Abdulmalik Bobo Complete Hausa Novel
Reading file: Abdulmalik_Bobo_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 1 of 4
[11/12, 2:10 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻.
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_story & editin_
*_aunty Bilyn Abdul_*
_Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty bilyn Abdul_*
*_Bismillahirrah manirrahim._*
*_gareku Readers._*
_assalamu alaikum, da farkodai nasan zakuyi mamaki, auntyna, bilyn Abdul itace tayi tallan buk d'in nan ABDUL-MALEEK, daga baya kuma sai tafasa rubutawa saboda wani aiki data zomata._
_to nikam nakaranta buk d'in danta rubutashi tuni a littafi yana ajiyene, littafin yayimin dad'i Dan haka nanemi izini tabarni na rubutamuku._
_nidai Marak'isiyya ba writer bace, wlhy koza'a kasheni bana iya rubuta page d'aya na novel, to amma yanzu zanyi muku copy insha ALLAH, ina fata zaku kasance dani kamar aunty bilyn Abdul, Dan labarin natane. Ngd._
*_sanda tayi tallansa ta rubuta sadaukarwa ga Abba Gana, batul mamman, bily giro, tonima zan cikamata niyyarta, Dan haka sadaukarwane ga wad'annan mutane uku._*
*_page 1⃣&2⃣_*
Kowa ka kalla yana harkokinsa acikin makarantar, wasu karatu sukeyi wasu kuwa hira da samarinsu ko k'awaye.
Shigowar wata bak'ar mota wulik cikin makarantar shine yaja hankalin mafi yawan d'aliban.
Safna tasaki Baki da hanci da ido itama tana kalo.
Motar tatsaya daidai wata bishiyar dalbejiya, ayanzu kallo yakomane akan Wanda zai fito daga cikin wannan mota mai k'yau da d'aukar hankali.
K'afarsa yafara zirowa k'asa maisanye da sauciki na farin takalmi, yakuma zuro d'ayar itama, saikuma yafito gaba d'ayansa.
Ajiyar zuciya safna ta sauke tareda fad'in ya salam!.
Zeenat tad'ago tana kallonta Dan ita kokad'an batasan bikin da akeyiba, tasaka iyafis akunne tana wayane.
Safna wai lfy mikike kallone haka kamar wata sakara?.
Safna da bakinta yaymata nauyi takasa cewa uffan, tad'aga hannu dak'yar tanuna mata matashin saurayin dake tsaye, Wanda ak'alla zaikai shekara 33 aduniya.
Masha ALLAHU zeenat tafad'a itama tana mik'ewa tsaye.
Farine sosai dogo kuma dankuwa yanada tsayi sosai, kallo d'aya zaka masa kagane k'ak'k'arfane saidai bashida k'iba, masha ALLAHU akwai k'yawun fuska, gashi kuma ya k'awata fuskar tasa da saje bak'i sid'ik, yakwanta sai wlk'iya yakeyi, sanyake da farar shadda wando da Riga d'inkin zamani, kayan sun masa k'yau....
Tunaninsu yatsaya lokacin dasukaga ya sunkuya yafiddo wata yarinya mai tsananin kama dashi, "bazata wuce shekara 6 ba aduniya.
Sanye take da doguwar riga ja iya kwaurinta Dan batakai k'asaba, ank'awata adon rigar da fararen filawoyi, kanta kam kalbace irin mai nannad'ewarnan kamar igiya (twisting), yasha ribom ja da fari, sai lilo sukeyi.
Ta rik'e d'an k'ugunta da hannu biyu tana kallon saurayin, baby inanenan mukazo?, tafad'a tana bin ko ina da kallo.
Murmushi yay mata Wanda yazauta dayawan 'yammatan gurin, musammamma safna, shima yarik'e k'ugunsa baby nan makarantace, munzo wajen uncle Hamza ne.
Lah baby dama uncle Hamza baigama makarantaba har yanzu?, yafayi babba sosai?.
🤦🏻♂kansa yadafe ya ce, "o,o me baby, kefa magana bata k'are miki, kinga muje ciki saiki tambayesa.
'Yar dariya tayi tareda kama hannunsa suka nufi office d'in uncle Hamza, Wanda yakasance lecturer a makarantar.
Cikin farinciki uncle Hamza yamik'e cike da murmushi yana fad'i oyoyo Nawal d'ina.
Itama sakin hannunsa tayi taje da gudu tashige jikin uncle Hamza, yarungumeta yana juyi da ita suna dariya.
Shikam yajingina da k'ofa yana musu murmushi, uncle Hamza ya ajiye Nawal suna sauke numfashi da dariya.
Sai sannan ya kalli saurayin, cikin zolaya ya ce, "oyoyo my Bobo!.
Shima hararsa yayi cikin wasa, kace hakafa yanzu, bayan baka kulaniba tun d'azu sai baby.
Hhhhhh afuwa kasan nida Nawal ba'a shiga tsakani, daga ina haka?.
Bobo yayi murmushi yana sauke numfashi, wlhy daga gidansu Ni'ima muke kasan mama babu lfy shine nace bari mubiyo mugaisheka.
Kai amma naji dad'i wlhy sosai, amma yajikin mama?, da sauk'ika gsky.
To ALLAH yak'ara sauk'i, nima anjima nashiga nak'ara dubata.
Okey ALLAH yakaimu.
Surutu Nawal takema uncle Hamza babu ko k'ak'k'autawa, shikam sai dariya yakeyi.
Bobo kam yamaida hankalinsa akan latsa wayarsa.
Aka kwankwasa k'ofar.
Uncle hamza ya ce, " ashigo."
Safna ce da zeenat k'awarta, risinawa sukai suna gaishesu, idon safna nakan bobo.
Uncle Hamzane kawai ya amsa, amma Bobo ko d'agowa baiyibama.
Safna incedai lfy?, uncle Hamza yatambaya yana kallonsu.
Zeenat ta zunguri safna dake kallon Bobo babuko k'yafta ido.
Uncle Hamza yana kallonsu, Dan haka ya girgiza kai.
Ina saurarenku yak'ara fad'a idonsa akansu.
Um....um sir dama..... Saikuma tayi shiru tana satar kallon bobo.
Bobo yad'ago yad'an kallesu fisha saikuma yamik'e, Ya Hamza bari muwuce mubarka da d'alibanka.
Baby oya tashi muje.
"Kai bobo da wuri haka?, cewar uncle Hamza yana kallonsa.
Karka damu gobe idan ALLAH yakaimu zanshigo na gaida aunty Ruky, baby taso mana.
Nawal ta mak'ale kafad'a zatayi kuka, a'a nidai zan zauna wajen uncle Hamza.
Harararta yayi baby banason rigimar banza fa kinsani, idan nabarki da aikinsa zaiji kokuwa da shegen surutunki magananniya.
Dariya uncle Hamza yayi, yashafa kumatun Nawal, kinga my durling kibisa kuje, idan natashi aiki, zanzo gidan Ammi na d'aukeki nakaiki wajen ya Ahmad ko?.
Da sauri ta d'aga kai tana 'Yar dariya, by by uncle.
By my Nawal.
Hannu bobo yabashi sukayi musabaha yafita rik'e da hannun Nawal.
Duk abinnan yana faruwane agaban su Safna.
Safna tabisu da kallo kamar ta had'iyeshi.
Murmushi uncle Hamza yayi, Dan yasan K'anin nasa yayi sata batareda yasaniba.
Ina jinku yafad'a yana maids hankalinsa kansu...........
_Ku kasance da Marak'isiyya_
*_(auntyna bilyn Abdul, abar alfaharina.)_*
Tana nan tana shiryo muku had'ad'd'en buk, saikungansa😉😘
[11/12, 2:10 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
3⃣&4⃣
........cikin in ina safna ta ce, "sir dama akan test d'in dakayi jiyane, wlhy banida lfy shiyyasa banshigo school ba.
d'an murmushi yayi kawai, yasan bayau yafara lecture safna bata nanba, amma bata ta6a neman afuwaba sai yau.
Ita kullum kanta Asama yake, tana gani tafi kowa, yasan yauma akwai abinda yakawota, bai wuce ganin bobo ba datayiba, Dan kallon datake masa kawai ya fallasa asirin zuciyarta.
Ajiyar zuciya yasauke tareda fad'in babu damuwa safna zan duba.
Godiya suka masa suka fice.
Binsu yayi da kallo yana girgiza kai, afili ya ce, " lallai safna kinada aiki, bakisan waye Abdulmalik bobo ba.
*_Wacece safna?._*
Alh Bilal mai Gold, shine sunan mahaifinta, cikakken bakano d'an asali, d'an kasuwane babba Wanda yake juya Gold yazama Naira.
Matarsa d'aya Haj Sa'adatu, suna kiranta (Ummi).
Yaransu hud'u mata biyu maza biyu.
Shaheed shine babba, yayi aure harda yara biyu, sai Muneer shima yayi aure, matarsa tanada tsohon ciki yanzu, sai Safna tana karatu yanzu, saikuma auta Rahma, bana ta kammala Secondary.
Yaran 'yan gatane sosai, saidai wannan baihanasu samun tarbiyyaba, iyayensu suna kula dasu sosai.
Saidai Safna batajin magana ko kad'an.
Wannan kenan.
++++++++++++
Suna fitowa daga office d'in zeenat taja tsaki, kai Safna ALLAH yau kinbani haushi, wai ina ajin nakine?, haba Dan ALLAH, jibafa kigani sabida wulak'anci kod'agowa yakallemu baiyiba yanata latsa waya, daga k'arshema saiyayi tafiyarsa.......
Kinga zeenat ya isheni haka, idanfa bazaki taimakamin nakai ga nasaraba tofa sauraramin, ninagani na ce, "inaso, angaya miki shi sakaran namijine da 1 time zai dubemu, ashema babu aji taredashi.
Mtsooow zeenat taja tsaki, aii idanshi ya iya rik'e NASA ajin, kekam naki yana hanyar zubewa.
Tana gama fad'a tayi gaba abinta.
Itama Safna abin yabata haushi, danhaka tashige motarta tayi gida
+++++++++
Bobo kam gida yanufa abinsa, yana tsaida motar Nawal tafita da gudu zuwa cikin gida, kansa yagirgiza yana fad'in ALLAH ya shiryeki baby.
(nace amin).
Bayan yakashe motar yakwashi wayoyinsa shima yay ciki.
Ammi dake zaune Nawal nakusada ita ta kwa6e fuska zatayi kuka, ta amsama bobo sallamarsa.
Yak'araso cikin falon yana kallon Nawal, kekuma lfy daga dawowarmu?.
Ammi tasauke ajiyar zuciya ta ce, " maganar kullumce dai takawo rigimar.
Shiru yayi baice komaiba.
Ammi takalli Nawal dahar tafara hawaye ta ce, "haba tagidan Appa kiyi hak'uri insha ALLAHU kinkusa ganin momynki kinji.
Da sauri bobo yad'ago yana kallon ammi, k'irjinsa sai harbawa yake da k'arfi, yakasa cewa komai.
Ammi takauda kai, ranta a6ace ta ce, " nagaji da ganin kukan yarinyarnan wlhy, amma babu komai bari Appanku yadawo, zand'auki mataki.
Hannun Nawal takama suka haura sama.
Bobo tamkar zai fasa ihu haka yakeji, yarintse idanu zuciyarsa na zafi, afili ya ce, "baby miyasa kikeson sakani a matsalane?.
Ganin babu maibashi amsa yamik'e yanufi d'akinsa.
*_Wanene Bobo_*
Abdulmalik d'ane ga Alh Aliyu Abdulmalik Hamshak'i.
d'an siyasa sananne wad'anda suke gwagwar Maya da ilimi dakuma nemawa talakawa 'yancinsu, matarsa d'aya Haj. Zahura (Ammi).
Yaransu shidda maza hud'u mata biyu.
Is'haq shine babba, yanada mata d'aya da yara hud'u, sai Sulaiman, shima yaransa uku da mata d'aya, sai Hamza matarsa d'aya shima da yara biyu, sai Abdulmalik (matarsa ta rasu) yarinyarsa d'aya, sai 'yan biyu duk mata basuyi aureba.
ALLAH ya azurta Alh Aliyu Hamshak'i da yara maza masu kwazo da himma, yaa is'haq ma'aikacine na banki, yaa Sulaiman kuwa likitane, sai yaa hamza lecture, sai Abdulmalik (bobo) cikakken lauya mai zaman kansa.
Kansu ahad'e yake, idan kagansu saika d'auka abokaine musamman ma yaa hamza da Abdulmalik, komai zasuyi saida shawarar junansu.
*_Abdulmalik_*
Mutumne mai zafi da sauk'i, gaba d'aya 'yan uwansa yafisu fad'a, saidai zasuzo daidai da ya is'haq (Dan shima mafad'acine).
Abdulmalik mutumne dabayason raini ko kad'an, baya wasa da mutane, baizama dolema kuzauna har kurabu kaga dariyarsaba, kullum cikin d'aurewa yake, amma yanada son jama'a sosai.
Abdulmalik bobo, yasamo sunan bobone tun yana k'arami, kasancewarsa mayen shan Bobo sai 'yan uwansa suke kiransa da bobo, ahankali sunan yay tasiri kowa Yakoma cemasa bobo, bayan ya girma saiya zama bobo na gsky saboda gayunsa ga k'yau ga kud'i ga ilimi, komaidai zam zam.
Bayan ya kammala karatunsa yafara aiki iyayesu sukace saura aure.
Yay tsalle yadire bashida budurwa, wannan yasa Appa yanema masa auren d'iyar k'anwar Ammi mai suna Ni'ima.
Da farko baya sonta ko kad'an, amma k'yawawan hali irin na Ni'ima yajanye hankalinsa harya tsunduma a k'aunarta.
Shekararsu biyu da aure ta haihu mace, wadda taci sunan Ammi, suna kiranta Nawal, shekarar Nawal d'aya Ni'ima takuma samun ciki, amma wajen haihuwa ALLAH yay mata rasuwa itada abinda ke cikinta.
Bobo yashiga rud'ani Dan saida aka had'a da addu'a sannan yadawo daidai.
Tundaga nan baisake kallon wata mace da sunan so ba, damashi matan bawani damunsa sukaiba.
Bobo yanada k'yau daidai gwargwado, gashi d'an gayu, akwai tsafta da iya d'aukar wanka, dolene mace mai lfy taga bobo ta k'yasa, kullum cikin k'amshi yake.
Shiyyasa Madeena ta k'yasa.
(To aunty bily dai ta ce, "ki kama kanki Dan bama kulaki zaiyiba, danshi aharkar mata ba gwani bane😜).
Shekarar Ni'ima 5 kenan da rasuwa amma bobo yak'i k'ara aure, iyayen sunata fama dashi amma yak'i sunata fama saidai yace zaiyi amma yak'iyi.
Kullum zancen Nawal akaita gurin momynta, haka take damunsu Ammi da Appa hardashi dadyn Nata, itadai tanaso taga momynta, kullum zancen kenan.
Abin yana damun yayyensa da iyayensa, shikam ko'a kwalar rigarsa, harkar gabansa kawai yakeyi.
Wannan kenan.
*_Mundawo labari_*.........
*_{Aunty bilyn Abdul na gaisheku masoya😘😍.}_*
[11/12, 2:10 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
5⃣&6⃣
........Safna tadanna hon afusace, da sauri maigadinsu yazo yabud'e mata get, ta danna hancin motarta cikin gidan, tana kashe motar tasuri jakarta da wayoyinta zuwa cikin gida.
Wani wawan tsaki tasaki Dan ganin Rahma k'anwarsu kwance akan cinyar ummi.
Daga Ummi har Rahma baki suka saki suna kallonta.
Ummi ta ce, "kekuma lfy daga shigiwa zakiyi mana tsaki?, wai Safna ban hanaki halinnanba ne?.
Baki ta turo gaba tana Harar Rahma, haba Ummi ALLAH wannan abun kunyane, wannan k'atuwar yarinyar shrkara 17 haryanzu bataida halin yaraba, aiiko jafar d'in ya Shaheed baya wannan ta6arar.
Rahma ta girgiza kai danjin akanta yayar tata take tada jijiyar wuya, tarasa miyasa basa shan inuwa d'aya da 'Yar uwarta, (ita aganinta abin yafara wuce fad'an sako da sako), afili kuma sai ta ce, " aunty Safna miyayi zafi shiba wutaba, zauna ki huta Dan ALLAH.......
Duka takaima Rahma ummi ta kare, Safna kishiga hankalinki danifa, uwarmi tamiki daga shigowa?.
Cikin huci ta ce, "ummi kinajinfa maganar datake fad'amin, ALLAH yarinyarnan ta rainani, zan koya miki hankali kwanannan wlhy.
Ummi ta tamke fuska tana nunama safna hanya, kinga tashimin anan.
Ran safna a6ace tabar wajen tanufi d'akinsu tana mita.
Rahma kam ta sauke ajiyar zuciya tana k'ara gyara kwanciyarta.
Ummi ma kai ta girgiza ALLAH ya shiryaki Safna tafad'a tana shafa kan Rahma.
Safna tacire kayanta tanata masifa harta shiga wanka, (nikam mamaki take bani, Dan banga abin fad'aba anan).
Rahma tanason shiga d'akinsu tayi wanka tana tsoron masifar Safna, Dan tasan wlhy bata bartaba, k'ilama yau kwana zatayi bala inta da mitar tsiyarta.
d'akin umminsu tanufa dantayi wankanta kawai, yafi sauk'i.
+++++++++++++++
Bobo yana kwance ad'akinsa sai juye2 yakeyi, barci yakesonyi amma yak'i d'aukarsa, maganar Ammi ce kemasa yawo akwakwalwa.
Yasan Ammi sairai babu sauk'ice, indai Abu ya6ata mata rai saita d'auki mataki, shikam yana tsoron zancennan yaje kunnen Appansu, yad'an cije le6e yana sauke numfashi, tund'azu soyake yafita amma yana shakkar had'uwa da Appa.
Yasan fita tazame masa tilas Dan dole zasu had'u wajen cin abinci.......
Bai rufe bakiba aka buga k'ofar, batarda ya d'agoba ya ce, "ashigo.
Khairiyyace k'anwarsa, cikeda da tsoro ta ce, " yaya kazo wai aci abinci.
Hannu yad'aga mata kawai, bata gane nufinsaba Dan haka ta ce, "ka k'oshi kuma yaa Bobo!?.
Harara ya watso mata sannan yamik'e, da sauri tayi waje, shikuma yad'auki doguwar riga fara yazura yafito.
Kowa ya hallara shikad'ai ake jira, rissinawa yayi yagaida Appa da Ammi sannan yazauna.
Khursiyya ta ce, " yaya ina yini, harara ya watsa mata, ya ce, "k d'azu dasafe miya hanaki wankemin bayi?.
Kanta ak'asa ta ce, " wlhy yaya ina uzirin makarantane, dakuma nadawo na manta.
Tsaki yaja kawai baisake cewa komaiva.
Ammi tazubama Appa abinci, tasakama kanta, kairiyya kuma tasakama bobo shima, suma suka zuba.
Nawal tana kusada Appa.
Suna cikin cin abinci kamar antsikari Nawal ta ce, "aunty khursiyya.
Na'am Nawal miya faru?, khursiyya ta fad'a.
Cike da murna ta ce, " Ammi tace nima ankusa kawomin momyna.
Ayya my dear natayaki murna.
Ran bobo yak'ara 6aci, fuska ad'aure ya gallama Nawal harara, Appa da Ammi suna kallonsa, amma basuce komaiba.
Itama Nawal saitayi shiru kafin ya bibbigeta, Dan dukda yana wasa da ita hakan bai hana yaci k'aniyartaba idan ta k'uleshi.
Harsuka kammala cin abinci babu Wanda yakuma cewa komai, bayan sun kammala kowa yakama gabansa.
Bobo yaji dad'i Affa baimasa maganaba har dare.
Da daddare yana zaune a babban falo daga can gefe, wasu buks yake dubawa, khairiyya da khursiyya da Nawal suna zaune suma kallo sukeyi, Ammi tasakko daga d'akin Appa, takkali Bobo da hankalinsa kekan bincike ta ce, "Mukarram kaje Appanku na kiranka.
Wani irin fad'uwar gaba da tsinkewar zuciya suka sameshi a lokaci d'aya, bakinsa yana rawa yace Ammi lfy kuwa?.
Babu komai mikake tunani?.
" kai ya girgiza mata yana sauke ajiyar zuciya."
Asanyaye ya haura saman Appa, Appa nazaune yana kallon labarai Bobo yashiga da sallama.
Fuska asake Appa ya amsa, bayan yazauna ya ce, "Appa gani.
Appa dattijo mai hikima da iya kama mutum, saiyayi murmushi, dama bawani Abu bane, inasonjin ya shari'arku da B.. Sadiq?.
Ajiyar zuciya bobo yasauke wadda hartaso bama Appa dariya amma saiya dake.
Komai yayi Normal Appa, Dan insha ALLAHU zuwa Monday komai zai k'are, alk'ali zai yanke hukunci.
A to Alhmdllh haka nakesonji, daga nan Appa yacigaba dajansa da hira harya saki jikinsa.
Cikin hikima Appa ya ce, "Mukarram waini yamaganar aurene?, kodai haryanzu?.
Bobo yad'an Sosa gefen wuyansa Appa Dan ALLAH kudaina yawan damuwa akan aurena insha ALLAH zanyi amma ba yanzuba.
Tofa, bayanzuba sai yaushe Mukarram?, koso kake saika tsufa agidane?, ai ko bakayi aure Dan kankaba kayi Dan Zuhra, kullum maganar yarinyar nan momy momy to yakamata asamo mata momyn nan.
Inkuma bazaka iyaba ba awannan karonma zan samo maka matar aure, Dan naga kai tsoron matan kakeji.
Appa kayi hak'uri, ak'aramin lokaci, insha ALLAHU nanda k'arshen shekara zanyi.
Appa yad'an zaro ido, Mukarram karshen shekarafa kace?, kai kana ganin zamu iya barinka harnan da watanni Tara babu aure, nifa nagaji da ganinka hakanan gsky.
Ammi tashigo hannunta d'auke da tire, yaa is'haq yana biye da ita.
Appa ya ce, "yauwa aii gara dakukazo.
To miya faru Alhaji?.
A'a wai Murarram nakeyima zancen sure, shine yake rik'ona abarsa sai k'arshen shekara.
K'arshen shekara kuma ya ishaq yafad'a yana kallon Bobo dayake wani 6ata rai. Kai idan anbarka zuwa k'arshen shekarar saika yarda?.
" emana yaya aii nake ganin zaifi ko?.
shin wai Abdulmalik kodai bakada lfy ne?.
Yaya banida lfy kuma kamar ya?.
Harararsa ya ishaq yayi ya ce, " bansaniba.
Appa ya k'atsemusu zancen dafad'in Ishaq babu wani abinda ke damunsa iya shegene kawai irin nasa. Amma nima abin yana bani mamaki wlhy, hakamafa lokacin aurensa na farko mukaita fama, kokuwa maganar ishaq gsky ce?.
Ran Bobo yakuma 6aci, aii dama yasan tunda wannan masifaffen yazo saidai ALLAH, gashinan yak'arama wutar fetir.......
Appa yakatsema Bobo tunani da fad'in Mukarram baka jinane?.
Kansa ya girgiza, murya a sark'e ya ce, "wlhy Appa lfy ta k'alau.
Appa ya kalli ammi, kai ammi ta girgizama Appa kawai.
Appa yayi murmushi, ya ce, " shikenan Mukarram tashi kaje, ALLAH yakaimu k'arshen shekarar.
Yakwa mik'e yana washe baki yafice, azuciyarsa ya ce, "su yaa Ishaq ansamu game over.
(Nikam dariya yabani, Dan k'ila shine mai game over d'in).
Ammi ta ce, " Alhaji nifa ban fahimcekaba?.
Appa yay murmushi, yanzu zan fahimtar daku, shekaran jiya naje mun gaisa da abokina Alh bilal, anan nakemasa maganar ranshin auren Mukarram abin yana damuna.
To yanzudai azancen nan danake muku munyanke hukuncin had'a auren mukarram da 'Yar wajensa.
Ammi tayi murmushi tana fad'in Alhmdllh, kai nayi farinciki wlhy, ALLAH ya tabbatar da alkairi.
Amin ya ishaq yafad'a shima fuskarsa cike da annuri.
Ya gaida Appa Dan ko gaisawa basuyiba ma, daganan suka tattauna akan bikin, ya Ishaq yatafi...........
*_rubutu hikimace da baiwa ta musamman gsky, shiyyasa bazan gajiyaba da yabonki aunty bilyna🤙🏻❣👌🏼._*
[11/12, 2:14 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
7⃣&8⃣
_washe gari_
Da wuri Bobo yatashi yay shirin zuwa wani bincike akan shira dazaiyi.
Fes yakejinsa akan maganar dasukayi jiya da su Appa.
Yafito sanye cikin shadda ruwan k'asa d'inkin boda, kayan sunmasa k'yau sosai, sai tashin k'amshi yakeyi, wayoyinsa yad'iba da jakar aikinsa.
Babu kowa afalon ya kalli bak'in agogon fata dake d'aure a tsintsiyar hannunsa 7:23am, yasan yanzu babu Wanda yatashi, Dan al'adar gidance indai sukayi sallar asuba sukoma barci, ficewarsa yayi saboda yanada uzuri.
Yabude d'ayan gefen motarsa yazuba kayan hannunsa sanan yazagaya yashiga ya zauna.
Saida yatsaya suka gaisa da maigadi sannan yafice, anguwar shiru babu hayaniya saidai iskar Safiya dake kad'awa, gakuma rana tad'an hasko maibada d'umi mai dad'i, cikin nutsuwa yake juya sitiyarin tamkar bayaso, yafito daga layin gidansu yahau babban titi, tafiya kad'an yayi saiya hangi taron jama'a a tsaitsaye agefen titi, wasuma daka gansu suna cikin rud'ani, harya wuce saiya dawo baya yanemi guri yay fakin.
Fitowa yayi daga motar yanufi wajen taron jama'a.
Malam lfy kuwa?, yatambayi wani matashin saurayi daketa zage2.
Saurayin ya balla masa harara, kacemin lfy kuwa, aii dama duk irinkune, kud'i sunsaku bakwa tsoron ALLAH, gani kuke komai kukayi kunada kud'i zasu kareku........ Hannu Bobo yad'aga masa, kaga bawannan nake tambayarkaba nikam, mike faruwa anan?.
Saurayin ya share hawayensa sannan ya ce, "wani mara imanine yayma yarinya fad'e yazo nan ya yardata.
Fad'e!!, Bobo yafad'a arazane, da sauri yafara kutsa kai cikin taron jama'ar batareda ya saurari maganar da saurayin yake masaba.
Innalillahi wa'inna ilaihirraji'u yafad'a yayinda yay tozali da k'aramar yarinya kwace tamkar gawa.
Da sauri ya rarumi yarinyar batareda yakula da jinin dake zuba ajikintaba, wasu daga cikin mutanen suka fara tambayarsa koya Santa?.
Bai sauraresuba yabud'e mota yasakata abaya, harya shiga mota yakira saurayin d'azu ya ce, " shiga muje.
Babu musu saurayin yashiga, Bobo yaja motar a 360 suka nufi asibiti.
Azuciyarsa yana Addu'a ALLAH yasa ya Sulaiman yana asibitin.
Suna Isa aka amshesu cikin gaggawa Dan ansanshi k'anine gamai asibitin.
Ma'aikatan masu gaisheshi ya tambaya ya sulaiman yazo?.
A'a baikai ga k'arasowaba wata matashiyar budurwa tafad'a cikeda sanabe.
Baibi takantaba yafara kiran ya sulaiman.
Bugu d'aya ya d'auka.
Cikin zolaya ya ce, "Bobon Ammi ya akayi?..
Muryar bobo na rawa ya ce, Yaya kana ina?.
Ina hanyar zuwa asibiti miya faru?.
Alhmddlh Bobo yafad'a, saika k'araso kawai, nima ina asibitin, baijira amsar ya sulaimanba ya yanke wayar.
Gudu ya sulaiman yak'ara danjin Bobo ya ce, " yana asibiti.
Cikin k'an k'anin lokaci ya iso, atsorace yake kallon jikin bobo da jini ya 6ata.
Bobo daketa safa da marwa ak'ofar d'akin da aka shigar da yarinyar ya hango yaa sulaiman yashigo cikin asibitin arazane.
Cikin hanzari yatareshi, yayana Dan ALLAH ka taimaki yarinyar nan karta mutu plzzz.......
Cikin rashin fahimta ya sulaiman ya ce, "nutsu Abdulmalik miya samu Nawal d'in?.
Yaya ba Nawal bace wata yarinyace, kaje wajenta zanmaka bayani daga baya plzzz.
Ya sulaiman yasan halin bobo da rikici Dan haka da Sauri ya afka d'akin Dan ganema idonsa.
Kansa yadafe cikin tashin hankali yafara yima Nos masifa akan sunzubama yarinyar ido babu abinda sukai mata.
Kayi hak'uri sir aikin banamu bane dole saikazo, inazaton Fad'e akamata.
Ajiyar zuciya ya sauke, taimakon gaggawa yafara bama yarinyar.
A waje kam Bobo yakasa zaune yakasa tsaye, sai kaida kawo yakeyi, hankalinsa atashe, yanzunan haka al'umma suka lalace akan zalinci?, insha ALLAHU saiya k'ar6oma yarinyar nan 'yancinta, zaiyi bincike kod'an gidan ubanwaye saiya gurfanar dashi a gaban shari'a.
Wayarsa dake wringing ya Ciro a aljihu, Br..... Kamal yagani, yarintse idonsa Dan yamanta abinda ya fiddoshi daga gida, bai d'agaba har wayar ta yanke aka k'ara kira.
Daurewa yayi ya d'auka suka gaisa, AA Hamshak'i wai ya akayine?, kacemin kafito gida amma najika shiru.
Sorry Kamal ina nan zuwa, wlhy wani abune ya rik'rni ahanya, amma plz kabani minti talatin zuwa arba'in zan iso.
Okey saina ganka.
A can kuwa bobo nabarin wajen police suka zo, mutane suka sanar dasu wani ya d'auki yarinyar zuwa asibiti.
Wane asibin ne?, wani d'ansanda ya tambaya fuska atamke.
Muma bamu saniba wlhy, amma antafi damai shagonnan, suka nuna shagon dake kusadasu.
d'ansandan baice komaiba yashiga mota suka juya.
Gulma mutanen gurin suka fara da zagin 'yan sandan, wai sai yanzu suka gadamar zuwa, bayan tun d'azu aka kirasu.
Wani ya ce, "bar munafukai malam aii k'asarnan munga takanmu, buharine kawai ke k'aunar talaka, (ALLAH dai ya k'ara masa lfy).
Amin ya rabbi Garzali.
+++++++++++++
Safna tafito sanye cikin atamfa Riga da siket, sunmata d'am kamar zata fashe.
Rahma ta kalleta ta girgiza kai, wannan lamari na 6ata mata rai, ita bataga wayewaba ga mace mai saka suturar dake fidda jiki, shiyyasa fad'e yaketa k'ara yawa aduniya, to matan basusan darajar jikinsuba, (suyita fiddo jiki tamkar akuyoyi da sunan wayewa).........
Me wait lfy kike kallona?, karfa ki cinyeni wlhy.
Rahma takauda kai saga kallonta, ta ce, " aikinsan Nina mayya bace.
Da sauri safna takai mata duka, to ubanwaye mayen?.
Rahma ta kauce tana dariya, maida wuk'ar ta hannun damar Abba, Dan ALLAH zanbiki makarantar wlhy zaman gidannan ya isheni.
Safna ta harareta tozoki hau kaina uwata.
A'a ALLAH yabaki hak'uri, yi tafiyarki zanje gidan yaa Munir nama taya aunty Naja'atu aiki.
Yafimiki sauk'i, dama da 'yan aiki kike kama aii, safna tafad'a tana ficewa.
Baki Rahma ta ta6e tareda Jan tsaki.
Ummi tafito tana fad'in kekuma lfy?.
Lfy lay ummi nida aunty Safna ne.
Ina Safna d'in?.
Tafita makaranta.
Shine yau ko sallama babu?, dariya Rahma tayi ta ce, "haryanzu aljanun masifar nasu saukaba.
Ummi batace komaiba tashige kicin.
+++++++++++++
Asibiti kam lamura saidai addu'a bak'aramar mugunta akaima yarinyarba, amma cikin ikon ALLAH yaa sulaiman yayi nasarar ceto ranta.
Bak'aramin lokaci ya6ataba kafin yafito, zuwa yanzu bobo na tsaye jingine da bango ya hard'e hannuwansa biyu ak'irji, k'afarsa d'aya dogare a bango fuskarnan d'aure tamau.
Ya sulaima yafito yana shere zufa, da sauri Bobo ya taresa, Yaya ya jikin nata??.
Alhmdllh. ya sulaiman yafad'a, yaja hannun Bobo suka shiga office d'insa.
Koda ya zaunar dashi saiya bude firij yad'akko fresh milk ya tsiyaya a kofi yamik'ama Bobo.
Bobo ya ce, "ya.... Hannu ya d'aga masa, kaga k'ar6a kasha kasamu nutsuwa, nasan ko karyawa bakayiba kafito.
Ajiyar zuciya Bobo yayi, yakar6i kofin yasa abaki, ahankali yakesha harya shanye tas.
Cikin zolaya ya sulaiman ya ce, " Bobon Ammi damadai yunwa kakeji, ko a k'ara?.
Murmushi yayi batareda yace komaiba, ya girgiza kai.
Ya Sulaiman ya zauna yana dariya, saida yayi rubuce2 sannan yad'ago ya kalli k'aninnasa, Abdulmalik ina kasamo yarinyarnan?.
Ajiyar zuciya Bobo ya sauke shima yayan nasa yake kallo, ya ce, ''Yaya wlhy abakin titi..... Nandai yakwashe komai yasanar dashi.
Girgiza kai ya sulaiman yayi, ya ce, ''ALLAH ya saka mata, amma yanzu yakamata musan iyayenta kafin ad'au mataki, sannan ina yaron dakace kunzo tare?.
Yana nan awaje.
Wani Abu ya sulaiman ya danna, saiga Nos tazo, ya ce, "akwai wani saurayi anan waje shigomin dashi.
OK sir.............
*_kuyi hak'uri ina muku typing bakamar aunty billy ba, wlhy akwai wahala, writers suna k'ok'ari gsky, ALLAH dai ya biyasu._*🙏🏻
*_" luv u aunty bilyn Abdul"_*
[11/12, 2:15 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
9⃣&🔟
Assalamu alaikum.
Wa'alaikassalam yaa sulaima da bobo suka amsama saurayin.
Gurin zama yaa sulaiman ya nuna masa, bayan ya zauna yabasa hannu sukayi musabaha.
Ya sulaiman ya ce, "d'an uwa ance awajenku aka samu yarinyarnan ko?..
Eh anan akazo aka yardata wajen misalin k'arfe 6:44am, fitowa ta kenan zan bud'e shagona naga wata jar mota ta tsaya agurin, nasan su basu ganniba nida abokina Nura, Dan saida suka wawwaiga sukaga babu mai kallonsu sannan aka turota waje.
Bobo ya cije le6ensa zuciyarsa na k'ara zafi.
Ya sulaiman ya jinjina kai, Yakuma fad'in to kunsanar da police?.
Eh suna barin wajen muka kira 'yan sanda, amma har bawan ALLAH nan yazo ya d'auketa basu zoba.
Ya sulaiman ya sauke numfashi, babu damuwa ayanzu nasanar da wani d'an sanda dan kes d'in dolene police sushiga, namata abinda duk yadace, kuma narubuta bayanai akan komai.......
Kwankwasa k'ofarne yahana yaa sulaiman cigaba da magana, wata nos tashigo tana sanar dashi wani police nason ganinsa.
Shigo dashi mana ya sulaiman yafad'a.
Bayan d'an sandan yashigo shida wani suka gaisa dasu bobo sannan sukayi musu bayani akan komai.
Har d'akin da yarinyar take aka kaisu, bobo tamkar yay kuka danganin yarinyar, shidama haka yake da tausayi dukda kasancewarsa masifaffe.
Bayan sun kammala komai 'yan sandan suka tafi, shima saurayinnan yatafi akan zasu sake nemansa.
Ya ce, "insha ALLAHU duk sanda sukazo zai basu had'in kai.
Godiya sukai masa yatafi, bobo yay masa alkairi.
Ya sulaiman ya kalli bobo, Abdulmalik kaima yakamata katafi gida ka canja kayannan duk sun 6aci da jini.
Sai asannan yakula, yad'anyi tsaki wlhy yaya bamma kulaba, bari naje wajen Br kamal Dan yana jirana, idan muka gama saina koma gidan.
Dadai kafara zuwa ka canja kayan tukunna.
To yaya bari naje, saina dawo.
Okey saika dawo.
Saida sukad'an rungume juna sannan sukai musabaha yatafi.
+++++++++++++++++
Rahma tafito sanye cikin dogon hijjab har k'asa yake ja, hijjabin mai hannune Dan haka hannunta rik'e da fos, sallama tayima ummi sannan tafito.
Ta wawwaiga bataga idiris diraiba ba, d'an tsaki taja ta k'arasa wajen mai gadinsu, rissinawa tayi ta gaisheahi.
Ya amsa cike da fara'a, yana k'aunar yarinyarnan saboda hankalinta da girmama nagaba da ita, halinta ya banbanta da yayarta sosai.....
Rahma tak'atse masa tunani da fad'in baba ina Idris!.
aiko d'iyata Idris yaje gida yanzu babu dad'ewa, kinsan suna cikin tashin hankalin 6atan k'anwarsu tun jiya da yamma.
K'anwarsu kuma?, 6ata tayi?.
Wlhy kuwa haka yake gayamin d'azu, wai tunjiya bata dawoba daga aikenta.
Tofa ALLAH yabayyanata, Toni bari naje na hau adaidaita.
diyata dakanki?, toki tuk'a kanki mana.
Murmushi tayi ta ce, "A'a baba, Abba ya hanani tuk'i."
ALLAH sarki 'Yar albarka, aii haka akeson mutum yaringa bin maganar iyayensa, ALLAH yay miki albarka, yabaki miji nagari.
Murmushi Rahma tayi, ahankali tace ngd baba saina dawo.
To adawo lfy.
Rahma tafito daga gida, tad'an wawwaiga anguwar babu mutane sosai, sai jefi jefi, dakuma motoci dake fitowa daga gidaje inaga masu Fita aikine da kasuwa.
Ajiyar zuciya ta sauke sannan tafara tafiya da addu'ar ALLAH yasa tasamu adaidaita da wuri, Dan tsakaninsu da titi da nisa.
Tad'anyi tafiya kanta ak'asa, jitai ance a'a Rahma sai Ina?.
Ad'an tsorace tad'ago takalli inda aka ambaci sunan nata, tayi murmushi lah ya kamal kaine.?.
Nine Rahma ykk?.
Lfy lau yaya, lfy naganka anan?.
Wlhy lfy k'alau wani abokina nake jira, amma shiru bai zoba shine naked'an shan hantsi anan.
Ayya, yasu momy da aunty Ameera.
Lfy lay suke, bazaki Shigabane?.
A'a yaya gidan ya Muneer zanje wlhy ka gaidaminsu.
Zasuji, to amma ina direbanku kika fito ak'afa.
Hummm wlhy wani d'an uzuri yarik'eshi.
Okey, to amma ba girmanki bane.
Dariya tayi kai yaa kamal to miye girmana?.
Kafin yabata amsa wata mota ta tsaya adaidai saitinsu.
Kamal ya ce, "ga abokina nan ya iso.
Waigawa tayi takalli motar, saikuma tadawo da kallonta kan kamal, tom nikam nawuce.
Bazaki tsaya Ku gaisaba.
A'a yaya aii bai sanniba.
Bobo yafito daga motar fuskarsa babu yabo babu fallasa, yad'an kalli Rahma datazo zata gitta ta gefensa, kanta ak'asa ta gaisheshi.
Ya amsa da lfy, yana kauda Kansa daga kallonta.
Gaba tayi tana Jan tsaki, dukda bata kalleshiba abin yabata haushi, tana bak'in cikin ta gaida mutum ya ce, " mata lfy."
Bobo yak'arasa wajen kamal suka gaisa, sannan suka Shiga cikin gidan.
Rahma kam tana k'ara 'Yar tafiya tasamu adaidaita tashiga.
.+.+.+.+.+.+.+.+.+.
Safna Ana makaranta, yau itace harda zuwa office d'in yaa Hamza amma ta tarar baizoba.
Basira ta kalli safna daketa jan tsaki tana kallon agogon hannunta, wai safna lfy kuwa?, naga kinsamu zuwa office d'in malam Hamza miye dalili?.
Zeenat dake zaune gefensu ta ta6e baki, kazar wahala ALLAH ya yanka mata shiyyasa tafara figa.
Kazar wahala kuma kamar ya?.
Zeenat tabama Baseera labarin abinda yafaru jiya, Dan ita batazo school ba.
Wata dariyar mugunta Baseera tasaki, o, ni Baseera wai yau Safna kece saurayi ya sacema zuciya?, lallai zanso ganin wannan guy mai suna Bobo, nasan tabbas ya amsa sunansa bobo.
Hummm kibari kawai Baseera wlhy jiya banyi barciba, mafarkinsa nayitayi, harda mafarkin munyi aure harda yara.
Dariya zeenat da Baseera suka saka harda cafkewa.
Safna ta 6ata rai tana hararsu, kuga nifa banason ciki da iskanci kunsani, zeenat damafa haushinki nakeji, Dan maganar jiya ta 6atamin rai wlhy.
Cikin dariya zeenat ta ce, "afwan Tawan, ALLAH yabaki bobo.
Amin, namasan yabani tunda har yasamun sansa azuciyata.
Zeenat tad'an ta6e baki tana fad'in garadai adogara ga ALLAH.
Baseera tai saurin kar6ewa toda dake tace ta dogara?, Safna karki damu ina bayanki d'ari bisa d'ari, kota halin k'ak'a saikin mallaki Bobo.
Safna tayi murmushi shiyyasa nakesonki k'awata ALLAH yabarmu tare ngd.
Zeenat tana jinsu bata kuma tankawaba.
+.+.+.+.+.+.+
_3:30pm_ Bobo yashiga cikin asibitin, kai tsaye office d'in ya sulaiman yanufa, suka gaisa ya tambayi yamai jiki?.
Da sauk'i Bobo, aiina zata bazaka dawoba?.
Tab yaya wlhy hankalina yana asibitin nan, yanzu haka bamu gama aikinba nabarma Br kamal nataho, yaya ta farka kuwa?.
A'a har yanzu tana barci, ana buk'atar tahuta sosai yanda zata tashi k'wak'wal warta Normal, ta wannan hanyarne kawai zamuyi saurin samun bayanai daga gareta.
Okey tom ALLAH yabata lfy.
Amin Mukarram d'in Appa, mai suna kalakala.
Dariya Bobo yayi ya ce, ''yaya aii duk kune kuka mak'ala mini.
Sukayi dariya harda tafawa kamar wasu abokai.
Sai k'arfe 5:00pm dai dai sukabar asibitin, kuma har sannan yarinyar bata farkaba, kai tsaye gida suka nufa har ya sulaiman shima zai gaidasu Ammi.
Kowaya yafito cikin motarsa suka nufi cikin gidan suna 'yar hira.
Gaba d'aya mutanen gidan suna falon sama, Dan haka suma can suka nufa............
*_luv u oll fan's d'in aunty bilyn Abdul❣💓❣😁👌🏼._*
_Ngd da had'in kanku_
[11/12, 2:15 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1⃣1⃣&1⃣2⃣
Da gudu Nawal ta taso ta rungume ya Sulaiman, yad'agata sama yana dariya, Nawal kin k'ara nauyifa yafad'a yana lakatar hancinta.
Ta kalli daddynta ta ce, "baby waikaji uncle yace nak'ara nauyi.
d'an hararta yayi cikin wasa, ya ce, "sai yanzu kika ganni baby.
A'a baby naganka tun d'azufa, nafara gaida uncle ne ko uncle?.
Ya Sulaiman yad'aga mata kai yana dariya, cikin falon suka k'arasa.
Bobo ya ce, "o kace yau family ya had'u?.
Ya Is'haq da ya Hamza, sukayi dariya suna mik'a musu hannu.
Khairiyya da Khursiyya ma dariyar sukeyi.
Guri suka samu suka zauna, ya Hamza ya ce, " ashe kuna tare?.
Eh wlhy muna tare, naje Asibitinne.
Tofa miya sameka?, cewar ya Is'haq.
No bani bane wata yarinyace......
Fitowar Ammi ta k'atse masa zance, tazauna cike da farin cikin ganin manyan 'yayan nasu.
Gaidata ya Sulaiman da bobo sukayi, fuskarta cike da fara'a ta take amsawa, tareda tambayar aikinsu dakuma iyalin ya Sulaiman.
Suna lfy wlhy Ammi.
Ammi ta kalli bobo, Mukarram yadai naganka wani iri?.
Fuska ya shagwa6e yana kallon Ammi, ALLAH Ammi nagaji over yau, kaina hard'an ciwo yakeyi.
Yanda yay maganar a shagwa6e saiya basu dariya.
Ya Is'haq ya ce, "Bobo shagwa6ar dakayi ko Nawal bata yinta.
Murmushi yayi kawai baice komaiba.
Ammi ta ce, " kubarmin Mukarram d'ina yayi shagwa6arsa lokacinsane ko bobon Ammi?.
Nanma dariya sukayi gaba d'aya, ya harari su khairiyya dake tuntsura dariya harda rik'e ciki.
Ku yarannan nakulafa kun fara rainani?.
Ya Hamza ya ce, "to aii abin dariya kayi, saika hanasu su dara?, kawai kayi maganin abun.
Bobo ya ce, " ta yaya kenan?."
Kayi aure kabar musu gidan cewar ya Sulaiman.
Mik'ewa Bobo yayi danjin and'akko maganar dabayaso, kunga bari nad'an watsa ruwa nadawo.
Baridai kagudu idan angama maganar kadawo, ya Is'haq yafad'a yana dariya.
Nanma dariya kowa yasaka harda Ammi.
Shikam yay shigewarsa d'aki yana fad'in kwa gaji kubarni.
Ammi ta ce, "nidai inaga Mukarram tare yake da aljana shiyyasa baya son maganar aure.
Ya Sulaiman ya ce, "Lah Ammi wane irin aljana kuma?, wlhy ras yake, shidai haka ALLAH yayosa bashida matsala da mace.
Hakadai kuke gani, nifa abinda na lura dashi ga Abdulmalik kawai bazai iya tunkarar mace ya ce, yana sonata bane, gani yake ajinsa zai zube kawai.
Hhhhhh wlhy hakane Hamza, Bobo dakake ji dagani akwai d'aukar kai agaban mata kai harma mazan, kamar wani jinin sarauta.
Dariya aka kumayi, Ammi ta ce, " aii yashafi sarautar, kunfa takurama yarona gsky.
Ya Is'haq ya ce, "ALLAH ammi yaron nan yawuce yanda kike zato, amma kwanannan zamuyi maganinsa, aure zamu MASA kawai.
Dakun k'yautamin wlhy, nidai nagaji da ganin Mukarram babu mata, nasan har yanzu rashin Ni'ima na damunsa, amma idan yayi auren ALLAH yasa aka dace da matar k'warai komai zai zama tarihi.
Insha ALLAHU ammi komai yazo k'arshe karki damu...
Daga nan suka cigaba da tattaunawa, annan ma ya Sulaiman take basu labarin yarinyar da bobo yakai asibiti da safe.
Zancen ya girgizasu daganan suka Shiga tattauna matsalolin fad'e da yara k'anan suke fuskanta ak'asar nan.
+
Bobo kam yana Shiga d'aki yacire kayansa, wanka yashiga yayo, yashafa mai yazura doguwar Riga blue da dogon wando bak'i.
Falo yadawo Inda 'yan uwansa suke akacigaba da hira da tattauna al'amuran rayuwa, ahaka har Appa yadawo.
Gaba d'aya suka mik'e cikin girmamawa sukayi MASA sannu.
Fuskar Appa cike da annuri yabi matasan samarin 'ya'yan NASA da kallo, masha ALLAHU yaukuma gidan cike yake da basawa.
Dariya sukayi danjin furicin mahaifin nasu.
Ya ce, " bari naje nawatsa ruwa sainazo ayi hirar dani ko?.
To Appa asakko lfy sukafad'a atare.
d'akinsa yanufa rik'e da hannun Nawal data k'ar6ar MASA jakka, dama kullum itace mai kar6a inhar tadawo school.
Hirarsu suka cigaba dayi, kiran sallah yasa suka mik'e sukayi alwala, Appa yafito ya samesu suka tafi masallaci abin gwanin sha'awa, shima Appa sai dad'i yakeji ganinsa cikin samarin 'yayansa ababen alfaharinsa.
Ko'a masallaci sun burge mutane, Dan a sahu d'aya suka jera reras.
Agidama khairiyya da khursiyya da Nawal sallar sukayi, ammi ma haka.
Bayan an idar ammi tasakasu suka shirya abinci a tsakkiyar falon Dan yau duk su ya Is'haq anan zasuci abinci, suka gama shirya komai da taimakon 'yan aiiki sannan suka koma d'aki domin gabatar da sallar isha'i da aka kira.
Basu dawoba saida akayi sallar isha'i, suka rankayo zuwa gida suna 'Yar hirarsu da tsokanar juna.
Afalon suka zube Appa ya ce, ''aini zuwannan naku yamin daidai, kamar kunsan dama ina nemanku.
Ya Hamza ya ce, "to Appanmu ALLAH yajishemu alkairi.
Amin suka fad'a gaba d'aya.
Ammi dasu khairiyya suka fito suma, rissinawa sukayi suka gaida Appa da yayyensu, Nawal taje jikin Appa tazauna.
Yashafa kanta yana fad'in amaryata kinyi sallah?.
Kai ta jinjina tana dariya.
Tomi kika rok'amana?.
Hannunta tasa abaki idonta na kallon p,o,p d'in falon alamar tunani, can takalli Appa tana washe wawulinta da hak'ori biyu yafad'i, ta ce, " Appa kasan mina rok'a?.
Saikin fad'amin amaryata.
Narok'i ALLAH ya kaimu Aljanna nida kai, da Ammi, da baby, da uncle Sulaiman, da uncle Hamza, da Uncle Is'haq, da aunty khursiyya da aunty khairiyya, da mom din gida uncle Is'haq, da momyn ya Ahmad da aunty Sameera, kuma nace ALLAH yasa muje makakka muduka sau dubu dubu babu iyaka muga kabarin Manzon ALLAH a madina.
Tafi sukai mata gaba d'aya suna fad'in ameen mai sunan manya.
Ya Is'haq dake kusada ita har sumbatar hannunta yayi.
Appa ya ce, ''lallai na more da amarya Ashe.
Ta ce, "Appa kasan mikuma na rok'a daga k'arshe?, ya girgiza kai yana murmushi, canayi ALLAH yasa nima naga momyna.
Gaba d'ayansu kallonta sukayi, tabasu tausayi sosai, Appa ya rungumeta cikeda tausayi, Bobo kam k'asa yayi da kansa zuciyarsa tayi rauni sosai, jiyake tamkar yafasa kuka saboda tausayin 'yarsa, tausayinta yana d'aya daga cikin abinda yasa yak'i k'ara aure, bayason ya auro wadda zata takurama d'iyarsa sanyin idaniyarsa.
Ya Hamza ya ta6ashi d'agowa yayi yana kallonsa, ya Hamza ya jinjina masa kai fuskarsa d'auke da tausayi.
Murmushi bobo yayi.
Saikuma ya kalli sauran 'yan uwannasa da iyayensa yaga dukshi suke kallo.
Kansa yamaida k'asa yana cigaba da murmushi mai ciwo.
Ganin haka Ammi ta katsesu da fad'in bismillah kusauka ga abinci.
Kowa ya sakko tskkiyar falon in da abincin yake.
Bayan Ammi tasakama Appa kowa yafa k'ok'arin zubama Kansa abinda yakeso.
Falon yayi tsit bakajin motsin komai sai k'arar filat da cokali, saikam surutun Nawal lokaci2.
Bayan sun kammala cin abincin 'yan aiki suka gyara wajen tsaf, Appa yakalli khairiyya ya ce, "auta zoki kaita d'aki ta kwanta.
To Appa khairiyya tafad'a tana mik'ewa, d'aukar Nawal tayi daga jikin Appa tanufi d'aki.
Falon yay tsit kowa ya maida habkalinsa kan Appa.
Appa yamusu sallama suka amsa.
Ya gyara zama cikin hikimar zance yafara musu nasiha da k'ara jaddada musu muhimmancin zuminci da hak'uri da juna, ahankali ya gangaro kan auren Bobo, Wanda tunda Appa ya ambaci sunansa gabansa yafad'i.
Appa yabasu labari kamar yanda yagayama su Ammi da ya Is'haq jiya.
Ya d'ora da fad'in yanzu dai mun yanke hukunci ranar juma'a idan ALLAH ya kaimu za'a tura dakomai har sadaki Dan badogon lokaci za'a d'aukaba, k'arshen watannan za'ayi bikin kowa ya huta.
Zuface tafara fita addukan sassan jikin Bobo, yakasa koda motsi dukda tsokanarsa da 'yan uwansa sukeyi suna fad'in ango kasha k'amshi.
Ammi ma sai dariya takeyi danjin dad'i, sai Alhmdllh take dad'i, su khursiyya kam harda 'yar bud'a.
Bobo ya galla masu harara.
Gaba d'aya akayi dariya harda Appa.
Daganan suka cigaba da tattauna yanda biki zai gudana da shagalin daza'ayi.
Appa ya ce, " suyi duk abinda sukeso bazai hanasuba, Dan Andad'e ba ayi wani shagaliba agidan.
Har k'arfe tara suna gidan, saida Appa yace yakamata sutafi gida hakanan wajen iyalinsu sanan suka mik'e kowa yanufi gidansa.
Bobo bayan yarakasu harabar gidan yanufi d'akinsa jikin a sanyaye, yama rasa wane irin tunani zaiyi shikam.............
_Tofa masu karatu, Yaya kenan?, shin ina Safna?, gafa gwaninta zai angwance, kowacece amaryar Bobo?, ya wannan zama zai kasance?, kudai biyoni kawai, basirar aunty bilyn Abdul ce, nikam copy nakemuku masoya._
*_hummm wasa farin girki, masoya yanzufa aka fara, kumuje zuwa wai mahaukaci yasai kura, yanzu muka dasa alk'alamin labarin Bobo!._*
*_masoya muna godiya ALLAH yanar zuminci._*
[11/12, 2:15 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1⃣3⃣&1⃣4⃣
*_Gidansu Safna_*
Safna na kwance akan gado tana chart, sai faman murmushi takeyi, da alama tana jin dad'in charting d'in.
Rahma dake zaune akan sallaya tana karatun alkur'ani ta waigo ta kalli safna dataketa 6a66aga dariya harda rik'e ciki, kai Rahma ta girgiza tareda fad'in ALLAH ya shirya azuciyarta.
Kanta tamaida tacigaba da karatunta.
Safna kam bamatasan tanayiba, dariyarta taketayi cikin farinciki, hira takeyi da Baseera akan nemomata Bobo, Baseera tana gayamata akwai wani guy a unguwarsu sunansa *boy shiyakama subama aikin, Dan tasan cikin sauk'i zai samomusu bobo da labarinsa.
Tak'ara wani d'an ihun farinciki, tareda fad'in saini mata agidan Bobo.
Rahma takuma kallonta cike da mamaki, ganin bazata barta tayi karatunta cikin Nutsuwaba yasa tarufe alkur'anin tayi addu'oin ta tamik'e ta ajiye alkur'ani ama'ajiyarsa.
Hijjabinta tacire tana fad'in aunty Safna kofa sallar magriba bakiyiba har anyi isha'i amma kina kwance kina charting akan abinda k'ilama bazai amfaneki da komaiba.
ALLAHU Akbar maikaratu nagaba, Safna tafa idonta akan waya, tacigaba da fad'in malama Rahma jawo wata ayar na haddace wannan.
Ajiyar zuciya Rahma ta sauke, ta ce, "Niba malamarki bace, kuma ba wa'azi nake mikiba, ina tunatar dakene dannaga kin shagala.
Wani wawan dundu safna tasaukema Rahma abaya, Dan ubanki idan aljanna takice ki hanani, shegiya 'Yar iska uwar tsari, kenikam daba agabana ummi ta haifekiba wlhy danace anmata canji a asibiti, anya kuwa acikin 'yan barka wata bata sace ainahin d'iyar da ummi ta haifaba ta ajiye mata ke?.
Rahma tashare hawayenta ta ce, " kije kitanbayeta k'iladai kece aka canja mata, Dan halinki daban dana mutanen gidanna.
Afusace Safna taduro daga gado tana d'urama Rahma zagi.
Tuni Rahma tafice tabar mata d'akin.
Afalo taci karo da abbansu yadawo masallaci, sannu da dawowa Abba. Yauwa d'iyar albarka ina zuwa haka?.
Ba inda zani Abba, nadai fito falone nasha iska.
Masha ALLAHU, ina 'Yar uwar taki to?.
Tana d'aki Abba.
Yauwa jeki kiramin ita zamuyi magana, ina umminku?.
Ganinan Abba Shaheed ummi dake fitowa daga d'aki tafad'a.
Tamai sannu dazuwa sannan tafara shirya musu abinci.
Rahma tatsaya abakin k'ofa ta ce, "aunty Safna kizo Abba yana kiranki.
Shegiya munafuka gulmata kina kaimasane?.
Niba munafuka bace, yace dai kizo..., tana gama fad'a tafice.
Safna tasakko daga gadon tana mita, zan koya miki hankaline 'Yar banza maikan dankali.
(Araina nace kekuma maikan doya ko?.)
Kusada Abba taje tazauna, Abba gani.
Kanta yashafa yana murmushi haba safnan Abba miya faru kika k'unshe kanki a d'aki?.
Zamanta ta gyara tana ballama Rahma harara, babu komai Abba nayi sallane INA zaune ina Azkar.
Da k'yau 'Yar albarka.
Rahma kam ido tazaro waje danjin k'aryar da safna ta gilla, saikuma ta k'unshe baki tana dariya.
Safna na kallonta, Dan haka haushi yak'ara kamata.
_(Hattara iyaye kuringa kula da addinin 'ya'yanku, akwai yara dayawa masu wasa da salla irinsu Safna, wata zakiga tana zaune tana chart za'a kira salla, amma ko'a kwalar rigarta, har Matan aurema akwai masu halinnan, musamman yanzu da karatun Novels sukayi tasiri arayuwarmu, yakamata duk lokacin da aka Shiga sallah kiringa lek'a d'akin yaranki kitabbatar suma suyi, ALLAH yasa Mugane)._
Ummi ta ce, "kutaso ga abinci, atare suka tashi har zuwa dani, anacin abinci Safna na chart saida ummi Tamata magana sannan ta ajiyewayar tana zum6ura baki.
Bayan sun kammala Rahma takwashe kayan, takaima masu aiki su wanke.
Falon tadawo Inda iyayenta suke zaune harda safna.
K'asa ta zauna kusada Abbansu.
Zamansu babu dad'ewa ya Shaheed da ya Muneer sukayi sallam.
Cikin girmamawa suka gaida iyayensu, suma suka tambayesu ya iyalinsu?.
Kowa ya amsa da lfy k'alau.
Suma su Safna suka gaishesu.
Bayan gama gaishe2 Abba ya ce, "dama bawani abune yasa na tarakuba zancen auren safna ne yatashi.
Wata irin d'agowa Safna tayi arazane, aurena kuma Abba tafad'a da k'arfi!!!.
Suduka kallonta sukeyi, Abba ya ce, " eh aurenki safna ta, kiyi hak'uri abin yazo miki wani iri kuma 1time, wlhy nima haka lamarin yazomin babu shiri.
Kuka safna tafasa tana fad'in itafa wlhy akwai Wanda takeso Dan haka bazata yardaba.
Ya Shaheed ya daka mata tsawa, wlhy idan bakimana shiruba jikinki zaiyi tsami, iskancim banza kawai, Abban kike fad'ama haka?.
Toni Dan ALLAH baza'a bari aji uzurinaba haka kawai amin auren dole, narantse bana sonsa karma afara wlhy.
Idan bahakaba kuma wlhy zanbar gidannan.
Duka ya Muneer yakai mata tatashi dagudu tashige d'aku tana kuka da fad'in wlhy itafa bata sonshi.
Ajiyar zuciya Abba ya sauke ya ce, "akwai matsala kenan?......
Babu wata matsala Abba Shaheed ashema ita ta haifemu bamu muka haifetaba, wlhy acigaba da hidima kawai, idan ankaita ta mutu aranar, ni wlhy dama halin Safna ya isheni agidannan.
Shikenan ummin Muneer yanzu dai munyi dasu ranar juma'a zasu kawo komai, nasanar da Alhaji Rabi'u, (yayan ummi), sannan kuma suma su yaya na sanar dasu shida Abubakar.
Tom ubangiji ALLAH ya tabbatar da alkairi yasa ayi damu.
Amin Abba yafad'a, ya kalli su Muneer ya ce, " to manyan yayye yakukace?.
Dariya sukayi, yayi daidai Abba ALLAH ya Sanya alkairi, insha ALLAHU zamu fara shirya biki.
Tattauna maganar bikin suka cigaba dayi har zuwa wani lokaci, daganan su ya Shaheed suka tafi gidajensu.
+.+.+.+.+.+.+.+.+.+.+.
A 6angaren bobo kam abubuwa biyune suka cinkushe masa tunani, ga tunanin yarinyar da akaima fad'e, gakuma tunanin zancen Appa na yau, yasan appa sarai mutumne mai sauk'i da sanyi, komai zaiyi zaiyishine cikin hikima da lallashi, to amma mutumne kaifi d'aya idan ya ve e babu maisakashi fad'in A'a, Dan duk abinda zaiyi baya yinsa da ka saiyayi bincike.
Yasan ko giyar wake yasha bai isa ya gujema Auren nan ba, to amma shikam harga ALLAH baiji zaiso wata mace bayan Ni'ima ba, duk macen datayi kuskuren shigowa rayuwarsa bazata samu wani farincikin saba, ya rintse idonsa, ahankali yak'asa gaban wani k'aton hotonsa shida Ni'ima, sunyi k'yau sosai ahoto, suna tsayene gaban wasu filawoyi sun fukanci juna, yad'an rissina yadafa cikinta sannan tanada cikin Nawal, itakuma tana kallonsa shida cikin tana murmushi.
Hoton sunyi bala'in k'yau, wasu hawaye suka zuraro akumatunsa, baidamu daya gogeba sai shafa hoton daya cigaba dayi, yad'au tsawon lokaci yana kallon hoton daga baya yafad'a kan gado yana hawaye kamar wani mace.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Babu 6ata lokaci aka su Appa suka kai k'ud'i da komai ranar juma'a, antarbesu tarba ta mutunci da girmamawa, cikin girmama juna komai ya gudana aka tsaida biki sati uku kacal, saidai daga amarya har ango suna cikin tashin hankali, garama angon yadaure sosai yamaida komai ba komaiba, harma yanad'an saka baki idan 'yan uwansa suna maganar shagalin bikin.
Haka yasa ammi taji dad'i sosai itada Appa, sai albarka suke saka masa.
Nawal ma sai murana take ankusa kawo mata momynta.
Shirye shiryen biki ya kankama sosai Dan hidima akeyi babu kama hannun yaro, abubuwa sosai su ya Hamza suke shiryawa.
+.+
Yarinyar da akaima fad'e tana samum sauk'i saidai har yanzu bata iya magana, kullum sai Bobo yaje asibitin safe da yamma, har yanzudai ba'a samu iyayentaba ana kan nema, gashi bata magana bare asamu wasu bayanai daga gareta.
'Yan sandama suna aikinsu na binciko Wanda ya aikata laifin ta hanyar Number motarsa da matashin nan ya d'auka.
To ALLAH yasa adace amin.
A6angaren Safna kam abubuwa sun cakud'e danta tsaya kaida fata batason auren, anbuga anbuga tak'i, anyi lallashin abanza, hardai takai yau ya Shaheed ya zaneta amma abanza, Dan tace wlhy aka matsa mata zatabar gidan.
Hankalin Abba yatashi sosai, yarasa mafita, gashi har anfara shirye shiryen biki, Dan gobe za'a kawo lefe............
*_Luv u oll fan's d'in aunty bilyn Abdul._*
[11/12, 2:15 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1⃣5⃣&1⃣6⃣
Tana kwance agadonsu tana sharar kuka Rahma tashigo, da sauri tak'arasa gaban gadon tana fad'in haba aunty Safna yakamata kibar kukannan haka, ko sokike kizo kanki yana ciwone?.
Safna ta tashi zaune dolene nayi kuka Rahma kinajindai yanda ya Shaheed yace aure babu fashi, wlhy nikuma bana sonsa....
Rahma ta katsemata zancen da fad'in toni aunty Safna ganinake tunda bawani kike soyayya dashiba kawai kiyima su Abba biyayya mana. Tunda kinsan bazasu cutar dakeba.
Safna takamo hannun Rahma tarik'e gam kamar tana gudun kar'a kwace mata ita, ta ce, "Rahma bazan 6oye mikiba, zan gaya miki dalilin bijirema su Abba.
Wlhy sati hud'u dasuka wuce zuciyata tayi tuntu6en kamuwa dason wani bawan ALLAH, a makarantarmu muka had'u kuma wlhy ina bala'in sonsa, kullum sainayi mafarkinsa.
Lokaci k'an k'ani guy d'in ya sace zuciyata, nikam nad'auki aniyar nemoshi duk inda yake, inaji ajikina shine uban 'ya'yana, yanzu haka nabada kwangilar nemosa, shiyyasa duk abindasu Abba zasuyi saidai suyi bazan yarda amin Auren doleba.
To amma aunty kina ganin kinyi dai dai kenan?.
Da Sauri tad'aga mata hannu kinga baneman shawara nakeba, nabaki labarin sirrin zuciyatane kawai, Dan haka sauraramin, ragamar rayuwata ahannuna take Dan haka bazan yarda azalunceniba inaji INA gani.
Ainaga kema kin isa auren, miyasa Abba bazai aura masa keba saini?, idan kinajin banyi daidaiba toke kice su aura masa ke, nikuma abarni da Wanda nakeso, danhaka tashimin anan banason shishshigi da k'wala kai afaranti.
Haka Rahma ta hak'ura dukda k'ok'arin datakeyi na fahimtar da yayar tata muhimmancin biyayya ga iyaye, da illar bijire musu, amma firr Safana taki'i saurarenta, daga k'arshema abin fad'a yaso yazamar musu.
Rahma tabata hak'uri ta tashi tafita.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Bikifa ya kankama, bak'i harsun fara sauka, ayau kuma za'a kai lefe Dan haka matansu ya Is'haq duk suna gidan.
Akwatuna har goma sha biyu nagani baje afalo, dangi anata d'agawa ana jinjina kai dayaba k'yan kayana, Appa da babban yayane sukayi lefe, ya sulaiman yad'auki nauyin duk wani abincin daza'aci, ya Hamza kam suna 6angaren cashiya, shine yahad'a faty za'ayi dina da daddare bayan an d'aura aure ankawo amarya.
Ammi ta had'a mother night ana gobe d'aurin aure.
Suma su khairiyya da matan su ya hamza ba'a barsu abayaba sun had'a Sisters day washe garin d'aurin aure da safe kafin ayi walima.
(Nace hummm kaga bikin d'an gata).
Ango kam babu abinda zaiyi saidai gyaran gidansa, Dan za'a canja MASA fenti da abundan ba'a rasaba tunda andad'e babu kowa agidan, "tun bayan rasuwar Ni'ima daya Shiga rud'ani kamar yayai hauka yasa Appa ya tattaroshi yamaido gida kusadasu.
Kayan lefe kam sunyi masha ALLAHU saidai mak'iyi aunty Rashida matar ya is'haq tafad'a tana fesama kanta turare.
Dariya suka shek'e da ita suduka, aunty Sameera matar ya Hamza ta ce, "k'yaface haka aunty Rasheeda tunda kina ragema amarya turare.......
To aii gara kafesa, k'ila idan amaryar tazo wannan mijin nata maikama da soja ya hanaka fesawa.
Dariya suka kuma shek'ewa da ita harda tafawa kamar wasu k'awaye.
Adai dai wannan lokacin kuma Bobo yashigo falon shida ya Hamza.
Ahankali suka fara tsagaita dariyar tasu, ya Hamza ya ce, " kukuma lfy?, miya sakaku dariya haka?.
Aunty Sameera ta maimaita musu abinda yafaru, dariya ya hamza yayi, bobo kam saiyayi murmushi yana kallon aunty rasheda dake dariya, ta ce, "ka kafeni da ido konayi k'aryane?.
Kauda Kansa yayi yana murmushi, ya ce, " aunty Rasheeda kenan, kisanifa saikin biyama matana turarenta babu d'aga k'afa.
Nanmadai dariya akayi, Aunty ummy ta ce, "lah bobo dama kanason auren nan amma idan anyi magana kaita wani basarwa?.
Okey da kin d'auka banasone aunty ummy?, tsaya kiga ikon ALLAH bayan d'aurin aure zakisha mamaki Romeo zan zama.
Dariya sosai sukeyi harda ya hamza da Ammi dake sakkowa daga saman Appa.
Shikam bobo d'akinsa yashige yana murmushi.
Bayan sunyi dariya mai isarsu suka koma tsokanar bobo ya Hamza yana kare masa, danshi tunda yashige d'aki yak'i fitowa.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Alhmdllh yau lefe ya iso gidansu Safna, anyima 'yan kawo lefe tarba ta girmamawa, kowa ya kalli lefen saiya jinjina kai, Dan kayane masu k'yau da birgewa.
Sund'an dad'e agidan sannan suka tafi cikeda tukuyci na girma.
Cikeda zumud'i Rahma tashiga d'akinsu, Safna tana zaune tana chart da baseera daketa k'ara zugata wai karta yarda da wannan auren, *boy ya ce, " yana gab da samo mata bobonta.
Murmushin jin dad'i taketa zabgawa, k'arar rufe k'ofa da Rahma tayi yasa Safna d'agowa, Rahma tak'araso gurinta tana washe baki, aunty Safna kinga kayan lefenki kuwa jar ubancan kai, wlhy kamar basusan ciwon kud'iba.
Baki safna ta ta6e sannan tagallama Rahma harara yarinyarnan na kula kemafa kanki da motsi, banace kidaina jingina aurennan danibane Dan uwarki, kakin yakamata kitaya farinciki Dan lefennan nakine baniba kam, saikuma tayi wata 'Yar dariya Rahma lefena yana nan zuwa daga Bobona, k'ilama sannan kinada ciki hhhhhjhhhh ta shek'e da dariya harda rik'e ciki.
"Na ce, " hummmmm".
Rahma kam girgiza kai kawai tayi, tana mamakin halin kafiya da dagiya irinna Safna, tanayin Abu kamar batada ilimin addini, ALLAH ya k'yauta tafad'a afili tana ficewa ad'akin.
Amin safna tafad'a ita tana Raka Rahma da harara.
Ran Abba a 6ace yake, sai safa da marwa yake afalonsa, gobe d'aurin aure amma Safna ta tsaya kaida fata bata son aurennan, yau Uncle Abubakar sau biyu yana dukanta shida ya Shaheed amma tace Sam batasan zancenba, daga k'arshema kayanta tahad'a waizata bar musu gidan.
Ya Shaheed ne yashigo falon Abba da sallamasa, Abba ya amsa yana mai tsurama Shaheed d'in ido kamar yau yafara ganinsa, ya Shaheed ya rissina ya gaida Abba sannan ya zauna ak'asa kan kafet.
Shima Abba saiya nemi waje ya zauna.
Ya Shaheed ya sauke numfashi Kansa ak'asa ya ce, "Abba dama wata shawarace nazo da ita.
Ina jinka Shaheed Abba yafad'a da hanzari.
" Hummm Abba inaga tunda Safna tak'i har yanzu, dataje tamana abin kunya inaganin kawai mubarta, inhar zasu yarda kawai abashi Rahma.
Abba yazaro ido waje, Shaheed baka ganin Rahma batayi k'ank'antaba!?.
Abba batayi k'ank'antaba, tafa gama secondary, kuma yanda nasan Rahma da hakuri da biyayya bazata bijirema umarninkaba kamar yanda safna tayi, nasan zata yarda ta auri Abdulmalik indai Rahma ce......
Dai dainan Rahma tashigo falon, tiren dake hannunta ya su6ce, abinda ke ciki yazube jikinta sai rawa yake saboda jin furucin ya Shaheed na k'arshe.
Ya Shaheed ne yamik'e da sauri yakamota ya zaunar, cikin taushin murya ya ce, kiyi hak'uri Rahma kibi umarnin Abba kifiddashi daga kunyar mutanen daya tara, kikalli gidannan cike yake da danginmu, wasuma daga wani gari suka taso, kituna d'unbin mutanene da Abba ya gayyata wad'anda zasu halarci taron d'aurin aure gobe idan ALLAH ya kaimu.
Rahma kema kinason Abbanmu yaji kunya?, kamar yanda Safna tayi, jibi kiga yanda hankalin Abba yake atashe akan abinda baifi k'arfiba daga garemu.
Rahma tad'ago kai takalli mahaifinsu dashima su yake kallo, gabad'aya fuskarsa ta canja, Abbansu muntum mai sauk'in kai da hak'uri amma yau 6acin rai ya maidashi wani iri, ita saitagama kamar yarame.....
Ya Shaheed yad'an ta6ata, da sauri takalleshi, ya ce, "baki aminceba kema ko?.
Yanda ya Shaheed yay maganar saiya bata tausayi shima, ahankali ta jinjina kai, cikin kuka ta ce, " nayarda yaya wlhy na amince zan fidda Abba kunya... Shashshekar kuka tahanata k'arasawa."
Cikin farin cikin ya Shaheed ya rungumeta, Abba kuma yarungumesu gaba d'aya.
Sai albarka suke saka mata da addu'ar fatan alkairi, itakam tana kuka tana sharar hawaye.
Abba yakira Appa ya sanar masa komai bai 6oye masaba.
Appa ya ce, "babu wani damuwa da Safna da Rahma duk d'ayane tunda daga tsatso d'aya suka fito, shima yayta sakama Rahma albarka.
Abba yaji dad'i sosai, sukayi sallama.
Ummi ma Abba yakirata tazo d'akin, jin abinda yafaru yasa ta rungume 'yartata cikeda farinciki dakuma saka mata albarka, saidai gefen zuciyarta tana tausayin Rahma, aganinta nawa Rahmar take, amma babu yanda zasuyi, sun tara d'unbin mutane wannan ne kawai mafita agaresu Baki d'aya.
Fatanta ALLAH yasa mijin nata yakasance mai kula da tausaya mata, Dan Rahma tanada rauni sosai, dukcikin 'yayansu babu Wanda yakai Rahma hak'uri, daga ita sai ya Muneer, sune suka d'ebo halin mahaifinsu Sak, na Rahma ma yafi nasa, Dan Rahma akwai hak'uri, kuma yaran gidan duk sunfita k'yau sosai.
Rahma ba fara bace amma tanada d'an haskenta daidai gwargwado, zamu iya kiran rahma tsaka tsaki batada tsawo bakuma gajera bace, tanada d'an jiki Dan 'Yar lukutar ummi ma da akece mata, idan akafad'a tayita kuka bataso, tanada k'yanta daidai gwargwado (saidai Safna tafita k'yau nesa ba kusaba), Abu mafi d'aukar hankali ajikin Rahma shine idanunta, wasu irin idanu Rahma take dasu masu hasken tsiya da girma kamar suffar kwai, duk yanda ran Rahma ya6aci basa canja kala saidai su k'ank'ance.
ALLAH yabama Rahma baiwar juya idanu, gasu masha ALLAHU da girma, sau dayawa idanun Rahma kan fisgi hankalin mutane kanta Dan danan tashiga ransu Dan ita mutumce mai saurin Shiga rai, indai zaka zauna da ita saita shiga ranka.
Wannan kenan.🤸🏻♀👌🏼
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Labaridai ya isa kunnene Bobo "wai Amarya bata sonsa", amma abin bai bashi haushiba sosai, tunda dama shima ba auren yakesoba, Dan haka da yarinyar tasoshi da karta soshi duk uwar ubansu d'aya ko akwalar rigarsa, shi dama wadda za'a bashi yanzu d'in ta ce, " itama bataso, da wlhy har k'yauta zai mata.
Na ce, "hummmm.........
❤❤❤❤❤❤❤ *_masoya kumuje zuwa yanzufa aka fara gashi suya sai ran sallah_*😂👌🏼
[11/12, 2:16 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
1⃣7⃣&1⃣8⃣
Kafin la'asar zazza6i yarufe Rahma, tana d'akin Abba kwance ak'udundune, ya Muneer yashogo da Dr kaleed har cikin falon Abba.
Abba da kansa yashiga d'akinsa yatasoda Rahma daketa rawar sanyi, saman kujera ya zaunar da'ita Doctor yashiga aikinsa, babu wata matsala Alhaji 'Yar damuwace kawai Dr Kaleed yafad'a.
Abba ya ce, "to Dr babu wani taimako da za'ad'an bata kenan?.
A'a zan mata allura da magani tad'an samu barci, insha ALLAHU daga nan zuwa yamma zata koma Normal, yanzudai idan namata allurar tad'an samu koda tee ne tasha saitasha magani tayi wanka da ruwa maid'an sanyi ta kwanta, insha ALLAHU normal zata tashi nanda anjima.
To madallah Dr mungode sosai.
Babu damuwa Alhaji aii aikinane.
Babu 6ata lokaci Dr yayma Rahma duk abinda yadace, ummi tabata shayi tad'ansha kad'an tabata magani Wanda tashashi da k'yar Dan Rahma akwai tsoron allura da magani, bataso ko kad'an allurarma saida lallashi akayi.
Bayan tasha maganin ummi ta taimaka mata tayi wanna a bayin Abba, kaya aka d'akko mata tasaka takuma kwanciyarta a gadon Abba sai barci.
Hummmm wai ina Safna?.
Tana nan acikingidan kuma labari yakai mata, ancanjeta da Rahma, Dan haka tadage tarink'a tsallen murna ita taci nasara, shikenan zata mallaki bobonta nanda lokaci kad'an, har ruwa tazuba k'asa tasha Dan dad'i.
Cikeda farinciki takira Baseera ta guntsa mata, murna sosai ta tayata harda jinjina da yaba k'ok'arinta na dagiya.
Bayan sungama da baseera takira zeenat itama, zeenat ta ce, " wlhy Safana kin tafka babban kuskure a rayuwarki, na tabata nangaba saikinyi Dana sani Mara iyaka, son zuciya yasa kin bijirema iyayenki akan Wanda baima San da zamankiba, ke kanki bakisan Inda yakeba yanzu, bakida tabbacin zai kar6eki kobazai kar6i soyayyarkiba, wlhy kidaina biyema hud'ubar baseera zatayita kaiki tana baroki a tashar wahala ne......
Safna ta k'atseta atsawace, kee!!! Dallah malama yimin shiru, nakiraki nafad'a mikine danki tayani murna ba surutun banzaba, aiikin banza kawai mtsowww taja tsaki tana yanke wayar.
"Daga can Zeenat ta girgiza kai tana fad'in ALLAH ya shiryeki Safna, amma zakiyi nadama wlhy na tabbatar."
Babu Wanda yakumabi takan Safna shagalin biki akacigaba da gudanarwa, itama tafita harkar kowa agidan lamuran gabanta kawai takeyi harda yima Rahma dariyar mugunta.
Na ce, "hummmm.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*
Bobo ya lalubo wayarsa dake wringing daga aljihun jins d'insa, ido yad'an zaro tareda kallon Ya Sulaiman dake duba yarinyar da akaima fad'e.
Lfy kuwa bobo?.
Tab ya Is'haq ne kasanfa sunacan suna jiranmu..... K'ara kiran da akayine yasa Yakuma kallon wayar, ya is'haq d'innedai, d'agawa yayi tareda yin sallama.
Abdulmalik wai kuna inane kaida sulaiman?, ya Is'haq yafad'a daga can.
Wlhy muna asibiti wajen yarinyarnan amma gamunan zuwa Ku k'ara hak'uri.
Tom yakamatafa kuyi sauri Dan akwai abubuwa agabanmu masu yawa.
Gamunan yanzunan insha ALLAHU.
yanke wayar yayi tareda dawo da kallonsa kan ya sulaiman, ya Sulaiman yakamatafa muje kasandai masifar babban yaya, muk'arasa kafin ya k'ulu.
Gsky ne muje kawai aii nagama harma takoma bacci.
Bobo yad'an lek'a fuskarta, ya ce, " baiwar ALLAH, wlhy rashin maganar yarinyarnan yana damuna, yakamatafa ace iyayenta sunsan halin datake ciki.
Hakane gsky to amma yazamuyi? tunda bamusan idan takeba, saidai mucigaba da addu'a. Idan kuma tak'ara samun lfy mubi shawarar Ammi mumaidata wajenta kawai.
To shikenan bobo yafad'a yana fitowa.
Waje yanufa shikuma ya sulaiman yashiga office Dan ajiye kayan hannunsa.
Babu dad'ewa yafito, mota yashiga Inda bobo ke zaune a mazaunin direba, bobo yatada motar suka fice daga asibitin.
.+.
Gidansu Safna kuwa anyi shirin kamu Wanda aka had'a a babban harabar gidan nasu, saidai matsalar amarya babu lfya tana d'akin Abba kwance tana barci.
Hafsat matar ya Shaheed ta kalli ummi, ummi to yanzu yaza'ayine harfa dangin angon sun iso ga babu amarya, dama Safna zata mana alfarmar yanzu kawai saita zauna amadadin Rahma d'in.
A'a barta kawai hafsat, nibanamaso muna saka Safna acinkin sha'anin bikinnan, takalli agogon dake hannunta, hafsat inaga bari kawai atada Rahma d'in dukda dai bata dad'e da kwanciyaba.
A'a ummi abarta kawai likitafa ya ce, tana buk'atar Hutu, gashi dangin ango since k'arfe tara akwai mother Night, yakamata tasamu ishashshen barci kafin sannan, yanzu bari nayima Basman aunty Yahanasu magana saita shirya tazauna amadadin amarya tunda kusan kansu d'aya.
Yauwa hakama yafi, dama gasu suna kama ba laifi.
Haka suka saka Basma aunty yahanasu k'anwar ummi tashirya tsaf tamkar amaryar, idanma baka saniba saika d'auka Rahma d'ince Dan suna matuk'ar kama, idanuwa kawai Rahma zatafi Basma.
Dahaka aka gudanar da kamu Wanda yak'ayatar da dangin ango, su khairiyya da khursiyya dasu aunty Rasheeda sai zuba lik'i suke wa amarya, Dan basusan ba amaryarsu bace.
Dahakadai taro yatashi gab da magriba Alhmdllh.
Duk shagalinnan da akeyi Safna tana d'aki kwance abinta, da barcima takeyi kid'an da'aka sakane yasa tatashi tana mita da tsaki anhanata barci wai, wayarta ta d'auka takira *boy danneman k'arin bayani akan aikin data bashi.
Ya ce, "mata yana nan yana k'ok'ari.
Tana yanke wayar takira Baseera sukaita labarinsu Rabi duk akan bobone.
Na CE hummmm.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Su bobo suna isa gidan suka Tatar da ya Is'haq da ya Hamza zaune aharabar gidan, harda wasu samari wajensu bakwai, cikin samarin danginsune, ya Hamza yana cikinsu sunashan shafta.
Ya Is'haq kam yana gefe zaune saman mota Dan bakomai yake Shiga cikinsuba kasancewarsa babba.
Bayan bobo yayi fakin suka fito, wajensu ya Hamza suka k'arasa, hannu sukaita bama matasan samarin ana musabaha🤝.
Bayan sun gama gaisawa Bobo yanufi Inda Ya Is'haq yake.
Hannu yabashi shima suka gaisa.
Ya ce, "kunje kun wani mak'ale a asibiti tamkar kun manta da abinda me gabanku.
Sorry babban yaya, bobo yafad'a yana had'e hannayensa waje d'aya alamar tuba🙏🏻.
Dirowa ya Is'haq yayi, to yazanyi idan ban hak'uraba ma.
Motocine suka fara shigowa gidan, bobo yabisu da kallon yana fad'in wannan gayarfa daga ina?....
Daidainan ya Hamza da ya sulaiman suka k'araso garesu.
Ya Hamza ya ce, " daga gidan amaryarka suke, sun halarci kamune.
Baki bobo yad'an ta6e ya Hamza miye kuma kamu?.
Kafin ya Hamza yabashi amsa aunty Rasheeda da aunty ummy suka k'araso, aunty sameera dasu khursiyya suna biye dasu.
Bud'a aunty Sameera tarangad'a akunnen bobo, yay saurin toshe kunnansa, saida tagama sannan ya kalleta fuska a shagwa6e, kai aunty Sameera dodon kunne zaki kashemin?.
Dariya suka shek'e dashi suduka, yayinda aunty Rasheeda tafara fesama bobo turare mai shegen k'amshi, kaima ankamaka kamar yanda mukaje kama amaryarka.
Dariya su ya Sulaiman suka saka danganin yanda bobo ya kwa6e fuska tamkar zaiyi kuka, ALLAH matannan nakula kun rainani yafad'a yana hararsu.
Dariya sukayi gaba d'aya harda wasu daga cikin dangi dasuka zagaye wajen.
Aunty ummy ta ce, "tab wlhy Bobo matarka ta had'u jar ubancan kai, kaiga wasu idanu masha ALLAHU, (" nace hum danma bakiga na asalin amaryarba kenan), tacigaba da fad'in aifa inaga aka kawo amaryarnan bazaka ringa fitaba, aikinma hak'ura zakayi dashi.
Dariya sosai ake shek'awa, dukda haushi da yacikama bobo ciki wannan bai hanashi murmusawaba, ya ce, ''yan sa ido, kunje kunata k'arema yarinya kallo, halan har muninta kun gano?.
Wata Zainab acikin danginsu ta ce, "wlhy ya Abdulmalik babu mai iya gano munin Rahma amarya, masha ALLAHU kam komai yaji zam zam..... Tak'are maganar da rufe baki.
Nanma dariya akayi, shikam ya ce, kwadaiji dashi sa'idinniya kawai masu barci da ido d'aya, yana gama fad'a yafito daga wajen.
Wasu daga cikin 'yammatan jisuke inama sune da wannan guy d'in, lallai yaci sunansa Bobo.
Wasukam kishine yacika zuciyarsu, Dan sundad'e suna nuna masa so yana basarwa saboda jin kai, wasukam har iyayensu saida sukai masa talla amma ya ce, "kai kasuwa.
Cikin gidan yashiga Dan soyake ya d'auro alwala, babban falon k'asa cike yake dam da mutane, yanashiga suka hau tsokanarsa wai angon k'amshi angon k'amshi."
" aransa ya ce, "za'a gogudai".
Haka yagaida wad'anda zasu iya jinsa ya haye sama d'akinsa bayi yashiga yad'auro alwala yafito, su aunty Sameera ma duk sunshigo ciki.
Yazo zai fita Ammi ta ce, " mukarram!.
"na'am Ammi ya amasa yana juyowa, k'arasowa tayi Inda yake takama hannunsa suka fito.
Wani d'an lungu tajashi ya ce, " Ammi lfy dai ko?.
Lfy lau mukarram dama tambayarka zanyi d'azu kuwa kaje gidansu amaryar taka?.
Gefen wuyansa ya sosa, afuwa ammi, wlhy abubuwane sun mana yawa.
Kanta ta girgiza haba mukarram ya inamaka kallon mai hankali amma kanason 6ata wayonka?, babu dad'ifa, iyayen yarinyarnan bazasuji dad'iba ace bakaje gidanba tunda aka fara maganar aurennan, shin kai zakaso ayima su khursiyya hakane?.
A'a wlhy ammi bana fata, amma Dan ALLAH kiyi hak'uri nayi kuskure, insha ALLAHU zan bata hak'uri anjima idan munje mother night.
To shikenan ammadai Baka k'yautaminba, Bahaka nasoba.
Tom kiyi hak'uri Dan ALLAH.
"Ya wuce."
Yauwa ammi an kar6o d'inkin Nawal kuwa?, wlhy namanta shaf, kuma harda wanda zata saka anjima.
Eh khairiyya ta amso d'azu kafin sutafi wajen kamu.
Yauwa harnaji dad'i, bari naje sallah ammi har an tayar inagama su yaya sun wuce.
To saikun dawo.
Masallaci yanufa ammi kuma takoma ciki.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Anayin Sallar magriba Safna ta sid'ad'e tabar gidan, sai gidansu kamal, acewarta bazataje wajen wani mother Night ba, saikuma tana zuwa gidan ta tarar dasu Ameera suna shirin zuwa harda momynsu.
Dayake momynsu kamal tasan komai Dan baba abubakar yasanar da ita, (k'anin Abba ne, kuma mahaifi gasu Br kamal abokin aikin bobo) batace mata komaiba itama, safna tashige d'akin Ameera tayi kwanciyarta, sukuma suka nufo gidansu Safna d'in, akabarta itakad'ai agidan sai 'yan aiki.
Rahma ta farka bayan sallar magriba, kasancewar tana fashin Sallah saikawai aunty Madeena matar ya muneer tasata tayi wanka.
Mai kwalliya tafara aikinta na fente fuskar Rahma.
Itadai Rahma bin kowa kawai takeyi da ido, kad'an kad'an saita share hawaye, saida mai kwalliya tamata magana sannan ta tsagaita da kukan aka tsantsara mata kwalliya ta d'aukar hankali.
Wani doguwar riga bubu aka bata tasaka, tawani material Orange da d'igo d'igon lemon green ajiki, aka nad'a mata lemon green d'in d'ankwali, sai fashion na 'yankunne da sark'a maid'an tsawo, tasaka bak'ar coka wadda ta manne awuyanta.
Yasalam nafad'a yayinda naga amaryar k'amshi tafito ras kamar ba Rahman ummiba, tayi k'yau masha ALLAHU.
Fos aunty hafsat tabata, wadda itama takasance lemon green, sannan tasaka takalmi lemon green shima mara tudu.
Hummm komaifa yaji ajikin amarya.
Ihsan k'anwar Br kamal tamatso kusada ita, kai Rahmana kinyi k'yau wlhy, na tabbata angonnan yaganki saiyace gwamma da akayi, wlhy saikin susutashi.
Basma ta ce, "ni tsorima nake karya rikice yace daganan sai gidansa.
Duka Rahma takai musu, cikin dasashshiyar muryarta datasha kuka ta ce, " yan iska kawai, aii dama halinku d'aya.
Dariya suka shek'e da ita harda tafawa.
*_Bobo_*..........
*_godiya muke masoya, ALLAH yabar zuminci._*
[11/12, 2:16 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
*_"wannan page d'in nakine Maman useey alkairin ALLAH yakaimki har gidan baban useey, ni marak'issiya naji sak'onki wajen aunty bilyna."_*
Luv u🤸🏻♀👌🏼
1⃣9⃣&2⃣0⃣
A 6angaren bobo kam bayan sun dawo daga masallaci aharabar gidan suka sake zama, hira aketayi da barkwanci, saida aka k'ara kiran sallar isha'i sannan suka mik'e, masu sake alwala suka sake, wadda tasu bata karyeba sukayi gaba.
Ana idar da sallah suka shigo gidan, shiri suka fara, kowa yana k'ok'ari kada time ya k'ure.
Bobo kam wanka shima yashiga, yafito d'aure da tawul fari a k'ugunsa, k'arami kuma yana goge kansa zuwa fuska da wuya har k'irjinsa zuwa k'asa.
Wurga tawul d'in yayi saman kujera, yaja kujerar madubi ya zauna, mai yafara shafawa, hardasu farar fauda afuska, yashafe kansa da mai mai k'amshi har zuwa sajensa dad'an gemunsa na gayu, yasa kum yak'ara taje kansa da gemunsa, sannan yay amfani da burosh wajen kwantar da sajensa, yako kwanta luf sai walk'iya yake da tashin k'amshi.
Turarurruka yad'auka kala kala yafeshe jikinsa, sannan yanemi guri abikin gado ya zauna batareda niyyar saka kayaba.
Atsakar gida kam mutane harsun fara fita, Dan kowa bayaso atafi abarsa, dandanan motoci suka fara d'aukar mutane, kowa ya cakire da kalar kayan dayakeso, manyan iyayene kawai suka saka wani Dan datsetsen less fari tas, suka nad'a Orange d'in gwagwgwaro, masha ALLAHU abin sai Wanda yagani.
Su khairiyyama ba'a barsu abayaba, sunci ado da dogayen riguna na lemon green d'in material sunyi k'yau masha ALLAHU, suda matansu ya sulaiman duk iri d'aya suka saka.
Nawal ma anshiryata cikin farin less irinnasu Ammi, doguwar riga aka mata, aka nad'amata Orange d'an kwali, yarinyar tafito d'as kamanninta da bobo ya k'ara fitowa.
Tare suka shiga Mota da Ammi.
Ya Hamza yafara waige waige, cikin Jan tsaki ya ce, "wai mi Bobo yakeyine tun d'azu yafasan saiyaje sun taho da amarya, gasu ammi harsun wuce.
Ya is'haq shima yay tsaki ALLAH yaron nan d'an wulak'ancine, Hamza kaje d'akinsa kaga miyakeyi?.
Ya Hamza yanufi d'akin Bobo, ya Sulaiman dai baice k'alaba.
La'ilah Abdulmalik minene haka?.
Bobo dake zaune yana latsa waya yad'ago yana kallon ya Hamza daya had'e cikin Farin Suit sai k'amshi yake.
Minayine yaya?.
Bansaniba, dallah malam kana 6atamana lokaci katashi kasaka kaya, su Ammi harsun wuce.
Baki yaturo kamar wani k'aramin yaro, nikam wlhy ya Hamza barcima nakeji.
A'a kakan barci kakeji ya Hamza yafad'a ahasale, wlhy zankira ya Is'haq.
Da Sauri bobo yamik'e, yafara saka gajeren wando da bes, ya warware had'ad'd'un Suit lemon green sai d'aukar ido sukeyi.
Wandon yafara sakawa da Orange d'in Riga mai dogon hannu, ya tsuke k'ugunsa da belt, ya Hamza yad'auki nektayit d'in green yafara saka masa, shi abumma dariya yabasa, amma baiyi dariyarba gudun kar ya Hamza yasake k'uluwa.
Da taimakon ya Hamza yasaka rigar Suit d'in, yafara saka botiran ya hamza na gyara ma kwala d'in. Takalmima saida ya taimaka MASA yasaka, sannan yak'ara feshe jikinsa da turare, yad'auki wayarsa d'aya yazura a aljihun Suit d'in, suna tafiya yana d'aura agogo.
Na ce o'o me bobon Ammi sai a slowly.
Saida ya Hamza yaga yashiga mota a baya, sannan shima yashiga mazaunin direba Nasiba d'iyar k'anwar Ammi na gefensa.
Suma su ya is'haq suka tada mota, suna gaba su bobo na bayansu har anguwar su Rahma.
Ak'ofar gida suka faka, ya Hamza yafita shida Nasiba har cikin gidan suka Shiga sukace afito da amrya ango yazo.
Gaban Rahmane yafad'i Ra's, jitake tamkar tafasa ihu, kowacce irin tarba angon zai mata ta tanbayi zuciyarta?.
Batada mai bata amsa, tana cikin zancem zuci aunty Ruk'ayya ta ce, taso Rahma angonki yazo.
Jitake tamkar ta ce, bazataba amma yazatayi.
Haka aunty Rukayya takamo hannunta sukayo waje, dama dayawan mutanen sun tafi sai k'alilan suka rage.
Kowa yashiga mota amarya kawai akejira.
Ya Hamza yabud'e d'ayan gefen da Bobo yake zaune Dan ganin amarya tafito. Azuciyarsa ya ce, ''masha ALLAHU, gsky amaryar auta ta had'u.......
Isowarsu ta k'atse masa tunani, yayinda gaban Rahma keta fad'uwa azatonta Ya Hamzane angon, kanta na k'asa aunty Ruk'ayya tasakata amotar.
Wani k'amshine da sanyi suka bigi hancinta, tashak'a talumshe ido azuciyarta ta ce, ''oh ALLAH, wannan wane irin k'amshine?.
K'ok'arin gyara zama tayi saitaji ta dunguri mutum, dasauri tajuyo ta kallesa, yana zaune ak'ame kamar wani jinin sarauta, saidaifa k'amshin amaryar tasa ta narkar da zuciyarsa, saiwani lumshe idanu yakeyi, ahankali yajingina bayansa da kujerar ya lumshe ido.
K'irjin Rahma sai dukan uku uku yake, jitayi wani sabon zazza6i yana neman rufeta, dukda kallon fisha tayima angon nata ta tabatar ya had'u masha ALLAHU.
YA Hamza dake tada mota ya ce, amaryarmu ykk?.
Muryar Rahma na rawa ta ce, "ina yini.
" lfy lau, ya fara hidima?."
Alhmdllh tayi maganar ahankali.
Tad'an kalli gefen Bobo ta ce, ina yini.
Dukda yagane dashi take amma yay shiru.
Takuma cewa ina yini, sai asannan ya amsa da lfy, ykk?.
Kasa amsashi tayi, sai kawai tayi k'asa da kanta tana wasa da zoben hannunta.
Sunkusa isa wajen faty d'in Bobo yatashi zaune sosai, wata leda yad'akko agefensa yazaro rafar 'yan 200 guda hud'u yad'ora saman cinyarsa.
Rahma data k'urama zonen hannunta ido saikawai taga mutum ya d'oro hannunsa saman cinyarta, gabanta ya ce, "wani Rasss!, fos d'inta yazare data d'ora saman cinyarta ta d'ora hannunta akai.
Tabud'e idonta ahankali daga rintsewar datayi, Fos d'in yabud'e yaga 'yan 50 rafa biyu sai wayarta, wayar yaciro yasaka kud'in daya ciro aleda yasa a fos d'in maida wayar yayi zai rufe fos d'in amma tak'i shiga dan tacika dayawa.
Ciro wayar yakumayi yarufe fos d'in yad'ora mata saman cinyarta, wayarta kuma yasaka cikin aljihun suit nasa, nufinsa idan sunje angama taron talik'a kud'in saiya bata.
Itadai Rahma batace masa k'alaba Dan batasan miyayi da fos d'inba.
Har gaf da d'akin taron ya Hamza ya faka, yafito yabud'e musu k'ofa, asanyaye Rahma tafito, duk kunya ta isheta tasaba duk inda zataje saida k'aton hijjab, amma yau gata kod'an gyale babu, sauk'intama Rigar bubuce kuma tabud'e bata matsetaba.
Su yaya Ishaq suma fitowa sukayi daga motarsu, suma kayansu iri d'aya dana ya Hamza.
Suma sun yaba da amaryar k'anin Nasu sai masha ALLAHU suke jerowa.
Ya Hamza yashiga d'akin taron yasanar da MC amarya da ango sun iso.
Aiko nanfa yafara kayayato, falon taron yay tsit anzuba ido aga amaryar Bobo d'an gayunnan maiji da kansa.
Ahankali Bobo yatako har zuwa gaban Rahma data duk'ar dakai k'asa kamar ace ar ta gudu.
Ahankali ya ce, "bismillah muje.
Jerawa sukai suna tafiya ahankali har cikin wajen, bayansu kuma su ya Sulaiman ne suka take musu baya.
Tunda suka shiga wajen taron jikin Rahma yay sanyi, Dan ita irin mutanan ne masu tsoron shiga mutane, dandanan tafiyarta ta sauya, sai wani sassarfa takeyi.
Raf raf raf raf!! d'akin taron yad'auki tafi lokacinda Rahma ta hard'e taigaba kamar zata fad'i, da sauri Bobo yaruk'o hannunta yana fad'in ezeee madam.
Ajiyar zuciya tasauke danjin bata fad'iba, a u okey?, yafad'a yana kallonta. Kai tad'aga da sauri.
Tom kiyi ahankali plzz karki ji ciwo.
Ngd tafad'a tana kallon k'asa, to muk'arasa ya nuna mata hanya.
Ahankali suka taka zuwa inda aka tanar musu, sunbirge mutane gsky saidai mak'iyi, kowa fad'i yake sun dace da juna, Ammi saijin dad'i takeyi Dan harga ALLAH Rahma tashiga ranta.
Suna zama DJ yasaki wak'ar because, i luv u. Wannan wak'ar Bobo ce dayake bala'in so sosai, ya Hamza yabada wak'ar asaka Dan Bobo.
Aikuwa sai sakin lallausan murmushi yakeyi danjin dad'in wak'ar.
Masu hotuna kam sai aikinsu suke, itadai Rahma kanta yana k'asa tana shak'ar daddad'an k'amshin turaren Bobo.
Bayan wak'ar tak'are aka fara gudanar da abinda ya tara mutane.
Ammi tayi bayani da godiya ga d'unbin mutane dasuka halarci mother's Night d'in, sannan taima amarya da ango fatan alkairi.
Rahma taji dad'in bayanin ammi itada danginta, wannan kad'ai ya isa yanuna mata dangin mijin nata suna sonta.
Ankira amarya da ango filin rawa, shuru sukayi kamar bazasu tashiba, kowa da abinda yake kitsawa a zuciyarsa, saida mc yasakeyin magana sannan suka mik'e ahankali.
Afilin rawar suka tsaya k'ik'am babu mai motsi balle rawa, itakam Rahma dama bata rawa da dadai safan ce kam wannan gwanace.
Bobo yafiddo rafar kud'i yafara lik'ama Rahma idonsa k'yam akanta, itakam kanta na k'asa, Dan danan guri yad'au ihu da tafi, jiki a sanyaye Rahma itama tabud'e fos d'inta danufin d'akko 'yan wazo d'inta saitaga kud'i dayawa.
d'agowa tayi ta kalli bobo, shikuma yad'aga mata gira kuwa, da sauri tamaida kanta k'asa, yamatso da bakinsa wajen kunnenta cikin muryarsa mai taushi da laushinnan ya ce, "ko bakisone?.
Ajiyar zuciya ta sauke itama ahankali ta ce, " ngd sosai".
Hak'k'ine akaina aii yafad'a idomsa agefe kamar bashi yayi maganarba.
Batace komaiba itama tazaro kud'in tafara lik'a masa gashi yamata tsawo, amma ahaka taringa masa lik'i ihun mutane da tafi yak'aru, masu hotuna da video sai haskasu sukeyi.
Ammi ta taso itama ta rungume Rahma tana saka mata albarka, tafara lik'ama Rahma 'yan dubu dubu, (abin na manyane masu karatu), Bobo ma yakoma lik'ama Ammi sai murmushi yake saki itama Ammi haka, Rahma kam kanta ak'asa itama tana lik'ama ammi.
Su yaya sulaiman ma suka taso, dandanan gurin ya kaure da lik'i kamar ba'asan ciwon kud'iba, k'awayen ammi da danginta duk suntaka rawar gani, hakama dangin Rahma ba'a barsu abayaba, kai wannan taro ya k'yatar masha ALLAHU.
*_(can na hango Aunty bilyn Abdul tana lik'a 'yan naira 5🤣😜🤐, ba ruwana kartajini)._*
_karfa kuce nina fad'a🤸🏻♀_
Sai k'arfe 11:30pm taro yatashi lfy, kowa yafara k'ok'arin tafiya, Rahma duk barci yacika mata ido, cikin mota take zaune tana jiransu bobo sugama sallamar bak'i shida yayunsa, saida kuwa suka gama sannan suka shigo, yanzu kam wani d'an uwansu bobone zai maidasu ba ya Hamza ba, su ya Hamza matansu suka d'auka da yaransu sukayi gida.
Rahma ta kifa kanta kan cinya harta fara barci, kallonta kawai yayi baice komaiba, shifa koma sunanta bai saniba, bai tada itaba har sukaje gidan.
Yay shiru yana tunanin yanda zai tasheta.
Lukman ya kallesa Bobo kona baku gurine?, a'a malam wane kabamu guri gida zata shiga, ita barcima takeyi.
To ka tada ita dare na k'arayi shabiyu saura fa.
Daurewa yayi yad'an ta6a bayanta, ko motsi batayiba, yakuma d'an bubbugawa, firgigit ta tashi da addu'a abakinta, tad'an kallesa, shima idonsa na kanta, munzo yafad'a akasalane.
d'auke kanta tayi tabud'e motar, saida safe tafad'a cikin muryar barci, harta rufe motar Lukman ya ce, "haba malam aii ka rakatadai kasani kotanada magagin barci.
d'an tsaki bobo yayi shima yafito, harta fara tafiya yad'an hanzarta ya cimmata, dama ita kad'ai mai gadi yake jira Dan haka k'ofar abud'e take.
Dariya Lukman yashek'e da ita, sai Bobon Ammi yafad'a harda dukan sitiyari.
Har k'ofar falonsu yarakata, saida takama k'ofar zata bud'e sannan ta ce, " saida safe.
ALLAH yakaimu yafad'a yana juyawa.
Amota yasamu Lukman yashiga gaba suka wuce gida suma..........
_masoya I luv u._
[11/12, 2:17 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
*_"dolene na gaisheku Nice Hausa novels, mungode sosai da k'auna, ALLAH yabar zuminci, Alkairin ALLAH yakai muku aduk inda kuke."_*
Luv u oll⛹🏻♀.
2⃣1⃣&2⃣2⃣
Jiki a sanyaye Rahma tak'arasa cikin falon, tamaida k'ofar ahankali tarufe.
Ajiyar zuciya ummi dake zaune a fallo tana jiran dawowar Rahma ta sauke.
Dama ita take jira dantaga kowa yashigo amma banda Rahma.
"Lah ummi bakiyi barciba?, Rahma tafad'a a sanyaye. Mik'ewa ummi tayi tana murmushi, inani ina barci auta bata dawoba.
Murmushi Rahma tayi kanta ak'asa.
Ummi ta taso takama hannunta suka nufi d'aki, mutane duk sunyi barci, wasukuma suna gidansu ya Kamal.
Rahma tarage kayan jikinta sannan tazauna bakin gadon inda ummi take zaune itama da wasu tarkacen robobi agabanta.
Ummi miye wad'annan?, Rahma tafad'a tana d'aukar wata robar Zuma tana kallo.
Maganin basirne, kinga k'ar6i wannan takardar kiduba, d'azu malam saddiqu na islamiyyarku yakawo bayan fitarku.
Cikin mamaki Rahma takar6a tana bud'ewa, murmushi tayi tareda d'agowa tana kallon ummi da itama kallonta takeyi, ummi wai kinsan miye?.
A'a saikin fad'a.
Sak'one daga islamiyyarmu, wai gobe idan ALLAH yakaimu sun shiryamin walima k'arfe 9:00am to 12:00pm, dukda abin yazo babu shiri.
ALLAH sarki bayin ALLAH, ummi tafad'a cikeda jin dad'i, aiko mun gode musu da wannan karramawa.
Aiko dai, Rahma tafad'a.
Abubuwa ummi ta rink'a dannama Rahma a darennan, harsaida Rahma ta ce, " ALLAH ummi nak'oshi cikina zai fashe.
Dariya ummi tayi ta ce, "to barshi haka saida safe.
Daga nan wasu kayan gyaran jiki ummi ta murjema Rahma jiki dasu sannan suka kwanta.
*_BOBO._*
suna Isa gida yanufi d'akinsa, kayan jikinsa yafara ragewa, yana k'ok'arin zaro wayarsa a aljihu saiyaga ta Rahma, Kansa ya dafe O ALLAH, namanta ban bata wayartaba, zubesu yayi a durowar gefen gadon harda tasa, daganan yacire kayan jikinsa, bayi yashiga, bayan wasu 'yan mintuna yafito, badai wanka yayiba.
Shirin barci yayi ya kwanta, saidai barcin yak'i d'aukarsa, fuskar Rahmace take MASA gizo, k'yawawan idanunnan NATA yake hangowa, yasaki wani lallausan murmushi Wanda bansan na miyeba, saikuma yaja siririn tsaki yana gyara kwanciya.
Nima waje nayo nabarsa.
*_Washe gari_*
Tunda sassafe Rahma ta tashi tai wanka kasancewar tana fashin sallah, Basama tafara yarfa mata k'unshi, masha ALLAHU nafad'a Dan k'unshin yana bada ma'ana.
Jikin Rahma duk yayi sanyi, ta tabbata yau babu fashi saita bar gidansu, cikin dabara take share hawayenta dankar Basma tagani dansukad'aine a d'akin.
Zuwa 8:00am angama k'unshin, yayi k'yau sosai, 8:30am akasa Rahma yayi wanka agurguje dantafiya walimar makarantarsu.
Shiri tayi cikin zani da riga na atanfa pink, ta d'ora bak'ar alk'yabba mai shara shara wadda amaren zamani ke yayi, tayi k'yau sosai dukda yau babu kwalliya afuskarta, dak'yarma tayarda Basma tasaka mata pink d'in janbaki Wanda shiga da kwalliyar alk'yabbar.
Wajen walimar yayi k'yau sosai, acikin harabar islamiyyar za'ayi, malaman sunyi k'ok'ari gsky dukda abin yazo babu shiri.
Wajen da'aka tanada na musamman dan d'alibai su Rahma suka zauna, iyayen yara dayawa sun halarci wajen, su Abba ma duk sunje, su ya kamal ya muneer ya shaheed, da sauran matasan anguwar da iyayensu, dan Rahma mutuniyar kirkice, tsakaninta da kowa a anguwar sai girmamawa, batada hayaniya wannan yasa takasance mai jama'a kowa yana sonta.
Gurin yayi tsit ana addu'a, shigowar wasu motoci hud'u yaja hankalin mutane kowa soyake yaga suwaye?.
Appa yafara fitowa shida wasu dattijai uku, da alama abokansane, mota ta biyu kuwa matasan family nasune, ta ukuma haka harda ya ishaq da wasu zasukai sa'anninsa, motar k'arshe kuwa, ya Hamza da sulaiman, Lukman da tauheed ne, sai Bobo Wanda yakashe kala cikin manyan kaya, purple d'in shaddace mai haske ajikinsa, rigar iya guywa d'inkin zamani, yayi k'yau sosai harda d'ora bak'ar hula.
Wow! Wasu 'yammata dake gefen Rahma suka fad'a, d'aya tace kai Ruma guy d'incan ya had'u wlhy, dama ya ce, "yana sona?.
Rahma tad'ago dantaga wanene wai suketa kurantawa haka?, gabantane ya fad'i tayi saurin kauda kanta.
Abbane yataso shida abokansa da shuwagabannin makarantar suka tarbi su Appa.
Masauki maik'yau aka basu kamar ansan da zuwansu.
Bayan gaishe2 akaima bak'i barka da zuwa.
Itadai Rahma tunda tamusu kallo d'aya bata sakeba.
Dukda da daddare yaganta hakan bai hanashi ganetaba, babu laifi yarinyar tanada k'yau da nutsuwa, bobo yafad'a azuciyarsa.
Mayun idanunsa yadasa mata batareda ya saniba.
Rahma datakejinta atakure, jikinta yana bata kallonta akeyi, tana d'agowa sukaima juna kallon ido cikin ido, Dan suna fuskantar junane.
Da sauri ta janye nata gabanta na fad'uwa, hular alk'yabbar taja takuma rufe fuskarta.
Samun kansa yayi da sakin lallausan murmushi, ya sauke ajiyar zuciya yana kauda kai daga kallonta.
Addu'a aka fara gabatarwa sannan aka buk'aci Rahma tafito tayi karatu.
Gabantane yafad'i, tatuna d'unbin mutanen dake wajen amma acikinsu akeso tafito tayi karatu?....muryar malaminsu taji yana k'ara nanata sunanta.
Ihsan ta ta6ata Rahma kitashi mana.
Ihsan inajin kunya wlhy.
Kinga saka wannan gilas👓 zaki rage jin kunyar.
Siririn farin gilas d'in takar6a tasaka, o ALLAH nafad'a danganin k'yawun da gilas d'in ya k'ara mata.
Ahankali tamik'e tak'araso har inda ake buk'atar ganinta, malam jamilu yabata abin magana.
Tunda tatsaya gaban tebir d'in da aka ajiye alkur'ani mutane ke kallonta, wasukam halittar ALLAH suke yabawa da nutsuwa Rahma.
Appa sai dad'i yakeji Dan yarinyar tashiga ransa.
Gurin yayi tsit danjin zazzAk'ar muryar Rahma tafara fidda sautin karatun alkur'ani mai girma cikin suratul Maryam.
Bobo yalumshe idanunsa danjin muryar Rahma na ratsa ko ina na sassan jikinsa, ALLAH ya albarkaci rayuwarki yafad'a azuciyarsa, ahankali yabud'e idonsa yasauke akan Rahma dake karatu tana hawaye Wanda gilas d'in bai hana agansuba.
Masu hotuna sai k'allata suke, wasu kuma da waya suke mata, harda masu vedio d'inta.
Saida takai har k'arshen surarar sannan taje ta zauna tana cigaba da share hawayenta Wanda narasa namiye?.
Angabatar da nasiha ga amarya da Ango mai ratsa jiki da 6argo, har malam yana tsokanar Rahma da ALLAH yasa wata shekarar su taru haka a sunan baby, dayawan mutanen wajen sunyi dariya dafad'in ameen, (bobo kam murmusawa yayi kawai).
Angabatar da k'yaututtuka ga amarya Rahma, Wanda makaranta suka karramata da yaba k'ok'arinta na hazik'ar d'aliba mai ilimi da girmama manya da rashin karya dokar makaranta.
Abba sai dad'i yakeji.
Cikin abokan Appa dasukazo tare yamik'e shima ya ce, "yayma Rahma k'yautar mota sabuwa dal saboda namijin k'ok'arinta.
(Kabbara akayi da tafi).
Rahma tamik'e tayi godiya, takuma godema iyayenta da malamanta dasuka taka rawar gani arayuwarta, ta ce, ''iyayena sune gatana dasuka tsaya tsayin saka Dan ganin ingantuwar ilimin mu na addini dana zamani, tana kuka tana godiya ga iyayenta abbanta da umminta da yayyaensu da malamanta,....... Kuka mai k'arfi yaci k'arfinta takasa magana sai shashsheka."
Ahankali bobo yamik'e yataka har Inda take, hanky yamik'a mata fari tas daketa tashin kamshin daddad'an turarensa.
Jiki a sanyaye takar6a idonta ak'asa ta ce, " ngd tafad'a cikin shashshekar kuka.
Abin maganar yakar6a daga hannunta, yafara mik'a godiya ga iyayensu da kuma malamai da 'yan uwa da abokan arzik'i dake wajen taron, yahad'a da sakama Rahma albarka da yaba mata.
Kabbara akayi da tafa MASA, abin ya burge mutane gsky, Rahma taji dad'i sosai, dukda tasan ba Sonta yakeba tunda had'asu akayi, amma yay mata wannan karamcin.
Abba da yayuntama sunji dad'i abinda bobo yayi.
Hakama su Ya Hamza bobo yaburgesu, fatansu ALLAH yasa yad'ore haka har gidan aurensu.
'Yammata kam dayawa sun k'yasa saidai sun 6oye kodan Rahma.
Bayan jawabin manyan bak'i da nasihohi taro yatashi lfy, daga nan akayi hotuna kowa yakama gabansa.
Kowa yana zuwa gida yafara shiri a gaggauce Dan ana sakkowa daga masallaci za'a d'aura auren.
Kowa yafito anata shiga mota Dan tafiya sallar juma'a da d'aurin aure.
Masha ALLAH nafad'a yayinda na hango muku ango Bobo yaci kwalliya cikin Sky blue d'in shadda harda babbar riga, wayyo masu karatu bayyana muku k'yan dayayi 6ata lokacine, ammafa ya had'u.
Masallaci suka nufa.
Bayan sakkowa suka wuce anguwar su Rahma.
_Alhmdllh anguwar tacika mak'il da jama'a, wasuma akan mota suke zaune, gurin yacika har babu gurin faking, dukda nisan da su Rahma suke dashi da titi, wasu sai abakin titi sukayi faking motarsu._
K'arfe 3:30pm d'umbin al'ummar Annabi suka shaida d'aurin auren *_"Abdulmalik Aliyu Abdulmalik hamshak'i, da amaryarsa Rahma Bilal Basheer mai Gold. "_*
(To ango da amarya saimuce ALLAH yabada zaman lfy da fahimtar juna ameen).
Dak'ar na iya samo muku Rahma amarya ad'akinsu itada gayyar k'awayenta Wanda yawanci duk yaran family nasune, wasu kuma 'yan islamiyyarsu da boko.
Tahad'u cikin less ja mai adon farin siton masha ALLAHU, amarya tafito ras saidai mak'iyi.
anacewa and'aura auren tafara kuka, su Ihsan suna lallashinta.
(To Rahma sai hak'uri aii).
*_Safna_*
Safna ana gidan su ya kamal, ita adole tayi gudun hijira, ko wanka batayiba bare kwalliya, tana kwance ad'akin Ameera tana chart abinta hankali kwance, fira suke da k'awayenta a group suna tsokanarta wai tamusu bak'inciki, dayanzu sunata shan shagalin biki.
Dariya tayi ta ce, " karku damu aii kwanannan zakusha bikin nida bobona.
Toma ALLAH ya kaimu...
Kafin tabada amsa Zainab autarsu Ameera tashigo tana fad'in an d'aura aunren.
Wata gagarumar fad'uwar gaba tariski safna dake kwance, tadafe k'irji tana fad'in ya salam, saikuma ta sauke ajiyar zuciya takoma takwanta, haka kawai taji jikinta yayi sanyi, zuciyarta tayi k'unci.
Zuwa wani lokaci kuma saitaja tsaki, tomima zai dameni tunda ALLAH ya tsallakar dani daga wannan auren k'addarar.
Rahma ALLAH ya yanka miki kazar wala sai aje aita figa.
Sainazo gayyatarki aurena da Bobo na.....
Na ce, "hummmmm.
*_" kuyi mana afuwa jiya bamuyi posting ba, mai copy d'ince take mura, nikuma nayi busy, amma gashinan yau nadage nayi muku kafin ta warke tacigaba."_*
Luv u oll.
_bilyn Abdul ce⛹🏻♀._
*luv u oll my fan's_*
*_(((S))).......2017._*
[11/12, 2:20 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
2⃣3⃣&2⃣4⃣
Biki yacigaba da gudana cikin farin ciki da Annashuwa, gidajen biyu anata hada hada.
Bayan kammala d'aurin aure anguna suka shigo cikin gida akayi gaishe gaishe da hotuna, itadai Rahma koda wasa bata yarda sun had'a ido da Bobo ba har aka gama hotuna suka tafi.
Shikam jinsa yake wani iri kuma cikin nishad'i, komai na Rahma yana burgeshi, musamman yanda take komanta cikin sanyi.
Haka suka k'arasa gidasu, nanma cike yake da mata, tunda suka shigo akai caa kan bobo, sai tsokanarsa su aunty Rasheeda sukeyi, baya cewa komai saidai murmushi.
+.+.+.+.+.+.+.+.+.+.+
*_5:30mp_* aka gama shirya amarya domin mik'ata gidan angonta, tana falon Abba inda dangi suka zagayeta anata nasiha gareta, sai rabzar kuka take tamkar zata shid'e, ummi ma kuka takeyi Dan takasa cewa komai yayinda aka kaimata Rahma gabanta dan taimata nasiha, babu abinda take fad'i sai ALLAH yay miki albarka Rahma, yanda kikai mana biyayya kema ALLAH yabaki 'ya'ya masu yimiki, kuka yaci karfin ummi takasa cigaba.
Haka aka hak'ura aka fito da Rahma, Abba dakansa yasakata mota tanata kuka, ya Hamza dazai tuk'a amarya jiyayi tabashi tausayi, shima kamar yay kuka yakeji.
Kuka sosai Rahma takeyi abin tausayi, momyn su Ihsan da Maman Basma suka shiga motar suma, tsakkiya suka saka Rahma daketa kuka har numfashinta na d'aukewa.
Yayinda Abba yaga motocin amarya sun Lula, yatabbatar da gsk yau Rahma ta barsu, sai kawai yaji hawaye sun cika masa ido, yasa gefen rigarsa ya share tareda juyawa gida.
Canma tararwa yayi ummi NATA kuka, yashiga lallashinta damata nasiha.
Gayyar amarya ta isa gidansu Bobo, Dan nan za'a ajiye amarya sai gobe idan ALLAH yakaimu amaida ita gidanta.
Har cikin harabar gidan aka shiga da motar amarya.
Suna fitowa saiga Ammi da gayyar k'awayenta, wasu sosuke kawai suga mace mai sa'a data samu bobo amatsayin miji, Dan sunsha bashi 'yayansu amma ya ce, a'a, (basu San itama had'asu akayiba ba soyayya bace).
Sanye Rahma take cikin shadda ruwan madara zani da Riga, ta lullu6a da k'aton mayafi ruwan k'asa mai turuwa, hakama takalmin k'afarta, kanta arufe yake shiyyasa masu tsogumi basu ganiba, Ammi tarungume Rahma tana lallashi, kama hannunta tayi takai har cikin d'akinta na sama, lallashinta tad'anyi na minti biyu saida taga tad'an tsagaita da kukan sannan tafito aka tura k'awayenta.
Gida ya harmutse Dan cike yake dank'am da jama'a, gashi yau Ammi takeyin yinin biki dama.
Sai bayan magriba dangin amarya suka juya domin zuwa suyi shirin tafiya wajen dinner daza ayi k'arfe 8:30pm to 12:00.
Gidan yad'an rage hayaniya kad'an tunda mutanen sund'an ragu babu laifi.
Duk wannan hidimar da akeyi bobo yana can cikin lambun gidansu da aka k'awata da haske, shikad'aine zaune akan kujera mai lilo idonsa alumshe yana duniyar tunanin rayuwarsa shida marigayiyya Ni'ima.
Yatuna itama haka akaiyi aurensu baya sonta, Dan ko taro d'aya bai halartaba alokacin na shagalin bikinsu, shiyyasa yake mamakin wannan karon komai Appa yace yayi baya musu saiyaje yayi.
(Wata zuciyarsa ta CE sannan ai kana kan hayak'in samartaka ne).
Hakane kuma yafad'a afili.
Bud'ar data cika gidance da k'aruwar hayaniya ta tabbatar MASA da amaryarsa ta iso, yamatse idonsa dake arufe tareda fad'in ALLAH yajik'anki Ni'ima ta, kifahimceni ba laifina baneba, nima sakani akayi dole badan inason aurenba."
Jiyay tamkar maganar Ni'ima acikin kunnanensa tana fad'i masa, _"karka damu mijina Nima zanyi farincikin kasancewar Rahma amatsayin matarka, kodan tarin alkairai dake tartare da ita, na tabbata Nawal tasamu uwa tagari wadda kullum take maka nacin samu, INA tayaku farincikin mallakar Rahma kaida Nawal, ka kwantar da hankalinka kakuma rik'eta amana"._
Shirun dayajine yasakashi mik'ewa zumbur yafara dube dube da mutsike idanu, Kodai mafarki yakeyi?, da gsk fa muryar Ni'ima yaji wlhy.
Jikinsane yafara Rawa, cikin Sauri yabar cikin lambun Dan aganinsa wata aljanace takeson bud'e MASA ido.
Cikin hanzari ya iso harabar gidan inda su ya ishaq suke, Dan bandasu wajen maida 'yan kawo amarya.
Najeeb abokin ya Ishaq ya ce, "ango lfy kuwa naganka a hargitse?, ko duk murnar zuwan amaryarne?.
Saurin saisaita nutsuwarsa yayi ya sauke ajiyar zuciya yanajan farar kukera d'aya ya zauna, babu komai ya Najeeb yafad'a ad'an d'arare.
Wai tun d'azu kana ina?, ya Ishaq ya tambayeshi.
Ina lambu." Yabada amsa atak'aice.
Hira su ya Ishaq sukeyi amma bobo kokad'an baya sakamusu baki, addu'oi kawai yake zabgawa azuciyarsa, fatansa ALLAH yasa abinda yaji ya tsaya iya haka.
Suna nan zaune har aka kira sallar isha'i suka tafi sukayi.
Amarya tanacan ana zabga mata kwalliya, da k'yar aunty Sameera da aunty ummy suka lallasheta tayi shiru aka fara kwalliyar.
Hummm amaryafa tagama had'ewa abin kamar babu gobe.
Shiryata akayi cikin farar doguwar riga ta aure, amma mai dogon hannu, aka nad'a mata d'aurin d'ankwali da bak'in d'an kwali, tasha sark'ar gold wadda k'yautace daga Abba, kai jama'a yaufa take sallah, amma awajen amarya da ango, amaryakam tayi d'am kamar kasaceta ka gudu, na tabbata ko bobo yagani yau saiya narke.
Shimadai ba'a barsa abayaba wajen d'aukar wanka cikin farar shadda harda babbar riga, ya murza bak'ar hula sai kyalli takeyi, sajensa da sumarsa sun kwanta luf luf sai tashin k'amshi yakeyi, cikin hanzari yake d'aura agogon azurfa ahannunsa saboda masifar da ya sulaiman yake masa.
Haba Abdulmalik kai kullum sai anjiraka?, aurenka nefa, kai yakamata ace komai kana gaba amma kaine abaya haba Dan ALLAH."
yi hak'uri nidai ya sulaiman muje nagama aii.
Haka suka fito sai zabga k'amshi yakeyi, yaukam amarya tarigasa, Dan tuni tana mota, bud'e masa Ridwan yayi yashiga inda Rahma take.
K'amshinsu yahad'e Dana mortar ga sanyin AC saiya bada wani yanayi mai dad'in gsk.
Rahma kam lumshe idanunta tayi dataji shigowar Bobo motar, kanta na k'asa Dan bataso su had'a ido ko kad'an.
Shikam saida ya zauna sosai harma sun fita daga gidan sannan yakai kallonsa kan Rahma da k'amshin turarenta ya addabesa.
Tsigar jikinsace ta tashi yarrrrrrr O ALLAH, yafad'a ahankali wandda har Rahma taji furicinsa, wani Abu yaji yana mintsinin zuciyarsa, da k'yar yay control d'in kansa, murya k'asa2 ya ce, yauma aramin fos d'inki.
Bata kalleshiba tamik'a masa bak'ar fos d'in wadda tasha adon fararen duwatsu sai kyalli suke.
Jiki a sanyaye yak'ar6a, yauma kud'i yazuba mata, rafar 'yan d'ari biyar Biyar, sababbi k'al.
Bai bata fos d'inba har suka isa wajen taron, itakuma bata tambayeshiba.
Bayan tsayawarsu Ridwan yabud'e musu suka fito, Rahma tana tsaye har bobo yak'arso wajen, hasken wutar lantarkin daya yalwatu awajen yabashi damar k'are mata kallo sama da k'asa, itadai kanta na k'asa Dan dukta Raina kanta kallon dayake mata.
Murmusawa yayi Dan ganin yanda take sinne kai k'asa, fos d'inta yamik'a mata, tasaka hannu biyu takar6a tareda fad'in ngd.
Baice komaiba yagyara tsayuwarsa suka jera.
A Bokansa da 'yan uwa samari da 'yammata duk suna bayamsu kowanne shida budurwa d'aya, gabansu kuma Nawal ce da Kaleel d'in ya Ishaq, suma anmusu kwalliya cikin kaya kamar su Rahma doguwar Riga Nawal, Kaleel ma kwalliyarsa kamar ta bobo harda malum malum.
Abin ya k'ayatar da jama'a masha ALLHU.
Ahankali taji Bobo yasak'a hannunsa mai azabar laushi da sanyi cikin nata, da sairi ta kalleshi, shima kallonta yayi da sauri danji wani laushi na musamman da hannun nata yakeyi, k'asa ta maida kanta danjin wani yarrrrr ajikinta saboda lallausan murmushi da Bobo yasakar mata.
Tafiya sukeyi ahankali Rahma tana zancen zuci, tunda aka fara bikinnan koda wasa bobo bai ta6a jikintaba sai yau, saikuma jiya data kusa fad'uwa awajen mothars night, wannan kuma takalleshine amatsayin taimako daya bata dankarta fad'i. Dan haka k'irjinta ya hau luguden daka, (zuciyarta ta ce, "yanzu kinzama matarsa sa6aninda daba halalinsa bace ke.)
Kobabu komai ya burgeta, tunda yakasance mumum mai sanin muhimmancim addininsa da bin dokokin ALLAH.
Har suka k'arasa inda aka tanadi kujeru biyu ajere dansu, saida tafara zama haryanzu hannunta na cikin nasa, sakin hannunta yayi ya tattare babbar rigarsa ya zauna shima fuskarsa ad'an sake babu laifi.
Nawal dasuka rakosu tazo kusada shi tatsaya, baby tafad'a ahankali.
Kallonta yayi yamata murmushi tareda kamo hannunta, babyna kinyi k'yau yau, miya faru?, tayi 'Yar dariya bakomai baby amma wacece wannan?.
Juyawa yayi yakalli Rahma da kanta ke ak'asa tana wasa da duwatsun jikin fos d'in ta, yay murmushi.
Zan fad'a miki amma ba yanzuba, kije ga ya Kaleel can yana kiranki Ku zauna wajensu momy.
To baby bye, tafad'a tana sauka daga wajen.
Shima hannu yad'aga mata yana murmushi.
Taro aka cigaba da gudanarwa yanda yakamata, yauma amarya da ango basuyi rawaba, saidai lik'i dasukaita zubama juna, yayinda dangima suka rufesu suna lik'a musu suma, mai wak'a yaga ruwan kud'i yakuma haukacewa yana wak'e ango da amarya.
Bayan sun koma mazauninsu akace su yanka cake.
Mik'ewa sukayi suka k'arasa inda aka ajiye cake d'in mai hawa uku, Wanda tasha ado mai k'yau, Rahma aka umarta tafara d'ora hannunta akan wuk'ar, sannan Bobo yad'ora nasa hannun akan na Rahma, bayan k'irga uku suka yanka, tafi akayi Raf raf raf.
Akace Rahma taciyar da Bobo, kunya dukta isheta amma yazatayine, haka taciro daidai bakinsa ta rissina tasaka masa abaki idonta ak'asa, aka kuma sakin tafi, tasaka masa kofin lemo abaki, kur6a biyu yayi tajanye tasaka hanky tagoge masa bakin, ihu aka saka ana bata tafi.
Itadai kanta nak'asa tayi d'an murmushi, bobo madai murmushi yakeyi.
Shima akace yabata.
K'aramin shima yaciro, yamatsa daf da ita sosai tamkar zai shige jikinta, batayi auneba taji yasak'alo hannunsa ak'ugunta, ajiyar zuciya ta sauke ahankali.
Cake d'in yasaka mata abaki, tafi mai k'arfi aka bashi, fuskarsa d'auke da murmushi yasaka mata cup d'in lemo, ku6arta d'aya ta kauda kai, yasaka hanky shima yad'an goge mata baki kad'an saboda janbakinta, sai kawai taji yabata Sumba akumatu (kiss) wani ihu aka saki gaba d'aya wajen ana tafi.
Rahma jitake kamar zata nitse awajen Dan kunya, gashi yak'i sakinta.
Dahakadai taro yatashi lfy, bayan hotuna da aka yi.
Amarya da ango suka shiga mota aka maidasu gida.
Luv u oll⛹🏻♀.
[11/12, 2:11 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_{Bobo}_
_Story & editin_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
✍🏿 _Written_
*_Marak'isiyya_*
_hak'in mallaka_
*_Aunty Bilyn Abdul_*
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Bily giro_*
2⃣5⃣&2⃣6⃣
Kowa yagaji, ana shiga gidan gurin kwanciya kawai mutane suke nema.
Rahma kam harma tafara barci a mota, saida bobo yatada ita, aiko ko kallonsa batayiba tafice saboda kunya.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Wanka yafarayi sanan yay shirin barci, kad'an kad'an saiyayi tsak'i dad'an cije le6e, candai yakasa jurewa yakira khursiyya.
Duk suna d'akin Ammi inda Rahma take harda matamsu ya Sulaiman Dan suma yau anan zasu kwana.
Sunata shirin Barci aunty Rasheeda na tsokanar Rahma tanata murmushi da 6oye fuska.
Aunty ummy tamik'oma Khursiyya wayarta.
Kai aunty waye Dan ALLAH a darennan?, ke Bobo nefa.
Ya bobo kuma?, lfy bayanzu muka rabuba?.
Cikin tsokana aunty Sameera ta ce, "kika sani ko muryar matarsa yakesonji........ Dariya sukayi yayinda Khursiyya tad'aga wayar tasaka akunne hello yaya.
Muryarsa can k'asa ya ce, " kidafamin Lipton kimatsa lemon tsami biyu manya aciki, baijira amsartaba ya yanke wayar.
6ata rai Khursiyya tayi tamkar zatayi kuka ta ce, ''kai wlhy nidai nabani, daga dawo ga barci inaji amma zaiwani sakani aiki, ALLAH yasa abaka matarka gobe kuwuce muhuta da saka aikin tsiyarka.......
Lafiya kekuma aunty Rasheeda ta tambayi Khursiyya?.
ALLAH ya Abdulmalik d'innan ne, wai atsohon darennan zaisha Lipton Dan iyayi harda lemon tsami, nibansan tsiyar dayakeji ashan Lipton da lemon tsamiba.
Dariya su aunty Rasheeda suka kwashe da ita harda tafawa, aunty Sameera ta ce, "aii dolene yay control kansa da lemon tsamin irin wannan Sumba d'azu dayabama amarya awajen Dinner, o ni Abdulmalik anaso ana kaiwa kasuwa, suka k'ara shek'ewa da dariya.
Itadai Khursiyya fita tayi tana k'unk'uni da kumbura Baki, Dan batasan Inda zancen matan yayen Nasu yadoba.
Itama Rahma ba fahimtarsu tayiba, Dan haka ta tashi tashige bayi dan k'imtsa jikinta.
Akicin ta iske Ammi tana d'ibar abinci.
Ke kuma lfy baki kwantaba?, wakikema k'unk'uni ma haka?.
ALLAH Ammi ya Abdulmalik d'innan ne mana, wai adarennan zaisha Lipton hardasu lemon tsami, kawai salon saka aiki.
To idan kinyi hak'urima aii yaune kawai, gobe iyanzu yana gidansa.
Hakane ammi, ammafa kullum kamar ibadar ALLAH saiyasha shayinnan. Azuciyar Ammi saitake mamakin halin Abdulmalik, yana cikin damuwa amma bazaiyi aureba sai ammasa ta k'arfin tsiya, shidai halinsa daban acikin 'yayanta, ALLAH ma kad'ai yasan tun yaushe yake acikin wannan halin.
Afili kuma saita girgiza kai tana fad'in kidafa masa to dare nak'arayi.
Bayan fitar Ammi Khursiyya tadafa Lipton tanata mita, ta matsa masa lemon tsamin sanan tasaka a k'aramin tire tafice zuwa d'akinsa.
Akwance tasameshi rufda ciki, sanye yake cikin kayan barci.
Yaya gashi tafad'a tana ajiyewo.
Baice mata k'alaba bare ya d'ago.
tajiye tafito cike da haushi, babu yanda za'ayi yasaka ka aiki kaimasa yaymaka godiya bayan kagama, duk cikin yayinyunsu shine halinsa da ban, duk masifar ya ishaq yafi yaya bobo sauk'i.
Shikam kobayan fitarta yakai Monti Biyar sanan yatashi zaune yana matse fuska.
Dukda turirin da shayin yakeyi saboda zafi, haka yayta shansa yana cije le6e, yana gamawa wata zufa tafara karyo MASA adukkan sassan jikinsa.
Kwanciya yayi ahankali yana sauke numfashi, bayan wani lokaci yasamu nutsuwar sarayar ciwon nasa.
Kwanciyarsa yagyara barci yay a won gaba dashi.
*_washe gari_*.
K'arfe 10:30am aka fara gudanar da sisters day aharabar gidan, masha ALLAH komai tayi k'yau, yaudai basuga idon bobo ba, yana d'aki kwance barcinsa yaketa kwasa na gajiya.
Sisters day kam yabada ma'ana, amaryama yau tasha k'yau, su khairiyya sun raba k'yaututtuka taro yatashi lfy.
2:00pm aka gabatar da walima, mutane suka fara kama gabansu, wasuma bak'in sun wuce tun safe, wassu kuma sai gobe idan ALLAH yakaimu.
Rahma dum jikinta yayi sanyi tunda aunty ummy tashigo tace ta shiraya da angama sallar isha'i za'a mik'ata gidanta.
Kallo ihsan dake zaune Kusada ita tayi, ihasan wai ina wayatane?, kwana biyu wlhy bangantaba nazata tana wajenki.
A'a wlhy wayarki bata a wajena, amma bari akira muji.
Kiran wayar suka farayi....
Bobo nazaune ad'akinsa yana danna laptop yaji wayar Rahma dake caji tana wringing, kamar bazai dubaba saikuma yamik'e yad'auka.
Ana d'agawa ihsan tamik'ama Rahma wayar tana fad'in and'aga.
Cikin sanyinta ta ce, "Assalamu alaikum.
Lumshe idanunsa yayi danjin sassanyar muryarta.
Wa'alaikissalam ya amsa cikin nutsuwa.
Gabantane yafad'i danjin murayarsa, taganeshi sarai amma saita dake ta ce, " Dan ALLAH wanene?.
Jin haka shima saiya basar ya ce, "kema wacece?.
Mai wayarce, Dan ALLAH ya akayi tazo hannunka?.
Murmushi yayi tareda shafa gemunsa na gayu, ya ce, " mijinkine, nasamu wayar ahanunkine kuma.
Ajiyar zuciya ta sauke, muryarta nad'an rawa ta ce, "to shikenan.
Yanke wayar yayi kawai yana murmushi shima.
Ihsan dataji komai bata Neman k'arin bayani dantaji komai.
Screen d'in wayar yadasama ido, photon Rahma ne ajiki da Safna, sunyi masifar k'yau ahoton.
Tunda wayar tazo hannunsa baita6a tunanin dubataba, Dan tunda ya ajiye baibi takantaba, yau yaji tanata kukan k'arewar caji shine yasaka mata cajin.
Yad'an lumshe idon yabud'e akan wayar, kowacece wannan kuma?, yafad'a aransa.
K'ila yayartace, (wadda tace bata sona kenan?) Afili yay maganar, bakinsa yata6e yana k'arema safna kallo, tabbas tafi rahma k'yau, amma Rahma tafita kwarjini da fuskar kamala.
Bakinsa yak'ara ta6ewa yamaida wayar a caji.
Hawowa gadon yayi yacigaba da aikinsa.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Bayan Sallar isha'i Rahma tagama shiri cikin kyakykyawar Shiga ta material siket dariya, tayi k'yau sosai kuwa, sai tashin k'amshi turare takeyi.
Haka wasu k'alilan daga cikin danginsu, dakuma su aunty Rasheeda sukai mata rakkiya had'ad'd'en gidan Bobo dayasha gyara tamkar sabo.
Idonta na rufe tanata sharar kuka, da tunanin gamonta da ango yau, koyaya zai k'ar6eta kuma?, dukda yanuna mata kulawa awajen taron bikin hakan baya tabbatar mata dazata samu kulawarsa ayayin zamansu.
Dan zai iya yuwuwa yayima iyayensa biyayyane kamar yanda itama tayima nata biyya......
Da wannan tunani su aunty Rasheeda sukaimata sallama harda su ihsan suka tafi.
Kuka sosai tashiga rabzawa harda shashsheka, tana tausayama kanta da rayuwarta. Amma tana rok'on ALLAH tazama mai hak'uri da juriyar biyayya ga ALLAH da MANZONSA, dakuma iyayenta.
Zamewa tayi ta kwanta tana cigaba da kuka maiban tausayi da tsuma zuciya.
.*......*.......*........*.....*.
A6angaren Bobo kam yana d'akinsa harya kwanta hankalinsa kwance.
Ammi takalli agogon falon karfe 9:53pm amma har yanzu Bobo bai fito yatafi gidansaba.
Mik'ewatayi ta haura saman Dan gidan mutane sun ragu sosai.
Kallon mamaki tabisa dashi.
Shima yad'ago yana kallonta, Ammi na lfy kuwa?.
Lfy lau, mikakeyi har yanzu baka tafiba?.
Cikin mamaki ya ce, "Ammi ina kuma zani?.
Gidanka mana.
Gidana kuma?, Ammi canakefa sai gobe?.
Harararsa tayi, cikin d'an fad'a ta ce, " tunda d'azu su Rasheeda suka dawo daga rakkiyar matarka, amma kananan zaune, katashi katafi gidanka anbarta ita kad'ai, nasan tanacan atsorace.
Bata jira amsarsaba tafice afisace.
Ajiyar zuciya yasauke yana turo baki gaba kamar wani k'aramin yaro.
Haka yatashi ya canja kaya kamar zaiyi kuka Dan haushi.
Farar shadda yasaka sai maik'o takeyi, yad'ora jar hula da silifas ja mai k'yau, turare yafeshe jikinsa dashi, sannan yajawo jakar lop-top d'insa yasaka duk abinda zai iya buk'ata na 6angaren aikinsa, yakashe kayan wutar d'akin yafito sai zabga k'amshi yakeyi.
Ammi yatarar afalonsa tana jiransa, ganin ranta ad'an 6ace yasa yasaki fuska, cikin murmushi da zolaya ya ce, "Ammi na nayi k'yau.
Itama fuska tasaki tana kallonsa, ta ce, " masha ALLAHU Mukarram d'ina kayi k'yau sosai, ALLAH yaymaka albarka kaji, yabada zuri'a tagari, ya albarkaci wannan aure.
Biyayyar dakake mana ALLAH yasa kaima 'ya'yanka suyi maka.
Ammin Ammi na ngd sosai da addu'arki gareni, bari naje wajen appa namasa sallama ina baby mutafi?.
A'a ita ba yauba, sai bayan sati d'aya tukkuna.
Ammi saboda mi?, cikin shagwa6a yay maganar.
Dariya ammi tayi ta ce, "shagwa6a66ena sai angama amarci tukkuna, idan d'iyata tagama hutawa da gajiyar biki saikazo kad'auki Nawal d'in.
Shike nan ammi, amma.......
Katsesa tayi da fad'in kaga jekayima Appanku sallama dare nak'ayi.
Haka yahak'ura yanufi d'akin Appa, bayan sun gaisa yaymasa nasiha sosai da saka masa albarka sannan yafito yatafi.
Mota yashiga yabar gidan cike dakewar iyayen NASA.
Awajen wani gasa naman kaza ya tsaya, yasayi guda biyar sai k'amshi sukeyi, yasayi kayan fruit dayawa yanufi gidansa zuciya acinkushe da tunani kala kala...........
*_" Alhmdllh. inaga 'yan uwa yakamata mudakata anan sai bayan sallah, gobe idan ALLAH yakaimu kowa zai nemi k'unshi da k'itso babu time d'in karatu, jibima haka ga aiki tunda daren sallah ne, Dan haka muyi hak'uri zuwa bayan sallah idan ALLAH yakaimu lfy."_*
_ina muku barka da sallah, inakuma baku hak'uri da godiyar had'inkai da kuka bani, ngd sosai, inaga ni anan zan barku Dan bayan sallah zan koma gida, gashi wayata ta lalace bana charting yanzu, dasai nacigaba damuku, dama da wayar aunty Billy nake typing d'in, amma ina rok'on ALLAH yasa tacigaba damuku, dukda naga tanada aiyuka agabanta._
_Na rok'ar muku ita sosai akan taringa muku typing d'in ko babu yawa sosai, Dan wlhy buk d'in yahad'u sosai masu karatu, shiyyasa Nima narikice nahau yimuku copy, lagwadar labarin nagaba, Dan akwai cakwakiya sosai acikin Novel d'in, kardai nacikaku da magana ALLAH yasa tayi muku._
_Wanda na 6atamawa Dan ALLAH ya gafarceni nabarku lfy._
*_taku Marak'isiyya ibraheem musa._*
Luv u oll.
By ✋🏻✋🏻✋🏻✋🏻masoya, ALLAH yahad'amu da alkairinsa.
Ngd.
Aunty bilyna gareki, Dan ALLAH kicigaba da gashi🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻plzzz.
[11/12, 2:21 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
🤝 *_Assalamu alaikum, ina mik'o muku sak'on barka da babbar sallah, ALLAH ya maimaita mana, muga ta bad'in bad'in bad'ad'a, saidai akwai matsala babu Wanda ya aikomin da kai da k'afafu, bare suya.☹😋😂_*
2⃣7⃣=2⃣8⃣
Hon yayi mai gadi yabud'e masa gate, saida yatsaya suka gaisa sannan yay cikin gidan, guri yasamu yay fakin zuciyarsa cike da tunani kala2.
Yafito tareda kwasan kayansa yanufi ciki, tafiya yake tamkar bayaso, zuciyarsa cike da waswasi, yaushe rabonsa da gidan nan a rin wannan lokacin?...... K'ofar falon yabud'e yashiga, wani k'amshin dad'i yadaki hancinsa, yashak'a ya lumshe idannunsa sannan yabud'e, bin ko INA na falon yakeyi da kallo, komai masha ALLAH, Iyayen amaryar tasa sunyi k'ok'ari gsky, komai na falon farine da ratsin golden.
Hasken fitilun yak'ara yalwata k'yawun falon sosai, ajiye ledojin yayi yad'au jakar lap-top d'insa kawai yanufi d'akinsa.
Yazube kayan tareda fad'awa saman gado yana fad'in wash ALLAH na.
Yay lamo yana tunani Wanda bansan namiyeba, yakai minti goma ahaka sannan yatashi, harya fara cire ma6allin wuyan rigarsa saikuma yatsaya yana tunani, koba komai yakamata ya lek'a d'iyar mutane, k'ilama bataci komaiba, mik'ewa yayi yafito falon, kicin yafara shiga yad'auki filet da Kofi yadawo falo yasaka kaza d'aya afilet d'in, hakama kayan fruits d'in yazuba awani filet d'in daban, yad'orasu saman babban tire harda ruwa da fresh milk sannan yanufi d'akin.
Tiren ya ajiye ak'asa saman kafet d'in dake gefen lafiyayyayen gadon nata, yabita da kallo tana kwance ta takure waje d'aya kamar tanajin sanyi, yad'anyi tsaki yana kauda kansa daga kallonta, "k! Yafad'a ad'an kausashe.
Komotsi batayiba Dan bama tasan yanayiba, fuska yak'ara had'ewa yana kuma fad'in " k!! Wai bak'ya jinane?, ganin bata motsaba har yanzu yasashi matsawa Kusada ita daf, ashema barci takeyi yak'arshe maganar da tsak'i. Hannunsa yasa ya bubbuga filon data saka kanta, firgigit ta tashi tana kad'a manyan danunnan NATA masu suffar kwai.
Kauda idonsa yay daga kallonta Dan idanunta suna masifar tafiya dashi babu k'arya, ga abincinan kitsashi kici yay maganar yana k'ok'arin ficewa daga d'akin.
Ngd, amma nak'oshi, nitsatstsiyar muryarta ta daki kunnuwansa, bai juyoba amma yatsaya, hannayensa cikin aljihu wandonsa ya ce, "wannan yarage kuma naki, yay waje abinsa.
(Ni bilyn Abdul nace sabon salo, bobo Yakuma zaka canja mana?, bamuyi zaton hakabafa☹).
Itakam Rahma hawaye tamatso takuma komawa takwanta, saida tayi kuka mai isarta sannan ta tashi zaune, afili ta ce, " dama nasan bazan samu farincikiba, duk wata kulawa Daka nunamin awajen taron bikin naganin idon danginane danaka, ya ALLAH ka kawoma rayuwata d'auki, kodan darajar biyayya danaima iyayena, nashare musu hawayensu alokacin dasuke zuba, Nima ALLAH kaji k'aina ka daidaita zamana da mijina yafuskanceni tamkar kowacce mace, takuma rushewa da kuka.
(Ayya Rahma tabani tausayi gsky).
Sauka tayi daga gadon tad'auki tiren tafito, kicin tanufa Dan saida su aunty Sameera suka Nuna mata ko INA na gidan kafin su tafi, firij tabud'e ta saka komai Inda taga yasaka sauran, tad'auki fresh milk d'in da kofin tafito.
ko tsayawa kallon falon batayiba takoma d'aki, saida ta kulle k'ofarta sannan tacire kaya tayi canji Dana barci.
Zama tayi bakin gadon tasha fresh milk d'in sosai sannan tashiga bayi tai burosh tadawo tai kwanciyarta bakinta d'auke da addu'ar barci.
Shima yana komawa d'aki kayan jikinsa yarage yasaka na barci yahau gadon yazauna, jakar dayazo da ita yabud'e ya fiddo lap-top d'insa yafara aiki.
Ganin ba kwanciya zaiba nayo waje nikam Dan barci nakeji sosai.
_washe gari._
Da asuba kafin yawuce madallaci saida ya kwankwasa mata k'ofa, saida yaji alamar ta tashi sannan yafice.
Jin yafita takoma tayi kwanciyarta Dan har yanzu tana Hutu.
Saida gari yay haske sannan bobo yadawo gida, barci Yakoma abinsa Dan yana buk'atar Hutu sosai.
*_7:48am_*
Rahma ta tashi, wanka tafarayi sannan tagyara gidan tsaf dukda ko ina fes yake amma tak'ak'k'ara gyarawa, tabud'e ko ina da k'amshi, tana k'ok'arin komawa d'aki taji ana kwankwasa k'ofa, saida tad'anyi shiru nawani lokaci sannan. Tanufi k'ofar tabud'e, ganin khairiyya da khursiyya yasata sakin murmushi, hanya tabasu suka shigo sannan tamaida k'ofar tarufe.
Itama zama tayi suka gaisa (Dan zasu iya zama sa'anni itada tagwayen Ammin), ta ce, "yasu Ammi?.
Lfy lau tanama gaisheki, ga break fast tace akawo muku.
ALLAH sarki Ammi mungo sosai.
Khursiyya ta ce, " Yaya fa?.
Saida tayi k'asa da kai sannan ta ce, "yana barci bai tashiba.
Khairiyya da khursiyya suka kalli juna suna dariya, saikuma suka mik'e tomu bari muwuce sai anjima.
Kai haba dawuri haka?, ALLAH nazata anan zaku wuni.
Rufana asiri wannan mijin naki bayason warigi, khairiyya tafad'a ahankali.
Saida tarakasu har bakin k'ofar sannan tajuyo ciki, kwandon abincin ta d'auka takai dinning, ta ajiye komai inda yadace, taje kicin tad'akko duk abinda za'a buk'ata ta ajiye, abincinta tad'iba takoma bedroom taci.
Bobo kam ana gado ana kwasar barci, sai 10+ yatashi yay wanka yashirya cikin k'ananun kaya yayi k'yau sosai masha ALLAH, yaci sunan nasa Bobo.
Yaji dad'in ganin falon fes dagani kasan yak'ara shan gyara, baibi takan Rahma ba yanufi firij d'in dani danufi d'aukar fresh milk yasha saiyaga abinci, ganin kamar kulolin gidan Ammi yasa yazauna yaci abincinsa yay nak sannan yafice.
(Araina nace yadace ace yalek'a yaga yata kwana aii).
Rahma tanajin fitarsa, danhaka tarabga tagumi tana tunanin sabuwar rayuwarta ta yanzu.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Asibiti yanufa Dan duba yarinyarnan da akaima fad'e, jikinta yayi kyau sosai Alhmdllh, saidai har yanzu bata magana, tsakaninta da Bobo saidai kallo, tana bashi tausayi sosai Dan yanajinta tamkar Nawal, yasan idan Nawal ce ko cikin 'yayan yayensa ko k'annensa mata biyu wata tashiga irin wannan halin yasan zasushiga cikin tashin hankali fiyema da haka, ALLAH kad'ai yasan itama halin da iyayenta suke aciki yanzu.........jiyowa yayi dasauri danjin an ta6asa, ya Sulaiman ne.
Kaikuwa miya fiddoka da sassafennan?.
Haba Yaya yanzune safiyar?.
Harararsa ya sulaiman yayi, ya ce, "amatsayinka na sabon ango wanda aka kaimar sabuwar amarya jiya baikamatama duk yau aganka awajeba, kai daganan harma sati d'aya.
Hummm Yaya kenan, amma yanada k'yau nazo naga jikin yarinyarnan, kagafa tunda aka fara bikinnan bana samun damar zuwa.
To aii yanzu kaganta saika koma.
Yay...... Hannu ya sulaiman yad'aga masa alamar baya buk'atar jin komai.
Bayanda zaiyi haka yaymasa sallama yatafi.
Indai tak'aicemuku bayani yau tsawon kwanan amarya takwas bata saka angonta a idoba, sadai taji motsin shigowarsa da fitarsa, ko motsin cin abinci, kulum tana d'aki, inkaga tafito wani Abu zata d'auaka shima saita daidaici baya falon.
Aganinta shine yakamata yajata ajiki ya sake mata, tunda shine mai gidan, ita yanzu tamkar bak'uwa take agidan.
Shikam yana ganin ita yakamata taringa masa abinda zai sake mata d'in Dan da wannan halin Ni'ima tai saurin cafe zuciyarsa har yake ganin tafi sauran mata............
To masu karatu kuyi hak'uri da wannan yau naje anguwane, Marak'isiyya ta mannamin aiki tagudu.
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S)))......2017._*
[11/12, 2:21 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
*_wannan page d'in nakine miss xoxona, inafata kinyi sallah lfy?, ALLAH ya maimaita mana._*
_Luv u wujiga wujiga_😂❣.
2⃣9⃣=3⃣0⃣
Kwance take akan had'ad'd'en gadonta Wanda yaji shimfid'u na alfarma, tajuya kwanciyarta zuwa rigingine, idanunta suka sauna kan agogon dake manne a bangon d'akin 3:42am.
Ta waro manyan idanunta Dan mamakin yanda lokaci yatafi, afili tafurta kai kenen na kwana banyi barciba?.
Taja dogon tsaki da k'arfi, dama da gsk ne idan mutum ya ce, "yakwana baiyi barciba?, gsky itakam tana k'aunar iyayenta, tanaso kuma tayimusu biyayya, saidai tunkan ayi nisa tafara hangen tarin matsaloli a rayuwar auren nata. Domin kuwa alissafinta yau kwana takwas da kawota gidannan, saidai tundaga randa aka kawota gidan bata sake saka angon nataba a idonta, saidai taji motsin shigiwarsa dakuma fitarsa, kocin abincinsa, idan tatuna kulawar dayayta bata awajen taron bikin saitaita mamaki wlhy, mutum tamkar mai aljanu, kodayake saitaga kamar itama akwai laifinta, tunda ad'aki take wuni, saidai idan taji yunwa tadameta tafita tad'ebo abincin da Ammi ta aiko musu, gidan kansa takasa nutsuwa taimasa kallon tsaf........
Kwala kiran sallar asubane yadawo da ita hayyacinta, tamik'e domin gabatar da sallar, jitayi jikinta duk yayi nauyi saida tayi wanka sannan ta d'auro alwala.
Tana idar da sallah taji wani irin barci na d'ibarta, tashitai ta haye gado ta kwanta, cikin 'yan mintuna barci yay gaba da ita.
A6angaren bobo kam yamaida dukkan hankalinsa wajen binciko Wanda yayma yarinyarnan fad'e, sukansu 'yansandan dukya addabesu da masifar basusan aikinsuba, sanin shi d'an babban mutumne yasasu dagewa sosai kuma ana hangen nasara zuwa yanzu.
Rahma kam yana buk'atar ganinta amma aganinsa ita yakamata tafara nemansa tunda shine babban, ganin kamar tana shamasa k'amshi shiyyasa yafita harkarta ya maida hankalinsa akan aiki.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Sai k'arfe d'aya Rahma ta tashi, takai dubanta kan agogo, kai harnakai haka ina barci?, lallai nasha barci sosai.
Wanka tashiga, bayan tafito tashirya cikin Riga da siket na atanfa kayan sun bala'in mata k'yau, tayi sallar azhur sannan tanufo kicin Dan cikinta yafara kiran ciroma, gashi jiya tacema Ammi adaina kawo musu abinci zata cigaba da girkawa, Dan aganinta yakamata tamik'e wajen juya akalar mijinta zuwa gareta.
Alokacin Bobo yana gidansu, Nawal tamak'ale masa saita biyoshi yakawota wajen momynta.
Ammi ta ce, "Mukarram inaga katafi da ita kawai nasan insha ALLAHU Rahma zata rik'eta da Amana, kasan yarinyarnan kullum burinta ta kasance da mamanta akullum.
Bobo yahad'iye yawu Ammi ba tafiya da Nawal bane matsalar ina ganin kamar idan nad'auketa ban k'yauta mukuba.
Ammi tayi murmushi Wlhy ko d'aya mukarram aii munsan ba k'waceta kayiba, dama tunjiya Appanku yay maganar yau idan kazo kawuce da ita.
To shikenan Ammi ngd, ahad'a mata kayanta to muwuce.
Ammi tahad'o mata kayanta, wasu kam sai ahankali aringa kaimata.
Nawal kam sai murna take yau zata wajen momynta.
Ammi bari mutafi naga Appa haryau bai dawoba, gobe idan ALLAH yakaimu ma had'u, Dan zan koma aiki.
Ammi ta ce, tom ALLAH yatsare, yakaimu lfy, tazo gefen Nawal tana d'aga mata hannu.
Bobo yatada mota, yauwa Ammi idansu khairy sun dawo suhad'amin kayana duka Nima.
To zan Sanar musu agaidamin da d'iyar tawa.
" zataji."
Haka suka fice ammi da Nawal suna d'agama juna hannu.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Rahma na zaune a falo tazurama filet d'in indome idanu, dukda 'Yar Karen yunwar datakeji amma abincin yagagara ciyuwa agurinta.
Tabi falon da kallo, caraf idanunta suka sauka akan wani hoton Bobo yana zaune akan wata kujera, fuskarsa d'auke da tsadadden murmushi mai kashe zuciya, saina kusadashi shida Nawal, wanikuma a can gefe shida yayyensa maza dasu Ammi da khursiyya da khairiyya, sunyi k'yau sosai, daka gansu Kasan ciki d'aya suka fito masha ALLAH....
DA gudu Nawal tashigo tana kiran Momy! momy!!, da Sauri Rahma tamik'e Nawal tafad'a jikinta, itama saita rungumeta.
Ahankali Nawal ta ce, momy I miss u.
Miss u too my baby Rahma tafad'a tana mamakin 'Yar waye kuma wannan?.
Nawal takatse mata tunani da fad'in , momy inakikaje kika barni?, kullum saina tambayi baby da Ammi sai sucemin kina zuwa amma baki zoba.
Cikin mamaki Rahma tad'agota daga jikinta tana kallonta, gata 'Yar mitsila sai zance irin na manya.
Bobo na a tsaye yana kallonsu, Wanda azahiri kallonsa akan Rahmane, Ashe k'yan dayake kallonta dashi awajen taron biki tafi k'yau a Natural batareda kwalliyaba..... Maganar Rahmace takatse masa tunani, ta kuma rungume Nawal tana fad'in tom gani nadawo babyna kiyi hak'uri kinji.
Ita sai yanzu tatuna ance mata Bobo yanada d'iyama, jitayi tausayin yarinyar ya mamayeta, ALLAH sarki Rayuwa, ALLAH baya Barin wani Dan wani yaji dad'i, tafad'a acikin ranta.
Nawal tazare jikinta tanufi Inda Bobo yake, hannunsa takamo cike da murna tana fad'in baby naga momyna yau.
d'an murmushi yayi ya ce, "natayaki murna babyna, karasowa cikin falon sukai yazauna.
Rahma ta daure ta ce, ina yini?.
Lfy ya amsa batareda ya kalletaba.
Rahma ta ta6e baki aranta ta CE, " dama baka amsaba aii, dama na gaidakaine saboda kana gaba dani.
Maganar Nawal ce tasakata dawo da hankalinta Kansu, Nawal ce takai bakinta Kusada kunnen Bobo wai zata masa Rad'a, amma kuma kanajin maganar tata.
"Baby mikayima momy tak'icin abinci?, koka duketane?.
Da sauri Bobo ya kalli Nawal a'a baby ban daketaba, k'ila batada lfyane.
Tamaido dubanta kan Rahma, momy waibakida lfy inji baby.
Rahma tayi d'an murmushi A'a lfy ta k'alau, to momy idan lafiyarki k'alau miyasa bakici abinciba?, ko kinaso baby yabaki dakansane?......
Kafin Rahma tayi magana Nawal tamaida dubanta ga Bobo, baby kabama momyna abinci abaki kamar yanda kake bani idan nak'ici.
Bobo ya ce, "to baby idan banda abinki....... Da Sauri ta ce, "baby indai baka bama momyna abinci abakiba mun 6ata daga yau, ta tashi daga kusadashi takoma kan cinyar Rahma data daskare azaune danjin furicin Nawal.
Rahma tadaure ta ce, ''kinga babyna zanci dakaina, Dan lfy ta k'alau, kibar Dady yahuta kinga ya gaji ko, tashima muci tare.
Nawal ta tashi zaune, Rahma taringa bata abincin itama tana dannawa badan yaymata dad'iba, saboda damuwar dataima zuciyarta yawa.
Bobo yanad'an satar kallonsu, tabbas yaji dad'in yanda Rahma takar6i d'iyar tasa wadda akullum yake zullumin sama mata madadin mamanta data rasa......
Yanata tunaninsa harsuka mammala, Nawal ma tafara barci, mik'ewa Rahma tayi da ita zuwa d'aki, dama zaman dukya gundireta.
Yabita da kallo k'asa k'asa babu laifi tanada k'yau daga na fuska harna jiki, saidai bazai sotaba Dan Ni'imarsace kawai keda gurbin zama azuciyarsa.
"na ce, "hummmm ALLAH yasa."
Itakam Rahma koda takwantar da Nawal saitayi zamanta bata sake fitiwaba, sai bayan sallar la'asar.
Sannan baya falon, tanufi kicin tana fad'in baridai yau nayi girki kodan Nawal, had'ad'd'en abinci na gargajiya tahad'a mairai da lfy, tagyara kicind'in tsaf kamar ba'ayi komaiba, hakama falon takuma bad'e ko ina da nau'in turarurrukan wuta.
Saida tayi Sallar magriba sannan tayi wanka tayima Nawal, shiri tayi cikin wando dariga na Pakistan sky blue, rigan iya cinya sai wandon yakamata sosai, amma tayi k'yau kamar kasaceta kagudu, itama Nawal tasaka mata 'Yar Riga Mara nauyi.
Harzasu fito Nawal ta ce, "saita goyata, Rahma taduk'a Nawal tad'ane.
Falon suka fito inda ta tarar da Bobo zaune akan kujera mai d'aya ya d'ora k'afafunsa saman k'aramin tebir na gilas yana karanta jarida, gefensa lemo na kwali da Kofi anzuba rabi, yana sanye da wando 3/½ fari da riga ja Mara hannu.
Masha ALLAHU Rahma tafad'a azuciyarta.
Baby kalleni Nawal tafad'a tana d'agama Bobo hannu.
d'an d'agowa yayi ya ce, " naganki baby yamaida Kansa.
Rahma tasauketa tana fad'in tonima gobe saikimin goyon.
Nawal tawaro idanu waje kamar wata babba, lah momy bazan iyaba saidai baby yay miki, taje tadafa bobo, baby.
Ya ce, "na'am.
Zaka ramama momy goyon data minko?, kagani ban girmaba, bazan iyaba..
Bobo yakalli Rahma dake zaune tana mamakin wayau da surutu irinna Nawal, Dan yau d'aya tafahimci Nawal d'in tanada shegen wayau irinna sai antona d'innan ake samun irinsu.
Ahankali ya janye idonsa yamaida kan Nawal eh zan rama miki.
Tanufo Rahma tana murna, momy taso baby yagoyaki kinji.
Rahma tayi murmushi k'arfin hali a'a babyna nayafe basai yagoyaniba, kinga muje kici abinci, tafad'i hakane Dan mantar da Nawal wancen zancen.
Ta kalli Bobo daya maida hankalinsa kan karatun jarida ta ce, "ga abinci dady.
d'agowa yay yana kallonta danjin takirasa da daddy, itakam tai k'asa da kanta, takirasa da dadyne Dan batasan yazatace masaba, kuma baikamata takira sunansa kai tsayeba.
d'an lumshe idanunsa yayi yana wani guntun murmushi, tabashi dariya wlhy, amma saiya dake, wai dady yakuma maimaita sunan azuciyarsa.
Haka yamik'e yanufi dinning d'in.
Tuwon shinkafane miyar Agusi wadda yaji busashshen Kofi da nama sai tashin k'amshi takeyi, saikuma lemon ayaba Wanda yaji had'i na musamman.
Aransa ya ce, " ya akai tasan abincin danafi so ko Ammice tasanar da ita?.
Itadai Rahma tazuba masa komai tatura gabansa.
Tayi mamakin yanda yaci abincin sosai, Dan ita tayi tunanin zaice bayacin tuwo, tunda taga d'an hutune.
Bobokam abincinnan yaymasa dad'i jiyayi Rahma tak'ara girmaba a idonsa, taburgeshi sosai gata yarinya k'arama amma ta iya girki mai dad'i.
Bayan sun kammala suka dawo falo..........
*_saidafa nace kuyi hak'uri dani, Dan wlhy akwai buk d'in danayi niyyar fara posting ba wannanba, amma babu yanda zanyi Marak'isiyya tafara wannan, naga kuma bai dace nabarshi ban k'arasa mukuba, randa nake da ishashshen lokaci zakuringa ganin 2page Dan inaso nakammala nafara wancan, randa kuma nake busy zakuga 1 kawai._*
_Bak'in Haure shine buk d'in dazan fitar muku Wanda zai fita akark'ashin wata k'ungiya dana sanar daku abaya, ina buk'atar addu'arku, ngd sosai da k'auna, ina k'aunar masoyana aduk inda kuke._
*_Luv u oll my fan's_*
*_(((S))).........2017_*
[11/12, 2:22 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
3⃣1⃣=3⃣2⃣
*_SAFNA_*
Tun bayan biki 'yan gidan suka fita harkarta gabad'aya, gaisuwarta kawai suke amsawa, itama aciki cikin.
Itako hakan bai dametaba Dan ta ce, "sagaji su sakkone tunda itaidai ALLAH ya tsallakar da ita daga auren dolen da akayi nufin k'ak'aba mata, to duk abinda zasu suyi tayi daga baya kenan.
Yau tana school, zaune suke itada k'awayenta zeenat da Baseera, hirarsu suke hankali kwance sunata shek'a dariyar shak'iyanci ga wani d'alibi bai suna Rabi'u, yayi wani dressing ne waishi adole babban yaro, yazo gurunsu yana fafa sukuma sai famfashi suke suna masa dariyar shak'iyanci.
*boy ne yak'araso wajen, tunda Safna ta hangoshi tafara washe Baki, ta ce, R.. Boy kaga k'ara gaba sai anjima mun had'u.
Sanin halin rashin mutuncin safna yasa Rabi'u barin wajen.
A'a *boy yayane?, incedai akwai labari mai dad'i?.
Aiko akwai labari mai dad'i saidai........
Saidai me?, kai dad'ina dakai komai dad'in zance saika nemo abinda zai 6atashi, baseera tafad'a tana hura hanci, Dan halinsu d'aya da Safna, shiyyasa sukafi shiri.
Muzauna kabamu misha zeenat tafad'a cikeda shak'iyanci.
*boy yakalli zeenat, zee baby yanajiki tsit ne.
Zeenat tayamutse fuska, babu Marsala kawai ina mamakin k'awatane yanda tarud'e akan wanj, saikace wata sakarai.
Harara safna ta watsa mata, indai bazaki dad'i alkairiba to kiyi shiru, Dan indai bansamu guy d'innanba to bak'in bakinkine yajamin.
Ido zeenat tazaro to ALLAH ya k'yauta yasa kisamu guy d'inki k'awata.
Baseera ta ce, "yanzu kikayi magana *boy jamuje.
*boy yagyara zama ya ce, " guy d'inki sunansa Abdulmalik Aliyu Abdulmalik, amma ana kiransa da (BOBO), lauyane maizaman kansa, mai tausayin talaka da kwatar musu 'yancinsu, danshi kud'i ba matsalarsa bace.
*boy yafara bama su Safna cikakken tarihin bobo daga farko har k'arshe, har aurensa nafarko da mutuwar matarsa, da kuma d'iyarsa Nawal.
Safna tazaro ido waje, *boy yanada d'iyafa kace?.
*boy ya ce, "shiyyasa nace, " miki akwai Abu Mara dad'i alabarin, ayanzu danake gaya miki kwana goma kacal da aurensa......
Aure kuma!!!?. suka fad'a suduka arazane.
Jikin safna Yakama rawa, tamik'e arazane batareda sha'awar jin k'arshen labarinba.
Zeenat tarik'eta da sauri, safna ina kuma zaki?, hannunta tafusge cikin rawar murya ta ce, "gidan zanje.
Gida kuma?, munfa kusa shiga lecture.
Tsaki taja batareda tabata amsaba tayi gaba.
Zeenat ta ta6e Baki tana fad'in 'Yar wahala.
Cikin masifa Baseera ta ce, "dammi zakice mata 'Yar wahala?, soyayyafa ba k'arya baceba.
Nima aii bance k'arya bace, amma ta safna batada tsari, kuma kad'anmma tagani indai tak'amarta bijirema iyaye, ta tashi fuuuu tabar wajen.
*boy ya ce, "nifa kuji dani Basee, cikon kud'inafa".
kaga dan ALLAH kaje idan mun had'u agida zanbaka, itama ta tashi tabar wajen.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Rahma tare sukai kwanciyarsu itada Nawal, koba komai tasamu 'Yar tayon kwana da hira, barema harga ALLAH tanason Nawal, jiya kad'ai dasuka rayu tare taji son yarinyar sosai a zuciyarta, dawuri ta tashi ta had'a musu break, kasancewar su Nawal suna Hutu yanzu bata tada ita daga barciba saidai tagama komai na gyaran gidan.
Tana d'aki zatayi wanka Bobo yafito cikin shigar suit bak'ak'e hannunsa d'aukeda k'atuwar rigar lauyiyi, d'ayan hannun yarik'e da jakar aikinsa da hular lauyoyi, yau yanada shari'a k'arfe 9:30am.
Ganin babu kowa Afalon saidai yasha gyara sosai sai k'amshi ke tashi, yad'an lek'a d'akin Rahma batanan sai Nawal kad'ai kwance tana barci akan gado, ahankali yak'araso yaymata kiss akumatu sannan yafito, dinning yanufa Dan yanajin kwad'ayin k'aracin abinci Rahma ayauma.
Itakam tana bathroom tana shirin yin wanka taji k'amshinsa, takafar mukulli tad'an lek'o ta hangesa yanama Nawal kiss akumatu, a ranta ta ce ,"yau albarkacin d'iyarsa anshigo d'akina kenan?, dukda dai bai nemi inda nakeba tad'an ta6e baki.
Shikam yana gama lodama cikinsa abinnan mai dad'i dasaka kunnen maici mik'ewa yatashi tareda yin hamdala dasakama Rahma albarka, agurguje yafice Dan time yawuce sosai.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Ikon ALLAH ne kawai yakai Safna gida, tana shiga d'akinta tanufa Dan falo babu kowa tasan ummi tana barci k'ila.
Tafad'a kan gado jagwaf kamar wadda akacema Abba yamutu haka tashiga kuka rurus, saidai tayi mai isarta sannan tayi shiru danba mai lallashi, yauce rana tafarko dataji kewar Rahma, Dan dukda tsangwamarta datakeyi indai yarinyar taganta cikin damuwa ita take lallashinta da kwantar mata da hankali, amma yau tamata nisa.
Tacije le6enta tana k'ara zubda kwalla masu zafi, ta ce, ''nad'au alk'awarin kota halin k'ak'a saina auri guy d'inanan, kuma saina rabashi da matar tasa Dan bazanyi shearing d'insa dakowacce maceba, banta6a Neman Abu narasaba a duniyar nan, nasan kaima bazan rasakaba bobona.
Ban ta6a bin malamaiba ko bokaye, bammasan inda sukeba, amma awannan karon duk inda suke saina nemosu, kuma zan kashe konawane Dan in mallakeka mijina, wasu zafafan hawaye suka zubo mata, kuka takeyi sosai da zuba sambatu harma da sa6o.
( Na ce, "hummmmm safna kenan, duk d'an daya hana uwarsa barci tofa shima bazai yiba).
------------------------:::::::::::
Agidan Bobo kam Rahma da Nawal ne suke wasan 'Yar 6oye, Rahma tarufe ido da k'yalle Nawal kuma ta6uya Rahma na nemanta, Nawal ta ta6ata tana fad'in momy kin ganni, da Sauri Rahma tajuyo inda taji maganar Nawal.
Bobo yashigo da sallama wadda babu Wanda yajita, tsayawa yayi yana kallonsu cike da burgewa, Rahma dake laluben Nawal tak'aro inda yake tana laluben Nema, jitayi ta damk'i wani hannu mai laushi da santsi.
Da sauri tacire k'yallen data rufe fuska danjin Nawal tana tafa hannu tana dariya dafad'in shikenan baby zai goya momy.
Kallon ido cikin ido sukaima juna shida ita saikuma suka dawo da kallonsu kan Nawal.
Baby ka ajiye jaka ka goya momy kawai.
Da sauri Rahma ta ce, " nikam Nawal na yafe.
Nawal ta k'ya6e fuska tana fad'in um um nidai sai yayi miki goyon, saikitacewa kin yafe kullum kullum.
Kan Rahma ak'asa ta ce, "toki bari yahuta kinga yazu yadawo daga aiki, tajawota jikinta tana lallashi.
Bobo yawuce d'akinsa yana murmushin darun Nawal.
Bayan yayi wanka yafito sanye da wando iya guywa da Riga k'arama, Rahma tamik'e kanta ak'asa ta ce, " ga abincifa.
Baice mata komaiba yanufi dinning, itama baya ta take masa, bayan ya zauna tafara had'a masa komai, sai satar kallonta yake k'asa k'asa, tagama takoma falo taja Nawal suka koma tsakar gidan dansu sha iska.
Bayan kamar minti 30 suka dawo, sannan bobo ya kammala yanazaune da jaridar tasa ta fama.
Nawal ta ce, "yauwa baby tashi kagoya momyn to.
Da sauri Rahma tanufi d'aki dantaga rigimar Nawal bazata k'areba.
Bobo yajawo Nawal yad'ora kan cinyarsa, kinga babyna kibari zan goya momynki amma ba yauba, kinga yau nagaji, yak'are maganar da sumbatar kumatunta.
Nawal ta k'ya6e fuska ita adole bata yardaba.
Ganin zata takura masa, shikuma soyake yahuta saboda yagaji sosai, ya ce, "to tashi muje na goyata, tamik'e yarik'e mata hannu suka nufi d'akin Rahma.
Tana zaune bakin gado tana wasa da wani d'an babyn Nawal, suka shigo, ta d'ago kai tana kallonsu, suna had'a ido da bobo ta kauda idonta.
Nawal ta ce, " momy tashi baby yamiki goyonki.
Rahma tabud'e baki zatayi magana Bobo yad'aga mata hannu, karki damu yarinyar nan taki ba k'yalemu zatayiba inhar ba'ayi goyonnanba, Dan haka taso kawai nayi muhuta.
Da sauri Rahma takallesa danjin furicin bakinsa, yama za'ayi harta iya yarda ya goyata saikace wata yarinya.
Bata ankaraba taga ya tsugunna yana jiran tahau kenan.
Cikin sanyin murya ta ce, "Dan ALLAH kayi hak'uri bazan iyaba.
Juyowa yay yana kallonta fuska a d'aure, ya ce, "amma dai kinsan Nawal dashegen naci, indai ba goyonnan nayiba ba barina zatayi na hutaba, nikam natsani adameni da hayaniya.
Ganin yanda yake magana cikin fad'a amma hakan baihana muryarsa fita cikin nutsuwa da taushiba yasa dole tasakko daga gadon, amma tayi tsaye takasa hawa saboda tana matuk'ar jin kunyaarsa.
Momy kihau baby yana jiranki Nawal tafad'a tana kallonta.
Hararar da Bobo ya watso matace tasata saurin d'anewa bayansa.
Shikuma yamik'e yanufi falo da ita, Nawal nabiye dasu tana dariya.
Yajuyo yana kallon Nawal to nagama ko baby?.
Lah baby saikaje d'aki da'ita sau uku kana dawowa, haka yayta zarya daga falo zuwa d'aki harsau uku, ana ukunne yadireta saman doguwar kujera yana fad'in wash bayana, wlhy momyn Nawal kincika nauyi.
Rahma tayi k'asa dakai cike da kunya, yabata dariya wlhy, sai wani yatsine fuska yake da rik'e k'ugu tamkar zaiyi kuka, amma saita gimtse, wai yau itace namiji yagoya, da gudu tabar wajen tanufi bedroom.
Shikam dariyama tabashi Dan haka yad'an murmusa tareda zama saman kujerar, wani nishad'i na musamman yatsinci kansa aciki, yajingina kansa da kujera tareda lumshe fararen idanunsa yana cigaba dasakin lallausan murmushi.
Har aka kira sallar magriba yafita Rahma bata sake fitowaba, gani take bazatama iya had'a ido dashiba aii.
Saida akayi isha'i yashigo gidan dakayan kwalam da mak'ulashe, Rahma najin motsin dawowarsa ta tura Nawal itakam tayi kwanciyarta tak'i fita.
Nawal taje tafad'a jikinsa tana masa oyoyo, shima rungumeta yayi yana fad'in babyna kinyi sallah?.
Eh nayi nida momy, harta koyamin karatu.
Ya ce, "iye kaga 'Yar gatam momynta, ina momyn taki to?.
Tana d'aki wai zatayi barci, nikuma nazo wajenka nayi fira.
Murmushi yayi Dan yagano tanajin kunyane dankarsu had'u, ya ce, " jeki kiramin ita.
Da gudu tanufi d'akin, tafad'a saman Rahma dake kwance kan gado, momy kizo baby na kiranki.
Rahma tadafe kai banace kice masa ina barciba?, kuma daga yau kiringa cemasa dady ba beby ba kinji babyna.
To momy zandinga fad'a tashi muje to.
Badan Rahma tasoba tasakko suka nufi falo itada Nawal.
Yana zaune idonsa akan Tv yana kallon labarai ta ce, "sannu da dawowa.
Yauwa yafad'a batareda ya kalletaba, ya ce, "ga wannan yamik'a mata ledan kayan motsa bakin.
ALLAH yasaka da alkairi tafad'a tana kar6a, kicin tanufa itada Nawal suka juyo afilat, wad'anda bazasu ciyuba tasaka afirij.
Takawo masa nasa itakuma tad'auki nasu danufi sutafi d'akinta suci, ya ce, " ina zakuje kuma?.
Kanta ak'asa ta ce, "d'aki.
sabodani zakuje d'aki cin abinci?.
Dawowa tayi tazauna batareda tabashi amsaba, saidai akunyace takeci, shikuma yana satar kallonta har suka gama tashige d'aki tabarsu shida 'yarshi.
Shirin barci tayi tai kwanciyarta, dama kayan barcine ajikin Nawal.
Yana gama kallon labarai shima yamik'e da Nawal ajikinsa datai barci, yakashe komai sannan yanufu d'akin Rahma.
Ahankali yasauke Nawal akusada ita, yay musu addu'a sannan yaja bargo yarufesu idonsa akan Rahma, yanda take barci hankali kwance sai fuskarta tayi wani wasai.
Jiki asanyaye yanufi d'akinsa yay shirin barci shima yakwanta...............
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S)))........2017_*
[11/12, 2:24 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
3⃣3⃣=3⃣4⃣
"K!, ina zakije da sassafennan?.
Safna ta kwa6e fuska, ummi munafa da Lectures k'arfe 7:30am kuma malamin baida kirki wlhy, gashi ya CE, " test zai mana, tak'are maganar da turo baki gaba.
Ummi ta ta6e Baki, ta ce, " shikenan jeki, amma idan kin dawo inason magana dake nida mahaifinku.
Gaban safna yafad'i ta ce, "ummi magana kuma?, tami to?.
" idan kindawo k'yaji, Dan inama son aikenki gidan Rahma.
Kai ummi gidan Rahma fa kikace?, saikace wata k'anwarta.
To tunda tarigaki aure aikin zama k'anwar tata aii, ko kina nufin dankince bak'yason mijinta bazakije gidantaba?.
Nifa Bahaka nake nufiba ummi, kawai INA dai ganin da kunya.
Harara ummi tasakar mata, o sai yanzu kika San kunyar?, alokacin dakikai shirin wulak'antamu kin manta da kunyar.
Nidai ummi ALLAH yabaki hak'u, ALLAH fa yariga yarubuta itace matarsa kawai, amma ni ban wulak'antakuba, kawai ina gudun kar asakamin kaina atunkunya ne, saina dawo, tayi saurin ficewa, Dan batason jin amsar ummi, tasan halinta sarai, yanzu saita hau sama ta 6ata mata shirinta, itako awannan lokacin bata fatan abinda zai hanata fita.
Ran ummi yak'ara 6aci, duk cikin 'yayanta babu Mara kunyar irin Safna, ita bata iya tauna magana ga mahaifaba, ta maidasu tamkar wasu k'awayenta, kodan gatan dasuka nuna matane abaya?.
Tana fita taci karo da Baseera ak'ofar gida.
A'a kice kina nan?, dafa shirin shiga gidanku nakeyi, to waima inbanda iskanci miye natsayawa anan?, gidan bak'onkine?.
Baseera tarufe murfin motar tana fad'in Bahaka baneba, banason nashiga mu 6ata lokacine kawai.
Dariya safna tayi, haba k'awata aganinki zan 6ata lokacine?, kenifa k'agara nayi gari ya waye, yanzun haka jinake tamkar nayi tsuntsuwa na ganni agaban malaminnan.
Baseera ta tuntsure da dariya kai k'awata kemafa bakida dama akan abinda kikeso, lallai guy d'innan yayi babbar sata.
Safna tak'ara dafe sitiyarin motar, ai wlhy Basee guy d'innan ba k'aramar sata yayiminba, wlhy gaba d'aya ya haukatani, saidai idan natuno kafinni harya zauna da mata biyu nakanji raina ya 6aci, badan ina sonsaba sosai da watsar dashi zanyi.
Shiyyasa Nima na d'auki alk'awarin saina mallakesa amatsayin miji kota halin k'ak'a, ke namiki mai kankat wlhy har yarinyarsa saina rabashi da ita, Dan dagani sai 'ya'yana nakeso mu zauna dashi.
Hummm 'yammata ace insha ALLAHU dai.
Safna ta gallama baseera harara, to aii dama komai insha ALLAHU ne, koko insha Baseera ne?.
A'a Dan ALLAH karki mana sa6o mudai kisa akifar damu, kefa wani lokacin kamar bakiyi islamiyyaba haka kike.
Banza Safna tai mata, Dan idan tabiye mata fad'a zasuyi, itakam lalla6ata takeyi tasamu arakata gun malami.
Sun isa gidan malam amma da mutane, Dan haka suka jira a mota.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*
Bobo a police tetion yasaka 'yan sanda gaba sai masifa yake musu, wai basu san aikinsuba.
Haba Dan ALLAH wai mikuka maida kankune?, yau sati nawa ace angagara nemo mai laifi, hanyafa mai sauk'ine gano koma wane d'an iskane, saboda anbaku no. d'in motarsa, wlhy nabaku nanda gobe idan ALLAH yakaimu inhar baku zomin da mai lafinnanba zan d'au mataki, Dan saina saka anta6a aikinku, tunda bakusan abinda kukeyiba...
Sudai 'yan sanda cikinsu ya d'uri ruwa Dan sunsan kowaye Abdulmaleek, tunda bayau yafara d'ora su akan aikiba.
Tsaki yaja yafice, afusace yashiga mota yafigeta.
Yayi nisa atafiyarsa sai masifa yakeyi shikad'ai amota, tamkar zai ari baki.
Wani haushine yak'ara turnik'eshi Dan ganin wani banzan Go slow mara dalili, kamar ance ya waiga idonsa yasauka akan number motar guy d'in dasuke nema.
Jikinsa har rawa yake yad'auki waya yakira 'yansanda, saidai yana yanke wayar ana sakin Go slow d'in, da hanzari yatakema motar baya, binsa yake cikin dabara har zuwa wani kantamemen gida, ya sauke numfashi afili ya ce, "gidan Alh Sunusi Dala kuma?, kenan wannan motar tanada alak'a da gidan?.
Wayarsa ya d'auka dake wringing 'yan sandane suke tambayarsa yana ina?.
Kusameni gidan Alh Sunusi dala.
Kansa ya kwantar jikin kujera, saiyanzu yagane abinda yasa 'yansandan suka kasa kama mai laifin, tabbas sunsan yanada alak'a da wannan gidan.......
Tunaninsane yatsaya alokacin da motar 'yan sandar ta iso, bai fitoba amma yabud'e murfin motar.
'Yan sanda biyu suka k'araso inda yake, fuska ad'aure yakallesu, nan gidan motar nan tashiga, Dan haka saikuyi aikinku.
Cikin d'an sanda d'aya yabada wani k'ululu, baki narawa sukace nan gidan kuma?.
Cikin daka tsawa ya ce, "e nan gidan, dama nasan kunsan Wanda ya aikata, amma kwad'ayi irin naku yasa kuka kasa d'aukar mataki, to yanzu saiku za6a, kamashi kokuma asarar aikinku......
Kafin yarufe baki sunnufi k'ofar gate d'in gidan, dak'yar maigadi yabarsu suka shiga.
Daidai nan Haneef yafito cikin sabuwar shiga danufin sake fita, harya fara k'ok'arin bud'e mota yadakata Dan ganin 'yan sanda.
K'arasowa sukayi har inda yake tsaye, sallama sukai masa, ko amsasu baiyiba, saima kallon banza dayake bisu dashi.
d'an sanda ya had'iyi wani yawu sannan ya ce, " yalla6ai u onder arrest.
Me!, Haneeff yafad'a cikeda rainin hankali, yacigaba da fad'in Ku harkunkai matsayin dazaku shigo cikin gidanmu kuce kunzo kamani?, toma awane dalili?.
Kayi hak'uri yalla6ai zamu maka bayani idan munje can, Dan duk abinda kafad'a anan zai iya zama hujja agareka a kotu.
Kan uba...... Saikuma yay shiru yakasa k'arasawa, yaja numfashi kumuje zan biku abaya, yayi hakane danya kafa musu tarko.
A'a kamuje kawai aiiba dad'ewa zakayiba.... Maganar Bobo tadaki kunnuwansu.
Kai kuma awa?, haneef yafad'a yana kallon Bobo.
Karka damu da matsayina, kaidai kadamu da kanka kawai my friend.
Cikin 6acin rai Haneef ya ce, "kadai iya bakinka k'aramin k'waro.
Wata banzar dariyar rainin hankali Bobo yasaki, wadda zan iya cemuku yauce rana tafarko danaga dariyarsa, ya kalli 'yan sandan ya ce, mikuke jira?, yana gama fad'a yafice daga gidan.
Cikin 6acin rai haneef ya ce, "kumuje to, ammafa yak'udiri aniyar wulak'anta d'an saurayinnan da 'yan barandarsa.
Haneef yashiga motar 'yan sanda, bobo kuma yashiga motarsa.
'Yan unguwar sai dad'i sukeji da ganin Haneef amotar 'yan sanda, yayinda agefe kuma tuni magulmata sunkira Alh Sunusi sunkai masa rahoton kama Haneef da 'yan sanda sukayi yanzu.
Hankalinsa atashe yabaro office yanufo gida.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Suna nan zaune har layi yazo kansu, sannan suka shiga.
Bayan sun gaisa da malam da'u safna ta ce, "malam......
Da sauri yad'aga mata hannu karkice komai, tunkafin kizo sud'an tsito sun sanar dani komai.
Kin kamu da son wani saurayi, kinkumasa ayimiki bincike akansa, yanada mata ba'a dad'e dayin aurenba, kuma yata6a aure matar tamutu harda 'ya atsakaninsu, koba hakaba?.
Cikin mamaki da rawar jiki Safna ta ce, " to amma ALLAH ya gafarta malam ta INA kasan wannan?.
Malam da'u yatuntsure da dariya, kai yaro yarone dai, kedai fad'i buk'atarki kawai 'yammata kiga aiki da cikawa.
Cikin tsoro Safna ta ce, "malam dama inaso shi wannan saurayin yazo dakansa gidanmu ya ce, " yana sona, kuma yasaki matarsa Dan wlhy inada kishi sosai malam, kuma inason sa sosai har inaji idan ban sameshiba zan iya mutuwa wlhy, Dan ALLAH malam ataimaka mini.
Malam da'u ya ce, "babbam taimako aljihunki 'yammata.
Baseera da dama tasaba indai bin malamine, hankalinta kwance ta ce, " malam kaima Kasan kud'i ba matsalarmu bace aii, inhar buk'ata zata biya to kad'auka kasamu kud'i konawane.
Malam da'u ya wangale bakinsa dake cike da damzar goro, wasu hak'oranma sun fita, ya ce, "baseera indai kece aii saidai nafad'ama wani, Dan haka kisanar da k'awarki tagama samun abin sonta.
Wani faranti yajawo dake cike da k'asa, yafara Zane Zane yana motsa baki, bayan yagama yamaida kallonsa Kansu, kince ya sunansa?.
Safna ta CE, " nidai bobo nasani, amma Wanda nasaka yamin bincike akansa ya ce, "Abdulmaleek.
Malam da'u yakuma maida kansa k'asa, shiru yayi Dan shikad'ai yasan miya gani, to ammafa yana fad'a mata gsky bazata sakar masa nairoriba, gata kallon d'aya zaka mata kagane kud'i sun jik'ata, Dan haka ya canja shawara, ya ce, " zaki gansa anan kusa kam, saidai bazan fad'a miki ranarba, sannan kuma saikun had'u zan fara aiki akansa, ga wannan yazama kwallinki, wannan kuma hoda.
Kar6a Safna tayi tai godiya.
50k suka ajiye masa suka tafi suna godiya.
Na ce, "hummmm.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Bobo har police tetion yaraka 'yan sanda, saida aka gark'ame Haneef Wanda tuntini hankalinsa yafara tashi, yaza'ai kamarshi d'an gata ace anakawoshi nan gurin?, gashi sun kar6e masa waya bare yakira dad nasa yasanar MASA halin dayake ciki.
Yad'au alk'awarin Indai yafita agurinnan saiya wulak'anta yan sandar nan da saurayin nan.
Saida yayama police d'in nanan gargad'i sosai akan wlhy kowaye yazo karsu bada belin Haneef, sannan yawuce yanufi office d'insa, yanason fara shirya yanda zasu shiga kotu.
+
Yaduk'ufa sosai wajen latsa lap-top, gaba d'aya hankalinsa yana wajen binciken family d'in Alh Sunusi Dala, da sauri yad'ago danjin an ta6ashi, jar uban nanan kai yafad'a cikin ihun farin ciki, rungume juna sukayi shida bak'on nasa.
Ammar yaushe a k'asar?.
Ammar yay dariya wlhy mutumin jiya da daddare, shiyyasa yau naimaka sakko amma natarar kafita.
Kabari kawai wlhy naje wajen yaranka ne sukamamin wani d'an iskan mutum.
Kai Bobo kana nandai baka canjaba?, yanzu kuma wa'aka kafama tarko ne?.
Wani murmushi bobo yasaki, kamar mai rad'a ya ce, d'a gurin Alh Sunusi Dala!.
Ammar yad'an zaro ido, Bobo Kasan kuwa sunanwa ka fad'amin?.
Kwarai kuwa nasani, ni kam ainafi kowa farincikin dawo warka wlhy, inason kaima yaranka magana su k'ara gark'ameminshi sosai, Dan ranar litinin nakeson mufara sharia.
Baka da damuwa da hakan abokina.
Yes sir!, Bobo yafad'a yana sarama Ammar.
Dariya ammar yayi yace d'an iska, ALLAH dai ya shiryaka, duk kabi katakurama 'ya'yan manyar garinnan, ina baby Nawal da amarya?.
Saida ya sauke numfashi sannan ya ce, "suna lfy.
Masha ALLAH, kasanar da amarya zanshigo weekend cin abincin amarci, daganan naga amaryar tamu, tunda ALLAH baisa ansha biki daniba.
ALLAH ya kawoka Bobo yafad'a.
Daga nana hirarsu suka cigaba dayi, dagani kasan sunyi bala'in shak'uwa da juna.
*Waye Ammar?.*
Ammar Khaleed Adam, d'ane ga Alh Khaleed Adam, abokin Appa na k'ut da k'ut wanda yayma Rahma k'yautar mota ranar walimar makaran tarsu, su 7 mahaifansu suka haifa, shine na biyar agidansu, yanada yayye maza da mata su hud'u, sai k'anne biyu mata, Ummy matar ya Hamza dakuma autarsu Lubna ita sa'ar su khairiyyace.
Tare sukayi karatu da Bobo tundaga primary har secondary, daganan kowa Yakama inda yafi wayau, Bobo yatafi karatun lauya, shikuma yafad'a aikin 'yan sanda, ayanzu haka shine Qumissioner of police na jihar kano, sun shak'u sosai da Bobo, bashida wani aboki sai Ammar da yayyensa.
Duk wani aiki da Bobo yarikito Wanda yake buk'atar tsaro to Ammar ne ke taimaka masa, yanzuma yayi wata 'Yar tafiyane ta wata biyu, shiyyasa baisamu damar halartar bikin Bobo ba.
Shima matarsa d'aya da yara biyu duk maza.
Wannan kenan.............
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S)))...........2017_*
[11/12, 2:25 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
3⃣5⃣=3⃣6⃣
Hankali tashe Alh sunusi ya iso gidansa, ko fakin bai bari direbansa yagamaba yafice.
Matarsa na zaune afalo itada k'annen Haneef d'in yafad'o ko sallama babu.
Arazane suka mik'e suna binsa da kallon mamaki, dukda ba yaune rana tafarko daya fara shigowa gida ahakaba.
Ina my son?, yafad'a aburkice.
Cikin mamaki haj Falmata ta ce, "Haneef?.
"Eh," ya bata amasa afusace.
Yanzu babu dad'ewa yafita aii, wani abune yafaru?.
Wata uwar harara yasakar mata, waike wace irin shashashar uwace?, wai kina nufin bakisan 'yan sanda sunzo har gidannan sun kamamin yaroba?.
Afirgice ta ce, "naga takaina ni Falmi, yaushe hakan tafaru?, yanzufa Haneef d'in yashigo gidannan ya sauya kaya yafita.
Bai sauraresuba yafice yabarsu cike da tashin hankali.
Abin kamar wasa Alh sunusi har dare yana Neman Station d'in da akakai Haneef amma babu ko Alamarsa, ransa yak'ara 6aci da harzuk'a, aiiko wlhy saiya d'auki mataki akan 'yan iskan police d'in dasukai k'arfin halin shigar masa gida harda kama masa tilon d'ansa namiji.
Gida Yakoma danufin zaije ga Qumissioner of police gobe idan ALLAH ya kaimu, saidai zuciyarsa namasa rad'ad'i idan yatuna Haneef zai kwana a Station yau.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
*_9:30pm_* ya isa gidansa duk agajiye, jinsa yake yau fes tunda ankama masa d'an iskan nan, bayan sun gaisa da mai gadi yashige cikin gidan.
Babu kowa afalon, har TV akashe yake ga gidan tsit kamar babu kowa, da alama masu gidan har sunyi barci.
K'ofar yamaida yarufe sannan yanufi d'akinsa, yazube kayan hannunsa cike da gajiya, babu 6ata lokaci yacire kayansa ya fad'a bayi domin yin wanka.
Bayan yafito yagabatar da shafa'i da wutiri, 'yan dube dube yafayi da alama akwai abinda yakeson gani, amma babu, d'an k'aramin tsaki yayi tareda mik'ewa yafice.
Cikin barci Rahma taji ana bubbugata, afirgice ta tashi, Dan dama tsorace takwanta, saboda rashin dawowar mai gidan.
Ganin shine atsaye yasa ta sauke ajiyar zuciya, ahankali ta ce, "sannu da zuwa.
Bai amsaba ya ce, " ina shayina?.
Tad'an dafe kanta, wlhy na manta ne.
Aii yanzu na tuna miki, yafad'a yana ficewa.
Asanyaye Rahma tasakko daga gadon, Dan barcin data fara yasa jikinta yin lakwas, haka ta k'arasa kicin tana jan k'aramin tsaki, idonta cike da barci tadafa masa shayin, tajuye akofi tareda yanka lemon tsami ta matsa aciki, tad'ora akan k'aramin tire tafice.
Ganin baya falo gabanta yafad'i, kenanfa d'akinsa zata kai masa?, tai shiru kamar mai nazari, zuciyarta ta ce, "kije kikai karya huce Rahma ki k'ara jama kanji wani laifin", tunda tazo gidan yauce rana tafarko dazata Shiga d'akinsa, Dan haka k'irjinta keta dukan uku uku, haka tadaure ta kwankwasa, saida tayi kusan Monti biyu sannan ya ce, " tashigo.
Ahankali ta tura k'ofar tashiga, wani k'amshi yadaki hancinta tashak'a talumshe idanunta, saikuma ta bud'e ta sauke akan Bobo dake zaune abakin gado yana latsa laptop, k'afarsa d'aya ak'asa d'ayar kuma ya tank'washeta a gadon, sanye yake da kayan barci ruwan ganye mai turuwa, tana mamakin yanda yakeson latsa laptop da karatun jarida.
Jin shiru bata ajiyeba, bakuma tayi maganaba yasashi d'agowa ya kalleta, shima baiyi maganaba saidai tura mata k'aramin tebir na gilas dayayi.
Ganin haka yasa itama tad'ora batareda ta ce, "k'alaba.
Bayan ta ajiye saikuma tayi tsaye takasa tafiya.
Yana danna laptop d'insa yana shan shayi, tsawon minti 7 ita batayi maganaba shikuma ya shareta yanata aikinsa, yakula bazatace komaiba, kuma akwai magana abakinta, Dan haka shi ya daure ya ajiye NASA shan k'amshin ya ce, " kinada matsalane?.
Kad'an ta kalleshi taga har yanzu idonsa nakan laptop d'in.
gyara tsayuwarta tayi, muryartan nan mai kasheshi ta daki kunnensa, dama sonake naji yau ko lfy Baka dawo da wuriba?.
Cak ya tsaya da abinda yakeyi, yad'ago fararen idanunsa ya sauke akanta, sanye take cikin dogon hijjabinta har k'asa, sa6anin d'azu daya Tatar da ita da kayan barci.
Ahankali yasauke ajiyar zuciya, koba komai yaji dad'in kulawarta agareshi, cikin miryarnan tasa ya ce, "babu wata Marsala aikine yamin yawa a office.
" okey saida safe."
Harta kai k'ofa yana binta da kallo, yadaure ya ce, "incedai babu wata damuwa daga babyn taki?.
Bata juyoba amma ta tsaya, Dan furucinsa na k'arshe yaymata dad'i, muryarta araunane ta ce, " a'a babu Marsala, saidai tata jiran dawowarka, harta gaji tayi barci..... Bata jira amsarsaba tafice.
Ajiyar zuciya ya sauke tareda lumshe idanunsa, zuwa wani lokaci ya bud'e idon, d'an murmushi naga yayi Wanda bansan da liliba, saikuma yacigaba da aikinsa yana shan shayi.
Itakam Rahma tana komawa d'aki tahaye gado ta kwanta abinta sai barci.
::::::::::••••••••••••:::::::::
Washe gari Rahma ta tashi kamar yanda tasaba ta had'a break fast da gyaran gida, taima Nawal wanka itama tayi, kwalliya sosai taima yarinyar tai tsaf da ita, Dama ga ruwan k'yau d'an Asali, kan baby Nawal yasha gyara Dan jiya da yamma Rahma tayi mata kalba, kasancewar yau juma'a.
Tana cikin saka mata janbaki yaturo k'ofar yashigo da sallama ciki ciki kamar Wanda akaima dole
Da sauri Nawal ta hantsilo daga kujerar madubi danta hango daddynta ta madubi, oyoyo papa na tafad'a cike da farinciki tana rungumesa, shima d'aukarta yayi yad'aga sama yana dad'in "I luv u my child," yasumbaci kumatunta.
Ta shagwa6e fuska, papa shine jiya kak'i ka dawo ko?, lah nadawo mana, saidai kinyi barci sannan kitanbayi momy kiji?.
Nawal takalli Rahma dake kallonsu cike da sha'awa, wai haka momy papa yadawo jiya?, kai Rahma tad'aga mata tana murmushin daya kusan narkar da Bobo atsaye, hakane babyna yadawo kina barci.
Nawal tasunbaci kumatun babanta da k'asunba ta kwanta luf tanata shek'in gara.
Shikam hankalinsa nakan Rahma yana mata wannan munafikin kallon NASA k'asa k'asa.
Talura dashi tsaf dan haka tatsargu, rissinawa tayi ta ce, "INA kwana?."
Lfy, yafad'a cike da basarwa shi adole ba ita yake kalloba.
Rahma ta d'an ta 6e baki, dukda ta fahimci salon amsa gaisuwarsa kenan...... Muryarsa ta katse mata tunani, kushirya idan mungama break gida zamu wuce, Dan duk juma'a a can kowa yake yini.
Ahankali ta jinjina kai kamar wata k'adan garuwa.
Shikam yajuya yafice da Nawal ahannu.
Itama fitowa tayi tahad'ama kowa abinci agabansa, hankalinsa kwance yakecin abinci shida d'iyarsa, amma Rahma duk atakure take, haka kullum take cin abin ci atakure, bakuma danwai bata saba da ahakan bane, saidai kawai nauyinsa datakeji, tunda agidansu gaba d'aya suke had'uwa suci abinci tuntana yarinya.
Tananan tana juya cokali haryagama shida Nawal, yad'auketa suka koma falo suna jiranta.
Ganin yatashi yasata sakin jiki taci abincinta sannan takwashe kayan taje ta d'auraye.
d'aki takoma tacanja shigarta cikin wani had'ad'd'en doguwar rigar shadda pink colour, kayan sunmata k'yau sosai, tasaka k'aton farin hijjabinta sannan tafito, babu kowa afalon, danhaka takashe komai na kayan wuta, gamawata keda wahala yafito shida Nawal daga d'akinsa, hannunsa rik'eda jakar aikinsa.
Kallo d'aya yaymata yad'aukekai, saidai har azuciyarsa yaji dad'in hijjabin data saka, yanason kamilar mace arayuwarsa, gaba yay suka bishi abaya.
Tashaya kulle k'ofar falon shikuma sukai gaba cikin mota shida Nawal.
Ganin Nawal abaya itama tabud'e bayan zata shiga, ahankali yay maganar tamkar mai ciwon baki.
"Halan ni direban kine?."
Cak tatsaya tafasa bud'ewa, kuma tak'i dawowa gaban.
Yakuma cewa kina 6atamin lokacifa, kuma wajen aiki zanje, jiki a sanyaye tabud'e gaban tashiga, shima baisake cewa komaiba yatada motar suka fice bayan sun gaisa da baba mai gadi.
Karatun Alkur'ani yasaka musu, cikin k'ira'ar shiek Abdurraham sudes, ahankali Rahma kebin karatun, yana kallonta ta gefen idonsa, jiyay tak'ara girma a idonsa.
Har sukaje gidan Appa babu Wanda yay magana, garama Nawal takanyi jefi2.
Saida yatsaya suka gaisa da baba mai gadi, yaymasa alkairi kamar yanda ya saba sannan yashige ciki.
Yana faka motar Nawal tafice da gudu zuwa cikin gidan, sukuma suka fito cikin nutsuwa, da gudu khairiyya da khursiyya suka fito, rungume Rahma sukayi suna farin cikin ganinta.
Ta ce, "aini nayi fushi, daga zuwa d'aya baku sakeba.
Kiyi hak'uri auntyn mu, Ammi ce ta ce, " mubari sai nan gaba.
Bobo yak'araso yana harararsu to maganannu ai kwabari kushiga gida dai ko?, yay gaba abinsa.
Khursiyya ta ta6e Baki, aifa yau munga banu jarabatu yazo, ALLAH yasa aiki zai wuce cewar Khairiyya.
Rahma najinsu dai tayi murmushi kawai.
Cikin gidan suka shiga, hakan tayi daidai da sakkowar Ammi daga saman Appa, Dan Nawal nazuwa canta haura.
Ta rungume Rahma tanamai jin dad'in ganinta, cike da kunya Rahma ta rissina ta gaida Ammi, ta amsa cikeda fara'a, da tambayarta ya zaman babudai wata Marsala ko?.
Kan Rahma ak'asa ta ce, "Ammi babu matsalar komai, to Alhmdllh d'iyata haka nakeson ji.
A'a mukarram d'ina lfy dai ko?, Ammi tafad'a tana kallon bobo dayay tsaye yana kallonsu tun d'azun.
yaturo baki gaba kamar wani yaro, yo Ammi sai yanzu kika san dani?.
Ammi taje takama hannunsa, o ni na isa namanta da babana, kawai ina murnar ganin d'iyatane.
Yakuma turo Baki, Toni bari nakoma tunda bak'ya murnar ganina, yanda yay maganar ashagwa6e yasa su khairiyya kwashewa da dariya.
Harara ya watsa musu suka bar wajen, itadai Rahma murmushi takeyi da mamakin Bobo, irin wannan shagwa6a haka kamar wani d'an shekara 5, anace mata tanada shagwa6a toga Wanda yatakata iyawa.
Ammi ta lallashesa suka haye sama domin gaida Appa.
Appa yaji dad'in ganinsu sosai, Dan haka yaymusu nasiha sosai sannan bobo yamik'e yaymusu sallama Dan wucewa aiki, saikuma antaso.
Yakalli Rahma k'asa k'asa ya ce, "saina dawo.
Kanta ak'asa ta ce, " ALLAH yatsare yabada sa'a.
Yaji dad'in addu'arta Dan dama ita yake son ji.
Ammi taji dad'in addu'ar da Rahma taima bobo, hakama Appa, suma sukai masa yatafi.
Zuwa 10:30 gidan yagama cika, aunty Rasheeda da 'yayanta, aunty Sameera ma da NATA, aunty ummy ma haka, mazan kuma suna ajiyesu suka wuce wajen aikinsu.
Dan danan gidan ya haukace da hayaniya, yaran duk suna falon sama wajen Appa, sukuma iyayen suna falon k'asa sunashan hira kamar wasu k'awaye, babu wannan shegiyar ak'idar ta kishin Sauri, hirarsu suke sosai, Dan danan Rahma tasaki jikinta dansu, su aunty Rasheeda akwai saurin shiga rai, gasu khursiyya iyayen shafta............
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S))).........2017_*
[11/12, 2:25 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
*_wannan shafin nakune sister's, Raheenat Mamoudou, billy ladan, Asmy b Aliyu, Aysha Umar Abubakar, Alkairin ALLAH yakai muku aduk inda kuke, ALLAH yabarmana zuminci._*
Luv u dayawa dayawa❤⛹🏻♀😂.
3⃣7⃣=3⃣8⃣
Safna da k'awayenta ne tafe, daka gansu kasan agajiye suke, fitowarsu kenan daga lectures.
Zeenat tasauke numfashi tana fad'in wayyoni ALLAH na yaukam munji jiki wlhy, hummm kema kike fad'a wani naji, cewar Baseera.
Safna dai batace komaiba, saima tsirama wani guri ido datayi, baseera ta zungureta Safna yadai?, mikike kallo hakane?.
Ajiyar zuciya ta sauke tareda kallon Zeenat, Zee Dan ALLAH kalli Sir Hamza sosai, baya miki kama da Bobo?.
Zeenat takalli ya Hamza dake k'ok'arin bud'e motarsa da takardu ahannunsa, Zeenat ta ce, "wlhy safna saifa yau nakula sosai, towaima miyasa bakita6a tambayarsaba?, tunda naga awajensa muka fara ganin Bobo.
Baseera ta ce, " kumafa hakane, ALLAH baita6a kawo mana wannan tunaninba.
Kunga dawannan surutun kumuje gunsa karya tafi to, cewar Safna.
Assalamu alaikum.
Wa'alaikummussalam, ya Hamza dake k'ok'arin shiga mota ya amsa tareda juyowa.
Gaidashi sukayi, ya amsa yana nazarinsu suduka.
Baseera mai ido atsakar ka ta ce, "sir Dan ALLAH munzo tambayar wanine agurinka?.
Tofa ALLAH yasa nasani.
Insha ALLAHU kasani, Dan ALLAH sir waye Bobo?.
Wani d'an murmushi ya Hamza yayi, ya ce, " miyasa kuke son sanin waye shi?.
Zeenat ta ce, "wlhy sir babu komai sai alkairi.
Motarsa yabud'e yashige, azatonsuma bazasu sami amsaba, amma bayan yazauna saiya kallesu, ya ce, " Bobo kanina ne uwa d'aya uba d'aya.
Wata sassanyar ajiyar zuciya Safna tasauke, jitake tamkar ansakata a aljanna, muryarta na Rawa ta ce, "sir Dan ALLAH kataimakamin da number sa mana.
Yay d'an Jimm sannan ya ce, " tom kid'anban zuwa Monday zan nemi izininsa tukunna, idan ya amince saina baki.
Dukda ba haka tasoba amma taji dad'i sosai, ta ce, "ngd sir ALLAH yakaimu lafiya.
Amin yafad'a yana rufe motarsa, sallama yamusu yabar wajen.
Safna ta ce, " guys insha ALLAH matsalata takusa k'arewa.
ALLAH yasa cewar Baseera da Zeenat.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Fitowarsa kenan daga wata shari'a, hannunsa d'auke da takardu da hularsa, sai kuma d'ayan hannun ya sak'alo k'atuwar rigarsu ta lauyoyi, ya k'arasa Inda Br Nazeefi yake sukayi musabaha, dashi suka kara yau, shi yana kare mai k'ara, Bobo kuma mai laifi, yanda suka gaisa cikin girmama juna da sakin fuska bazakace sune yanzu suka d'auki zafiba akotu ba.
Wayar bobo tafara ruri, hannu yasa cikin aljihun wandon jins d'insa ya d'aukko, Br Nazeefi yaymasa sallama, shikuma yafar'a k'ok'arin kiran Ammar Dan wayar ta katse.
Bayan sun gaisa dad'an tsokanar junansu, Ammar ya ce, "nakirakane na gumtsa maka labari, tund'azun nake Neman wayarka akashe.
Eh wlhy muna shari'ane, wane labari kasamo mana my Guy?, nasanka baka labarin banza.
Ammar yay dariya, mutuminkane yazo wajena d'azu a haukace.
Mutumina kuma wakenan?.
Alh Sunusi dala mana, ahargitse yazomin yanason Sanin Inda d'ansa yake, nikam namasa kwatance, bayan kamar awa d'aya saigashi yadawomin da kud'i wainasa asakar NASA d'ansa, Dan yasan kud'i nake buk'ata.
Na ce, " masa karya damu zuwa Monday zamukaisa kotu.
Hankali tashe ya ce, "wai akan mima aka kama masa d'a?.
Shine nace masa ana zarginsa dayima yarinya fad'e.
Indai tak'aice maka bayani yashiga zage zage wai sharri akaima d'ansa, wlhy saimunyi Dana Sanin kama masa yaro, harda cewa zaije yasamu dady yaji idan shine yasani naringama mutane rashin mutunci, kajimin mutumfa.
Dariya sosai bobo yakeyi, ya ce, " shashasha kawai, baimaga komaiba saiya wayi gari d'ansa a prison.
Ammar ma dariyar yakeyi, ya ce, "mutumina bakada dama wlhy.
Dariya sukayi gaba d'aya, sukai sallama bobo yashiga mota sai gida.
Gidansa Yakoma yay wanka, cikin wata d'anyar shadda blue yashiya, abinka da fari sai d'aukar ido yakeyi, yad'ora farar hula da farin takalmi, (araina nace kai guy d'innan fa yaci sunansa bobo gsky, ya iya d'aukar wanka babu k'arya), haka yafito yanata zabga k'amshi kamar Wanda yay 6arin turare, mota yashiga sai gidan Appa.
.*.*.*.*.*.*.*..*.*.*.*.*.
Sukam su Rahma bayam sungama shaftarsu kicin suka Shiga kamar yanda su aunty Sameera suka saba duk randa sukazo, sukeyin girki.
Yauma haka suka dafa abinci kala kala, Ammi sirikar arzik'i, mai d'aukar matan 'yayanta tamkar yayan ta, sai saka musu albarka takeyi.
'Yan aikin gidan suka gyara ko ina, akaima yaran wanka kafin iyayensu su k'araso, Dan tare zasuje masallaci, kowa aka shiryashi tsaf.
Sumadai iayayen wanka suka sakeyi.
Rahma takar6i kayan su khairiyya tasaka Dan bata d'akko wasu kaya dabanba, kayan summata k'yau sosai kamar Dan ita akayi, dama jiya suka kar6osu faga wajen tela.
Suna d'aki suna surutu harsu Bobo suka k'araso suka kwashi yaran sai masallaci, harda Appa amota d'aya suka fice, dama duk juma'a haka suke tafiya gwanin sha'awa.
Sun gama suka mik'e da niyyar fitowa falo Rahma tad'auki hijjab zata saka, aunty ummy tarik'e, haba amaryarmu abari ango yazo yaga kwalliyar mana, Rahma data duk'ar dakai ta ce, "Anty ummy plzzz kibarni.
Aunty Rasheeda takwace hijjabin ALLAH bazaki sakaba, sokike kima auta bak'in cikin kallon kwalliyar?, kunga kumuje, babu yanda zatayi haka tabiyosu.
Abinci suka shirya a tsakkiyar falon, bayan an shifid'a k'atuwar ledar cin abinci, sungama shirya komai aka manta da wani Abu, Rahma ta ce, " bara nad'akko.
Gaf taji tayi karo da mutum, da sauri tad'anja baya, tad'ago ta kallesa Bobo ne tsaye cikin gayunsa.
Maida kanta tayi k'asa Dan yaymata k'yau da kwarjini, kayi hak'uri ban ganiba.
Baice mata komaiba, saidai binta da kallo dayakeyi kamar yau yafara ganinta, kayan sunyi mugun mata k'yau da kama jikinta Dan siket da rigane, kuma tad'anfi su khursiyya jiki, ganin bai tankaba kuma yak'i bata hanya tawuce, ta ce, "sannunku da dawowa, zan wuce.
Nanma bai motsaba, wani haushi ya turnuk'e Rahma, saikawai tajuya zata koma, caraf ya damk'e hannunta, abirkice tajuyo tana kallonsa, ga maganarsu Appa tanaji dasuke tahowa.
Baki na rawa ta ce, " plzz gasu Appa nanfa...... Bata gama rufe bakiba suka k'araso wajen, ya Sulaiman ne agaba, sai ya Hamza abayansa, sai yara da Appa da ya ishaq abaya.
Ya sulaiman da ya Hamza suka kalli juna suna murmushi, tuni Rahma tayi k'asa da kai, jikinta harya fara d'an rawa, amma d'an bala'in naku yak'i sakinta.
Ya Hamza ya ce, "romeo d'anbamu hanya mudai.
Saiyanzu yadawo hayyacinsa, Dan ba k'aramin narkar dashi Rahma tayiba yau, yasaki hannun Rahma, aiko takwasa da gudu tai ciki.
Abin yabama Bobo dariya, Dan haka yay murmushin gefen Baki, karasowar su Appa yasa ya sulaiman yaja hannunsa sukayi ciki.
Sannu da zuwa da gaisuwa Matan nasu suka Shiga mik'owa, bayan sun Risina sun gaida Appa, Rahma tanacan bayan khursiyya tamak'ale kamar wata muna fuka.
Appa ya haura sama Dan rage kayan jikinsa.
Waimiya faru naga kin dawo baki d'akkoba?, cewar Aunty Sameera dake kusadasu Rahma.
Tad'an Sosa wuyanta, aunty harfa natafi naji maganarsu Appa nadawo.
Dariya aunty Rahma tayi, takira Taufiq babban d'an ya ishaq ta aikesa ya d'akko.
A can kuma ya Hamza ya kalli Bobo ya ce, " mutumina kafa fetsare soyayya har a gabammu.
d'an tsaki yaja Mara sauti, Yaya nifa bawata soyayya nakeba, bigenifa tayi.
Ya Sulaiman dake jinsu yay dariya, danta bigeka saika damk'e mata hannu kaki saki, kumafa kallon soyayya kake mata.
Shiru yayi bai tankaba, ya Hamza da ya Sulaiman suka shek'e da dariya.
Ya ishaq ya ce, "kukuma lfyarku?.
Bobo daya fara k'uluwa yamik'e daga tsakkiyarsu yana fad'in inafa sukaga lfy Yaya, Kusada ya ishaq yakoma yazauna, saiyayi fesin d'in Rahma sosai.
Ya Hamza ya ce, " habawa auta munfa gane wayonka na komawa nan saboda..... Basu k'arasaba suka kuma saka dariya.
Suma sauran duksai Kansu yakawo musu wuta, suka kalli Bobo suka kalli Rahma, sai kawai suma suka shek'e da dariyar, shimadai awannan karon ya murmusa, Dan wlhy baima kawo kamai aransaba yadai zaunane kawai saboda bayaso su ya Hamza sucigaba da takura masa.
Fitowar Ammi da Appa yasa suka tsagaita, Ammi ta ce, ''tomikuma yafaru?.
Ya Sulaiman ya ce, "ba komai Ammi, autanki ne zai mana gulma, yanaso yana kaiwa kasuwa.
Ammi da Appa sukayi murmushi dansun gane inda zancen yadosa.
Kubarmin babana yasha iskar marece, cewar Appa.
Yauwa Appa na fad'amusu, wlhy sun takuramin, Bobo yay maganar cikeda shagwa6a.
Shagwa6ar tasa tabama kowa dariya, harda yaran, shikam yasaki baki da hanci yana kallon Rahma dake tuntsura dariya sosai, baiyi tunanin tana dariyaba.
Tana d'agowa suka had'a ido saikawai ta gumtse dariyar tadaina.
Anty Rasheeda da Anty Sameera sukace kai ALLAH yayi magulmatan masoya awajennan.
Kowa yaga abinda yafaru tsakanin Bobo da Rahma Dan haka dariya hardasu Appa da Ammi, bayan an tsagaita Appa ya ce, " to ya isa haka, asauka aci abinci.
K'asa suka sakko sukaima falon zobe, ga abinci atsakkiya, Ammi tana kusada mijinta, sai yaran sun sakasu tsakkiya, dandanan kuma gidan yay tsit bakajin komai sai k'arar filet da cokali, kowa abinda yakeso yakeci, family's d'in Alh Aliyu hamshak'i yahad'u masha ALLAH.
Shida Ammi, 'Ya'ya shidda, surukai hud'u, jikoki goma cif.
Yaran ya ishaq, Taufiq, Sageer, Zainab, muhseen.
Yaran ya Sulaiman, Sumayya, mustapha, Jiddah.
Yaran ya Hamza, Ahmad, Kamal.
Sai Bobo, Nawal.
Bayan sun kammala cin abincin, 'yan aiki sukazo suka gyara ko'ina yakoma tsaf, yaran suka fice tsakar gida suna wasa.
Sukuma sunata hirarsu.
Duk juma'a haka suke zama, Appa yashige tsakkiyar iyalinsa asha fira, da karantar halayen dasuke ciki, babu ruwansa har matan 'ya'yansa 'ya'ya yad'aukesu.
Afirarne yake sanar dasu maganar kawo kud'in auren su khairiyya dukda su mazan duk sun sani, kowa yayi murna, dafatan ALLAH yasa akai da rai.
Kiran sallah la'asar ne yatadasu, mazan suka tafi masallaci sukuma sukayi agida.
Har dare suna nan, akasha shafta sosai, tuni Rahma tasaki jikinta acikinsu, hakan yayma kowa dad'i sosai.
Bayan isha'i sukaci abincin dare, kowa yakwashi matarsa da 'ya'yansa sai gida.
Rahma kam jitake kamar ayita zama ahaka, Dan taron yaymata dad'i sosai.
Kafin su Isa gida har Nawal tayi barci, Rahma tasa6eta sukayi ciki, shiya bud'e gidan suka shiga, kowa yanufi d'akinsa, babu maimagana saikace wasu kurame.
Dama anyima su Nawal wanka a can, sai kawai ta canja mata kayan barci, itama tashiga wanka, bayan tafito tayi abinda yadace, harzata kwanta tatuna da shayin oga.
Babu shiri tafito zuwa kichin, shayin tadafa takai masa, sallah ta tarar yanayi, Dan haka ta ajiye tafito abinta........
*_Happy juma'at Mubarak_*
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S))).......2017_*
[11/12, 2:51 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
3⃣9⃣=4⃣0⃣
_washe gari_
Rahma tatashi tayi duk abinda tasabayi dukda tasan yau weekend Bobo bazai fitaba, tana cikin saka turare a falo bobo yafito sanye da jallabiya ruwan toka mai gajeren hannu, rissinawa tayi ta gaidashi, kamar yanda yasaba ya amsa da lfy.
Amsa gaisuwar nan nabama Rahma haushi, amma babu yanda zatayi.
Yad'anbi falon da kallo komai tsaf, gawani k'amshi na musamman, yana jin dad'in kasancewarta mace mai tsafta.
Itadai cigaba tayi da abundan takeyi. Ya ce, "bari nad'anje wani waje nadawo.
Aranta tace kofa wanka bakayiba, amma afili ta ce, " to ga Break.
No barinaje nadawo, aiba dad'ewa zanyiba, yafad'a yana ficewa.
Itama ta ce, "ALLAH ya tsare.
Dukda yafita amma yajiyo addu'arta.
Bayan takammala saka turaren zuciyarta tabata shawara dataje ta gyara masa d'akinsa, kamar bazatajeba saikuma tatuna nasihar mahaifiyarta da ummansu Basma.
d'akin tanufa da tunanin ALLAH yasa bai rufeba, tana tura k'ofar tabud'e, k'amshinnan yana nan kamar kullum, yau tanutsu takalli ko ina na d'akin, komai farine tas, aranta tace farin Abu name tsaftane.
Sai manya manyan hotunanan Ni'ima Maman Nawal, bani gurin ita kad'a, wani gurin kuma shida ita.
Ko kad'an bataji haushiba bare kishinta, Bata 6ata lokaciba tafara gyara ko ina, Dan danan tagama d'akin yak'ara d'aukar haske komai yana d'aukar ido.
Bathroom tashiga zata wanke saitaga kaya ajik'e abokiti.
Shiru tayi tana tunanin ta wanke kota barmasa abinsa, wata zuciya ta ce, " ki wanke, kobabu komai zaki samu lada aii.
Haka tazauna tahau wankin gajerun wandunansa da vest, akunyace take wankin tamkar tana gabansa, gudu gudu sauri sauri tagama bataso yazo yataddata tanayi.
Dandanan tagama tawanke bayin, tad'auki kayan tafito waje, acan baya taje tashanyasu sannan tadawo d'akinta tashiga wanka, Dan Nawal bata tashiba.
Shigarta wanka babu dad'ewa yashigo gidan, d'akinsa yanufa kai tsaye, baki da hanci da ido yasaki yana kallon d'akin NASA, yalek'a bayi nanma fes, bokitin daya jik'a kaya wayam, wani lallausan murmushi yasaki, labulen window d'insa yad'aga, can yahango kayan ashanye.
Jiyay wani Abu nata6a zuciyarsa, afili ya ce, ''ALLAH yaymiki albarka.
Fitowa yayi yanufi d'akin Rahma, hakan yayi daidai da fitowarta daga wanka, daga ita sai guntun tawul iya cinya.
Wata tsayuwar sojan badakkare bobo yayi, sai Raba idanu yake akan Rahma, da wannan munafikin kallon nasa k'asa k'asa.
Itakam dukta rikice, waige waigen abinda zata rufe jikinta kawai takeyi, can ta hango hijjabin sallarta, amma dole saitabi tagabansa zata d'auka, ganin haka saikawai takoma cikin bayin da sauri.
Murmushi yayi tareda sauke ajiyar zuciya, yak'arasa inda hijjabin sallarta yake yad'auka, ahankali yak'arasa har k'ofar bayin ya kwankwasa, Rahma dake jingine da k'ofa tagwalo ido waje, k'irjinta sai dukan Tara Tara yakeyi.
Yak'ara kwankwasawa.
Muryarta narawa tamkar zatayi kuka tace yes, yanda tayi maganar tabashi dariya amma saiya gimtse ya ce, "bud'emin k'ofar.
Innnalillahi tace azuciyarta, wai mi mutumin nan yake nufi.........maganarsa ta katse mata tunani, " wai kobaki jinane?.
Bayan k'ofar takoma tala6e sannan tabud'e, gaba yay tamkar zai Shiga, saikuma yamik'a mata hijjabin, dasauri takar6a tamaida k'ofar burum tadatse.
Girgiza kai yayi yanad'an ta6e bakinsa, yazauna bakin gadon yana shafa kan Nawal daketa barcinta hankali kwance, shi mamakin kansama yakeyi, wai miyake jirane?, zuciyarsa ta ce, "kanason sake kallon Rahma ne.
d'an tsaki yaja yamik'e yafice, shi adole zuciyarsa tayi k'arya.
Saida taga yafita sannan tafito, taje tasakama k'ofar key, sannan tazauna tagyara jikinta, tasaka Riga da wando na Pakistan, nakula tana son irin kayannan sosai.
Nawal ta tashi itama tayimata wanka tashiryata cikin wandon Jin's da pink d'in T shert mai k'yau.
Falo suka fito, fitowarsu babu dad'ewa shima ogan yafito, haryayi wanka yashirya cikin jins blue da farar Riga sai zabga k'amshi yakeyi.
dinning suka nufa, Rahma sai sinne kai takeyi Dan kunya, shikam ko'a kwalar rigarsa, yanacin abinci Nawal namasa surutu, iyakarsa Yamata murmushi koya d'aga kai.
Rahma ta ce, " azuciyarta, muskili kafi mahaukaci ban haushi.
Suna kammalawa Nawal taja hannun Rahma wai suje tamata lilo, fitowa sukai sukabarsa kwance saman doguwar kujera yana kallon film.
Sunacan a lambu Rahma NATA biyema Nawal suna lilo, jiyay falon babu dad'i Dan haka yafito, jiyo dariyarsu alambu yasashi nufarcan, Rahma na zaune akan lilo, Nawal na shillata suna dariya, k'arasowarsa yasa Nawal cewa lah papa kaima zona lilaku.
Kai ya girgiza mata alamar A'a.
Takwa6e fuska zatayi kuka, cikin takun k'asaitarsa yak'arasa wajen lilo d'in, Rahma tayi yunk'urin sauka Nawal ta ce, "momy kubiyufa zanyimawa, sandarewa Rahma tayi azaune, kafin ta farga Bobo ya haye lilo d'in amma d'an nesa da ita.
Da k'arfi Nawal ta hankad'a lilo d'in, aiko sukayi gaba kamar zasu fad'i, da Sauri Rahma ta ruk'unk'ume Bobo, shima yarik'eta.
Nawal Yar kwal uba tacigaba da lila lilo da k'arfi, basuda za6i bayan rik'e junansu dak'yau, Nawal dai sai dariya takema iyayen nata, saida tagaji Dan kanta sannan tadaina lilasu.
Bobo yabud'e idanunsa ahankali danjin lilo ya tsaya, ga Rahma na mutsu2n kwace kanta, yana sakinta tasauka, da Sauri tabar wajen, binta da kallo yayi yana murmushi, Nawal takatse masa tunani, baby d'orani muyi tare tunda momy tagudu.
daukarta yayi yad'ora sukacigaba da lilonsu zuciyarsa cikeda tunani kala kala.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Safna zaune gaban Abba da ummi da alama fad'a ake mata, Dan fukarnan adagule take.
Abba ya ce, " wlhy nabakinan da wata uku zuwa hud'u kifito da miji a had'a aurenku keda amira, inbandama auren ameerar da sati biyu zan baki, amma Abubakarne yaceceki ya ce, "abari ahad'a bikin dan a samu sauk'i."
To saikiyi gaggawar sanar da Wanda kikace kinason harkikaso wulak'antamu akansa.
Insha ALLAHU Abba zan kawoshi, nidai kuyi hak'uri kubar ganin laifina, ALLAH yariga yarubuta Dama shid'in Mijin k'anwatane baniba...
Dallah yimana shiru!!, ummi takatseta atsawace, Mara mutunci kawai, Indai duniyace aigaki gata nan, kuma koyaya Wanda kikace kinason yake wlhy haka ZAMU aura miki shi, kijecan kiji da bak'in halinki, tashi kibamu waje mu.
Mik'ewa Safna tayi tabar falon tana k'unk'uni.
Na ce, " ALLAH ya shirya to.
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Ad'an hanzarce takeyin aikin gidan, Sauri take tagama dawuri taje tayi girki Dan maigidan ya ce, "mata yau abokinsa zaizo da iyalinsa, tagama komai tsaf har girkin ta kammala d'akin bobone kawai yarage mata shima Dan yana kwance ad'akinne.
Saiwajen 12 yafito daga d'akin yafita danufin siyo ruwa datace masa babu.
Yana fita tashiga d'akin Dan gyarawa, tagama aikinta lfy lau, tsautsayi yasa takai hannunta kan wani hoton Ni'ima datayi bala'in k'yau, Ashe bai zauna da k'yauba aiko yafad'o jikake taratsatsa!!! ya tarwatse ak'asa abinka da gilas.
Hakan yayi daidai dashigowar Bobo falon, da hanzari yanufi cikin d'akinsa, aiko abinda yake zarginne yagani, dandanan fuskarsa ta canja kama idonnan sukayi ja danshi aganinsa da gangan Rahma tayi saboda batason ganin hotunnan tunda dai yasan mata da kishi.
Tunda yashigo jikinta ke rawa, tabud'e baki arazane zatayi masa magana yadaka mata tsawa.
Dallah yimin shiru, dama kina shigowa gyaramin d'akine danki kashemin hotuna?, to wlhy idanma kishi kikeyi da ita kidaina Dan babu yanda kika iya da ita, wannan dakike gani itakad'aice nabawa zuciyata, daga itakuwa babu wata mace dazata samu haka daga gareni, wlhy akan wad'an nan hotunan sainayi mugun sa6a miki, banason cikin da iskanci.
Rahma tamatso danufin tsugunnawa tabashi hak'uri amma abisa tsautsayi ta taka gilas ak'afa, runtse idonta tayi saboda azaba, dama ga hawaye tuni sun wanke mata fuska.
Tsawa yasake dama mata, dallah malama fitarmin ad'aki, kuma karna sake ganin k'afarki ad'akina.
Ran Rahma ya6aci sosai ganin yanda yake cimata mutunci akan hoto, Wanda inyanzu yaso zaikai amaida gilas d'in daya fashe, haka tataka k'afa tabar d'akin tana kuka, tanazuwa tazube akan gado, ga azabar da k'afarta take mata amma bata kulaba, sai kuka maicin rai data saki.
Duk abinnan yake faruwa Nawal tana can baya tana wasa, Rahma taturata wajene dantabarta tayi aiki, batason surutu.
Bobo kam tana fita yadurkushe agaban hoton, d'agosa yayi yana gogewa tamkar zai fasa kuka, muryarsa na Rawa ya ce, "kiyi hak'uri Ni'imana bada sanina tayiba, ALLAH ya gafarta miki ya yafe miki kinji.
Nawal tashiga d'akin Rahma tana kwala mata kira momy! Momy!!, tak'arasa cikin d'akin da murnarta, amma ganin jini ahanyar sai jikinta kuma yay sanyi, tak'arasa har bakin gadon tana kallon k'afar Rahma da gilas ke jiki ga jini yanata zuba ak'asan wajen.
Fitowa tayi da gudu tanufi d'akin Papan ta, har yanzu yana gaban Hoton adurk'ushe, papa papa zokaga k'afar momy jini yanata zuba dayawan tsiya.
d'agowa yayi yana kallonta, yanda tabirkice shima sai jikinsa yay sanyi, mik'ewa yayi suka nufi d'akin Rahma d'in, gsky shima abin yabashi tsoro ganin jinin dad'an yawa, ga gilas babba kafe ak'afarta, tana kwance rubda ciki tana darzar kuka.
Tsugunnawa yayi Kusada k'afar yakama gilas d'in zai cire tasaki wata k'ara wadda tasaka Nawal fashewa da kuka itama, ga gilas d'in yakafe dayawa, ganin karya k'ara jimata ciwo yasa yamik'e dasauri yaje d'akinsa yad'akko key d'in mota.
Dawowa yayi ya ce, " tashi muje asibiti acire miki wannan kwalban.
Banza tayi masa tacigaba da kukanta, wani haushi yak'ara turnik'eshi, baisan lokacin daya sungumetaba yay waje da itaba, Nawal nabinsa abaya, Nawal tabud'e masa k'ofar motar yasakata aciki, suma suka shiga sai asibiti.........
_kuyi hak'uri da wannan yau kaina namin ciwo._
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S)))..........2017_*
[11/12, 2:51 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*
4⃣1⃣
Asibitin ya sulaiman sukaje, ALLAH yasosu sun tarar dashi.
Aiko ansha fama wajen cire gilas d'in nanan, Rahma tasha kuka dukta fita hayyacinta, ga k'afar harta d'an kunbura.
Shikansa Bobo ya tausaya mata, saiyanzu yake ganin abinda yay mata bai k'yautaba, to amma idan yatuna miyakai hannunta wajen hoton saiyaji ransa ya 6aci.
Da hakadai aka kammala, ya Sulaiman yamata allurai tad'an samu nutsuwa.
Bayan an kammala bobo ya ce, "ya yarinyar nan kuwa?.
Jikinta kam saidai muce alhmdllh, ammafa yakamata asan iyayen yarinyar nan Abdulmaleek, gashi kace zaku fara shiri'a ranar talata, kasanfa Alh sunusi dala mutumne mai had'arin gsk, sarai zai iya bincike akan yarinyar, kuma zai iya aikata kimai Dan ganin d'ansa ya ku6ta.
Hakane Yaya, amma inata iya k'ok'arina wajen Neman iyayenta, saidai kutayamu da addu'a kawai.
To ALLAH ya taimaka.
Amin dai, bari mubiya muganta saimu wuce gida.
Okey, kardai kamanta kusiyi maganin.
Babu damuwa, k'arasawa yay inda Rahma take fuskarsa babu walwa, yakama hannunta ta sakko.
Ya Sulaiman dake kallonsu ya ce, " saidaifa kad'auketa kamar d'azu, Dan babu yanda za'ayi ta iya taka wannan k'afar.
K'ara 6ata rai yayi, kamar bazaiyi maganaba, saikuma ya ce, "Yaya ba ancire ba?, eh ancire, amma karfa manta yanda gurin yake a yanzu, idanmma kunje gida ad'an gasa k'afar da ruwan zafi.
Baice komaiba ya d'auketa, saiwani kauda kai yake daga saitin fuskarta, itama saita runtse ido Dan bata son ganinsa.
d'akin da yarinyar nan take yakaita, yadireta saman kujerar gaban gadon, lahh Muheebat! kece?, Rahma tafad'a tana kallon yarinyar.
Itama tashi tayi zaune tana dariya Dan ganin Rahma.
Bobo ya ce, " kinsanta ne?.
Eh nasanta, K'anwar direban muce idris, dama sunata nemanta tun tuni wlhy.
Ajiyar zuciya bobo ya sauke ya ce, "Alhmdllh, yaciro wayarsa yakira Ya Sulaiman, babu dad'ewa kuwa ya iso, shima yaji dad'i sosai dajin labarin.
Sun ajiye magana akan anjima zasuje gidansu Muheebat, dukda bata iya magana to tanajin abinda suke fad'a, Dan haka taita murmushi.
Bobo Yakuma d'aukar Rahma zuwa Mota, daganan sukayi gida, motar tsit babu mai magana kamar wasu kurame, Bobo sai shan k'amshi yakeyi, itama ganin haka saita d'auke kanta, dama can suka baro Nawal zatabi ya Sulaiman gidansa.
Koda suka shiga harabar gidan saiya bud'e motar yay tafiyarsa ciki yabarta.
Rahma tayi wata dariya azuciyarta ta ce, " kama dawo wlhy, dan babu inda zan motsa.
Aiko tayi zamanta amotar, shikam haryaje k'ofar falon saiyaji babu motsinta abayansa Dan haka ya waiga, can ya hangota cikin mota ko motsawa batayiba, afili ya ce, "wai mi waccan abar take nufi da nine?, koni bawantane dazanta d'aukarta ina ajiyewa mtsooow, yak'arashr maganar dajan tsaki.
Komawa yayi wajenta sai wani d'aurewa yakeyi, Rahma ta hangoshi yana tahowa, tayi murmushin mugunta tana fad'in kadaiji dashi.
Bemata maganaba yabud'e motar ya d'auketa, itako ta lumshe idonta kamar mai barci, haushine yak'ara turnuk'e zuciyar bobo, gani yake tana k'ara langya6ewa ne kawai.
Koda yadireta a gadon bai kalletaba yajuya ya fita.
Ita kuma taimasa gwalo😜, wai dole dai ad'auketa. lol.
Tana nan zaune har kusan minti talatin, harta fara tunanin yanda zata fita taci abinci Dan yunwa takeji sosai, tayunk'ura zata tashi taji wani azababben zafi, danhaka takoma ta zauna, wai miyasama tabar Nawal tabi ya Sulaiman ne?, yanzu da tananan ai data rage mata wani abun.........bata rufe bakiba taji anturo k'ofar.
Kamshinsane ya tababbatar mata dashine, Dan haka tak'i d'agowa danko sallama bataji yayiba.
Tire yadire ak'asa na kayan break, Rahma tayi kamar bata ganshiba, shima ko kallo bata isheshiba yad'akko kofin tee ya mik'a mata.
Kamar bazata amsaba saikuma ta amsa Dan ganin yayi tamau da fuska kamar bai ta6a dariyaba, yamik'o mata filet d'in soyayyar doya.
Saman kujerar dake d'akin Yakoma ya zauna yana danna waya, ganin haka yasa tadake taci abincinta Dan yunwa takeji sosai.
k'asa² yake kallonta, aransa ya ce, "k'aryar ciwo kikeyi yarinya, tumda har kika iya share filet guda na doya, Rahma ta kalleshi ta ce, " nagama.
Banza yay mata yacigaba da danna wayar, saida ya mula Dan Kansa sannan yataso yazauna saman durowar gefen gadon, maganin yacira yabata.
Tofa anan akeyinta, Rahma tayi kwalkwal da ido zatayi kuka, tsak'i yayi yana harararta, idan bazaki amsaba kibarsa kece zakisha wahalarki ke kad'ai wlhy, danni yanzuma zanbar miki gidan.
Yanda yake zabga ruwan masifa yasa ta k'ar6a, saidai tana hawaye tana sha, idan tasha d'aya saitayi kamar zatayi amai saikuma ta daure, shidai yana kallonta ta gefen idonsa Dan yacigaba da latsa waya, hakadai tadaure tasha maganin.
Tashi yayi ya d'auki kwanukan yafita dashi, babu dad'ewa yadawo da k'aramar roba da ruwan zafi aciki, sai k'aramin tawul.
Baiyimata maganaba yajawo d'ank'armin tebir na gilas dake kusada kujera ya zauna, Rahma ta ce, "kasada aranta.
K'afarta yad'auka yad'ora saman stool na madubi, itadai ikon ALLAH take kallo kawai.
Dukda yaga kallon datake masa bai kulaba yafara aikinsa batareda yabi takantaba, yasaka tawul d'in aruwan zafin yad'an yamatse, daganin yanda yake matsar tawul d'in kasan ruwan da zafi, amma Dan bak'ar mugunta ahaka ya nanama Rahma akan k'afar, wani wahalallen ihu tasaki, yay saurin rik'e k'afar yana harararta, kawai saitaji hawaye nabin kumatunta.
Raguwar banza yafad'a afili.
Itama ta ce, " ruwanfa da zafi wlhy, yanda tayi maganar ashagwa6e saiya tsaya yana kallon bakinta, ta kauda fuskarta tana tura Baki gaba.
Shima bakin yata6e yacigaba da aikinsa.
Da zame zame da mazurai aka gama wannan gashin k'afar, yad'auki maganin shafawar ya shafa mata sannan yakwashe kayan yafice itakuma ta kwanta tana sauke numfashi.
Bai sake shigowa d'akinba harsu Ammar suka iso shida matarsa da yaransu biyu duk maza.
Cikin farinciki yataresu, yanda yaketa murmushi saika d'auka bashibane yagamawa Rahma mazuraiba yanzu.
Cikin falon suka k'araso, Sumayya matar Ammar ta ce, "nibanga amaryarba ko ka sakata ta 6uyane?.
Murmushi yayi ya ce, " 6uyan lfy, tana d'aki kwance batada lfy.
Ammar yashek'e da dariya mutumina komun samu k'annen Nawal ne?.
Harararsa yayi kaifa bakada kirki wlhy, to Abu ta taka ak'afarta d'azu da safe.
Ammar ya ce, "ayya ALLAH yakiyaye gaba, amma yanda na sanka d'innan ai yanzu munsami baby duk wani zame ²n ka.
Kadaiji dashi d'an iska, bobo yafad'a yana nufar d'akin Rahma.
A zaune ya Tatar da ita tagama saka kaya, Dan k'afar tad'an saki shine taje tayi wanka.
Ki taso su Ammar sunzo.
To. tafad'a atak'aice, haryaje k'ofa takatseshi dafad'in bafa zan iya fitaba.
Cak yatsaya kuma bai juyoba, yakai minti uku ahaka saikuma ya waigo, yawani saki murmushin mugunta danyasan maganar dazaiyi, okey kinaso nad'aukeki Dan kinji Ammar ya ce, " namiki ciki ko?, kinaso su tabbar kenan?.
Ido Rahma ta gwalalo waje ta ce, "nid'in?.
Baki ya ta6e tareda takowa har inda take, taho na d'aukeki nikuma namiki alk'awarin tabbatar musu da hakan.
Matsawa tayi gefe, ta ce, " kabarsa kawai zan iya.
Dariya yayi ya ce, "Yar rainin hankali, yana gama fad'a yafice yana cigaba da dariyarsa.
Rahma tarike baki o ni Rahma dama haka mutumin nan ya ke?, barikiga natashi kafin yaje ya nafkamin wani sharrin.
Haka ta d'ingisa har zuwa falon, ta zauna suka gaisa sunata tsokanarta, itadai bata iya cewa komai sai murmushi, mik'ewa tayi danufi basu ruwa da abin motsa baki, ya ce, " ina zaki?.
Ruwa zan basu tafad'a tana tafiya da d'ingishi.
Sumayya ta ce, "kinga dawo kizauna amarya, bari na d'akko mana aimu ba bak'i bane, Rahma ta ce, " haba daga zuwanku sai asaka ki aiki?.
Karki damu kinji, idanma kika kusa haihuwa nan gidan zan dawo, hannu tasa tarufe fuskarta Dan kunya, Ammar Kuma yayi dariya, Bobo ya ce, "Ashe na huta nikam?.
"Aiko ka huta."
Sumayya ce tamusu komai daya dace Rahma tayi, abincima atsakar falon sukaci, mutuminku sai wani kaffa² yakeyi da Rahma, ita abunma kunya da dariya yaringa bata, idan kukaga kulawar dayake bata saika d'auka haka suke kullum.
Har dare su Ammar suna gida, sai bayan isha'i suka tafi, bobo kuma yatafi d'akko Nawal Dan gobe zasu koma makaranta.
Rahma tad'an daddogara kamar gurguwa tad'an gyara abinda yadace sannan tayi wanka, shirin barci tayi tazauna jiransu.
Bayan wasu 'yan mintuna da zamanta saigashi ya iso da Nawal akafad'a tayi barci.
Saman gadon ya kwantar da ita, Rahma ta ce, " sannu.
Yauwa, tafad'a atak'aice.
Batabi ta kansaba harya sauyama Nawal kayan barci, shima baice mata komaiba yafita, babu dad'ewa saigashi da ruwa da Kofi, abakin gadon ya zauna yaciri magungunanta ya mik'a mata, tuni ta 6ata rai amma babu yanda zatayi haka ta amsa tana matse ido ta shanye, hawaye harsun cika mata ido.
Baki yata6e yayi kamar baiga hawayenba, yad'auki maganin shafawar yad'ago k'afarta yad'ora saman cinyarsa, maganin yashafa mata, ta lumshe idanu danji take kamar yana mata tafiyar tsutsa.
Shikanshi cikin nishad'i yake shafa k'afar, Dan yakai minti 7 yana shafa maganin, saida tad'an janye k'afarta sannan yadakata.
Mik'ewa yayi yamusu sallama yafita.
Rahma ta sauke ajiyar zuciya aranta ta ce, *_"Zaki na Ammi da Appa kafi karfin wargi"._*
_(Nikam Bilyn Abdul kirarin nata yabani dariya, nima zan kiya naringa yima my Abdul d'ina lol.)_
.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.
Yau bobo dakansa yayma Nawal wanka, yaymata shirin makaranta, Rahma kuma tadaure tahad'a musu break da abincin Nawal na makaranta.
Sauri² sukayi break d'in suka fita.
Har harabar gidan Rahma tarakasu, tana musu addu'a, bobo daya tada motar yalek'o kansa yana kallon Rahma, 'Yar gurguwar gidanmu akuladai karkuma akarya d'ayar.
Yana gama fad'a yafigi motar suka fice.
Ita maganar tasama dariya tabata wlhy, afili ta ce, "dama yanama mutane wasa?.
Tayi murmushi tareda shigewa ciki.
---------------------------+
Yana ajiye Nawal a school yanufi office, amma duk saurin dayakeyi saida yatadda mutane na jiransa, ciki harda Alh Sunusi Dala.
Kasancewar kowa yasan waye Alh sunusi dala suka barsa yafara shiga domin ganin Bobo.
Hannu yabashi suka gaisa, sannan ya ce, " Alhaji mike tafe dakai?.
Alh sunusi yasauke ajiyar zuciya, Brr... abunda ke tafe dani babbane kuwa, d'ana 'yan sanda suka kama tun ranar juma'a, kuma sunk'i bamu belinsa wai saisun kaimu kotu, gashi lauyana baya k'asarnan naturashi wajen wasu kayana a k'asar Chaina.
Alh to yanzu ni mikakeso namaka?, bobo yayi tambayar kamar baisan komaiba.
Saboda sunce munemi lauya, nasa abincikamin kwararren lauya shine aka kawoni wajenka, kuma nima idona ya tabbatar mini da hakan.
Shiru Bobo yayi yana karantar Alhaji sunusi, saida yaja minti biyu sannan ya ce, "Alhaji kozan iya ganin takardar sammacin da aka baku?.
A wannan mai sauk'ine aii Brr, Alh sunusi tafad'a yana mik'ama bobo takardar.
Saida yagama karantawa sannan ya ce, " Alhaji gsky akwai Matsala?.
Matsalarmi kuma Brr......?.
Wato wad'anda suke k'arar d'anka sunzo sun sameni tun ranar juma'a, kuma nine lauyansu.
Wani huci Alhaji yasauke, saikuma yay k'ok'arin 6oye 6acin ransa, ya ce, "Brr kataimakeni kamaida musu, ni namaka alk'awarin zan biyaka nikin baninkin d'in abinda suka baka wlhy.
Murmushi bobo yayi, sorry Alhaji hakan bazai yuwuba, duk Wanda yad'aukeni aiki a farko shinake yimawa gsky, inabaka hak'uri akan hakan, saidai nace maka mutari gaba kuma........
Kai k'aramin shashasha!!!! Alhaji sunusi yakatse Bobo a tsawace.
Shima Bobo ya katseshi ta hanyar d'aga masa hannu, Alhaji sauraramin nan office d'inane ba gidan kallon boll ba, ra'ayinane kuma nayi duk abinda nakeso alokacin danakeso gakuma Wanda nakeso, Dan zaman kaina nakeyi bana waniba.....
Kwafa Alhaji sunusi yayi tareda mik'ewa, yanuna Bobo dad'an yatsa yaro yarone, nakula bakasan koni wayeba, amma ina gab da sanar dakai, ni nafika zafin kai Brr...... Dan haka muzuba nidakai.
Mtsowwww muzuba mana Alhaji, nidakai za'a tantance damisar takarda.
Fuuuuuuu alhaji Sunusi yafice, masu tsaronsa suka take masa bayan.
Bobo kuma yaja wani wawan tsaki tareda zama saman kujerarsa.
*_" hummm masu karatu, bobofa yad'ebo ruwan dafa Kansa, kokuwa Alhaji sunusi ne yay gamo da gamonsa?, to kudai biyo d'iyar malam Ibraheema mata agidan Abdus'salam kusha labari."_*
_labarin bobo bagajeren lbr bane, idan na gajarceshi kuma bazakuji dad'iba, Dan haka karku damu da basarwar bobo zai dawo hanyane😂🤸🏼♂._
💃🏻💃🏻💃🏻yeeeeee ruwa akemana yanzun nan🌧🌧🌧.
*_luv u oll my fan's_*
*_(((S))...........2017_*
[11/12, 2:52 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻typing........
❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣
_•{BoBo}•_
*_NA_*
_*Bilyn Abdul*_
_sadaukarwa_
*_Abba Gana_*
*_Batul mamman_*
*_Billy giro_*