Abu Maleek Complete Hausa Novel
Reading file: Abu_Maleek_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 1 of 3
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
*NA*
NA'IMA SULAIMAN SARAUTA
Nimcyluv
20/11/2021
21/7/1443AH
*DEDICATED TO* ALL _ONLINE WTITERS, AL'KAIRIN ALLAH YA KAI MU, ALLAH YAY MAKU LIƊIFI DA KUMA JAGORA UBANGIJI YA KYAUTATA ƘARSHENKU YA YI RIƘO DA HANNAYENKU_
BOOK 1
PAGE 1-2
Edo/ Benin City state
Iska mai daɗi ce take Kaɗawa a garin, yayinda da samaniya tai wani kalar gwanin sha'awa, duk da cewa dare ne,Amma hakan bai hana ƙwantaccen hadarin dake ƙasan gajimare baiyana ba.
Yayinda gajimaran ke haske yana bada wani ƙara mai nuni da cewa hadarin gab yake da tashi.
Musamman yadda garin yay jajir baka jin sautin komai sai na tsuntsaye da kuma sassanyar iskar dake KaÉ—awa a garin.
Yadda hadarin ke ƙara haɗi da wani bada kalar sauti mai rugugi yana ƙara shaidawa mutanan garin cewa Tabbas ruwan gab yake da sauka, sbd yadda gajimaran yake ta gudu yana haɗa kansa hakan ya data hankalin tsuntsayen dake saman bishiyoy da Flowers damar tashi domin samun mafaka.
Yayinda da a gefe guda ƙaramin Yaron wanda bai zai gaza shekara 15 yake tafe cikin sassarfa sbd samun damar shigewa makwancinsa,
Gaba É—aya hankalinsa a tashe yake sbd ruwan da yake jin ya fara sauka, sosai Allah ya É—arsa masa tsoran saukar ruwan sama.
Fararan kayan baccin sa dake manne a farar fatar jikinsa suka ƙara mannewa.
Kasancewar su masu tsantsi da kuma sulɓi.
Tsayawa yay cak sbd sautin tafiyar da yaji a bayansa, gaba É—aya a tsorace yeke, domin wannan shine karansa na farko daya fito cikin dare.
Juyawa yay yaci gaba da tafiya har ya samu damar cimma shashin nasa yana gab da buɗe ƙofa.
Aka sakar masa wani doka a tsakiyar kansa.
Ƙara ya saki yana mai dafe da kansa nan da nan kuma jini ya fara gudana ta ƙasan kansa ya shiga sauka saman wuyansa zuwa kafaɗarsa,
yayinda idanunsa suke lumshewa, sabida tsananin azaba haɗi da zugi wanda yake ƙara hargitsa masa dukkan tunaninsa, Tabbas da gaske dokan ya shigesa har baya iya gane inda yake.
Maimakon ya shige part É—in nasa sai kawai ya juya ya nufi wani sashin.
Gefe guda kuma, wani ƙyakƙyawan Yaro ne Shima wanda bazai wuce 15yrs ɗin ba.
Ƙyakƙyawa ne ajin farko, ɗan leƙawa yay yaga da gaske babu kowa duk da cewa bashi da tsoro amma shi ɗin Mutum ne mai son kare martabar sa, ga isa da kuma ikon gaske baya shayin kowa..
Da sauri yabar wajan sabida foot sounds da yaji.
Yana mai dafe da kansa dake ɗan zubar da jini ya ƙarasa inda take tsaye,
Ganinta a wajan ne kuma yasa gaba É—aya ya nufi inda take gadan-gadan, ihu tasa amma duk da hakan bai hana shi rapping É—in ta ba, sabida shi É—in stubborn ne very stubborn bai ji sam, duk da cewa yana da tsoro.
Ganin abinda ya aikata
ne kuma yasa cikin sauri ya tashi yana mai naÉ—e wandonsa yabar wajan yana sakin tattausan Murmushi.
*SAHEL*
Wani yanki da cikin garin Sahel, San sanin Fulani ne wanda ya daÉ—e da kafuwa duk da kasancewar duk Fulanin wajan Makiyaya ne,
Masu tashi su sauya sheƙa a duk sanda suka so,
Gaba ɗaya cikin rugar bukkoki ne da ko wanne waje ga tarin garken shanu da ragona haɗi da raƙoma,
Amma gaba É—aya shanun wajan sunfi ko wacce dabba yawa a cikin garken,
Dare ne mai cike da tsoro haÉ—i da tsantsar fargaba, gaba É—aya Fulanin rugar sun hana idaniyar su bacci sabida tunanin abinda zai je ya dawo,
Gaba É—aya basu da wata kwanciyar hankali kullum suna rayuwa cikin tsoro da tarin fargaba gaba É—aya an hanasu kwanciyar hankali da farin ciki,
Basu da wata walwala ko kaÉ—an,
Misalin ƙarfe 2:30 ma daran yanar juma'ar kamar a mafarki Fulanin cikin rugar suka fara jiyo saukar bindiga da ƙarar fashewar abu kamar bom,
Cikin sauri ko wanne magidanci da kuma samarin rugar suka fara fitowa ɗauke da makamai yawanci kuma bawai makaman arziƙi bane,
Duk da yawanci jama'ar Duniya bawai gari ba sunawa Fulani kallan mugwayen mutane marasa tsoran ALLAH,
Amma a zahiri kuma ba haka bane, Fulani sam basu ƙaunar tashin hankali sabida sam basu sama da shi ba,
Kasancewar gaba É—aya rayuwar daji suke rayuwa mara Æ´anci,
Sosai hankalin Fulanin rugar ya tashi sabida kafin su yi wani tunani,
Tuni mugwayen mutanan sun ƙaraso cikin rugar suna harbin dukkan wanda suka yi katari da shi,
A can gefe guda kuma Wani magidanci ne ya fito daga cikin bukkar sa yana riƙe da hannun matarsa,
Wacce take dafe da cikinta wanda ya cika wata 9 a duniya,
Cikin sauri yake mata magana suna tsaka da tafiya taji mijin nata ya saki ihu,
Da sauri ta juya taga ashe harbinsa akai baki ta buÉ—e zatai ihu,
Yay saurin sanya tafin hannunsa ya toshe mata baki dashi,
Cikin fitar rai ya cire wani (GURI) nasa ya damƙawa matar tasa,
Yana shirin yin mgn sai Numfashin sa ya É—auke alamar dai rai yay halinsa,
Cikin sauri ta miƙe Idanunta na zubar da waye, a ranta take addu'ar tsira da abinda yake cikinta,
A haka ta kawo gaɓar wani kogi,
Sabida tashin hankali da yay mata yawa yasa naƙuda ta kamata, nan kuma take ta samu nasarar haifar farar jaririyar ta,
Wacce dunda tazo dubiya ta cilla yatsarta a baki, alamar haƙuri ya bayyana a tare da jaririyar, wacce aka haifa cikin tashin hankali,
Kuka ta fara hakan ya jawo hankalin mutanan da suke ta kaÉ—a shanun rugar suna gaba dasu cike da mugunta da kuma son zuciya,
Zanin Jikinta ta cire ta naÉ—e jaririyar da shi,
Kamar daga sama taji wani yace.
"Kawo ta nan"
Bata tsaya jiran abinda zaice ba tai saurin sauyawa yarinyar (GURI) wanda mijinta ya bata,
Da sauri kuma ta faki idanun mutanan wanda suke rufe da fuskokin su, kana tai azabar cillah jaririyar cijin ƙaton kogin dake gudana wanda babu wanda yasan inda ya tsaya,
Tana cillah Yarinyar suna sakar mata harbi.
(MAFARIN buɗewar ƙaddarar kenan)
*BAYAN SHEKARU ASHIRIN*
ALAAFIN OF EDO/BENIN *(MASARAUTAR KANZAF)*
Babbar Masarauta tace ta Yarabawa, Masarautar ta samu a sali tun iyaye da kuma kakanni,
Kowa yasan Yarabawa da riƙe Al'ada, basu wasa da dukkan abinda zai shafi kima da kuma matarta barsu,
Tun a ginin masarautar zaka tabbatar da ƙarfin iko na masarautar,
An ƙawata Masarautar da ginin jar ƙasa,
Mai ratsin fari da kuma Maroon,
A Ƙofar farko akwai Fadawa masu tsaron ƙofa sama da mutum Ashirin,
Babban cikinsu shi ne OBA LEKUN (SARKIN ƘOFA).
harabar wajan kuma sauran Fadawa ne cikin yadin uniform É—in su,
Daga wannan babbar ƙofa,
Sai wata ƙofa wacce aka gina ta ɗan yar Azurfa, banda sheƙi babu abinda take, ga kuma tambarin masarautar (Alaafin means Masarauta) a jikin ƙofa,
Nan ma Fadawa ne da kuma tarin barori da kuyangi kowa yana aikin gabansa,
Sosai masarautaru take da tsari mai kyau gwanin sha'awa ga baƙon da mai taɓa saninta ba.
Da sauri bisa sassarfa yake taka ƙafafuwansa a ƙasa, kansa a sunkuyar duk inda ya ratsa mutane zubewa suke suna gai dashi,
Hannayensa cikin Alƙyabbar lokacin zuwa lokacin yakan kawo gefe da gefen Alƙyabbar ya ƙara rufe jikinsa da ita,
Fari ne tass dashi amma fuskarsa babu walwala ko kaÉ—an,
Kana kallonsa kasan yana cikin matsanancin damuwa da kuma tarin fargaba domin duk yadda yakai
Da ɓoye abinda yake zucyarsa tuni fuskarsa ta riga ta fallasa asirin zuciyarsa,
Yana gab da shikewa wani babban sashe yaji anyi gyaran Muryar daga gefensa,
A hankali yakai dubansa ga wajan ɗan Murmushin sa na gefen baki ya sauke mata yana mai ƙara gyara tsaiwarsa sabida ya fuskanci akwai tarin magana a cikin bakin nata,
Kamar bazai magana ba sai kuma yace.
"Shirwa kike baki jewar banza, mene a ƙasa?"
Murmushin jin daɗi IYALODE (Jakadiya) tayi kafin ta rusuna tana ƙara ɗaga hannunta sama tace.
"Kifi na ganin ka mai jar koma, Wahainiya kake mai wahalar fahimtar launi bare kuma a fahimci naka launin, gaisuwa nake uban gidana, É—an sarki jikar sarki wanda ya gaji Sarautar a nono,
Kaga sarkin Masarautar Kanzaf na gobe"
Murmushi yana mai É—an janye fararan idanunsa daga gare ta,
Sosai ya ke jin daɗin yadda Iyalode take ƙara karfafa masa quiwwa bisa ganin muradinsa ya cika,
Muradin da aka haifesa da shi wanda a yanzu yake ganin tarin nasara da kuma haske na cikar muradin,
Fuskarsa ya shafa yana gyara zaman Alƙyabbar jikinsa yace.
"Aku sarkin labari, ai ni damusa ne mai farautar fukkan wanda yace zai ga baya na, shiyasa King (Oba, Sarki, Mai martaba) yake min kirari da SAHUN GIWA ÆADDANA RAƘUMI"
Jinjina kai Iyalode tayi zuciyarta fal farin ciki tace..
"Kaya ya sauka da zafinsa"
Ajjiyar zuciya Aremo Shakiru (Prince, Yarima, Shakiru) Ya yi yana mai juyawa kaÉ—an ganin babu kowa yace.
"Ya launin kayan suke?"
Kai tsaye Iyalode (Jakadiya) tace.
"Kayan suna da nauyi da kuma wahalar fahimtar launin su, Amma ga Damusa Aremo Shakiru Tunde Muhammad Jalal abin mai sauƙi ne"
HaÉ—e fuska Aremo Shakiru yay yace.
"Fasaltamin kayan, tun kafin ki tunzura zuciyata ki sanya mutanan cikin Kanzaf su shiga uku"
Da sauri tace.
"MALEEK ya mutu, Amma Mai Babban É—aki da Oumuu-Ayman sun toshe ko wacce hanya da zata tabbar da mutuwar MALEEK É—in"
Wani mahaukacin sauke ajjiyar zuciya Aremo Shakiru yay tare dayin baya cikin farin ciki da kuma jin daÉ—i yace.
"MALEEK!? Mutuwar MALEEK ta ƙara tabbatar min Eh lallai tabbas Muradina na gab da cika maza jeki kuma ki tabbatar da cewa babu wanda ya san wannan Maganar idan kika sake wani yasan maganar to tabbatas kin kawa iyalanki masifa"
Yana faÉ—in haka ya nufi Shashen damansa yana mai É—aure fuskarsa.
Bayansa Iyalode tabi da kallo kafin ta saki dariya yana tafa hannu tace.
"Da Iyalode kake Magana, sai na tabbatar ka kusa cika muradin naka ni kuma zan kaika ƙasa, domin Kimata tafi wannan muradin naka"
Tana faɗin haka ta juya kamar walƙiya tabar wajan.
Kai tsaye Aremo ɓangaren OBA TUNDE MUHAMMAD JALAL ya nufa.
A bakin ƙofar shiga tirakar tasa ya tsaya kasancewar yau ko waje King Tunde Muhammad Jalal bai leƙa ba,
Haka kuma ya hana kowa zuwa
Inda yake shima yanzu zai amfani da Soyayyar da King Tunde yake masa,
Yasa zai shiga tirakar tasa yaga meke faruwa, tsayawa yay yana ƙarewa masu tsaran Kofar kallo,
Cikin isa da gadara haɗi da ƙarfin iko yace.
"Yimin iso wajan King"
Ya faÉ—a yana kallon É—aya daga cikin hadiman King Tunde É—in,
Jininta na rawa sabida tsoran Aremo Shakiru Tunde Muhammad Jalal É—in tace.
"Afuwa Uban É—aki na, Tuba nake kayi min rai kada kasa na karya dokar King Tunde"
Gajeran tsaki Aremo Shakiru yay yana cillawa Hadimar kallo yace.
"Meye dokar?"
Cikin bashi girmansa na kasancewarsa ÆŠA a wajan King Tunde,
Ƙara ƙasa tayi da kanta tace.
"Umarni ne daga Oumuu-Ayman cewa kada wanda aka bari ya shiga cikin tirakar ta King Tunde, kuma Umarnin itama daga sama ya sameta wajan Mai Babban É—aki"
Shu'umin Murmushi Aremo Shakiru yay ba tare da yace komai ba ya juya kai tsaye zuwa shashin OLORI AYOOLA (Queen, matar sarki, Olori Ayoola).
A can ɓangaren Oumuu-Ayman kowa tana zaune a saman Sallaya idar da sallar ta kenan,
Tayi Shiru tana tunanin sabon al'amarin daya kunnu masu kai ba tare da sanin hakan zai faru ba,
Sai yaushe ne komai zai dai-dai-ta? Sai yaushe gaskiya zata bayyana ne? Sai yaushe Allah zai kawo lokacin da za'a warware wannan cukurkuÉ—aÉ—É—an wannan Lamari?
Ubangijin Jallah wa'azam! Ne kawai yasan abinda yake ɓoye, amma a kullum tana addu'ar Allah ya kawo ranar da gaskiya zatai halinta,
Abubuwa suna ta faruwa wanda ba'a san ta inda abin ya kunnu kai ba,
Numfasawa tayi a hankali sabida jin maganar Hadima Akin a gefenta,
Kallonta tayi tana sakin ƙyakkyawar fuskarta mai cike da kamala haɗi da zallar haƙuri tace.
"AKIN ya akai?"
ƙasa Hadima Akin tayi da kanta tana mai jan numfashi tace.
"ina fatan uwar É—aki na Oumuu-Ayman zata fahimci wannan sabun lamarin da yazo ma?"
Jinjina kai Oumuu-Ayman tayi tana mai É—an sakin murmushi tace.
"Mene ya faru kuma Akin?"
Juyawa Akin tayi kamar mai tsoron faÉ—in abinda yake bakinta, ganin hakan kuma yasa Oumuu-Ayman tace.
"Kada ki samu babu kowa ni É—aya ce"
Æoyayyiyar ajjiyar zuciya Hadima Akin tayi tace.
"Queen Ayoola ta matsa dole tana son sanin inda MALEEK yake"
Lumshe idanu Oumuu-Ayman tayi tana jin wani irin yanayi mai kama da ruÉ—ani yana shiga zuciyarta kafin ta numfasa tace.
"Wacce Amsa kika bata?"
Kai tsaye Hadima Akin tace.
"Haba Uwar É—aki na, bayan ni kaina bansan Inda MALEEK yake ba, tayaya zan bata amsa"
Hamdala Oumuu-Ayman tayi a ranta tana mai jin daÉ—i da farin cikin Babu wanda yasan abinda yake faruwa,
Kamar ba zatai magana sai kuma tace.
"Ya Rabb! MALEEK na shashin Mai Babban É—aki ai, tashi maza jeki wajan aikin ki"
Fita Hadima Akin tayi ba tare data fahimci komai a fuskar Oumuu-Ayman ba hasali ma sai tarin gaskiya da kuma kamewar dake saman fuskarta.
Tana fita Oumuu-Ayman tabi bayanta da kallo zuciyarta fal wasi wasi.
A hankali kuma ta miƙe tana ɗan gyara murya tare daci gaba da tasbihi ga Ubangijjn sammai da ƙassai.
Aremo Shakiru na shiga sashin Queen Ayoola ya sameta zaune,
Saman wata lallausar ladduma irin tasu ta masu mulki,
Ga Hadimanta sun yi mata ƙawanya, Wasu na firfita,
Wasu nayi mata tausa a ƙafarta kege guda kuma wasu na mata massaging a kanta wanda ta ɗan sutale hular Alƙyabbar jikinta,
Hannunta riƙe da Apple tana sha a hankali tana ɗan ɓata fuska,
Ganin Aremo Shakiru kuma É—an nata ne yasa ta saki Murmushi tare da bawa Hadiman nata damar tafiya zuwa anjima,
Zama yay ƙasan ƙafafuwan ta, yana mai gaisar da ita yace.
"Queen Ayoola Mumyna, ina fatan wannan yanayin da muka riski kanmu yana maki daÉ—i?"
Murmushi tayi a hankali ta miƙewa tsaye tana mai ɗaukan Inibi takai bakinta tace.
"Uhm, Akwai abinda yake faruwa da King Tunde wanda ba'a so jama'ar Kanzaf su sani, amma menene shi? Ta ina zan sani wannan shi ne abinda nake tunani tun safe, tunda na nemi izinin wajan waccar funafukar Oumuu-Ayman akan tayi min iso wajan King Tunde tace na tara wani lokacin banda wannan satin nasan Tabbas akwai matsala"
Murmushi Aremo Shakiru Tunde Muhammad Jalal yay domin ya daÉ—e da fahimtar mene ya faru,
Tunda Iyalode ta faÉ—a masa komai,
Amma sai yay kamar bai sani ba yace,
"Ina Mamaki sosai ainun ace mutum da mijinsa sai wata tana da dama Matarsa zata ganshi,
Ko kuma duk adalilin ba'a so a san Meke faruwa a cikin Alaafin (Masarautar)?"
Murmushi Queen Ayool tayi tace.
"Wannan ba Shine damuwa ta ba, yaushe ne burina zai cika yaushe ne zai dawo?"
Aremo Shakiru yace.
"Queen Ayoola wakike magana akai?"
Daga bakin ƙofar shigowa tirakar ta akace.
"Mahaukacin a koda yaushe zaki iya samun labarin ya dawo, idan har Oumuu-Ayman da Otun (Galadima) basu ɓoye zuwan nasa ba"
Matashin saurayin ya faÉ—a yana shigowa ciki tare da tsayawa a gaban Mahaifiyarta sa"
Cikin farin ciki Queen Ayoola tace.
"Da gaske JALALULDEEN TUNDE MUHAMMAD JALAL ya kusa dawowa?"
Jinjina kai SHAREFUDDEEN yayi yace.
"Bana kuskure a abinda na faÉ—a kuma za Kice na faÉ—a maki"
Yana faÉ—in hakan ya juya ya fice daga cikin tirakar Aremo Shakiru yabi bayan Sharefddeen da kallo yana mai kissima abu a ransa.
A can shashin Mai Babban É—aki kowa Adams ne zaune a gabanta yana jin abinda take faÉ—a amma sam baya shiga kunansa,
Cikin gajiyawa kuma da maganar ta yace.
"Zan wuce"
Kallonsa kawai Mai Babban É—aki tayi tana mai jin tausayin yaran a ranta tace.
"Har yanzu babu labari dan gane da ɓatan QUEEN ROOMANA?"
girgiza kai Aremo Adams yay yace.
"Babu fa, daga Daran jiyan da aka nemeta aka rasa zuwa yanzu babu wanda yasan inda take"
Mai Babban ɗaki na shirin yin magana Amintacciyar King Tunde ta Shigo da gudu Idanunta na zubar da ƙwalla dukkan Jikinta rawa yake,
Ganin Hadima Zubaida ya tayar da hankalin Mai Babban É—aki zuciyarta ta tsanata bugu,
Tsoro da bargabar abinda Hadima Zubaida zata faÉ—a mata yasa tayi saurin faÉ—in.
"Ya Rabbi, Ya Rahamu"
Adams Hadima Zubaida ya tsorawa idanu yana son jin abinda zata faÉ—a domin tun safe yasan akwai abinda yake
Faruwa a cikin Masarautar, duba da yadda King Tunde yau gaba É—aya bai zauna a fada ba, gashi a wannan satin yace zai fita ran gadi,
Ganin kallon da Adams ya kewa Hadima Zubaida yasa Mai Babban É—aki É—aukan sandan hannunta ba tare da tayi magana ba,
Tasa tafin hannunta ta kama hannun Hadima Zubaida ta jata zuwa cikin uwar ɗakinta wanda babu wanda ya taɓa shigarsa sai a lokacin
Data ja Hadima Zubaida ciki,
Zuwa lokacin kukan Hadima Zubaida ya tsananta bakinta sai rawa yake,
Ruwa mai sanyin gaske Mai Babban É—aki ta É—auko a fridge ta bawa Hadima Zubaida tasha,
A hankali ta shiga sauke numfashi har lokacin kuma
Hawaye bai daina fita daga cikin idaniyyarta ba,
Cikin fargaba haÉ—i da zullumi Mai Babban É—aki tace.
"Mene ya faru Zubaida?"
Kukan Zubaida ya tsananta kawo lokacin kuma Mai Babban É—aki ta fara tunanin ko dai wani abu ya samu Oumuu-Ayman ko kuma Jalaluldeen?"
Hadima Zubaida na sakin wani gigitaccen kuka mai tafe da fitar hayyaci tace.
*AUTHOR'S NOTE*
_BANA SAURI CIKIN WANNAN LITTAFIN, BA KUMA GUDU NAKE BA, YADDA KO GANI KO KARANTA SHI A HAKA, DOMIN INA DA TABBACIN ZA'A KAWO GAÆAR DA A YINI GUDA BAZA KUJERE BA IDAN MACE MAKU BABU POSTING, LITTAFIN ACE BOOK 1 2 3 NE, HAKAN KAWAI ZAI TABBATAR MANA TAFIYA CE MAI ÆŠAN NISA, AMMA GARE NI IDAN INA TYPING SAM BABU NISANTA, A HAR KULLUM KUNA KARANTA LITTAFI NA DA SIGA BIYU, ILIMIN CIKINSA, DA KUMA FAÆŠAKARWAR CIKIN SA, I'M NOT PERFECT AMMA DOLE ZAN CE MAKU AKWAI HIKIMA CIKIN WANNAN LITTAFIN NA *ABU_MALEEK* KADA KO KARANTA DOMIN JIN DAÆŠIN KU, DOMIN AKWAI SANDA ZAKU NEMI DAÆŠIN KO KARASA SAI ZALLAR ƘUNAR ZUCIYA DA KUMA TASHIN HANKALI, ME ZAI FARU? MENE A LABARIN? NO ONE'S KNOW DOLE SAI NI._
DAN HAKA NAKE CEWA KO GYARA ZAMA KANA KO KAKKAÆE ZANI.
SHARE PLEASE AS SO MUCH AS YOU CAN HABIBATIES, KUYI SHARE FISABILILLAHI SABIDA ALLAHðŸ˜ðŸ˜ðŸ‘ðŸ»
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
*NA*
NA'IMA SULAIMAN SARAUTA
Nimcyluv
BOOK 1
PAGE 3-4
"Jikin King Tunde Muhammad Jalal ya tsananta, babban tashin hankalin yadda yake ta kiran sunan Queen Roomana"
Dam dam dammm zuciyar Mai Babban É—aki ta bada sauti,
Cikin tashin hankali da kuma tsoro haÉ—i da zullumin daya gama ratsa zuciyar mai Babban É—aki,
Ta sanya tafin hannunta tare da dafe gishintuta shiga sharfe zufar da yake karyo mata,
Baya tayi kaÉ—an tare da fesar da numfashi haÉ—i da kallon,
Hadima Zubaida cikin jarumta tace.
"Kije ki kira Oumuu-Ayman ta sameni a tirakar King Tunde,
Sannan ki kiramin OTUN (Galadima), shima ya sameni a tirakar King Tunde"
Cikin ladami da girmamawa Hadima Zubaida ta sunkuya har ƙasa tace.
"FaÉ—e taki cikawa tawa,Mai Babban É—aki"
Kai kawai Mai Babban É—aki ta jinjina,
Shekarunta sun ja, amma komai na rashin tsoran Allah da kuma son zuciya ƙara bayyana yake,
A cikin Alaafin (Masarauta).
Hadima Zubaida na shirin fita Mai Babban É—aki tai saurin faÉ—in.
"A tsananta tsaro a shashin, ki tabbatar babu wanda ya san da maganar ciwon na King Tunde,
Hatta matarsa kada ki faÉ—a mata, sannan ko sirikan gidan nan kada suji wannan labarin mai tarwatsa zuciya,
Ki sani fitar wannan al'amarin yana nufin rushewar Wannan Masarauta wacce ta kafu shekara da shekaru,
Ki kiyaye da wannan Hadima Zubaida, duk abinda yaje ya dawo kiyi kuka da kanki"
Ƙara sunkuyar da kai Hadima Zubaida tayi cikin son bawa Mai Babban ɗaki girmanta na mahaifiyar King Tunde tace.
"Ubangijin Al'arshi yana kallon komai,
Kuma yana ji yana gani, idan har maganar ta fita dukkan hukunci daya dace aimin ni Hadima Zubaida na aminci"
Tana faÉ—in hakan ya juya da sauri domin zuwa sashin Oumuu-Ayman.
Ajjiyar zuciya a karo na barkatai Mai Babban ɗaki ta ƙara saukewa,
Zuwa yanzu abubuwa sun fara mata yawa,
Tana son samun mataimaki Tabbas,
Amma yaushe? Ta ina? Wace zata zama hasken da zai yaye duhun dake cikin Alaafin?
Shine abinda har yanzu bata sani ba,
Yadda shekarunta suka ja hakama Oumuu-Ayman ba komai zata iya ba,
Jigon gidan biyu ne, gashi an wayi gari babu Queen Roomana,
Ɗaya ɓangaren wanda ya kasance haske da kuma tauraron gida ƙaddarar sa kaɗai da ishesa,
Ƙaddarar kuma da ita ce sanadiyyar faruwar dukkan wani mugun tuggu dake cikin Alaafin,
Miƙewa tsaye tayi tana runtse ƙafarta wacce take mata,
Tsananin zafi da kuma zugi domin kwana biyu,
Ciwon ƙafar ya dawo mata sabo fill har bata iya taka ƙafafuwan ta,
Tana dogara sandar zallar azurfa ta mai sheƙi ta nufi Parlo idan Kuyanginta suke jiranta.
A can tirakar King Tunde kowa Oumuu-Ayman ce zaune a gefe guda, sai Otun da kuma Hadima Zubaida.
Gaba É—aya Babban shashin wanda ya kasance shine sashin Oba watu sarki ya cika da masu tsaro ko alamun fara'a babu a fuskarsu bare ka tabbatar cewa idan kazo zasu barka ka shiga,
Mai Babban ɗaki ce ta ƙarasa shiga ciki yayinda kuma,
Kuyangunta suka tsaya can nesa da Babbar ƙofar shiga tirakar ta King Tunde,
Tana shiga Oumuu-Ayman ta Miƙe tsaye sabida nuna girmamawa,
Cikin sabon tashin Hankalin daya samesu bayan wanda suke ciki,
Mai Babban É—aki taja Jikinta can gefe kusa da King Tunde tana faÉ—in.
"Kiloshèle?" (Meke faruwa)
Cikin jan wahala da kuma tsananin a zabar da King ya keji a cikin zuciyarsa ya sanya tafin hannunsa,
Dake É—igar da gumi yace.
"A nemu Queen Roomana duk inda take,
Kada a bari a rasata, Tabbas jikina yana bani akwai wani abu,
Ban san mene shi ba, ban kuma san yaushe ya faru ba,
Amma Queen Roomana itace hasken Alaafin"
ÆŠauke kai Oumuu-Ayman tayi sabida hawayen daya sakko daga cikin idanunta,
Babu abinda yake tayar mata da hankali irin rashin Queen Roomana,
Babban abin fargabar har kawo yazo babu wanda ya faÉ—awa,
Jalaluldeen sabida tsoran abinda zai yi,
Tana tsananin son Jalaluldeen so mai yawa musamman idan ta duban mummunar ƙaddarar data hau kansa,
Gyara zama Mai Babban É—aki tayi tace.
"Babu abinda zai faru da Queen Roomana, ka kwantar da hankalinka, na tabbatar ko babu Queen Roomana akwai hasken da zai zo cikin Alaafin yay fatali da duhun da yake cikinta,
Tabbas nayi imani da hakan lokaci kawai muke jira"
Ta ƙare maganar tana tasbihi a ranta,
King Tunde kallon mahaifiyar tasa yay yace.
"Wanne haske ne wannan wanda ya wuce na Queen Roomana?,
Bana jin akwai wani haske da zai yi iya yaye wannan duhun dake cikin Alaafin"
Murmushi Mai Babban É—aki tayi tace.
"Da kasan zaka samu Queen Roomana? Ko kuma kasan zaka samu MALEEK yaro mai fikira da hikimar gaske, to mafarki na bazai taɓa gayan ƙarya ba,
Sai dai bansan lokacin da mafarkin zai zama gaskiya ba"
A can waje kam wata mai matukar kama da Hadima Zubaida ce ta nufi cikin sashin Kinga Tunde,
Yayinda gaba É—aya kayan jikinta irin na Hadima Zubaida ne babu wani bambanci,
Hannunta ɗauke da ƙwayar zumar da aka haɗawa King Tunde ta nufi wajan,
Sanin cewa kowa yasan ita É—in itace Babbar Hadima kuma Amintacciyar King Tunde yasa babu wani shamaki aka buÉ—e mata tafkekiyar Kofar glass É—in ta shiga ciki tana mai sakin tattausan murmushi.
Tana shiga ta samu ta silale ta shige cikin wata ƙatuwar akwati wacce duk yadda kakai da fahimta baza ka taɓa fahimtar abinda yake faruwa ba,
Ƙara ƙasa kunne tayi sabida jin Oumuu-Ayman tana faɗin.
"Maleek yana raye, sam bai mutu ba, kawai rayuwarsa tana cikin hatsari,
Kuma shine kaɗai ƙarfin guiwar mu, shine last hope ɗin mu,
Shine zai sanya mu tuni ƙaryar da take ɓoye shekara da shekaru"
Oumuu-Ayman ta ƙare maganar tana sakin tattausan murmushi domin ita kaɗai tasan abinda yake zuciyarta,
King Tunde ya ja numfashi yana ƙara kallon Oumuu-Ayman da kuma Hadima Zubaida wacce take tsaye gefe guda yace.
"Bikin (ODUN EGUN) saura sati biyu,
Bana jin cewa zakai wannan lokacin ina raye,
Amma a tabbatar cewa ko na mutu sai a gudanar da wannan bikin, domin shine zai tabbatar wa da al'ummar Kanzaf Alaafin tana cikin ƙoshin lafiya,
Ban yarda a binne gawata ba har sai an gabatar da wannan bikin al'adar"
Cikin sabon tashin hankali Oumuu-Ayman tace.
"Meke faruwa dakai ne King Tunde? Ka sanya zuciyoyinmu cikin zullumi, ka sanya zuƙatan mu cikin juyayi"
Murmushin baƙin ciki king Tunde yay kafin yace.
"An samin goba cikin abincin sha na, ina jin zafi da raÉ—aÉ—in ta, jikina kamar ana hura min wuta haka na keji, babu mai magance min wannan cikin sai Aremo JALALULDEEN TUNDE MUHAMMAD JALAL"
Shiru sukai sabida tashin hankali gaba É—ayansu zufa ke karyo masu,
Fake Hadima Zubaida dake cikin akwati wacce tai pretending kamar itace Hadima Zubaida ta gaskiya,
Tai saurin fitowa tana rufe bakinta domin,
Dukkan abinda ya dace ta samu labari akai yanzu taji komai,
Da sauri ta juya ta fita fuskarta cike da farin ciki da kuma daÉ—in samun nasarar da tayi.
Washe gari
Tsaron cikin Alaafin ya tsananta matuƙa, haka kawo lokacin babu wanda yake da labarin abinda yake faruwa,
Kowa ya tambaya Meke faruwa ana bashi bayanin cewa sabida bikin ODUN EGUN da Za'ai shiyasa aka fara shiri tun yanzu!
Sabida bikine da ake yinsa duk shekara wanda ake gayyatar,
Manyan sarakuna da kuma manyan mutane,
Biki ne dake nuna wa jama'ar Kanzaf cewa ƙwarai da gaske Oba (sarki) da jama'ar cikin Alaafin suna lafiya,
Rashin yin bikin kuma yana nuni da cewa akwai wani,
Gagarumin abu dake faruwa a cikin Alaafin wanda hakan zai iya tada hankalin jama'ar Kanzaf.
Wannan dalili yasa gaba ɗaya Hankalin Mai Babban ɗaki da kuma Otun da Oumuu-Ayman ya tashi matuƙa,
Domin sunyi imani cewa mutum É—aya ne zai iya zama ya gudanar da wannan bikin al'adar ba tare da an samu wata matsala ba,
Amma su gansu basu da tabbacin cewa zai amsa kiran king Tunde É—in ko kowa?
Rabonsa da cikin Alaafin (Masarauta) yanzu kimanin shekaru wajan 20 kenan,
Yaya ya koma? Ya yake yanzu no one's know!
Gaba ɗaya suna zaune a saman babban danning table wanda a ƙalla yake da kujeru wajan 20 ciff, wanda sukaiwa table ɗin ƙawanya,
Bisa al'adar mutanan cikin gidan ne duk ranar juma'a tare suke zama yin breakfast, lunch, and dinner!
Yanzu ma suna zaune Mai Babban É—aki ce a babban kujera, gefenta kuma Queen Ayoola ce, daga É—aya gefen kuma Oumuu-Ayman ce.
Sai kuma sirikan gidan wanda suke cikin kaÉ—ai ci da kuma kewar mijinsu,
BOLA, sai kuma KUBRAAH, sai kuma Aremos (prince's) Adams, Shakiru, Sharefddeen, Femi, kana Salimerh.
A hankali kowa keyin breakfast ɗinsa baka jin ƙarar komai saita Spoons knives and forks!
Boola ta É—an ja Ajjiyar zuciya tana ta juya Arish É—in dake plate É—inta ta gagara cin komai,
A tsanake Mai Babban É—aki tace.
"Kiloshèle Boola?"
Marai-raice fuska tayi a hankali kuma hawaye ya sakko daga cikin idaniyyarta zuwa kan farar ƙyakkyawar fuskarta tace.
"Allah ya ƙara maki lafiya da kuma yawan rai, abubuwa sun fara min yawa, babu miji babban tashin hankali yadda ake nemi Mami aka rasa!
Yanzu da wanne kalar baki za muyi wa Jalaluldeen bayani? Wanne hali Mami ke ciki tana ina ta mutu ko tana raye babu wanda ya sani"
Runtse idanunsa sosai Adams yay yana jin zcyarsa na tafasa ainun, wane zata rainawa hankali,
Bayan a jiya ya gama fahimtar komai cewa Jalaluldeen ya sanya aka sace Queen Roomana (Mami) sabida cimma buƙatarsa,
A hankali jikinsa ya É—an shiga rawa kana a zafafe kuma ya hankaÉ—e plate É—in gabansa yana mai jin yadda zuciyarsa ta cika da tsanar Jalaluldeen.
Mai Babban É—aki bayan Adams tabi da kallo tana mai son karantar yanayinsa amma ta kasa.
Cikin tarin mamaki na sauyin yanayin Adams da juya dubanta ga Boola tace.
"Kuyi addu'a, in sha Allah! Babu abinda zai faru da yardar Ubangiji tana cikin kariyar Allah, ita É—in haske ce koda an rasa ta Tabbas Ubangiji zai kawo mana madadinta wacce zata kula da komai na cikin Alaafin Tabbas"
A tare Queen Ayoola da Aremo Shakiru suka kalli Mai Babban É—aki cikin son kawar da abinda yake ransu a tare abin kamar haÉ—in baki suka furta.
"In sha Allah!"
Sharefddeen kam abincinsa kawai yake ci yana mai tunanin abubuwa da dama.
Rarraba idanu Kubraah ta fara kafin cikin nutsuwarta haÉ—i da kamewa tace.
"Ina Maleek ne?"
Dam zuciyoyinsu suka buga a tare musamman Oumuu-Ayman, wacce tuni zufa ya gama wanke ta kanta a ƙasa,
Hannunta mai É—auke da spoon ya shiga rawa sabida tsananin ta'ajjujin tambayar ta Kubraah domin sam ba tayi tunanin hakan ba a kuma dai-dai wannan lokacin..
Cikin rashin sanin amsar kuma daza su bawa Kubraah ne yasa a sukwane Oumuu-Ayman ta ɗaga hannunta daga cikin plate ɗin tare da miƙewa tsaye,
A hankali cikin nuna cewa tana da cikakken hankali da kuma tarin nutsuwa ta nufi shahinta,
Ganin haka yasa Mai Babban É—aki gyaran murya a hankali tace.
"Ki Sanarwa Hadima Zubaida cewa ina nemanta yanzu da gaggawa"
Mai Babban É—aki ta faÉ—a tana kallon hanyar da Oumuu-Ayman tabi.
Da "to" Oumuu-Ayman ta amsa tana mai yin gaba abinta,
Kubraah ganin babu wanda ya amsa ta yasa taja bakinta tai shiru,
Shakiru wani kasalallan Murmushi ya saki yana mai jan gemunsa da hannunta,
A ransa yake faÉ—in.
"A juri zuwa rafi da tulo.."
Wajan 11:30 Mai Babban É—aki na zaune saman ladduma idar da walaha É—inta kenan Hadima Zubaida tayi sallama bayan ta nemi isu wajan Hadimar Mai Babban É—aki wato Hadima Akin.
Zubewa tayi gaban Mai Babban É—aki tana mata kirari kamar yadda ta sama,
A taushashe cikin son ƙara jan kunan Hadima Zubaida tace.
"Zubaida ina mai ƙara jan kunanki game da wannan sabon al'amarin, mu huɗu muka san da wannan maganar, ni Oumuu-Ayman sai King Tunde da kuma Otun (Galadima),
Idan maganar rashin lafiyar king Tunde ta fita da kuma É—aya maganar wacce tafi komai muhimmanci a gare mu ta rashin mutuwar MALEEK ta fita, Tabbas kada kiyi tunanin zan goyi bayan ki,
Dukkan abinda ya faru ki kuka da kanki"
Cikin gamsuwa da maganar Mai Babban É—aki Hadima Zubaida ta jinjina kanta tace.
"Raina fansa ne ga Alaafin, dukkan abinda zai cutar da jama'ar cikinta kuma ina yaƙi dashi, na aminci da dukkan hukuncin da Za'ai min idan har wannan Maganar ta fita"
Murmushi jin dadi Mai Babban É—aki ta saki domin ta aminta da Hadima Zubaida sosai fiye da jikokinta.
"Ke nemu min Amintacciyar kuyangar Jalaluldeen yanzu"
Da makaki Hadima Zubaida tace.
"Ai Jalaluldeen bashi da wata Amintacciyar kuyanga, rabonsa da Nigeria yanzu kimanin shekaru ashirin kenan ciff"
Da sauri kuma Mai Babban É—aki tace.
"Ai haka ne, daman na kiraki domin naja kunanki ne"
Murmushi Hadima Zubaida tayi sabida rikitar tsufan Mai Babban É—aki, danma tana jajir cewa,
Cikin ƙasa da kai tace.
"Ai kin faÉ—an"
Kallonta tayi sai kuma tace.
"Au toh! Toh! Shikenan, kawo min zuba yanzu da madarar shanu mai zafi, ki haÉ—a da Algaragis"
Miƙewa Hadima Zubaida tayi ta nufi babban kitchen ɗin Mai Babban ɗaki ta a shirin shiga ciki Mai Babban ɗaki tace.
"Ki haÉ—o min da Algaragis"
Hadima Zubaida tai Murmushi tace.
"Ai kin faÉ—a min"
Jinjina kai tayi tace.
"Toh! Toh! Shikenan"
Haɗo mata komai tayi kana ta kawo mata wajanta tare da Miƙewa tace.
"Na barki lafiya Mai Babban ɗaki Allah ya ƙara lafiya"
Jinjina kai kawai Mai Babban É—aki tayi ba tare da tace komai ba,
A hankali kuma ta sanya hannunta mai cikakkiyar lafiyar ta cire Inibi guda É—aya mai sanyin gaske tai Bisimillah tare da sanyawa a bakinta.
A can ƙofar sashin Mai Babban ɗaki kowa cikin nutsuwa Hadima Zubaida take tafiya harta isa sashinta domin hutawa,
Kai tsaye gaban babban mirror'n dake maƙale a jikin bangon parlon ta kalla.
A hankali kuma ta fara ɓaɓɓaka dariya har hayaƙi na fita daga cikin bakinta,
Tana gama dariyar ne kuma ta tsuke fuska tare da sanya hannunta ta cire fake fuskar data maƙala irin ta Hadima Zubaida,
Nan take fuskar.....
*SHARE FISABILILLAHI DAN ALLAH*
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
NIMCYLUV
BOOK 1
PAGE 5-6
Robar ta faɗi ƙasa, cikin sauri kuma ta ɗauka tare da mayarwa saman fuskarta tana sauke ajjiyar zuciya.
A hankali kuma cikin son tunanin abinda zai faru gaba shiga yawo cikin kwanyar kanta.
Tabbas rashin lafiyar King Tunde tai matuƙar faranta ranta sosai fiye da sosai ma.
Kawo lokacin harshashen kasancewar ta Sarauniyar Kanzaf take.
Cike da farin ciki da kuma jin daÉ—in,
Sabuwar nasarar dake shirin tunkaro ta, ta tsirawa mirror'n idanu tana hango zallar kyau da kuma tarin haibar dake saman fuskarta,
Lallai Tabbas Hadima Zubaida tana da amana da kuma riƙo da gaskiya wannan dalilin ya sanya ta zama Amintacciyar Hadimar King Tunde.
Baya tayi kaÉ—an tana watsa hannayenta sama cikin dakakkiyar murya ta mai cike da isa da kuma gadara tace.
"Easy! Easy! Wannan lokacin tunani ne bawai shirme ba, wanne dalili ya sanya Oumuu-Ayman da Mai Babban ɗaki suke son ɓoye MALEEK? Har suke laƙaba masa kalmar mutuwa kalmar da ita a rayuwa ma mancewa take da ita, idan har ba gani tayi wani ya faɗi ya mutu ba"
Shiru tayi da zan can,
Ta shiga kewaye cikin ma dai-dai cin Parlon nata,
Murmushi tayi kana ta É—ura hannayenta duk biyun ta bugi tsakiyar kanta tace.
"Perfect idea, dole Tabbas ya kamata MALEEK yayi mutuwar gaskiya, domin shi kaÉ—ai zai hanani zama sarauniyar Kanzaf"
Ta faÉ—i hakan tana mai faÉ—awa saman kujera 3seater tare da sauke gwauron numfashi.
Misalin 11:30 na safe Salimerh ta fito sanye da wani tattausan farin voyal na mata.
Wanda yake É—auke da red torches, masu kyau da kuma walwali suna É—aukan idanu,
A ƙalla voyal ɗin Jikinta zai kai adadin kuɗi kimanin 1500k (dubu ɗari da hamsin).
Sai milk ɗin Alƙyabba data sanya a saman voyal ɗin,
Wanda ta haddasa fitowar a salin kyanta kuma ta ƙara shaidawa jama'a Tabbas, ita ɗin jinin Alaafi ce,
Salimerh tana da sanyayyan kyau bata sa jiki sosai sai tsayi da take da shi,
Ga kuma fara'a da kyautatawa, amma tana son nuna cewa iya É—in da gaske jinin sarauta ce,
Wanda ko da ace bata nuna ba to zallar jin kanta da kuma isarta haÉ—i da Izzarta ka É—ai zai shaidawa mutane cewa ita É—in jinin King Tunde Muhammad Jalal ce.
Hannunta riƙe da wayarta mai ƙirar Iphone 12pro max,
Kanta a ƙasa take taka Fararan sahunta wanda suke sanye cikin wani takalmin fata,
Mai tsananin kyau ga wani gashi gashi dake a jikinsa,
Daga bayanta kuma Hadimanta ne suke riƙe da school bag ɗinta da kuma Iphone system ɗinta,
Duk inda ta gilma bayi ne ke zubewa suna gaida ta, duk da cewa abinda take dubawa yana da matuƙar muhimmanci amma haka take daurewa tana ɗaga masu hannu,
Sabida wulaƙanci bana ta bane, infact ma bata iya sa ba.
Wani babban dogari ne ya ƙara su da sauri ya buɗe mata back seat na motar mai ƙirar Mahindra XUV7000 ash color!
Da sauri ta faÉ—a mota tana mai gyara zaman farin iphone bluetooth É—in ta,
Driver na ƙoƙarin jan motar, taji an buɗe ƙofar left hand side ɗin ta an shigo,
A hankali ta saki numfashi tana mai ɗan taune laɓɓanta, tuni ƙamshin perfume ɗinsa ya shaida mata ko wanene,
Ba tare kuma da tayi magana ba taci gaba da searching É—in dake na *Criminology*
Kasancewar yau ne First time da zata halarci *Dean Of Law* (University of Benin) a hankali kuma ta shiga typing É—in “Define Criminology¿â€
Cikin abinda bazai wuce wasu daƙiƙo ba goggle ɗin suka watso mata amsar.
_Criminology is a_ _multidisciplinary science that studies a diverse set of information related to criminal activities such as individual and group criminal activities, perpetrator psychology and effective means of rehabilitation._ _Criminology degrees examine social reaction to crime, methods and procedures to prevent and combat crime and social protection from crime. Criminology combines theories from other disciplines like psychology, sociology and law_
Anya zata iya wannan karatun mai wahalar gaske da kuma tarin hatsari,
Wata zuciyar ta bata amsa da.
"Dole za kiyi, kada ki mata wannan karatun shi ne hope É—in ki, kuma shine abinda kike so kiyi Achieving a rayuwa, kuma yin wannan karatun shi ne zai baki damar tsare jama'ar Alaafi da kuma al'ummar Kanzaf,
Wannan karatun shine zai baki damar fahimtar mugwaye kuma azzaluman da suka jima suna zuluntar É—an uwanki, wanda har kawo yazo babu wanda yasan ko suwane bare yasan plan É—insu na gaba"
Fesar da iska tayi a hankali kuma ta juya ta kalli wanda yake kusa da ita.
Tattausan Murmushi ya sakar mata, a hankali kuma yace.
"Ina kiranki baki picked mene dalili my princess?"
Kauda kai tayi dan sam ko sau É—aya bata jure kallon sa,
Domin yana da cikar haiba ƙwarai da gaske, jan numfashi tayi dai-dai kuma lokacin,
Da driver yaywa motar key suka fara tafiya tace.
"Bro! Nayi busy sosai ne"
Ta faÉ—a tana yin baya tare da kwanciya a jikin kujerar motar.
A lokacin ne kuma drivern ya cilla motar saman titin masarautar ya nufi babban gate.
Junaid ya fidda wani emotional sound mai É—auke da manufofi da dama,
Kana ya shigayiwa Salimerh wani kallo wanda yake nuni da zallar so da kuma ƙauna kafin ya numfasa cike da jarumta da nuna cewa shima ɗin jinin sarauta ne, domin Junaid ɗane a wajan Otun (Galadima) yace.
"Nawa Abba magana akan abinda yake tsakanin mu, seriously bana son wani long time, please my princess help me"
Idanunta a lumshe sam a wannan lokacin bawai tunanin Junaid É—in take ba,
Gaba É—aya tunaninta ya tafi akan brother nata, wanda yake É—aukan damuwar ta a matsayin tasa,
Amma yay mata nisa mai yawa yaya za'ai ta dawo dashi Nigeria zuwa Kanzaf, domin ya ziyarci bikin ODUN EGUN na wannan shekarar?
Ganin tai nisa sosai cikin tunaninta yasa Junaid miƙa hannu a taushashe ya kama nata hannun yace.
"Look! My princess love me or hate me is not my problem, amma dan Allah ki aminci da auran mu please dear"
Cikin rashin sanin abinyi kawai da jinjina masa kanta,
Cike da farin ciki ya zame hannunsa a nata yana faÉ—in.
"Ohh Wow! Junaid you're the best thank you My princess"
Murmushi kawai tayi tana ci gaba da duba courses É—in da zata karanta onder criminology justice kamar su.
Introduction to Criminology.
Theories of Crime Causation.
Human Behavior and Victimology.
Professional Conduct and Ethical Standards.
Juvenile Delinquency and the Juvenile Justice System.
Dispute Resolution and Incidents Management.
Criminological Research.
*🇪🇸SPAIN/ MADRID*
Only you hotel atocha!
Babban hotel ne, wanda kana ganinsa kan cewa bana Æ´an zauni gari banza bane.
Musamman yadda tun farkon titin da zai sadaka da hotel É—in yake É—auke da manyan jami'an tsaro (Securitie's).
Haka kuma cikin hotel É—in tun kafin ka shiga sai na'ura ta cajeka tsaf ta tabbatar babu abin cutarwa jikinka sannan za'a baka damar shiga.
Tun a reception na fara ganin manyan Æ´an wasan Madrid sanye da farar riga wacce a gaban rigar aka sanya (Emirates fly).
Kowa na É—auke da small bag a bayansa sai gorar ruwa mai sanyi.
Sai fitowa suke daga cikin room É—in su gasu nan irin su ALABA, LUNIN, MARCELO, KROOS, ISCO.
BENZEMA ne ya É—an ja Sirrin tsaki yana mai juyar da kansa gefe cikin harshen turanci yace.
"What the fuck"
Ya faÉ—a yana fesar da iska,
Sarai sauran sun fahimci dalilin daya sanya Benzema yace haka, amma no one's talk dole su jira domin umarnin coach.
A can cikin room 212 kowa baka jin komai sai ƙarar gudun A.C da kuma ƙarar gudan ruwan dake zuba daga cikin shower, alamar dai wani ke wanka a ciki.
A hankali ya sauke wata zazzafar iska tare da sanya fararan teeths ɗinsa ya datse jajayen laɓɓansa da haƙoran,
Hakan ya samu asali ne sabida sanyin ruwan showern daya sauka saman ƙwantaccen gashin kansa wanda yake da tsayi sosai ainun domin ya sauka har ƙasan wuyansa,
Gashin baƙi ne siɗik amma daga ƙarshen gashin wanda ya samu nasarar kwanciya a bayan wuyansa ya kasance coffee,
Da sauri da sauri kuma ya shiga sauke ajjiyar zuciya yake ya ɗaga kansa sama ruwan da dukan fuskarsa yana sauke saman faffaɗan ƙirjinsa wanda yake cike da baƙin gashi,
Sun manne da farar fatar sa,
Idanunsa da sukai jajirr kuma yaja ya rufe bayan ruwa ya gama dukansu,
Yana da ƙirar sosai ga tsayi da kuma faɗin ƙirji ƙwayar idanunsa blue ce kana ganinsa zaka tabbatar cewa shi ɗin half-caste ne (ruwa biyu)
Gaba É—aya jikinsa yana É—auke da gargasa hakan yasa yake da yawan jin zafi,
Wannan dalilin yasa bai fiya zama da complete dress ba idan yana cikin room É—in nasa,
A kasalance ya miƙa hannunsa tare da kashe shower,
Kana ya shiga wanke bakinsa da brush da yana gamawa kuma ya É—auki bathrobe fara tas ya saka cikinsa,
Ya fito daga cikin bathroom É—in kai tsaye kuma ya tsaya gaban dressing mirror,
Bai wani shafa komai ba sabida weather garin is too high!
Farin wando ya sanya wanda ya kasance 3gauther sai farar singlet,
A hankali ya sanya hannunsa ya É—auki wani perfume Tom-ford ya fesa a jikinsa a saman singlet É—in,
Duk wannan abinda yake kansa yaƙi tsayawa waje guda, sabida tsananin zafi da kuma azabar da yake masa,
Ga wani irin nauyi yau da kan yay masa yana jin komai ya tsaya masa sai wani shuuuuuu ya keji a cikin kunnuwansa!
IWC Schaffhausen Rolex ɗin dake tsintsiyar hanunsa ya duba yaga 3:48 gajeran tsaki yaja yana taune leɓansa tare da tsotsar na ƙasa ya shiga ganawa kansa a zaba,
Ƙara sauke numfashi yay yana mai tsitsyaya win a cikin glass cup kana ya kafa a saman bakinsa ya shanye tass,
Idan ta sabon shan win ya riga daya saba domin ya É—auke ta kamar ruwa ne,
Amma duk da hakan tasbihi baya barin bakinsa yanzu ma cikin ransa yake faÉ—in.
"Astagafirullah wa'atubu ilaik!"
Ƙara duban agogon yay yaga 3:50 dai-dai kuma 4:00 za'a dake wasa wanda ya kasance wasan cikin gida, ma'ana zasu buga wasa tsakanin Madrid da Chelsea.
Bayan ya gama shan win É—in ne kuma ya É—auki farar rigar Madrid ya sanya a jikinsa nan take harafin A.M ya bayyana a bayan rigar,
Da sauri kuma ya ɗauki bag ɗin ɗinsa da lemon power horse energy ya fita zuwa reception ƙafarsa sanye cikin combust.
A can reception kowa gaba É—aya Æ´an wasan sun yi gaba kaÉ—an ya rage, cikin nutsuwa yake tafiya idanunsa yay jajir jijiyoyin kansa sun fito sunyi raÉ—a raÉ—a gaba É—aya jikinsa tsuma yake,
Shi kaɗai yasan yadda ya keji, sosai naman jikinsa yake rawa kamar zai zame daga jikin ƙashi ya faɗo.
Coach É—in Madrid mai suna Carlo Ancelotti, yana ganin fitowar sa yay saurin kama hannunsa cikin harshen turanci yace.
"ABU_MALEEK time is not our side, kasancewa kai ne ma dadin Christiano Ronaldo, kawo lokacin da muka rasa Ronaldo matsayin ɗan wasan Madrid muka fara samun matsala, amma daga lokacin daka dawo club ɗin mu komai ya dai-dai-ta, da buga ƙwallonka dana Ronaldo babu bambancin sam, But why are you doing this? Kana behavior like wani mental problem"
Ya ƙare maganar yana jan hannun wanda aka kira da ABU_MALEEK ɗin wanda a taƙaice mutane suke cewa A.M
Abu_maleek sam bai fahimtar zan can Coach É—in nasu,
Banda duhu babu abinda yake gani dan haka kawai yake biye da Coach É—in har zuwa cikin wata babbar mota lafiyayyiya,
Kai tsaye kuma suka nufi *Santiago Bernabèu Stadium*
Lokacin tuni ƴan wasan Chelsea sun gama zuwa kowa yana riƙe da hannun yaronsa,
A.M na zuwa Coach ya É—auki wani yaro sai bawa Abu_maleek da sauri kuma cikin tsananin a zabar daya keji yay gaba abinsa,
Dan a duniya ko kaÉ—an bai son ganin yaro musamman Namiji, hakan na tayar masa da tsohun tsumin dake zuciyarsa,
Kai tsaye kuma ƴan wasan suna fara shiga cike da ƙwarin qwiwwa musamman yanzu da suka san cewa Abu_maleek yana tare dasu, domin shine hope ɗinsu a wasan.
Yana gab da shiga tsakiyar filin wasanne kuma yaji kansa ya tsara nan take yaga wasu stars a cikin idanunsa a hankali kuma wani majic na shekara da shekaru suka fara gilmawa ta cikin blue eyes ball É—insa,
Nan da nan kuma jikinsa ya É—auki rawa idanunsa suka firfito sosai,
Coach da tsoro ya kamasa zuciyarsa cike da fargaba ya ƙarasa inda Abu_maleek yake cikin rashin sanin abinda ke damun A.M ɗin ne kuma yasa Coach ɗin faɗin.
"Abu_maleek my champion what happened to you?"
Banza Abu_maleek yay masa a zahira ma sam baiji mai yace ba domin yanzu yana É—aya cikin duniyar tasa ya fita daga asalin
Abu_maleek É—in da suka sani,
Ganin hakan ne kuma yasa Coach cikin É—aga Murya yace.
"Abu_maleek It's 4:15 Already an take wasa me kake haka? Meye ya shiga cikin tunaninka ne? Ko kuma wasan ne baka so"
Abu_maeek ya juya da sauri sabida bazai jure ihun da Coach ɗin yake masa ba, yana ɗaga ƙafa da niyyar shiga cikin Stadium ɗin ne kuma yaji gaba ɗaya ya gama shiga ɗaya duniyar tasa a hankali ya ɗan dafe kansa yana taune leɓansa tare da furzar da iska daga cikin bakinsa cikin zafin harshe kuma yace.
"O'ohhhh"
Coach da ransa ya gama ɓaci ya ɗaga hannu zai riƙe A.m da wani irin zafin nama irin na ƴan ball da kuma juyewar tunani Abu_maleek ya sanya hannunsa ya shaƙe wuyan Coach tare da yin sama dashi.
*SHARE FISABILILLAHI SABIDA ALLAH*
_Bana sauri acikin tafiyar rubutun nan nawa, dan haka karatu za kuyi cikin farin ciki da kuma kwanciyar hankali, fatana kuci gaba da bin littafin *ABU_MALEEK* domin tafiya ce mai cike da Æ™addara za kuji sabbin abubuwa wanda dole za kuyi mamakin su amma babu mamaki a ikon Ubangiji, a next page ne kuma za kuji wani sabon part mai tarwatsa zuciya, ku nutsu ko fahimta sosai🥰☺ï¸_
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
NIMCYLUV
BOOK 1
PAGE 7-8
Idanun Coach É—in ne suka fito waje sabida tsananin azaba haÉ—i da ficewar hayyaci,
Ba ƙaramin shaƙa Abu_maleek ya yi masa ba,
Sabida ko buÉ—e idanu ba ya iyawa, A.m kam cikin rashin sanin abinda yake aikatawa yay cilli da Coach É—in gefe guda,
Yana sakin numfashi tare da fesar da iska, gaba ɗaya blue ɗin ƙwayar idanunsa ta rine tai jajirrr tamkar gauta!
Yana dafe bango cikin zafin nama kuma kamar walƙiya ya ɓace daga wajan ɓat, da idanu kawai Coach yabi bayan A.m a ransa yana mamakin wanne kalar Mutum Allah ya haɗasa da shi,
Gaba ɗaya gane inda Abu_maleek ɗin ya nufa wahala ne, kaifi ɗaya ne shi, idan yace zai yi Tabbas zai yi, duk tsayin lokacin da suka ɗauka da Abu_maleek babu wanda ya taɓa ganinsa ya tsaya da wani yana magana irin mai muhimmanci ɗin nan,
Bare kuma ai tunanin friendships bashi da yarda ko kaÉ—an, gani yake kowa zai iya cutar da rayuwarsa, da alama akwai abinda ya gana masa a zaba a rayuwarsa wanda har lokacin babu wanda ya san menene shi.
Maza na rungome matayensu amma shi wata Æ´ar farar magensa wacce yake ce mata SWEET, ita ta maye masa gurbin mata, uwa da uba,
Magen zai sanya gaba yay tai mata surutai kuma abin mamaki sosai take iya fahimtar kurman baƙin nasa,
Abu_maleek bai son ihu yanzu zaka hargitsa masa tunaninsa bare kuma ka sashi gaba kace zakai masa faÉ—a, yana da wani Æoyayyan hali wanda har yanzu babu wanda ya samu nasarar gane wane hali ne Abu_maleek yake É“oyewa wanda bai son kuma a gani? Yana da saurin É—aukan zafi da kuma saurin yanke hukunci shiyasa baya shiga sabgar duk da bai shafesa ba.
Ajjiyar zuciya Coach ya sauke tashin hankali kuma tsantsa ya bayyana a saman fuskarsa, yanzu yaya zai yi? Da wanne ido duniya zata kallesa? Musamman yanzu da kowa ya saka wa wannan babban wasan nasu ido, idan ta tabbata Chelsea sun ciye ƙwallayen ina ya dosa to? Abu_maleek shine hope ɗinsa, cikin sauri ya juya tare da shigewa cikin Stadium ɗin idan da yiyuwar ɗaga ball ɗin sai ai masa alfarma amma abu ne mai wahalar gaske.
A hankali yake tafiya yana haɗe hanya kamar ɗan shaye-shaye, daya rufe idanunsa zai fara ganin wani tsuhun tarihi yana gilmawa cikin ƙwayar idanunsa,
wanda tunusa a yanzu dai-dai yake da bugawar zuciyarsa, hannunsa dafe da goshinsa dake tsastsafar da gumin wahala,
Duk mutanan da suke hanya sai sun tsaya sun kallesa cike da mamaki domin sun san ko waye,
Wasu ma waya suke ɗaukowa suna masa vedio da picture, domin babu wanda ya taɓa ganinsa haka without his guards.
Yana tafe a tsakiyar titin yayinda ya kejin gaba É—aya duniyar na juya masa a wannan karan ko idanunsa baya iya gani, a dai-dai kuma tsakiyar kan titin ne kuma wata mota tazo da mahaukacin gudu gaba É—aya tayo kansa,
Cikin ikon Allah, motar ta tsaya cak wata ƙyakkyawar Badurwa ce a ciki sanye da ƙanan kaya masu matukar kyau da kuma ɗaukar idanu, idanunta manne cikin wani tafkeken glass,
Ganin Abu_maleek a gaban motar ta yasa ta saki baki With much surprise ta shiga kallon A.m domin kallo É—aya tai masa ta gane wanene!
Amma mamakin ganinsa ya kasa barinta ta tabbatar ce eh lallai shi É—in ne da gaske ba wani ba,
Ganin jini na zuba a gefen kansa dalilin buga kansa da yay daga jikin bango yasa tai saurin buɗe ƙofar motar ta fito,
Tana zuwa ta nufi inda yake tare da leƙa farar ƙyakkyawar fuskarsa tace.
"Sir Are You okey? The you need some help?"
Ta jera masa tambayar lokaci É—aya!
Ganin mutum kusa dashi yasa a hankali cikin rashin sanin mene yake aiwatarwa ya shiga miƙa hanunsa yana ƙoƙarin kama hannun budurwar da niyyar kare kansa daga faɗuwar da yake ƙoƙarin yi,
Ganin haka yasa budurwar saurin matsawa gabansa Musamman da taga few people suna kallon su, ita kam abin farin ciki ne a gareta da kuma ci gaba a ganta da Abu_maleek mutum mai zarrah,
Wanda sai ka shafe shekaru baka gansa ba indai ba'a t.v ba.
Abu_maleek cikin sabuwar duniyar daya shiga ta juyewar tunani da kuma win É—in data fara aiki a jikinsa yasa gaba É—aya, jikinsa ya saki yay kan budurwar baki É—aya tare da kifa kansa a saman wuyanta, tsananin farin ciki yasa budurwar faÉ—in.
"Supia my name sir, lemme help you"
Ta ƙare maganar tana ɗura hannunta a saman waist ɗinsa wanda yake da faɗi sosai, nan take ta lumshe idanunta sabida wani firgitaccen ƙamshi daya daki hancinsa.
Abu_maleek jinsa a jikin wani abu ya tabbatar masa da cewa ya samu kariya ne, a hankali yaja numfashi mai Æ™arfin gaske, tare da sauke wata Æoyayyiyar ajjiyar zuciya a hankali kuma ya shiga motsa jajayen laɓɓansa masu kauri da kuma sheÆ™i, cikin rashin sani ya manna softness lips É—insa a kunan Supia kana ya datse bakinsa da wani irin emotional sound ya ware laɓɓansa cikin tsakiyar kunanta yace.
“Sweet, Mami, Secretâ€
Ya faɗa lokaci ɗaya tare da zare bakinsa yana jin yadda zuciyarsa take masa lugude sosai, har yana jin kamar zata faso ƙirjinsa ta fito.
Da sauri Supia ta sanyashi mota tare da shiga da Wani irin speed taja motar tare da nufar gidanta.
A bakin wani tangamemen gate tai horn cikin sauri security dake gadin gidan yazo da sauri ya buÉ—e mata gate,
Kai tsaye ta cilla hancin motar cikin katafaran compound É—in gidan me cike da Flowers.
Da ƙyar ta samu taka A.m cikin gidan sabida nauyin da yay mata ga wasu surutai da yake mata wanda bata san ko mene yake faɗa ba.
Cikin farin ciki Supia ta kwantar da A.m saman makeken royal bed É—inta wanda yake É—auke da white bedsheet
Tana kwantar da shi ta nufi cikin bathroom ta sauya kaya wannan lokacin bambamcinta da tsirara babu shi,
Kana ta shiga gyara gashin kanta tana wargatsa shi, wayarta mai ƙirar Iphone 11 max pro ta ɗauka ta nufi cikin bedroom ɗin inda ta kwantar da shi domin tuni bacci yay gaba dashi.
A can Stadium kowa kamar yadda Coach ya yi tunani haka ne ta kasance, domin sam ba'a ɗaga masa ƙafa ba duk da ya shaida masu cewa ɗaya daga cikin masu buga Wasan ne babu lafiya amma sam sukaƙi yadda, haka aka fara wasa tun kafin aje ko ina Chelsea ta lallasa Madrid da ƙwallo biyu da nema.
Supia matsawa tayi sosai jikin A.m bayan tayi nasarar zame rigar jikinsa, ta shiga ɗaukan su selfie, ƙara matsawa tayi dai-dai saman ƙirjinsa ta ɗura bakinta dai-dai saman nasa nan ma ta ɗauki selfie bayan vedio'n da tayi masu yawa!
Sosai take farin cikin kasancewa da sananne wanda duniya ta sani, tana gamawa ta ɗauki bowl da tewel ta haɗa warm water ta shiga goga masa domin shi ɗaya sai zufa yake haɗawa tana gamawa ta miƙe tare da barin bedroom ɗin ta koma Parlo ta fara watching TV tana jiran tashin sa.
A can Cikin University kowa Salimerh ce zaune a cikin hall ɗin da suka gama ɗaukan lectures, ganin ita kaɗai ya rage yasa, ta ɗan taɓe baki tare da fesar da iska cikin nutsuwa ta shiga latsa keyboard ɗin wayarta tana sanya wasu Numbers, tana gamawa
Kuma tai dailing number tare da mannawa a kunanta,
Bisa mamkinta a karo na farko bayan shekara biyu kenan taji number data kira tana ringing.
Cikin Zallar farin ciki tare da nuna jin daÉ—in ta,
Ta shiga faɗaɗa fuskarta da Murmushi, kira wajan 5 amma babu response dole ta haƙura ta maida wayar jeka,
A hankali kuma wasu siraran hawaye suka shiga fita daga cikin idanunta,
Yaushe zata samu damar da zata fallasa asirin wanda zuciyarta ke zargi ne? Yaushe ne gaskiya zata bayyana a cikin Alaafin, mene yasa gaba É—aya kowa kansa ya sani?
Abubuwa da yawa suna faru, babban tashin hankalin ta bai wuce rashin ganin Queen Roomana da ba'ai ba, innocent woman like Her ace wani ya cuci rayuwar ta ya sace ta,
Domin har kawo lokacin bata yarda cewa ɓata tayi ba tayi amana da cewa wani ya ɗauke ta sabida wani banzan dalili nashi mara toshe.
Misalin 7 na dare ya shiga buÉ—e manyan idanunsa wanda sukai masa nauyi, ga wani irin raÉ—aÉ—i da suke masa,
Bakinsa ɗauke da addu'a ya fara sauke ganinsa a saman tafkeken photon Supia dake maƙale jikin bangon ɗakin nata,
Da mamaki saman fuskarsa,
Ya shiga ware gajiyayyun idanunsa wanda yake jinsu tamkar an zuba masa yaji sabida zafin da suke masa,
A hankali kuma ya shiga bin bedroom ɗin da kallo kana ya ɗaga hannunsa da ƙyar,
Ya sauke a saman ƙirjinsa nan mamakin sa ya ƙara tsananta sabida ya jisa naked babu kaya,
Jikinsa yabi da kallo yana taune leɓansa tare da runtse idanunsa cikin ƙarfin hali ya buɗe bakinsa tare da faɗin.
“O'ohhhhâ€
A hankali kuma ya miƙe tsaye tare da ɗaukan kayansa ya sanya a zuciyarsa kuma ya mamakin reason ɗin daya kawo sa cikin wannan banzan gidan,
Yana gama sa kayan Supia na shigowa,
Kallo ɗaya yay mata ya kawar da idanunsa kefe nan take yaji kuma tsanar mace ta ƙara nunkuwa ainun fiye da baya a cikin zuciyarsa,
Ko inda take bai kalla ba kansa a ƙasa idanunsa a lumshe yay waje, da sauri ta mara masa baya tana faɗin.
"Sir! Sir! Sir!"
Amma ina ko tsayawa bai ba da yaga ta fiya binsa sai ya tsaya yana kwaɓe fuska tare da marai-raice fuska ya shiga langwaɓar da kansa gefe kamar ƙaramin yaro murya can ƙasa yace.
"O'ohhhh, stay away for me Ma'ah"
Yana faÉ—in haka yay waje kai tsaye kuma ya shiga gudu kasancewar sa É—an ball ya saba da gudu yasa gaba É—aya baya jin gudun duk da cewa bai daÉ—in jikinsa ya keji ba,
Babu jimawa ya ƙarasa hotel ɗin,
A reception yaci karo da Coach kallo guda yay masa ya É—auke kai, zuciyarsa cike da tarin tambaya,
Ko wasan aka fasa yau? Mene yasa ya ganshi a gidan waccen Æ´ar shilan da baki kamar alawar madara,
A haka dai cike da sassarfa ya shige room É—insa,
Coach kawo yazo labarin Abu_maleek ya daina bashi haushi sai tsoro da yake basa,
Cike kuma da tsananin mamakin yadda yaga kamar blood a jikin farin wandonsa ya bisa da kallo!
Yana shiga room É—in ya nufi bathroom É—in sa bayan ya sutale kayan jikinsa ya sakarwa kansa shower wata wahalalliyar ajjiyar zuciya ya sauke yana matse jikinsa waje guda,
Sharp-Sharp ya yi wanka ya É—aura alwala kana ya fito É—aure da towel É—in a jikinsa.
Yana fita magensa ta taho da gudu ta haye jikinsa tana sakin ƙara wacce take nuna alamar cewa taji daɗin ganinsa kuma tai kewarsa.
Rungome ta yay sosai yana shagwaɓe mata fuska tare da motsa bakinsa yace.
"O'ohhhh my sweet i miss You"
Ya faÉ—a yana É—urata saman wuyansa tare da É—aukan wata farar Jallabiya ya sanya a jikinsa.
Tana gefensa ya gabatar da sallah, yana idarsa ta haye cinyarsa tana kallon fuskarsa,
Ƙuri yay mata da idanu sai kuma ya langwaɓar da kansa gefe guda cikin nutsuwa haɗi da kamewa da kuma zallar jarumta ya shafi kan magen yace.
"Sweet i need my mother, i need a shoulder to cry sweet, why dukkan mutane mugwaye ne, the you know what sweet?"
Kamar mai fahimtar zan cansa magen ta girgiza kanta tana buÉ—e baki, shafa kanta yay yace.
"O'ohhhh sweet na hannu da fitinanniyar yarinya,
Mai ido a tsakiyar kai, look! Duk girman jikina bata ji tsoro na ba, nikam I'm scared sweet idan naga mace zuciyata bugawa take"
Ya ƙare maganar yana sauke numfashi tare da janye idanunsa ya lumshe, zame jikinta tayi daga nasa da sauri kuma ta nufi deep frizer ɗin bedroom ɗin,
Da ƙafarta ta jawo wani basket ta shiga zaƙolo fruits irin su Apple, Inibi, strowbeery , hadda tomato's da gauva,
Da ƙafarta ta shiga jan basket ɗin zuwa gabansa,
A karon farko ya sakar mata lallausan murmushi wanda ya haddasa lomawar dimples É—insa tare da bayyanar teeths gave É—insa wacce take siririya,
A hankali yay kissing kanta tare da ɗaukan Apple guda ɗaya ya sanya bakinsa, tsananin sanyi da kuma zaƙin da yaji ya tilasta masa lumshe idanunsa har ya manta how long ya kasance babu abinci.
Jin ƙarar abu ne kuma yasa ya juya a hankali, ganinta yay tana ƙoƙarin jawo masa win hakan yasa ya taɓe bakinsa tare da taune leɓansa cikin ƙasa da Murya yace.
"It's okay! Sweet, stop hurting yourselfâ€
Apple da Inibi ta sha sosai kafin yaja sweet su kwanta saman bed É—in sa bayan ya sauka kayan bacci zuwa Panjams, ya rungome ta sosai nan take bacci ya É—auke sa.
Masarautar Kanzaf
Sosai tsaron da ake baya Alaafi ya tsananta matuƙa,
Tashin hankalin su ya ƙaro amma har kawo lokacin babu wanda yasan cewa King Tunde bashi da Lafiya,
Haka kuma babu wani labari game da ɓatan Queen Roomana,
Adams ya fice a hayyacinsa, ya rasa maka ma da kuma abinyie,
Rashin uwa ba ƙaramin giɓi bane a Rayuwar yara,
Hadima Zubaida kowa taci gaba da rike sirrin da aka bata, duk da cewa tana samun matsala amma Allahamdulillah babu wanda ya takura mata da son jin yadda King Tunde yake,
Zuwa yanzu kuma Sharefddeen ne yake zama a fada mutanan da suke zuwa kawo gaisuwa daga Kanzaf,
Ake faɗa masu King Tunde yana shirin bikin ODUN EGUN kowa ya shirya wannan ranar akwai biki wanda ba'a taɓa yinsa ba a jahar Benin ɗin.
Duk da a gefe guda jikin King Tunde ya rikice babu wanda yake fargabar bari a wannan duniya face mutum biyu, Jalaluldeen sai kuma wani giɓi na rayuwar tasa!
*GUINEA*
Tarihi Fulani makiyaya sun yi kiwo a cikin filayen da ke kewayen yankunan Sahel na Yammacin Afirka, wani bangare saboda yanayin muhalli da ke iyakance yawan filaye don dalilan noma, wanda ke haifar da gaba mai tsanani a fili tsakanin manoma da makiyaya.
bayan yawan fari a yankuna masu bushewar Sahel, Fulani makiyaya a hankali sun koma kudu zuwa Guinea savanna da yan kunan daji na wurare masu zafi, wanda hakan ya haifar da gaba kan hanyoyin kiwo tare da manoma.
Manoma sun koma arewa tare da karuwar yawan mutane.
RUGAR MAHINJO
saukar su kenan wani yanki dake ƙasar Guinea a ƙallah sun ɗauki Shekaru masu tsayi a hanya kafin su iso wannan waje mai tarin Ni'ima,
Domin waje ne mai cije da bishiyoyi da kuma ƙurama,
Gaba É—aya dai dajin ruwa ne ya kewaye shi, shiyasa yake É—auke da wani kalan ni'im taccen sanyi da kuma yashi mai É—auke da ruwa.
Babu jimawa Fulanin wanda suka kasance Fulani makiyaya suka shiga haÉ—a Bukkoki, da kuma wani gini da ake kira da “Suudu hudoâ€
Sunyi Bukkokin da ciyayi ne, tun lokacin rani shiyasa duk inda zasu suke tafiya da ita domin samun sauƙin kafawa!
Gaba ɗaya shanun wajan da kuma raƙumi da sauran dabbobi akai masu wani ƙaton waje wanda ya cinye kusan rabin filin sabida yawan dabbobin.
Sanyin safiya ne gaba É—aya fulanin Rugar Mahinjo sun tafi kiwo, hakan yasa Rugar tai shiru sai sanyi dake KaÉ—awa.
Daga can cikin wata bukka wata tsuhu ce kwance tana numfashi da ƙyar ko Idanunta bata iya buɗewa sabida tsananin yunwar data keji.
Idanunta a rufe ta miƙa hannunta tare da shafa kan yarinyar dake kusa da ita wacce ta sunkuyar da kanta ƙasa.
Gaba ɗaya yarinya ba zata wuce Shekara 17 ba, kayan jikinta fare wanda suka kasance na Fulani sunyi baƙiƙƙirin sabida dauɗa.
Tulin sumar kanta kuma an naɗeta da wani baƙin zare, duk da hakan gashin rawa yake ita kanta yay mata yawa.
Cikin kulawa Yakumbo tace.
"Ko damata maa?" (Meke damunki?)
A hankali ta shiga jan numfashi a wannan lokacin bata damu da nata cikin ba, burinta kawai ta samu abinda zata bawa Yakumbo taci,
Domin Yakumbo itace rayuwarta itace wacce take gani taji daÉ—i a duk faÉ—in wannan rugar,
BuÉ—e idanu Yakumbo tayi ita kanta ta san abu nai mai wahala ta wuce yau ba tare da aljalinta ya risketa ba, cikin tausasa murya Yakumbo tace.
"Kayi haƙuri yarona JULDE komai yau tsanani akwai sauƙi cikinsa kaji ko?"
Ta faÉ—a tana shafa kan wacce ta jira da sunan JULDE É—in,
shirun da Julde taji ne yasa ta ɗago fuskarta wacce ta ɓaci da hawaye,
Yasubuhanallah! Ubangiji yay halittar kyau a nan, fara ce tass kamar jini zai tsar tuwa a Jikinta, madadin ƙwayar idanunta ya kasance baƙi kamar na kowa sai akai dace ƙwayar Idanunta ya kasance blue amma a juye suke, tana da dugwan hanci, ga lip's ɗinta so pink.
A rikice ta shiga lalubar inda Yakumbo, cikin Muryar kuka Julde tace.
"Har ki mutu ki barni a Wanga duniya Yakumbo, kai ne komai nawa, kada ka barni a cikin wannan azzaluman Yakumbo"
Ganin da gaske Yakumbo bata motsi yasa da sauri ta lalubi inda sandar ta take,
Cikin fahimtar hanya da kuma baiwar da Allah yay mata na cikin ƙwayar Idanunta, duk da kasancewar ta Makauniya amma tana iya fahimtar inda zata nufa.
Fitowa tayi daga cikin Bukkar tana bin hanyar da sandan ta ke mata jagora hannunta riƙe da wata ƙaramar ƙwarya,
Akwai tarin dukiya a Rugar amma ita da Yakumbo É—inta sam dukiyat batai masu wani amfani ba,
Sai su wuni su kwana da yunwa ko madarar shanu ba za'a basu su gasa cikin su ba.
Ganin yanzu Lokaci fita kiwo ne yasa kai tsaye ta nufi ke wayan shanun, domin tasan dole za'a bar wasu musamman masu ciki.
Idanunta na zubar da ƙwalla, ga yadda kayan jikinta suka yage har suna shirin fito da ƙyakkyawar surar da Allah ya bata, musamman ƙirjinta a zahiri ko ruwa mutum bazai iya sha a inda Julde take ba sabida wani irin warin ƙazanta da take.
Haka take tafiya babu ko takalmi dan ma garin akwai Ni'ima.
A haka ta isa garken shanun kai tsaya inda taji kukan wata Nagge (shanuwa) tana zuwa fuskarta É—auke da Murmushi sabida jin daÉ—i da tayi zata samu madarar da zata bawa Yakumbo É—inta tasha.
Bayan ta tatsi nonon ne kuma ta É—auki hanyar komawa, tana tsaka da tafiya taji an rafka salati tare da faÉ—in.
"Shai gyan yaro mai satar madara, woooo! Su Julde anji kunya jama'a ga ɓaro mun kama"
Nan da nan aka tarawa Julde mutane sabida tsananin tsoro da firgici tuni tai cilli da ƙwarya hannunta,
Gaba É—aya suka É—auke ta zuwa wajan ARÆŠO cikin tsana da kuma Allah wadai da hali irin na Julde yace.
"Walle ka bani kunya yaro ashe duk madarar da muke rasawa kai kake sacewa kai da uwarka"
Cikin tashin hankali Julde ta shiga girgiza kanta, sosai take son magana amma bakinta ya gaza furta komai.
Babban tashin hankalin yadda bata jin maganar Modibbo, ga babu idanun gani bare taje wajansa neman taimako, wani daga cikinsu mai suna Labbo yace.
"Ai jiyama shi ne yaje har garke ya tatsi nono ƙwarya biyu"
Zaro ido ARÆŠO yayi yace.
"Wallai dole ai maka hukunci dai-dai da abinda ka shuka"
Ya faÉ—a yana kallon wani Mutum yace.
"Maza É—auko Aska"
Jin an ambaci Aska yasa Julde zubewa a wajan ta shiga rufe sumar kanta, tuni wanda akace ya É—auko Aska yaje ya É—auko ya dawo,
Yana zuwa wajan ARÆŠO yace.
"Maza aske min gashin kansa, cire sumar kai masa ƙwalƙwal"
Kasancewar Fulani mace ita suke bawa kalmar Namiji hakama namiji su bashi kalmar mace,
Ihu Julde ta sanya ta shiga kiran sunan Yakumbo da kuma Madibbo, LamiÉ—o tuni ya sanya hannunsa ya cafki sumar kanta tare da cire É—aurin nan take gashinta ya sauka har wajan waist É—inta,
ARƊO ya ƙara cewa "maza cire gashin kada abar masa komai kai masa irin na jariri arado"
Cikin rashin imani da tsoran Allah LamiÉ—o ya É—aga Askar tare da....
SALON NA MUSAMMAN NE🥰💃🻠KADA A BARKA ABAYA.
*ABU_MALEEK NA KUƊI NE, IT'S 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 GA ƳAN UWA ƳAN NIGER KUMA SUYIWA NANA AI'CHA MAGANA AKAN WANNAN NUMBER 84506476*
KASAN MUTUM NA FARKO WAJAN BIYA DOMIN SAMUN DAMAR SHIGA VIPâœðŸ½
KUYI SHARE FISABILILLAHI SABIDA ALLAHðŸ‘ðŸ»
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
NIMCYLUV
BOOK 1
PAGE 9-10
Cafkar gashin kanta, sabida tsananin zafin daya ratsa jijiyoyin kan Julde ya sanya bata san lokacin data saki wani gigitaccen ihu tare da fasa ƙara da dukkan ƙarfinta,
Wanda hakan ya ƙara haddasa juyewar blue ɗin Idanunta wanda suka gama rinewa da jaaa sabida azabar da tayi mata yawa.
Baya Arɗo yayi cikin matuƙar jin daɗi da kuma farin cikin yau ya kama ɓarauniyar da take shiga cikin garken shanun har take samun damar tatse masa madarar shanunsa,
Zabura yay cikin son dukiyarsa da kuma son bawa dukiyar tasa kariya yace.
"Billahi Yaron nan ya kashe mu, madarar shanu ƙwarya biyu, dole ai masa hukuncin da yafi wannan, dole sai kayi mana kiwon shanu na mako biyu"
Da Zallar mamaki LamiÉ—o ya tari numfashin ArÉ—o yace.
"Tayaya ne wannan ƙaramin yaron zai iya kiwon Nagge wajan guda 100?"
Murmushi ArÉ—o yayi yana mai jinjina kansa domin shi kaÉ—ai yasan dalilin daya sanya yace haka,
Ba tare daya bada waccen amsar ba cikin bada umarni ya ƙara cewa.
"Cire sumar nan yanzu wannan kuma shi ne hukumcin ɓarawon madarar shanu, barin irin wannan a Rugar Mahinjo babban hatsari ne, domin cigaban faruwar hakan zai iya kawo daƙoshewar tattalin arziƙin Fulani makiyaya, kunfi kowa sanin cewa wannan shanun sune arziƙin dukkan wani ɗan Rugar Mahinjo,
Da kuma madarar shanun muke samun kuɗaɗan kula da wasu dukkan Nagge da suke ƙarƙashin kulawar mu"
Cike da fahimta kowa na wajan yay na'am da maganar ArÉ—o, domin yay amfani da abu mafi suyiwa a zuciyar fulanin wato shanunsu,
Babu wani abu dake baƙanta ran Fulani makiyaya irin nakastuwar shanunsu.
LamiÉ—o ya jinjina kai tare da murmusawa, shi kaÉ—ai shima yasan dalilin daya sanya ArÉ—o faÉ—in hakan,
Da ƙarfi kuma ya ƙara jan sumar kan Julde wacce har yanzu ya kasa kama ƙarshen sumar sabida tsayin da gashin yake dashi,
Ganin yadda Julde take ihu tare da ƙoƙarin fisgewa zata gudu yasa Arɗon Rugar Mahinjo faɗin.
"ÆŠaure shi, maza kawo igiya a É—aure wannan mugun irin"
Julde numfashinta ne ya kusa É—aukewa sabida sabon tashin hankali,
Ita burinta a yanzu ta koma wajan Yakumbonta bata san halin da yunwa ta sanya ta a halin yanzu ba,
Da rarrafe taja Jikinta ta shiga lalubar inda take jiyo muryar ArÉ—o, duk da cewa bata gani amma tana iya bin sautin Muryar mutum ta isa inda yake.
Tana zuwa wajan Arɗo ta rirriƙesa tare rushewar da wani irin raunataccen kuka mai tarwatsa zuciyar dukkan wani mai imani da kuma tausayi,
Kuka take wanda yake nuni da irin hali ƙunci da kuma takurar da take ciki,
Kuka take da dukkan ƙarfinta zuciyarta, kuka ne wanda yake nunawa duk wani Mutumin dake wajan irin halin yunwa da kuma ƙishin da suke ciki ita da Yakumbo,
Kuka ne wanda yake nuni da halin ƙazantar da suke ciki domin rabonta da wanka a rayuwa harta manta,
Balle ai maganar gyaran jiki duk da cewa da fulanin daji irin su ba'a san so da haka ba.
Cikin muryar da kuka ya gama cin ƙarfinta tace.
"Kayi mini rai Arɗo, ka taimaki rayuka biyun da basu da wani mataimaki sai Allah, dan Allah kada ki cire min sumar kai ma, za'a min dariya kuma zan zama abin kallo da ƙyamata wajan mutanan Mahinjo,
Kaimin dukkan wani hukunci amma ka janye maganar cire min sumar kai, Ni macace ne, kada kuyi abinda zaku mai dani ta namiji,
Ban taɓa sata ba, yanzu halin yunwar da muke ciki ne yasa Ni fitowa neman abinda zan bawa Yakumbo,
Dan Allah ArÉ—o ki taimaka kada yunwa ta kashe shi, kada yunwa ya kashe Yakumbo, ka bani madarar ko kaÉ—an ne na bashi yasha"
Zame ƙafafuwansa Arɗo yayi yana ƙara kallon ƙyakkyawar fuskar Julde wacce take masa kama da wata halitta,
Kallon JULDEN kuma na ƙara ta fasa zuciyarsa, yana san yashi tuno da wani shuɗɗaɗan tarihi wanda tuno sa a yanzu dai-dai yake da bugawa zuciyarsa,
Cikin ɓacin rai yasa ƙafa tare da hankaɗe Julde wacce ta kasance bera a Rugar Mahinjo bata da kowa sai Yakumbo da Madibbo,
Da sauri kuma LamiÉ—o yazo ya fisgi gashin kanta ya fara janta jikin wata bukka,
Gaba ɗaya mutanan Mahinjo suka mara masa baya domin suma a lokacin cike zuciyoyinsu suke da tsanar Julde wacce take shirin ganin bayan tattalin arziƙin su,.
Wani tsuhu kowa tuni ya koma gefe ya kuka wiwi, sabida a jikin shanuwarsa Julde ta tatsi nono, gashin Naggen tana da ɗauke da tsohun ciki wannan dalili ya ƙara tayarwa da tsohun hankali a tunaninsa shike nan Julde ta kashe masa abinda yake cikin shanuwarsa.
Cikin rashin Imani haÉ—i da rashin tausayi, LamiÉ—o ya fara zubawa Julde ruwa mai sanyin a tsakiyar kanta tare da É—aukan wani abu mai kama da sabulu ya shiga goga mata akai,
Cikin rashin Sa'a sabulun ya fara shiga cikin nakasassun Idanunta,
Wani kalar ihu da kurnani Julde ta fara wanda sabida tsabar kuka ko muryarta ba'a ji.
Wata duguwar aska Lamiɗo ya ɗauka sabu tass da ita sai sheƙi take, ya kafa askar a gaban ƙwantaccen sumar dake gaban goshinta, tunda ya ɗura askar bai dire ba sai daya zabtare gaba ɗaya rabin sumar kan.
*ABU_MALEEK IS NOT FREE BOOK, IT'S 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616, ƳAN NIGER SUYI MAGANA TA WANNAN NUMBER 84506476*
A can cikin Bukkar su Julde kowa, Yakumbo wani kalar numfashi take,
Gaba É—aya ta galabaita takai munzalin da idan Numfashin ya fita baya dawowa, a hankali ta buÉ—e bakinta ta shiga kiran sunan Julde tana faÉ—in.
"Hai kizo nan, kizo na faɗa maki wata magana kafin Ubangiji ya ɗauki raina, Julde!! Julde!! Julde!!!...." Kafin ta ƙara cewa komai numfashinta ya fara fisga ta shiga miƙewa domin babu komai Cikinta rabon da suci abinci ita da Julde har sun manta sabida zafin talaucin da suke ciki.
Shin su ba ƴan garin bane? Ko kuma dai basu da kiwo ko guda ɗaya ne wanda za suyi taƙama dashi suma a matsayin su na Fulani makiyaya?
Ko kuma dai akwai wani dalili daya sanya su cikin wannan halin?
Tabbas ruwa baya tsami banza..
Salati Yakumbo ta fara kumfa na fita ta cikin bakinta hannunta riƙe da wani abu wanda take sakinsa, a dai-dai lokacin da Lamiɗo ya gama yiwa Julde aski tass ya zamana ko jaririn da aka haifa yau ya fita sumar kai nesa ba kusa ba,
A kuma dai-dai lokacin ne Ubangiji ya amshi ran Yakumbon Julde, wanda ta tafi lahira ne cike da burin faÉ—awa Julde wata muhimmiyar magana Amma Ubangiji ya fita sanin komai dake cikin wannan duniyar mai cike da ruÉ—ani da kuma tashin hankali,
A kuma wannan lokacin ne Madibbo yake can cikin daji yana haƙa rami da kuma ɓoye wani muhimmin abu, hakan ta sanya bai san abinda yake faruwa cikin Rugar Mahinjo ba.
A can Madrid kowa yau ya kasance weekend, wato ranar daya kasance hutu ga dukkan wasu ma'aikatan gwamnati,
11 dai-dai na safiyar lahadi wato Sunday, A.m ya shiga buÉ—e nauyayyen idanunsa wanda suke cike da tarin bacci da kuma gajiya,
Tunda ya buÉ—e idanunsa yaga duhu daga cikin bedroom É—in sabida kashe hasken É—akin da yay ya maida idanunsa ya rufe,
A hankali kuma cike da tarin gajiya da kuma ciwon da kansa yake masa a Æ´an kwanakin nan,
Ya sanya hannunsa tare da É—urawa a tsakiyar goshinsa yana murzawa a hankali sabida zufar da yaji tana tsastsafo masa,
A wannan lokacin tunani ne yake ta ziyartar ƙwaƙwalwarsa,
Wanda Yawan tunanin yake ƙara haddasa juyewar tunaninsa a koda yaushe,
Abunka da mara cikakken lafiya, wanda hankali irin na sauran mutana ne bai gama ratsa shi ba.
Tunanin Mami, da kuma kuma matar data zame masa tamkar uwa yake a wannan lokacin yake, yaya suke? Meke faruwa dasu babu abinda ya sani,
Sosai yake son zuwa gare su koda ace bazai zauna tare dasu ba,
Wata lafiyayyiyar ajjiyar zuciya ya sauke yana mai ganganro da hannunsa zuwa tsakiyar ƙirjinsa wanda yake ɗauke da kwantacciyar suma,
Mai kyau da tsari,
Fuskarsa, bugawar zuciyarsa ce ta tsananta da sauri ya sanya hannunsa a saitin ƙirjinsa yan kwaɓe fuska tare da marai-raice wa, kamar ƙaramin yaro,
Cike da tsoro ya ƙara buɗe idanunsa ya shiga rarraba su a cikin tafkeken bedroom ɗin nasa,
A sanyaye ya buɗe ƙyakƙyawan laɓɓansa wanda suke fresh so pink damn cute and softness, cikin can ƙasan maƙoshinsa yace.
"Ya Rabbi! How can that be possible?,
Mene yasa ya kejin tsoro da kuma fargaba ne?"
Ya shiga yiwa kansa tambayar can kuma yasa hannu ya ɗan matse kansa a fili cikin slow voice ɗin nan nasa mai narkar da zuciya cike da tarin shagwaɓa yace.
"You're mad Abu_maleek" zare ido yay sosai tare da pouting kansa da finger yace.
"What? Mad me? No!!! No!!! I'm not ni ba mahaukaci ba and never na zama mahaukaci"
Ya ƙare magana tana tsotsar laɓɓansa,
Ɗan juyawa yay kaɗan yana lumshe idanunsa sabida motsin da yaji a gefensa ana yaye duvet ɗin jikinsa, Sweet ce take yaye masa duvet ɗin, farar mage ƙyakƙyawa gata ƙatuwar gaske rainon madara,
Ganinta yasa ya É—an yi Murmushi har sai da dimples É—insa ya luma tare da bayyanar teeths gave É—insa kana ya sanya hannunsa ya É—auke ta cak yana shafa kanta yace.
"Mrng sweet, how was your night?"
Ya tambaye ta yana kissing goshinta, tare da rungome ta sosai ya shiga sauke ajjiyar zuciya, domin bashi da wani wanda zai magana dashi ta fahimta har ya fahimci maganar tasa a tunaninsa sama da magensa,
Yana sonta sosai, domin idan bata da lafiya sam bashi da walwala,
Kowa yana amsa sunan sa dana mahaifinsa amma shi madadin haka sai ake kiransa da sunan wani can daban, sunan da bai san lokacin daya fara ba shi dai ya riski kansa a ciki ne.
Ware idanunsa yay yana ya mutsa fuska yace.
"O'ohhh yunwa sweet lemme freshen up"
Ya faɗa yana sakinta da sauri ta sauka daga jikinsa kai tsaye shima ya miƙe sai lokacin ƙyakkyawar halittar jikinsa ta ƙara bayyana kana ganin Abu_maleek kansa cewa give of Allah bawai haka kawai ya kasance a duniya ba,
Akwai tarin ƙaddarori a tare da shi.
Kai tsaye bathroom ya shige yana zuwa ya sakarwa kansa shower, duk da cewa yau gashin akwai sanyi sosai ga snow da take ta zuba.
Ruwan shower na sauka a jikinsa yana sakin ajjiyar zuciya yana gamawa yay brush kana ya nufi mirror'n dake bathroom É—in gigice kuma yay baya da sauri sabida idanunsa da suka sauka akan.
*ABU_MALEEK NA KUƊI NE, IT'S 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 ƳAN NIGER SUYI MAGANA TA WANNAN NUMBER 84506476*
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
NIMCYLUV
BOOK 1
PAGE 11-12
*INA MARA BA DA WANDA ZA'A TALLATAWA HAJARSA (BUSINESS)*
Baƙin zanan dake saman ƙirjinsa, zuwa ƙasan cibiyar sa, gaba ɗaya zanan wanda akai da baƙin abu ya mamaye ilayin farar fatar cikinsa,
Sai ya zamana kamar anyi masa zanan Tattoo ne,
A duk lokacin daya buɗe idanunsa yaga zanan sai yaji zuciyarsa ta halba tare da buga masa da ƙarfi,
Yana samun kansa cikin ruÉ—u haÉ—i da fargaba,bai san lokacin da zanan ya kasance a jikinsa ba,
Shi dai ya buÉ—e idanunsa yaga zanan,
Menene shi? Wane yay masa gaba É—aya bashi da masiyyar komai,
Amma yana ji a ransa Tabbas akwai Æoyayyan abu game da wannan zanan,
Shiyasa baya taɓa bari wani ya gani,
Duk da cewa baya son zafi da kuma manyan kaya amma yana ƙoƙarin ainun wajan ganin ya bawa zanan kariya,
Lumshe idanunsa yay tare da cafko laɓɓensa na ƙasa wanda ya gama jiƙewa da ruwa ya shiga tsotsa tare da cijawa,
Ƙuri yaywa zanan da gajiyayyun idanunsa masu kaifi da sanya mutum cikin firgici,
Shi kansa a wannan lokacin yana son ya fahimci zanan menene? Amma duk yadda yakai dan son fahimta baya gane komai na jikin zanan,
Sai kuma baƙin zanan ya ƙara haska farar jikinsa, ya zama kamar wani adoo ne a jikin masa musamman shi da yake tare da turawa,
Cikin nutsuwa haɗi da kamewa ya miƙa hannunsa tare da ɗaukan bathrobe ya sanya jikinsa tare da covering ƙirjinsa sosai,
Idanunsa a lumshe lashes ɗin nan zara-zara, sai ɗigar da ruwa suke ga girar a cike baƙa sosai da ita.
Yana fitowa ya nufi dressing mirror yana daga tsaye ya ɗauki wani lotion mai kyau da ƙamshi ya shafa, sabida garin sosai yake da sanyi,
Yana gamawa ya É—auki body spray ya fesa saman fatarsa,
Sai kuma ya ɗauki handrayer ya shiga gyara sumar kansa, ya shafa oil a ƙwantaccen sajansa,
Nan da nan kyau da kuma haibarsa haÉ—i da cikar zatinsa suka bayyana yay wani mugun kyau like takeaway,
Wata red É—in Armless ya É—auka wacce take da zip daga gaba amma yay unzipping rigar, sai hula red daya É—auka ya sanya saman sumar kan nasa,
Ta rufe iya saman gashin banda wanda ya kwanta can ƙasan wuyansa,
Yasubuhanallah! A.m ya zama wani damn cute are extremely É—in nan,
Long wando sleeves ya sanya wanda ya kasance blue black,
Yana gamawa ya juya walking slowly ya nufi Parlo hannayensa sanye duk cikin aljihu, duk da cewa sanyin bai damunsa amma yana jin yadda tsigar jikinsa ke tashi,
A Parlo ya samu sweet kwance saman 3seater tana bacci duk ta cure waje guda,
Tattausan Murmushi ya saki wanda iya saman laɓɓansa ne kawai, gently kuma ya nufi wajan deep freezer ɗin dake Parlon ya ɗauki zallar madarar shanu mai ɗan zafi kasancewar yau setting ɗin freezer,
Yana ɗaukan madarar shanun ya cire tankar Inibi guda ɗaya a hankali cike takun ƙasaita ya juya ya zauna kusa da kitty ɗinsa.
Daɗi da garɗin madarar ya haddasa masa rufewar idanuna ba tare daya shirya ba, sosai yake son madarar shanu tana ƙara masa kuzari musamman idan ta kasance zallar ba haɗi.
Idanunsa ya rufe sabida murÉ—awar da cikinsa yay, a hankali ya shafa cikinsa wanda ya kusan haÉ—ewa da bayansa,
Daga can outside kowa wanda maid É—in hotel É—in ce ta shiga danna blet É—in door É—in tana jiran permission,
Taɓe baki yay kana ya Marai-raice fuska kamar wanda aka tilastawa magana yace.
"Come in"
Tuni daman ya buÉ—e da remote a hankali take turo table breakfast É—in nasa,
Ko inda take bai kalla ba, sai rufe idanunsa da yay ya haÉ—e rai sosai,
Ƙasa tayi da kanta tace.
"Sir! Breakfast is ready"
Shiru yay mata ita kuma ganin hakan ya sanya ta ƙara maimaita wa idanunsa a rufe yace.
"Out"
Da sauri ta juya zata fita Murya can ƙasa yace.
"Come and pick your jagwalgwalo"
Yana faɗin haka ya miƙe tare sanya hannunsa ya ɗauki sweet kai tsaye art room ɗinsa ya shiga,
Ya É—auki pen da different colors a hankali ya fara zanan idanunsa a lumshe a haka yake zanan,
Yana gamawa ya buɗe idanunsa dai-dai lokacin sweet ta farka ƙuri yaywa zanan yana kwaɓe fuska ya ɗauki sweet ya rungome tare da faɗin.
"What I'm did? Mace na zana ko namiji? Why kai babu gashi but ƙirji yay the same dana mace mai...,"
Da sauri ya shiru yana ƙara kallon zanan shikam duk sanda ya rufe idanunsa yay zanan abinda yake zanawa kenan ya rasa wacce kalar halitta ce macace ko namiji kullum kuma idanun a rufe suke mikewi yayi tare da rungome sweet wacce take ƙara shigewa jikinsa.
Alaafi Kanzaf
(Masarautar Kanzaf)
Da sauri yake tafiya cike da tashin hankali, ko inda Barori da Fadawa suke baya kalla,
Bare ya samu zarafin amsa masu gaisuwar da suke masa,
Yana tafe sanye da baƙar Alƙyabba mai ratsin fari,
Idanunsa sun kaÉ—a sunyi jajir sabida tsananin tashin hankali da kuma damuwar da yake ciki,
Kai tsaye sashin Mai Babban É—aki ya nufa,
Yana zuwa masu tsaron ƙofa suka buɗe masa, cikin sauri ya sanya kansa ciki,
A babban parlo ya sameta zaune saman wata haÉ—aÉ—É—iyar ladduma, an cika gabanta da kayan itatatuwa,
Yana zuwa ya zauna a gabanta tare da haɗe ƙafafuwansa waje guda fuskarsa nan tasa kamar hadari babu walwala sam ko guda a cikinta,
Ganin yanayin da Adams ke ciki yasa Mai Babban É—aki fahimtar Tabbas akwai abinda yake damunsa, ko kuma ya samu wani labari akan Mahaifiyar sa Queen Roomana.
Cikin nutsuwa da kuma son kwantar masa da hankali tace.
“kiloshèle?†(Meke faruwa?)
A hankali ya É—aga idanunsa da suka rine da jaa,
Ya kalli Grandma ɗin tasa cikin yanayin dakewar zuciya da son ɓoye mata abinda ke faruwa dashi,
Ɗan ƙasa yay da Muryarsa very slow yace.
“shè Oba wani Aà fin?†(King yana cikin Masarauta?"
Da mamakin tambayar rainin hankalinsu ta kallesa, ba tare kuma da tace komai ba taci gaba da duba azkar ɗin hannunta kasancewar ta mace mai tsananin riƙo da addini.
Ganin yadda Mai Babban ɗaki ta share tambayarsa yasa Adams yaji zuciyarsa ta ƙara gamsuwa da abinda yake shirin faruwa a cikin Alaafin ɗin,
Yau kimanin sati guda kenan babu King Tunde Muhammad Jalal a cikin fada, ko tirakar sa babu mai shiga,
Ga tsananin da aka ƙara a cikin Alaafin ɗin, ko ina ka zaga securitie's ne ta ko ina, ba kuma iya cikin Alaafin ɗin abun ya tsaya ba,
A'a hadda cikin Kanzaf ɗin, abinda ya ƙara tada hankalin sa da kuma jama'ar dake cikin Kanzaf ɗin,
Domin babu wani bikin ODUN EGUN da aka taɓa yi aka shirya wannan tsaron sai na wannan shekarar,
Cikin nuna rashin damuwa yace.
"Wani abu na faruwa a cikin Alaafin ana ɓoye mana, menene wannan abun, wannan tsaron duk na menene? Shin mu baza mu iya kare Alaafin daga abin cutarwa bane sai an kawo wasu securitie's? Mene yasa King Tunde baya fitowa? Ance MALEEK ya mutu mene yasa bamu ga gawarsa ba why all this happened?"
Ya ƙare maganar in a commanding tune.
A É—an gigice Mai Babban É—aki ta kalli Adams, cikin Zallar mamaki da kuma al'ajabi ina ya samu wannan maganar? Yaya akai yasan cewa MALEEK ya mutu?
Cikin haÉ—e gira sosai tace.
“Kilodé to fè má inkán ton shèlé Ni Aaafin? Omà da ti obálé gbágbé oró na, ko béré sini ronú ibi ti iya re Oloori Roomana wá, shé won ti ku tábi won wá layé? Lati ma inkán ton shélé Ni Aaafin ma soro gidigà n. Kodi dádán Kori gbogbo owùn to shélé Adamsâ€
Abinda tace a hausance Shine “Mene yasa kake son sanin abinda yake faruwa a cikin Alaafin? Zai fi kyau ka manta da wannan zan can, ka fara tunanin inda Mahaifiyar ka Queen Roomana take, da gaske tana raye ko kuma ta mutu? Sanin abinda yake faruwa a Alaafin zai maka matuÆ™ar wahala, kuma sai sanya baka son abinda ba lallai ka samesa ba Adamsâ€
Kallon Mai Babban É—aki yay yace. "I have the right to ask, É—an uwana yay nesa dani, an wayi gari babu Mami, yanzu ana maganar jinin É—an uwa na, yanzu kuma almost 1week babu King Tunde, then Aremo Sharefddeen shike Zama a madadin King Tunde a fada"
Jinjina kai Mai Babban ɗaki tayi, idan hankalinta yay dubu to ya tashi, ganin bata da niyyar magana yasa Adams ya miƙe a fusace tare da yin waje.
Da idanu ta bishi domin tuni ta fahimci zafin kishi ke damunsa na ganin Sharefddeen a kan kujerar karaga.
Adams na fita ya haÉ—u da Iyalode ( Jakadiya) a hanya tana tafe tana Æ´an dube dube kamar mara gaskiya,
Kwallon yadda bakinta yake rawa yayi, alamar dai akwai abinda yake cin zuciyarta, washe baki tayi tare da suma yi masa kirari sosai, domin shi ne bai fiya sakar mata fuska ba, sabida kasancewar sa mutum bai jin kansa da kuma tarin izzar Sarauta,
Kallonta yayi fuska babu yabo ba fallasa yace.
"Tauraruwa mai wutsiya..., Kura kike ga tsoro ga ban tsoroâ€
Ya ƙare yana cije bakinsa tare da binta da kallo, for the frist time kenan da yaji yana son yaji salon nata gulman dan haka ya bata all his attention.
Murmushi tayi tana ƙara waigawa kafin ta numfasa tace "Gobara daga Teku maganinta sai Allah, wani kaya ne ya sauka nasan za kaji daɗin kayan, musamman idan kaga launin su, amma kada ka faɗawa kowa nice na fara sauke maka tallan kayan kaji ko?"
Jinjina kai yay tana shafa ƙwantaccen sajansa kafin yace.
"Kice yau dawa tayi nama kenan, ta ina kayan ya sauka? A kuma hannun waya sauka?"
Da sauri tace.
"Naji labarin cewa, Oba zaiyi murabus wannan dalilin ya sanya Aremo Sharefddeen yake zama a fada ma dadin King Tunde, Ni kowa nace wannan ai son zuciya ne, da nuna bambanci ko dan anga babu idanun uwar É—aki na"
Sai kuma ta fashe da kuka,
Tare da kama bakin zani ta shiga sharce majina da gefen zaninta, kana tace.
"ALLAH sarki uwar ɗaki na, nifa sam ban yarda da ɓatan ta ba, ƙilama ƙuruciya akai mata sabida mugun nufi"
Nan take zuciyar Adams ta hau bugawa idanunsa ya ƙara yin jaa da sauri yace.
"Naji daɗin wannan labarin, akwai kyauta mai tsoka anjima zan nemeki, amma da Sharefddeen ya hau kujerar nan ƙwara ni dashi mubar duniyar"
Yana faÉ—in hakan yay gaba kamar shirwa, har wani duhu yake gani a cikin idanunsa,
Yana barin wajan Aremo Shakiru na zuwa tun daga nesa Iyalode ta saki kuka tana rafka salati,
Da mamaki Shakiru ya kalleta kafin yay magana tace.
"Muhammadur Rasulullah (S.A.W) ashe kowa mugu ne, wallahi mutumin nan ranka yake nema, nikam nace sam bazan yaudareka ba, yooo ina dalili fisabilillahi? Gashi dai fari tass dashi kamar nunanniyar kabewa amma baƙar zuciya garesa kamar yadda fuskarka take baƙa"
Cikin rashin fahimta Aremo Shakiru yace.
"Meke faruwa? Waye? Kamata ace za'a ga baya na? Never wallahi?"
Cikin ƙara matso ƙwallar idanunta tace.
"Abun ba daɗin ci, nikam nace ƙilan yau ba zaka iya bacci ba, yanzun nan Aremo Adams yake tambaya ta, wai Meke faruwa menene sirrinka domin yasan ni kaɗai na san komai naka"
Dariya Shakiru yay sosai kafin yace.
"Nasan hakan zai faru, dan haka babu wanda yasan abinda nake shiryawa rabo dashi kawai, komai yace maki ki faÉ—a min"
Kai ta É—aga masa a zuciya take faÉ—in "É—an banza da hanci kamar bushasshen kifin miya"
Yana faÉ—in haka ya yi gaba abinsa,
Dariya sosai Iyalode (Jakadiya) tayi tace.
"Me nayi yanzu? Na ƙara wuta fetur kenan? Yanzu aka fara wasan?"
*ABU_MALEEK PAID BOOK NE, BIYA KUƊIN KI, DOMIN KASANCEWA MUTUM TA FARKO WAJAN SHIGA VIP GA PROMO ƊIN DANA BAYAR, IT'S 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 ƳAN NIGER SUYI MAGANA TA WANNAN NUMBER 84506476*
Washe gari da maraice, Salimerh na zaune a lambu, iska mai daÉ—i tana kaÉ—a yalwaraccen ganin kanta,
Tana sanye da Black Silk short robe, La Perla company's, hannunta riƙe da wani ƙaramin bowl mai kyau cikinsa cike da cin cin da Samosa, daga gefenta kuma wata duguwar kujera ce mai kyau, irin ta hutawa,
Gaba É—aya lambun cike yake da shukoki.
Yanzu saura 1week bikin ODUN EGUN kuma shi ne mutumin daya dace ya fita matsayin Masquerade amma baya nan yay za tayi yanzu? Shine kaɗai zai iya dakatar da komai cikin sauƙi, wayarta ta ɗauka a hankali ta shiga dailing number sa, cikin Sa'a number ta fara ringing,
Kamar a mafarki taji yayi answering call É—in, da sauri ta juya domin ta tabbatar cewa babu kowa, cikin farin ciki har hawaye na zubu mata tace.
"ZAKI!" Sai kuma tai Shiru saboda kukan da yaci ƙarfin ta, jin yana ƙoƙarin kashe kiran yasa da sauri tace.
"Akwai Matsala zaki, how long zaka kasance a inda kake? Shin zaka dauwama a inda kake ne? Mene yasa baka tunanin kabar ni, kamar Abba, kamar Mami? Please come back to us kaji Zaki"
Shiru tayi tana sauraran abinda yake cewa duk da ba wata magana yake mai tsayi ba, amma yadda yake Maganar kaÉ—ai zaka san cewa bai saba dayin maganar ba, ga voice É—in nan very slow kamar mara lafiya,
Kuka ta sanya masa sosai tana ɗan buga ƙafarta, can sai dabara ya faɗo mata da sauri tace.
"What? King Tunde ya mutu? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!"
Shiru tayi sabida jin yadda yaja wata wahalalliyar ajjiyar zuciya mai ƙarfi, cikin farin ciki tace.
"Ok Zaki, come back soon, but nan da 3days kaji"
Jin ya amsa da "ok" yasa ta kashe wayar tare da miƙewa tsaye, tana ɗan tsallan farin ciki, domin idan har Zaki yazo to tabbatas komai yazo ƙarshe (anya?).
Da sauri Junaid take bakin ƙofar shigowa yay sauri ya juya cike kuma da tashin hankali, ya nufi sashin Otun (Galadima).
Mai Babban ɗaki da Oumuu-Ayman zaune a saman dinning table suna yin dinner a hankali suke magana yadda babu mai jin abinda suke cewa, Oumuu-Ayman na Shirin yin magana su kaga Bola ta ƙarasu wajan ita da Hadimanta, kamar zata tashi Idanunta ya kumbura saboda kukan data sha,
Tana zuwa ta kalli Mai Babban É—aki da Oumuu-Ayman kafin cikin kiÉ—ima tace.
"Da gaske MALEEK ya mutu? Shin da gaske ne an zubawa King Tunde Muhammad Jalal Goba a cikin Abin shansa? Da gaske ne kuma MALEEK ɗin ba mutuwa yayi ba ɓoye sa akai?"
*FREE PAGES YA KUSA ƘAREWA🥱 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616*
Wata zufa ce ta shiga karyuwa musu, gaba É—aya tashin hankali ya gama baiyana a fuskokinsu, kenan Hadima Zubaida ce ta yaÉ—a Wannan maganar ko mene? Ko kuma wani ne yake bibiyar su ya kejin abinda ke faruwa da kuma abinda suke shiryawa?
Oumuu-Ayman bata iya magana ba, sai sunkuyar da kanta tayi ƙasa tunu Jikinta ya fara rawa shikenan kashin su ya bushe, rayuwar MALEEK ta faɗa garari.
Mai Babban É—aki cike da nutsuwa ta kalli Bola tace.
"Ina kika samu wannan labarin mai kama da almara fa?"
Nan take Bola ta zaro wayarta tare da danna wani vedio nan take fuskar Hadima Zubaida ta bayyana, a tare cikin kuma tashin hankali da kuma rashin Sanin abinyi suka miƙe tsaye tare da haɗa baki sukace.
"Hadima Zubaida!!!?"
*ABU MALEEK, IT'S 500 08119237616*
Rugar Mahinjo.
Tashin hankalin da Julde da Madibbo suka shiga ba'a magana,
Julde ta ƙara shiga rayuwar ƙunci da kuma baƙin ciki,
Yanzu bata da kowa mai sonta sai Madibbo,
Bukkar aka shigo Madibbo ne riƙe da ƙwarya wacce ya ciko ta da Madarar shanu,
Jikinta duk rawa yake saboda yunwar daya gama cinta,
Idanunta na zubar da hawaye ta kafa kanta a ƙwayar ta shanye Madarar shanun tass.
Da kallon tausayi Madibbo yabi Julde a ransa yake tunanin tabbas yanzu lokaci Yayi da Julde zata san komai,
Da sauri ya miƙe ya fita bayan bacci ya ɗauke Julde wacce yanzu ta koma namiji sanadiyyar askin da akai mata, tudun manyan ƙirjinta ne kaɗai zai tabbatar maka cewa Julde macace,
Sabida Allah ya albarka ce da manyan ƙirji so ma sha Allah!
A can wajan Bukkar kowa, ArÉ—o ne da LamiÉ—o sai É—an gidan ArÉ—o mai suna Barkido, ArÉ—o yace.
"Domin tabbatar da ƙudirinmu akan wannan yaron Julde dole sai ya zama Namiji"
Gaba É—aya suka kalli ArÉ—o, Barkido yace.
"ArÉ—o Tayaya mace zai zama Namiji kamanta da kalar Halittar su da nono ne?"
Dariya ArÉ—o yayi yace.
"Wannan ba matsala bace, zamu sanya ƙwarya mu murje Nonon nata, yadda zasu koma ƙanana daga nan kuma zamu sanya igiya mai faɗi mu ɗaure sauran"
LamiÉ—o yay dariya yace.
"Amma menene damar maida Julde namiji?"
Barkido ne ya cafki zan can da faÉ—in.
"Domin zamu turata kiwo tare da addini shanu guda É—ari, kasance wa har yanzu muna samun barazana ga mutanan da bamu san ko su wanene ba, to matsalar yanzu basa kashe mata, mu koma burin mu a kashe Julde, wannan dalilin ya sanya zamu maida Julde namiji"
A tare suka saki dariya kana ArÉ—o yace.
"Maza Lamiɗo jeka ka ɗauko mana Julde naga Madibbo ya fita yanzu, shima da sannu zan nemu abinda yake ɓoyewa"
Can jikin dare kowa ya kwanta bacci, Julde na kwance tana bacci sai sauke Ajjiyar zuciya take, ga kannan nata sai ƙyalli yake, can cikin baccinta taji an fara janta da sauri ta farka ta shiga lalubar sandanta cikin siririyar muryarta tace.
"Madibbo na?"
Shiru taji hakan ya sanya ta ƙara buɗe baki zatai magana taji anyi......
SHARE FISABILILLAHI PLEASE HABIBATIES🥰
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
NIMCYLUV
BOOK 1
PAGE 13-14
Modupé pupo lowó éyin alá báko èwé , modupé gidà ni owó yin, papá juló *Elegant online writers,* áti *Mumyn Real ladingo*, *Anuty Zuwairiyyah gere*, mótún dupé lowó *Anuty Nazeefa sabo nashe*😠modupé pupó pélu bi éshé gbáruku tÃmi *Oga Nasir nid*🙇ðŸ¾â€â™€ï¸ áti gbógbó *Online writers* monà iféyiñ gidigà n, *Billygaladanci,* *Mai dambo*, Iyawo *mss flower,* modupé *Haseenatou,* epó gidigà n, omó iyamî *BABYLUV* moni ifé yin dadá
Sama da ita, tare da sanya tafin hannu aka toshe mata baki, duk yadda Julde tasu buÉ—e baki domin tayi ihu ko zata samu mataimaki kasawa tayi,
Da rayuwar ƙarfinta ta shiga kokawa da mutumin amma ina, tuni yasa mata ƙarfi tare da yin waje da ita tana sakin tattausan murmushi mai cike da mugunta, haɗi da wasu manufofi yay waje da ita,
Yana tafe yana duba hanya gudun kada yayi karo da Madibbo.
A can cikin wata bukka wacce take ƙarshen rugar Mahinjo yaje ya sanya Julde ciki, yana fitowa Arɗo da Barkido ka zuwa,
Cikin tarin farin ciki wanda ya kasa ɓoyuwa a saman fuskar Arɗo ya dubi Lamiɗo yace.
"Hee za kaje ka riƙe ta, Barkido kuma ya rufe mata baki, Arado ni da kai na zan murje wannan rushehen abun"
Murmushi LamiÉ—o yayi cike da gamsuwa da zan can na ArÉ—o yace.
"Suu shai muyi maza kada wani ya tashi cikin daran nan, babu da wani lokaci"
Barkido wanda tunda suka tsaya bai magana ba, ya kalli ArÉ—o yace.
"Baka jin shi yaron zai waÉ—awa wani?"
Buga sanda ArÉ—o yay yace.
"Aii shaii ya waÉ—i naji? Wallahi ina kaishi lahira da wannan sandan nawa"
LamiÉ—o ya amshi maganar da faÉ—in.
"Babu wanda zai zamu bari yaji wannan zan can, har shaii burin mu ya cika Arado"
Yana faÉ—in hakan ya shige bukkar Barkido ya mara masa,
Sai kuma LamiÉ—o ya mara masu baya gaba É—ayansu suka shige Bukkar da LamiÉ—o ya sanya Julde a ciki.
Allah sarki baiwar Allah! Tana zaune ta cure waje guda,
Dukkan Jikinta rawa yake, ga babu idanun ganin ma suyi mata wannan cin zarafin, balle kuma tayi tunanin gudawa,
Fuskarta tayi jajurr sabida kukan da take kawo yanzu ko muryarta ba'a ji, sai Ajjiyar zuciya take saukewa, da sauri ta É—ago kanta,
Sabida sahun tafiyar da taji da kuma tsaiwar da taji anyi a kanta,
Ba tare da sunyi magana ba, gudun kada ta fashimci su waye a kanta,
Da sauri Barkido yayi bayan Julde tana Shirin ja baya ya wani sa hannunsa ya jawota baya, tare da tsugunawa,
Ya haɗa dukkan ƙarfinsa ya matse bakin Julde, Ganin hakan ne kuma ya sanya Lamiɗo shima ya durƙosa dai-dai inda take,
Tare da sanya hannunsa ya riƙe ƙafafuwan ta sosai, daman Barkido ya haɗa da hannayenta ya riƙe,
Cikin zafin nama kuma ArÉ—o ya fito da ludayin duma, irin babban nan mai É—an faÉ—i,
Kana ya durƙosa dai-dai ina take riƙe da hannunsu Barkido,
Jikinsa har rawa yake sabida burinsa bai huce yaga buƙatarsa ta biya,
Burin da yake dashi na shekara da shekaru ace ya cika ba,
Ƴar ƙaramar rigar dake jikinta irinta Fulani wacce ta kasance ƴar guntuwa,
Hannunsu ya saka ya É—aga rigar, nan take manyan tsayayyun brest É—inta suka bayyana wanda duk cikinsu babu wanda bai zare idanunsa ba,
Suka shiga kallon juna sabida yadda brest ɗin ta suke da tsayi gasu farare tass, ga nippy ɗin so pink ma sha Allah! Barkido da zuciyarsa ta buga da ƙarfi kuma ya ƙasa ɗauke idanunsa daga kan halittar nata, fesar da numfashi yayi kafin ya ɗago kansa ya kalli Mahaifin nasa Arɗo kana ya maida idannunsa kan Lamiɗo da wani irin sauri kuma ya.
*Free pages ya kusa ƙarewa🥱 hanzarta biya, it's 500 via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616*
Mayar da idanunsa kansu, kana cikin zafin nama yay ƙasa da kansa da niyyar sanya baki,
Cikin sauri ArÉ—o ya taresa tare da faÉ—in.
"Babu wannan a tsarin mu, ardon Allah ka kiyaye ni"
Jinjina kai kawai Barkido yay amma jikinsa duk rawa yake, Arɗo tattara nutsuwarsa yayi, cikin rashin tsoran Allah, da kuma rashin imani ya sanya ludayin Dumar a saman halittar ƙirjin nata,
Ya fara dannawa tare da murzawa da dukkan ƙarfinsa, Yasubuhanallah! Wani irin gurnani Julde ta suma jikinta ya ɗauki mazarin azaba, ga wani irin numfashinta mai kama dana ɗaurewar rai ya fara fita daga cikin hancinsa domin ko ihu ta kasa sanadiyar danne mata baki da Barkido yayi,
Ganin ludayin Dumar ba yayi masa yadda ya keso ne, ya sanya ya ɗauki ƙwarya ya shiga murjesu da ita,
Nan da suka fara yin ƙasa, sabida tsanani azabar da yayiwa Julde yawa tuni ta sume a jikin Barkido ga wani fitsarin wahala daya kwace mata,
Ganin yayi yadda ya keso ne, ya sanya ya ɗauki igiya ya shiga naɗe ƙirjinta da ita,
tuni ƙirjin ya faɗa wata sabuwar wahalar ta ƙara farfaɗo da ita, ko motsi ta kasa sai kumfa da take fitarwa ta cikin bakinta tana fidda numfarfashi, ƙirjinta yay mata wani bala'in nauyi da ƙyar zuciyarta take harbawa,
ÆŠauka ta suka sakeyi tare da mayar da ita cikin bukkar suna barin wajan Madibbo na zuwa.
A can Alaafi kowa, tashin hankalin da Oumuu-Ayman ta shiga har ba'a magana,
Mai Babban É—aki kowa abin tamkar almara yazo mata,
Kenan da gaske dai Hadima Zubaida ita ta fidda Sirrin da suke ɓoyewa? Kallan Amintacciyar Hadimar tayi wato Hadima Akin tace.
"Maza jeki nemo min Hadima Zubaida yanzun nan"
Da sauri Hadima Akin ta miƙe tsaye tare da faɗin "faɗe taki cikawa tawa"
Tana faɗin hakan ta miƙe tsaye tare da ficewa waje,
Shiru Mai Babban É—aki tayi tana nazarin abun, babu mai fidda wannan maganar face Hadima Zubaida,
Amma mene yasa ta aikata hakan? Ko dai daman bada zuciya guda take tare dasu ba? Ajjiyar zuciya ta sauke kana ta sanya hannunta ta cire Apple guda tare da kaiwa bakinta,
Hadima Zubaida na zaune hannunta riƙe da wani ƙaramin jariri fari tass dashi, tana bashi nono, idanunta ta lumshe har yanzu gaskiya zatai halinta ne? Har yaushe za taci gaba da zama a haka ne? Mene ya sanya rayuwa take mata haka ne? Tana jin tausayin mutanan cikin Alaafin ƙwarai da gaske, amma bata da ikon karesu daga abinda yake ƙoƙarin samunsu,
Jin kamar alamar za'a shigo mata ne ya sanya ta miƙe da sauri tare da zuwa wajan akwati ta sanya jaririn ciki, kwana ta dawo wajan ƙofar tana ɗan goge hawayen idanunta,
Kallon juna sukai ita da Hadima Akin kafin Hadima Akin ta shaida mata umarnin Mai Babban É—aki,
Ba tare da tunanin komai ba Hadima tace.
"Yanzu zan amsa kira in sha Allah"
Murmushi Hadima Akin tai mata kana ta juya tare dayi mata sallama,
Da sauri ta juya tare da ƙara bawa Jaririn Mama bayan yasha sosai bacci ya ɗauke sa, kana ta mayar da shi akwatin dake can ƙuryar ɗakin ita kuma ta fita bayan ta rufo daƙin.
Bola kasa zama tayi ta tashi hankalin kowa, ita dai kawai a fito mata da MALEEK, ga zance ya riga ya fito dole a É—auki MALEEK a bata duk da irin hatsarin dake bibiyar rayuwar Maleek É—in.
King Tunde na kwance bayan yaji dukkan abinda ke faruwa, ya kuma tabbatar cewa Hadima Akin baza ta taɓa aikata hakan aresa,
Cikin mutuwar jiki da kuma fidda rai da rayuwa ya miƙe tsaye tare da ɗaukan sandar girmansa, yabi wata siririyar hanya wacce babu wanda ya san da ita,
Kai tsaye shashin Hadimai yabi harya isa wani É—aki, a hankali ya zaro wani key ya buÉ—e É—akin, kai tsaye ciki ya shige yana zuwa ya nufi wajan akwatin tare da sanya hannunsa ya É—auki jaririn dake kwance cikin akwatin yana bacci,
A gefen gadon ɗakin ya zauna yaywa jaririn ƙuri da idanu, kafin a hankali ya cikin sauri kuma ya.
*Mace mai aji, da kuma cewa ita wata ce, ita kaÉ—ai zata gujewa abin sata, kiji tsoran Allah idan kin biya kada ki fitarwa waje, ina masoya a motsa a fara payment lokacin ya kusa*
Rungome jiririn tsam a saman ƙirjinsa, yana jin so da kuma ƙaunarsa na ratsa Dukkan wata ƙofa ta cikin Zuciyarsa,
A hankali a hankali kuma ya shiga sauke ajjiyar zuciya kafin ya sakko da jaririn ya shiga duba baƙin zanan dake saman ƙirjinsa zuwa ƙasan cikinsa, wani ƙaramin siririn zoban Azurfa ya sanyawa jaririn,
Kana ya miÆ™e idanunsa cike da soyayyar jaririn ya mayar da shi cikin akwatin kafin yabi Æoyayyiyar hanyar ya koma sashinsa ba tare da kowa ya ganshi ba.
Hadima Zubaida tana fitowa sashin Mai babban ɗaki ta nufa, tana zuwa bata sha wata wahala ba, kasancewar masu tsaron ƙofar sun san Wacece ita,
Bakinta É—auke da Sallama ta shiga, Oumuu-Ayman ce ta amsa mata, sai kuma Queen Ayoola kana Mai Babban É—aki, daga can gefe kuma Bola ce sai share hawaye take,
Tunda ta gansu taji zuciyarta ta buga da ƙarfi cikin dauriya taja jikinta tare da ƙarasawa inda suke,
Kana ya zube a gabansu cike da girmamawa ta shiga gai dasu, Queen Ayoola ce ta amsa mata, sai kuma Oumuu-Ayman, Mai Babban ɗaki da al'ajabin Abin yaƙi sakinta sai kallon Hadima Zubaida take,
Mace har mace mai fuskar nutsuwa da kuma haquri amma ace duk yadda suka ɗauke ta Shine zatai masu zaƙon ƙasa? Lallai duniya ba kowa zaka yarda kuma ka aminta dashi ba,
Gyaran murya Mai Babban É—aki tayi cikin nutsuwarta haÉ—i da sakin fuska ta dubi Hadima Zubaida tace.
"Kina da girma a idanuna sosai, wannan dalilin girman ya sanya King Tunde Muhammad Jalal ya amsheki matsayin Amintacciyar Hadimar sa, shakera da shekaru muna faɗa maki dukkan wani sirri namu, kin san komai amma mene yasa a lokacin da kuma gama baki yadda da kuma dukkan wani aminci namu ke kuma kike mana zaƙon ƙasa kike son ganin kin kai mu ƙasa? Zubaida kin ruguza dukkan wani shirin mu, maƙiya wanda babu san ko suwaye ba yanzu sun samu dama akan MALEEK da kuma Mutanan Alaafin haɗi da jama'ar Kanzaf mene yasa kika aikata haka Hadima Zubaida?"
Tunda Mai Babban É—aki ta fara magana,
Hadima kuma Jikinta ya É—auki rawa, tashin hankali ya gama bayyana a saman kamilalliyar fuskarta,
Tsoro da kuma tashin hankalin abinda ke shirin faruwa ya gama ratsa dukkan wasu kofofin zuciyarta,
Wata zufa ta shiga karyo mata, abinka da mai É—an yan jiki,
Bakinta kawai rawa yake ta kasa furta komai dabida yadda abinda yazo mata a bazata.
Mai Babban ɗaki baya tayi a hankali ta ɗan jan casbahar hannunta, sosai tashin hankalin data gani a saman fuskar Hadima Zubaida ya ƙara ɗaga mata hankalin, tsoro abinda zai faru da Hadima Zubaida ya shiga yawo a zuciyarta,
Sosai take tausayinta tasan kuma ba lallai ta aikata hakan ba, Amma babu wanda yasan ɓoyayyan Sirrin nasu sai Hadima Zubaida, dan haka dole ta amshi hukuncin daya dace da abinda ta aikata, ajjiyar zuciya ta sauke tana ƙara kallon Hadima Zubaida kafin tace.
“O dalé Hadima Zubaida†(kinci Amana Hadima Zubaida).
Kana ta É—ura da faÉ—in
"Idan Sirrin mu ya fita wanne abu kika faÉ—a da bakinki wanda za'a É—auki hukunci a kanki Hadima Zubaida?"
Hadima Zubaida a fili ta sauke wata zazzafar iska idanunta ya cika da ƙwalla, shikenan wannan mai bibiyar rayuwarta ta tayi nasara, ta samu abinda take buƙata, yanzu ina zata saka amanar data amsa? Ina zata sanya ɗan ƙaramin jaririn da bai san komai ba, waye zai Kula mata da innocent boy ɗinta? Oumuu-Ayman kasa kallon Hadima Zubaida tayi saboda tsakanin tausayin data bata,
Bola wacce a yanzu bata buƙatar komai sai ganin Maleek ta ƙara fito da wayarta tace.
"Ina zaune Hadimai nayi Mani tausa sai gashi ta nemi iso waje na, gaba ɗaya ta shigo min afirgice, ganin Hadima Zubaida bata taɓa zuwa sashina ba, ya sanya na bawa Hadimai na Umarnin fita domin naga alamar akwai Magana a bakinta, kamar nasan da wannan abun na shiga yi mata vedio ha tare data sani ba"
Da sauri Hadima Zubaida ta kalli Bola cike da tashi hankali, kasa magana tayi yaushe taje wajan Bola? Yaushe ta zauna sa Bola ta faɗa mata wannan maganar? Innalillahi wa'inna ilaihir Arjun! Tabbas akwai masu buƙatar wani abu a tare da ita da kuma Maleek kana King Tunde babu kuma abinda zata iya faɗa wanda zai wanketa, to surar mata da take jikin vedio'n ta tabbatar cewa Hadima Zubaida ce, domin shigarta da komai da muryarta duk ita ce, sunkuyar da kanta ƙasa tayi trying to remembered abinda ya huce amma bata iya gane komai.
"Kiyi magana mana Hadima Zubaida, domin ƙila kina da abinda zai iya kareki daga wannan musamman abun"
Cewar Oumuu-Ayman wacce tausayin Hadima Zubaida ta gama cika mata zuciya,
Baki Hadima Zubaida ta shiga motsawa, bisa mamakin ta tuni harshen ta Ya maƙale, ta shiga buɗe baki a ƙoƙarin na son cewa wani abu, amma ta gagara magana sai abu take kamar kurma,
Murmushin takaici da kuma sabon rainin hankalin da Hadima Zubaida tazo musu dashi, Queen Ayoola tuni hawaye ya wanke mata fuska saboda rayuwar zuciyar da take dashi,
Gyaran murya Mai Babban ɗaki tayi cikin ƙaramin lokaci wasu zaratan maza wanda suka kasance masu tsaron gidan kurkukun cikin Alaafi suka shigowa,
Da wani irin sauri Hadima Zubaida ta miƙe tsaye tana masu nuni hannayenta alamar jaririnta amma babu wanda ya saurareta,
Wani irin raunataccen kuka Hadima Zubaida ta miƙe tana riƙe ƙafafuwan Mai Babban ɗaki,
Cikin damuwa mai Babban ɗaki ta miƙe tsaye tare da faɗin.
*It's 500, via 0116886423 sulaiman Naima s union bank, free pages sun kusa kammala*
"Kusan hukuncin da akewa wanda yaci amanar Masarauta, Ello ti sì inú yárá okún Hadima Zubaida (kuje ko ɗaure ta a ɗakin duhu) ɗakin ƙarshe, sai lokacin da aka ɗibar mata ya cika"
Tana faÉ—in hakan tai gaba abinta domin itama zuciyarta a raunace take na tausayin Zubaida,
Ganin yadda Hadima Zubaida ke maganar kurame gashi basa fahimta yasa ɗaya daga cikinsu ya daka mata wata gigitacciyyar tsawa tare da tisa ƙeyarta zuwa kurkuku wacce take can bayan Masarauta.
Tsaro sosai aka ƙara a cikin Alaafin sabida Dawowar JULALUDEEN TUNDE MUHAMMAD JALAL, kawo lokacin kuma babu wanda ya san da dawowar Jalaluldeen sai Salimerh da Oumuu-Ayman kana Mai Babban ɗaki, Oumuu-Ayman da kanta ta shirya tsaro mai girma da kuma tsanani a cikin Alaafin, dawowar Mutumin da suke ta saka rai sai gashi Ubangiji ya amsa addu'ar su, ya dawo da shi a lokacin da ake buƙatarsa.
_Madrid_
A nutse ya sakko da dugwayen ƙafafuwan sa dake sanye cikin Black brian Atwood brand loafers kafin ya fito baki ɗayan sa, cikin Ralph Lauren brown suit data ƙara fiddo da asalin zallar kyansa da kuma farar fatarsa ta asalin KapurShab.
Kallo guda zakai masa kasancewa cewa Tabbas shi É—in Mutum ne na musamman, sabida haiba da tarin kamalar dake tare dashi,
Yana da kwarjini hakan ya sanya ba kowa ke iya jaa dashi ba, kana kallonsa zaka É—auka mai cikakken hankali ne amma idan ya samu juyewar tunani sai kowa ya raina kansa.
Cikin nutsuwa da kamala haɗi da kamewa yake taka ƙafafuwansa a filin jirgin zuwa cikin jirgin, yana tafe hannunsa riƙe da jibgegegiyar Kitty ɗinsa,
Fara tass da ita, sai kwantar da kai take a ƙirjinsa, time to time ya hakan taune leɓansa kana ya lumshe idanunsa, daga bayansa kuma wasu guards ɗin sane ke biya dashi tare da kayansa,
Baya taɓa tafiya dasu infact ma mancewa yake dasu, a hankali ya fara taka strains ɗin jirgin a can vip ya zauna sweet ɗinsa a jikinsa, tun a airport ɗin ne kuma guards ɗin suka juya bayan sunyi masa fatan alkairi,
A hakan jirgin ya ɗaga zuwa sararin samaniya, tafiya ce ta wasu hours a haka jirginsu yay saukar ungulo a airport, shine mutum na ƙarshe wanda ya fito,
Yasubuhanallah gaba ɗaya kallo ya dawo kansa musamman ƴan matan da suke airport, kyawawan blue eyes ball ɗinsa ya lumshe, a hankali yaja dugwan numfashi yana ƙara buɗe ƙofar hancinsa ya shiga shaƙar iskar Nigeria,
ÆŠan siririn tsaki yaja saboda kallon da yaga ana masa, shi sam bai ga abin kallo jikinsa ba, shima mutum ne kamar kowa meyasa suke kallonsa kamar shi É—aya ne a cikin airport É—in.
Sweet ce ta zame daga jikinsa ta fara gudu, dafe kai yay a hankali ganin tana shirin basa wahala a hankali ya furta.
"O'ohh come here sweet",
Ya faɗa yana sauka daga strains ɗin jirgin, nan kallo ya ƙara dawowa kam ABU_MALEEK,
da sauri ya sanya fararan hannunsa ya ɗauke ta cak, yana taɓe baki tare da marai-raice fuska, da sauri kuma ya juya ya shige jikin wata ƙaramar Honda Amaze blue black, yana shiga akaja motar da wani irin speed tare da barin cikin airport ɗin.
Queen Ayoola ce tsaye Idanunta ya kaÉ—a yayi jajurr sabida kuka, Aremo Adams dake tsaye gabanta yana son yaji dalilin daya sanya ta kirasa,
Cikin kuka Queen Ayoola tace.
"Nasan za kace ƙarya nake, ban taɓa tunanin haka zata kasance ba, ban taɓa tunanin ɗan uwanka wanda kuke uwa ɗaya uba ɗaya dashi zai ci amanarka ba"
Cikin rashin fahimta Adams ya É—an zaro manyan idanunsa cikin son jin abinda ke faruwa yace.
"Meke faruwa? Me kike son faÉ—a ne Mumy?"
Hannunta ta sanya saman shoulder É—insa tana sakin kuka tace.
"Believe me My son Adams, ba zan maka ƙarya ba, ina son faɗa maka gaskiyar abinda yake faruwa saboda ka daina tunanin
Mahaifiyar ka Queen Roomana ta mutu"
Jin an ambaci sunan Queen Roomana ya sanya Adams jin gabansa ya faɗi zuciyarsa ta shiga bugawa da ƙarfi, cikin ɗaga murya yace.
"What happens to my mother? Where is she?"
Ya ƙare maganar cikin ɗaga murya jijiyoyin kansa duk ya tashi,
Cikin tausayin Adams É—in tace.
"Adams É—an uwanka shine ya É—auke mahaifiyarka sabida gudun kada ta tuna masa asiri, yayi amfani da soyayyar da take maka ya É—auke ta sabida yaji labarin kai za'a bawa Sarautar Kanzaf"
Dafe kai Adams yayi yana fesar da numfashi kafin yace.
"Waye? Wanne É—an uwan nawa daga cikin guda huÉ—u?"
Kai tsaye tace masa.
"JALALULDEEN TUNDE MUHAMMAD JALAL"
SHARE FISABILILLAHI SABIDA ALLAH DA ANNABIðŸ‘ðŸ»
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
NIMCYLUV
BOOK 1
PAGE 15-16
Da wani irin firgici Adams ya runtse idanunsa, yana jin saukar maganar ta Queen Ayoola kamar saukar ruwan sama,
Tayaya JALALULDEEN zai É—auke Mami?
Mene ya sanya ya aikata hakan?
Akan wanne dalili? Mene hujjar Jalaluldeen da zai sanya a É—auke masa mahaifiya?
Tayaya akai ya faru? Bayan shi É—in ba mazaunin gari bane?
Hannunsa ya sanya tare da share zufar data yanko masa,
Cikin KaÉ—uwa da kuma tashin hankali Aremo Adams yace.
"Mumy! Ina kika samu wannan labarin wanda jinsa dai-dai yake da bugawar zuciyata, kada ki sanya na tsani jinina kuma É—an uwa ne"
Ka faÉ—arsa ta dafa tare da É—an matsawa ka É—an tace.
"Haba Adams Tayaya kake tunanin zan sanya maka tsanar É—an uwanka, na faÉ—a maka haka ne domin na isa na shaida maka abinda ke faruwa"
Kuka ta sanya masa tana ƙara faɗin.
"I'm just care about your mother ne, noting else dake da Jalaluldeen ai duk ɗaya ne, kasan Jalaluldeen he's stubborn bazai taɓa tsayawa yaji abinda zan faɗa masa ba,
Amma kai zaka iya tararsa kai tsaye ka faÉ—a masa, ko baya so dole ya saurare ka Tabbas zaiji maganarka Adams, ina cikin damuwa da tashin hankalin rashin Mahaifiyarku"
Jinjina kai yay cike kuma da son Queen Ayoola ya É—an bata side hug tare da faÉ—in.
"I'll talk to him Mumy, tabbas zan nuna masa kuransu dole duk inda ya kai min Mami ya fito da ita"
Kansa ta shafa kasancewar yau nrml shigar Yaruba yayi ko hula bai sanya ba bare wata Alƙyabba kafin tace.
"Let me have my way, kasan an fara shirin bikin ODUN EGUN"
Jinjina kai yayi domin baya jin zai iya magana a dai-dai wannan lokacin, tunani da kuma baƙin cikin abinda Jalaluldeen ya aikata wa mahaifiyar su,
Cikin damuwa yaja ƙafarsa tare da shigewa sashinsa, yana zuwa kayan jikinsa ya zame tare da faɗawa saman 3seater, tsaki yaja kana ya ƙara Miƙewa tsaye ya nufi fridge ya ɗauki ruwa mai sanyi yasha a hankali ya shiga sauke ajjiyar zuciya,
Sabida tafasar da zuciyarsa yake masa, a ransa yana kissima abinda zaiwa Jalaluldeen da zarar ya dawo, baya tunanin zai iya jiran dawowar sa dole yabi jirgi zuwa Madrid.
Da wannan tunanin Adams ya kwanta saman kujerar bayan ya gabatar da sallar Asar!
Da wani irin gudu ƙaramar motar ta shiga ta can bayan motarsa inda ƙofar baya take, wanda ba'a buɗe ta,
Daga ƙofar kuma zuwa sashinsa babu nisa, yana jin gine a bayan motar idanunsa a lumshe ya ringing sweet sosai wacce take ƙoƙarin kwacewa sabida mugun riƙon da yayi mata bana wasa bane,
Kwaɓe fuska yayi sabida wani irin bugawa da zuciyarsa take masa,
Kamar zata faso ƙirjinsa ta fito saboda yadda take harba masa,
Tafin hannunsa ya sanya ya É—an tura cikin sumar kansa ya shiga hargitsa tulin sumar try to control his self,
Amma abinda ya kejin yafi ƙarfin ya samu nutsuwa,
Idanunsa a lumshe yaji anyi parking a motar, a hankali ya shiga buÉ—e idanunsa mutanan kuma daya gani yasa yayi saurin maida idanunsa ya rufe,
Ganin securitie's ɗin ne kuma ƙara sanya shi gasgata zan can Salimerh, Tabbas akwai abinda ke faruwa a cikin Alaafin,
Bawai dan za'ai bikin ODUN EGUN ya sanya aka haÉ—a wannan tsaron ba,
Jin ƙarar buɗe murfin motar ne ya sanya ya ɗan ƙara buɗe idanunsa ganin Oumuu-Ayman ya sanya shi shagwaɓe fuska,
Cikin faɗaɗa fuskarta cike kuma da farin ciki ta miƙa masa fararan hannunta,
A karo na farko daya yayiwa wani murmushi kenan, cikin nuna jin daɗin ganin Oumuu-Ayman yasa A.M sakin lafiyayyiyan murmushi yana tsotsar laɓɓansa,
Tare da sanya tafin hannunsa cikin na Oumuu-Ayman, lumshe idanunsa yay lallai ya tabbatar yayi missed family nasa,
Yana fitowa daga cikin motar ya É—an matsa kusan Oumuu-Ayman tare da shigewa Jikinta,
A hankali ya sauke Ajjiyar zuciya lallai Tabbas yayi rashin jikin uwa, jikin Oumuu-Ayman kaÉ—ai yasa yaji nutsuwa inaga ya shiga jikin Miminsa?.
Kansa ta shafa tana É—an Murmushi mai sauti tace.
"Wlcm back zakin zakuna"
Jinjina kai yay ba tare da yace komai ba, da sauri securitie's É—in suka shiga shimfiÉ—a masa wani farin carpet mai É—auke da sunan JALALULDEEN TUNDE MUHAMMAD JALAL.
ganin ako wanne lokaci wani zai iya zuwa duk da cewa ba lallai ba, a hakan yasa Oumuu-Ayman sakinsa tare da yin gaba,
Cikin nutsuwa Abu_maleek ya sanya hannunsa tare da É—aukan sweet,
Sarai yaga Salimerh yana sane kuma da kallon da take masa na ya naga guy É—in nan ya zama Bature ne,
Carpet É—in ya shiga takawa hakan yasa da É—an sauri Salimerh tabi bayan A.m, yana gama shigewa sashin Salimerh ta shiga, securitie's É—in suka rufe da sauri tare da jan motar suka bar wajan,
Suna barin wajan Aremo Shakiru na zuwa kunansa maƙale da waya.
A.m kai tsaye sashinsa ya nufa ganin hakan yasa Salimerh yin gaba tare dabin wata hanya tabar sashin gaba É—aya,
Domin babu wanda ya taɓa shiga sashin A.m dan haka ta rabu dashi sai ya huta sosai zata nemesa,
A gajiye ya shiga kutsawa cikin tafkeken sashin nasa wanda yake É—auke da part biyu, amma da part 1 yake amfani,
Komai na sashin fari tass parlon farko wasu haÉ—aÉ—É—un kujerun ne farare dasu,
Sai fridge da ƙatuwar t.v ga a.c ta ko'ina sabida sam bai son zafin,
Tun daga ƙaramin parlonsa wanda daga shi sai bedroom ɗinsa ya fara zame kayan jikinsa, sweet kam tuni ta fara tsalle,
Yana zuwa bedroom ya faɗa bed ɗinsa tare da lumshe idanunsa yana cije bakinsa Wheel zuciyarsa na wani irin bugawa da ƙarfi wacce bai san dalili ba.
Turo baki yayi yana shafa sumar kansa tare da jan nippy ɗinsa a sanyaye cikin zazzaƙar Muryarsa yace.
"Yeah, i love my family but zaman Alaafin it's difficult to me, ihu, surutai, hayaniya cai cai cai i hate Wannan Al'adun, Ya Rabb!"
Ya faÉ—a yana dafe goshinsa,
Miƙewa yayi tare da shigewa bathroom y sakarwa kansa shower ruwa mai sanyin gaske ya shiga sauka a saman farar jikinsa, da sauri ya shiga sauke ajjiyar zuciya so da ƙaunar ganin Maminsa ya saukar masa,
Uwa mahaifiya yau kam a jikin Maminsa zai kwana.
Murmushi ya saki yana tsotse ruwan dake saman lips É—insa a fili yace.
"She will be proud of me, nasan za tace na zama ƙatutu na zama saurayi big boy, and I'll tell har faɗa zan iya tarewa kai na, bana faɗa ma Mimi cewa zanyi ƙarfi ba"
Ya faɗa yana jinjina kai irin saima wani ya taɓa sa ɗin nan.
A haka ya gama wankan ya fito sanye da bathrobe, jikinsa yana É—igar ruwa ya É—auki wata Armless mai shot hand ya sanya kana ya zuga zip É—in,
Sai 3gauther daya sanya ya fesawa jikinsa turare,
Wani Vally’ Slippers ya sanyawa fararan sawayansa,
Kafin ya ɗauki ribbon ya tare sumar kansa waje guda ya ɗaure, murɗaɗɗan jikinsa ya bayyana sosai, ya zama ƙato mai cikar zati da haiba ga kuma tarin kwarjini,
Kai tsaye fita yayi daga sashin ya nufi main Parlo ɗan zaro idanunsa yayi saboda ganin Oumuu-Ayman zaune da table ɗin lunch yana ganinta ya shagwaɓe fuska,
Tare da ƙarasawa kusa da ita ya zauna ba tare da yace komai, ba tare da tace komai ba ta shiga haɗa masa lunch ɗin Yam-flour (Amala) sai Ofada rice with Efo riro (vegetable soup) yana jin ƙamshin abincin ya lumshe idanunsa tare da matsawa sosai kusan Oumuu-Ayman ya matsu yaji abincin a bakinsa sosai yayi missed traditional food ɗin su.
Abincin ta É—auka zata basa a baki, yace.
"No! Oumuu"
Kai ta girgiza masa tace.
"Yaushe rabon dana baka abinci a baki"
Lumshe idanunsa yay Lokacin daya buɗe ƙaramin bakinsa ta sanya masa abincinsa, daɗin abincin ya sanya ya lumshe idanunsa tare da ƙwace spoon ɗin a hannun Oumuu-Ayman yana faɗin.
"I'm 35 yrs Oumuu, so I'll peed myself na girma yanzu"
Jinjin daɗin ganin Jalaluldeen yasa Oumuu-Ayman ta kasa ɗauke idanunta daga kansa, ya zama wani ƙatoto kamar basamude.
Duk kallan da take masa yana sane, a haka yaci abincin sosai kana yasha ruwa mai sanyi,
A hankali yayi hamdala kada ya kwanta jikin Oumuu-Ayman tare da juya mata bayansa ta gane abinda yake nufi, bayansa ta shiga shafawa har sai da yayi ƙyasa kamar jaririn da yasha Nono.
Miƙewa yayi zubbur da sauri itama Oumuu-Ayman ta Miƙe tare da faɗin.
"Ina zaka kuma, yana da kyau ka huta kasan babu wanda yasan ka dawo, kuma bana son a san ka dawo har sai bikin ODUN EGUN yazo"
Girgiza kai yayi a can ƙasan maƙoshinsa yace.
"Oumuu, Mami nake son gani, ina son naga how is she, then Dady wallahi i missed them sosai"
Zuciyar Oumuu-Ayman ta buga da ƙarfin gaske ta san cewa wannan surutan ita kawai zaiwa sai Mai Babban ɗaki da King Tunde da Mami, banda haka tari ma sai ya zama dole zai yisa, amma ya zama dole ta faɗa masa komai sabida sai yafi fahimta rashin gaya masan kuma babbar ilane, yanzu zai hauka Alaafin ta san halinsa tun yana Ƙarami har kawo lokacin daya bar Alaafin saboda ƙaddarar data faɗa masa, kama hannunsa tayi ta zaunar tashi cikin nutsuwa tace.
"Abu_maleek abubuwa da yawa sun faru, ina fatan zaka fahimta da kuma saurara, nasan baka shiga sabgar kowa amma a wannan lokacin dole ka sanya idanu a kan takun kowa, dole ka kwatarwa kanka Æ´an ci da kuma É—aukan mataki akan wanda suke son ganin bayanka"
Kallonta yayi da idanunsa wanda suka fara sauya kala kafin ya sauke numfashi ba tare da yace komai ya maida kansa ƙasa tare runtse idanunsa ya shiga taune leɓansa.
Cikin nutsuwa ta zayyana masa dukkan abinda yake faruwa, daga ɓatan Queen Roomana zuwa rashin lafiyar sarki, kawo ɓoye Maleek da sukai, zuwa Ɗaure Hadima Zubaida.
Tunda kafin ta gama magana jikinsa ya ɗauki ɓari jijiyoyin kansa suka miƙe tsaye,
Banda karkarwa babu abinda jikinsa da yake musamman kansa.
Ganin abinda ke shirin faruwa ya sanya ta riƙe sa sosai, tare da kama kansa ta shiga tofa masa addu'a, almost 10minute kafin ya shiga sauke ajjiyar zuciya a haka har bacci ya ɗauke sa.
Zamewa tayi ta kwantar dashi saman kujerar tare da ƙaro gudun a.cn kana ta fita.
Rugar Mahinjo
Tun daga lokacin dasu Arɗo suna ganawa Julde azaba, basu ƙara waiwayar inda take suna jiran ranar da suka ɗaukan mata ya cika.
Julde kam kullum da wani irin azababban ciwon ƙirji take kwana, har lokacin kuma ta kasa faɗawa Madibbo abinda akai mata,
Har lokacin kuma igiyar da suka ɗaure mata nono tana jikinta dalilin daya sanya take kasa Numfashin yadda ya kamata. Rayuwa tai mata zafi da ƙuna duniya tai mata duhu sosai babu wanda take buƙata a yanzu face wanda zai taimake ta, ya ɗauke ta daga cikin Rugar baki ɗaya.
*Gobe in sha zan gama free pages wanda suka kasance na farko wajan biya za'a sasu a vip, ma'ana inda za'a dinga posting biyu kullum kenan*
Tun daga wannan lokacin Abu_maleek ya daina fara'a bare walwala Hatta Oumuu-Ayman daina yi mata magana yayi,
Ya keɓe kansa shi ɗaya baya cin komai sai fruit sosai yake neman wanda zuciyarsa zata tattauna dashi amma ya kasa bawa Kowa wannan damar.
Æangaren Adams kam shirya yadda zai tafi Madrid yake domin yaje yaji dalilin daya sanya Abu Maleek ya sace masu uwa.
Kawo lokacin kuma babu wanda ya san da zuwan Abu Maleek É—in.
Kwanci tashi babu wahala Yau ya kasance gobe ya kasance ranar da Za'ai bikin ODUN EGUN tun yammacin yau manyan sarakuna da kuma manyan mutane jirginsu ya dinga sauka a garin Benin.
Mutanan Kanzaf kowa ka gani yana cikin farin ciki musamman daya kasance zasu haÉ—u da nagartaccen Oba É—insu mai jin tausayin su.
Tun a Subhi tsaron Alaafi ya tsananta baka ganin komai sai securitie's,
Shiri na musamman ake, har lokacin kuma babu wanda yasan cewa King Tunde Muhammad Jalal babu lafiya.
Biki yayi biki taron jama'a a cikin Alaafi ba'a magana, banda busa da sarewa haÉ—i da kide-kide babu abinda ake.
Wani mutum ne ya shigo filin wajan an rufe masa jiki ana kiÉ—a yana rawa wasu kuma suna Performance magic,
Bayan haka aka dafa doya aka bawa Kowa, sannan aka raba wa kowa emu (win) daga nan aka fara sanarwar ga King Tunde Muhammad Jalal ne zai fito yaywa jama'ar Kanzaf godiya ya kuma shaida masu yana mulki cikin jin daÉ—i da kwanciyar hankali.
A hankali ya shiga sauke sandar hannunsa a ƙasa yana taka ƙafafuwansa cike da zallar isa haɗi da kamewarsa, yayi shiga ta sarkin Yaruba, ya rufe fuskarsa,
Sai kirari ake masa ana buga tambura, Abu Maleek runtsa idanunsa yayi yana jin kansa kamar zai rabe gida biyu,
Idanunsa yayi jajurr saboda kiÉ—an dake hawar masa ka,
Da wani irin sauri kuma zuciyarsa ta shiga bugawa tashin hankalin ya ƙaro,
A hankali ya shiga É—agawa jama'ar wajan hannu alamar gaisuwa har ya isa mazauninsa yana shirin zama, maimakon ya zauna sai aka ga ya zabura tare da yin.
*DAN ALLAH ALLAH DAN ANNABI KADA KI SIYI LITTAFI NA DA NIYYAR YAÆŠA MIN SHI, KIJI TAUSAYI NA, KI DUBA GIRMAN ALLAH DA ZATINSA, IDAN KINA SO KI SIYA DOMIN ABINDA KAKE SO BAZAI TAÆA FIN ƘARFIN KA BA*
Baya ya juya da sauri dafe da kansa ya juya masa yana jin kamar zai rabe gida biyu,
Da mamaki gaba É—aya jama'ar wajan suka fara bin bayansa da kallo, sam ba haka King Tunde Muhammad Jalal ya zaba yin bikin ODUN EGUN É—insa ba,
Abu Maleek kai tsaye part É—insa ya shige yana jin kamar duniyar zata kife dashi.
Yana shiga ya fara cilli da kayan jikinsa yana watsarwa,
Taune leɓansa yayi tare da sanya hannunsa ya dafe kansa dashi, cikin ƙasa da Murya yace.
"O'ohhhh"
Wannan alama ta cewa gab yake da shiga É—aya duniyar tasa tunaninsa na neman juyewa.
Saman bed ya faɗa yana ƙanƙame jikinsa waje guda, ga wani irin ɓari da jikin nasa yake masa, a haka bacci yay gaba dashi,
Da ƙyar yayi sallar Subhi, a lokacin ne kuma zan can rashin lafiyar King Tunde ya bazo a cikin Alaafi dama Kanzaf baki ɗaya, al'amarin daya tayar da hankalin jama'a kenan kuma an rasa ta yadda zan can ya fasu.
Misalin 11 na safe Abu Maleek na zaune saman kujera watching TV amma gaba É—aya hankalinsa baya ga abinda yake kalla,
Tunanin sabuwar rayuwar daya tsinci kansa ya yanzu ita take masa yawo a zuciya shi kam sam bazai iya ba,
Madrid zai koma bazai iya zama cikin Alaafin ba abubuwan cikinta sun sama girma.
Da sauri ya miƙe ya shiga haɗa kayansa, yana shirin fita aka shigo Sashin nasa da sauri kallon juna sukai shida Salimerh wacce Idanunta ya kumbura saboda kuka cikin tashin hankali tace.
"Abu Maleek kazo inji Mai Babban É—aki, jikin Dady ya tashi sunanka yake kira"
Wani irin dafe ƙirjinsa yayi saboda tsallan da zuciyarsa take masa,
Bata tsaya jiran komai ba taja hannun Abu Maleek zuwa sashin King Tunde Muhammad Jalal.
Tun daga bakin babbar ƙofar yasan cewa Tabbas babu lafiya, idanunsa ya runtse tare da tura kansa ciki,
Gaba É—aya kallo ya dawo kansa, idanun Kubraah da Bola ne suka firfito saboda tsananin mamakin ganin mijin nasu,
Sharefddeen, Shakiru, Adams, da kuma É—an gidan Otun (Galadima) wato Junaid duk suka tsora masa idanu da Alhinin ganinsa, hakama Otun yabi Abu Maleek da kallo,
Babu kamar Queen Ayoola.
Babu wanda ya kalla a cikinsu ya nufi wajan mahaifin nasa tare da zuwa wajansa hankali tashe saboda ganin baya motsi sai kumfa dake fita a bakinsa, jikinsa yayi wani mahaukacin zafi.
Miƙewa yayi zai fita saboda sai a lokacin ya tuna shifa likita ne mai zaman kansa.
Otun ne yay gyaran murya da sauri Malamin dake duba Kinga Tunde Muhammad Jalal yace.
"Ciwonsa bana asibitin bane, domin samu maganin da zai warkar da King Tunde Muhammad Jalal dole ne aje BIRNIN BERA"
gaba É—aya suka haÉ—a baki wajan faÉ—in "BERA??"
kai ya jinjina masu yace.
"Tabbas, a can ne kawai zai samu wani babban Malami ya bashi maganin da za'a bawa King Tunde,domin mutum shike ne kawai yake da wannan maganin, dan haka a cikin Aremos dole É—aya zashi"
Adams najin haka ya miƙe tare da ficewa a hankali Shakiru ma ya miƙe alamar ba zasu wannan garin da ake cinye mutanan da ransu ba,
Kai tsaye Sharefddeen yace.
"Ga Abu Maleek nan I'm sure zashi, Daman shine yake son tafiyar nesa"
Kubraah da Bola suka shiga girgiza kai alamar ba zashi ba shima.
Oumuu-Ayman ce tace.
"Tayaya Abu Maleek zashi garin da babu wanda ya sani, kusan shin da ƙin yarda babban matsalar kuma kunfi kowa sanin ciwonsa lokacin da ciwon ya tashi Tayaya zai kare kansa? Waye zai taimaka masa?"
Kafin wani yay magana Abu Maleek yace.
"Zani, ku shirya tafiyar zuwa gobe"
Jinjina kai Malamin yayi yace.
"Domin zuwa Birnin Bera, dole ka zama mahaukaci, domin za kace kai kake fama da ciwon, dole za'a aske maka gashin kanka, za'a cire maka sumar fuskar ka, kuma dole za'a shafa maka baƙin fenti domin basa son farara mutane, idan ba haka ba kana zuwa sukai ido huɗu dakai suka kalli fatar jikin ka fara to Tabbas sai dai wani bakai ba.....
*KUN SHIRYA...????? GUY'S U CAN START YOUR PAYMENT 500- VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616*
SHARE FISABILILLAHI SABIDA ALLAH DA ANNABIðŸ‘ðŸ»
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
NIMCYLUV
BOOK 1
PAGE 17-18
Da wani irin sabon tashin hankali Oumuu-Ayman ta shiga girgiza kanta,
Abu Maleek ko a jikinsa ya shirya idan har Mahaifin nasa zai samu lafiya,
Ya rasa uwa mahaifiya dan haka ba zai yi saken da zai rasa mahaifin sa ba,
Oumuu-Ayman ce taka numfashi tare da kallon makamin gaba ɗaya hankalinta yaƙi kwanciya da wannan tafiyar da Jalaluldeen zaiyi,
Cikin damuwa tace.
"Jalaluldeen zai zauna da mahaifinsa, zan sanya É—aya daga cikin fadawa suje nemu maganin"
Da sauri Makamin ya girgiza kansa yace.
"Hakan bamai yiwuwa bane, jinin King Tunde Muhammad Jalal ake buƙata yaje da kansa, idan ya shirya tafiyar zan faɗa masa ta ƙasashen da zaibi"
Kafin kowa yayi magana Abu Maleek dake zaune ya rungome King Tunde a hankali ya fesar da numfashi tare da sauke ajjiyar zuciya,
Cikin rashin damuwa da haÉ—arin da tafiyar take dashi yace.
"Gobe zan tafi, ka faÉ—i da komai na tafiyar"
Gaba ɗaya suka kallesa, sosai Abu Maleek ke ƙaunar iyayensa kamar yadda suke ƙaunar sa,
Cikin fahimtar maganar ta Abu Maleek Malamin yace.
"Ta kasashe biyu zaka shige ƙasar dake gaban Guinea itace Birnin Bera, zaka tsaya a wata rugar Fulani, wacce ake ce mata Rugar Mahinjo, daga nan zaka samu dukkan bayanan da zai sadaka da Birnin Bera"
Ya faÉ—a yana zaro wata peper daga cikin aljihunsa,
Kana ya É—ura da faÉ—in.
"Wannan taswirar wajance koda zaka ɓata a hanya, kana duba taswirar zaka Fahimci inda kake"
Abu Maleek bai ce komai, idanunsa akan fuskar King Tunde Muhammad Jalal wanda kawo yazo ko buÉ—e ido baya iyawa,
Hannunsa ya ƙanƙame a hannun Abu Maleek,
A cikin ransa ji yake inama zai iya buÉ—e baki yayi magana ko kuma zai iya rubutu,
Da babu abinda zai sanya yabar Abu Maleek ya yi wannan tafiyar,
Yayi imani abinda suke tunani sam ba haka bane,
Shi kaÉ—ai yasan abinda ya samesa jiya bayan kowa ya tafi wajan bikin ODUN EGUN.
Oumuu-Ayman ce ta amshi taswirar idanunta ya ciccika da ƙwallar tausayin Abu Maleek da kuma halin da zai iya tsintar kansa a cikin tafiyar.
Sallama Malamin yayi masu kana yabar wajan Otun ne ya miƙe tare da mara masa baya saboda rakasa hanya.
A sanyaye Abu Maleek ya kwantar da king Tunde, kana ya gyara masa kwanciya, ba tare daya kula kowa na wajan ba, ya nufi sashinsa fuskarsa a É—aure kamar hadari.
Yana miƙewa Kubraah ta miƙe tare da mara masa baya, yana tafe dafe da kansa Kubraah na bayansa, sarai yaji footsteps,
Amma bai kawo cewa Kubraah bace, shi harga Allah mantawa yake yana da wasu mata,
To ba dole ya manta ba, aure har biyu without his permission,
Babu wacce yana so daga ciki gwamma Auran Bola ƙaddara ta haɗa Auran,
Amma ko a yanzu da zai san gaskiyar dake ɓoye Tabbas itama da bazai zauna da ita ba,
Shi babu mace a sabgarsa, mantawa yake akwai wani abu dake shiga tsakanin ma'auratan,
To kuma ya sani ba sai yana da lafiyar yi ba, yana shiga Main Parlo nasa ya tsaya cak,
Sabida yana son yajin dalilin daya sanya Oumuu-Ayman take biyosa, idan ma tazo domin ta hanasa wannan tafiyar to tabbatas ta makara,
Yana nan tsaye yana sauke numfashi tare da taune leɓansa wanda sukai jajirr saboda yawan tsotse su da yake,
Bai an kara ba yaji Kubraah ta faÉ—a jikinsa ta baya tare da rungomesa.
*Karatun ABU MALEEK yana buƙatar nutsuwa, daman na faɗa maku salonsa nada banne, zazzafar soyayya ce wacce tafi ƙarfin a haɗa ta data Laylerh da Majanun, balle kuma ta ROMOE DA JUILET, zata fi dacewa ka haɗa ta da Film ɗin TAITAINIK🥰💔*
Wani irin sarawa kansa yayi ransa ya ɓaci sabida tsabar raini, kamar shi wata zata haɗa jikinta da nasa,
Cikin sabon wani ɓacin ran, ya wani juya da sauri tare dasa hannunsa ya ɓanɓareta a jikinsa,
Kuka Kubraah ta sanya tare da ƙoƙarin ƙara rungomesa,
Da wani sauri yaja baya ya shiga nuna mata hanyar fita daga sashin nasa, cikin kuka tace.
"Why? Mene yasa Abu Maleek? Ni matar kace, tunda akai Aure na dakai babu taɓa magana ba, ban taɓa sanyaka a cikin idanuna ba, balle na zauna muyi magana dakai har naji ɗumin jikinka,
Nifa macace ina da rauni idan zaka iya zama ba tare da mace ba, ni sam ba zan iya zama babu namiji ba, da haƙurin mata dana maza ba iri ɗaya bane,
Ka tausaya min Abu Maleek ka sauke haƙƙin dake kanka kafin ka tafi, babu da tabbacin zaka dawo a raye ko kuma ajalinka zai riskeka a can ne, pls My dear try to understand my feelings"
Tunda ta fara magana ya kafeta da Manyan gajiyayyun idanunsa, so itace second wife É—in da Salimerh tace King Tunde ya aura masa ita,
Why duk samarin gidan sai shi za'a aurawa mata har biya, matanma da babu wacce ya taɓa cewa yana so,
Ko kuma É—an taure ya zama suna ganinsa yana bin mata a guje shiyasa sukai decided na aure mace ba tare da izininsa ba,
Shi gaba É—aya baiga abinsu a jikinsu, ko wacce Æ´ar banza da nono bai fi tafin hannunsa ba,
Gajeran tsaki yaja tare da juya zai shige part ɗinsa yaji ta ƙara.
*Yau free pages zasu ƙare hanzarta biya domin ki zama mace ta farko da zata shiga vip, it's 500 for vip posting biyu kullum, and 300 for nrml grp ba kullum za'a ake posting ba via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616*
Sanya masa wani gigitaccen kuka, wanda ya ƙara haddasa tsarawar kansa,
Wannan idan bai taka mata birki ba, Tabbas zata mayar da shi mahaukaci,
Cikin ƙosawa da ihun nata yaja jikinsa zuwa jikin wata luntsumammiyar kujera ya zauna,
Idanunsa yaje ya rufe, a jikinsa yaji ana kallonsa ware jajayen idanunsa yay idanunsa ya sauka akan Kubraah wacce ta tsorawa faffaɗan ƙirjinsa idanu,
Da wani irin sauri ya tattare rigarsa tare da rufe ƙirjinsa baki ɗaya, kafin cikin haɗa fuska yace.
"Me kike buƙata?"
Da sauri taja jikinta zata zauna kusa dashi yayi saurin É—aga mata hannu,
Hakan ya tilasta mata tsayawa tace.
"Sleep with me tonight, ka kwanta dani Abu Maleek koda baka sauke nauyin dake kanka ba, just romance is okay to me"
A fili yace "O'ohhh"
Jin kalmar Romance yasa ya taɓe baki, kada Allah ya kawo masa wannan ranar da zai ƙwaƙume mace kamar maye, shi gaba ɗaya ba'a fahimtar wanene shi, bashi da lafiyar zaiyi wata tarayya da mace, shiyasa ya ƙauracewa duk wata sabga ta mata,
Domin baya son raini da wulaƙanci, mace kowa da zarar ta Fahimci baka da ishasshiyyar lafiyar da zaka kwanta da ita shikenan ka shiga uku,
Miƙewa yayi tsaye ya shiga taka ƙafafuwansa cike da zallar isa nutsuwarsa,
Al'amarin daya ƙara rikita Kubraah kenan taji gaba ɗaya babu wanda take buƙata a yanzu sai mijinta,
Cak ya tsaya ba tare daya juya ba yace.
"You're dreaming you poor Kubraah Kabal, jikina sai daga nesa"
Cikin ɓacin rai ta kallesa wato yana san full name ɗinta kenan ko?
Kamar zatai masifa sai kuma tace.
"Idan haka ne, kenan ya tabbata cewa kai lusari ne, wanda bashi da cikakkiyar Lafiya, ko dai abar taka ce bata aiki shiyasa kake ɓoyewa now i understand, to bazan iya zama da namiji lusari ba ina da cikakkiyar lafiyar"
Hannayensa ya watsa irin i don't care É—in nan kafin yace.
"Ok I'll divorce you Kubraah Kabal"
Ba tare da tunanin da gaske zai iya aikata abinda yace ba tace.
"So What? Nasan wallahi u can't divorce me, na same maka ƙarfan ƙafan Jalaluldeen Tunde Muhammad Jalal"
Taɓe baki yayi domin ta fara cikasa da magana kamar zai gaba ya barta sai kuma yace.
"Saki É—aya, saki biyu saki uku, no more relationship between us"
Yana faɗin hakan ya ɓace daga gabanta kamar walƙiya,
Tashin hankali wajan Kubraah Kabal ba'a magana, ihu ta fara tare da cire zani ana faɗuwa ƙasa,
Da gudu kuma ta nufi sashin Mai Babban É—aki, tana zuwa ta sameta ita da Oumuu-Ayman,
Ganin tashin hankali a fuskar Kubraah Kabal ya sanya Mai Babban É—aki kwallon ta, ba tare kuma da tayi magana ba, taci gaba da duba kayan da Abu Maleek zai tafi dasu.
Zubewa tayi gaban Mai Babban É—aki ta shiga surutai,
Wata Æoyayyiyar ajjiyar zuciya Oumuu-Ayman ta sauke, at least wani mummunan shashi yabar Abu Maleek,
Mai Babban É—aki ta ja numfashi tare da kallon Kubraah Kabal tace.
"Kinyi kuskure biyewa Zaki, kinsan matsalar sa kin san damuwar sa musamman yanzu da yake cikin damuwa, kamata yayi ki samu ki kwantar masa da hankali, yanzu ba lallai yana cikin hayyacinsa yay maki wannan sakin ba,
King Tunde yana da mata biyu, Queen Ayoola sai kuma Queen Roomana, Queen Ayoola yaranta guda uku ne, Aremo Shakiru, Aremo Sharefddeen, gaba ɗaya kuma sune manya ƙaramar su ce Salimerh, Queen Roomana tana da yara biyu Babban shine Aremo Adams sai kuma Zaki na Jalaluldeen wanda ake ce masa Abu Maleek,
Junaid ɗane wajan Otun (Galadima) Galadima kuma ƙanine wajan King Tunde Muhammad Jalal, mene ya sanya kaf cikin samarin babu wanda yake da mata sai ƙaramin cikin su Abu Maleek? Mene yasa kuma aka haɗa shi da mata har biyu? Baki da Wannan masaniyar ko? Mene yasa sunan Abu Maleek ya bisa? Baki sani ba? Kin san dai cewa MALEEK ɗa ne wajan Jalaluldeen, to Kubraah Kabal bani da abin cewa kin rusa damarki da kanki, saki har guda uku ai ba wasa ba, dan haka ki koma Masarautar ku komai ake ciki zamu tura wasiƙa"
Tunda ta fara magana Kubraah Kabal take Kallonta a haukace, wato yasan ya kwanta da matarsa Bola har ya bata ciki ta Haihu ita ya mayar ƴar iska, anyi auranta dashi baya ƙasar even miss call ko text message babu, and yanzu ya dawo shi ne ya bita da saki,
Miƙewa tayi ba tare da tace komai ba ta nufi hanyar fita, sa sauri Bola dake baƙin ƙofar shigowa ta juya.
A can sashin Queen Ayoola kowa, Aremo Shakiru ne yake ta Safa da marwa,
Wato a kullum dama ƙara zuwar masa take ba tare kuma daya sha wahalar komai ba,
Murmushi yayi tare da kallon mahaifiyarsa wace take tsaye tana gyara zaman Alƙyabbar jikinta,
Cikin farin ciki yace.
"What a great idea Mumy? Wow! Harna fara jiyo ƙamshin nasara"
Murmushi tayi cike da ƙasaita tare dayin baya ta nemi kujera ta zauna tace.
"Haka ne, Amma dai kayi a hankali domin lamarin akwai sarƙaƙiya cikinsa, wanne yake suffar Hadima Zubaida? Wane ya sace Queen Roomana? Sannan jiya an ƙara ɗurawa King Tunde goba, wannan dalilin ya sanya aka hana Abu Maleek ya dubasa a matsayinsa na babban likita, domin ana da tabbacin zai iya bashi kariya, wannan dalilin ya sanya aka shirya tafiyar Abu Maleek zuwa Birnin Bera, duk waye yake shirya hakan? Kaga muma kanmu dole mu sanya idanu, domin duk Mutumin da yake haka akwai abinda yake buƙata wanda zata iya kasancewa abinda muke so shine yake so"
Shiru Aremo Shakiru yayi sai yanzu shima ya fara wannan tunanin da sauri ya juya tare da nufar inda zai samu Iyalode.
Da daddare bayan sun yi sallar IsshÄ wajan 9 na dare kowa ya kasance a saman dinning area, kowa duk Family É—in suna wajan hadda Oumuu-Ayman da Mai Babban É—aki,
Cikin nutsuwa yake taka ƙafafuwansa zuwa wajan dinning ɗin,
Ƙamshin turarensa ya sanya duk suka fahimci shine yazo, basu taɓa tunanin zuwan nasa a dai-dai irin wannan lokacin ba.
Da Murmushi Salimerh ta miƙe tare daja masa wata haɗaɗɗiyar kujera a gefen Oumuu-Ayman,
Lumshe idanunsa yay yana sanye da wasu fitananun Panjams masu santsi da taushi, ƙwantaccen gashin kansa yay luff dashi,
Ya ƙara faɗi sosai da kuma tsayi, gaba ɗaya ya kerewa sauran ƴan uwan nasa.
Zama yayi tare da sunkuyar da kansa ƙasa, yana taune bakinsa, Sharefddeen ne yay Murmushi yace.
"Bari na gaisheka ni, how are you Brother? Ya Madrid da kewar ƙwallon ƙafa?"
Ya ƙare maganar cike da zulaya,
Gently ya É—ago da kansa, tare da tsare Sharefddeen da idanu,
Kamar bazai magana ba sai kuma yace.
"Allahamdulillah Bro"
Shakiru shima ya saki Murmushi yace.
"Nine ba za'a kula ba? Sabida kaga bani da ƙaton jiki kamar naka ko? To ya kazo Nigeria ya kuma masoyiya ball?"
Ya ƙare maganar with smile on his face,
Taune baki Abu Maleek yayi kafin ya ɗan sauki Ajjiyar zuciya yana lumshe idanunsa cikin ƙasa da murya yace.
"Na sameku lafiya?"
Suka amsa da "Allahamdulillah" Adams kam ko kallon inda Jalaluldeen yake bai ba, shima Abu Maleek ya lura da hakan sai kawai ya share duk da cewa yake kewar É—an uwan nasa.
"My son ya zama Basamude Ma sha Allah"
Cewar Queen Ayoola, Bola kam ko abincin kirki ta kasa ci saboda yadda Abu Maleek yayi kamar bai san da ita a wajan ba,
Oumuu-Ayman ce ta shiga haÉ—a masa dinner kana ta tura masa gabansa,
Girgiza kai yayi idanunsa a lumshe yace.
"Just coffee Oumuu"
Ta san daman ba lallai yaci komai ba, tana haɗa masa Coffee ɗin ya miƙe tsaye sabida kallon da Bola take masa,
Yana É—aukan mug É—in Coffee É—in yayi gaba walking slowly ya nufi Sashin King Tunde bayan ya duba jikinsa ya fito ya nufi nasa sashin Mai kyau da kuma tsari.
Abu Maleek na zuwa sashin sa, ya zauna saman kujera a hankali ya dinga spending coffee É—in a bakinsa,
Gefensa kuma tankar Inibi ce wacce tayi sanyi sosai,
Yana zaune yaji ana É—an tafiya a hankali, tsaki yaja saboda zuwa yanzu yana son ya jisa shi É—aya,
Yana Buƙatar nutsuwar ƙwaƙwalwa domin ya samu lokacin yin tunani,
Yana ƙoƙarin miƙewa tsaye yaji an faɗa jikinsa tare da rungomesa ana jan sajan fuskarsa, wata irin bugawa zuciyarsa tayi tare dayin wani tsalle ta cikin ƙirjinsa kamar zata faso ƙirjinsa ta fito, da wani irin sauri ya buɗe idanunsa da sauri ya rufe saboda arba da yayi da.
*Littafin ABU MALEEK na kuÉ—i ne, biya 500 domin samun posting sau biyu kullum, biya 300 amma posting ba kullum ba via 0116886423 sulaiman Naima s union bank*
Kyakkyawan farin yaro ɗan kimanin shekaru 10 a duniya, fari ne tass kamarsa da Jalaluldeen harya ɓaci, MALEEK kenan yaron da dukkan Alaafin ta sanyawa idanu,
Wangale fararan haƙoran sa yayi yace.
"Bà ami Ãróyin sómi gidigà n" (Bà ami nayi kewarka sosai).
MALEEK ya faÉ—a yana kwantar da kansa a jikin Abu Maleek É—in.
A.m runtse idanunsa yayi yana jin gudun zuciyarsa na ƙaruwa sosai,
Gaba É—aya mantawa yake yana da wani É—a a duniya, cikin jarumta da kuma dakiya Abu Maleek yasa hannunsa ya shafa sumar kan Maleek ba tare da yace komai,
Miƙewa yayi dashi ya nufi bedroom ɗinsa mai kyau,
Wata ƙatuwar chocolate ya ɗauka tare da bawa Maleek still bai ce komai ba, tun kallon farko da yayi masa bai ƙara ƙoƙarin kallonsa ba.
Bathroom ya shiga tare da sakarwa kansa shower kana ya shirya cikin fararan kayan bacci Panjams..
Yana gama shiryawa ya samu MALEEK yayi bacci kusa da Sweet,
Wani bathroom ɗin ya shige tare da kwanciya bayan ya ƙure gudun a.c ya daɗe kafin bacci yayi gaba da shi.
Rugar Mahinjo.
Julde ce zaune a cikin bukkar ta sai sauke Ajjiyar zuciya take tana jan numfashi da ƙyar,
Hannunta riƙe da ƙirjinta saboda ciwon da yake mata ga wani irin nauyi da ƙirjin yayi mata,
Tana zaune taji an shigo cikin bukkar Ajjiyar zuciya ta sauke tana É—an lalubar hanya tace.
"Madibbo na, yunwa zata karni bani madarar nasha"
Ta ƙare maganar hawaye na saukar mata, Barkido kowa Murmushin jin daɗi yayi yau ya samu Julde ita kaɗai,
Zai aiwatar da abinda yake ransa, yau ƙwaɗayin sa zai faɗa, jikinsa na mazari yayi kan Julde take ƙoƙarin miƙewa tsaye,
A rikice Julde tace.
"Madibbo!! Madibbo!! Madibbo na?"
Jin Shiru ya sanya ta shiga ƙoƙarin Miƙewa tsaye tana miƙewa Barkido na sanya hannunsa yayi....
Saura page 1 free pages ya ƙare🥱
SHARE FISABILILLAHI SABIDA ALLAH DA ANNABIðŸ‘ðŸ»
🌈🌈🌈🌈
*ABU_MALEEK*
🌈🌈🌈🌈
NIMCYLUV
BOOK 1
PAGE 19-20
*Feedyn Bash* osà pámà lèriñ là nà 😂, emi kinshè *Yoruba* fa, *Hausa* pà nbélé nimÃ, so fún *Bassh* pé aro rén somÃ.
Sama da rigar jikinta, tare da ƙoƙarin kunce igiyar da aka ɗaure mata ƙirji da ita.
Wani masifafan ihu Julde ta sanya, saboda tsananin tsoran daya shigeta,
Ta shiga kare ƙirjinta da dukkan hannayenta, Jikinta duk rawa yake, cikin rawar murya da gigita tace.
"Waye kai? Me kake so? Noi indema?"
Ta jera masa tambayar lokacin, saboda jin wanda ya Shigo É—in yayi shiru,
Gashi yana ƙoƙarin yi mata tsirara, Barkido kam tuni ya fara fidda numfashi yana sakin Ajjiyar zuciya saboda santala santalan cinyoyinta da suka bayyana,
Duk da cewa warin dauÉ—a take amma hakan bai hana cinyarta yin wani kyau ba,
Ganin tana shirin bashi wahala kawai ya sanya hannunsa tare da kama kanta ya gwarata da bango,
Wani gigitaccen ihu ta sanya lokaci guda kuma jini ya ɓalle daga goshinta ya shiga zuba yana sauka zuwa saman fuskarta,
Kafin ta sulale a wajan babu numfashi, wani irin Murmushin jin daɗi yay kana ya miƙe ya shiga ƙoƙarin zame kayan jikinsa,
Da wani irin sauri Barkido yaja baya tare da ɓoyewa a bayan ƙofar bukkar, hakan ya faru ne saboda jiyo Muryar Madibbo yana faɗin.
"War Julde, Hai kazo kana ina?"
Ya faɗa yana leƙawa tare da ƙarasawa inda ya hangi Julde kwance dafe da ƙirjinta babu numfashi,
Da wani irin saurin gigita Madibbo ya ƙarasa shiga cikin bukkar tare da nufar inda Julde ke kwance,
Yana shiga Barkido ya fita da sauri yana Murmushin jin daÉ—in babu wanda ya kansa.
Jawo Julde yayi jikinsa yana jijjiga ta tare da kiran sunanta, ganin ko motsi ba tayi yasa Madibbo faÉ—in.
"Ko dama ta maa?" (Meke damunki?"
Da sauri kuma ya kwantar da ita tare da fita da sauri ya nufi inda yake É“oye, Æoyayyan Sirrin da yake É“oyewa Julde daman irin wannan ranar yake jira,
Wacce ta tazo ya faÉ—a Julde komai dake faruwa Wanda bata san shi ba.
Yana fita ya nufi can wata ƙuryar duhuwa duk da cewa dare ne Amma haka ya shiga cikin duhuwar tare da haƙe ƙasar ramin daya ɓoye abun.
Yana gama tunuwa ya miƙe da sauri tare da fara tafiya ya nufi cikin Rugar,
Murmushi Arɗo da Lamiɗo sukai, a hankali kuma Arɗo ya saki wani zabgegen Maciji dake hannunsa zuwa ƙasa,
Kai tsaye macijin kuma wajan Madibbo yayi saboda yaga gilmawarsa,
Sosai Madibbo ke sauri domin ya isa ga Julde ya faÉ—a mata shuÉ—É—aÉ—an tarihin daya huce kafin Zuwan wannan ranar.
Kamar daga sama yaga saukar Macijin a gabansa yana sara kai tare da fiddo da harshen bakinsa, ya shiga wa yiwa Madibbo tsartuwa,
Wani irin kyarma jikin Madibbo ya É—auka, gashi ya kasa koda mutsawa, tsoro da gigita suka cika masa zuciya.
Wani irin tsalle Macijin yayi tare da.
*Daga wannan page É—in na gama free pages, sabida halin rashi da ake ciki na raba tsarin biyan gida biyu, 500 for VIP posting safe da yamma, 300 for nrml grp, posting idan anyi yau babu gobeðŸ‘🻠via 0116886423 sulaiman Naima s union bank evidence of payment 08119237616*
Sarawa Madibbo bakinsa a dai-dai satin ƙahon zuciyarsa, nan take kuma Madibbo ya faɗi yana fitar da wata iriyar kumfa daga cikin bakinsa,
Kullin abinda ke hannunsa wanda yake son faɗawa Julde ya ƙwace daga hannunsa tare da faɗuwa ƙasa,
Æat kuma kamar Aljani Macijin ya É“ace daga wajan,
Kakarin mutuwa Madibbo ya fara idanunsa ya shiga lumshe bakinsa É—auke da sunan JULDE,
Arɗo da Lamiɗo ne suka ƙarasa inda yake kwancan tare farayi masa dariya,
A hankali kuma LamiÉ—o ya É—auki kullin ba tare daya buÉ—e yaga ko menene ba, ya cilla kullin sama,
Kana sukai gaba Abunsu cike da farin cikin samun nasarar raba Madibbo da ransa,
Bakinsa É—auke da salati Ubangiji ya amshi ran Madibbo.
Sanyin safiya mai cike da dadÉ—ar iska ne ya farkar da Julde daga suman da tayi,
Wata ƙaƙƙarfar ajjiyar zuciya ta sauke, tare da runtsa idanunta wanda suka kumbura saboda kuka, ga kuma rashin wadatacciyar lafiya da idanun yake da shi,
A hankali ta miƙe zaune tare da kifa fuskarta a tsakanin zuciyoyinta ta saki wani irin raunataccen kuka!
Hakiƙa tana buƙatar mataimaki a rayuwarta, amma waye zai zama gatanta? Waye zai zama Garkuwa a gareta? Waye zai zama tubalin da zai gina mata sabuwar rayuwa harta mata da wannan rayuwar da take mata ƴanci?
Waye zai zama Muradin ranta? Wanda zai zama madubi abin haska zuciyarta? Ko dai TABI ABINDA ZUCIYAr take faÉ—a mata ne?
Kuka take mai cike da ladamar rayuwa ƙunci kuma da baƙin ciki,
Ganin bata da wani gata sai Allah, bata da wanda zaice mata tayi shiru ya sanya ta sassauta kukan tare da É—aukan sandar ta, ta shiga laluban hanya idanunta na É—an juyawa,
A haka ta samu ta fita daga cikin Bukkar hannunta É—auke da ruwa,
Can bayan Bukkar ta tsuguna tare dayin fitsari kana tayi alwala ta koma bukkar tare da gabatar da sallah bayan ta yane kanta da wani siririn abu.
Tana idarwa ta fara jin surutai bata motsa ba, sai da taji ana faɗin Madibbo ya mutu, kusan mutuwar tsaye tayi, jinta da gaba ɗaya ya ɗauke, bugawar da zuciyarta take ya ɗan tsaya na wasu daƙiƙo,
Farkawa tayi ta kanta kwance ashe tun a lokacin ta suma sabida trumer É—in data shiga.
Yini tayi kuka babu abinda ke tsayar da ita sai Sallah, daman sallar ba wata iyawa tayi ba sosai, bare kuma ta iya yiwa mamaci addu'a,
Haka ta ƙara kwanciya bacci banda ruwa babu abinda yake cikinta,
Ji take kamar itama tamar Duniyar ko zata huta, idan tana da rabon jin daÉ—i a lahira sai ta samu,
Washe gari da safe, ArÉ—o ya sanya wasu mutane zuwa su tafi da ita, kwallon ta ArÉ—o yayi yace.
"Wato kai yaron nan bakaji ko? Haii sai da ka sake sace mana nonon nagge ko? Gashi dalilin hakan ka sanya Nagge ya mutu"
Jikin Julde ya É—auki rawa, domin ba zata mance da cin zarafin da akai mata na aski ba, ga azabar da aka gana mata na murje mata nono,
Kuka ta sanya ta shiga rarrafawa duk da bata ganin kowa amma a haka ta ƙarasa gaban Arɗo tare da riƙe masa ƙafa tace.
"Kayi min rai Arɗo, kada ko sake murje min nono, da ƙyar nake numfashi saboda abinda kuka sanya Min, Aradon Allah ban saci komai ba"
Da sauri LamiÉ—o yace.
"Arado ƙarya ka, Arɗo zai maka ƙarya? Da kanshi ya ganka kana tatse mashi nono, dole ka kiwata mana Nagge guda ɗari bisa abinda ka aikata"
Zuciyar Julde ta buga da ƙarfi Tayaya zata iya kiwo? Tayaya ne zata iya kula da Nagge guda ɗari?"
Gaba É—aya wajan suka sanya ihu akan dole Julde tayi masu kiwo ai tana sandar ganin hanya,
ArÉ—o ne yayi gyaran murya yace.
"Maza ki haÉ—a mana Nagge guda É—ari a fito dasu daga garke yanzun nan, kuma kada ka sake a rasa guda É—aya idan hakan ya fara to walle kai ma saika matu"
Allah sarki baiwar Allah bata da wata mafaka dole tabi abinda sukace mata,
Yin kiwon ma zai sanya tana samun abinci ci,
Haka ta tisa Nagge guda ɗari a gaba zuwa daji, tana dafe da ƙirjinta da yayi mata wani irin nauyi, da ƙyar take jan numfashi,
Tana zuwa wata ƙorama taja ta tsaya tare da kwanciya wajan ruwa ko taji sauƙi daga azabar da ƙirjinta yake mata gaba duniyar tayi mata zafi,
Ajjiyar zuciya ta sauke tana ƙara riƙe ƙirjinta a haka wani wahalallan bacci ya ɗauke ta.
Slowly ya shiga É—aga eyes lashes É—in idanunsa, wanda suke zara-zara sunyi kwance luff saman fatar idanunsa,
Tun bayan yayi sallah ya koma bacci sai yanzu ya samu zarafin tashi daga nauyayyen baccin daya É—auke sa,
Ƙuri yayiwa tafkeken photon Queen Roomana wacce take sanye da milk ɗin voyal ta ɗura light blue ɗin Alƙyabba, wacce tai mata kyau sosai,
Tayi Murmushi wanda ya haddasa fitowar teeths gave É—inta irin na Abu Maleek,
Idanunsa yaja ya rufe ya yana taune leɓansa a hankali ya shiga sauke ajjiyar zuciya, ɗan ware gajiyayyun idanunsa yayi sabida motsin da yaji,
Yana juyawa idanunsa ya sauka kan MALEEK dake tsaye rungome da Sweet,
Da sauri ya juya kansa yana rufe idanunsa,
Shi sam ya manta da batun cewa Maleek É—in yana sashinsa,
A duk sanda yay arba dashi sai yaji zuciyarsa ta buga,
Kuma yana ɗaya daga cikin dalilin daya sanya yabar ƙasar baki ɗaya,
Miƙewa yayi a hankali yana ɗan kwaɓe fuska ganin hakan yasa Maleek matsawa kusa dashi yace.
"Èkaro Bà ami" (ina kwana Baba?)
Fesar da iska Abu Maleek yayi ba tare daya amsa gaisuwa ta Maleek É—in ha yayi gaba zuwa toilet,
Ganin hakan ya sanya Maleek sakin Sweet tare da buɗe baki ya sanya kuka yana buga ƙafa,
Cak Abu Maleek ya tsaya kafin a hankali ya sanya hannunsa a saman goshinsa ya shiga murza,
Maleek soyayyyar mahaifin nasa ce ta tare masa a zuciya shiyasa yau yake son kasancewa dashi,
Domin yaji É—umi irin na mahaifinsa, amma a koda yaushe mahaifin nasa gudunsa yake ba tare daya san dalili ko kuma aibun dake tare dashi ba,
Ganin kukan na Maleek yayi yawa ne yasa a hankali Abu Maleek ya sulale a wajan tare da zama a armchair, yana ware firgitattun idanunsa,
Cikin nutsuwa ya miƙa wa Maleek ɗin hannunsa alamar yazo,
Da gudu ya ƙaraso wajan mahaifin nasa, yana sakin dariya tare da shigewa jikin Jalaluldeen,
Kallon yaron yayi yaga babu wata kama tasa wanda Maleek bai kwashe ta ba tass,
Kenan dalilin daya sanya King Tunde da kuma su Mai Babban ɗaki ƙaunar Maleek ɗin kenan?
Ya tambayi kansa a zuciya, a fili kuma wani ƙaƙƙarfan Numfashi ya sauke,
Gently kuma ya É—ura softness hands É—insa duk biyun a saman sumar Maleek,
Kamar mai koyan magana ya shiga kokawa da laɓɓansa,
Da ƙyar ya samu kalmar.
"Shè layó lábo?" (Fatan kana lafiya?)
Kalmar datai fitar gurbi kenan daga cikin bakinsa ba tare daya shirya hakan ba,
Cikin tsananin farin ciki da kuma jin daÉ—i Maleek ya rungome Dad É—in nasa,
Yau rana ce babba a garesa tunda har Abu Maleek ya fito da kansa ya tambayi lafiyarsa,
Cikin soyayya da kulawa Maleek ya ɗan shagwaɓa fuska yace.
"Baà mi baka sona da gaske? Me mayi maka? Kullum kana gudu na, a school kowa Bà ami ɗinsa ke zuwa ɗauko sa, amma ni bana ganinka, ina kake ɓoyewa? Meyesa kuma baka sona?"
Ya ƙare tambayoyin nasa idanunsa na zubar da hawaye kasancewar Maleek yaro mai shegen wayo,
Sarawa kansa yayi sabida tambayoyin ba zata da Maleek É—in ya jefesa dashi, a zahirin gaskiya shima bashi da amsar wannan tarin tambayoyinsu, balle ya bawa Maleek É—in amsar su,
Shi mamakin surutun yaron yake, ga kuma shegen zaƙin murya kamar tasa, ganin yana shirin yin wata tambayar ne ya sanya Abu Maleek saurin taran Numfashinsa tare da faɗin.
"Ya school?"
Washe baki Maleek yayi yace.
"Ina jin daÉ—i karatu sosai BÃ ami, kasan me zan zama idan na girma?"
Girgiza kai Abu Maleek yayi yana mai ɗan ƙara kallon yaron a kaikaice,
Baya Maleek yayi kaɗan kafin ya shagwaɓe fuska, tare da rausayar da kansa gefe yace.
"O'ohhhh ABU MALEEK"
Wani Murmushi ne ya suɓuce wa Abu Maleek, wato Maleek yana son buga ƙwallo kenan,
Jinjina kansa yayi tare da Miƙewa ya shafa kan Maleek ɗin,
Ba tare kuma da yace komai ba ya nufi bathroom.
A can shashin King Tunde Muhammad Jalal tuni kowa ya halarci wajan, ana jiran zuwan ABU MALEEK,
Ƙarfe sha ɗaya da ƴan mintuna Abu Maleek ya fito daga sashin sa, bayan ya shiga part ɗin gym ɗinsa,
Cikin nutsuwa haɗi da kamewa Abu Maleek yake taka ƙafafuwansa a ƙasa,
Yana sanye da wata fara jallabiya talitha kaftan, mai taushi da kuma santsin gaske, sai maiƙo dake sabida santsin yadin jallabiyar,
Jinjina kansa kawai yayi yana sauraran abinda Salimerh take faÉ—a masa,
Itama cikin wata haÉ—aÉ—É—iyar jallabiya ta mata La Doublej milk colour,
Ta sanya duka hannayenta cikin aljihun Jallabiyar,
Cikin ƙasa da Murya saboda tasa baya son ihu akai, tace..
"Zaki, ka kula dan Allah, kasan kana da matsala kada kace zaka nuna miskilanci a ƙasar daba taka ba, ina jin tsoran wannan tafiyar sosai a raina, amma babu yadda zanyi tunda ka amince da zuwan"
Taune baki yayi yana jin zancan da take wassafa masa, shi surutunta ya bashi mamaki, cai cai cai aita magana,
Ganin yaƙi magana ta marai-raice fuska tace.
"Please Zaki"
Da gajiyayyun idanunsa ya juya ya kalleta ba tare kuma da yace komai ba, ya jinjina mata kansa, a haka suka isa dinning room,
Zama yayi ita kuma ta shiga haÉ—a masa breakfast wanda Oumuu-Ayman ta bata da kanta, domin babu wanda ta amince ya bawa Abu Maleek É—in amince,ita take shiga kitchen da kanta ta bashi.
Akara ne, da Ewa Agayin, sai chicken and waffles with Anadama bread, sosai yaci traditional food É—in kana ya É—ura da power horse energy mai sanyi,
Sauran tarkacan ko taɓa sa bai ba,
Yana gamawa ya miƙe tsaye, walking slowly ya nufi Sashin King Tunde Muhammad Jalal, a hanya suka haɗu da Junaid kallo guda yayi masa ya ɗauke kai,
Junaid kam ɗan Murmushi yayi idanunsa akan Salimerh wacce tayi masa matuƙar kyau, kamar ya sace ya gudu,
Ba tare shima da yayi Magana ba yabi bayan Abu Maleek yana sakin Murmushi,
Zuwan Abu Maleek ne kuma ya sanya gaba É—aya mutanan wajan baida idannunsu kansa,
A kullum Abu Maleek sauyawa yake tamkar wanda ya kejin naman mahauniyya,
Yanzu kam zallar kwarjinin sa ne ya baiyana ga kuma wata haiba da izza,
Ba tare daya kalli kowa ba, ya ƙarasa inda King Tunde Muhammad Jalal yake kwance, yana zuwa ya rungome sa sosai tare da tsora masa idanu kamar mai son fahimtar wani abu,
Da wani irin sauri kuma ya.
*Last free page via 0116886423 sulaiman Naima s union bank*
Tallafo fuskar King Tunde yana ƙoƙarin sanya bakinsa cikin na King Tunde domin ya tabbatar da abinda zuciyarsa take zargi,
Da sauri Malamin yace.
"Babu lokaci, gaba É—aya kwana goma sha biyu ya rage maka, tafiyar kuma tana da tsayi gaske, daga rugar Mahinjo zuwa garin ma sai kayi kwana biyu"
Sauke numfashi yayi a hankali ya zame fuskarsa ba tare daya aiwatar da abinda yake shirin yi ba,
Otun ne yace.
"Za'a sauya maka kama, ta yarda babu wanda zai san cewa kai attajiri ne"
Kallonsu kawai yake ba tare daya ko motsa ba,
Malamin ne ya fito da baƙin fenti da wasu caloli,
Oumuu-Ayman miƙewa tsaye tayi sam zuciyarta ba zata jure hakan ba, Aremo Shakiru da Aremo Adams da Aremo Sharefddeen duk suna zaune ba tare da kowa yace komai ba,
Yaci ace su da suke manya masu ishasshiyyar lafiya sune za suyi tafiyar nan, amma sai gashi karami cikinsu wanda yake da matsalar ƙwaƙwalwa shi ya ɗauki hatsarin tafiyar ba tare da tunanin abinda zai je ya dawo ba.
Cikin nutsuwa Malamin ya shiga har gitsa gashin kan Jalaluldeen tare da yiwa lallausan baƙin gashin nasa rini da wata kala ja da kuma kuriya,
Yana gamawa ya ɗauki baƙin fenti ya shiga shafawa a saman ƙyakkyawar farar fuskar Abu Maleek, fuska mai tsananin kyau haiba da kuma kwarjini,
Fuskar da take Bara zana wa Æ´an mata,
Few minutes fuskar Abu Maleek ta zama baƙa ƙirin, banda idanunsa da suke farare kuma manya, sai jajayen laɓɓansa da suke masu taushi da laushi,
Kana aka dawo hannayensa zuwa wuyansa, ana zuwa za'a buɗe ƙirjinsa yayi saurin damƙe hannun Malamin,
Kallonsa yayi yace.
"Ka bari a shafa har Nan saboda gudun samun matsala"
Shiru yayi baice komai ba, hakan yasa Malamin ƙara nufar ƙirjinsa zai zame rigar, bakin Abu Maleek na rawa da karkarwa yace.
"Stop"
Ya faɗa a lokacin da gaba ɗaya jikinsa ya ɗauki rawa ya shiga langwaɓar da kansa gefe idanunsa suka shiga fitowa,
Malamin kam sam bai lura da yanayin da Abu Maleek ya shiga ba, ya ƙara nufar ƙirjinsa karyar da wuya Abu Maleek yayi tare da buɗe baki yace.
"O'ohhhh"
Yana faɗin hakan ya zabura tare da shaƙe wuyan Malamin jikinsa duka tsuma yake da karkarwa, taɓe Baki Adams yayi tare da miƙewa ya fice daga cikin tirakar,
Sharefddeen ne ya miƙe tare kallon Abu Maleek yace.
"Let go of him, sake sa Jalaluldeen"
Wani kallo da Abu Maleek yayiwa Sharefdeen sai da yaji hantar cikinsa ta juya, da sauri kuma ya sakesa tare sayin baya,
Ganin yana ƙoƙarin yin kisa ne gashi kowa ya kasa ƙwatar Malamin daga hannun Abu Maleek,
Cikin tsayawa da kuma ɗaga Murya Oumuu-Ayman dake bakin ƙofa tace.
"JALALULDEEN TUNDE MUHAMMAD JALAL SAKE SA"
sakinsa Abu Maleek yayi tare da sulalewa a wajan ya zube saman ƙafafuwansa,
Ana sakin Malamin ya kwashi kayansa da sauri yabar wajan,
A hankali Oumuu-Ayman ta ƙarasa inda yake durƙoshe jikinsa na rawa tana zuwa ta zauna tare dasa hannunta ta jawosa saman cinyarta,
Har zuwa lokacin jikinsa bai bar rawa ba, addu'a ta shigayi masa, tana shafa sumar kansa wacce aka ɓata da kala,
Idan ka kalli Abu Maleek a wannan lokacin zaka tabbatar cewa eh da gaske mahaukaci ne shi,
Irin masu dukan nan, Cikin kuka Queen Ayoola tace.
"Yanzu a haka za'a barsa yaje? Wannan wacce irin jarrabawa ce Ubangiji yake sanya mu cikinta ne?"
Ta ƙare maganar tana sakin Kuka, Mai Babban ɗaki wanda wacce tana zaune ko motsi ba tayi ba, tai gyaran murya tare da faɗin.
"Kowa yaje waje"
Queen Ayoola ce ta Miƙe, kana Bola sai kuma Junaid sai Shakiru da Sharefddeen, ya rage daga Otun sai Oumuu-Ayman da Mai Babban ɗaki,
A nan jikin Oumuu-Ayman bacci ya É—auke sa, sai da yayi baccin awa guda sannan ya farka yana tashi Oumuu-Ayman ta bashi ruwa mai sanyi ta bashi yasha, kana ya gavatary da sallar zhur,
Nan aka fara shirya tafiya yayinda aka hana zuwa kowa yiwa Abu Maleek sallama,
A hankali ya tura ƙofar parlon Adams, yana tsaye hannunsa riƙe da File, kallo guda yayiwa Abu Maleek ya ɗauke kai,
Abu Maleek kam cikin soyayyyar É—an uwan nasa ya nufi Adams, da niyyar ya rungomesa da sauri Adams yaja baya tare da É—aga masa hannu yace.
"Mene ya kawo ka?"
Da mamaki Abu Maleek wanda ya zama mahaukacin gaske idan ba sani kayi ba yake duban Adams kafin yaja numfashi yace.
"I'm going now, nazu just to say i miss You Bro"
Murmushi Adams yayi kafin yace.
"Uhm! Kazo sace ni ne kamar yadda ka sace mun Mahaifiya tunda naga kai ba sonta kake ba"
Zare ido Abu Maleek yayi yana faÉ—in "sace Mami?"
"Yeah, of course koda yake mahaukaci like you babu abinda bazai iya ba, musamman yanzu da sanyi zai fara hauka kuma sai Allah, ina jan kunanka Jalaluldeen duk inda ka kai mini mahaifiya ka gaggauta fito da ita, if not Uhm you have no idea akan abinda zan maka, mahaukacin banza"
Yana faÉ—in hakan ya shige cikin bedroom É—insa,
"O'ohhh"
Shine abinda Abu Maleek ya samu zarafin faɗa, tsoro da tashin hankali ya bayyana a saman baƙar fuskarsa,
Juyawa yayi ya fita.
Sosai Oumuu-Ayman taci kuka ita ɗaya hakama Salimerh, Mai Babban ɗaki kam rungomesa tayi, bayan yaje ya ƙara duba King Tunde ya ɗauki sweet a hannunsa kana ya shiga mota aka fita dashi daga cikin Alaafin.
Kwanakin Julde biyar kenan, a cikin jejin
Yanzu ma tana tafe dafe da ƙirjinta idanunta cike da hawaye, ga yunwar da tayi mata illa,
A haka take dogara sandar tana lalubar hanya, gaba ɗaya zanin jikinta ya gutsire yayi kamar ƙaramin wando 3gauther,
Ga kan nan nata sai ƙyalli yake, yay wani babba tashi, sai jajayen laɓɓanta da suka ƙara wani jaa saboda taunewa da take,
Tazu dai-dai gaɓar wani ƙaton kogi ta sulale a wajan, sabida yunwa da ƙishin da take ji,
A hankali kuma ta rarrafa ta shiga lalubar Nagge tana jin wata kusa da ita, ta kafa bakinsa a nonon naggen ta fara zuƙa tana shaa, sai da tasha sosai, kamar daga sama kuma ta fara jiyo sautin bindigo alamar masu satar shanu sun kawo mata hari kenan, cikin kiɗima da kuma gigita ta fara ƙoƙarin neman wajan ɓoye, gashi babu idanu,
A haka take tafiya ba tare da sanin inda take nufa ba,
Ta ɗaga ƙafarta kenan zata sauke ji kake cindummmmm ta faɗa cikin tafkeken kogin da babu wanda yasan ida ya tsaya.
Miƙewa yayi daga zaman da yake, shigowar kenan cikin ƙasar Guinea, yayinda yaya da zango daga ɗan nesa da rugar Mahinjo,
Gaba É—aya dashi da Sweet a galabaice suke, har baya iya buÉ—e idanunsa,
A wahalarce yake ɗaga ƙafarsa yana saukewa, kai tsaye kuma ya nufi inda yake hango wani haske na tashi,
A haka ya isa gaɓar kogin cikin farin ciki ya zauna tare da sauke sweet, yana sauketa ta faɗa cikin ruwan ta shiga sha, farin ciki itama ya sauka akan fuskarta,
Abu Maleek a hankali ya sanya tafin hannunsa ya É—ebi ruwan yakai bakinsa, wani irin lumshe idanunsa yayi saboda daÉ—i da kuma sanyin ruwan da yaji,
Kasa É—aurewar yayi ya Kafa bakinsa ya shiga shan ruwan,
Yana ɗago kansa idanunsa ya sauka akan wani gawar ƙaramin yaro fari ƙyakƙyawa dake yawo saman ruwan,
Cike da tausayi ya runtse idanunsa abin kuma mamaki gaba ɗaya gawar ƙara kusanto inda Abu Maleek yake take,
Sweet ma tsayawa tayi tana karkaÉ—a jela,
A haka gawar tazo dai-dai inda Abu Maleek yake kai tsaye kuma ta shige jikinsa,
Ware idanunsa ya yi cike da tsoro saboda yadda ruwa ya kumbura cikin yaron Kallon fuskar yaron yayi, gashi fari ƙyakƙyawan gaske,
Ga laɓɓan yaron masu kyau wanda bai taɓa ganin irinsu ba, a hankali kuma rigar jikin yaron ta zame daga jikinsa tabi ruwa,
Igiyar dake ɗaure jikin yaron ta bayyana ba ƙaramin ɗauri akaiwa ƙirjin ba,
Sosai Abu Maleek abin ya bashi mamaki, babu mamaki kuma ɗaurin ƙirjin nasa ne ya sanya shi faɗa ruwan ya mutu.
Cike da tausayin yaron ya tallafo sa zuwa faffaɗan ƙirjinsa yana shafa fuskarsa, hannunsa ya ƙara a hancin yaron yaji numfashi na fita,
Julde kam cikin rashin sanin inda kanta take ta kama hannun Abu Maleek tare da mannawa ƙirjinta a ƙoƙarin ta na son cewa ya cire mata ƙullin kasa nononta ya fashe,
Cikin Zallar tausayin yaron Abu Maleek ya jawo yaron jikinsa sosai tare da É—ura hannunsa a kan igiyar ya shiga kuncewa, wata wahalalliyar ajjiyar zuciya Julde ta sauke saboda kunce É—aurin da Abu Maleek yayi kafin kuma cak numfashinta ya tsaya da harbawa,
Cikin son taimakon yaron Abu Maleek ya mirgina yaron a ƙoƙarin sa na son danna masa cikin ruwan da yasha ya fita,
Cikin rashin Sa'a kuma idanunsa ya sauka akan.....
*LAST FREE PAGE🥱*
AUTHOR NOTE👇ðŸ¾
*ALLAHAMDULILLAH A NAN NA KAWO ƘARSHEN FREE PAGES ƊIN ABU_MALEEK, WANDA YA KESON CI GABAN BOOK 1 2 3, ZAI BIYA 500 POSTING KULLUM SAFE DA YAMMA, GA MASU ƘARAMIN ƘARFI ZASU BIYA 300 AMMA POSTING IDAN ANYI YAU BA ZA'AI GOBE BA, VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616 GA ƳAN NIGER SUYI MAGANA TA WANNAN NUMBER 84506476, DAN ALLAH DAN ANNABI IDAN HAR VIP KIKE SON SHIGA MAGANA 500 ZAKI BIYA KIMIN ADALCI KI TURO MIN KUƊIN TA ASUSUN BANKI NA, SABODA BAN FIYA AMFANI DA KATIN WAYA BA, IDAN BABU BANKI AKWAI P.O.S A KO'INA, MASU 300 MA HAKA SAI BABU YADDA ZA'AI SANNAN ZA'A TURA KATIN MTN*
*A KULLUM INA GODIYA GAREKU MASOYA NA, A DUK INDA KUKE FARIN CIKINKU SHI NE NAWA, A FITO A NUNA MIN ZALLAR SOYAYYA A BIYA KUÆŠIN ABU MALEEK ASHA KARATU, MACE MAI AJI BATA TSAYAWA JIRAN KAYAN SATA, MAI ZUCIYA KUMA AKE GAYAWA ABU BA MAI DUKIYA BA, DAN HAKA KI FIDDA KUÆŠI KI SIYA KISHA KARATU CIKIN NUTSUWA, DAN ALLAH IDAN BA SIYA ZAKI BA KADA KIYI MAGANA PLEASE*
1.ME ABU_MALEEK YA GANI?
2.ME ARÆŠO ZAI AIKATA WA JULDE NAN GABA?
3. MENENE TSAKANIN JARIRIN WAJAN HADIMA ZUBAIDA DA KUMA KING TUNDE?
4. WACECE TAKE SHIGAR HADIMA ZUBAIDA?
5. A INA QUEEN ROOMANA TAKE? DA GASKE JALALULDEEN NE YA ÆŠAUKE TA KO KUMA A'A?
6. MENE ZAI FARU BAYAN TAFIYAR ABU MALEEK?
7. WANNE HALI ABU MALEEK ZAI SHIGA NAN GABA?
8. MENE YA SANYA ABU MALEEK BAYA SON MALEEK?
9. WANNE IRIN ZANE NE A JIKIN ABU MALEEK?
UHM KADA KUYI MISSED KO HANZARTA BIYAN KUÆŠI DOMIN A CILLAKU CIKIN ORIGINAL ABU MALEEK GROUP.
NAGODE SOSAI DA SOYAYYA, DAGA LITTAFIN ABU MALEEK KUMA IN SHA ALLAH ZAN ÆŠAUKI HUTU, KOMA ZANYI RUBUTU SAI A WATTPAD.
SHARE FISABILILLAHI SABIDA ALLAH DA ANNABIðŸ‘ðŸ»ðŸ‘ðŸ»ðŸ‘🻠LAST FREE PAGES💃ðŸ»âœðŸ½
Lafaffan cikinta sakamako cirewar da rigar Jikinta yayi, hakan ya haddasa bayyanar ƙatuwar cibiyar ta, wacce akewa laƙabi da (Cibi).
Wata kalar bugawa zuciyarsa tayi da wani irin sauri kuma yaja gargasar idanunsa ya Lumshe sosai
Yana mai taunawa laɓɓansa wanda suka ɗan bushe saboda tsananin ƙishi da wahalar da yasha a hanya shida sweet,
Cikin tsananin Mamaki da kuma ta'ajjujin ganin ƙatuwar cibiyar ta Julde, Abu Maleek ya fesar da da wani irin gwauron numfashi yana mai ɗan jujjuya harshe sa dake cikin bakinsa.
Cikin tausayin yaron ya ƙara kai hannunsa dai-dai tsakiyar ƙirjinsa domin a gaba ɗaya tunaninsa ya gama bashi da namiji yake tare,
Duba da yadda yaga kai babu gashi ko kaÉ—an ga yanayin shigar yaron,
Kamar wando ne 3gauther a jikinsa,
Babu zato balle tsammani yaji hannunsa ya sauka kan abu mai tsananin laushi da kuma taushin gaske,
Da wani irin sauri yay ya zame hannunsa zuciyarsa na wani irin harbawa da sauri da sauri tamkar,
Zata tsaga ƙirjinsa ta fito,
A kiÉ—ime a kuma gigice ya buÉ—e rinannun idanunsa,
Abinda idanunsa kuma ya gani ne ya haddasa masa rufe idanunsa ba tare daya shirya hakan ba,
Da wani zafin nama yasa hannunsa tare da yin cilli da Julde wacce take kwance bisa tattausun cinyoyinsa, duk jikinsa rawa yake mamaki yana hana shi koda motsi bare magana,
Still kuma idanunsa a rufe suke rufe, jikinsa duk rawa yake, ga wata kalar sarawa da kansa yake, abinda bai taɓa expecting cewa zai taɓa sanya hannunsa a kansa ba, fesar da numfashi yayi tare da jan jikinsa can jikin wata ƙatuwar bishiya mai ɗauke da manyan fasadabir sun nuna sosai.
Ganin hakan ya sanya sweet binsa da gudu tana kaÉ—a jela tana zuwa ta faÉ—a jikinsa tare da kallonsa saboda yadda ta lura da rawar da jikinsa yake.
Julde kam bata san abinda yake faruwa ba, bare tasan abinda Abu Maleek ɗin yaci karo dashi a Jikinta, tun lokacin daya kunce mata igiyar dake ɗaure bisa ƙirjinta, taji wani abu mai nauyin gaske ya sauka daga ƙirjinta yayi cikinta, ga wani sanyi da daɗi haɗi da nutsuwa data samu,
Yayinda da kuma manyan matasan brest É—inta sukai fitar gurbi dalilin kunce igiyar da akai masu, suna mai farin cikin samun Æ´an cin da sukai hakan ya haddasa ko wanne jan jikinsa waje guda suna wani kalar numfashi, sun ya mushe sosai saboda tsananin azabar da suka tsinci kansu a ciki.
Tun lokacin kuma Julde tada sauke wata wahalalliyar ajjiyar zuciya shikenan kuma jinta da numfashinta suka tsaya cak,
Al'amarin daya haddasa tsayawar bugun zuciyarta kenan, a dalilin cillin da yayi mata ne kuma yasa ta ƙara gangarawa gefen kogin,
A karo na barkatai ya ƙara sauke numfashi tare da buɗe bakinsa kaɗan ya fito da tongue ɗinsa tare dayin gefe dashi ya shiga tsotsar laɓɓansa yana cizonsa,
Tarin tunani ne fal kuma a ƙasan zuciyarsa, is she a girl or boy? Shine tambayar da yayiwa kansa,
Da sauri kuma ya girgiza kansa cike da rashin gamsuwa kuma ya ware jajayen laɓɓansa tare da marai-raice fuska yana kwaɓe ta a fili yace.
"How can that be possible? Ba gashi akai? Then akwai Mama"
Ya faÉ—a yana É—an zare idanunsa da sauri kuma ya sanya tafin hannunsa tare da rufe bakinsa sabida ambaton sunan Mama da yayi,
Yana ki shin giÉ—e kuma jikin bishiryar Fasadabir wani wahalallan bacci yayi gaba da shi ba tare daya shirya ba,
A hankali yake fidda numfashi yana sauke ajjiyar zuciya, time to time kuma yana tura baki gaba tare da kwaɓe fuska tamkar zai sanya kuka,
Sam bai saba da wahala ba, ya gaji ainun idan ka ganshi a wannan lokacin zaka ɗauka Tabbas da gaske mahaukacin ƙarfi da yaji ne.
After some hours
Sanyin ruwan da yaji a saman fuskarsa ne ya tilasta masa buÉ—e gajiyayyun idanunsa wanda sukai jaa, saboda baccin daya kwasa a hanya na wasu kwanaki,
Taɓe fuska yay tare da tsotsar laɓɓansa cikin marai-raice fuska kuma ya buɗe bakinsa a taushashe yace.
"Why sweet? Kin san me kike course if you wake me up? Allah ban gaji da bacci ba, mun ɓata yau"
Ya faɗa yana sanya hannunsa tare da miƙa wa saman kansa,
Tana tsaye a saman sumar kansa Jikinta jiƙe da ruwa saboda wasa da ruwan da tayi a gefen kogi,
Girgiza Jikinta kuma da take ne ya sanya ruwan zuba saman fuskar Abu Maleek,
Cirota yayi daga saman kansa yana haÉ—e fuska kana ya ajjiyeta can gefe dashi fuska a haÉ—e kuma yace..
"Ohyyyah! Have your way"
Ya faɗa yana lumshe idanunsa a hankali kuma ya miƙa hannunsa tare da ɗurawa saman lafaffan cikinsa saboda ihun yunwar da yake masa, yana faɗa masa cewa yana neman taimakon gaggawa,
Tsaki Yana gaba É—aya ya fara sarewa da wannan neman maganin,
Jin sweet ta ƙarayi tsalle ta faɗa jikinsa tana karkaɗa jelar Jikinta, ya motsa fuska yayi a hankali Murya bata fita sosai yace.
"What again?"
Ya faɗa yana buɗe gajiyayyun idanunsa masu cike da bacci, haɗa idanu sukai da Sweet tsora mata idanunsa yayi kafin a hankali yaja numfashi ya miƙe tsaye tare da kama ƙugunsa da hannayensa yace.
"Ohyyyah! Muje naga what happened me kike son faÉ—a"
Jin abinda Abu Maleek ya faÉ—a ne ya sanya sweet yin gaba da sauri tare da nufar wajan kogin,
A hankali cikin nutsuwa da kuma yanayi na zallar gajiya yake bin bayan sweet É—in,
Da sauri kuma jibgegegiyar magen tasa take taka sawayanta a ƙasa, tana nufar gaɓar kogin a haka harta isa inda Julde take yashe a wajan gaba ɗaya ta zame ƙafafuwanta sunyi cikin ruwan,
Tana zuwa dai-dai saitin kan Julde ta tsaya cak tana mai kallon fuskar JULDEN kafin a hankali ta juya ta kalli Abu Maleek,
Tunda ta sweet ta fara tafiya yake biye da ita, har lokacin kuma data tsaya akan Julde, zuciyarsa ce ta buga da ƙarfi al'amarin daya haddasa rufewar idanunsa,
A sanyaye kuma ya miƙa hannunsa tare da dafa kansa yana mai murza goshinsa, gaba ɗaya sam ya mance da batun wannan yaron domin har yanzu bai amince mace bace,
Ya sanyata a matsayin mata zama, buɗe sanyayyun idanunsa yayi a hankali kuma ya mannasu a saman fuskarta yana mai ƙare wa ƙyakƙyawan fuskar idanu, babu abinda yake bashi mamaki ga yaron sai irin jajayen laɓɓansa, wanda a duk sanya ya kallesu sai yani zuciyarsa ta buga da ƙarfi,
Gargasa jikinsa ta shiga mimmiƙewa, cikin kasala da kuma tarin gajiya da yunwar daya keji ne ya sanya durƙosa tare da zubewa dai-dai kanta,
Sam ya rasa mai zai mata da sauri ya sauke numfashi saboda tunawa da yayi shi ɗin cikakken likita ne a ɓangaren gynaecology, zama yayi sosai a gefen ruwan da yake ɗauke da wani sassanyar yashi,
Kana kuma ya miƙa lallausan hannunsa tare da kama tsintsiyar hannun Julde,
Cikin tsoro da kuma fargaba haÉ—i da zallar ta'ajjujin taushin fatar jikin Julde yaja idanunsa ya runtse,
Kana kuma ya É—an matsa jijiyar hannunta cikin Sa'a kuma yaji tana harbawa,
A sanyaye ya cire hannunsa, kana kuma ya É—ura duka tafin hannun nasa a saman jikinta ya shiga dannawa,
Cikin Sa'a kuma ruwan data sha ya fara fita ta cikin bakinta da hancinta,
Almost 3minutes kenan kafin yaga ruwan ya daina fita,
Ajjiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi, cikin taɓe baki kuma yasa tafin ƙafarsa ya zungureta, a tunaninsa zata motsa amma shiru ko numfashi bai ba,
Tsaki yaja, kana a hankali yaja jikinsa can gefe guda yana cikinsa na kukan yunwa, sweet ce ta ƙara hawa jikinsa tana karkaɗa jelar Jikinta a hankali ya buɗe idanunsa yana kwaɓe fuska kamar zai sanya kuka yace.
"Sweet baki tausayi na, uhm ban waje nace munyi faɗa, yanzu me kikeso naiwa yaron nan? Look! Na ciresa a ruwa na fitar da ruwan cikinsa idan bai mutu zai tashi, I'm scared ƙilan Aljani ne"
Ya faɗa yana ɗan rarraba idanu tare da ƙara satar kallon inda Julde take yashe, jin yunwa na neman yiwa cikinsa da kuma lafiyar jikinsa illa ne ya sanya ya miƙe, tare da nufar bishiryar Fasadabir ɗin da niyyar cira ya sha,
Hakan da yayi ne kuma ya sanya sweet bin bayansa da gudu tana tsalle a haka harta cimma masa sabida yanayin yadda yake tafiyar a sanyaye cike da tarin nutsuwa,
Yana zuwa ya sanya hannunsa ya cire Fasadabir É—in guda biyar ciff kana ya cirarwa sweet,
Domin da irin tarkacan zagin nan ya raineta, zama yayi bayan ya wanke shi tass sa ruwa, yana gamawa ya sanya a baki tare gutsira zaƙi da kuma ɗanɗanon da yaji ya ratsa saman harshen sa ya sanya ya rufe idanunsa sosai Fasadabir ɗin yayi masa daɗi.
Sanyin da yayi yawa a wajan ne ya haddasa farfaÉ—o War Julde daga cikin gudun suman da tayi,
Da ƙarfi ta sauke ajjiyar zuciya tare da sanya hannunta a tsakiyar ƙirjinta tana shafa sabida daɗin da taji duk wani nauyi da yake mata ya kau,
Sanyin wajan ne kuma yanzu yake shirin illata rayuwarta, cikin yanayin sanyinta da kuma zallar damuwar da take ciki ne ya sanya cikin ƙaramar muryarty tace.
"Maddibo na!"
Ta faɗa yayinda wasu zafafan hawaye ke fita daga cikin idanunta, zubbur kuma ta miƙe tsaye saboda tunawa da tayi da tarin naggen da take tafe dasu,
Ga yanzu babu sanda ta ina zata lalubi hanya? Ta ina zata fara neman tarin shanun da aka bata kiwonsu?
A hankali ta fara tafiya tana mimmiƙa hannunta gaba gudun kada taci karo da abu, gaba ɗaya ta mance cewa babu riga Jikinta,
Tana tsaka da tafiya ne taji ta bugi wani abu, da sauri tayi baya da ƙafarta,
Abu Maleek kam dake durƙoshe ya sanya goshinsa a ƙasa yana gabatar da sallar magrib ba tare da sanin lokacin ta yayi ko bai ba,
Shi dai kawai yayi duba da duhun garin,
Yazo sujjadar ƙarshe ne kuma yaji an bugi ƙafarsa,
ÆŠan runtsa idanunsa yayi ba tare daya motsa ba,
Julde kam sam bata fahimci inda take fa bare tayi tunanin cewa mutum ne a gabanta,
Ba tare da tunanin komai ba a karo kuma na biyu ta ƙara ɗaga ƙafarta babu zato babu tsammani taji ta sauke ƙafar a
*LITTAFIN NA KUÆŠI NE, BIYA 500 DOMIN SAMUN DAMAR KARANTA WA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK 08119237616*
Saman cinyarsa wacce take da laushi da kuma taushi,
Gaba É—aya tayi kansa saboda jirjin dake kwasarta,uwa uba kuma babu idanun gani balle ta kare kanta daga faÉ—uwar,
"Auchhhiii"
Ya furta saboda yadda ta faÉ—a masa tare da danne masa yatsar hannunsa,
Da sauri ya janye fuskarsa saboda wani wari da kuma ɗuyin daya dakar masa hanci, da sauri ya miƙe tsaye tare baya yana dafe da cikinsa dake bala'in juya masa,
Tunda yake bai taɓa jin wari irin wannan saboda tsananin shaƙar warin da yayi ne kuma ya shiga kelaya amai a wajan,
Gaba É—aya Fasadabir É—in daya sha sai daya dawo da shi, kallon sweet yayi wacce take kallonsa,
Kwaɓe mata fuska yayi kafin gently ya miƙe walking slowly ya nufi wajan kogin,
Zuwa yanzu kam tunu gari ya fara duhu yana zuwa ya wake bakinsa tass, yana sakin numfashin wahala,
Jan jikinsa yayi can gefe yana mai dafe da kansa,
Sam ba warin ne ya damesa ba, illa surar jikin Julde wacce take bara zana wa gangar jikinsa,
Duk da cewa bai taɓa samun kansa a feelings na wata mace ba,
Amma a duk sanda ya tuna lokacin da hannunsa ya sauke a ƙirjinta sai yaji zuciyarsa tayi tsalle sosai, gargasar jikinsa ta shiga mimmiƙewa,
Gajeran tsaki Abu Maleek yaja, sosai yake son É—ago kansa amma yana tsoran abinda idanunsa zasu gani,
Tsayin wajan ne da yayi wa ya sanya Julde ta kurewa waje guda tare da rufe ƙirjinta da dukkan hannayenta,
A sanyaye ya miƙe tsaye tare da sanya hannunsa ya zame jallabiyar jikinsa ba tare daya kalli inda take ba ya cilla mata rigar yana mai ɗan taɓe fuskarsa,
Duk da cewa yana matuƙar son sanyi amma sanyin wajan is worse yayi baƙin yawa mai Illata gangar jiki da lalata lafiyar mutum,
Baya yayi tare da zama daga shi sai baƙar singlet ɗin dake jikinsa tare da long sleeve jeans,
Jingina yayi da jikin bishiryar tare da É—aukan sweet ya rungome ta sosai saboda taji É—umin jikinsa ya lura da rawar sanyin da take,
JULDE tana zaune taji ya cillo mata rigar da sauri ta ɗauka ta sanya jikinta tana sauke numfashi, sosai kowa jallabiya ta rufe mata surar jikinta, ta samar da ɗan ɗumi kaɗan duk da cewa har yanzu tana jin sanyi na ratsa ta, runtse idanunta tayi sosai tana jin yunwa na ƙwaƙular cikinta bakinta ne ya shiga rawa da sauri kuma cikin muryar rauni tace.
"Bawan Allah"
Saukar muryarta cikin kunan Abu Maleek yayi dai-dai da bugawar zuciyarsa wanda ya haddasa lumshewar idanunsa tare sanya fararan teeths ɗinsa ya datse jajayen laɓɓansa,
Taɓe fuska yayi a cikin ransa yace.
"Wayyoooo Oumuu, it's a Baby girl"
Ya faɗa yana fisgar numfashi, jin shirun ne ya sanya Julde ƙara ƙasa da murya cikin rashin kuzari ta ƙara buɗe baki tace.
"Mace ko Namiji?"
Ta ƙara murya can ƙasa, ƙara marai-raice fuska yayi yana rufe idanunsa domin jin muryarta yake kamar ana zuba masa dalma a zuciyarsa,
Kuka Julde ta sanya tare da haɗe hannayenta alamar roƙo tace.
"Dan Allah wanene kai? Ko kurma ne baka magana ne, naji wani ƙamshi a kayan daka bani, naji rigar nada tsayi sosai, daga haka na fahimci da Namiji nake tare, dan Allah wanene"
Dafe kai A.m yayi yana jin yadda kansa yake sarawa,
A hankali kuma ya ɗaga idanunsa tare da saukewa a saman fuskarta duk da cewa duhu ya fara yana hango ƙaramin bakinta da take mamul mamul dashi,
Kamar bazai magana ba sai kuma ya buɗe bakinsa cikin ƙasa da murya kuma yace.
"Aljani ne"
Ya faÉ—a a fili yadda zata iya ji a zuciyarsa kuma cewa yayi.
"Ɗan banzan baki ɗan ƙaramin dashi sai surutu cai cai cai"
Karyar da wuya Julde tayi kafin ta sanya hannunta saman lafaffan cikinta tace.
"Ayyah! Aljani taimakamim da abinci dan Allah"
Ta faÉ—a cikin karyar da Murya hawaye na sakko mata,
Banza yayi mata ya koma ya jingina tare da ƙare rungome sweet sabida shima yana samun ɗan tsuwa a jikin magen tasa,
Bisa dole ta haƙura ta kwanta tare da naɗe Jikinta ciff a cikin jallabiyar tasa wacce tasha rana da kuma iskar duniya,
Abu Maleek kam tuni bacci yayi gaba dashi bai ƙara bin shirman yarinyar ba.
Can cikin dare ihu da kuma ƙugin hadarin dake ƙasa ya fara tasuwa, wanda ya sanya Julde farkawa daga baccin wahalar daya ɗauke ta,
Sosai cikin jejin Mahinjo yake iska bishiyoyi na KaÉ—awa, ga samaniya ta haÉ—e jikinta tana gab da zubar da ruwa,
Cike da tsoro ta fara jan cikinta tana kwaɓe fuska zata saki kuka,
Allah yayi mata tsoran ruwa sosai rasa nutsuwarta take inda daga ana ruwa,
Dab da inda Abu Maleek yake ta tsaya saboda karo da tayi da ƙafarsa,
Abinda bata sani ba tuni ya farka sani ƙara da kuma rugogin hadari, tsoro ne ya hana shi motsawa,
Kamar yadda Julde take bata son ruwan sama shina garesa haka ne, baya son iska sabida lalurarsa gashi babu Wanda ya sani a nan,
Idan ciwonsa ya tashi bai san wanda zai taimaka masa ba,
A hankali kuma ruwa ya fara sauka wanda ya sanya Julde sakin numfashi tayi tana ƙara matsawa inda take jiyo Numfashin Mutumin da yace sunansa Aljani,
Tana matsawa kuma iska mai ƙarfi na tashi cikin gigita da tsoro ya buɗe idanunsa ganin fuskarta dab da tashi ne ya sanya ya kwaɓe fuska,
Yana shirin janye jikinsa daga inda take ne ruwan mai ƙarfi tare iska ya kece, can ƙasan zuciyarsa yace.
"O'ohhhh"
A fili kuma ya ware laɓɓansa yace "Ya hayyu ya ƙayyumu!!"
Ya faɗa yana ta kurewa waje guda danma Allah ya sanya a ƙasan bishiya suke,
Baki JULDE ta ɓare tare da sanya masa ihu wanda har sai da ya sanya hannunsa ya rufe kunansa cikin tsoro daya shigeta tace.
"Dan Allah Aljani ka ɓoye ni a jikinka tsulo ina ji"
Ta faÉ—a tana Marai-raice fuska tana da jan majinar daya sakko mata,
Ya tsuna fuska Abu Maleek yayi yana jin yawo na tarar masa sabida majinar da yaji tasha gaba ɗaya yarinyar ƙazama ce,
Bai taɓa jin karo da mai wari marasa wanka irinta ba,
Tsaki Yana yana tsotse laɓɓansa a hankali ya yunƙura da niyyar tashi tsaye yabar mata wajan, duk da cewa fal zuciyarsa take da tsoran ruwan, babu zato bare tsammani yaji Julde ta...
*ABU MALEEK NA KUÆŠI NE, IT'S 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616*
*BY*
*NIMCYLUV*
*23-24*
Fasa wani gigitaccen ihu tare da cusa fuskarta a tsakiyar ƙirjinsa, gaba ɗaya jikinta rawa yake al'amarin daya kusan ɗauke numfashinta kenan,
Gudun ruwan saman da taji mai É—auke da iska haÉ—i da tsawa ya haddasa mata tsayawar numfashinta na wani lokaci,
Abu Maleek kam sandarewa yayi waje guda, tare da ko mawa baya ya jingina da jikin bishiyar, gaba É—aya ta gigita sa ya É—auka Aljanin gaske ta gani koma wani abu cutarwa,
Sauke numfashi yayi tare da fesar da iska daga cikin bakinsa, daga can ƙasan zuciyarsa kuma wani irin ɗaci da ƙona ya keji,
Ga wani juyawa da kayan cikinsa su kayi sabida wani mugun wari daya shaƙa, ya kuma tabbatar a jikin Julde aka samu warin, tamkar mushe ya mutu.
Gajeren tsaki yaja yana mai cije bakinsa da sauri kuma ya sanya ƙafarsa ya tureta daga jikinsa, a ransa yake faɗin.
"Mayya"
Ya ƙare zan can zucin yana matsawa can gaba, tare da haɗe jikinsa waje guda sai tsuma yake saboda gudun ruwan ya firgita sa ainun,
Ga wani sanyi dake ratsa kofufin jikinsa,
Wanda yake gab da illatasa, da kuma tasu masa da tsuhuwar cutar daya manta da ita.
Da wani irin sauri ya tura kansa tsakanin ta fukan hannayensa, saboda wata gigitacciyyar tsawa da akai,
Wacce ta tawo da wani irin ruwa mai ƙarfin gaske har bai sai lokacin daya buɗe baki cikin Muryar kuka da kuma wanda tsoro ya gama ratsa wa yace.
"Wayyoooo Oumuu na"
Ya faɗa yana shagwaɓe fuska, jin Muryarsa kamar yana shirin sanya kuka ne kuma ya sanya ta tsayar da nata kuka tana mamaki hali irin na Abu Maleek
Domin ta tabbatar shi É—in babbane irin sosai É—in nan.
Amma mene ya sanya ya saki wannan ihun, Shiru tayi tana sakin Ajjiyar zuciya kafin taja numfashi tare da É—an juya juyayyun idanunta,
Cikin siririyar muryarta kuma mai ɗauke da ƙuruciya da kuma zallar shagwaɓa tace.
"Kai ma kana jin tsolo ne?"
Ta ƙare maganar tana mirgina kanta can gefe alamar ita tsoran ta keji,
A karo na farko kuma ya É—aga idanunsa tare da saukesu a saman innocent face É—inta,
Kyakkyawa ce sosai, amma yunwa da kuma wahalar rayuwa sun ramar da ita,
Fuskarta firit idanunta ya tsorawa idanu ganin yadda take kallonsa,
Kafin ya taɓe bakinsa kamar bazai magana ba sai kuma ya cije lips ɗinsa yana fidda numfashi,
Can ƙasan maƙoshinsa yace.
"Daina kallo na, ko na tsole idanun, witch"
Ya faÉ—a yana mai É—auke idanunta daga gare ta, saboda mugun haushin ta ya keji,
Da ace bata zo inda yake ba ai da shima bai ji tsoran saukan ruwan saman ba,
Turo baki tayi tana marai-raice fuska, ita mugun daÉ—i ta keji ganin mutum kusa da ita,
Tayi imanin bazai cutar da ita ba,
Gashi ita tana bala'in sunyin magana dashi amma ta fahimci ɗan neman rigima ne, kuma shagwaɓaɓɓe ne shi ɗin daga jin muryarsa,
Matsawa tayi gefe kafin ta haÉ—e Jikinta waje waje da sauri kuma tace.
"Ayyah! Nifa ban kalle ka ba, babu wanda na taɓa gani a duniya"
Ta faÉ—a Idanunta na cika da hawaye,
"Ji wani iya shege, duk manyan idanun nan ace bata kansa ba to uban ne take kallo, da wani ɗan ƙaramin baki kamar iloka"
Ya ƙare zan can zucin yana murguɗa mata baki kamar wata mace,
"Me kace?"
Cikin damuwa ya taɓe baki yana shagwaɓe fuska tare da haɗe hannayensa yace.
"Ƙilan aljanu irinki kike gani, Momo"
Washe baki Julde tayi har sai dai dafaffun haƙuronta suka bayyana, da sauri ya sanya hannunsa ya toshe bakinsa sabida wani mugun wari daya kawo masa ziraya daga cikin bakinta zuwa hancinsa,
Juyawa yayi tare da bata baya,
Julde da bata san abinda yake faruwa ba, cikin son yi masa magana da kuma surutun da take da shi tace.
"To aini bana gani, ban taɓa ganin kowa ba, ni Makauniya ce fa, ban taɓa damuwa da sai naga wani ba, amma kai dai ina son ganinka saboda ina son ganin yadda Aljanu suke"
Ta faÉ—a tana zare idanu alamar É—an tsoro,
Jin shiru yayi yawa yasa ta ƙara matsawa gaba idan take tunanin yake zaune tace.
"To kaima kana kallo na ko? Kaga askin da akai min? Ko gashi ya fara fesuwa ne?"
Ta faɗa tana shafa kanta jin kan suwait ne babu alamar gashi yasa ta kwaɓe fuska, tare da yin shiru tana sauraran kalar numfashin da Abu Maleek yake fiddawa Murmushi tayi tace.
"Ayyah ashe aljanu ma nayin bacci, nima bari nayi"
Abinda bata sani ba, tunda ta fara magana ya sanya tafukan hannayensa ya toshe kunnuwansa, ya shiga sauke numfashi,
Yana jin yadda cikinsa ke juyawa ga wani yawo da yake tarar masa,
A ransa yake faÉ—in "zata kashe ni da wari, Uhm datti girl"
Sanyin safiya ne mai ɗauke da daddaɗar iska mai daɗi, ga wani ƙamshi ƙasa dake tashi, domin ruwa akai sosai jejin Mahinjo yayi wani irin daɗin gaske,
Saboda tarin ni'imar dake garin, ga kurayen ciyayi sunyi sharr dasu, bishiyoyi sai KaÉ—awa suke.
A hankali ya shiga buɗe gajiyayyun idanunsa, kana kallon yadda ya kwanta kasan ba daɗin baccin yake ji ba, babu wanda zai taɓa cewa Abu Maleek zai iya shiga wannan garin bare har yayi rayuwa cikinta,
Amma Ubangiji shike tsarawa mutum rayuwa yadda kake so sam ba haka kake samu ba,
Kyawawan farar idanunsa ya ware sosai a cikin jejin,
Shi kansa jejin da kuma wether wajan yayi masa bala'in kyau,
Miƙewa yayi tsaye tare da ɗura hannayensa a saman waist ɗinsa ya shiga kallon wajan sosai,
Ajjiyar zuciya ya sauke a hankali kuma ya juya sabida motsin da yaji,
Sweet ya gani a gefensa tana girgiza Jikinta ga wani ƙaton kifi a bakinta sai motsi yake,
Idanunsa ya zare tare taune bakinsa,
Ba tare kuma da yace komai ba,
Ya nufi wajan wani ƙwantaccen ruwa mai kyau wanda ya kwanta a cikin rami, tsugunawa yayi ya shiga ɗaura alwala, kana ya wanke bakinsa tass, gently ya miƙe tsaye ya nemi wani waje mai Tsarki ya gabatar da sallah,
Lumshe shanyayyun idanunsa yayi, sai yaushe zai cimma Birnin Bera ne? How long zai kasance a haka duk wanda ya kansa sai ya É—auka mahaukaci ne,
Ajjiyar zuciya ya sauke yayi kewar abubuwa da yawa masu muhimmanci ƙwarai da gaske a rayuwarsa amma yaushe ne komai zai dai-dai-ta, wannan dalilin ya sanya baya son zaman 9ja, ba komai brain ɗinsa take ɗauka ba,
A karo na biyu ya ƙara sauke ajjiyar zuciya yana jan numfashi kaɗan, Miƙewa tsaye yayi yana ɗan shaƙar iskar dake Kaɗawa, tunanin abinda zai samu ya sanya a jikinsa yake, gaba ɗaya yunwa ta gaba wahalar dashi, bai da cin abinci amma duk bayan 1hour sai ya sanya wani abu a bakinsa ko Inibi ko Apple,
Walking slowly ya fara yana ƙarewa cikin jejin da kallo.
Ruwan dake ɗiga ɗis ɗis ɗis daga jikin leaf zuwa saman fuskarta, ya sanya ta shiga motsawa a hankali da yin miƙa, tana ware blue ɗin Idanunta,
Shiru tayi kamar bai nazari sai kuma ta kwaɓe fuska tace.
"Ayyyah ya tafi kenan bai tashan ba har gari yayi haske"
Ta ƙare maganar tana Miƙewa tsaye tare da tattare duguwar Jallabiyar data yi mata yawa sosai, a hankali ta fara tafiya tana ɗan mimmiƙa hannunta a haka take samawa kanta hanya,
Harta isa gaɓar kogin daya cika sosai, Kamar zai ambaliyya, sam ta manta da batun ruwan dake cikin jejin.
Abu Maleek ƙara ware gajiyayyun idanunsa yayi a gefen ruwan yana kallon tarin manyan kifin da suka fito daga cikin ruwan, zuwa gefen gaɓar kogin, sanadiyyar ruwan da akai sosai, sweet nacan gefe tana ta kokawa da wani ƙaton kifi, ajjiye kifin tayi ta taho da gudu zuwa inda Abu maleek yake tsugune,
Tana zuwa ta tsaya gabansa tana kaÉ—a jela, slowly ya É—aga idanunsa ba tare da yace komai ba,
Ganin kallon da yake mata ne ya sanya ta tafi da gudu a hankali ya shiga Binta da kallo har zuwa inda yaga taja ta tsaya,
Fararan yatsun ta ya zurawa idanu, kamar ka taɓa jini yayi tsartuwa,
Tsaki yaja sai kuma a lokacin ya kula gaba ɗaya tazararta da cikin ruwan bashi da yawa, bawai kuma tsayawa tayi ba ci gaba da tafiya tayi, al'amari daya sanya take ƙara kusantar ruwan kenan,
Gajaran tsaki yaja yana tunanin wannan guntuwar Yarinyar sai ta bashi ciwon kai kafin ya bar wannan garin,
Miƙewa tsaye yayi yana mai harɗe hannayensa,
Tare da ƙare mata kallo, ganin yadda take mimmiƙa hannunta gaba, sai a lokacin ya tuna da maganarta dake cewa, bata gani bata taɓa gani kowa ba,
Da gaske Makauniya ce? Is she a blind? Mamaki ne ya kamasa ga idanunta manya kuma blue kamar nasa amma duk wannan ƙaton idanun ace bata gani,
To mene ya kawo ta cikin wannan jejin mai tarin hatsari? Me take a cikinsa? Shi kaɗai yake wa kansa wannan tambayar ganin ita kaɗai zata bashi amsar tambayar yasa ya yatsunsa fuska yana mai shigar da laɓɓansa cikin bakinsa ya shiga tsotsa.
Julde cikin nutsuwa da kuma ƙarancin kuzari taci gaba da jefa ƙafafuwanta,
A haka ta isa dab da gaɓar kogin, cikin rashin fahimtar inda take sanya ƙafafuwansa ta ɗaga ƙafarta damanta da niyya ci gaba da tafiya,
Babu zato bare tsammani taji.
*DAN ALLAH DAN ANNABI KIJI TSORAN KADA KI KARANTA MIN LITTAFI BA TARE DA KIN SIYA BA, 08119237616*
An sanya ƙafa tare dayin ball da ita gaba ɗaya tayi baya zata faɗi ya sanya ɗaya hannunsa ya daga tsaye ya riƙo gaban rigarta, wahalalliyar ajjiyar zuciya ta sauke tana mai zare manyan Idanunta,
Ta gaba sanya ran cewa taje ƙasa, ƙuri tayiwa wani waje hakan ya sanya Abu Maleek yin tsaki tare da sakinta gaba ɗaya ta faɗa saman,
Jiƙaƙƙen yashin dake wajan, gani yake kamar tana sani take zare masa ido, a fili kuma ya lumshe idanunsa tare da faɗin.
"Kamar wani tafi ido"
Ya faÉ—a yana mai É—aukan babban kifi tare da yin gaba Sweet ma kifi É—aya ta É—auka ta biyo bayansa.
Dafe kai Julde tayi abinka da kai babu gashi, Idanunta ne ya cika da hawaye sosai taji zafin faÉ—uwar da tayi ko kuma tace ya yar da ita,
Baki ta murguÉ—a a fili tace.
"Wayyoooo kai na"
Ta faɗa tana runtse idanunta, ganin zaman sam ba zai mata ba ya sanya ta miƙe tare yin alwala duk ba wani iyawa tayi ba,
Sallah tayi kana ta zauna a wajan tana mai jin yunwa ga kuma ciwon da ƙirjinta yake mata.
Bayan yayi kyasto, ya haÉ—a dotsen wuta da wani a saman É—an busassun itacen daya samu, nan da nan wuta ta tashi,
Faɗaɗa fuskarsa yayi da Murmushi yana bala'in son tsuntsaye da kuma irin wannan halittun, kifin daya suke a cikin wani ƙaton sanda ya ɗauko,
Kana ya É—ura saman wutar ya fara gasawa,
Almost 20minutes kafin kifin ya gasu sai tiriri yake yayi jajir dashi, gashi ƙato mai tsuka da yawa,
A saman wani ƙaton ganye ya ajjiye kifin kana ya fara ci cikin nutsuwa, sweet ma baki ta sanya ta fara yagar wanda ya sanya mata,
Sai da yaci sosai yabar raguwa kafin yaje yasha ruwa,
Gyara tsaiwa yayi tare da É—aukan sweet ya fara duban hanyar da zaibi domin ya isa cikin Rugar Mahinjo a yau É—in nan,
Motsin da yaji a bayansa ya sanya ya juya da sauri ganin Julde tsaye fuskarta cike da hawaye,
Ya sanya ya ɗauke idanunsa da sauri yana mai taɓe bakinsa,
Julde kowa ƙara banza hanci tayi saboda ƙamshin data ji ya sanya cikin siririyar muryarta tace.
"Zanci kifi, zaka sammin ko?"
Zare ido yayi yana mamakin yadda take iya fahimtar wani abun Kamar ba Makauniya ba, tsaki yaja yana Lumshe idanunsa kafin a ransa yace.
"Witch"
Ya faɗa a taushashe cike kuma da gajiya, ganyen ya ɗauka ta cilla mata saman ƙirjinta, da sauri ta ɗauka tana sauke numfashi da kuma Murmushin jin daɗi,
Zama tayi tare da tanƙwashe ƙafafuwanta, ta fara yagar tsukar kifin tana kaiwa ɗan ƙaramin bakinta,
Janye idanunsa daga kan guntun bakin nata, wata dabara ce ta faɗo masa, a hankali yayi baya yana mai shafa ƙirjinsa magana yake sunyi amma sam ya gaji da surutun wannan mai bakin akun,
Yana lumshe idanunsa tare da motsa bakinsa da ƙyar yace.
"Heyyy blind ina ne Mahinjo!!!?"
Ya faÉ—a yana mai É—an É—aga Murya tare da lumshe idanunsa,
Ambaton sunan Mahinjo da yayi ne ya sanya ta tsaya da cin kifin Jikinta ya É—an É—auki rawa,
Sai kuma a lokacin ta tuna da shanun da aka bata kiwo,
Cikin sauri ta miƙe tana jujjuya Idanunta kafin a hankali ta sulale ƙasa cikin Muryar kuka kuma tace.
"Na buni, dan Allah ba kaga shanuwa ba? Wayyoooo Madibbo shikenan zasu kashe ni an kwashe masu shanu"
Da mamaki yake binta da kallo ko kalma guda na maganarta bai fahimta ba,
Tsaki Yana cikin É—aga murya haÉ—i da tsayawa ya koma Abu Maleek É—insa wanda yake na asali bawai yanzu da aka sanya ya zama mahaukaci ba yace.
"Noi inde wuroman?" (Ya sunan garin ku).
Ya faÉ—a in a serious tone.
Cikin firgici ta tarin tsoro tace "Rugar Mahinjo"
Æoyayyiyar ajjiyar zuciya ya sauke yana mai É—an jin daÉ—i dan ko babu komai sai ta rama masa taimakon da yayi mata cikin haÉ—e fuska kamar tana kallonsa yace.
"Let's go"
Ya faɗa yana yin gaba, dafe ƙirji tayi tana sakin kuka kafin tace.
"Dan Allah ka barni a nan wallahi kashe ni ArÉ—o zaiyi"
Haɗe fuska ya ƙarayi saboda yarinyar ta fara bashi ciwon kai, haushi da kuma takaicin tsayawa inda take ma yake,
Gyara tsaiwa yay kafin cikin kakai murya yace.
"Su kashe ki mana, ni dai ba ruwana saikin raima min abinda nayi maki dan kiji"
Kuka ta sanya masa shi kam ko a jikinsa juyawa yayi ya É—auki sweet kana kamar mai raÉ—a yace.
"Muje"
Bata taɓa tunanin bashi da kirki ba sai yanzu, da alama shima daga rugar yake saboda taji yayi fulatanci,
Kanta ta sunkuyar ƙasa kafin tace "bani da sanda ai, bazan iya tafiya ba"
Ta ƙare maganar Idanunta na zubar da hawaye,
Ba tare daya kalleta ba domin shi ya ƙosama yabar inda mayatacciyar yarinyar take, wata igiya ya ɗauka tare da cilla mata yana ɗan yatsuna fuskarsa yace.
"Tied your hand"
Sharrr hawaye ya ƙara sakko mata ta ɗaure hannu kuma? Dabba ce ita da zata ɗaure hannayenta, ganin tana ɓata masa Lokaci ne yasa ya ɗan ƙara daka mata tsayawa wanda shima da kansa sai daya dafe kansa sabida tsorata da tsawar da yayi,
Da sauri ta riƙe igiyar duk Jikinta rawa yake kana ta naɗa a hannunta idanunta na zubar da waye,
Shima yayi hakan ne sabida bai tsayawa kusa da ita bare har ya yi tunanin riƙe mata hannu,
Tana gama ɗaura igiyar ne shi kuma ya riƙe bakin igiyar tare da fara tafiya da sauri yana janta da sabida igiyar dake ɗaure a hannunta.
A haka suka fara tafiya domine isa Rugar Mahinjo.
A can cikin rugar kowa ArÉ—o ne da Barkido sai kuma LamiÉ—o zaune, suna tattaunawa gyara zama LamiÉ—o yayi kafin Yace.
"Na aikata da mutane a sirrince domin su duba min abinda ke faruwa a sakamakonsa harbin da mukaji, sai dai abin mamaki gaba É—aya Shanuwanmu suna nan amma an nemi Julde an rasa"
Da sauri Barkido ya kalli LamiÉ—o tare da faÉ—in.
"Kamarya an nemeta an rasa? Kana nufin ba'a ganta ba ko mene? Tayaya za'a ga Nagge amma ba'a ga mutum ba"
Kallon Barkido arɗo yayi sabida ya gama fahimtar ɗan nasa cewa ya faɗa tafkin soyayyar Julde, shi kam rashin Julden ba ƙaramin daɗi yayi masa ba,
Rashin nata kuma ya ƙara tabbatar masa da cewa Tabbas burinsa zai cika koma yace ya cika, dan matsalar sa ɗaya Madibbo do ya gama da Yakumbo ya gama da Madibbo mai uwa a gindin murhun ma ya gana da shafin ta,
Gyaran murya yayi kaÉ—an kafin ya kai dubansa ga Barkido yace.
"Meye damuwarka? Mene tsakaninka da ita, daman ai burinmu ace yau babu ita, domin idan har tana raye Tabbas burinmu bazai taɓa cika ba, kafi kowa sanin yadda muka sha wahala kafin mu kawo iya zo, dan haka ina gargaɗinka idan ma wani abu zuciyarka take kissima ta daina, Aradon Allah ina ci maka mutunci"
ArÉ—o ya faÉ—a yana nuna Barkido da hannunsa, kafin kuma ya fuskanci LamiÉ—o yace.
"Wane mahaukacin daya Shigo cikin jejin?"
LamiÉ—o ya kalli ArÉ—o kana yace "Barkido babu waje"
Tashi yayi zuciyarsa cike fal da tarin baƙin ciki, tattaunawa sukai kafin ko ya tashi ya nufi makwancinsa sabida dare yayi, gari yayi tsitt.
Ganin duhu yayi sosai ya sanya Julde zamewa a hankali ta kwanta tana sauke numfashin wahala,
Shi kansa Abu Maleek ya gaji tunda suka taho babu abinda yake tsayar da su sai sallah, gashi dare yayi duhu ba zai sanya suci gaba da tafiya ba,
Bisa Dole shima ya nemi waje ya kwanta yana sauke ajjiyar zuciya tare da rufe idanunsa,
Julde numfashi ta ƙara ja da ƙyar tana riƙe da saitin zuciyarta dake wani irin harbawa sabida tsananin ciwon da ƙirjinta yake,
Cikin fidda sauti da kuma da kuma tarin wahala da kuma ciwon dake ƙirjinta ta cije bakinta, tana murje ƙirjinta dake mata wani iri zafi da raɗaɗi,
Zame idanunsa yayi daga kanta yana jan tsaki a ransa yake faÉ—in.
"Guntuwar Yarinya sai ƙaton nono mtwss!!!"
Ya faɗa yana mai kwanciya a saman wata ciyawa dake jiƙe da ruwa.
Washe gari da sassafe sukaci gaba da tafiya ba tare da sunci komai ba,
Tunda suka tafi babu wanda yace komai, yana janye da ita da igiya wajan sallar Zhur sukaiwa Rugar Mahinjo tsinke,
Lokacin gaba É—aya kowa yana cikin Rugar ana hutawa tare kuma da tarin Alhinin rashin ganin Julde wanda tsirari daga cikinsu suke.
Cikin rugar Abu Maleek yabi da kallo yana kalla kuma yaji kansa ya sara da ƙarfin gaske, zuciyarsa ta harba da ƙarfi,
Hakan nan ya samu kansa cikin tarin fargaba kasancewar sa ba komai ne kai bayyana a fuskarsa ba ya sanya ko alamun tsoro bai nuna ba,
Fitowar LamiÉ—o kenan daga cikin bukka idanunsa ya sauka akan Julde da sauri yace.
"ArÉ—o!! ArÉ—o!! War, War ArÉ—o"
Jin Muryar LamiÉ—o ne ya sanya Jikinta ya shiga rawa nan da nan idanunta ya fara zubar da hawaye shkknan yanzu zasu kasheta, abinda take rayawa a zuciyarta kenan,
Yana yana cikin bukka hannunsa riƙe da wata paper wacce babu wanda yasan da ita wajansa, sabida babu wanda ya iya karatu bare rubutu a cikin Rugar.
Yana tsaka da duba paper ne yaji Muryar Lamiɗo yana kwala masa kira da dukkan muryarsa, da sauri ya ɓoye paper kana ya fito,
Abinda idanunsa suka gani ne ya sanya shi zare ido,
Julde a hankali tayi bayan Abu Maleek tana ɓoye fuskarta domin a yanzu shi kawai take tunanin zai taimaka mata,
Gyara ArÉ—o yayi kafin yace.
"Ardon Allah ƙarya kake, shaiii kaci Ubanka ka biya mu Naggen mu, Lamiɗo kawo mana ita nan ka tara mana jama'ar gari"
Jin haka ya sanya Julde sanya ihu a gigice kuma ta sanya dukkan hannayenta a saman ququn Abu Maleek tare da ɗura fuskarta a tsakiyar bayansa ta ƙanƙamesa, da sauri ya runtse idanunsa sabida sarawar da kansa yayi masa ga wata halbawa da zuciyarsa tayi masa,
Kasa motsawa yayi da sauri kuma yasa hannunsa ya dafe kansa saboda yadda yaji Julde ta ƙara....
*ABU_MALEEK NA KUÆŠI NE KIJI TSORAN ALLAH KADA KI TAFI LAHIRA DA ABINDA BA NAKI BA, IT'S 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK 08119237616*
*_Nimcyluv 25-26_*
Manne Jikinta a bayansa, tare da ƙanƙamesa sa sosai, hawaye na zuba daga cikin Idanunta, yayinda dukkan Jikinta ya ɗauki rawa tamkar mazari,
Abu Maleek kam abun ne yazo masa a bazata, jin yadda Julde ta rungomesa tana manna fuskarta a bayansa ne ya sanya shi janye idanunsa a hankali tare da rufe su ruff, ya shiga sauke numfashi a hankali yana mai ɗan taune jajayen laɓɓansa,
Arɗo dake tsaye ya ƙara duban Lamiɗo yace.
"Maza ka É—auka shi ka kawo min shi nan"
Ya faɗa yana mai kallon Abu Maleek kafin Lamiɗo yayi magana Arɗo ya ƙara cewa.
"Kai mahaukaci mene ya kawo ka rugar Mahinjo, me kazo yi a wannan rugar, ko kuma kasan wannan yaron Julde ne?",
"JULDE!!!?"
Sunan da Abu Maleek ya ƙara maimaita wa a cikin zuciyarsa kenan, to mene ma'anar wani suna Julde ne?
A zahiri kuma raunatattun idanunsa ya buɗe tare da saukesu akan Arɗo, ƙara ware idanunsa ya yi akan Arɗo fari ne tass ɗan shawalwali dashi, baya da wani jikin arziƙi sai dugun wuya,
A ƙallah zai iya kaiwa Shekaru arba'in, janye idanunsa yayi ba tare kuma da yace komai ba, domin shi ba wannan yake buƙata ba,
All abinda yake buƙata shine hanyar da zata sada shi da Birnin Bera wannan shi ne,
LamiÉ—o ne kai tsaye ya nufi inda Julde take manne a bayan Abu Maleek tare da rufe fuskarta da tsakiyar bayansa, sai tsuma Jikinta yake,
Yana zuwa ya miƙa hannu zai jawo ta tare da rabata da jikin Abu Maleek ance.
"Wait"
Jin sautin zazzaƙar Muryar mai cike da ilhama da kuma tarin nutsuwa da kamewa ya sanya, Lamiɗo tsayawa cak, sosai Muryar ta dakar masa zuciya ta sanya shi tuna wata makamanciyar Murya data huce a shekarun baya,
Da sauri Lamiɗo na ya ɗaga idanunsa ya kalli Abu Maleek cikin azama kuma ya janye idanunsa dan baya jin zai iya, ci gaba da kallon ƙwayar idanunsa sai zuciyarsa ta buga,
Ya kuma janye idanun ne dalilin wani tarin nutsuwa da kuma kwarjinin daya hango a cikinsu,
Tsoro da fargaba duk ya cika zuciyarsa, saukar Muryar Abu Maleek kuma ya haddasa masa wani irin faÉ—uwar gaba, sosai Muryar tayi masa kama data wani can a shekarun baya,
Cikin son dakewa da kuma mazewa ArÉ—o yace.
"Haii yaron arziƙi wasa ina maka, Hai ka fito daga Bayan wannan Mutumin"
Ya faɗa yana sakin Murmushin takaici, domin ba ƙaramin cika masa ido Abu Maleek yayi ba, baya jin zai iya yiwa Julde wani abu akan idanunsa,
Jin abinda Arɗo ya faɗa ya sanya ta sakin ajjiyar zuciya a hankali ta shiga zare Jikinta daga bayan Abu Maleek idanunsa a Lumshe tana shaƙar wani fitananan ƙamshi daya kawowa hancinta ziyara,
Kallon ArÉ—o LamiÉ—o yayi da alamar "ya haka?" Girgiza kai ArÉ—o yayi kafin ya juya da baya yana faÉ—in.
"Noi indema?" (Ya sunanka)"
Sarai Abu Maleek ya fahimci maganar kuma ya san dashi ake, sabida yana É—an jin fulatanci ba tare da kowa ya sani ba ake koya masa,
Na zai manta sanda Hamida Zubaida take koya masa ba, akwai sanda Oumuu-Ayman ta koya masa,
LamiÉ—o ne yayi murmushi yana kallon Abu Maleek cike da mamaki gashi dai sak mahaukaci amma sam muryarsa ba tayi kama data mahaukaci ba,
"Muje daga ciki"
Lamiɗo ya faɗa yana mai ɗan dai-dai-ta Hausar sa, yadda Abu Maleek zai fahimta, jinjina kai yayi tare dabin bayan Lamiɗo jin haka ya sanya Julde ɗan miƙa hannu zata riƙesa da sauri yayi gaba yana mai harɗe hannayensa a ƙirjinsa,
Tsaya tayi cak jin ance.
"Ko damata maa?" (Meke damunki?)
Zare idanu tayi waje tana dafe ƙirjinta saboda jin Muryar Barkido,
Murmushi Barkido ya saki yana ƙarewa Julde kallo, yana jin wata zallar soyayyarta a zuciyarsa,
Wanda bai san lokacin daya fara ba haka kuma bai san lokacin da zai goshe ba,
Ja baya tayi tana ɗan girgiza kai ganin tsoransa ta keji ya sanya cikin ƙasa da murya yace.
"Babu abinda zan maki Julde kiyi haƙuri dana baya ma"
Ya faÉ—a yana juyawa sabida baya sun ArÉ—o ya fito ya samesa a wajan, shiru tayi ba tare da tace komai ba,
Kamar zai kuka Barkido ya ƙara buɗe baki yace.
"Julde kiyi haƙuri jin? Zaki haƙura ko, bana ƙara yi maki komai"
Ya faɗa idanunsa na ciccikowa da hawayen so da kuma ƙaunar ta, ƙasa tayi da kanta a hankali cikin ƙaramar muryarta tace.
"To na haƙura"
Ajjiyar zuciya ya sauke kafin yace "Nagode, muje ciki na baki kindirmo mai zafi"
Farin ciki ne ya kamata hakan ya sanya ta fara bin sahun tafiyarsa har suka isa wata bukka, ciki ta shiga tana zaune ya je ya kawo mata kindirmo mai yawa a ƙwarya, kana ya sake fita babu jimawa ya dawo hannunsa ɗauke da wasu kayan Fulani masu ɗan haske ya bata tasa.
ArÉ—o ne a gaba Abu Maleek na bin bayansa a hankali cike da Zallar nutsuwarsa irin ta Æ´ar Æ´an sarakai, wanda jinin sarauta ya gama ratsa su,
Wata bukka mai kyau wacce aka cikata da kayan ado irin nasu na Fulani, Arɗo ya sanya kansa cikin Bukkar, Abu Maleek kam tsayawa yayi cak,yana mamakin ta inda zai shiga bukkar gaba ɗaya bukkar a tsakiyar cikinsa ta tsaya, baya tunanin cikin bukkar ma zai Wada cesa, waro manyan gajiyayyun idanunsa yayi waje ganin yadda Arɗo ya sunkuya sosai kamar zai dafa ƙasa kafin ya samu ya shiga cikin bukkar, cije lips ɗinsa yayi yana fesar da iska daga cikin bakinsa, a hankali cikin kuma ƙasaitacciyar muryarsa mai cike da kamala ya ware softness lips ɗinsa masu taushi da ɗan kauri cikin ƙasa da murya very slow yace.
"Goodness"
Ya faɗa yana janye idanunsa daga kan Bukkar, Arɗo dake ciki ne yaji Shiru baƙon mahaukacin nasu bai shigo ba, ya sanya shi leƙo dakai ganin Abu Maleek yayi a tsaya hakan ya sanya yace.
"Ai shaii ka rarrafa ka shigo"
Arɗo ya faɗa yana mai tsare ƙirjin Abu Maleek da kallo saboda wani baƙin zane daya hango, kwance a saman faffaɗan ƙirjin nasa,
Ganin hakan ya sanya Abu Maleek haÉ—e rai kafin ya É—auke idanunsa yana faÉ—in.
"Wicked and stringy man"
Ya faɗa a fili amma Murya ƙasa, Murmushi kawai Arɗo yayi ba tare da yace komai ba,
A hankali ya sunkuya sosai, cikin rashin Sa'a kansa ya bugu da gefen bukkar, kwaɓe fuska yay sosai kamar zai sanya kuka, a hankali cikin Muryar taɓa ra yace.
"Auchhhiii! Daman salon mugunta akai wannan guntuwar abar, an san ai baƙi zasu iya zuwa, mtwss!"
Ya faɗa yana ƙarasa shiga cikin Bukkar duk ya marai-raice fuska kamar zai kuka, ganin ya shigo yasa Arɗo fita tare da ƙwarya a hanunsa, Not too long ya dawo da ƙwaryar cike da kindirmo mai kyau, wanda yake zalla babu algus,
Kindirmon yabi da kallo kafin a hankali ya haɗe ƙafafuwansa waje guda, bai son Kindirmon sabida sam bai yarda da tsaftar mutanan garin ba,
Amma idan yaƙi sha bai san abinda zai samu nan gaba yaci ba.
Zama Abu Maleek ya gyara tare da ɗaukan ludayin Dumar ya sanya cikin ƙwayar kindirmon da aka kawo masa, ganin yadda Kindirmon yake da haske sosai ga wani irin kyau da yayi masa a idanu, ya sanya a hankali cike da nutsuwa ya ƙara naɗe ƙafarsa kana ya ɗebi Kindirmon yakai bakinsa, da sauri ya ja idanunsa ya rufe saboda wani daɗi da kuma garɗi daya ratsa cikin kunnuwansa, shan Kindirmon kuma ya taso mata da duka yunwar daya keji a haka yaci gaba da sha, sai da yasha fiye da rabi kana ya ajjiye,
Murmushi ArÉ—o yayi yace.
"Birnin Bera kace ko, haii daga wannan rugar sai Birnin Bera tafiyar kwana guda ce rakk, amma haÉ—arin tafiyar yafi na shekara guda"
Kallonsa Abu Maleek yayi sai kuma ya ɗan taɓe baki, yana tsotse laɓɓansa wanda har yanzu daɗin Kindirmon yaƙi barin saman harshansa,
Lumshe idanunsa yayi harga Allah matsu ya samu maganin ya koma Benin kana ya ga King Tunde Muhammad Jalal ya samu lafiya daga nan kuma sai koma Madrid baki É—aya, ya samu ya huce dukkan gajiyarsa a can!.
Kai tsaye waje ArÉ—o yayi yana zuwa ya nufi wajan LamiÉ—o ba tare da yayi magana ba, yaja hannun LamiÉ—o zuwa wata bukka,
"Meka fahimta dan gane da wannan baƙon?"
ArÉ—o ya tambayi LamiÉ—o yana share zufar data karyo masa,
Gaba É—aya Abu Maleek ya gama firgita ArÉ—o da kwarjininsa, har baya iya tsayawa inda yake saboda tsoro,
LamiÉ—o ne yaja numfashi kafin yace.
"Ban fahimci komai ba, amma dai kamar bashi da lafiyar ƙwaƙwalwa, duba da yanayinsa da kuma shigarsa, ga kuma yadda kansa gaba ɗaya yaƙi tsayawa waje guda"
Jinjina kai ArÉ—o yayi kafin yace.
"Haka ne,amma akwai lauje cikin naɗi, mene ya kawo sa wannan garin? A cewar sa dai wai Birnin Bera zashi, amsar magani kuma babu wani magani da ake bayarwa, uhm! Kasan babu wanda ya taɓa shiga Birnin ya fito da ransa, saboda haɗarin da mutanan garin suke da shi, kasan mutanan tamkar kuraye haka suke, su kuma kalar tasu maitar a fili suke cin shan jinin Mutum, kuma da sun cijeka shikenan kai ma harbo wannan maitar"
Cike da gamsuwa Lamiɗo ya jinjina kansa kafin yace "haka ne, amma wannan mutumin kamar da sammu a jikinsa, ina kallonsa naji hankali na yaƙi kwanciya, ina ganin mu taimaka masa mu faɗa masa gaskiya zaifi"
Murmushi ArÉ—o yayi domin shi ya gama tsara Abinda zaiyi,
Juyawa yayi tare da nufar bukkar da Julde ke kwance har zai shiga sai kuma ya fasa ya juya yana mai sakin murmushi.
Cikin dare Abu Maleek yana kwance tunani fal ransa, idan ka ganshi zaka É—auka da gaske bacci yake amma idanunsa biyu,
Ƙara yaji kamar na ringing ɗin waya daga bakin bukkar, mamaki ne ya cika masa zuciya domin yasan babu yadda za'ai a samu waya a wannan garin, garin da ku service bashi dashi, gashi ya lura ko addini basu iya ba,
Ware fararan idanunsa yay yana da É—an kasa kunne muryar ArÉ—o yaji yana faÉ—in.
"Sir trying to remembered it, nayi ƙoƙarin ganin na aikata hakan but it's difficult to me, gaskiya i can't do that I'm sorry!"
Shiru yayi yana mai ƙara juya gudun kada wani yazo ya riskesa a haka, jinjina kai yay kafin yace.
"That's great job, any way duk yadda mukai I'll get back to you"
Ya faÉ—a yana mai kashe wayar tare zuge ta zugen wandonsa, a cikin aljihun 3gauther ya sanya wayar kana ya shigo cikin bukkar,
Da sauri Abu Maleek yaja idanunsa ya rufe mamaki ya hanasa tunanin komai bare ya fahimta, Tabbas akwai abinda yake faruwa a wannan Rugar mene shi, yaya akai Shugaban Rugar Mahinjo ya iya sarrafa harshe haka? Da wannan tunanin bacci ya É—auke sa.
Washe gari waje ya samu mai kyau ya É—an watsa ruwa a tsaye gudun infection,
Bayan ya shirya cikin wasu fararan kayan Fulani masu kyau, ya fito daga cikin Bukkar yana mai É—an fesar da huci daga cikin bakinsa,
ArÉ—o dake gefe yace.
"Har ka fito?"
Kallon Mutumin yayi a ransa yace "munafuki"
A zahiri kuma idanunsa kawai ya lumshe tare da buÉ—e su,
Gyara tsaiwa ArÉ—o yayi kafin ya kalli Abu Maleek yace.
"Haii ka buɗe kunne da kyau kaji baƙo, babu wani magani da ake bayarwa a Birnin Bera, gaba ɗaya mutanan garin masu shan jini ne, a tarihi ma babu wanda ya taɓa zuwa koda ƙofar garin ne balle ya shiga, duk wanda yace kazo garin to bayanka ya keson gani Aradon Allah"
Kallonsa A.m yake domin yana son ya fahimci asalin Maganar, babu Abinda Ya gani a idanun ArÉ—o sai zallar tarin gaskiya tsagwaronta,
Juya idanunsa yayi kana ya mirgina kansa gefe yace.
"Are you sure?"
Ya faɗa yana cije bakinsa dan nan da nan yani kansa ya fara sarawa, sosai maganar ta dakesa, mene ya sanya akai hakan? Wane ya sanya Malamin Alaafin ya faɗi haka, lallai Tabbas biri yayi kama da mutum dalilin daya sanya kenan suka hana ya duba King Tunde Muhammad Jalal sabida suna tunanin zai iya fahimtar wani abu, Tabbas dole ya koma Benin ba tare da ɓata wani lokaci ba.
A can Alaafi Kanzaf kowa, tsaro aka ƙara mai tsananin gaske, cikin Alaafin yayi shiru baka ganin komai, ko jin motsin wani face na securities, tsaron da aka ƙara yafi na kullum, babu mai shiga babu mai fita, Al'amarin daya tayarwa da jama'ar Kanzaf hankali kenan,
Kana kuma ya sanya masu tsoro da tarin zullumi a cikin zuƙatansu,
Yau wajan sati guda kenan da tafiyar Jalaluldeen Tunde Muhammad Jalal kenan, tafiyarsa kuma ta haifar da tarin matsaloli wanda ba'a san ta inda suke kunna kai ba.
Salimerh ce zaune a saman bed É—in ta tana sanye da kayan bacci dark brown panjamas, masu kyau,
Waya ce maƙale a kunanta tana sauraran abinda Junaid yake faɗa mata,
Daga can ɓangaren Junaid gyara kwanciyar sa yayi a hankali cikin ƙasa da murya yace.
"My princess kina son zuciyata ta buga saboda soyayyyar ki da tayi min yawa ko? I can't control my self idan ina wajanki ko su kike ba aikata abinda ba Shikenan ba?"
Ya faÉ—a yana jan numfashi, girgiza kai Salimerh tayi kafin tace.
"Ba haka bane, ni aure a yanzu ta kurani zai, ina karatu akwai tarin abubuwan da yake gabana masu muhimmanci"
Uhm kawai ya iya cewa kafin yace.
"Kenan baki sona?"
Girgiza kai tayi tace "i love You, ina sonka Junaid but...,"
Ka tseta yayi da "if you really love me, then marry me"
"I'll" da sauri yace "then when? Kinga stop pretending gobe zanwa Otun magana ya nemi Agba Akin (CHIROMA)domin a nema min Auranki, I'm tried My princess ki shirya zama matar Junaid soon"
Bai jira tayi magana ba, ya katse kiran yana mai mamakin yadda sam bata fahimtar son da yake mata,
Ajjiye wayar tayi domin ita sam babu maganar aure a tsarinta yanzu, tana big issues dalilin daya ta zaɓi karanta Law kuma ɓangaren criminology justice.
Washe gari da yamma Adams ya fito daga shashinsa cikin shigarsa ta ƙasaita, yana sanye cikin wani tattausan farin yadi mai manyan zane, anyi masa ɗinkin half body sai shot hand, yayi masu kyau sosai, ya ɗura wata hula mai gashi sai manyan murjani daya sanya a wuyansa,
Yana tafe a hankali a haka ya isa dinning room ɗin, Oumuu-Ayman ce zaune sai Mai Babban ɗaki da kuma Queen Ayoola, kana Bola lunch suke ga Cook yana serving kowa, lafiyayyan Moi-moi ne wanda yaji bushasshen kifi da kwai, kana da curry da kayan magi, ga wani ƙamshi da yake fitarwa musamman da aka samu wanke mai kyau..
Sai vegetable soup wacce tasha carot da beans sai zallar hanta wacce aka yanka manya,
Kujera yaja ya zauna, yana mai É—an cilla idanunsa ganin babu Shakiru babu SHAREFUDDEEN, motsawa yayi kafin yace.
"Barka da rana Granny Oumuu, Mumy"
Duk suka amsa da "yawwa" a hankali ya fara yin lunch kafin ya kalli Mai Babban É—aki yace "yau zan tafi Cairo"
Da mamaki ta kallesa kafin tace.
"Daman akwai tafiyar ne ko yanzu ka shirya?"
Kallon Salimerh yayi dake fitowa cikin shirin ta mai ɗaukan hankali, tana riƙe da hand bag sai kuma school bag ɗinta, da sauri ta zauna ta fara luch ɗin,
ÆŠauke idanunsa yayi yace.
"Na daÉ—e shirya tafiyar sai yanzu komai ya dai-dai-ta, zuwa dare jirgin mu zai tashi"
Kallonsa Oumuu-Ayman tayi tana jin sam bata yarda da tafiyar amma bata ce komai ba.
"Da ka haƙura zuwa lokacin da ɗan uwanka zai dawo, muga jikin Mahaifin ku zaifi"
Miƙewa yayi yace "nasu yin hakan, amma tafiyar ta zama dole but ba daɗewa zanyi ba"
Jinjina kai tayi tace "Allah ya bada Sa'a"
Queen Ayoola ma Miƙewa tayi tace "za muyi missed babu kai babu Shakiru balle Sharefddeen, ga kuma tashin hankalin da muke ciki na rashin lafiyar King"
Kallonta kawai yayi ba tare da yace komai ba, tafiya yayi kai tsaye zuwa sashin King Tunde Muhammad Jalal domin dubasa, Salimerh ma makaranta ta nufa.
A daran jirgin Adams ya É—aga zuwa Cairo.
Washe gari Otun ya samu Agba Akin da maganar Auran Junaid da Salimerh, suna cikin maganar ne kuma saƙo ya riskesu jikin King Tunde Muhammad Jalal ya tashi,
A ranar babu wanda ya runtsa dan yin Bacci fargaba da cika zuciyar kowa,
Banda sunan JALALULDEEN TUNDE MUHAMMAD JALAL babu sunan wanda yake kira sai sunan Little wanda ba'a san ko sunan waye ba, kawai sun É—auka zafin ciwo ne, a haka gari ya waye masu suna tare da shi sai kumfa yake fitarwa ta cikin bakinsa, ga wani irin zafi da jikinsa ya É—auka jikin yayi jajurr dashi.
Kimanin kwana uku kenan da zuwan Abu Maleek Rugar Mahinjo, rabonsa da Julde tun ranar da suka shigo garin gaba ɗaya, ya manta da babin rayuwarta, shirin komawa ƙasar sa yake,
Domin kwana biyun nan hankalinsa sam yaƙi kwanciya,
Yanzu ma fitowar sa kenan daga cikin Bukkar da yake kwana, a hankali yaja idanunsa ya rufe yana shaƙar iskar dake Kaɗawa,
Cikin Rugar yayi tsitt duk sun tafi kiwo,
Walking slowly hannayenta a saman ququnsa yake tafiya yana É—an sauke ajjiyar zuciya,
A haka ya isa can gefen wata bishiryar mango wanda sukai manya sunyi jawurr dasu,
Daga can gefe kowa Labbo ne tsaye a gaban Arɗo yana faɗin "Da gaske ina sonta kuma na shirya auranta" ƙirjin Arɗo ne ya buga da ƙarfi, yana shirin yin magana kenan sai Barkido yace.
"Nima ina son Julde kuma auranta na ke sonyi"
Da wani irin sauri ArÉ—o ya kalli É—an nasa yana zufa na yanko masa, LamiÉ—o ne yayi murmushi yace.
"Kenan ShaÉ—i ya wajaba a cikin wannan Rugar ta Mahinjo, ga Labbo ga Barkido mazaje a motsa"
ArÉ—o kasa magana yayi sosai tashin hankali ya wanzu a saman fuskarsa, Tayaya Barkido zai ce zai auri Julde bayan yasan burinsu? Kuma yana da tabbacin Barkido zai iya shanye dukkan bulalar da Za'ai masa.
Hannunsa ya miƙa ya ciri Mango tare da cillawa sweet ɗinsa, tsalle tayi tare da buɗe baki Mangon ya faɗa bakinta,
Lumshe idanunsa yay a hankali kuma ya ware bakinsa yace "O'ohhhh" yayi hakan ne saboda zuciyarsa da yaji ta tsananta bugu kwanan nan, musamman yanzu da yaji ta wani harba masa, mango ya cira manya guda biyu kana ya ɗauki Sweet domin komawa cikin bukka, a hankali yake tafiya cike da tarin nutsuwa kamar ance ya kalli gefensa da sauri ya runtse idanunsa kafin ya buɗe idanunsa a hankali, tana zaune hannunta riƙe da sanda ta tura ƙaramar yatsarta a cikin baki tana tsotsa,
Taɓe baki yayi ganin ta ɗan sauya kaya kanne dai yana nan kamar na namiji, gajeren tsaki yaja cikin ransa yace.
"Empty head"
Har ya tafi sai kuma ya tsaya a fili yace "Allah sai na rama tsoran da kika ban, ina sane ai"
Sweet ɗinsa ya cilla mata da ƙarfi kuma yace....
*ABU MALEEK NA KUÆŠI NE, BOOK 1 2 3 SHINE 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616*
*BY*
*SARAUTAR MARUBUTA*
*_Nimcyluv 27-28_*
"Ga maciji nan"
ya faÉ—a cikin É—an É—aga Murya yadda za taji abinda yace, kai tsaye kuma magen ta sauka saman kanta,jelar magen tayi kwance a wuyanta,
Wani kalar numfashi Julde taja saboda laushi da kuma sanyin jikin magen daya ratsa fatar Jikinta,
Tsoran da yayiwa Julde yawa ne ya sanya ta fita cikin hayyacinta tun daga wannan Numfashin data ja bata sake motsawa ba, balle taja wani Numfashin,
Sosai take da jin tsoro abu kaɗan ke firgitar da ita, sweet da itama ta firgita, da sauri ta sauka a jikin Julde ta buɗe baki tare dayin ƙara kana ta nufi wajan Abu Maleek da gudu, tana zuwa ya durƙosa ya ɗauke ta tare da rungome ta, yana shafa bayanta a hankali, kana cikin ransa yace.
"Bana faÉ—a maki ba? Gashi nan tsoro ya hanaki magana"
Ya faÉ—a yana shigewa cikin bukkar gaba É—aya bai lura da halin suman da Julde ta shiga ba.
Barkido dake can tsaye yayi saurin ƙarasawa inda dake tare da durƙosawa, inda take ganin bata numfashi ya sanya ya ɗan firgita, da sauri kuma ya miƙe babu jimawa ya dawo ɗauke da ruwa a hannunsa,
Yayyafa mata ruwa yayi, cikin Sa'a kuma ta sauke ajjiyar zuciya tare da sanya kuka ta ƙoƙarin Miƙewa tsaye Jikinta sai rawa yake.
"Julde, nine Barkidon ki"
Ya faɗa yana yana ƙoƙarin riƙe hannunta, zamewa tayi ba tare data bashi damar riƙe hannun nata ba, cikin shagwaɓa fuska tace.
"Shine ya tsorata ni yayi tafiyarsa ko?"
Barkido da bai fahimci maganar taba yace.
"Waye kuma? Me yayi maki?"
Ya tambaye ta, yana mai É—an juya sai dai baiga kowa ba, turo baki tayi tana sakin ajjiyar zuciya kafin a hankali cikin Muryar rauni tace.
"Wannan baƙon mutumin, Allah bashi da kirki gashi da miskilanci"
Cike da tausayawa Barkido yake kallonta ganin duk ta tsorata har bata iya ɓoye tsoran dake zuciyarta, gashi nan ya fito ya bayyana sosai a saman fuskarta,
Ƙasa yayi da murya yace "Ayyah kiyi haƙuri kinji? Ƙilan bai sani ba"
kwaɓe fuska tayi tace "Allah nima sai na rama, nasan ramawa yayi"
Jimm Barkido yayi zuciyar nayi masa zafi sosai, kafin ya haÉ—iye abinda ya keji yace.
"Kin san shi ne? Me kikai masa da har zai rama yanzu?"
Ya tambaye domin zuciyarsa bata aminta da maganar ta ba,
Hannayenta ta watsa masa irin ohuu É—in nan sai kuma tace.
"Ihu nayi masa akai fa, kuma ai tsolo ruwa inaji"
Jinjina kai yayi alamar gamsuwa, kafin ya gyara zamansa sosai yace.
"Julde ina son muyi magana, nasan ba lallai ki fahimta ba, amma dole zan faɗa maki, kafin nan ina ƙara baki hqr akan abinda nai maki, nasan Ubangiji ne ya rama maki, ta hanyar sanya mini soyayyyar ki mai tsanani a Zuciyata, wallahi Aradon Allah ina sonki kuma Auranki na kayi"
Maganar taji kamar ba zata, tasan cewa bata ilimin soyayyya bata san yaya take ba, dan haka bata kawo wannan tsarin rayuwarta, ita idan aka barta da ranta da lafiyarta da kuma abinda lafiyarta zata samu, ya wadatar da ita, sai kuma ilimi bata ƙaunar zamanta a cikin jahilci,tana buƙatar samun ƴanci kamar kowa, duk ta san abune mai wahala ta samu wannan saboda lalurar rashin ganinta.
Ganin tayi shiru ne kuma ya sanya Barkido yaji zuciyarsa ta buga baya fatan yayiwa Julde dole akan ta susa, yasan Tabbas zai sameta saboda shi É—in jarumi ne zai iya jure dukkan wata bulala da Za'ai masa a wajan shaÉ—i.
"Kina jin tsoro na ko? Saboda abinda muka aikata a gareki? Ban san komai ba Julde duk abinda nayi sanyani akai, ban kuma san dalilin daya sanya Arɗo yace nayi hakan ba, kiyi hqr ina ƙara baki hqr amma ina sonki da gaske, zan baki farin ciki bazan taɓa bari wani ya cutar dake ba"
Shiru tayi tana nazarin kalaman sa saboda Allah ya bata ƙwaƙwalwa duk da cewa bata gani amma tana iya fahimtar kalaman mutum har ta fahimci inda zan can ya dusa,
Ajjiyar zuciya ta sauke kafin tace "zaka sani makaranta? Ina sonyi karatu sosai domin na samu hanya mafi sauƙi wajan kare rayukan jama'a da kuma gano inda mugwayen mutane suke"
Abu Maleek dake can bayansu yana ɗan shan mango a hankali yana jin gaba ɗaya zaman garin ya ishesa, ya ɗan taɓe bakinsa saboda yana jin abinda suke faɗa kasancewar yana da saurin ji kamar maciji, cikin ransa yace.
"Daman kalar zaran dole sai kalar yadin, kayan Shirme sai shirmammu"
Ya faÉ—a yana jan tsaki tare da juya zuwa cikin bukkar,
Barkido ƙara kallon Julde yayi sosai kafin yace.
"Karatu kikeso?"
Da sauri ta É—aga masa kanta tana zare yatsarta daga cikin baki, Murmushi yayi yace.
"Na maki al'ƙawarin indai kika aure ni ko mene kikeso zan maki, wannan al'ƙawarin na ɗauka"
Washe ƙana nan jerarrun dafaffun haƙuronta tayi cikin sanyin murya da kuma ɗan farin cikin daya shigeta tace.
"To Shikenan"
"Kin Aminci zaki auran?"
Ya faɗa yana mai kallon saman ƙirjinta tare da sauke ajjiyar zuciya, kafin tayi magana yaji daga bayansa ance.
"Jarumtar ka itace zata tabbatar cewa ka dace da auranta ko kuma a'a, ka daina saye zuciyarta domin zaka cutar da ita, saboda ba kai ka ɗai kake sonta ba ka mari ƙarfinka ya baka ita"
Labbo ya faɗa yana dire sandar hannunsa, Miƙewa Barkido yayi kafin ya fuskanci Labbo yace.
"Idan batu kake na Jarumtar ka ɗauka Julde ta zama tawa, idan kana magana ƙarfi ne kasan cewa wajan ka tarar, idan maganar saye zuciya kake wannan saƙo ne daga zuciyar da take so zuwa zuciyar da akeso ina fatan ka fahimta?"
"Aradon Allah ƙarya kake, Julde Matana ce nine zan aureta, idan baka shirya ba ka shirya shaɗi Arado jikinka zai faɗa maka"
Juyawa yayi ya kalli Julde saboda yaga yaya yanayin ta yake, tana nan zaune ta cure waje guda sai faman juya idanu take da dukkan alamu fata fahimci inda zan can yake ba,
ÆŠauke idanunsa yay kafin ya juya ya kalli Labbo yace.
"Na daÉ—e da shiryawa, ina maka fatan samun nasara"
Yana faÉ—in hakan ya juya zuwa cikin wata bukka, bin bayansa Labbo yayi da kallo, kafin ya maida idanunsa zuwa ga Julde dake zaune tana aikin tsotsar yatsarta,
Kamar zai mata magana sai kuma kawai ya juya tare da nufar bukkar Mahaifiyar sa.
Abu Maleek na shiga cikin bukkar kowa zamewa yayi tare da cire rigar jikinsa, Lumshe idanunsa yayi yana daɓe baki kafin ya ware laɓɓanta cikin gajiyawa yace.
"Kaya duk wari, Uhmmm"
Ya faɗa yana cilli da rigar tare da sanya hannunsa ya saman ƙirjinsa ya shiga shafa ƙwantaccen gashin ƙirjinsa, tunani ne fal zuciyarsa a yanzu kuma tunanin Mami Shine yafi damun zuciyarsa, ina take? Wane ya ɗauke ta? Mene ya sanya Adams cewa shi ne ya ɗauke mahaifiyar su? Mene ya sanya yake zarginsa? Wannan tambayoyin sune suka tare a cikin zuciyar Abu Maleek, amma sam bashi da amsar su, gaba ɗaya yaushe ya dawo garin ma? Tafin hannunsa ya sanya a saman goshinsa ya shiga ɗan murza goshinsa a hankali yana sauke numfashi, taune leɓansa yayi yana zuciyarsa na tsananta bugu, a hankali ya sauke wata wahalalliyar ajjiyar zuciya tare da sanya hannunsa a dai-dai tsakiyar ƙirjinsa ya ɗan matse wajan,
Idanunsa ne ya sauka a saman zanan dake ƙirjinsa har zuwa ƙasan cibiyar sa, lumshe idanunsa yay a hankali ya furta.
"Where are you Mami? Ina nothing without you, ya rabbi! Come to our family Mami"
Ya ƙare zan can yana ɗan runtse idanunsa da wannan tunanin kuma bacci ya ɗauke sa.
A can wajan ruga kowa tuni ArÉ—o ya sanya aka buga tambura na sanarwar, kafin kace me dukkan jama'ar dake cikin Rugar maza da mata yara da manya sun halarci kiran ArÉ—o,
Bayan kowa yazo ne ArÉ—o ya gyara zamansa tare da fuskarta jama'ar Rugar yace.
"Kamar yadda muka sani a al'adance idan mane ma sukaiwa yarinya yawa, akwai wata hanya domin kawo mafita da kuma samun sauƙi wajan ware mutum guda wanda ya amsa sunan Jarumi da zai zama miji ga wannan Yarinyar haka ne?"
Gaba É—aya suka amsa da
"Eh"
Gyara zama yayi yace "akan maganar Julde ne, Yaro Labbo yaga Julde yana so, ga wannan yaro nawa Barkido yaga Julde yana so, kowa kuma ya cancanci a bashi a auranta, bisa wannan dalilin ya sanya za muyi abinda muka saba a al'adance, ma'ana zamu gabatar da SHAÆŠI tsakanin ma nema biyun, wanda ya samu nasara shikenan ya zamu auran wannan yarinya"
Gaba É—aya sukai na'am da zan can ArÉ—o kafin É—aya daga cikinsu yace
"Yau she ne za'a gabatar da SHAÆŠIN?"
Arɗo na Miƙewa tsaye yace.
"Babu jira ai, dukkan mane man su shirya gobe za'a gabatar da komai"
Wani Murmushin jin daɗi Barkido yayi yana mai Miƙewa tsaye tare da shigewa bukkar Adda Manga (Senior sister) domin ta fara shigarsa daman ya daɗe da shiri saboda zuwan irin wannan ranar, shima Labbo wajan iyayensa suka nufa nan kowa ya fara shiri,
Abu Maleek kam dake bacci mai san meke faruwa ba, yana jiyo hayaniya sama² dai amma baya fahimtar komai,
A wannan ranar babu wanda ya kwanta bacci gaba aka fara shirin shaÉ—i sai tsuma samari biyun ake wanda suka kasance ma nema aure ga Julde wacce itama bata san abinda ke faruwa ba, ta bukka tana bacci yatsarta sanye cikin bakinta.
A can Alaafi kowa yammaci ne mai É—auke da wata sassanyar iskar dake KaÉ—awa, alamu ne dake nuna cewa yanayin damuna zai fara, duba da yanayin yadda samaniya ta cika da gajimare mai duhu da kuma jaa, gaba É—aya weather ta sauya sai iska ake garin yayi kyau sosai ga wasu kukan tsuntsaye dake tashi a hankali.
Junaid ke tafiya cikin kuzari da kuma izza, yana sanye da black É—in shadda mai kyau,
Sosai fuskarsa ta faɗaɗa da Murmushi tunda yaji saƙon cewa an bashi auran Salimerh duk sanda ya shirya ya fito, dalilin fitowar sa ma tun jiya yake kiran Number bata answering shiyasa ya yanke shawarar zuwa ya sameta.
Yan tafe bayi da barori na gaishesa, a haka ya isa cikin sashin Queen Ayoola tana zaune saman wata lallausar kujera mai kyau, ga hadinkai sai fifita suke mata duk da uban sanyin dake tashi a parlon nata,
Ga wasu kuma na matsa mata ƙafafuwansa ta, wasu kuma ma jera mata kayan motsa baki,
A bakin ƙofar parlon ya tsaya tare da neman iso, wajan Queen Ayoola,
Ba jima aka bashi damar shiga, bakinsa ɗauke da sallama ya shiga,ganin mai shigowar ne ya sanya Queen Ayoola yin wani ƙawataccen Murmushi tare da bawa Junaid umarnin shiga, bayan sun gaisa ne Junaid yace.
"Mai Kanzaf da Alaafi baki É—aya Salimerh fa?"
Cikin jin daÉ—i maganar ta Junaid tace.
"Tana sashin Bola, kaje mana"
Miƙewa yayi yana faɗin "godiya nake, na barki lafiya Jagorar Alaafi"
Da Murmushi tabi bayansa da kallo, kai tsaye kuma shashin Bola ya nufa, bayan anyi masa iso ne ya shiga,
Suna zaune a parlo suna cin abinci idar da sallar su kenan ya shiga,
MALEEK dake zaune saman sofa yayi saurin tashi yana sakin kuka tare da nufar inda Bola take zaune,
Murmushi yayi yace.
"Maleek ka girma till now bak daina gudun mutane ba?"
Bola da ajjiye spoon ɗin hannunta tare da Miƙewa bayan tasha ruwa tace.
"Ai na rasa irin Maleek, bashi da yarda gaba É—aya"
Ta ƙare maganar ta kama hannunsa tare da nufar side ɗin ta,
Salimerh abinci ta keci a hankali ganin bata da niyyar yi masa magana yasa shi miƙewa tare da jan kujera ya zauna yana mai kallon fuskarta yace.
"Congratulations Madam!"
Juya idanunta tayi tace
"For???"
Murmushi yayi tare da fara cin abincin plate É—inta yace "uhm soon zamu zama miji da mata"
Daga yaci gaba da janta da Shira.
Washe gari bayan tayi shirin tafiya Makaranta ta nufi Sashin King Tunde Muhammad Jalal, tana zuwa ta samu Oumuu-Ayman zaune a gefe tana masa sannu, zama tayi cikin damuwa tace.
"Yaya jikin nasa yanzu Oumuu-Ayman?"
"Jiki Allahamdulillah Salimerh"
Ta faÉ—a a hankali gudun kada hayaniya ta damesa, Shiru tayi tana kallon Mahaifin nata, kafin tace.
"Wai wanne irin ciwo ne haka? Ace har yanzu babu sauƙi"
Ajjiyar zuciya Oumuu-Ayman ta sauke tace
"to yaya za'ai da ikon Ubangiji Auta? Muci gaba da addu'a Allah ya dawo da Zaki lafiya"
"Ameen" tace Idanunta na sauka a bakin King Tunde Muhammad Jalal ganin wani farin yawo na fita daga cikin bakinsa yasa a hankali ta sanya yatsarta ta shafo yawon ganinsa yana yauƙi ne ya sanya tai saurin kai yatsar bakinta, wani ɗaci taji ya game bakinta da sauri ta Miƙe tsaye tana faɗin "Garin meriz??? Innalillahi wa'inna ilaihir Arjun gubar ƙune jini"
Rugar Mahinjo
A hankali yake buÉ—e idanunsa wanda sukai masa nauyi, bakinsa É—auke da addu'a,
A hankali kuma ya yunƙura tare da tashi zaune,
Hakan nan yay yake jinsa wani iri jikinsa yayi masa nauyi yana buƙatar motsa jiki sosai,
Idanunsa ya É—aga ganin ArÉ—o ya shigo ga kuma kiÉ—a dake tashi a Rugar, tun kallon farko da yayiwa ArÉ—o bai sake kallonsa ba.
"Kamar dai julal ya bayyana, what the fork" ya faÉ—a yana jan numfashi duk abi an cika mutane da ihu, Kallonsa ArÉ—o yayi kafin yace.
"Wasan motsa jiki ne"
Da sauri ya buÉ—e idanunsa kamar bazai magana ba sai kuma yace.
"Uhm ball or what?"
Ya faɗa yana Miƙewa tsaye tare da yin waje domin jikinsa duk ciwo yake masa, yana fita kowa ya mutane da yawa sai kiɗe-kiɗe ake.
Bayansa ArÉ—o ya biyo yace "ko kana so ne?"
Lumshe idanunsa yay tare da buÉ—ewa ArÉ—o yace.
"To muje na gabatar dakai"
Gently yabi Arɗo jiki babu ƙwari, Barkido ne da Labbo a tsakiyar filin kowa jikinsa da guro jikinsu sai rawa yake, ga wata zabgegiyyar bulala a hannun Barkido da alama shine zai fara dukan Labbo, kana ganin bulalar kasan tayi shekaru a jiƙe saboda yadda ta kumbura,
ArÉ—o ne yace.
"An samu ƙarin ma nemi, yanzu jaruman namu guda uku ne"
Jin haka yasa Labbo tsorata da kuma firgita, a hankali ya dinga janye jikinsa kafin kace me ya nausa cikin jeji domin tsira da ransa, domin labari yazo masa hadda kitsan kibari aka saka wa bulalar Barkido,
A hankali Abu Maleek ya dawo tsakiyar filin a ransa yace "bana faÉ—awa Oumuu na girma ba, bari naiwa wannan duka zan bata labari"
Ya faÉ—a yana cije baki, Barkido ne yace "kai baka san komai akan wannan abun ba, kada kayi a sarar ranka, ka janye ka bar min kamar yadda É—ayan ya gudu"
Abu Maleek damai san kan abun ba ya kalli Barkido yana mai ɗan tsotsar laɓɓansa kafin yace.
"Uhm ba'a sauya min ra'ayi, idan nace zan yi to zanyi kada ka cikani da ihu kayi abinda ya dace"
Ran Barkido ne ya ɓaci a ransa yace "za kaci Ubanka yanzu mahaukacin banza kawai"
Ya ƙare maganar yana fincike rigar jikin Abu Maleek nan da nan surar jikinsa ta bayyana mai cike da haiba, ga zanan ya fito raɗau gwanin sha'awa, ƙuri Arɗo yayi masa da ido, a na haka aka bawa Barkido umarni,
Gyara tsaiwa yayi sosai tare riƙe bulala hannunsa da kyau, babu zato babu tsammani Abu Maleek yaji an zabga masa bulalar a tsakiyar bayansa, runtse idanunsa yayi saboda tsananin azaba da kuma raɗaɗin daya shige sa a lokacin guda,
Kafin ya dawo daga gigin dukan Barkido ya ƙara shimfiɗa masa wata bulala a tsakiyar bayansa zuwa tsakiyar kansa, dunƙule hannu Abu Maleek yayi tare da langwaɓar da kansa gefe guda cikin a zababban zafin daya ratsa masa jijiyar kansa ya buɗe bakinsa yace.
"O'ohhhh"
*Abu Maleek na kuɗi kada ki karanta bada izini na ba, kiji tsoran Allah idan kina buƙata kiyiwa wannan number mgn 08119237616*
*_Nimcyluv
29-30_*
Ajjiyar zuciya Abu Maleek ya sauke, tare da runtsa idanunsa saboda wani azaba da yaji ya ratsa saman fatarsa, yana neman gigita masa lissafi.
A hankali kuma wata zufa ta fara yanko masa, yadda jikinsa ke rawa kaɗai zai fahimtar dakai Tabbas bulalar ba ƙaramin shigarsa tayi ba.
Jikinsa ya cure waje guda, yana jin yadda naman jikinsa yake rawa tamkar zai ciro daga jikin ƙashin sa ya faɗo ƙasa.
A hankali ya fesar da numfashi daga cikin bakinsa yana mai jan numfashi tare da gyara tsaiwarsa,
Yana mai shigar da lip's É—insa cikin bakinsa yana tsotsa.
Sweet dage can gefe ta shiga tsalle tana sakine ƙara, tare da ɗaga jela, ƙurie yayi mata da idanunsa,
Kafin yaga wasu ruwa na taruwa a cikin Idanunta, ƙara runtse idanunsa yayi a hankali kuma jikinsa yaci gaba da ɓari, yana mai ɗan taune leɓansa.
A karo na uku kuma Barkido ya ƙara saita bulalar hannunsa tare da sakarwa Abu Maleek a tsakiyar bayansa,
"Uhmmmmm"
Shine kawai abinda bakinsa ya iya faÉ—a,domin azabar da yaji ta huce ya buÉ—e bakinsa yayi ihu,
Gaba É—aya tsukar jikinsa rawa take,
Bai taɓa samun kansa cikin a azaba mai raɗaɗi a jikin irin yau ba.
Wata kyakkyawar ajjiyar zuciya ya sauke, tare da taune leɓansa gumi ya shiga tsastsafo wa a tsakiyar goshinsa lokacin,
Da Barkido ya sakar masa bulala ta biyar.
Cikin jin daɗi da kuma farin cikin samun nasara kuma Barkido ya ƙara sakarwa Abu Maleek bulala ta goma a gefen hannunsa,
Yana tsaye cirr daga inda yake ko motsi ba yayi, kansa a ƙasa ilahirin jikinsa kowa rawa yake,
Ga wata zufa dake yanko masa,
A dukkan kofufin gashin jikinsa, laɓɓansa sai rawa suke saboda tsananin a zaba, da kuma raɗaɗi haɗi da zugin dake gigita masa fatar jikinsa.
Gefe kowa Arɗo ne da Lamiɗo zaune suka kallo mamaki duk ya cika su, ganin ko wani ƙyakƙyawan motsi Abu Maleek bai ba, bare a sanya ran cewa zai sanya kuka kana ya gudu daga cikin rugar baki ɗaya.
LamiÉ—o ne ya gyara zamansa tare da sakin murmushi kana ya fuskanci ArÉ—o yace.
"Da kasantuwar Baƙon Mutumin nan zai shanye dukkan bulalar da Za'ai masa, yanzu ana bulala ta ashirin da biyu ne bulala takwas kawai ta rage masa, amma ko motsi bai ba, bare kasa ran cewa hawaye zai zuba daga cikin idanunsa, na tsorata da al'amarin sosai"
Murmushi Arɗo yayi kafin ya juya ya sauke idanunsa akan fuskar Barkido wanda shima tashin hankali ya bayyana ƙarara saboda ganin ya yi bulala ta wajan ashirin da biyar amma babu alamar Abu Maleek zai kuka ko kuma ya gudu daga cikin filin baki ɗaya,
Idanunsa ya É—auke daga kallon Barkido kafin ya juya ya kalli LamiÉ—o yace .
"Burina daman Wannan mahaukacin ya shanye wannan bulalar nan, domin ba ƙaunar Barkido ya auri wannan Yarinyar, kasan abinda yake gabanmu, kasan kuma dalilin daya sanya na raba Madibbo da ransa, wannan dalilin ya sanya itama nake son ganin bayanta amma Allah bai ba, nayi amfani da wannan damar ne wajan ganin tayi nesa damu baki ɗaya, yadda zata mance data taɓa rayuwa cikin Fulani balle kuma ta tuna sunayen mu, jin daɗin kuma duk inda ta ganmu ba zata taɓa fahimtar su waye ba, balle kuma ta kama sunayen mu a baki,
Zanyi farin ciki sosai ace wannan Mahaukacin ya samu na sara yaje can su ƙarata shi da ita"
Cike da gamsuwa LamiÉ—o ya jinjina kansa, kafin ya juya ya kalli Abu Maleek a dai-dai lokacin da Barkido yake sauke masa bulala ta talati cifff,
Juyawa yayi ya kalli ArÉ—o yace.
"Tayaya kake tunanin bulalar da akai masa zata damesa? Kallesa da kyau, wanne bashi kaÉ—ai bane akwai tsari mai yau gaske a jikinsa wanda shi kansa bai san dasu ba, hatta wannan magen da yake tare da ita rai da rai ban amince da ita ba,
Tabbas akwai wani Æoyayyan al'amari da yake tare da shi Tabbas, akwai kuma tarin Æ™addarori a cikin rayuwarsa"
Miƙewa tsaye Arɗo yayi kafin yace.
"Ba wannan ke ban mamaki, tsarin kyahun halittarsa, haibarsa da zallar isa ƙasaita, zanan ƙirjinta yana fisgata sosai, kana ganinsa kaga babban mutum Wanda rayuwa cikin talakawa sam bai saba da ita ba, sauƙin kansa kuma abin burgewa ne,yana rayuwa damu babu ƙyamata, abu ɗaya na lura baya son ihu a saman kansa, raɗashi yake, tambayar a nan mene ya sanya ya zama mahaukaci? Mahaukacin gaske ne ko kuma na ƙarya? Wanne dalili ya sanya ƴan uwansa turosa cikin Birnin Bera ko ƙaunarsa ne ba sayi?"
Shiru gaba É—aya sukai, tare da nufar inda Abu Maleek yake, Barkido kam baya yayi tare da neman waje ya zauna, shi kansa da yayi dokan jikinsa mugun ciwo yake sosai, amma al'amarin Abu Maleek ya firgita sa sosai, yana danne wa saboda kada mutane su Fahimci halin da yake ciki.
Abu Maleek kam gaba ɗaya baya gane abinda yake faruwa ya daɗe da shiga ɗaya duniyar tasa, tun lokacin da yace "O'ohhh" hannunsa gaba ya dunƙule waje guda jikinsa duk ɓari yake,
Yayinda jijiyoyin kansa suka fito sukai raÉ—a raÉ—a a saman goshinsa,
Jin alamar tafiya ne kuma ya sanya ya juya ya kalli gefensa, Ganin ArÉ—o da LamiÉ—o na nufu inda yake tsaye ne ya sanya da wani irin sauri ya juya ya nufi wata bukka dake kusa dashi, ko kallon gabansa baya iyawa,
Sweet na ganin haka ta rufa masa baya, jikinsa na wani irin ɓari na azaba ya faɗa cikin Bukkar tare da faɗawa saman wata tabarma kaba daya gani.
A hankali ya É—aga hannunsa da niyyar ya jawo sweet jikinsa, jin babu sweet kusa sai kamar mutun a kusan shi, ya sanya bai jira tsayawa komai ya sanya tattausan hannunsa wanda yake fidda wani irin gumi mai zafi ya jawo wanda kusa dashi jikinsa,
Cikin bacci Julde taji an matse ta sosai, kamar za'a rabata gida biyu, a hankali ta motsa domin yin baya, amma riƙon da Abu Maleek yayi mata bana wasa bane, ya matseta sosai a jikinsa, tamkar zai mayar da ita ciki,
Yadda jikinsa ke rawa haka nata ya shiga rawa domin tsoro ne ƙarara ya ratsa mata zuciya.
Wata lafiyayyiyar ajjiyar zuciya A.m ya sauke yana mai ƙara shigar da Julde jikinsa, a wannan lokacin baya gane fari balle baƙi burinsa kawai ya jisa jikin wani ko zai samu nutsuwa, ga wani sanyi da yake ratsa masa kofofin jikinsa,
Jin wani ɗumi na fitowa daga Jikinta ne ya sanya ya ƙara sauke numfashi tare runtsa idanunsa yana taune leɓansa wanda sukai jajirr zai ɓari suke.
A hankali ya ƙara sauke wani Numfashi, yana ɗan tura kansa cikin tsakiyar cikinta, ɗumi da kuma taushin fatar ta ya sanya ya ɗan fesar da numfashi,
Cikin son samawa kansa nutsuwa daga cikin azabar daya keji ne, ya sanya gaba ɗaya ya mirgina gefe guda, yana mai ƙara sanya dukkan hannayensa guda biyun,
Tare da matse ququnta wanda har sai da Julde ta saki wata ƙara tana kwaɓe fuska zata saki kuka,
Jin sautin ƙara a kunansa ya sanya a hankali ya ɗan matsa ququn nata, domin gani yake Kamaru daga nan ɗumin jikin nata yake fitowa, shi kan san bai san Wacece ko kuma waye a kusa tashi ba, All what he needs yaji sassauci daga azabar da Barkido ya gana masa,
A hankali kuma ɓarin da jikinsa yake ya fara raguwa, yana mai ɗan ƙara shigar da ita faffaɗan ƙirjinsa ganin bata cika ƙirjin nata bane,
Ya sanya a hankali ya ƙara tsuke hannayensa domin ya samu yaji ɗumin sosai.
A hankali numfashin cikin bakinsa yake fita yana dukan saman fuskarta, wanda ya sanya take sauke ajjiyar zuciya, saboda ƙamshin Spraymintt and Freshmeltz with strowbeery mouth freshnerh data ke shaƙa, ƙamshin da bata taɓa jin irinsa ba,
So take tasan wanene amma babu idanun gani, shiru tayi ta zubawa sarautar Allah idanu.
Abu Maleek kam a hankali kuma a wahalarce yake fidda wani numfashi mai mai zafin gaske, sai taune leɓansa yake,
Cikin ransa banda
"Ya Allahu Ya Rahamu"
Babu abinda yake ambata,
A hankali kuma ya tura tafin hannunsa cikin rigarta tare da manna Tafin hannunsa dake fidda wani gumi a tsakiyar Jikinta, Ajjiyar zuciya Julde taja saboda wani a zababban zafi daya ratsa mata fatar Jikinta,
Almost 20minutes
Kafin ya fara sauke ajjiyar zuciya numfashi na sauka a hankali, gaba É—aya jikinsa ya saki cikin nutsuwa kuma yake zamewa daga Jikinta yana mirginawa baya,
Sai kwaɓe fuska yake yana tsotsar laɓɓansa wanda sukai jajirr saboda taunesu da yake, a haka baccin wahala ya ɗauke sa.
Baya tayi tana É—an zaro ido waje tare da turo bakinta gaba,
A hankali ta miƙe zaune tare da ɗaukan sandar ta, cikin nutsuwar da take tattare da ita,
Ta fara lalubar hanya a haka ta samu ta fita daga cikin Bukkar,
Still kuma hancinta bai bar jiyo mata ƙamshi da ɗumin bakinsa ba, kwaɓe fuska tayi a fili tace.
"Mugunta kawai, wannan ƙamshin sai kace me"
Ta ƙare maganar tana murguɗa bakinta,
Arɗo da Lamiɗo wajan Barkido suka nufa kafin suzo inda yake ya miƙe tsaye yana kallon Mahaifin sa yace.
"Na cinye ShaÉ—i nike da Julde, dan haka a É—aura mana aure kawai"
Kallonsa ArÉ—o yayi kafin yayi murmushi yace.
"Daka dakesa kaga Hawaye ya fita daga cikin idanunsa? Ko kuma kaga ya motsa daga inda yake bare kayi tunanin zai gudu, Tabbas ka dakesa amma hakan baya nufin kai ne da Julde"
LamiÉ—o ne ya kalli Barkido kafin yace.
"Yadda ka dakesa shima zai ya rama wannan dokan, idan ka shanye bulala talatin ɗin da zai maka kamar yadda ya shanye, to sai a nemi mafita domin duk kun cika Jarumai,idan kuma ka kasa shanye bulalar to tabbatas Wannan baƙon mutumin shike da auran Julde"
"Yaushe zai rama dokan nasa da nayi masa? Uhm! Tayaya kuke tunanin wannan zaimin dukan da zanyi kuka, sai dai ayi kukan doki"
Barkido ya faɗa yana cije bakinsa domin yasan Abu Maleek bazai taɓa yi masa dukan da zai gigita masa lissafi ba.
ArÉ—o ne ya kalli jama'ar wajan baki É—aya tare da faÉ—in.
"Kamar yadda kuka sani, idan anyi SHAƊI, ba'a mai da martani sai shekara ta zagayo, amma duba da yadda abun yazo a ba zata babu zato balle tsammani wannan baƙon mutumin ya shiga cikin jerin mutanan da suke son wannan yarinya,
Bisa wannan dalilin ya sanya gobe Za'a maida martani idan baƙo ya samu nasara akan Barkido shike da yarinya, idan sunyi kunan doki ma'ana Barkido bai kuka ko ya gudu ba, to sai a bawa yarinya zaɓi ta a cikinsu wanda ya zaɓa shi za'a bata"
Gaba É—aya mutanan Rugar Mahinjo suka haÉ—e baki wajan faÉ—in
"hakan yayi kyau"
A haka taro ya watse wasu nayiwa Barkido fatan nasara domin shi ne nasu, wasu kuma na yiwa Abu Maleek fatan samun nasara, domin sun san cewa Julde ba daɗi ta keji ba a wajan su Arɗo, tsoron kuma da akewa Arɗo ne ya sanya duk matan Rugar suka kasa ɗaukan Julde su riƙe a wajansu.
ALAAFIN KANZAF
Salimerh ce tsaye da Oumuu-Ayman, tana sauraran abinda take faÉ—a mata.
Ajjiyar zuciya mai ƙarfi ta sauke kafin ta juya taga babu kowa a wajan cikin ƙasa da murya cike kuma da damuwa tace.
"Oumuu-Ayman yanzu wa kike tunanin zai bawa King Tunde Muhammad Jalal Garin meriz na ƙuna jiki, wato dalilin daya sanya aka tura Abu Maleek kenan Saboda ansan zai iya gane gaskiya, Innalillahi wa'inna ilaihir Arjun Oumuu-Ayman kullum Dady ƙara kusantar lahira yake, gaba ɗaya sannu a hankali jininsa ya ƙune, mene ya sanya hakan? Mene yasa mutane basu da tsoran Allah ne? Me yasa kowa kansa ya sani?"
Ta ƙare maganar tana sakin kuka mai ratsa zuciya,
"Know one's care about my father's sick, kina kallo Babu Aremos na Alaafin, Ba bro Shakiru ba Junaid balle babbansu Sharefddeen mene ya sanya hakan ne? Why basu son zama tare damu"
Jan numfashi Oumuu-Ayman tayi kafin a hankali ta sanya hannunta, ta kama hannun Salimerh suka nufi sashinta.
Suna barin wajan Iyalode dake laɓe ta riƙe haɓa, da sauri kuma ta juya ta nufi sashin Queen Ayoola,
Tana zuwa Queen Ayoola ta bata umarnin shiga,
Zubewa tayi gabanta tare da faÉ—in.
"Ina miƙo gaisuwa, uwa ga Alaafin ja gaba ga mutanan Kanzaf, Allah ya ƙara maki lafiya mai ɗakin King Tunde Muhammad Jalal"
Jinjina kai Queen Ayoola tayi kafin a hankali ta gyara zama, tana mai sauke ƙafafuwan ta ƙasa, idar da sallar ta kenan.
"Meke tafe dake?"
Ajjiyar zuciya Iyalode taja tare da gyara zama tace.
"Abunne babu daÉ—in ji, ban san me mutane suke so ba"
Fashewa tayi da kuka tare share majina kafin tace.
"Wai ashe bawan Allan nan duk irin ciwon da yake wai Guba aka bashi a cikin abinci"
A gigice Queen Ayoola ta miƙe tsaye tana cewa.
"What Guba? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, wanne mara tsoran Ubangiji ne wannan"
Ta fadi hakan Idanunta na kawo ruwa tashin hankali ya ƙarara ya bayyana a saman fuskarta.
Iyalode tana ƙara sakin kuka tace.
"Daman ko waye wannan bazai wanye lafiya ba, Fisabilillahi mai ya aikata masu, amma dai wannan mazai ga Annabi ba, yanzu idan muka rasa Garkuwan mu yaya zamuyi, babu wanda zamu samu wanda zai zama tamkar King Tunde Muhammad Jalal sai Uban gina Jalaluldeen Tunde Muhammad Jalal Allah sarki bawan Allah"
Wani irin kallo Queen Ayoola ta yiwa Iyalode sai kuma ta É—auke kanta tana mai tunanin wanda ya sanya Wannan gubar,
Taɓe baki Iyalode tayi ganin hakan ya sanya Queen Ayoola tace.
"You can leave"
Da sauri ta juya tana zuwa waje ta sanya dariya tace "Munafuka nifa ban yarda da wannan matar ba, Shegiyar isa da izza kamar ƴar gidan ƙaruna"
Oumuu-Ayman ce riƙe da Hannun Salimerh har suka isa can cikin baban Parlon ta mai kyau da tsari, sosai Parlon ya ƙawatu da kayan zamani.
Zaunar da ita tayi kafin ta juya cike da nutsuwa ta nufi wajan wani fridge ta É—auki ruwa mai sanyi tare da wani glass cup mai kyau,
Zama tayi kusa da Salimerh kafin ta tsiyayi ruwan a cup ta bawa Salimerh,
Karɓa tayi a sanyaye ta fara sha tana sauke ajjiyar zuciya,
Sai da tasha ruwan sosai kafin ta sauke wata wahalalliyar ajjiyar Idanunta cike da hawaye taja ta lumshe,
Dole ta ƙara dakewa wajan ganin ta haɗa karatun ta na Criminology justice shi kaɗai zai bata damar tunawa da wanda take zargi asiri,
Gashi a yanzu idan tace zatai magana dole ta nemi hujja amma bata da wata hujja ko guda É—aya a tare da ita.
Kallon yadda take sauke ajjiyar zuciya Oumuu-Ayman tayi, hakan ya nuna cewa zafin da zuciyar take mata ya fara sauka,
Gyara zama tayi cikin lallashi da kuma kalamai masu daÉ—i tace.
"Look! Salimerh,you got to understand that some people don't come in your life to love you, They come into your life to see you, They don't come to bring to your life, They come to take from you.
  They don't see you as a person, They see as a opportunity, These are the type of people that don't love you for you, They love you for what they can take from you.
  They're not loyal to you, They're loyal to the benefits that Come with you, That's why they never show up.
   No matter how many times you showed up for them, That's why they never offer help, No matter how many times you helped them"
Ajjiyar zuciya ta sauke kafin ta É—auki ruwa itama tasha saboda zuciyarta gab take da karyewa, kafin ta kalli Salimerh wacce tayi shiru tana Kallonta tace.
"Kinga kenan, ba kowa ke sonka saboda Allah, maƙiyi yana da saurin ganewa, amma mu maƙiyanmu masu son rusa TUBALIn da aka gina na wannan masarautar, sun zo mana a siffar masoya kuma na jinin mu, kina gane su zai mana tuƙar wahala, dole komai sai anbi a hankali, kuma I'm sure Duk wanda ya aikata hakan zai ƙara ƙoƙarin aikatawa nan gaba, ina roƙan Allah kuma kada ya sake Bashi damar Cutar da kowa dake cikin Alaafin, Everything will be fine by the grace of God kawai keep praying"
Oumuu-Ayman ta faɗa tana mai ɗauke idanunta saboda hawayen da suka cika idanunta, Miƙewa Sakine tayi tace.
"Bari naje na duba jikin nasa, ƙilan a yau zan nemi prvt jet domin fita tashi wata ƙasar"
"Allah ya bada Sa'a ya tsare ya kiyaye"
Shine kawai abinda Oumuu-Ayman ta iya faÉ—a, domin tasan a koda yaushe za'a iya samu King Tunde Muhammad Jalal ya rasa ransa, wannan dalilin ya sanya ko wajansa bata iya zuwa.
Kai tsaye Salimerh Sashin King Tunde ta nufa, kanta a ƙasa Idanunta kuma cike da hawaye,
Dubawa tayi da Mamaki taga babu duk securities É—in wajan, dole kawai dalilin barin su wajan,
Tana cikin tafiya ne taji an jawo ta, tare toshe mata hanci da Cocaine, tana shaƙar powder kuma Idanunta suka lumshe Jikinta ya saki baki ɗaya,
Tana ji baya iya kallo akai sama da ita tare da suma tafiya da ita, a haka taji lokacin da aka shiga mota tare da shigar da ita ciki aka kwantar, gaba É—aya jijiyoyin Jikinta sun saki, wannan dalilin ya sanya ko yatsarta bata iya motsawa, a haka taji an yiwa motar key tare da yin waje da gudu....
*ABU MALEEK NA KUÆŠI NE IT'S 500 VIA 0116886423 SULAIMAN NA'IMA S UNION BANK EVEDANCE OF PAYMENT 08119237616*
*BY*
*SARAUTAR MARUBUTA*
*_End of book 1_*
*_31-32_*
ShaÉ—i day
Sassanyan numfashi ya fesar a hankali tare da mirgina idanunsa gefen daya kejin motsin, ganinta yayi tsaye tana ƙoƙarin gyara zanin dake shirin kunce mata.
Julde kam gaba É—aya ta mance cewa tun jiya daya shigo bukkar ta bai fita, hakan ya sanya kai tsaye take gudanar da al'amuran ta ba tare da tunanin yana ciki ba,
A hankali ta kama bakin zanin zata gyara cikin rashin sani zanin ya kwashe daga hannunta tare da yin sama.
Kwaɓe fuska tayi cike da gajiya da ɗaurin zanin cikin siririyar muryarta mai daɗin saurare wacce take ɗauke kuma da shagwaɓa tace.
"Ayyah, yayi min kaÉ—an ai"
Ta faɗa tana sunkuya wa tare da ɗauko zanin ta fara ƙoƙarin ƙara ɗaurawa.
Abu Maleek ƙuri yayi mata da gajiyayyun idanunsa masu kaifi, ganin tana ɗaure zanin babu zato babu tsammani kuma ya ga zanin ya ƙwace daga hannunta yayi ƙasa.
Zuciyarsa ce ta harba da ƙarfin gaske, lokacin da surar Jikinta ta bayyana, yayinda manyan ma dai-dai-tan hips ɗinta suka sauka a cikin Idanunsa,
Da sauri ya runtse idanunsa cikin rashin sani kuma ya ware laɓɓansa tare da furta.
"Wayyo Oumuu!!"
Ya faɗa yana jan numfashi da sauri ya miƙe tare da ficewa daga cikin Bukkar hannunsa dafe da kansa.
Julde a ɗan hargitse ta ƙarasa ɗaure zanin domin yayi mata kaɗan, kasantuwar tsarin halittar Jikinta masu girma ne,
Tana da hips so ma sha Allah! Masu faÉ—i da kuma É—an tuni,
Ga kuma Brest É—inta a tsastsaye, farare tass dasu, nippy É—in nan so pink,
Kwaɓe fuska tayi tana jinta duk a dame saboda sosai abinda Abu Maleek ya faɗa na "wayyoooo Oumuu" ya ratsa cikin dodon kunanta,
Ƙara marai-raice fuska tayi tana turo baki gaba tace.
"Aljani kawai"
Ta faÉ—a tana murguÉ—a bakinta tamkar yana gabanta.
Juya tayi tare da sanya hannunta ta riƙe ququnta tana hararar gefe guda tace.
"Shine zaka wani zo ka tsaya akai na ko? Ka kalle ni ko? Daman na san kai ne jiya hadda wani shigewa jikina ko?"
Ta ƙare y idanunta na kawo ruwa, cikin ƙasa da Murya dai-dai yadda na kusa da ita zaiji tace.
"Uhm, amma bakinka ƙamshi, nasan kuma farare ne ko? Dan Allah ko zaka sammin abinda kake sawa bakinka?"
Ta ƙare maganar tana ɗan haɗe hannayenta waje guda alamar roƙo,
Bata san cewa duk wanda ta kewa surutun ya riga daga fice a ɗakin bai san me take cewa ba, balle yaji roƙon nata.
Yana fita ya tsaya cak sabida taron mutanan da suke wajan, gaba É—aya shi ya ma manta da batun cewa yau zai raba dukan da akai masa,
Tsaki yaja danshi baiga amfanin wannan game É—in ba, domin har yanzu bai san dalilin yin game É—in ba,
Kawai dai salon mugunta da salon cin zalin mutum, ya ƙare zan can a ransa yana cije bakinsa.
Arɗo dake tsaye yana jiran fitowar Abu Maleek yayi saurin ƙarasawa inda yake tsaye fuskarsa ɗauke da Murmushi yace.
"Gashi zaka tafi har yanzu bamu san sunanka ba?"
Ya tamabaya yana mamakin yadda Abu Maleek yake marai-raice fuska tamkar zai sanya kuka, domin har yanzu bulalar da akai masa tana mugun damunsa, sosai dukan ya ratsa jikinsa.
Yi yayi tamkar bai ji maganar da ArÉ—o yayi ba, sai ma É—auke kansa da yayi can gefe guda,
Murmushi kawai ArÉ—o yayi kafin yace.
"Lokaci yayi muje ka fara ga bulalar can"
Juyawa yayi gaba É—aya tare da fuskarta ArÉ—o domin Mutumin ya fara damun rayuwarsa, ya fara shige masa, bai san takura ko kaÉ—an gashi yaga mutumin É—an hayaniya na bala'i.
Fesar da numfashi yayi a hankali kuma ya sanya hannunsa tare da É—urawa a saman goshinsa, ya shiga murza tsakiyar forehead É—insa, yana jin yadda kansa yake sarawa,
Cikin É—an É—aga Murya kaÉ—an yadda sautin Muryar ba zai damesa ba yace.
"Uhm! What i have done to you? Nazo garinku kun bani kulawa ok fine thank you, but please stay away for me, I'm tried! Haaaa, duka kuma kana sane ka bari aka daken ai dan mugunta, Ni kuma banyi na yafe kuje can kuci kanku"
Ya ƙare zan can yana dafe ƙirjinsa tare da sauke wata zazzafar iska daga bakinsa, ya shiga sauke ajjiyar zuciya a jajjere,
Kallonsa kawai ArÉ—o yayi ya fahimci cewa haushin dukan ne har yanzu bai sake sa ba, shiyasa yake son huce haushinsa akan sa,
Ba tare da damuwa ba ArÉ—o ya kalli Abu Maleek yace.
"Tunda har ka bari aka dake ka, ya zama dole ka rama, rashin ramar kowa yana nufin kai lusari ne, wanda bai cika jarumin Namiji ba, rashin ramar na nufin Tabbas baka amsa sunanka na Namiji sai dai mata maza, kuma zaka bar garin nan ana maka ihu ne, tare da jifan ka, idan ka aminci shikenan sai a raka ka sa jifa da duwatsu"
Ya ƙare maganar yana sakin dariya, domin yayi hakan ne domin ya tun zura Abu Maleek, babu shakka kowa haƙƙarsa ta cimma ruwa,
Abu Maleek daya ke jin maganar ArÉ—o kamar Almara, shi za'a ma ihu? "Uhm" kawai yace yana yin gaba domin zuwa cikin inda ake jiransa, tuni kuma jikinsa ya fara rawa.
Yana shiga ya gyara tsaiwarsa, tare da lumshe idanunsa,
Barkido dake tsaye ya ƙara gyara tsaiwarsa yana mimmiƙa hannunsa, alamar dai shima a shirye yake da karɓar dukan na Abu Maleek,
Kallon gefe Abu Maleek yayiwa Barkido yana faÉ—in
"zakaci gidanku, fuska kamar Salad"
Lamiɗo ne ya miƙa wa Abu Maleek wata zabgegiyyar bulala sai ƙyalli take,
Hannun damansa yasa ya amsa a cikin ransa yake faÉ—in
"Bisimillah Rahmanir Rahim"
Ya faɗa yana gyara zaman bulalar a hannunsa, kallon Bulalar yayi sosai, kafin ya ɗaga kansa ya kalli Barkido, nan take kuma yaji wani haushi da baƙin cikin dukan da Barkidon yayi masa,
Hakan ya sanya ya ƙara riƙe bulalar sosai, a hankali kuma ya ware bakinsa cikin sarrafa harshe yace.
"Ya Rahmanu ya Rahim!"
Ya faÉ—a yana mai shafe bulalar da tafin hannunsa, a hankali kuma ya É—aga bulalar kafin cikin wani zafin nama ya saukewa Barkido bulalar a tsakiyar bayansa.
A gigice Barkido ya ware mitsi mitsi idanunsa tare da kame jikinsa waje guda, domin tashin farko Barkido idanunsa ya raina fata,
Bai dawo hayyacinsa ba yaci Abu Maleek ya sake sakar masa wata Bulalar, wacce ya sanya ya furta "Auchhhiii!"
Da ɗan ƙarfi saboda tsananin zafin shigar bulalar da yaji ya ratsa masa dukkan wata gaɓa ta jikinsa,
Abinka da cikakken namiji, kuma ƙaƙƙarfa, wanda ya saba motsa jikinsa ta hanyar yin gym kala-kala, Uwa uba kuma FOOTBALLER, shiya sanya ya zage dukkan ƙarfinsa yana laftar Barkido da dukkan ƙarfinsa, a ransa yana ambaton sunan Allah,
Barkido tuni idanunsa ya fara kawo ruwa, zufa ta wanke masa jikinsa sai tsuma yake,
Idanun Abu Maleek ne ya sauka akan wata bulala dake hannun LamiÉ—o da sauri yasa hannu ya amsa, ya haÉ—a hannu da dama, ya shiga Laftar Barkido wanda tuni ya fara kurma Ihu yana yin baya,
Sosai Abu Maleek ya gigita sa, ya ruÉ—a masa jiki da duka ganin babu sarki sai Allah yasa Barkido faÉ—in.
"Wallahi na bar baka ita, na yafe bana sonta ka rabu dani haka"
Ina sam A.m baya gane karatun bare yayi masa hadda, duk inda Barkido yayi sai ya bisa ya daka, ganin idan bai yi da gaske ba, sai iya rasa ransa ya sanya ya ɗaga ƙafafuwansa, tare da arta ana ƙare ya nausa cikin jeji kamar yadda Labbo yayi.
Æoyayyiyar ajjiyar zuciya A.m ya sauke yana jin zuciyarsa wasai, bashi da wata damuwa wacce ta shafi wannan dukan domin sai da yayiwa Barkido duka wajan hamsin,
Fesar da numfashi yay yana É—an cusa hannunsa tare da hargitsa gashin kansa wanda ya kejin yayi masa nauyi sosai, saboda rashin saloon da bai ba.
Mutane da yawa sai da suka yi mamakin yadda Abu Maleek ya iya dukan Barkido, ArÉ—o wani lafiyayyan murmushi ya sauke kafin a hankali yace.
"Lamiɗo kirawo min Jon wuro, domin ya zama wakilin Wannan baƙon, kai kuma ka zama wakilin Julde"
Jinjina kai Lamiɗo yayi kafin ya miƙe ya nufi bukkar Jon wuro,
Babu jimawa suka dawo a tare fuskar Jon wuro ta faÉ—aÉ—a da Murmushi.
Jalaluldeen can ya nema ƙasan wata bishiyoyi wacce ƙasanta yake ɗauke da yashi mai sanyi ga ruwa na ɗan tsastsafo wa ta ƙasan wajan,
Yana zama Sweet tazu ya shige jikinsa, kwaɓe fuska yay yana ɗura haɓarsa a jikin sweet,
Kafin cikin ƙasa da murya yace.
"I'm tried sweet, ina son gida, i need to hug my Grandma, Oumuu, And my world my everything Dadyna, nayi kewar su sweet"
Ya ƙare maganar yana shafa gashin sweet ɗin wanda ya ɗan hargitse, saboda yawon da suka sha.
Gyara zama Jon wuro yayi tare da kallon ArÉ—o yace.
"A matsayi na, na Uba a wajan Wannan baƙo, ina nemawa ɗana Auran ƴar ka Hawwa'u (Julde), ina fatan zaku bani wannan aure cikin girma da mutun ci haɗi da karramawa?"
Jinjina kai ArÉ—o yayi yana mai sakin murmushi yace.
"Ni kuma a matsayi na, na uba a wajan Hawwa'u, ina mai farin ciki sanar dakai cewa na bawa É—an ka auranta halak kuma malak"
"Allahamdulillah"
LamiÉ—o ya fara kafin Jon wuro ya É—auki kuÉ—i ya bawa ArÉ—o yasa hannu ya amsa, nan suka shaida auran Hawwa'u Julde, da kuma Jalaluldeen Tunde Muhammad Jalal, akan shaidu wajan mutum goma.
Tsakanin Julde da Abu Maleek babu wanda ya san abinda yake faruwa, sai da su ArÉ—o suka gama komai, sannan ArÉ—o da Jon wuro suka nufi inda Abu Maleek yake zaune shida sweet yana mata surutu ita kuma sai jela take É—agawa.
Suna zuwa suka nemi waje suka zauna, Jon wuro da yafi shekaru akan ArÉ—o ya fuskanci Abu Maleek sosai, tare da faÉ—in.
"Yaro na, Allahamdulillah! Kayi na sara akan abokin adawarka, ka shiga neman aure ba tare daka san komai ba, amma cikin ikon Allah gashi ka samu damar samun Yarinyar da ka shiga ShaÉ—i a kanta"
With much surprise Abu Maleek yake binsu da kallo, Shaɗi? Yaushe ya shiga shaɗi? Wacce yarinyar suke magana? Wannan sune tarin tambayoyi da suke danƙare a cikin zuciyarsa,
Jon wuro ne ya ƙare zama sosai ya fuskanci Abu Maleek cikin nutsuwa da kuma halin daddako yace.
"Tabbas wasan da Arɗo ya faɗa maka ba wasa bane haka kawai, shaɗi ne wanda ake yinsa yayin neman aure, Barkido da Labbo sune suka shiga shiga cikin shaɗin, kafin kai kuma ka shiga daga baya, shigarka kuma ya sanya Labbo fita, gashi kuma kayi nasara duk da cewa baka san, dalilin yin hakan ba, to Allahamdulillah a yanzu haka Hawwa'u ta zama matarka bisa jagoranci mu gaba ɗaya, na zama wakilinka wanda na amsar maka auran a wajan Arɗo na bada Sadaki kuma da hannu na, Julde ta zama Matarka halak malak, kuma a yanzu zaka tafi da ita zuwa ƙasar ku"
Wata zabura Abu Maleek yayi, jikinsa na rawa ya shiga nuna Jon wuro da hannu cikin tsantsar ɓacin rai da kuma tarin talaucin abinda sukai masa yace.
"What? Aure? Haaaa! Dawa ɗin ni dai? Goodness saboda kun rasa yadda za kuyi da ƙaramar yarinyar ku shine zaku liƙa min ita? Uhm wallahi za kuyi dana sani bana sonta ko ɗaya kamar yadda kuka liƙa min ita haka Nima zan mayar da ita baiwa, daman ai ba ƙaunar ta kuke ba, Wheel Nima haka kunga anyi 50% kenan"
Ya faÉ—a yana sakin wani zazzafan huci daga cikin bakinsa idanunsa ya kaÉ—a yayi jaa, kana kallonsa zaka fahimci how sad he is,
Gaba ɗaya ya birkice gargasa jikinsa duk ta mimmiƙe, Jon wuro kallonsa yayi domin yasan za'a rina,
Kuma tun yanzu ya fara tausaya Rayuwar Julde zata shiga hannun wanda baya sonta, amma zamanta a wajan zaifi daÉ—i fiye da zamanta a wannan rugar,
ArÉ—o kam ko a jikinsa domin shi ko Abu Maleek zai tafi da ita ya yankata ya zubar da gawarta ko a jikinsa,
"Zuwa yanzu da Julde amana take a wajan ka, kasan duk wanda yaci amana Shida Ubangijinsa, bazan maka dole ka sota ba saboda so halitta ne, amma ina fatan wata rana ka zame mata garkuwa, bangon da zata jingina taji daɗi, duk abinda ya samu da rayuwarta a yanzu kuma KAI NE SANADI, kayi haƙuri ka zame mata Tubalin da zai gida rayuwarta, ko ba zaka so ta ba, ka kula da rayuwarta"
Yakai ƙarshen maganar cikin sigar rarrashi da kuma ban baki,
Abu Maleek huci kawai yake saukewa jikinsa duk rawa yake.
Da kallo kawai suke binsa ganin yadda naman jikinsa yake rawa, ga yadda jijiyar kansa ta fito sosai, hannunsa ya sanya ya É—auki Sweet tare da kallonsu yace.
"Bazan ce a'a ba, amma duk abinda ya faru kune kuka ja mata, bani da lokaci Ni tafiya zanyi"
Ya ƙare maganar cikin ɗacin rai, Arɗo ya miƙe babu jimawa ya dawo tare da Julde, da kuma wani kuttu guda biya ɗaya ya cika masu Kindirmo, ɗaya kuma ruwa ne mai kyau,
Bawa Abu Maleek yayi ganin da gaske Tabbas zai iya neman abu a hanya ya sanya ya amsa, ba tare da yace komai ba ya nufi cikin jejin da zai fitar dashi daga cikin garin baki É—aya,
Yana tafe tana biye dashi a hanya jama'ar garin na É—aga masu hannu,
A haka suka fara nausawa cikin jejin ita dai Julde katari sahunsa kawai take bi,
Tsayawa yayi tare da juyawa ya ganta can nesa ga yamma nayi shi kuma a yau yake son barin wannan gantalallan garin wanda bai masa amfanin komai ba,
Gajeren tsaki yaja da wani irin sauri kuma ya nufi inda take yana zuwa yasa hannunsa yay cilli da sandar haÉ—e Jikinta tayi waje guda hawaye ya shiga sakko bata,
Kafin tayi wani motsi taji ya sanya hannunsa ya É—auke ta cak tare da sanyata a tsakiyar bayansa kana ya goyata a faffaÉ—an bayan nasa....
Sai mun haÉ—u a book 2
Gobe akwai tattaunawa akan book 1 kowa yayi joining na comment section.
*Abu Maleek na kuÉ—i ne, biya 500 domin yin karatu cikin nutsuwa 08119237616*
*BY*
*SARAUTA*
*HADEEYATULLAH*
BONUS kuma kuji ɗan abinda ƴan PAID suka gani😆
*LITTAFIN KUÆŠI NE KI BIYA KI KARANTA HANKALI KWANCE,DUK WACCE TA KARANTA MIN BOOK KYAUTA DA WACCE TA TURO DA WADDA TA GAN SHI A WANI GROUP ITA MA TAYI SHARING IN KUN YI DAIDAI KUN SANI🤷ðŸ»â€â™€ï¸ mai son biyan kuÉ—in karatu sai ta tuntuÉ“e ni ta WhatsApp* +22795045822