar da Abdallah ya rufe cikin sassarfa ya zagayo
''mintina hamsin sun isa naje gida na dawo,kafin cikar minti hamsin din ki fita kamar zaki wani abu ne awaje ki dawo ki sameni a bakin titi sai na daukeki mu wuce''cikin gamauwa ta gyada masa kai,ta juya da sauri ta koma bqngqren naau shi kuma ya tada motar cikin sauri,mai gadi ya dage masa get ya wuce
qurar motar nene kawai ta gani ta iso gin tana tambayarsu wanda ya fita daga gidan,daya dagq cikin security din daya fusu jin hausa yace
''abokin oga ne,oga hisham''tayi qaramin mirmushi hadi da cije lebanta,cikin salon mugunta kana ta hade ranta
''dagq yau kada ku sake barinshi ya shigo cikin gidan nan,duk wanda ya kuma kuskura ya barshi ya sake shigowa to ya tabbatar ranar a bakin aikinshi''
cike da biyayya suka qameta tare da cewa''yes madam''

bedroom din nasu ta koma ta tattara 'yan qananun abubuwan da tasan zasu mata amfani ta dauki 'yar jaka qarama ta zuba aciki,ta koma kan sofa ta zauna lokaci lokaci tana duba agogo,cikar mintina arba'in da biyar da fitarsu kenan don haka ta miqe ta rurrufe duka dakunan baccin da saman ma baki daya ta fito zuwa harabar gidan

A nutse tazo fitar tata bata samu wata matsala ba don sukkansu sun ruga da sun san wace ita cikin gidan tana sake taku na fita daga gidan zuciyarta na kuma bugawa,sai data tqbbatar ya fice daga gidan baki daya kana ta qara wani irin saurin kamar zata tashi sama,ji take kamar za'ace da ita ke dawo,ajiyar zuciya ta saki da taga motar hisham na jiranta,ba bata lokaci ta hude ta fada kana ta maida murfin ta rufe,idanunta na rufe suka hau kan titi kana ta saki wata ajiyar zuciya,hawaye ne ya balle mata ta kalli hisham
''amma hisham mami fa?''
kanshi ya girgiza
''sun san sun gama da mami,bata da ikon hanasu komai sai abunda suka shomfida,babu wani abu da zasu iya yi mata,addu'a zamu bita da ahi kafin mu samu nutsuwa mu zauna mu samar da mafita,don tabbas akwai abinda ke faruwa,na tabbatar mummunan qulli ne a binne a qasa wanda bamusan inda yake ba sai Allah''

Cikin nishadi nene ta sake dawowa bakin get din zuciyarta na sake kururta mata ita mai nasarq ce,korar hisham da maryam daga rayuwar abdallah cikin lokacin da take qoqarin kau da shi ba qaramar nasara bace don a idonta maryam ta fita,sake tambayarsu tayi don tabbatarwa suka amsa musu eh itace
''goo,itama bana son ta sake shigowa cikin gidan nan ko ita ko wani nata har abada''kallon juma suka shiga yi don dukkansu sunsan wace maryam cikin gian sun san matsayinta,ganin suna son saka tantama cimin ranau yasa ta daka musu tsawa
''ko baku jina ne,wallahi zan iya yiwa mutim kowanne irin hikunci matiqar ya saba umarni na,kubar ganinku garada''ta musu wani kallo na izgili,da sauri suka amsa suna bata haquri,juya watayi tana fadin Allah yasa daya daga cikinsu ya sabawa umarnin ta

sai da ta dubi bangaren abdallah ta qyaqyace da dariya
''Allah ya jiqanka abdallah,taka kuma ta qare,wataqila kafin gove azo gamawa da kai yunwa da qiahirwa sun zama ajalinka''ta wuce sashenta tqna wani irin taku cike da nishadi da jiyo qamshin nasara

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶4⃣4⃣

*_An karbo daga abu hurairah R A yace:Manzan Allah S A W yace:babu wata rana da gari zai waye face sai mala'iku biyu sun sauko,sai daya daga cikinsu biyun yace ''YA UBANGIJI KA BAWA WANDA YAKE CIYAR DA DUKIYAR SA NINKIN ABINDA YAKE DA SHI'',dayan kuma sai yace''YA UBANGIJI KA BAWA WANDA YAKE QIN CIYAR DA DUKIYARSA ASARA A CIKIN DUKIYAR (WANDA YAKE ROWA BAYA CIYAR DA ITA GA MABUQATA DA MASU NEMAN TAIMAKO)_*

🕋🕋🕋

*ina taya daukacin al'ummar musulmi murnar shigowar sabuwar shekarar musulunci,dukkan wani alkhairi na duniya da lahira dake cikin shekarar ka hadamu da shi,ka kare mu da dukkan wani musulmi da sharrin dake cikinta,ka bamu lafiya da zama lafiya da kwanciyar hankali da yalwar arziqi ameen*

Daf da zata qarasa bangaren nasu tana ci gaba da babaka dariyarta suka ci karo da baaba uwani,wata uwar tsawa ta daka mata
''ina zaki je uwar kinibibi?''
jikin baaba uwani na rawa tace
''ah....ummm...zani mi gaisa da hajiya ne?''
tsatstsareta nene tayi da idanu
''me nace dake tsohuwar banza?''
''ahh...kince....kince ne kada ki sake ganina bangaren ku indai ba inaso ma rasa aiki na ba'' gyara tsaiwarta tayi
''kin shirya rasa aikin naki kenan?''
girgiza kai ta shiga yi
''a'ah,don Allah hajiya nene kiyimin afuwa''
''kinsan me nakeao dake?,matuqar bakison rasa aikinki cikin gidan nan kada na sake ganin qafarki a harabar gidan nan,daga yau ziwa gobe jibi ke har gata ma,kina jina ko?''

da sauri take gyada kanta ,kana ta bata umarnin ta koma inda ta fito
hawaye ne kawai ke zuba daga idon nene tana sharewa,idan banda darajar mami da take tausayawa babu abinda zai zaunar da ita a gidan,abubuwa marasa dadi da idanunta ke gane mata wanda ke faruwa shine ummul aba'isin zamanta cikin gidan badon wani abu ba

🍂🍃🍂🍃🍂

babu wanda ya sake cewa komai har suka qarasa gidan hisham din,gida ne madaidai ci mai kyau wanda ke dauke da makeken falo kitchen dining area sai dakunan bacci guda hudu

A falo suka tadda abdallah kan kujera,gwiwarta a sanyaye ta qarasa gurinshi kanshi na duqe a qasa,a gabanshi ta durqusa ta sanya hannunta cikin nashi tana kallonshi,sam yaqi daga idanunahi ya kalleta,hakan na nuna mata cikin tsananin bacin rai yake,ta leqa fuskanahi idanunahi biyu don tana iya ganin qiftawar idanunshi,sai zuciyarta ta karya ta tura kanta tsakanin cinyoyinsa da fuskarsa sai a sannan suka hada idanu,ya zuba matq idanun naahi da suke har yanzu kalar ja

shigowar hisham falon ya sata miqewa,ya taimaka suka shiga da abdallah daya cikin dakunan dake falon,dakine mayalwaci mai hade da toilet,gado madubi side bed sai cupboard da kujera doguwa qwaya daya da carfet da ya malale qasan dakin da shi a maimakon tiles
''zan fita amma bazan jima ba zan dawo''
ya qarasa gaban abdallah yace
''abokin sai na dawo mintina kadan zan dawo''kai kawai ya gyada masa ya miqa masa hannunshi sukayi musabaha

🌲🎄🌲🎄🌲🎄

Qarfe goma na daren ranar suka fito daga maboyar da nene tayi musu cikin dakunan barcinta,gaba dayansu baqaqen kaya ne ajikinsu hatta da mask din da suka sanya,kowannensu wuqa ce boye a jikinsa

taku daya biyu nene tayi ta tsaya a gabansu,dukkansu sun fita tsawo nesa ba kusa ba,ta dubesu daya bayan daya
''banason a samu kuskure ko sabani cikin aikin nan,shekaru na kwashe masu yawa ina neman wannan damar,saboda haka ku tabbatar komai ya tafi yadda ake so''
dqya daga cikinsu wanda da alama shine oga ya buda hanci ya shaqi iska
''haj,sanin kanki ne munsan aikin mu dalilin da yasa kema kika neme mu kenan''
gyada kai tayi
''haka ne kam''

da daya da daya suka dinga fita har suka isa sashen abdallah,jijjiga qofan suka yi suka jita gam hakan ne ya tabbatar musu a kulle take,don haka kansu tsaye ba tare da wani tsoro ko shayi ba tunda sun san cewa babu security ko daya cikin gidan bare su jisu duka nenen ta bawa kowa aikin da har su gama abinda zasuyin ba zasu riskesu ba,take suka hau lallauya qofan da wani shegen qarfe suka ajjiyeta saahe guda kana suka kutsa ciki

Sau uku yama luma wuqa kan tarin filallukan dake tare a kan gadon ganin qamas babu alamun jini ya sanya su yaye bargon,a mamakance suka kalli juna kana daya daga cikinsu ya ciro waya ya kira nene,da zumudinta ta daga kiran ga tsammaninta sun cika aikinsu
cikin mamaki da fushi take fadin
''wanne irin babu kowa?kada ku gauamin maganar banza mana,yaron da ko motai bai iyayi ina zaije?,kuma tun jiya babu kowa a tare da shi balle ace ya fidda shi?''
cikin ciccijewa ya maida mata amsa
''kinga hajiya duk ke kika san wannan,kizo kawai idonki ya gane miki''
da azama tq fito ita da zahariyya da danan suka bazamo bangaren abdallan,surutai take tayi kamar wadda ta samu matsala a qwaqwalwarta don bata taba sawa cikin lissafinta cewa wannan karon akwai cikas din da zasu samu ba

cirko cirko sukayi cikin dakin bayan kammala duba ko ina na cikin gidan ciki har uwar dakin mami wadda batasan me ake nema ba,ta dai ga nenwn kai tsaye ta ahige mata daki tana dube dube daga bisani ta fito
''taya ya abdallah ya fita daga cikin gidan nan''
''ke za'a tambaya hajiya''cewar ogansu yana maida locker da tasa ya balle ta dakin abdallan wadda basuyi katarin samun komai ba sai rafar din dubu hamsin

''miqo min wadan nan kudaden,yanzu hatta da takardun kadarorinsa ma ace babu su cikin dakin nan,anya wani baisan abinda muka shirya ba kuwa cikin gidan nan,anya banu mai,mana labe da leqen asiri?''ta fada tana zare ido kamar wata zautacciya
kudin ya kalla kana ya dubeta
''ban fajimci me kike fada ba,wannna kidi ai namu ne ladan zaunar damy da kika yi nuka kwana cikin gidanki,ai lissafi zamuyi kawai ki cika mana sauran miliyan dayan da mukayi da ke zaki cika mana''
''idan aiki yayi kyau ba,ana ta kai wa yake ta kaya,kwananku kuma cikin gida na ai ku kuka qaru da ni bani na qaru da ku ba asara ce ma ta hauni goma da goma,tunda har 'yata na baka ta tayaka kwana ko?baya ga haka ma ni a yanzu bani da miliyan daya bani da dalilinta,da aiki yayi kyau ne ma na tabbata cikin dukiyar da zamu samu ba komai bane cire miliyan daya daga ciki ''ta fada tana matsowa gabansa tare da zazzare idanuwa,don ji take su suka ma ja mata duk wata asara da ta fada matan

Dariya ya sheqe da ita
''haba hajiya,kinci qarya kin kwana da yunwa,muba qananan makasa bane ba irinnu akewa haka ba''ya sake matsowa inda take har tana jin warin wiwinshi na dukan hancinta,yatsunshi ya daga guda uku
''kwana uku kacal na baki ki turo mana ragowar kudinmu,wlh wlh wlh ko ke kikayo naqudata matuqar baki turo da sauran kudin nan ba ke da 'ya'yanki ki tabbatar kuna cikin masifa,domin duk ranar dana waiwayeku sai kun buraci mutuwarku akan rayuwarku,na baku dama ku gaggauta warware harqallar da kuka qulla dani''

ya juya zai wuce adnan yasha gabansa cike da taurin kai da jin shima karansa ya kai tsaiko yana ciccije lebe cikin son nuna shima jan wuya nebayan shi kansa yasan fanko ne lamba daya,kafin yace komai yasa kan wuqar hannunshi ya daki kanshi saiga adnan din a qasa,ihu nene ta saka tayo kansu,da tsinin wuqar ya juna ta ta koma baya tayi luf sai da suka kammala ficewa ta saka kururuwa ta biyo bayansu ko Allah zaisa taci sa'a wani daga cikin security din sun dawo suyi ram da su,saidai ina,babu wanda ta samu bakin get din kamar yadda ta watsa su don gabatar da aikinta

🍃🍂🍃🍂🍃🍂

ta kai ta kawo tayi hakan ya kusa sau goma sha biyar,ji take kamar zata hau bori ko hauka kafin ta samu guri ta iya tsugunnawa,ta dubi adnan da kanshi yasha dauri da bandeji da zaharkyya wadda ke zaune tana faman hade fuska,babu wanda take ganin laifi sama da nene,don ita kam ta gaji da wanna jeka ka dawo din,ta riga da ta yanke ma kanta hukuncin abinda zata aikata matuqar wannan karon haqarsu bata cimma ruwa ba kamar sauran lokutan baya
''babu shakka cikin hisham da maryam akwai wanda ya fidda abdallah daga cikin gidan nan,ko kuma daya daga cikinsun ya aikata hakan,kuma nafi zargin wanna shaidaniyar ce marya,tabbas kuwa''ta fada tana guada kai hadesake tabbatarwa kanta
''qwarai kuwa nene,nima na zargi haka tunda kinga fitarsu ana gobe za'a gudanar da aikin,cikinsu akwai wanda yake da hannu kan tsirar abdallah''inji zahariyya,shikam adnan ya kasa magana ta kanahi yake,tsanin ciwo yake masa kamar zai tsage gida biyu har
zumbur nene ta miqe tana fadin
''wallahi basu isa ba dukkansu,duk wanda yaci tuwo da ni miya yasha''

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

Tana cikin kitchen tana qoqarin hada masu abincin rana ta jiyo hisham na qwalla mata kira,cike da mamaki ta ajjiye abinda take yi din ta fito don bata taba jin ya mata makamancin irin wanna kiran ba
tashin hankali ta gano qarara cikin idanunshi
''dauko duk abinda kika san kina da buqata ki sameni a mota na riga da na kai andallah ciki,babu lokacin bayani na miki shi a hanya''
bata tsaya tambayar ba kuwa,ta koma kitchen din a gurguje ta kashe gas din ta ahiga dakinsu da suka sauka ta dauki iya abinda take jin zata iya buqata ta fito ta taddasu cikin mota

Tafiya yayi ta kusan mintina hamsin har suka fara barin ainihin qwaryar birnin kano sanna yayi parking a nutse ya dubeta
''maryam,na samu bayanan sirri daga daya daha cikin security din gidansu abdallah wanda nake biyanshi bayan barinmu yake samin ido kan duk wani motsi da yanayi da gidan ke ciki,don na tsammaci dama lallai wani abu na iya faruwa kan barinmu gidan da abdallah da mukaui,hasashena kuwa ya tabbata ya zama gaske iya,suna na ne ma farko cikin jerin mutanen da nene ke tuhuma,don ta saka amata bincike kan inda nake,yanzu haka mutanen na kan hanyarsu ta zuwa gidana,dalilin barowarmu gidan kenan''

kuka ne ya qwacewa maruam,wannan wace iriyar mace ce nene?me ta dauki rayuwar duniya,baza'a mutu ba?dawwama kowa zaiyi yana abinda yaga dama?,me take nema ne cikin duniyar da dukkanta bata kai qima da darajar fika fikin sauro ba agun Allah,wanne jin dadi ne a ginta ta kashe ran mumini wanda qimatsa tafi ka'aba agun Allah?,tana tsammanin idan ta aikata hakan taci bulus ne ko kuwa,zata taira daga hisabi da zabar Allah ne?dukkan amsar itace a'ah,babu

''a halin da muke ciki maryam kuka babu amfanin da zai mana,ki tsaida kukan mu nemi mafita''
tabbas maganar hisham haka take,ba bata lokaci ta ciro wayarta ta sake kiran mama wadda basu yi awa biyu da yin waya ba,magan sukayi ta kimanin minti talatin da ita kana ta kashe wayar ta dubi hisham kasancewar handsfree ta saka yaji komai
kansa ya gyada
''maganar mama gaskiya ce,kuma tsarin nata yayi,nima da mun isa gobe zan wuce katsina hometown namu''ya fada yana mai gamsuwa da bayanin maman yana kuma sawa motar key,ta juya ta sake kallon abdallah har yanzu idanunshi a lumshe yake,babu baki balle ya bayyana abinda ke cin ransa,ta tabbata ba magana daya ke dawainiya da zuciyar abdallah ba,suna da dama,koda bao jude idonsa ba,koda baiyi,magana ba tana ki a jikinta zuciyar abdallan a quntace take,takan tashi kokawa afili da boye duk da shi din tsananin jarumtarsa bai taba barinta taga hawayensa ba

Da taimakon bayanin da mama ke masu a waya suka kai ga isa qauyen NI'IMA dake cikin qauyen gaya,tun daga shigowarka garin zaka bawa kanka amsa,tabbas qauyen yaci sunanshi ni'ima,qauye ne da Allah ya wadata su da yawaitar korayen shuke shuke qoramu dabbobi da lullumi ma'ana rashin haske da zafin rana
duk da haka sai da sukayi tambaya kafin su kai ga isa ainihin gidan da suke nema,gaya garin kakanninta ne tana zuwa lokaci bayan lokaci saidai qauyen ni'ima din zata iya irga iya adadin zuwanta tunda bata da wani shaqiqin da zata zo gunsa face wannan tsoho qwaya daya da yake qanin kakanta

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[6:27pm, 9/22/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

▶4⃣5⃣

*_Mazan Allah S A W yace:ku umarci 'ya'yanku da yin sallah suna da shekaru bakwai,sannan ku dakesu saboda ita idan suka kai shekaru goma,kuma ku rarraba musu gurin kwanciya(ma'ana ya zama gurin kwanan maza daban gurin kwanan matan daban yayin da suka cika shekaru goma)_*

Gida ne ginin qasa kamar yadda yake kasancewa ginin gidajen qauyuka,saidai wannan ya dan banbanta da nasu damin uasha shafe da ruwan makuba,hakanan ginin sumul sumul yake sakamakon fulastar kar qasa da aka yi masa da kuma makubar da akabi aka shafe ginin da ita.

Maryam ce ta fara shiga,kamar yadda muka sani yan uwanmu na karkara basa gini quntatacce hakan ce ta kasance ga wannan gida,babban tsakar gida ne mai girma wanda babu sumunti a qasan sa,turbaya ce saidai ta sha shara fes da ita,ga alamun shatin tsintsoya ne,daga can quryar katangar gidan garkene na dabbobi dake a tsaftace shima,sai rijiya daura da shi wanda lema ce duk a bakinta da tukwanen qasa da aka kikkife da alamu wanke wanke aka gama agun babu jimawa.

ta sake yin sallama kin shiru ba'a amsa ba karo na uku,cikin daya daga dakuna hudin dake jere taji muryar matashiya na amsa mata,ta fito sanye da roga da zani na atamfa wadan da suka danyi haske saboda dan jimawar da sukayi a duniya,maryam ta duba itama ta kalleta
''don Allah inna wuro fa?''maryam ta tambaha,sai ta juya ta kalli dakin kana ta kalli maryam
''tana ciki salla take amma yanzu zata....'''
''wake sallama ne mero,a shigo mana''
muryar inna wuro ta katsesu
''inna wuro baqi kikayi''
''kaddai ace su meramu ne har sun iso haka da wuri''ta fada tana yunqurin fitowa,kasancewar ta san zasu zo din mama ta kirata awaya ta mata bayanin zasu zo din ta wayar mustafa jikan gidan.

hannunta dauke da tabarmar kaba sabuwa dal ta fito,dattijuwa ce wadda aqiyasce zata doshi shekaru sittin,tsaf da ita cikin cikin atamfar itama da hijabi ruwan madara,fuskarta ta fadada da fara'ar ganin maryam din
''to kuma ya na ganki ke daya''itama murmushin ne afuskarta
''inna suna qofar gida''
''to yi maza kice musu su shigo daga ciki mana''ta fada yayin da take shimfida tabarmar.

Tare suka shigo hisham na tura abdallah kan wheelchair
''hukumullahu min zalika,Allah mai yadda yaso da bayinshi''inna wuro ta fada tama kallonsu
''sannu dam nan sannu''ta qara fada tana kuma gyarq musu gun zama
matashiyar da inna wuro ta kira da mero dazu ta qaraso dauke da kwanonsha cike da ruwan tulu mai sanyi fari tas ta ajjiye gabansu,kanq ta ja hijabinta daga kan igiya tana fadin
''inna zanje gida,idan na dawo r
yau to,idan kika ga ban dawo ba kuma sai gobe''
''to mero na gode Allah ya huta gajiya,ki gaida su azimin''

Bayan gaishe gaishe shiru,ne ya biyo baya inna tana kallon ikon Allah
''yanzu mairamu tun yaushe lalurar ta sameshi?''a nutse tayi mata bayani,kamq bqki innan tayi
''matsalar ku kenan mitanen binni,boko tasa baku da kulawa sam,ni kam ba wai zato ba amma wanna lalura ta yaron nan batayi kama da komai ba face sihiri,kuma kinsani sarai qanin kakanki masani ne kan irin wannna matsaloli baki tuntiba ba,yanzu ma zuwa kukayi kenan idan qura ta lafa ku koma ba neman magani ya kawoku ba''
hisham ya guara zqma jin hanyar waraka na shirin samuwa
''a'a inna,har maganin ma mun zo mu nemeshi''
shiru tayi ma wasu 'yan mintina kana tace
''to Allah yasa adace,insha Allahu Allah zai kawo qarshen abun nan kusa''

maryam ta dubi inna wuron
''ina tsoho alhajin ne?''
''kinsan watan tafiya gabas ne,bana Allah ya kirashi yana can qasa mai tsarki,ina tsammanin yau duka kwananahi uku da tafiya,amma muna sa ran nan da sati uku zuwa hudu zasu dawo insha Allahu''
''Allah ya dawo da ahi lafiya''suka hada baki ita da hisham wajen fada
''daya dawo insha Allahu zan masa bayanin komai,idan rabo sai kuga ya warke''
''Allah yasa''inji hisham cike da fata.

In banda sannu babu abinda inna wuro kema abdallah,gaba daya tausayinshi ke damunta,irin wanna lalura mai fama da ita kadai yasan yanayin da yake ciki,da kanta ta bude musu wani daki can bangare daya,ba laifi dakin akwai girma,malale take da leda duk da cewa ba sabuwa bace,akwai labulaye a window da qofar,sai tsohuwar katifa da kujera qwaya daya,a ahare dakin yake fes kasancewar inna wuron bata lamuntar qazanta
hisham ya qarewa dakin kallo kana ya girgiza kai
''rayuwa mai juyi kuyi,Allah mai yadda yaso''ta karanci me yake nufi,tabbas ita kanta ta sani abdallah dan gata dan gayu,young millonier yafi qarcin zama cikin qauye ma baki daya ba dakin ba.

maganar hisham ta katse mata zancan zucin da takeyi
''abdallaj bazai iya zama cikin dakin nan haka ba maryam,zan ahiga na laluba inda zan samu kayqn buqata da za'a ma dakin kwaskwarima''kai ta jonjina babu bata lokaci ya fice,ta kalli abdallah suka hada ido uana mata nacin kallon nan nashi
''bari naje nayi alwala nayi sallaar la'asar,idan na dawo sai in maka alwala kayi taka sallar''ta fada kanta aduqe sabida naugin idanunshi da take ji
kai ya jinjina mata kana itama ta fice.

Sai bayan sallar magariba sanna hisham ya dawo niqi niqi da kaya cikin akori kura,cikin mintina qalilan da taimakon yaran maqota da kuma taimakon mustafa aka gama ahigowa da komai,kayan daki ne da suka hada da katifa labulaye kujeru cusion guda biyu fanka ta tsaye carfet mai girma da zai iyacinye dakin,robobin wanka food falask har da risho dan madaidaici da set na tukwane,kayan sawa nashi da na maryam akwati wadda zata iya cinye musu kayan,duk dai wani kayan amfani da zasu iya buqata,hatta da kayan abinci ruwan roba da lemuka creet na qwai da sauransu
ba inna wuro ba hatta maryam ta jiniina siyayyar,sai da ya niqi tafiya har cikin jigawa sannan ya jado siyayyar,tunda su sinyi tsaki,yasunyo nisa da cikin birnin kano kuma basu qarasa jigawar ba.

A daren mustafa ya taimaka masa ya shimfida carfet da kujeru da katifa suka shimfida sabon zanin gadon cikin dakin hisham ya kwana tare da abdallah ita kuma ta kwana tare da inna wuro

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

zuwa goma na safe dakin ya zama gwanin sha'awa tamkar ba shi ba,sha daya na rana sai ga mutane daga company mtn sunzo hada solar,da mamaki maryam ta dubi hisham
''hidimar nan tayi yawa hisham,sai kace zamu dawwama ne a garin?''
murmushi yayi kana ya girgiza kai
''maryam kenan,baki san waye abdallah ba aguna,abdallah shine tsani na dukka wata rayuwa ko matsay da na take ko nake kan takawa a yanzun,ba don Abdallah ba ina zaton da tuni na jima gidan mahaukata,abinda abdallah ya yimin bazan iya biyanshi ba,ya taimakamin da jikinsa da aljihunsa da lokacinsa ta qwaqwalwarsa ma baki daya,Allah ne kadai zai iya biyanshi abinda yayimin a rayuwa,babu abinda bazan iya bawa abdallah ba,wannan abun da nake masa ban masa kaso daya cikin darin abinda ya yimin ba,abdallah dan halak ne dole nima na nuna masa halacci''
kallo daya ta masa ta tabbatar daga qasan zuciyarsa abinda yake fita bawai daga fatar baki ba

cikin qasa da awa uku suka kammala wearing din baki daya aka kunnata ta fara zuqar chargy,sai gidan ya zama abin kallo,al'ajabin yadda za'a samu hasken qwan lantarki daga hasken rana sukeyi har hakan yaso bawa hisham da maryam dariya,musamman yadda mero da inna wuro suka ce su kuwa zasu ga ikon Allah.

Qarfe biyar sukayi sallama da hisham ya wuce katsina,kafin nan sai da ya danqa mata duk wasu takardu na abdallah da ya debo,qememe taqi karba tace sam,shi yafi cancanta ya riqesu a hannunsa
atm,card ya bata shima da fari cewa tayi bazata karba ba don basu buqatar komai,yace a'a,kowanne lokaci buqata na iya kamasu,ta karba din don ya riga da ya kouawa mustafa yadda ake cirk kudin ta wani atm machine da suka gani cikin garin gaya,idan tana da buqata ta bashi ya ciro musu
''saidai akwai magana daya,maryam gwamnati na fara matsantawa da hutun da mukace abdallah ya dauka ne,sabida akwai cases manya da ya fara aiwatarwa kafin cutar nan ta sameshi,so na rasa me zan ce da su,don ina magana da su ne amatsayin abdallah''

shiru tayi na dan qanqanin lokaci
''yanzu idan ka nemi alfaramar qarin watanni bitu zasu qara din?''
''eh...don sunce na fadi iya kwanakin sa,zai dawo ba tare da ya sake dagawa ba,don qasa na da buqatarsa''
''to shikenan ka fada musu watannin biyun,kafin nan muga yadda Allah zaiyi''
''Allah ya iya mana,ya bashi lafiya cikin sauri''
''ameen''inji maryam,ta rakashi ya yiwa inna wuro sallama cike da kewa ya tafi don a zamansa na kwama dayan har sun soma sabo

🍃🍂🍃🍂🍃🍂

firgigit ta farka daga baccin da ya dauketa kan abun sallah,da sauri ga leqa fuskan abdallah dake baccinshi ta tabbata lafiyanshi lau,komawa tayi ta jingina da bangon dakin tana share zufa tare da tuno mafarkin da tayi,tabbas Allah ne ke mata ishara,sam kamar wadda aka dakawa gudumar mantuwa ta mance da mafi yawa daga cikin addu'o'inta,ta waiwaya ahankali ta kunna wayarta ta kawo haske,qarfe uku,na dare agogon ya nuna mata,ba zata iya fita alokacin ta daura alwala ba din haka ta janyo carbinta taci gaba da ja tana ambaton Allah lokaci lokaci tana leqa abdallah

🍂🍃🍂🍃🍂🍃

Tana bakin murhun tana dama musu kunun duk da hanatan da inna wuron tayi qoqarin yi amma ta qiya,don tsakanin kwana ukun da sukayi cikin gidan indai ta kunna risho to abdallah zata dafawa wani abu,ta riga ta saba don rayuwar gidan sun data tashi cikinta marabarta kadan ce da wannan

Mero ce tayi sallama ta shigo gidan,ta dubi maryam tace
''takwara ina kwana''ta waiwayo fuskarta dauke da 'yar fara'a ta amsa mata
''a'ah,mero,yanzu kuma sammako zuwa min aka koya kenan,kodon,kinga kin samu abokiyar hira ne?''inji inna wuro dake fitowa daga daki
dariya tayi
''wallahi kuwa inna,na samu larabawa abokan hira''haka take kiransu maryam sabida farin da suke da shi,duk da itama din farar bafulatana ce saidai nata farin baikai nasun ba

Ta shiga dakin inna wuro da suke zaune da mero,suna hira suna cin gyada marau marau,gefansu ta samu ta zauna kana tace da inna
''inna don Allah ina zan samu ganyan magarya?''
''ganyan magarya me zakiyi da shi?''
ta danyi murmushi,a zaton innan ko maganin mu na mata takeson ta hada
''akwai cikin kayan malam,amma ina tsammanin busashshiya ce,idan danya kike so saidai ko a yago miki can qofar gidan malam haladu''
''sai nasa yara su ciro miki,yaya abdullahi zakiyiwa magani?''inji mero wadda ta cafe zancan,kallonta maryam din tayi,ta lura da yadda take yawan kulawa da duk wani lamari da ya shafesu hakan yasa ta dan saki jikinta da ita
''eh''maryam tace mata,take ta miqe tana jawo hijabinta tana yafawa
''bari na kawo miki''ta fada tana ficewa,mero sunanta maryam,tsirar gidaje biyu ne kawai tsakaninsu da gidan inna wuro,irin marasa shi din nan ne na azo a gani,hakan ya sanya hatta aurenta iyayenta suka kasa,hakan ya sanya take shigowa take taya inna wuro aikace aikacen gida,taci kuma na rana da dare wani lokaci harda na safe agidan bayan wanda tsoho malam yasa ake zubawa akai gidan naau sabida iyayenta da qannenta

zama tayi suka ci gaba da hira da inna wuron bayan ta mata tayin gyadar,cikin minti goma saiga mero da ganyan kore shar mai yawa kuwa,maryam ta miqe tana mata sannu ta saka hannu zata karba
''bari na kai miki dakin ma''kafin tace wani abu har ta fice ta nufi dakin nasu,binta tayi da kallo har ta dagaabulen dakin ta shiga,duk da ta koma ta zauna amma sai hankalinta ya kasu jiyi ganin ahiru meron bata fito ba,miqewa tayi taa cewa inna wuro
''bari na daura alwala naga an kusa azahar inna''
''to...to,nima tashin zanyi''.

sai data daura alwalar sannan ta nufi dakin,kan kujerar dakin ta tadda meron tana faman zuba surutu idonta kan abdalladake kwance,abdallah na daga kwancen yana kallonta
qarasa shigowa tayi
''kin manta bai da lafiya ne,mara lafiya baison surutu''ta fada tana qarasawa kan katifar
''amma meramu har mirmushi ya yimin fa''sai taji wani dim,ta waiga ta kalli abdallah,idanunshi na alaumshe sabanin dazun da yake tar a bude.

sauka tayi kawai ta janyo,abun salla ta shimfida sannan ta kalli mero
''ya kamata kije kiyi sallah ko,don lokaci yayi''
''shi kuma abdullahin fa?''
''zaiyi shima''ta bata amsa tana tada kanbbarar sallah,sai data kusa raka'a uku kafin meron ta tashi ta fita tana yiwa abdallah sallama
roba ta saka ta masa alwala sanna ta juyar dashi bangaren gabas,kafin ya idar ta zuba abinci cikin plate ta ajjiye,bayan ya gama ta dora mishi kan,fillow a saman cinyanshi don hisham yace a dinga barinshi wani lokaci ya dinga ci da kanshi don hannun ya dinga motsawa ya dinga jin qwarinshi sosai,ta koma saman kujera ta ta samu roba daya ta zuba ganyan magaryan tana gyarashi tare da cire qayoyin jiki

shirun da taji alamun bai fara ci ba ya sanyata dago kanta,hada idanu sukayi da sauri ta janye idonta,ta rasa dalilin da a kwanakin nan bata iya hada ido da shi na tsawon lokaci,jikinta yaci gaba da bata kallonta yake,a sace ta kuma daga kai zata saci kallonshi suka sake hada ido,ya lumshe idon nashi da sauri ya bude,sign ne da ta lura yana yawan yi mata amfani da shi idan suka hada ido,batasan me yake nufi ba saidai a duk lokacin da yayi hakan takan tsinci kanta cikin wani irin feelings,wani irin abu ne cikin qwayar idanun abdallan da bata taba ganinshi cikin idanun wani ba

ta janye idonta tana fadin
''kaci abinci kada ya huce''kai ya girgiza mata alamun a'a,babu yadda bata masa ba amma yaqi,qarahe sai daya bar abinda take yi din ta dawo kan katifar ta karbi plate din,ta debo ta miqa mishi,babu musu ya bude bakinshi ya karba yana kallon fuskarta,ganin ya karba sai ta ajjiye cokalin tana fadin ''bismillah to''tana maida fuskarta gefe
a tausashe taji an kamo habarta ana qoqarin juyo da fuskarta,qin kallonshi tayi kamar yadda shima sam ya hanata sakewa har sai da suka sake hada ido,ture plate din abincin yayi da hannunshi guda kana ya jawota ta fada jikinshi.

tayi ta qoqarin tashi,saidai ya hanata,har mamakin yadda ya iya riqeta haka tayi,kamar zata yi kuka tace
''abdallah,bafa mu kadai bane cikin gidan nan ka sani''shiru taji,alamun bazai kulata ba,tilas ta haqura da yunqurin tashin tayi luf cikin jikinshi,ya lalubi hanninta ya saka nashi ciki ya jade yatsunsu guri guda tare da sauke ajiyar zuciya wadda ta haddasa mata sauyawar yanayin jikinta gaba daya,ta runtse ido tana jin fitar numfashinshi.

*_kuyi haquri da wannan_*

*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽
[1:55pm, 9/24/2017] Huguma👑: 💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
🌺 *ABADAN*🌺
💖💖💖💖💖💖
🌺🌺🌺🌺🌺🌺
💖🌺💖🌺
💖🌺💖
🌺💖
💖

*WRITTEN BY SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA*
🌺💖🌺💖🌺💖
🌺💖🌺💖
🌺💖🌺
💖🌺
💖
© *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡
*_home of expert and perfect writers_*

4⃣6⃣

*_Annabi Muhammad S A W yace:duk wanda yaje gurin boka ko dan duba haqiqa ya kafircewa abinda annabi muhammad tazo da shi,hakanan ba za'a karbi sallarsa ta kwana arba'in ba(ba yafe masa su akayi ba,kuma ko yayi Allah baya buqata baxai karba ba,babu wani abu da zaka/ki aikata ya zama kaffarar wannan zunubin da kikayi face ki tubarwar Allah tuba na haqiqa ba tuban muzuru ba,kuma kada ki yarda qafarki ta sake kusantar gurin bama zuwan ba,shin me kike tsammani idan Allah ya dauki ranki a gun ko a hanyar zuwa kota dawowa?,Allah ya kare mana imsninmu,ya,cire mana dukkan wani qulli dake zuciyoyinmu game da 'yan uwanmu musulmi)_*

*_Manzan Allah S A W yana cewa''ka tuna Allah lokacin da kake cikin jin dadi da yalwa,shi kuma sai ya tuna da kai lokacin da ka shiga qunci da matsi da wahala(ba wai ka xauna kara zube ba don kana cikin jin dadi da wadatar rayuwa,ba zaka tashi addu'a ko tuna Allah da girma yake ba sai bala'i da masifu sun maka katutu,wannan kuskure ne babba,Allah yana fushi da bawan da baya roqarsa haka annsbi S A W yace mana,Allah kasa mu dace)_*

Saukar numfashinsa ne ya alamta mata bacci ya daukeshi,ta zare jikinta cikin dabara ta maye gurin da fillow,fuskarshi tarwai,kyawunshin nan mai daukar hankali yana nan,ta zuba masa ido tana tuhumar kanta na wasu 'yan lokuta,ta janye idonta ta lumshesu hadi da sakin ajiyar zuciya,mero ta fado mata arai,sai ta ja siririn tsaki kana ta sauka daga katifar,hijabinta na kanta don haka abun sallah kawai ta gyara ta zauna akai bayan bayan ta samu roba daban ta saka ganyen magaryar qwalli bakwai aciki,a nutse tayi bismillah cikin madaidaiciyar murya ta soma karanta suratul baqara cikin robar da ta zuba ganyan magaryar da ruwa aciki,da ka take karatun cikin daddadan sauti mai cike da nutsuwa,don surar na daya daga cikin surorin data haddace saboda muhimmancin surar.

cikin barcinshi ya dinga jin tashin sautin karatun,sai ya gaza bude idonshi duk da ya farka,sosai yake jin dadin karatun,wani yanayi mai dadi na ratsashi,sannu a hankali ya dinga daga idanun nashi har ya kammala budesu gaba daya,ya zubesu fes kan fuskarta
kallonta yake da yadda bakinta ke motsawa cikin gwaninta da ita karanta alqur'ani da bawa kowanne harafi haqqinshi,ba kadan ba ta burgeshi,komai nata mai kyau ne da nutsuwa,saita tunasar da ahi ahima wani bangare mai girma daya manta ko ya saki na karatunshi ya daina tilawa.

kan idanunahi ta kammala,ko kadan batasan yana kallonta ba har ta gama ta karanta falaq da nasi da suratul ikhlas aciki ta girgiza ahi sosai har ruwan ya soma kumfa ta samu murfi ta rufe,ta zare hijabinta saboda zafin data fara ji sakamakon rashin kitso,Allah ya bata yalwar suma kamar yadda ala sana salin fulani ke da ita,ta zare ribbom dinta ta fara sake qoqarin tattara gashin guri gida donta daureshi,bin sumar tata yayi da kallo,don iya zamansu bai taba ganin gaahibta haka ba,ba qaramn hirgeahi abin yayo ba,yana son mace mai yalwar gashi sosai,shi ua sanya yawancin lokuta a zamanin quruciya shi yakewa mami tsifa,rabi wasa rabi tsifa da haka suke gamawa,ya dan lumshe idonshi kana ya bude saboda wani abi da ya soki zuciyarahi da tunawa da mamin da yayi,qaunarta da kewarta ta zamar masa sabuwa.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.