Best / Popular Hausa Novels

Aljanar Ruwa Ce Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Aljanar_Ruwa_Ce_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 5 of 6

Cigaba da tuki yusuf yayi, Har suka isa gida,

Tuki yake yi batareda yasan inda yake nufa bah, magannanun ta ne suka Fara mai yawo acikin kwakwalwar sa, bakasan irin muguwar tsanan da Nayi maka bah, tsanan da koh ma'auni bazai iya aunawa bah. Kuma kayi na farko kayi na karshe, kada koda gigi yasa ka Kara aikata min aka Dan wallahi abunda zan maka bazaka jita da dadi bah.

dafa kansa yayi, yayinda idanuwansa sun kada,sunyi jajir kamar garwashi. Burki yaja ya tsaya abakin hanyar titi, dafa stairing motan yayi, ya Kalli mirror cikin motan, yaga shatin hannunta a fuskarsa, shafa fuskarsa yayi, yayinda yake jin zuciyar shi nayi masa tiriri, da kuna, yace, ni Kabeer, Mace ta mara, Kuma banyi komai akai bah, how is that possible.

Duda cewar bah mutum bace, ALAJANR RUWA CE, amma akan bazai sa na kasa daukan mataki bah, dole ne hukunta ta, Daidai da laifin ta, Kuma zata min bayani wanene wancan, malohon wanda take kira masoyi. Horn yaji Hana masa, akan yasa ya tada mota yabar wajan, direct gida ya nufa, inda body guard suka bude masa gate, koh gama parking baiyi bah, yashiga cikin gidan.

Ganin ranshi a bace yasa "Mom tace, son what happened? Wani ya bata maka rai ne? Ko kuma zainab" bata yi maka bah, Kabeer yace yes, wallahi bazan boye miki bah, i don't like that girl, idan na aureta wahala kawai zata sha, domin kwata kwata, yarinyar bata kai level din da zangan ta na yaba Ba,

Please Mom ki taimaka min, Murmushi Mom tayi tace son kenen, yanzu Zainab Meyasa meta Da zaka ce bata yi maka bah, and wallahi kun dace da juna,

Kabeer yace, ba dacewa bah koma menene, nidai yarinyar nan bazan aureta bah, that's the fact.

Kabeerrr ! .... Mom ta fada a tsawa ce, Tareda nuna shi, tace idan har kaci ka Dan halak, toh kada ka aureta, Kaga abunda zan maka, tsawar Mom ne yafuto dasu Dad dakuma Aunty amarya, sai su Nadira .

Dad yace Karima meyafaru? Meyasa kikayi Ihuun sunan kabeer, Mom tace Dad kabeer can you imagine this what you called son, Dad yace i don't get you, kabir bah danki bane bah, ai bai kamata ace ki dunga tsawatar mai bah, kamata ai ace ki gargade shi, ko kuma kibashi Shawara, abunda ya kamata kenen, please Karima banason abunda zai tayar wa kowa hankali.

Tukun nan mah, menene ya faru? Dad ya tambayi Mom, girgiza kai Mom tayi tace, no need, bah bukata, kowa zai iya tafiya, rasa abun cewa kabeer yayi, nufan inda Mom take yayi yace, Mom Allah ya baki hakuri, kiyi hakuri ki yafemin, na miki alkawarin cewar bazan kara bijire wa umarnin ki bah, zanyi Duk abunda kikeso,

Bazan kara bata miki rai bah, am sorry Mom, dakatar dashi Mom tayi da fadin, i don't need your sorry, bana bukata rike abun ka, Kuma banason ka auri Zainab din, shikenen hankalin ka ya kwanta bah, toh na fada, na cancelled din auren ka da zainab.

Dama nasan Wannan
Na'ananniyar Yarinyar Chan ce tayi maka asiri, tunda nake baka taba bijire wa maganata bah, amma Zuwan Amriya gidan komai ya chabe, babu daman Nayi maka magana kaji, saboda ta asircemin Kai.

Karimaaaa! Dad ya fada a tsawa ce, Cikeda baccin rai Dad yace Karima mind your words, ina ruwan Amriya a wannan zance, Dan ita ta kasance bah mutum bah, shine kike zargin ta da mugun nufi, ni mama fara zargin ki wallahi, maybe mah abunda Amriya ta fada a kanki gaskiya ne bah karya bah,

Fashe wa Mom tayi da kuka tace, shikenen hankalin ta ya kwanta, Gashinan tana kokarin raba ni da ahalina, wannan wace iriyar masifa ce, nida gidana amma ake kokarin rabani da y'ay'ana.

Kallon su Nadira da khaleed Aunty amarya tayi, tayi musu nuni da hanyar waje, jiki a sanyaye, suka Mike Tareda fucewa daga part din.

Aunty amarya tace, Noo Mom bai kamata ace mahaifiya kamar ki na irin wannan furucin bah, kema fah kin haifa, Kuma bazaki so aci mutuncin Y'ay'an ki bah, ki kwantar da hankalin ki, komai zaiyi daidai, bai kamata kina tayar da hankali akan abunda bai Kai ya kawo bah,

Mom tace, kenen bansan abunda nake yi bah koh, koh ance miki kema bansan, kulla kullan da kike yi bah, toh wallahi zainab, ki kiyaye ni, ni bah sa'ar wasar ki bace bah, ki rike girman ki, na rike nawa, karki sa na daina ganin mutuncin ki,

Grandma tace wai, meyake damunki ne Karima, shin wani abu yau kika sha kome, yanzu tsabar rashin kunya, a gaban nawa kike fadan irin wannan magannanun, koh kunya baki ji bah, toh maza maza koh wa ya watse kafun na bata muku rai.

Kwan kwasa kofan gidan, doct khadija tayi, tashi daya daga cikin body guard din yayi, yanufi wajan gate din Tareda bude kofan, ganin doct khadija ne, ya sashi yin sauri ya bude kofan.

Shiga ciki doct khadija tayi, Ta Kalli koh ina na harabar gidan, sa'anan ta girgiza kanta tace, shekara da shekaru kenen, rabon da na dora kafana akan wannan gidan, wacce tayi sanadiyan barina gida nan, itace takuma yin sanadiyan dawowa ta, yau bah gobe bah, kowa zai San abunda kika shuka Karima.

Chan cikin gidan ta nufa Tareda Kwankwasa kofan parlour, Aunty amarya tace Grandma kamar naji Hana Kwankwasa kofa, barana je na bude kofan.

Bude kofan Aunty Amarya tayi, taga bakuwar fuska, gaisheta Aunty amarya tayi, doct khadija ta amsa , sannan doct khadija tace, Karima na nan kuwa?, Aunty amarya tace Eh Tana nan, shigo

Shigowa ciki doct khadija tayi, kamar ance Mom ta juya , Juyowa Mom tayi ,lokaci daya suka hada ido da doct khadija.

Gaban Mom ne yayi mumunan faduwa! , yayinda zuciyar ta ya fara Duka uku uku, Murmushi doct khadija tayi tace, kina mamaki ne, Kinga ban mutu bah koh, bakici galaba akaina bah,

Cikin fusata, Dad yace meya dawo dake gidan nan, bayan bakin ciki da kuncin da kika sanya mu aciki, wato Kara dawowa kikayi domin ki kara, saka mu a wani kuncin kamar yadda kikayi shekarun baya da ya wuce.

Maza zo ki futa, Bamua bukatar, ma Yaudariya, maciya amana, Grandma tace Muhammad barta tukunan, ni zanyi maganin ta

Ke khadija, kalle ni nan, Kallon ta doct khadija tayi, Grandma tace kalle ni da kyau, baka nake bah fara nake bah, wato Kara dawowa kike, domin kikara haddasa wani fituna koh, toh ta Allah ba taki bah, baki isa kin kara yiwa wannan ahalin komai bah, Dan aka maza ki fuce, kafun na dauko tabarya,

hawaye nee suka Fara saukowa daga kuncin doct khadija tace, bazan ga lafin ku bah, laifin wacce ta hada mu daku, zan gani, nazo gidanan ne badan komai, bah sai Dan na tona asirin abunda Baku sani bah, na tsawon shekara da shekaru, inason ku bani Dama, Dan Allah zan fada muku gaskiyar abunda ya faru,

Kallon Dad doct khadija tayi tace, tabbas abunda Amriya ta fada muku gaskiya ne, babu karya, first wife dinka , wato Fatima Tana raye bata mutu bah, Kuma tana kulle ne acikin wannan gidan na tsawon shekaru, batareda ansani bah, Amriya ce kawai ta iya gano, inda Matarka take.

Kallon ta Dad yayi, yace Dama wanda ya ruga ya rasu yana dawowa ne, wato zuwa kikayi domin ki cusa mun bakin ciki a zuciyata koh, leave now, banason jin komai dazai futo daga bakin ki.

Doct khadija tace, zant tafi, amma bazan bar gidanan Ba Tareda na tona asirin wannan shedaniyar bah.

COMMENT & SHARE PLS
ALAKALAMIN
AISHA M.B(BABY ISHA)

BISSMILLAHI RAHAMANI RAHEEM.
ALJANAR RUWA CE PAGE 46 ?47
WRITTEN & DIRECTED BY AISHA M.B (BABY ISHA)

-----------------------------------------
Murmushin k'eta Mom tasaki sa'anan tace,
Yanzu khadija wane laifi na aikata da kike son wargaza gidana, mene na aikata miki? Wane abu na tsare miki a rayuwar ki .

Meyasa kike son ganin baya na ta karfi da yaji, Grandma tace, Karima ki rabudani ita, so take ta lalata miki aure, toh ta Allah na Tata bah, maza zoki futa kafun na sakar miki karnukan gidanan, suyi hawan gaba da ke.

Wani kukan bakin ciki ne ya ziyarci Doctor Khadija, doct khadija tace, ku yarda dani wannan matar shedaniya.

Mom tace DAD Kabeer Dan Allah ka roke ta, ta bar mana gida, saboda wannan matar munafuka ce.

kece dai babbar munafuka!" sukaji kalisat tafada! ,ta cigaba da fadin kwarai kuwa, kece munafukar,

Tsinka mata mari doct khadija tayi tace, Duk abunda zai faru, karki kuskure kikara ce mata munafuka, saboda a haifa ta haifi sama dake. Kuma itadin a matsayin mahaifiyar ki take.

Allah ya kiyaye, Allah ya mun katangar karfe da wannan shedaniyar algunguma, mara imani. Wannan matar bata cancan ci akirata da Kalman uwa bah, domin kuwa yin akan kuskure ne.

Dad yace, ke Kalisat," kinsan abunda kike fada kuwa, kina da hankali, bakisan cewar, Tana a matsayin mahaifiyar ki bane, ya karashe maganar ranshi a matukar bace

kalisat tace, Dad am sorry to say", gaskiya, ita ba'a matsayin mahaiyata take bah, saboda mahaifiyata ta fita daraja da kima, kuma ita wannan azzaluma ce, mara zuciyar tausayi.

Magannanun tane suka sauka akan dodon kunuwan Khalid dakuma su Kabir dake sauk'owa daga upstairs, bata hankara bah taji sauk'an mari akan kuncinta, Dafe kuncinta kalisat tayi,

Idan ran Khalid ya Kai dubu toh ya baci, yace kalisat, kina cikin hayyacin ki kuwa, wacce ta raine mu, ta kula damu tamkar yaran ta, ta nuna mana soyayya kamar yadda itama Mami iya karkarin abunda zata iya kenen, shine yau kike kallon tsabagen Idanuwanta kina fada mata magana son ranki, kamar itadin sa'ar kice.

Kalisat tace wallahi matar nan, bata son mu Illah son cutar da mu da take kokarin yi, Amriya ce kawai take dakatar da ita, amma na tunan ta gama da yahya kabeer ya kashe kowa na wannan family.

Fashewa Mom tayi da kuka!, tace, Yau a gaban idona ake min karya cewar ina kokarin cutar da ahalin nan, meyasa zanyi muku aka, kalisat. Duda irin alkhairy da nayi muku amma da irin wannan abun zaku saka min dashi Dama ance Dan adam butulu ne, Hatake ta Fara tarin karya, tana zubda hawaye

Hakuri su Kabir da Dad suka Shiga bata, cikin fusata Kabir ya nufi inda kalisat ke tsaye, Ba tareda bata lokaci bah ya fuzgo ta, sa'anan ya shake mata wuya yace, ke mahaifiyata sa'ar ki ce, wallahi Kuma idan wani abu yasami mahaifiyata saikin dandana kudarki,

Murmushi kalisat tayi tace, mahaiyar ka, ko mahaifiya yar basaja, ta dolantar daku, tasaka ku cikin duhu, babu abunda idanuwan ku ke gani sai duhu, Amriya tayi kokarin fidda ku cikin aske, amma kuka ki ku fahimce tah.

Da wacce kake Kira mahaiyar na sonka baza tayi kokarin cutar da rayuwar ka bah, idan akane meyasa ta kashe Ummi.

Da sauri Kabir ya sake ta, ya dago da idanuwansa wanda suka kad'a sukayi ja.
yace, what nonsense are you talking about.

Kalisat tace am not saying nonsense, amma ni nasan tabbas Mom itace ta kashe Ummi, kuma sa'anan ta batar da Salma.

Gabadaya suka hada Baki wajan fadin what! Dad yace toh menene hujjar ki na fadin akan, gayamin Wacece hujja.

Nice hujja . Sukaji an fada, juyawar su keda wuya suka ga, Salma duk ta bi ta rame, tayi baki. Da sauri su nadira sukaje suka rungume ta, fashewa Salma tayi da matsanan cin kuka mai taba zuciya.

Nadira tace, Salma Wacece tayi miki aka, ina kikaje cikin wadanan kwana kin, ba Tareda kin dawo bah,

Salma tace babu inda naje, asali mah Mom ita ta bayar dani, ba Tareda kowa ya sani bah, kuma tabbas itace makashiya, wacce ta raba Ummi da rayuwar ta, saboda son kanta da son abun duniya.

Dafa kanshi Kabir yayi Wanda yake mugun saramai, Kallon Mom wacce tayi zuru zuru, Kabir yayi yace, Mom" shin abunda Salma ta fada gaskiya ne koh kuwa karya take miki? Shiru Mom tayi, ta rasa wane karya zata Kuma yi a wannan karan.

Grandma tace, ba shiru aka ce kiyi bah Karima, tambaya ce mai sauk'i, shin kece kika kashe Ummi, kuma kika batar da Salamatu,

Mom" tace wallahi karya take yi, saboda me zan kashe Ummi, me ta, tare mun, menene riba ta idan na kasheta, wallahi wannan abun kawai hadamin akayi domin kawai aga an rabani da gidan aurena.

Kabir" yace toh Salma kindai ji abunda Mom ta fada, tace ita batasan wani batun kisa bah,

Salma tace Aba Mom, ramin fah karya kurarre ne, say the truth and shame the devil, kiji tsoron Allah Mom, duda cewar ta sanadiyan ki nazo duniya amma akan bazai sa na rufa miki asiri bah,

Kiyi hakuri Mom, ke mahaifiya ta ce, amma dole yau sai gaskiya tayi halinta, tabbas babu karya ke kika kashe Ummi, a gaban idona, ta dunga baki hak.. Bata karasa bah kuka ya kufce mata, sosai take kuka idanuwanta suka koma ciki sukayi jajirr.

Cikin sheshekar kuka, Salma tace, babu abunda Salma bata ce bah, don kawai ki rabu da ita, babu koh d'igon tausayi kika samu, kwalba kika fasa mata Kai, akan baisa ta daina rokon ki bah, na dafa kafanki, nace kidau raina a madadin nata, amma kika ki, saboda son zuciyar ki, aka kika samu wuka kika kashe wacce bataji bah, bata gani bah. Ta karashe maganar tareda fashewa da wani kukan.

Jikin kowa na parlour ne ya dau zafi, wani iriyar kasala ya ziyarci kowannen su.
Kalisat tace, koh yanzun mah Baku yarda bah, toh inada wani prove din, zira hannu tayi cikin aljihun rigarta ta dauko waya,

Sannan tayi connecting da TV, tasa play, Mom ce bayyane akan screen din TV , inda Ummi ke bata hakuri, amma samm tsabar rashin imani, ta kashe ta.

Cikin kowa ne ya duri ruwa, a Hatake Mom ta hade rai. Cikin dak'a tsawa Dad yace Karima! Shin wannan kece da gaske.

Mom ta Bashi amsa da fadin kwarai kuwa nice, tabbas nice nan bah kowa bah, kuma ba iya ita kadai bah, sai na hallakar da kowa na wannan family kamar yadda na tsara,

Kabir kamm ji yake kamar mafarki yake, Dad yace Karima why? Dama Allah ya Barnum raina ne domin na ga wannan bakar ranar, Dama cin amanar ahalin nan kike da koh Y'ay'an ciki kin ki, baki Bari bah, why Karima? Why?

Mom ta Bashi amsa da fadin, FANSA, tabbas na shigo wannan ahalin ne badan komai sai dan na dauki fansar abunda aka aikata min na wajan shekara da shekaru,

Kuma tabbas saina dauki fansa akan wannan ahalin, Tana kaiwa nan ta kwashe da dariya, Tana mai fadin, wallahi Baku ga komai bah,

Kai kuma Kabir, tabbas bani ce mahaifiyar ka bah kamar yadda Amriya ta fada tun farko, ni kawai na rike Kane a matsayin d'ana domin idan lokacin salwantar da rayuwar ka yayi wa qungiya ta, saina kashe ka.

hawaye ne suka Fara bin kuncin Kabir yace, Mom please na roke ki kice min karya kike, wasa kawai kike yi. Hade rai Mom tayi tace, kwarai kuwa bah karya na ke fada bah, gaskiya na fada nidin, bah mahaifiyar ka bace,

Jiri ne ya fara diban shi, faduwa Kabir yayi sumamme. Hankali tashe su Dad sukayi kansa, da sauri, Tareda fara jijigashi, babu abunda kakeji a gidan sai kukan su nadira.

Ruwa Khalid ya dauko, sannan ya watsa masa, amma still bai koh Motsa bah, hankalinsu bah karamin Kara tashi yayi bah,

Cikin baccin rai Dad ya shake wuyan Mom yace, Dama da tantiriya, nake rayuwar aure ban sani bah, ban taba zaton aka daga gareki bah, tabbas dole ki girbi abunda kika shuka.

Ture Dad Mom tayi, ya fadi, da sauri su Sadiq suka nufi inda yake, d'aga shi sukayi.
Tareda zaunar dashi. Babu bata lokaci high blood pressure din Dad wato BP, ya tashi,

Hankalin kowa na gidan bah karamin tashi ya karayi bah, fashewa da dariya Mom tayi, tace ina farin cikin ganin wannan ahalin cikin kunci da damuwa, kamar yadda kuka sakani kunci, nima saina ga bayan ku,

Cincibar Dad da Kuma Kabir sukayi, suka nufi hanyar waje dashi, cikin mota suka nufa da su, Khalid ya tada motan, sannan yayi wa su body guard magana dasu bude kofan.

Ganin koh yunkurin bude kofan basuyi ba, yasa ran Sadiq baci, futowa Sadiq yayi daga cikin motan, yace bakuda hankali ne, Baku ga rayukansu na cikin had'ari bane, maza ku bude kofan kafun, ranku ya baci.

Daya daga cikin body guard din yace, ba'a bamu umarnin mu bude muku kofa ba. Aka zalika, wannan gidan mallakin uwar shedanu ne, babu wani ma'aluki da ya isa yayi kokarin futa daga gidan nan, domin wannan gidan makabartar ku ce.

Mutuwar tsaye Sadiq da Khalid sukayi! Ya rasa abun cewa, jiyayi gabadaya duniyar ta isheshi.

Dariya gabadayansu suka kwashe dashi, daya daga cikin su yace kuna mamaki ne, toh mudin bah body guard dinku bane, kamar yadda kuka tsammani, mudin yan qungiyan asiri ne, uwar shedanu kawai muke wa aiki, Baku bah, mun zo gidan nan ne badan komai bah, sai don mu taimaka mata, ta cika burinta, akan ku.

Hada hannayen sa, Sadiq yayi waje guda, yace, Dan Allah badan mu bah, ku taimaka, ku barmu, mu futa, kuna dai ganin rayukansu yana cikin hatsari, kubari mu kaisu, asibity, Dan Allah, ya karashe maganar hawaye na shirin zubo masa.

Dariya suka kuma kwashe dashi a karo na biyu, suka hada baki wajan fadin, kuda futa, saidai gawar ku, baku bah, ran Sadiq da Khalid ne ya baci, lokaci daya, sukayi kan body guard din, domin, su koya musu hankali. Kokawa suka farayi da juna.

Cikin rashin sa'a kuwa ,yan qungiyar asirin suka hadu, suka dunga dukan su Khalid, babu gaggauta wa.

Gasu Dad da kabir rai a hannun Allah, saida suka farfasa wa su Khalid jiki, sa'anan suka wurgar dasu. Basu jisu a ko ina bah, sai jikin bishiyar gidan, yayinda kan sadiq ya fashe, yafara jini, shi Kuma Khalid ya suma.

Cikin tsanani da ciwo, Sadiq yayi yinkurin mikewa, amma akan ya cutura, Hatake jiri suka dibe shi, ya fadi sumamme.

Wallahi Baku ga komai bah, saina azabtar daku, irin azabar da ko da sunan ku baza ku iya tunawa bah.

Fatima dake d'ad'aure, tace Karima, ki dakata aka, kin ruga da kin azabtar da ahalin nan, ya isa aka, Dan Allah, kiyi hakuri, ki yafe Duk abunda akayi miki, koh Allah munayi masa laifi yana yafe mane, bare Kuma mutum Dan Adam.

Mom tace, ni kuma Banida zuciyar yafiya, bana yafe Duk abunda mutum yayi mun, kamar yadda na fada tun farko, dole saina kawo karshen wannan ahalin tukunan zan samu sukuni.

Doct khadija tace, Karima why, shekaru kenen kina gallaza wa wannan ahalin Ba tareda kowa yasani bah, aka kika rabani da ahalina kikamin sharri akan abunda ban aikata bah kika ce nayi, mene kuma ya rage, muguntar ta isa aka, kodan kinga baki samu wacce zata taka miki Burki bah,

Toh ni inada wacce zata taka miki Burki, wallahi, saikin gana wa aya zakinta.

Mom tace toh shikenen, inajiran Duk wacce zaki kirawo, ina jira,

Da sauri su, Aunty amarya da doct khadija, suka nufi hanyar waje. Tarar da su Sadiq sukayi a yashe cikin jini. Sosai su ke kuka, sun rasa yadda zasu sa rayuwarsu.

Cinci barsu sukayi suka nufi part din Su nadira dasu, inda kowacce ta Fara kula da mijin ta. Kwantar da su Dad akayi, yayin da Aunty amarya ta Bawa Dad magani, yasha,

bayan hour 3, jikin kowannen su ya lafa, yayinda su sadiq sun farka, kuma doct khadija tayi musu treatment, kowa aikinsu ya tashi, amma banda Kabir da haryanzu baiko Motsa bah.

Hankalin su Khalid ne ya kara tashi, Dad yace Meyasa Haryanzu Kabir bai tashi bah, Dan Allah ku ceci rayuwansa, banason wani abu yasami d'ana, doct khadija tace, nayi iya bakin kokarina wajan ganin ya farka, amma babu alamun zai farka, ina tunanin fa ya fada a doguwar suma.

Gaban kowannen su ne ya tashi, grandma tace khadija doguwar suma fah kika ce, yanzu menene mafuta.

Dafe kanta Aunty amarya tayi, tana mai nazarin mafuta a garesu. Da sauri Aunty amarya da Dag'o, sa'anan tace, akwai mafuta, juyowa gabadayansu sukayi, suka hada baki wajan fadin, menene mafuta?

Aunty amarya ta basu amsa da fadin, "Amriya", kwarai kuwa Amriya itace mafuta, zata iya, da taimakon ta, da taimakon Allah, zata iya cetan shi.

Doct khadija tace da kyar Amriya ta yarda, tazo, saboda ta fadamin cewar bazata kara tako kafarta cikin wannan gidan bah, kuma yanzu bah karamin tsana tayi wa Kabir bah, da kyar mu iya shawo kanta tayi. Tazo, Khalid yace insha Allah zamu yi iya bakin kokarin mu, wajan ganin ta zo. balla kofa sukaji anyi.

""""""""""""''''''''''''''''''''''""""""""""""""""""
Rasss gaban Amriya ya fadi ! , zuciyar ta, yafara Dukan uku uku, dafa ta doct Amina tayi tace, y'ata Amriya meyafaru?

Amriya tace, Ammi", jikina yana bani cewar, ahalin dana baro suna cikin halin tsaka mai wuya, tundazu gabana yake ta faduwa, yusuf yace toh kije ki gani mana, ko kuma muje,

Sai a lokacin Amriya ta tuna da irin cin mutuncin da suka mata. Amsa ta bawa yusuf da fadin, bazanje bah, na fasa, na ruga dana daukar wa kaina alkawarin bazan sake sanya kafafuwa na a wannan ahalin bah, dan aka, su nemar wa kansu mafuta, batareda taimakona bah.

COMMENT & SHARE PLS.
ALKALAMIN
AISHA M.B

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE91

https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*??
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ?asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sau?i_.??

ALJANAR RUWA CE ??♀??
PAGE 4??7????4??8??
WRITTEN & DIRECTED??
BY AISHA M.B (BABY ISHA) ???

----------------------------------------

cikin rashin fahimtar maganar Amriya Doct Amina tace, taimako Kuma! Wane taimako kike musu? Ganin aka yasa Amriya Saurin chanza magana da fadin, Aa Ammi kawai dai nafada ne cewar bazan Kara taimakon su bah, amma wasa nake babu wani abu.

Rike hannunwan ta Ammi tayi tace Amriya kenen, yanzu kenen baki yarda dani bah, kinai tsoro ne? na ruga dana fada miki cewa ki dauke mu tamkar ahalin ki, ki daukeni tamkar mahaifiyar ki, ki fadamin gaskiya,

Dan jimmm Amriya tayi, sa'anan tace ina tsoron bayyana muku wacece ni ne saboda, dalilin akan ne yasa wancan ahalin suka koreni, Kuma ina tsoron kada kuskure daya faru ya Kara maimai ta kansa.

Kallon ta bban yusuf yayi, yana mai fadin, Aa y'ata babu abunda zai faru, ki shafa wa zuciyar ki ruwan sanyi, bazamu taba butul talki bah kinji,

Gyaran murya Amriya tayi sa'anan tace, a gaskiya nidin bah mutum bace kamar yadda kukayi tsanmmani, nidin ALJANAR RUWA CE, Amma Dan Allah kuyi hakuri ban fada muku asalin wacece ni bah kafun na Fara zama daku a matsayin bakuwa, ni yanzu mah zan tafi,

Kallon Ammi Amriya tayi tace, gaskiya Duk wacce ta sameki a matsayin uwa, toh tabbas bah karamar yar sa'a bace, rayuwata bah karamin kyau zaiyi bah,
Ni yanzu zan tashi na tafi zanje na cigaba da lallaba rayuwata.

Jin kalaman ta, yasa Jikin kowanne sune yayi sanyi, shafar fuskar ta Ammi tayi tace, Aa Amriya kada kidamu muna tare dake Duk rintsi Duk wuya, baza mu taba rabuwa dake bah, Sanin cewar ke bah mutum bace akan bazai sanya mu gujeki bah, koh kadan baki yi kalan wa enda suke cutarwa bah, Kuma nidin zan kulada ke tamkar yadda mahaifiya zata kuka da yarta .

Ki sani mu dake gabadaya ahalin ne yanzu, kada ki kara bambamta kanki damu kinji, nima na rasa y'ata mafi soyuwa a gareni kamar dai yadda kema kika rasa mahaifiyar ki, dan aka yanzu kinzama y'ata

tabbas kedin yar sa'a ce, na tabbata da mahaifiyar ki tana nan zata yi farin cikin ganin wannan d'iya tata wacce take tattare da sa'a da Kuma alkhairy, na tabbata a koda yaushe zata kasance tana Alfa'ari dake.

Murmushi Amriya tayi sa'anan tace nagode sosai Ammi, hakika kedin mahaifiya ce ta kwarai, bazan taba mantawa da irin alkhairy da kika aikata a gareni bah, rungume ta Ammi tayi Tana Mai fadin Allah yayi miki albarka y'ata.

Tura baki gaba Yusuf yayi Tareda cewar, wato yanzu Ammi kinsamu Auta, ni kuma za'a manta dani koh, murmushi Ammi tayi tace Yusuf kenen sarkin k'ishi toh kaima tawo na sama albarka,

Tashi yayi ya nufi inda su Amriya ke Zaune, yana isa ya zauna a kusada Ammi yace, toh nima asaka min albarka,

Tom shikenen yusuf Allah yayi maka albarka, Allah ya baka Mace ta gari wacce zata haifa min jikoki,

Yusuf yace, Aba Ammi jikoki kuma tun yanzu, Abba yace, toh yusuf idan bakayi aure ka haifan mana jikoki bah, me kake so kayi, wai yaushe zaka futo da mata nee,

Yusuf yace kada kadamu Abba nan bada dadewa bah insha Allah, Amriya tace Kardai ka dauko mana mumuna irin wannan budurwar taka dana gani.

Kallon sa sukayi baki daya, Ammi tace Dama kanada wacce kakeso baka taba Sanar mana bah, Sosa k'eya yusuf yayi Tareda fadin, Hmmm Ammi fah karya Amirya takeyi, babu wata budurwar danake da.

Amriya tace Bawani karyar da nayi, ai ranar nan na ganta, yusuf yace a ina kika ganta din? a awajan nan.. ganin Amriya na shirin tona masa asiri yasa yayi Saurin daukan pillow zai buge ta dashi,

Amriya na ganin aka tayi Saurin mikewa tareda nufa hanyar daki da gudu, Ammi tace Kardai ka cutar min da d'iya, dan bazan kyale ka bah, Yusuf yace Kinaji fah Ammi wlh karya take min

Abba yace mum yarda karya take amma kada ka Bari wannan watan ya Kare baka kawo mana suruka bah kaji na fada maka,

Yusuf yace aba Abba wata daya fah, ina laifin shekara, yanzu ni ina zanje na samo budurwa na nawa maka cikin wata nan,

Abba yace Oho duk inda Kaga yayi maka ka samo , mudai burin mu ka kawo ta mugan ta, inba aka bah da kaina zan aurar dakai.

Shagwaba fuska yusuf yayi, yana mai fadin Ammi kinajin mijinki koh wai ni zai aurar, kenen auran dole za'a min. Ammi tace kwarai kuwa auren dole za muyi maka, danna ga idan bah auren dolen muka makaba, toh bazaka futo mana da suruka bah.

Yusuf yace Tom shikenen zan futo da mata, amma gaskiya sai an karamin lokaci, danni bah yaro bane bah, Ammi tace kaji dashi dai,

-----------------------------
Cikin tsorata gabadaya suka juya don ganin wanene, juyawar su keda wuya suka ga Mom a tsaye ta dora wuka akan wuyan Fatima wato matar Dad,

dayan hannunta kuma rike take da files, Gyaran murya tayi sa'anan tace kuna ji kuna gani zan kashe ta a gaban ku batareda kun ceci rayuwarta bah,

Dafe zuciyarshi Dad yayi wanda yakeji tamkar zata fashe sabida kunci da takaici,

Cillawa Dad document din hannunta mom tayi, tana mai fadin wannan itace kadarorin ka gabadaya, ka saka hannu, kasaka cewar wannan kadarar Ba taka bace ta Karima ce, in Kuma bah aka bah, kana gani zan kashe ta har lahira.

Kallon Fatima Dad yayi wacce ta rintse idanuwan ta hawaye na zubowa kan kuncin ta, sannan yace dama Fatima kina a raye ban Sani bah, meyasa baki fadamin cewar kina raye bah Tsawon wadanan shekarun, kinsan wane Hali na Shiga tsawon wadanan shekarun da bakya tareda dani.

Kallon shi Fatima tayi tace, Bah lafi na bane, danasan aka zata kasance daban saka rayuwar ku da d'ana a cikin hatsari bah.

Aunty amarya tace bake kika saka rayuwar mu a hatsari bah, wannan shedaniyar matar ce,

Cikeda baccin rai Mom tace kwarai kuwa, nice nan, Wato har kun manta abunda kuka aikata mu shekarun baya da suka gabata kenen, kun manta yadda kuka Shiga tsakanina da yar uwata kuka saka mu cikin kunci da bakin ciki,

Dad yace wai waye yasa kaki kunci,shin nasan ki ne a da? Fadamana me muka aikata miki,

Mom tace bani zaka tambaya bah mahaifin kah dake Kabari zaka tambaya, danshi yasan komai da komai da yafaru, abunda ya aikata shi yake shafar y'ay'an sa kuma gashi harda jikokin da yatara,
Wato kun taru kuna cin Dukiya kuma kudin haram, kun taru kuna siyan tufafi abinci, yin abunda kuka gadama da kudin da ba naku bah ,

Kuma a akan kuke tunanin zan barku ku sha, akan bazata faruba, maza maza kasa hannu akan takardan nan in bah aka bah na yanka wuyan ta yanzu nan.

Cikin fusata Dad yace bazan saka bah, Kuma baki isa kiji mata koda kwarzane ne,

Murmushi mom tayi ta cilla mahaifiyar kabir gun Dad, babu bata lokaci Dad yayi Saurin riketa,

Mom ta kallesu tace, na baka nan da 24hours, da zaka sa hannu akan files dinnan, in bah aka ba, toh na rantse da ubangijin da nake bautawa, gabadaya saina kona ku da ranku, karasa maganar ta keda wuya ta fuce daga cikin dak'in.

Rungume Mahaifyar Kabir Dad yayi, yana mai fadin, ki gafarce ni Fatima, kiyi min aikin gafara, danasan kina raye kuma kina cikin gidanan, dana saka police sun kama Karima. Kiyi hakuri,

murmushi Mahaifyar Kabir tayi tace, babu abunda ka aikata min, yanzu burina shine na sanya d'ana a cikin idona, ina d'ana yake,

Nuna mata inda Kabeer ke kwance Dad yayi, Kallon wajan tayi, yayin da ta sauke idanuwanta akan kabeer, Wanda ke kwance har yanzu ba ya motsi.

Tashi tayi da sauri tareda nufan inda yake, kuramasa idanu tayi hawaye na sauka kan kuncin ta, tace Allah sarki d'ana, wancan azzalumar matar ta rabani dakai, bata Bari naji dimin ka bah, ta dauke min Kai, yanzu bah lallai ka soni kamar yadda ka sota a baya bah.

Tabbas yanada wuya ka iya yarda cewar ni asalin mahaifiyar ka ce, domin kuwa zaka kuma dauka ko wani raina mah hankali za'a kuma yi, tunda na haifo ka wannan duniyar baka taba ganina bah, bare ka kirani mama, ka taimaka ka kirani mahaifiyar ka koda sau daya ne kafun numfashi na na karshe, tana kaiwa nan ta fashe da kuka mai ratsa zuciya,

Jikin gabadayan su ne yayi sanyi, yayin da su kaji tausayin ta ya matukar kamasu. Hawayen dake shirin zubowa Dad yayi Saurin sharewa, tareda fadin, kada kidamu Fatima" yanzu ai kin dawo rayuwar shi, tabbas nasan bazai guje ki bah, Kuma na tabbata zai rike ki hannu bibbiyu,

Fatima tace da wuya ya yarda ni Mahaifyar sace, kasan yadda zuciya ta ke kuna da radadi, kasan yadda naji yayin da ina ji, ina gani, aka raba ni da dana daya tilo, shin meyasa bata dau raina bah ta barni a raye tana gallaza mun azaba, babu irin azabtarwar da bata yi min bah, tabbas laifi na ne, dana dora mata yarda ta, daban dora mata yarda ta ba, da bata aikata akan agareni bah.

Cikin rashin fahimta Dad yace, kamar ya? Shin dama kin San tane tuntuni? Shiru Fatima tayi ba tareda ta bawa Dad amsa bah.

Daga sama sukaji Doct khadija tace, Kuyi hakuri, ku gafarta min, duk abunda ke faruwa da ahalin nan gabadaya laifi na ne,
Tabbas a yau zan bayyana muku gabadaya abunda ya faru, da har kukaji nice da laifi,
Dakatar da ita Dad yayi da fadin, Bamua son jin komai daga gareki, kawai kiyi shiru khadija, hawayen ta Doct khadija ta share, tareda fadin Yahya a matsayina na kanwar ka, ka taimaka kabani Dama daya kacal, zan bayyana Duk kulla kullan da Karima ta aikata. Kaima kasan bazan taba maka karya bah.

Ka yarda dani, Dad yace khadija a matsayin ki na kanwata ai bai kamata ki aikata aka a garemu bah, meyasa kika ci amanan wannan ahalin, meyasa kikayi mana karya, ga mama nan kema kinsan yadda mama take matukar kaunan ki duda cewar bah ita ta haife ki bah, amma tafi rubuta ki akan mu.

Lokacin da Abban mu ya kawo ki gidan mu a matsayin marainiya, aka muka dauke ki tamkar yar ahalin mu har kika girma, soyayya, kulawa, da qauna, babu wanda bamu nuna miki bah, bamu taba bamban ta kan mu da ke bah, amma akan bai hanaki guduwa da wani namijin a wajan bikin ku wanda za'a muku keda Maryam bah, sannan kika je kika aure shi. kinsan halin da muka Shiga da muka ji labarin kin gudu da wani saurayin,

Kinsan kunya da bakin cikin abunda kika aikata ya sanya mahaifin mu har silan akan yasa ya rasa rayuwar shi, meyasa tun farko baki fada mana ga wanda kike so bah, ai dashi zamu baki, basai kin kunyata mu a idanuwan jama'a. Amma bakomai komai yayi farko zaiyi karshe.

Hawaye ne yafara gangaro wa daga idanuwan Doct khadija, cikin sheshekar kuka tace Dan Allah kubani dama daya zan fada muku duk abunda ya faru , tabbas kun yimin gurguwar fahimta ne, ku tsaga ku saurare ni.

Grandma tace toh shikenen y'ata munajin ki, Muhammad Kabari ta fada mana abunda ya faru,

Dad yace Tom shikenen muna jin ki, Kallon su Khalid da su nadira Dad yayi yace, ku bamu waje zamuyi magana.

Dakatar da Dad doct khadija tayi da fadin Aa zuyi zaman su, suma aiba yara bane, ka barsu Suji abunda ya faru.
Amma dan Allah kafun na fara inaso kowa ya bada hankalin shi wajena.

Zama sukayi baki daya, yayin da kowa ya nutsu, tattaro nutsuwan ta Doct khadija tayi,
ta fara magana kamar aka.

Asali nida Karima babban kawaye ne tun muna bording school, zaro ido gabayansu sukayi, what! Dad yafada.

Kwarai kuwa nida Karima babban kawaye ne, Kuma itadin sunan ta hassana ne, sudin yan biyu ne, but not identical twins, abunda yasa bakusan Karima bah shine bata taba yarda tazo gidan mu bah, saidai Ni dakuma Amina, koda tazo bata taba yarda ta shigo bah.

sunan yar uwarta Amina , mun taso Cikeda kaunan junan mu, ko ina tare muke zuwa gidane kawai ke rabani dasu, saboda qaunan junan da mukeyi har alkawari muka daukan wa junan mu cewar Duk y'ay'an da muka Haifa saimun hada su aure, domin akan takara mana zumunci

Nida Amina yar uwarta mun kasance masu kokari a class, yayin da ita bata da kokarin ko kadan, akan yasa muke yawan samu matsala da ita, take nuna k'ishin ta a bayyane, koda gasa ake ta makaranta toh nida Amina ne kawai ake kira gasa.

Amina itace hussainan ta. Amina ta kasance Mace mai hakuri da Kuma kawaici, Tana da farin jini sosai a makaranta, Duk inda Ta shiga mutane na yabon ta.
Ashe akan na bakan tawa Karima, kwatsam wata rana Aka aiko mana da sakon gayyata na makarantu wanda za'a fafata tsakanin dalibai.

Kamar yadda muka saba, a lokacin ne itama Karima tace tanason Shiga gasar da akeyi, Tana son ta nunawa duniya cewar itadin bah doluwa bace bah, abunda yar uwarta keyi zata iya yin finsa mah.

Malaman makaranta kuwa basu ja da akan bah, amma suka mata gargadin cewar indai ta bawa makaranta kunya toh za'a sallameta daga makarantar, cikin rashin tsoron abunda zaizo ya biyo baya Karima ta amince da Sharadin da malamai suka fada mata.

bayan nan, gabadaya makaranta muka hallarci wajan taron daliban da akeyi, yayin da akace Duk wacce taci za'a bata babban kyauta dakuma scholarship na makaranta.

Ni da Kuma Amina mun fafata Kuma munyi nasara, yayin da Karima kuwa ta bamu kunya a bainan jama'a, ganin hanata mata dariya yasa bakin ciki da kuncin ya dameta ta futa daga cikin hall din da gudu tana kuka.

Yayin da mu Kuma aka bamu kyautu tuka da Kuma scholarship, iya kyauta muka karba bamu karbi scholarship bah, akan bah karamin bawa mutanen wajan mamaki yayi bah, inda dalibai suke fatan su sami scholarship, amma mu mun samu munce bamua so, dalilin akan kuwa shine Karima,

Domin kada Karima taji Ba dadi akan yasa muka ki karba, bayan koma wan mu hostel, Karima ta daina mana magana, koh mun mata magana bata kula mu, saidai taita kula wasu kawayen banza marasa tarbiya, akan bah karamin damun yar uwata keyi bah,

Hana tsaka da aka, wani matashi Mai suna Habib Dan sarkin bauchi ya fada a soyayyar Amina, sosai masoyan nan suke shan soyayya, Wanda baki bazai iya masalta irin son da suke wa junan su bah,

Lokacin da muka rubuta WEAC din mu, muka futo da sakamako Mai kyau Dama mu a bangaren science muke nida Amina Ita Kuma Karima ART class, amma duda akan bata futo da sakamako Mai kyau bah.

Akan bah karamin bata ran mahaifin su yayi bah domin kuwa mahaifinsu yana da kudi, dukiya, da Kuma wadatar arziki. Amma ace yarsa bata da kokari koh kadan, cikin baccin rai kuwa, budar bakin mahaifin su keda wuya ya kirata da Mai kwakwalwar kifi, jin akan datayi yasa tun daga ranar ta dora tsanan duniya ta dora mana. Amma akan baisa ta bayyana mana bah.

Hana aka Habib yaje wajan Amina hira, daidai lokacin itama ta ganshi taji duk duniya babu Wanda takeso kamar shi,

Ni kuma a lokacin ne mahaifin ku yace yayi min miji nida Maryam, daga nan sai na dora karatu na a inda na tsaya ban musa bah Kuma na amince da maganarshi, saboda a lokaci Banida wani a raina,

Lokaci zuwa lokaci Habib ke zuwa gidansu Karima har wani sa'in yake futa damu shopping, Hana aka har labari yaje kunnen iyayen su, har sukace masa ya turo magabatan sa, jin akan bah karamin sanya shi farin ciki yayi bah,

yayin da aka ce itama Karima ta futo da miji. Jin akan da Karima tayi yasa ta bayyana wa kowa abunda ke cikin ranta, jin akan kuwa bah karamin bata ran mahaifiyar su mai suna Jamila yayi bah, da Kuma y'ay'an su Suleiman bah.

Amina tace tayi hakuri domin kuwa bazata iya sadaukar da soyayyar ta bah, ita kuwa Karima ta nuna mana cewar, komai ya wuce babu komai a zuciyar ta, ashe itadin munafuka ce.

Bayan wasu kwanaki Habib ya turo magabatan sa , yayinda aka tsaida auren Amina da Kuma Habib.

Ni kuma a lokacin an kusa bikin mu nida Maryam. A lokacin kuwa, Karima ta bijiro da kule kulen samarin, harta kawo min wani saurayi mai suna Harun, wai yana sona, ta karfi da yaji, Karima tasa na fada a soyayyar Harun,

Yayinda muke soyayya Cikeda burgewa, Harun, ya kasance masu matsakaicin karfine, amma akan bai hana ni k'in sonshi bah,

Ranar aure na kuwa, ta zuga ni wai mu gudu da Harun, ni kuwa nace mata gaskiya bazan iya butulci bah, kunyi mun abubuwa da dama, amma in rasa da abunda zan saka muku sai wannan.

Aka dai taita zuga ni, nace indai saboda soyayya zaisa na gudu toh saidai na hakura, data ga nak'i sauraron ta, ta shakamin abu a hanci na, cikin kankanin lokaci bacci yayi hawan gaba dani. Aka suka cincibe ni suka kaini daji batareda nasan inda kaina yake bah,

Bayan farfado wata, take fadamin cewar saita dau fansar abunda muka aikata mata nida Amina, lokacin ne Harun ke fadamin cewar bah sona yakeyi bah ita ta biyashi danya cimin zarafi Kuma nasa ahalin da suka yarda dani, su tsaneni, Suji kaff duniya babu ma yaudariya maciya amana sama dani,

Kuka kamm nasha shi Harna godewa Allah, Hana tsaka da aka, Harun ya bayyana mun soyayyar sa agareni, tareda cewar shin zan auresa, Babu bata lokaci na yarda muka daura aure nidashi, yayin da ya gina mana gida na masu rufin asiri,

Ashe a lokacin Karima ta dai photo na da Kuma Harun ran auren mu, ta tura muku, akan yasa kuka nuna baccin ranku akaina, rana bazata tashi ta fadi ba Tareda nayi kuka bah,

Hana aka naji labarin itama Amina an daura mata aure da Habib, murna sosai nayi shi, domin kuwa har naso zuwa inda gidan ta yake amma kuma bansan gidan ta bah. Ba yadda na iya, aka na hakura na fauwala wa Allah komai, domin shine Mai jikan bayinsa.

Babu bata lokaci, Harun ya neman mu makarantar Jami'a, na fara zuwa Harna karanci medicine, yayin da itama Amina abunda ta karanta kenen.

Hana aka mukaji labarin cewar Abba ya mutu bisa hatsarin mota daya gamu dashi, kuka mai cike da danasani nayi, saboda a ganina nice sanadiyar mutuwarsa .

Bayan lokaci ne Kuma naji labarin kayi aure ka auri Fatima. saboda kunya abunda na aikata bah Lallai ku yarda dani bah yasa nak'i zuwa auren.

Hana aka kwatsam watarana na fara amai mukaji asibity, hanan likitoci suke sanar mana da cewar ina dauke da cikin wata biyu.

Sosai mukayi murnan wannan cikin yayin da Haruna ya dora son duniya akaina har cikin yakai wata Tara.
Ganin muna rayuwa cikin farin ciki da qaunan juna, yasa Karima ta kuma dawowa cikin rayuwar mu, a wannan karan bah ita daya bane, su dayawa ne domin kuwa tayi joining yan kungiyan asiri .

Lokacin ta umarci mijina Harun da ya dunga mata aiki, shikuwa yace bazai taba aikata akan bah. Kuma yace da ita sai ya tona asirin ta a idon jama'a, ya dau Wayanshi Tareda kira police.

Karima na ganin akan ta harbe shi da buduga, ya fadi a wajan mutacce, daidai lokacin kuwa na kuda ya kamani.

Babu bata lokaci police zuka zo, suka kamata, aka kaita police station.

Ni Kuma a lokacin na Haifi dana, kuka nashashi Harna gode Allah, yayinda aka suturta harun aka kaishi gidansa na gaskiya.

Bayan shekaru biyu na gama makaranta na nayi NYSC na a garin Kano, yayinda akayi posting dina'a hospital, na Fara aiki

bayan wasu lokaci naji labarin ta futo daga cell, akan bah karamin tayar min da hankali yayi bah, domin kuwa bansani bah ko wannan futowar tata ya kasance wani gagarumar matsalan, cikin sa'a kuwa ta daina bibiyar rayuwa ta.

Hana aka na shirya Domin naje na nemi gafarar ku, zuwa na keda wuya naganta acikin gidan nan wai a matsayin matar aure, ganin aka bah karamin tayar min da hankali yayi bah, domin kuwa nasan da cewar bah alkhairy ne ya kawo ta wannan gidan bah.

Akan yasa na juya na tafi gida na cigaba da lallaba rayuwata da Kuma na dana. Ina nan duty na a hospital naji kira ya shigo bah bata lokaci, na d'aga Kiran tareda karawa a kunne na,

Muryar dana ji ne yayi matukar girgiza ni, muryar dana ji kuwa bata kowa bace illa na Amina, sosai Nayi murna Mara misaltuwa a ranar, mu ka taba hira, Kuma tace min zata dawo asibity da nake aiki.

Nadira tace kina nufin Doct Amina itace yar uwar Mom, Doct khadija ta bata amsa da fadin kwarai kuwa itace yar uwata, amma kuma har yau har gobe babu wani a tsakanin su dayasan cewa sudin yan uwa bane, domin kuwa, duk saida na bi hanyan danasan cewar Karima baza ta ga Amina bah, domin karta ganta.

Kamar yadda nake fada, bayan kwanaki aka kawo matar yahya, asibity zata haihu, yayinda iyaka Karima take na kuda, a taredai naga kun kawo su asibityn, ganin akan dana yi yasa nasa face mask ta yadda baza ku gane ni bace,

Na karbi haihuwar Fatima da Kuma na Karima, cikin rashin sa'a Kuwa, dan da Karima ya haifa ya ruga mu gidan gaskiya,

Shine sai Karima tamin barazana da d'ana, tace idan ban sauya yaron bah, na bata na Fatima saita kashe d'ana, jin akan yasa na dauki video a memory na, sannan na chanza danta da Kuma dan Fatima, yayinda ta kuma cemin, nace Fatima ta mutu, koh Kuma ta kashe dana, jin akan danayi bah karamin tsorata ni bah, amma ba yadda na iya aka na dauk'i wannan babbar kasadar, nace muku dan ku dakuma Fatima sun rasu.

A lokacin naga hankulan ku bah karamin tashi yayi bah, bayan na isa gida nai ta kuka da danasanin abunda na aikata a gareku. Tabbas ban muku adalci bah, Kuma banyi wa Fatima adalci bah, domin kuwa babu abunda Fatima tayi wa Karima amma saboda rashin imani irin na Karima ta sa na raba da da mahaifiya. Kuma har yau har gobe, ban sake hada ido da dana bah, bansani koh yana raye koh Kuma ta kashe shi bah.

Tana kaiwa nan ta fashe da wani matsanan cin kuka mai cin rai. Hada hannayen ta guri guda tayi tace, iya abunda nasani kenen dan Allah ina neman gafarku daku yafe min, dan Allah ku yafemin tabbas na aikata muku kuskure,

Jikin kowannen su ne yayi sanyi, Hawaye yafara gangaro wa a idanuwan Fatima, fatima tace ni na ruga dana yafe miki duniya da lahira.

Tashi su Nadira sukayi ,tareda rungume ta, Dad yace mun ruga damun yafe miki yanzu babu komai a zuciyoyin mu kinji kanwata.

Kuma insha Allahu Karima saita gurbi abunda ta shuka. Domin kuwa bata ci bullus bah. Amma shin meyasa take cewa mun ci mata dukiya, fansa zata dauka, doct khadija tace wannan Kuma ita zata bada amsa Domin ni kaina bansan me take nufi bah.

Dad yace toh amma shin Amina bata haihu bane har yau, Doct khadija tace ta haife danta Kuma saikuma karamar yarta amma bata kai shekara bah ta rasu.
Allah ya jikan ta, gabadaya suka amsa da Ameen.

Khalid yace yanzu ya zamuyi mu futa muje wajan Amriya Domin ta tashi Kabeer, Aunty amarya tace, inada wata hanya wanda bah kowa yasan da hanyar bah a gidan nan, domin ta hanyar nake bi nake zuwa kungiya,
Kamar hadin baki suka ce, kungiya Kuma!

????????????????

WANNAN NA KUNE FAN'S, ASHA RUWA LAFIYA.

COMMENT & SHARE PLS ?
ALKALAMIN ??
AISHA M.B
(BABY ISHA) ???

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE91

https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*??
(J.W.A)
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ?asaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sau?i_.??

ALJANAR RUWA CE ??♀???
PAGE 4??8????4??9??
WRITTEN & DIRECTED ?? BY
AISHA M.B??
(Baby isha)

--------------------------------------
Kwarai kuwa kungiya, nima ina daya daga cikin yan kungiyan asiri ,amma bah nashiga bane don cutar da al'umma, nashiga ne kawai Domin tseratar da rayukan ahalin nan, da Kuma na Kabir, so da dama tayi yinkurin kashe Kabir, amma Allah bai bata ikon yin akan bah.

Dan Allah karku yimin gurguwar fahimta, yanzu zaku iya bin nan hanyar Ba tareda kowa ya ganku bah, tashi su Khalid sukayi Tareda daukan mukullin mota,

Doct khadija tace me Kuma zakuyi da makullin mota, Khalid ya bata amsa da fadin, ai da mota zamuje, doct khadija tace toh kenen dai Baku shirya zuwa neman Amriyan bah gaskiya,

Kamar ya Khalid yafada, kamar dai yadda kaji, Baku shirya zuwa bah, ya za'a yi ace zakuje da mota, bayan kasan body guard dinnan na wakan sun zagaye gate baki daya, toh yanzu fadamin ta ina zaku futa da motan.

Sai a yanzu Khalid ya tuna da cewar tabbas akwai yan kungiyan Mom a wajan, sadiq yace toh yanzu a ina zamu je kenen?

Aunty amarya tace, abunda zakuyi shine ku tafi a napep, shine kwanciyar hankalin mu.

Tom shikenen bara mutafi, amma doct khadija zaki biyomu, koh saboda bamusan gidan bah, yes of course doct khadija ta Bashi amsa, tashi gabadayansu sukayi, inda sukayi musu fatan nasara daga bisani su ukun suka fuce daga cikin gidan.

Tafiyar su keda wuya, Mom ta banko cikin dak'in, a razane gabadayansu suka mike tareda ja da baya.

Kallon su Mom tayi tareda watsa musu banzan kallo tace, me kuke shirya wane, koh Kuma shirya yadda zaku tseratar da rayukan kune,

Nadira ta bata amsa da fadin, kwarai kuwa, idan mun tseratar da ran mu laifi ne? Koh kuwa akan ya shafe ki, buge mata baki Aunty amarya Tayi, tana mai fadin Nadira ki kiyaye ni, kada ki kuskure na karajin ki hanan,

Maida Kallon ta kan Mom aunty amarya tayi tace, kiyi hakuri Karima, kinsan har yanzu yarinta ne ke damun ta,

Murmushin mugunta Mom tayi tace, yarinta bah, toh shikenen Tunda yarinta ke damun ta, nima zan gwada salon yarintar tawa, Tana kaiwanan ta zaro wani zabgegen dorina, a hassale tayi kan Nadira da dorinan.

Su Abdul na ganin aka, suka nufi inda take tareda ririke ta, Grandma tace yauwa ku rike ta, shegiya annamimiya, munafuka, da sauri Adeef ya futa, ba'a fi mintuna bah, ya shigo da doguwar igiya.

Kwace kanta daga garesu mom ke sanyi amma ina akan ya cutura, daddaure tah sukayi, saida sukayi mata d'aurin rago, sannan suka rabuda ita. yayin da Grandma ta wafce dorinan daga hannun ta, tace

Wato ke nan uwar shedanu koh, bah uwar shedanu bah, in mah kece kakannin mayu da aljanu, wannan bai shafeni bah, munafuka mai hanci socket, bamu zaki daka bah toh ni barana nuna miki salon yadda ake jibgan karnuka da akuyoyi irin ki,

Tana kaiwanan, bata yi wata wata bah, ta fara shauda mata ajiki, ihuu Mom ta fasa, da sauri Amar ya toshe mata baki da zani, ya yinda yayi mata alama da hannunsa tayi shiru,

Tattaro karfin ta gabadaya Grandma tayi, ta fara zuba mata dorinan Ajiki bah kakkautawa, ihuu Mom keyi da iya karfin ta, yayin da takejin dorinan na Shiga har cikin kwakwal war ta da Jikin ta, cigaba da zuba mata dorinan Grandma tayi, tana mai fadin,

Bake uwar shedanu bah, toh yanzu ki ceci kanki a wajena,ai yau koh wallahi Mai cetan ki a wajena sai Allah.

Tausayin Mom ne ya Kama kowannen su na dak'in, Dad yace Mama ki rabu da ita kawai, Kibari Allah yayi ikonsa akanta,

Grandma tace, bazan barta bah, Tunda ita uwar shedanu ce, toh ta kira shedanun tah zuzo su ceceta a wajena,

Saida Grandma taga Mom ta cigata, sa'anan ta rabuda ita, tareda danna mata rankwashi akai,

gabadaya Mom ta zama abar tausayi, idanuwanta sunyi jajir kamar tsohuwar mayya. Kallon shi gabadaya tayi, yayin da take hayyana irin azabtar war da zata musu .

------------------------
Ammi bara naje nasha magani, naji kamar zazzabi nason kamani, Tom shikenen yusuf amma ka tabbatar kasha fah, Tom shikenen Ammi insha Allahu zansha. yinkurin tashi yusuf keyi amma ya kasa, inda a karshe yayi nasaran tashi,

Hatake jiri mai karfi ya dauke shi, luuu ya tafi tareda faduwa a wajan sumamme.
Innalillahi wa innahilahi rajihun! Ammi ta fada tareda nufan inda yusuf ke yashe a kasa tafara jijigashi, ganin koh motsi Bayayi, yasa ta kwalla wa baban yusuf kira,,

Cikin kankanin lokaci, baban yusuf ya bayyana a wajan, ganin yusuf a kwance bah alamun motsi a tattare dashi ga kuma Ammi Tana ta faman kuka, akan yasa yayi Saurin isa inda suke.

Amina meyafaru da yusuf? Ammi ta Bashi amsa da fadin wallahi bansani bah kawai muna Zaune yace min yanajin zazzabi, shine yace min Zaije ya shafa magani, ban hankara bah naga ya fadi, dan Allah kayi wani abun.

Jin kamar Hana kuka yasa Amriya futowa daga cikin daki, tareda nufan hanyar falo, abunda ta gani ne ya girgiza ta, da sauri ta nufi inda su Ammi suke, tana mai fadin, Ammi meyafaru? Tun daga abunda yafaru harkashe Ammi ta zayyane wa Amriya.

Kallon yusuf Amriya tayi tareda shafa kansa ta rintse idanuwan ta. Da sauri ta Bude idanuwan ta tace, yana bukatar taimakon gaggawa, ya ka mata mu kaishi asibity yanzu nan.

Mikewa Ammi tayi tareda hawa kan upstairs da sauri, ta dauko hijabin ta da kuma na Amriya. Daukan car key baban yusuf yayi, sanya hijabin Ammi tayi, sannan ta bawa Amriya itama hijabin, karba Amriya tayi tareda sanya wa ajikin ta.

Yinkurin daukan Yusuf babansa keyi amma ina akan ya cutura, wani dabara ne ya fadowa Amriya, saita hannun ta tayi daidai inda yake yashe, sannan tayi amfani da karfin ta na ALJANAR RUWA. ta Fara ju yashi,

Bah bata lokaci, yusuf yayi sama, hanyar waje Amriya tayi da gangar jikin sa, su Ammi naganin akan suka biyo bayansu,

Masu tsaron gidan na ganin aka, sukayo wajan da sauri, yayin da kowannen su ya tada mota, shigar da yusuf sukayi cikin mota, bah bata lokaci suma suka Shiga mota.

in da masu gadi suka bude musu kofar gate, daya bayan daya, motocin suka Fara futa har suka gama futa baki daya.

motocin gidan ne suka jeru akan titin, ganin goslow yayi yawa, babu hanyar da zasu bi, gashi bangare guda Kuma trailers sun tare hanya, yasa Ammi dora hannu a Kai tace shikenen zan rasa dana kamar yadda na rasa y'ata,

Amriya tace insha Allahu babu abunda zai faru dashi, da yardar ubangiji babu abunda zai same shi.

Kallon motocin da suka tare hanyoyin Amriya tayi, ta rintse idanuwan ta ,tareda saita hannunta daidai wajan motocin, tafara yin wasu abubuwa da hannayen ta, Hatake motocin suka Fara rarrabuwa, ya yinda trailers din suka samu hanyar wucewa,

Sosai mutanen wajan suka Shiga yin mamaki, daya daga cikin masu tuka trailers din yace, taya akan ta faru motoci su raba kansu, kuma ta bada hanya ba tareda wani ya tu kasu bah, tabbas abun al'ajabi baya karewa.

Barin wajan su Ammi sukayi, direct general hospital suka nufa, inda nurses suka futo tareda bawa yusuf gado suka Shiga dashi cikin emergency room, bah bata lokaci suka Shiga bashi taimakon gaggawa.

Zama Ammi tayi ta kafa tagumi, zuwa Amirya tayi inda Ammi ke Zaune tareda rungume ta tace, Ammi Dan Allah kada ki sa kanki cikin damuwa. Aduar ki kawai yake bukata.

Kallon Amriya Ammi tayi tace, wallahi Amriya tsoron abunda yafaru baya nakeyi, banason tarihi yakara maimaita kansa, kanwarsa cutar Asma ne ya kashe ta,

Yanzu shima gashi yana cuta, ina tsoron kada shima ya tafi ya barni kamar yadda itama ta tafi ta barni. Amriya tace ki kwantar da hankalin ki, Kisa a ranki cewar danki yasa mu lafiya.

Daya daga cikin nurses din ce ta futo, Ammi na ganin aka tayi Saurin mikewa, tareda nufan inda nurse din ke tsaye, shima abban Yusuf ya nufi wajan.

Amriya tace ya jikin Mara lafiyan, Nurse din ya basu amsa da cewar da sauk'i, amma danku yana bukatar jini sosai saboda jinin shi yayi kasa, kuma akan kan iya sa wani Bangare na jikin shi yasamu matsala.

Dole dai hana bukatar blood group wato (Onegetive) in bah aka bah, am sorry to say, zamu iya rasa shi.

Rass gaban Ammi ya buga, yayin da Abban yusuf yace nurse dole ne sai irin jinin sa za'a bashi? Nurse ta bashi amsa da cewar yes of course and we need the blood urgently, Tana kaiwa nan, ta shige ciki.

Dafa kanta Ammi tayi, yayin da takejin kanta na mugun saramata , Abba yace toh mu bashi mana jinin koh,

Kallon Abban yusuf Ammi tayi tace, ka manta mu bah O negative bane, ka manta bazamu iya bashi jini bah, Abban yusuf yace but why?, Ammi ta bashi amsa da cewar wato har ka manta yusuf Adopted child ne, ka manta da cewar yusuf bah dan mu bane,

Sai a yanzu Abban yusuf ya tuna da cewar tabbas yusuf bah dansu bane adopted child ne.

Kallon su Amriya tayi cikin rashin fahimtar maganganun su tace, Tunda yana bukatar jini ku bashi mana koh Kuma ni na bashi nawa.

Kallon ta Ammi tayi tace, ke Amriya kina dauke da ciki bazai yu ki bashi jini bah, muma Kuma bazai yu mu bashi jinin mu bah, amma saboda me? Amriya ta tambayi Ammi,

Ammi ta bawa Amriya amsa da cewar, saboda yusuf bah dan mu bane bah.

Zaro ido Amriya tayi tace mee, kina nufin yusuf bah danku bane, toh wacece mahaifiyar sa? Ammi tace wallahi muma bamu sani bah, a bakin hanya muka tsince shi lokacin baya cikin hayyacin shi, baisan ciwon kansa bah, a lokacin muna fama da rashin haihuwa, sai Kuma Allah ya bayyana mana yusuf a matsayin da a garemu.

Kuma a halin yanzu dole Mahaifyar sace kawai zata iya bashi jini.

----------------------
Kwan -Kwan -Kwan, su Khalid suka Shiga Kwankwasa kofan gidan, daya daga cikin masu tsaron gidan ne ya Mike tareda nufan hanyar gate din ya bude musu gidan.

Kallon su Mai gadin yayi, ganin doct khadija ce yasa yayi Saurin wangale gate din, tareda gaisar da ita, amsawa Doct khadija tayi tace, shin mutanen gidan suna nan kuwa?

Mai gadi ya bata amsa da fadin, wallahi gabadayan su, Sun futa, dansu ne bah lafiya, yanzu mah suna Chan babban asibity,

Innalillahi wa innahilahi rajihun! Doct khadija tafada, babu dai abunda ya same shi koh, Mai gadi yace babu abunda yafaru, amma yana ga kamar hankalin ki ya tashi, cewar Mai gadi.

Doct khadija tace babu komai shikenen, Kallon su Khalid tayi tace, ku tawo mu wuce asibity suna Chan,

Tarar napep sukayi, yayin da suka Mai kwatan cen asibityn, direct Asibityn Mai napep ya nufa dasu, ba'a fi mintuna ashirin bah suka isa wajan. Futowa sukayi daga cikin napep din, yayin sadiq ya biyashi kudin sa.

Shiga ciki sukayi, inda suka tarar da su Ammi a zazzaune, Amriya na ganin zu Khalid tayi saurin kauda Kanta gefe. Da sauri Doct khadija ta nufi inda Ammi ke Zaune.

Ganin Doct khadija, yasa Ammi yinkurin mikewa, zaunar da ita Doct khadija tayi tace Aa kawata basai kin tashi bah, ya jikin nasa yanzu, Ammi tace da sauki, amma nurse tace dole yana bukatar karin jini Kuma Onegetive, in bah aka bah zai iya rasa rayuwar sa .

Doct khadija tace jini na Onegetive ne, muje zan bada nawa jinin, Aa khadija you don't need to stress yourself, Doct khadija tace no Amina what are we friends for, na taimake ki, kema ki taimaka min, yusuf shima a matsayin dana yake , kinga bazan ga yana cikin magagin mutuwa Kuma naki taimakon sa.

Tashi Doct khadija tayi tareda Shiga cikin room din, tareda Sanar da nurse din cewar zata bada jinin ta,

Kwantar da ita akayi sannan aka zuki jinin ta, yayin da nurse din ta bawa Doct khadija Apple ta ci. Saida aka ibi wajan leda guda na jinin Doct khadija, sannan aka sanya wa Yusuf.

Yin kurin tashi Doct khadija keyi, Nurse din ta dakatar da ita da fadin, Aa bai kama ta ki tashi bah yanzu, kina bukatar ki kwanta, ku huta, Doct khadija tace na ruga dana kwanta babu damuwa inason zanyi wani abu mai mahimman ci ne, Tana kaiwa nan ta fuce daga dakin.

Su Amirya na gani ta suka isa Inda take, Ammi tace har kin bada jinin, Doct khadija ta bata amsa da cewar Eh na bada, godiya sosai Ammi tayi mata, yayinda Doct khadija tace babu godiya a tsakanin mu.

Kallon Amriya Doct khadija tayi tace, Amriya muna bukatar taimakon ki, Kabeer yana cikin halin tsaka mai wuya, kuma da taimakon ki da taimakon Allah, zaki iya fidda shi daga wannan halin da ya shiga, Dan Allah Amriya kada kice baza ki je bah.

Kallon ta Amriya tayi tace, bazan taba zuwa wannan gidan bah, na ruga na yi alkawarin bazan Kara sanya kafana a gida nan bah, kuma dalilin Kalb, bazai sa na karya alkawari na bah,

Khalid yace, Amriya Dan Allah badan Halinsa bah ki taimaka mana, cikin fusata Amriya bazan jee bah, bana sonsa, bana kaunar ganin sa, kuma bazan taba taimaka masa bah, tun wuri kune mi inda dare yayi muku.

Idan mah kuna tunani zanje gidan nan wai da sunan taimako, toh ku maida ita tatsuniya, domin kuwa bazan je bah. Sadiq yace amma fah Amriya, kabir zai iya rasa rayuwar da, idan baki taimaka masa bah.

Amriya tace toh ni mene nawa, ai nauyi bah akaina yake bah, Allah ne sai bayarwa Kuma shine Mai karbe abarsa, Dan aka idan lokacin sa yayi Kaga saidai muce Allah ya jikan sa.

-----------------------------------------
COMMENT & SHARE PLS ???
ALKALAMIN ??
AISHA MUHAMMAD BASHIR ???
(BABY ISHA)

?BISSMILLAHI RAHAMANI RAHIM ?

ALJANAR RUWA CE ??♀???
PAGE 4??9????5??0??
WRITTEN & DIRECTED?? BY AISHA M.B??
-----------------------------------
Dan jimm Ammi tayi, tace Maganar ki hakane Amriya, amma da mutane zasu bi ta halin koh in kulan da ake nuna musu, koh irin rashin mutum cin da akayi musu, da babu Wanda zai Kara taimako a duniya, Dan aka baza kiyi wannan taimakon danshi bah, amma kisa a ranki cewar zaki taimake shine Dan Allah.
Amriya tace hakane amma kuma na ruga danayi alkawari, kuma banason na kasance mai karya alkawari, domin kuwa karya alkawari ba abu bane mai kyau.
Akane Amriya, amma Domin cetan Dan uwa, mu kan iya sadaukar da komai na mu, harda alkawarin mu domin cetan rayuwar sa daga cikin hatsari, nasan da cewar kin tsani kabeer, amma danne zuciyar ki zakiyi, kije ki cece shi, ke kanki zaki yi farin cikin cewar kema kin ceci rai daga mutuwa,

kuma zakiyi tsanan da kike zai tafi, kije Insha Allah komai zaiyi sau?i. Amriya tace naji shikenen zanje, amma har abada tsanan da zai cigaba da kasance wa acikin zuciyata, domin kuwa Shida kansa ya dasa min tsanar sa a zuciya tah. Ku taso mutafi cewar Amriya.
Murna sosai su Khalid sukayi ganin ta amince zata bisu.

Mikewa Amriya tayi , tareda fucewa daga cikin reception din, su Doct khadija na ganin aka ,suka bi bayan ta da sauri, tarar musu napep sadiq yayi, tareda yiwa mai napep din ?watan cen gidan. Hawa napep din sukayi, basu suka isa gida bah, sai wajan la'asar.

Futowa sukayi saga cikin napep din, yayin da sadiq ya biya mai napep din hakkin sa. ?arewa gidan kallo Amriya tayi, Tana mai fadin, ban taba jin koda sau ?aya nayi kewar gidan nan bah, Wanda nasan nayi kewar su a gidan nan sune, Aunty amarya, Dad, da Kuma Grandma.
Doct khadija tace, Allah sarki Amriya suma yan gidan abunda yasa kika ga sun miki aka, saboda idanunwan su ya rufe ne basusan gaskiya bah, amma kinga yanzu, sun fahimce ki, kuma sun gane gaskiyar lamari ,

Sadiq yace kwarai kuwa, a lokacin bamusan menene gaskiya bah, amma yanzu mun gane gaskiya Kuma insha Allah zamu kiyaye gaba, Dan Allah ki tawo mu Shiga please,

Ku shiga ciki zan biyo ku daga baya cewar Amriya, Khalid yace, kin tabbata zaki biyo mu, Amriya ta Bashi amsa da fadin kwarai kuwa zan biyo ku,

Suna jin akan yasa kowannen su Shiga ciki, yayinda suka bar Amriya a wajan.
Share hawayen dake shirin zubo mata tayi, Tana mai fadin, ban yi niyan zuwa gidan nan bah, amma zuciya ta baza ta iya juran ganin sa acikin wannan yanayin bah, dole ne na ceci rayuwar sa badan halin sa bah.

Bangaren su Doct khadija kuwa, suna Shiga ciki suka tarar dasu, Grandma a zazzaune kowa na tofa albarkacin bakin sa akan Mom,

Mamaki ne ya kamasu, ganin Mom a daddaure jikin gado, ga idanuwan ta sun kada, sunyi jajir saboda duka, cikin kidima Doct khadija tace waye yayi mata wannan dukan?

Grandma ta bata amsa da fadin, i tasidi madam, kwarai nice nan, koda magana,
Doct khadija tace babu komai, amma kuma yadda kika yi mata dukan nan, zuciyarta Kara hassala zaiyi, kuma zaku kara tunzura tane.

Grandma tace, bah tunzura bah koma sauya kammani zatayi ta koma shedaniya, bai damen bah, Tunda nidai na daki na jaki a jikin ta, an wuce wajan,

Wallahi akan mah kadan ta gani, shegiya dangin gajeru kawai.

A hassale Mom tace wallahi halima zaki gane kuren ki,

Grandma tace, kutusin karan chan, bala'i, yau akwai gagarumar fad'a a gidan nan, ni kika kira da suna na, koh sanda Maman ki saratu take yawo akan keke, koh nono bata Fara bah, bata isa ta kirani da sunana bah,

toh ki sani, wallahi yau saina ci ubanda yayi tattalin goron auren bikin gyatumar ki.

Tana kaiwa nan ta dauki dorinan ta nufi kan Mom, daga hannun ta tayi sama da zimmar sha?awa Mom bulala, ba zato, bah tsanmani taji an rike mata hannu.

Da sauri ta juya DAN ganin wanda ya dakatar da ita, hatake ta hada ido da Amriya, da sauri ta saki bulalan, tana mai fadin, Allah sarki y'ata Amriya kin dawo kenen, yau ke nake son kiyi wa wannan balamar dukan ja da baki.

Karbar dorinan Amriya tayi daga hannun Grandma, tare da, jefar dashi gefe tace, duk Bakua bukatar wadanan abubuwan, ka mata ai ku barta domin kuwa yadda kike zagin ta, kina rage mata zunubi ne.

Koh Baku yi mata Komai bah, watarana zata gurbi abunda ta shuka. Dad yace kwarai kuwa y'ata, maganar ki gaskiya yace, zamu rabu da ita, amma dan Allah kizo ki duba mijin ki haryanzu bai farfado bah,

Shidin bah mijina bane, ku bazai taba kasancewa mijina bah cewar Amriya.

Tom shikenen Amriya Amma Dan Allah ki taimaki rayuwar shi, cewar Mahaifyar kabeer.

Da sauri Amriya ta juya kamar ta taba jin wannan muryar, juya warta keda wuya suka hada ido da Fatima wato Mahaifiyar Kabeer, da sauri Amriya ta nufi inda take tareda rungume ta tace.

Dama kin futo, yanzu sungane kece asalin mahaifiyar Kabir koh, gaskiya nayi murnan ganin ki, Murmushi Maman kabeer tayi tace kuma ina farin cikin sake ganin ki, yanzu bah wannan bah, ki taimaki rayuwar dana, badan halin sa bah, for my sake kinji.

Girgiza kai Amriya tayi cikin garin ciki tace, ai kodan ke mah, dole na Samar masa da lafiya karki damu Insha Allah zai samu sauk'i.

Tashi tayi tareda nufan inda Kabir ke kwance, kare masa kallo tayi, tana karajin wani sabo tsanan da acikin zuciyar ta.

Daukan hannun sa wanda zoben ta ke sanye a jiki tayi, tareda rike zoben tsamm , yayin da ta rintse idanuwan ta.

Jikin shi ne yafara motsawa kadan kadan, yayin da zuciyar ta ke Duka da sauri sauri, amma duk da akan bata sake shi, saida takai kusan minty ashirin amma bai farfado bah.

Ganin aka yasa ta ta Fara hawaye Hatake hawayen ta ya disa akan zoben, cikin kankanin lokaci zoben yayi aske wanda ya gauraye gabadaya dak'in.

Jikin kabeer ne ya fara karkarwa, ganin akan yasa Amriya rungume shi a jikin ta,

A hankali yafara bude idanuwan sa, inda daga karshe, yayi nasaran bude su baki daya. Sakin shi Amriya tayi tareda kwantar dashi ta mike da niyar tafiya, bah zato taji ya damke hannun ta, yayin da hawaye ke bin gefen fuskan sa.

Hatake taji wani irin kasala Tareda jin tausayin shi ya Kama ta, wafce hannun ta tayi daga nasa, da sauri su Dad suka nufi inda yake a kwance, daga shi Dad yayi tareda rungume sa yace, kana lafiya dai koh Kabir,

Nufan hanyar waje Amriya tayi ba tareda ta Bari kowa ya ganta bah, Kallon su tayi gabadaya, tareda sakin murmushi daga bisani ta fuce daga gidan .

Doct khadija ce tace, Kabir Kaga asalin mahaifiyar ka nan, itace Maman ka, itace ta kawo ka wannan duniyar,

Kallon mahaifyar sa, Kabir yayi hawaye na bin kan kuncin shi yace "Mama", jin akan yasa Fatima fashe wa da kuka, rungume Kabir tayi tana mai fadin, ka yafe min dana, laifina ne, ban taba bayyana a gareka na nuna maka cewar ni mahaifiyar kace, ka gafarce ni.

Kabir yace babu abunda kika min Umma, nine ya ka mata na nemi yafiyar ki, dan Allah ki yafe min, Fatima tace na yafe maka duniya da lahira Kabir, Allah yayi wa rayuwar ka albarka.

Bangaren Mom kuwa ganin kowa hankalin shi nakan Kabir yasa ta Fara yunkurin kunce kanta, inda a karshe tayi nasaran kunce zaren da suka daure ta dashi.

Mikewa tayi da sauri, ta Kare musu kallo, sannan ta fasa wani mahaukacin dariya.

A firgice gabadayan su suka waigo, tareda kura mata ido, Mom tace wato ni zaku daure koh, you saina kashe ku baki daya,

Tashi Kabir yayi cikin kasala yace, menene muka aikata miki Mom meyasa kike haddaban rayuwar mu, indai saboda kudi ne koh dukiya, gasunan duk ki dibi na iba ki bar na bari, amma meyasa kike fadin Lallai sai kin kashe mu, ki barmu da bakin ciki da kuncin da kika sanya mu mana, iya akan bai wadace ki bane,

Mom ta bashi amsa da fadin kwarai kuwa akan bai ishe ni bah, Nadira tace Mom meyasa kike aka, ga y'ay'an kinan suma kin hada dasu, duk mene aka, menene silan aka, Grandma tace kwarai kuwa, ki fada mana wane abu aka yi miki da kike son daukar fansa?

Mom tace Yunusa yusuf wato mijin ki, shine silan komai da ke faruwa daku,

Grandma tace yanzu mijin nawa mah saboda Allah da annabi baza a bar ruhin sa yasamu salama bah, sai anyi masa sharri,
Tabbas nasan karya kike bawani mijina da ya miki wani abu. Dakatar da Grandma Kabir yayi da fadin ki bari muji menene yafaru, maida Kallon ta kan Mom yayi, yana mai fadin, ki fada mana abunda ya faru.

Dad yace dakata tukunan, dole Sai Maryam da Habib suna nan domin banason ayi komai a bayan idonsu, yanzu ku kiramin Habib da Kuma Maryam yanzu, suzo, daukan wayar sa, Sadiq yayi tareda Kiran Abban sa wato Habib, sannan shima Khalid ya dau waya Tareda kira Mahaifyar su Mami.

Bayan wasu hawanni kowannen su ya hallara .
Dad yace toh Alhmadulillah kowa yana nan, yanzu zaki iya magana

Kallon su Mom tayi tace.
SHEKARU BAYA DA SUKA GABA TAH.

Mahaifina da Kuma mahafin ku, wajen bussiness dinsu daya, Kuma sudin sun kasance babban abokai nee. Komai tare suke yi, amma mahaifin ku yafi mahaifina kudi nesa bah kusa bah, duda aka kakan ku bai taba nuna wai shidin wani ne.

Hana aka sai suka samu sab'ani Shida babana, akan wani maganar kudin da suka samu wajan Millions of Naira, sai mahaifin ku ya yanke cewar za'a kai gidan marayu, Wanda babana tsam bai amince da akan bah domin shi a ganin shi da akai kudin gidan marayu gwanda su Kara wa kansu jari, shikuwa kakan ku yace, indai rabuwa ce saidai su rabu amma bazai taba bin maganar sa bah.
Aka kuwa akayi yayinda kowannen su yayi hanyar sa, babu wanda yakara kula wani acikin ku.

Hana aka karayar arziki ta samu babana, yayinda muka talauce, koh gishiri Bamua samu mu siya saboda tsanannin talauci, a lokacin mahaifina ya yanke cewar zai Shiga qungiyar asiri domin yayi kudi ya zama sananne wanda babu kamar sa.

A lokacin yaje yayi joining qungiyan asiri, amma a lokacin aka gargadi mahaifina da cewa
kada ta kuskure ya fadawa kowa, Kuma dole ya kawo babban abokin sa wanda yake matukar kauna, sannan yayi sadaukar wa da jinin sa.

Mahaifina baiyi jayayya da akan bah, ya yarda da umarnin da aka bashi. Bayan wasu kwanaki. Mahaifina yayi kudi, dukiya suka habbaka, yazama sananne wanda babu kamarshi, haryazo yafi mahafinku kudi.

Hana aka, babana ya nemi suyi sulhu da mahaifin ku, shikuwa mahaifin ku, ya hakura suka koma normal yadda suke a da.

Sosai suka kara kaunatar junan su, inda mahaifina ya yanke cewar zai fada wa mahafin ku komai da komai, abunda yasa arzikin shi yayi yawa...

Hana tsaka da aka, baba na, ya nemi su fita da Mahafin ku, babu jayayya Mahaifin ku ya amince da akan, inda baba na ya kaishi Chan cikin jeji, sannan ya Kalli abokin nasa ya ceda shi,

Tabbas Kai abokine na kwarai, Amman inason na fada maka wani sirri na, Kuma Dan Allah inason ka adanamin, karka Bari duniya ta sani, mahafinku ya ceda baba na,

Menene sirrin? Meyasa ka kawo ni daji? Me kake shirin aikata wa?

Hatake baba na ya kira sauran yan qungiyan, lokacin da mahafin ku ya gansu, yayi matukar tsorata sosai,

A lokacin babana ya sanar dashi komai da komai, inda mahaifin ku yak'i amince a sadaukar da jinin sa inda a karshe yace saiya tona masa asiri, duniya tasan cewar shidin maciyi amana ne,

Shi Kuma a lokacin mahaifina ya Shiga bashi hakuri, Kuma yayi masa alkawarin cewar zai bashi kudade Duk abunda ya keso, amma Dan Allah kada ya tona asirin shi a idanun duniya, Hatake mahaifin ku ya kira police officers, suka zo suka tafi da baba na,

Shi Kuma mahaifin ku ya kwashi kudaden baba na, ya kaiwa su police, inda police din suka raba kudin a tsanin su.

Yayin da Baba na ya tafi magarkama na wajan shekaru goma, bayan ya futo, yaga komai nasa ya yi kasa, kudaden da ya Tara da duniyan da yake dasu duk babu, akan ya sashi cikin damuwa har yasamu ciwon zuciya,

yana cikin kakarin mutuwa ya kirani, ya sanar dani duk abunda ya faru, hawaye ne suka Fara bin kan kuncin Mom, sannan ta cigaba da fadin,

Baba na yace na daukan masa alkawarin cewar zan daukar masa fansa, bazan taba rabuwa da ku bah, ni kuwa na daukan masa alkawarin cewar saina ga bayan ku baki daya, bazan bar koda kud'a wanda nasan ya futo daga gidan nan bah, saina raba ku da farin ciki, saina sanya ku cikin kunci da bakin ciki,

Ina kaiwanan, Baba na ya tashi da zummar yaje zai kaini na Shiga qungiyar asiri, rike hannu na yayi yayin da muka futa wajen layin,

Ban hankara bah, naji han fara je fawa baba na Duwatsuna, da Kuma rodi, kuka a lokacin nai tayi, yayin da na dunga rokan su, subar min mahaifina, sannan ta Kalli Amina da Kuma mahaifiya ta, wacce ke a tsaye basu tanka wa mutanen bah,

A lokacin raina yayi matukar baci, ganin mahaifiya ta da yar uwata, basu tanka wa mutanen bah, a lokacin naji tsanan kowannen su a raina,

Aka suka cigaba da jifan Baba na har saida numfashi ya futa daga jikin shi, sannan suka barshi a wajan, sukayi tafiyar su.

Babu wanda ya taimaka min, ni da kaina na dauki gawar mahaifina sannan ta kaishi makabartar yayin da yan qungiyan asiri suka taimaka min, muka bunne sa,

Tunda ga lokacin na Shiga cikin yan qungiyan asiri, yayin da jini na ke tafarfasa, fansa kawai take son dauka, hana aka na Fara bibiyar mahafin ku, ban daina bibiyar sa bah, har saida naga na kawar da rayuwar sa, bayan nan kuma, naje gidan mu sannan na lashe mahaifya ta,

Itama Amina zan kashe ta, amma abunda yasa ban kashe ta bah tana gidan mijin ta a lokacin, yasa na barta da ranta amma duda akan bai hanani bibiyar rayuwar ta bah.

daga nan kuma na shigo cikin ahalin nan a matsayin mata, na saka Y'aya na Suleiman ya bani kai a matsayin mata, Kuma na shigo gidan nan domin daukar fansa .

Kuma bazan dakata bah, har sai na cikawa mahaifina burin shi na karshe kafun na sarara Wannan shine .

Ajiyan zuciya gabadayan su sukayi, inda Mami ta fara magana kamar aka, toh mahaifin ki ya mutu, amma ai bah mahafin mu ne ya kashe shi bah,

Kwarai kuwa mahafin ku ne ya kashe baba na, da mahafin ku bai fada wa duniya wanene baba na bah, da haryanzu nasan yana raye, Kuma na ruga dana daukan wa Baba na alkawarin cewar, Har jikokin Yunusa yusuf, bazan bari bah, Domin har su zan hada na kashe. Kuma shine zai sa a kara mun matsayi acikin kungiya.

Doct khadija tace, amma meyasa ni kika kashe min dana, Kuma kika kashe yarinyar Amina. Kuma kinsan da cewar Amina batasan cewar ke yar uwarta bane Domin rabonda ku hadu yakai,

kusan shekaru talatin da yan Kai, amma ke kingane ita din yar uwarki ce, yayinda ita bata sani bah,

Mom ta bawa Doct khadija amsa da fadin, ni ban kashe danki bah domin kuwa danki yana raye bai mutu bah, zaro ido Doct khadija yayin da jikin ta yafara karkarwa tace yana ina Dan Allah ki kiramun dana, inason na ganshi.

Mom tace zan fada miki Amman kafun nan, ki kiramun yar uwata Amina da Kuma danta da mijin ta yanzun nan,

Cikin rawar jiki, Doct khadija ta dauki wayar ta, Tareda dialling number Ammi wato Amina, ringing biyu Ammi ta dauka Tareda karawa a kunnen ta tace, hello Salamu alaiki, Amsa sallamar Doct khadija tayi tace,

Yar uwa, Dan Allah keda mijin ki da Kuma danki Duk kuzo yanzun nan, Ammi tace, amma dai lafiya koh, Doct khadija tace lafiya ce ta kawo akan karki damu babu komai kuzo kawai,

Tom shikenen gamu nan zuwa gidan su Kabir din, katse wayan Ammi tayi, yayin da ta Sanar da Abban yusuf komai da komai, sannan ta samu yusuf wanda yasamu sauk'in jikin shi sosai, tace masa ya shirya zasu je gidan su Kabir, bah jayayya, yusuf yace Tom shikenen,

Cikin kankanin lokaci suka isa gidan su Kabir, yayin da Amar ya kaisu dak'in da gabadayansu suke, Shiga ciki sukayi sallama rike a bakin su.

Amsawa su Grandma sukayi, guri su Ammi suka samu sannan suka zauna, Abban yusuf yace lafiya dai koh naga kowa ya taru hanan, Aunty amarya tace lafiya lau wallahi, Dama wani Dan karamin issue ne ake tattauna wa akai.

Kallon Ammi Aunty Amarya tayi tace shin Maman Yusuf kinsan wannan matar ta fada Tareda nuna Mom, Kallon Mom Ammi tayi tace, Aa ban Santa bah, amma nasan cewar itace Maman Kabir, Kuma tana min Kama da yar uwata hassana.

Doct khadija tace idan na fada miki wani abu zaki yarda?, Ammi tace me zai Hana, zan yarda mana,

Doct khadija tace, toh dai wannan da kike gani itadin yar uwarki ce wato hassanan ki, wacce kanku ya rabu akan Abban yusuf,

Da sauri Ammi ta Mike, Tareda Kallon Mom tace, da gaske kece hassana ta? Mom ta bata amsa da fadin kwarai kuwa nice nan, nina hanaki sukuni a gidan auren ki, na saka kika rasa yarki wacce kike mugun qauna wato Sabreena,

Kallon ta Ammi tayi a hassale tace, dama kece, ina kika kaimin y'ata, bayan kinsan cewar ita kadai na haifa, wato dana kaita asibity lokacin da Asman ta ya tashi ke kika kashe ta koh, Meyasa zaki aikata min aka bayan kisan ita kadai gareni.

da kallon mamaki Yusuf ya Kalli Ammi, sannan yace, Ammi ni din fah, ni bah danki bane.

Kallon shi Ammi tayi tace kwarai kuwa kai bah dana bane, Kai adopted child ne, zama Ammi tayi hawaye na bin kan kuncin ta, tace kayi hakuri nayi boye maka gaskiya na tsawon shekaru, tabbas Kai bah dan mu bane, sabreen itace kadai yar dana haifa.

Hatake kan Yusuf yayi mugun saramai, dafa kanshi yayi, yafara karanta adu'oin rage radadi, dago kai yayi sannan ya tambayi Ammi yace, toh Wacece mahafiya ta,

Kafun Ammi tayi Magana, Mom tace khadija itace mahaifiyar ka, zaro ido gabadayansu sukayi, cikeda mamakin kalaman Mom, Ammi ta kalle ta tace, khadija Kuma! taya kika san khadija ce mamar sa,

Mom tace saboda ni da kaina na dauki Yusuf sannan na hajiye shi a kofan gidan ku, a lokacin Kuma na buya, bayan kun dawo daga asibityn da kuka je akan rashin haihuwa da kike, kuka ganshi sannan kika yanke cewar ku dauke shi.

Kallon Doct khadija Yusuf yayi yace, kenen Doct khadija itace mahaifiya ta, akan bazai taba yuhuwa bah, da sauri doct khadija ta Mike, sannan ta isa inda yusuf ke tsaye, ta Kalli bayan wuyan sa ta tabo dake wuyan sakk irin na wancan,

Sannan tace, tabbas kaine dana, kaine dana, Dama, zan sake Ada ido dakai a duniya, rungume ta yusuf yayi, yace kiyi hakuri umma tun kwanakin nan bansan cewar ke din mahaifya ta bace, sai yau, na miki alkawarin zan rike ki hannu bibbiyu, bazan taba rabuwa dake bah.

Sosai Ammi tayi murnan ganin asalin mahaifiyar Yusuf, Abba wato mijin Ammi ne ya katse su da fadin, toh ita y'ata Sabreen Tana ina? Ina kika kaita,

Dariya Mom ta kwashe dashi Tareda fadin kuna Tareda yarku, amma Baku san itace yarku bah, Dad yace bah abunda aka tambaye ki kenen bah, tambaya itace, ina yarsu take Kuma wacece yar su ,

Mom tace bah kowa bace yar su, illa "Amriya, tabbas Amriya itace yar ki.

????????
COMMENT & SHARE
PLS ???

ALKALAMIN ??
AISHA M.B (Baby isha )
???

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE91

?BISMILLAHI RAHAMANI RAHIM ?
ALJANAR RUWA CE ??♀???♀?? PAGE 5??0????5??1??
WRITTEN & DIRECTED ?? BY AISHA M.B??
-----------------------------------------
Zaro idanuwa gabadyansu sukayi, suka hada baki wajan fadin What!, jiri ne ya fara daukan Ammi, da sauri tayi saurin dafe kanta, Tana mai fadin Amriya, itace sabreen dita, kenen itace y'ata, why? Meyasa tsawon wannan lokacin ban gano cewar ke y'ata bace, ta karashe maganar tareda fashe wa da kuka .

Mamaki ne ya Kama kowannen su na dak'in, Nadira ce tayi karfin halin fadin, idan Amriya yarki ce, that means itadin mutum ce, toh tayaya ta zama ALJANAR RUWA How?

Dariya Mom ta kwashe dashi, tareda fadin nice nan, na maida ta ALJANAR RUWA, Kuma ni kadai ce nasan a inda zata samu maganin waraka ta, ta koma asalin mutum,

Amma bazan fada bah domin nice nan zan ga bayan tah.

A fusace Ammi ta Mike tareda nufan inda Mom take tareda shake ta tace, kin rabani da y'ata na tsawon shekaru, akan bai ishe ki bah, meyasa kike son daukar rayuwar ta?

Kin ruga kin maida ta ALJANAR RUWA, akan bai wada ce ki bah, menene ta tare miki da kike son ganin bayan tah.

A fusa ce, Mom ta Kalli Ammi tace, tambaya ta kike me ta taremun, toh bude kunnuwan ki kiji, yarinyar ki ta tare min abubuwa da dama, idan bakusani bah toh yau kusani,

Ita ta hanani kashe ku tun wuri, ita take Kare Kabir a koda yaushe, lokacin birthday Nadira, ni na saka wa kabir guba, sannan ita Kuma Amriya ta dauka tasha, akan ya bata min rai sosai, banso akan bah, naso ace Kabir ne yasha sannan ya mutu,

Amma ganin akan danayi yasa na kira police domin su dora masa laifi akansa, amma still yet saida ta cece shi a wajan Police, ta hana aka ki tafiya dashi.

Babu abunda banyi bah, dan ganin na kawar da Kabir d'aga doron duniya, Amma wannan yarinyar Amriya ta Hana ni, ita take dakatar dani, nayi yinkurin kashe ku amma a koda yaushe ta kasance tana taimaka muku,

kowane shiri na toh saita san yadda tayi ta wargaza min plan's dina, now tell me, bata tare mun abubuwa bah?.

Hawaye ne ya fara bin kuncin kowannen su na dak'in, Mami ce tayi karfin halin fadin, Allah sarki Amriya, yau gashi dai gaskiya tayi halin ta, hakika kedin mace ce ta gari, duk Wanda yayi nasaran samu Mace irin ki toh hakika wannan mutum, zai kasance a koda yaushe Mai sa'a.

dafa kanshi Kabir yayi, yayin da yake jin zuciyar shi na masa zafi da kuna, tareda fadin, ki gafarce ni Amiriya, tabbas nayi dana sani, a koda yaushe kina yawan fadamin cewar, watarana saina yi dana sani, kuma saina san mahimman cin kasantuwar ki a rayuwa ta.

Tabbas maganar ki ya zama gaskiya, dan Allah ki taimaka ki yafe min yana kaiwa nan, ya mike tsaye, tareda fuskan tarsu yace, zanje na nemo matata, zan nemi gafarar ta, Kuma sannan na nemi ta dawo cikin rayuwa ta bah, domin kuwa in har Amriya bata kasance a rayuwa ta bah, toh zama na a duniyar nan ya Kare.

Tashi Ammi tayi tace, kwata kuwa Kabir nasan bazata wuce gida na bah, amma bazan bar gidan nan bah, har sai Karima ta fadamin tayaya ta maida y'ata ALJANAR RUWA, Kuma menene dalilin ta na yin akan.

Wannan shine sila, Mom ta fada tana mai nuna abban yusuf, Kallon ta Abban yusuf yayi mamaki bayyane a fuskan shi yace ni Kuma! , ta yaya nazama nine sila?

Mom tace kwarai kuwa kaine sila, Amina baki taba fada masa irin tsakanin sonda nake mishi bah, sai a lokacin Ammi ta tuna da irin tsakanin sonda Karima ta nuna wa habib shekarun baya da suka wuce,

Kallon ta Ammi tayi tace, Amma ke baki ji kunya bah, mijin yar uwarki kike so, duk mazan duniyar nan baki gansu bah, sai mijin yar uwar ki, Anya ke jini na ce kuwa, hanya tare aka haife mu, ki rasa da abunda zaki sakamin sai da wannan abun.

Toh fada mana tayaya kika mayar da Amriya ALJANAR RUWA?......

shekaru baya da suka gaba ta.
ganin auren ki da Habib, akan yasa ni cikin bakin ciki, ya sanya ni kunci wanda akan ya kusan sanadiyar rasa rayuwa ta,

Ganin bazan iya jure ganin ki, kina farin ciki, ni kuma, ina bakin ciki, akan yasa na na dau alwashin cewa saina ga bayan ki, a lokacin na tafi wajan shugaba mu na Qungiyar devilish. nace dashi inason na kawar dake daga duniya,

Inason ya zamto cewar ni kadai ce zan kasan ce a rayuwar Habib, Kuma nace da shugaban mu, banason ki haihu a gidan auren ki, inason ki kasance a koda yaushe kina kunci.

Shugaba yace min, wannan abu mai sauk'i ne, amma kada nayi gaggawa, na bari lokaci zaizo da zanyi akan, yanzu koh yayi bazai shafe ki bah, domin kuwa a koda yaushe Amina tana yawaita adua tsari daga mutum koh aljan, bazai yu na kusan shi inda take da mugun nufi baht, bazamu iya tura mata aljanu bah domin kuwa akwai kariya a jikin tah.

Amma zamu iya Hana ta haihuwa, saina ce mashi shikenen, mu Hana ta haihuwa, aka kuwa akayi, Amina bata taba batan wata, bare Asa ran tana da ciki bah.

Lokacin ne Kuma na dauke dan khadija, sannan na ajiye shi a gaban gidan su, saboda kada su je suce a musu Adu'oin samun haihuwa,

A gaban idona a lokacin naga kun dauke shi, sannan kuka dunga rainan shi kamar danda kuka haifa.

Bayan wasu shekaru kawai naji labarin cewar kina dauke da juna biyu, hankali na bah karamin tashi yayi bah, babu bata lokaci na wuce cikin qungiya, sannan na sanar da shugaban mu halin da ake ciki.

Shi kuwa ya tabbatar min da cewa, baza ki taba haifo wannan yarinya ta cikin ki bah, yana kaiwa nan ya dauki madubin tsari, da muke amfani dashi wajan kashe mutane da mukeson kashe wa,

A lokacin madubin tsafin, ya hasko Amina a ciki tana kwance akan bed, shugaba na ganin akan ya nemi da daya daga cikin yan qungiyan ya kashe yarinyar dake cikin Amina,

Aka kuwa akayi, daya daga cikin mutanen ya dauki sanda na tsafi, sannan ya saita daidai cikin Amina, ya fara magganganu, cikeda mamakin mu kuwa, muka ga ya kwalla uban ihuu, yayin da ancin shi da bakin shi ya fara zubda jini, sannan ya fadi a kasa yafara shure shure, yana kakarin mutuwa, daga bisani Kuma ya mutu a wajan.

Hankalin kowa na kungiya bah karamin tashi yayi bah, Hatake shugaban mu, ya Kalli cikin dake jikin Amina, sannan ya ce dani, tabbas kawar da wannan cikin na jikin ta abune Mai wahala, indai har munason mu kasance a raye toh tabbas sai mun bar cikin nan,

dole mu barta ta haifo yarinya, domin kuwa alamu ya nuna cewar yarinyar yar baiwa ce. Kuma jinin yarinyar nan zaisa karfin mu, da ikon mu ya karu, ya ninka na da, sai yace dani mu hakura ta haifo yarinyar.

Jin akan yasa raina yakai kololuwar bacci, sannan nace Allah ya kawo ta duniya, in har da raina toh bazan taba barin yarinyar nan bah.

Bayan wasu watanni, Allah ya sauk'i Amina, ta haifo santaleliyar yarta kyakyawa, son kowa, kin wanda ya rasa. A lokacin danaji labarin ta haifi yarinyar, yasa na fara shirye shiryen Yanda zan dauke yarinyar daga gare ta,

Aka kuwa akayi, domin kuwa na hallaci Sunan Amriya, yayinda naga duk fuskokin ku lullube yake da farin ciki da annashuwa.

Akan bah Karamin Kara tunzura ni yayi
bah, a lokacin nayi kokarin dauke Amriya, amma Allah zai nufa bah, akan yasa naji bah dadi, amma ta bangare guda naji dadi, saboda nayi nasaran bata wani kwayoyin cuta tasha,

Bayan watanni, kuwa ta Fara cuta, Tana rashin lafiya wanda ya tsanan ta, har kuka kaita asibity, ni kuma naje asibityn, sannan na dauke yarinyar, na mu sanya Amriya da wata yarinyar, na sanya mata kamanni Amriya sakk, sannan nayi fuce wa ta daga asibityn.

Bayan fuce wa ta, nurses suka gano cewar yarinyar da na musanya ta mutu, sannan suka zo suka fada muku cewar yarku ta mutu, hankalin ku bah karamin tashi yayi bah, yayin da aka Baku gawar ta, kuka suturta ta, sannan kuka kaita gidan ta na gaskiya.

Ban nufi koh ina da Sabreen wato Amriya
Bah, sai fadar mu na cultism. Bayan na kaita, na hajiye ta agaban gunkiyar mu, a lokacin shugaba ya dauki takobi, sannan ya nufi Amiriya da zummar kashe ta, lokaci daya muka ga ya kurma ihuu, sai ji mukayi ya naku da kasa,.

Cikin fargaba da tsoro na mikar dashi, sannan nace masa, yanzu me zamu yi mu kawar da yarinyar, a lokacin yake Sanar dani cewar, me kashe yarinyar nan saiya shirya, babu wani mutum koh aljan, da ya isa nufan inda take da zimmar cutar wa, in kuma mutum yayi kokarin yin akan toh shi zai bar duniya bah ita bah.

Jin akan danayi yasa gaba na ya fadi, sa'anan nace dashi babu wata hanyar da zamu bi mu nesan ta yarinyar da mahaifiyar tah, shugaba yace mun akwai hanya guda daya, saidai idan sauya mata halitta zamu yi mu turata Chan cikin wasu jinsi daban, sannan shine burin na zai cika.

A lokacin nace ayi duk abunda ya kama ta, indai har zata Nisan ci inda Amina take babu damuwa, a lokacin Shugaba na, yafara wasu tsafa ce tsafa ce, inda a karshe yayi nasaran maida ta ALJANAR RUWA.

Cikin tsoro da fargaba na kalli Amriya sannan nace yanzu ya zamu yi da yarinyar, shugaba ya bani amsa da cewar, na dauki yarinyar na kaita nesa Chan katuwar teku inda nasan bazasu Kara haduwa da mamar taba, aka kuwa akayi, na dauki Sabreen na kaita tekun garin Lagos sannan na jefa tah aciki.

A lokacin nake ta murna cewar burina ya kusan cika, bayan komawa na cikin kungiya, na tarar shugaba ya ruga daya mutu, dalilin yinkurin kashe Sabreen da yayi.

Ganin akan yasa, nasa aka kwashi gawar sa aka yi sadaukar wa dashi, sannan aka nada ni a matsayin shugaba na kungiya.

Bayan wasu lokacin, na dunga mafarkai munana, wanda ake son daukan raina acikin mafarkin, ganin akan yasa nayi hanzarin nufa kungiya, Sannan nasamu mahaifa na mace, naci daga nan ban kar mafarkai bah. Kuma na bar farautar rayuwar Amina, nayi concentrating akan yadda zan ga bayan wannan ahalin.

Hankali na, bai tashi bah, sai lokacin da naga Sabreen ido da ido a wajan kungiya, ta saka mayafi ta rufe fuskan ta sannan tayi mana gargadin cewa kada mukara bibiyar rayuwar Kabeer, hankali na bah karamin tashi yayi bah, ganin cewar tabbas ta dawo duniyar tah, Kuma nasan da cewar itace,

A lokacin na Kuma tada makaman yak'i na, dole na kashe mutanen gidan nan, domin na cimma burina da Kuma na mahaifina. Kuma maganin dawo da ita asalin Mutum ni kadai ce nasan shi.

Wannan shine.

Innalillahi wa innahilahi rajihun! Innalillahi wa innahilahi rajihun, la'ila a'illa anta subha'anaka inninkun tun minan zalumin, Allahumma ajirni fi musibati.

Abunda kowannen su ke maimai tawa kenen. Hawaye mai zafi ne ya farabin kuncin Ammi, Kallon Mom tayi cikeda takaici da bakin ciki tace, naji kunyar kiran ki yar uwata, yanzu ke kin rabani da farin ciki na, kina walwalar ki, bakya jin cewa fah akwai hakkin wasu akan ki.

Wannan wace iriyar bushashiyar zuciya ce, toh ni yanzu bah wannan bah ki fadamin inda zansamu magani y'ata ta warke please na roke ki,

Kwashe wa Mom tayi da dariya tace, bansani bah, bani ya Kama ta ku tsaga ku kalla bah, yanzu Kuje ku nemi inda Sabreena yarki take tukunan,

Da sauri gabadayansu suka mike, yayin da su khalid suka samu suka daddaure Mom. Daga bisani suka fuce daga dak'in.

Daukar Motoci sukayi, yayin da sukayi bribing din body guards din da su barsu su futa, ganin kudade yasa, yan kungiyan asirin bude musu kofa suka fuce daga gidan,

Bayan fucewar su, Mom ta kunce kanta, sannan ta Kalli zoben Amriya da tayi nasaran zare shi daga hannun Kabir ta saki murmushi, daukar wayar ta tayi, ta kira Zainab, cikin kankanin lokaci zainab ta Iso gidan, yayin da Mom tayi mata rada a kunne, ni koh nace idan tayi tsami aji, daga bisani naga ta tattara gabadaya yan kungiyan, suka fuce daga gidan.

Direct gidan Ammi suka nufa baki daya, yayin da masu gadi suka bude musu kofa, suka Shiga ciki,

Futowa gabadaya sukayi daga cikin motocin, suka nufi cikin gidan.

Shiga parlour sukayi, cikin rashin sa'a kuwa su kaga Amriya bata gidan, ta karda Salma ta gani akan table, dauka tayi Tareda mikawa Mami, karba Mami tayi sannan ta Fara karanta wa kamar aka.

Assalamu alaiki Ammi, na rubuta wannan Sakon ne badan komai bah, saidan na gode miki akan abubuwa na alhery da kika aikata min, hakika kedin uwa ce ta gari, bansan da wane kalma zanyi amfani wajan gode miki bah, naso ace na sami irin ki amatsayin mahafiya, amma abunda Allah ya kaddara, babu wani Dan Adam da ya isa ya chanza shi, Dan aka ina godiya a gareku baki daya, ni zan tafi, zanje na cigaba da lallaba rayuwa ta, zanje na hafi danda ke cikina, a wani gurin daban, idan kuma lokacin mutuwa na yayi na mutu domin kuwa ina da tabbacin cewa tunda babu wannan zoben mutuwa zanyi, zanyi kewar ku baki daya, Dan Allah ki fadawa ahalin su Mom cewa ina matukar sonsu sosai, bazan taba mantawa da hallaci da kulawa da suka nuna min bah, ni na tafi kenen, bazaku Kara ganina bah ar abada, na koma duniya ta, duda sanin cewa ni ALJANAR RUWA CE, akan baisa kun gujeni bah, tabbas ku mutanen kirki ne, Kuma kiyi wa diyar ki Adua na sauka lafiya. nazo duniyar ku, na dandani dadin ta da Kuma rashin dadin ta, nasan yadda kuke mu'amala da mutane dakuma dabbobi, tabbas zanyi kewar ku sosai da Kuma duniyar ku, ina son ki Mika gaisuwa ta ga ahalin kalb, kice ina matukar sonsu, ban taba jin koda sau daya soyayya su ta zama kiyayya a zuciya ta bah. Ina fatan zaki karanta wannan sakon.
Na barku lafiya.

Zama gabadyaansu sukayi, yayin da gabadaya suka nemi kuka suka rasa. Rike kanshi Kabir yayi, yana ji kamar ya mari kanshi. Kallon Ammi yayi yace, kenen dama, Amriya tana da cikin dana bansani bah.

Share hawayenta Ammi tayi tace, kwarai kuwa Tana da juna biyu, Kuma danka ne.

??♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀???♀?

Comment & share
pls???
ALKALAMIN ??
AISHA M.B ???
(Baby isha)

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JYYV16dbYaX1dykLX7EE91

?BISSMILLAHI RAHAMANI RAHIM?
ALJANAR RUWA CE ??♀???
PAGE 5??1????5??2??
WRITTEN & DIRECTED ?? BY A'ISHA M.B??

-----------------------------------------
Amma wai shin meyasa baka son Amriya?, shin bata kai a sota bane?, meyasa a Koda yau she kana cikin kuntata mata,

Kabir ya bata amsa da fadin, Ammi bawai sonta ne bana yi bah, kawai dan inada wata a raina ne shiyasa, Nadirah tace Amma yahya ita ce dai wacce kake so, wacce ta cece ka acikin teku, tabbas itace,

Kuma wannan zoben na tane, bana kowa bah, so da dama tayi ?o?arin sanar dakai amma tsam baka fahimta, kuma yanzu saura wasu watanni ka?an kafin ta mutu,indai har bata samu wannan zoben bah, toh tabbas mutuwa zata yi.

Zama kabir yayi, yana jin zuciyar sa na masa kuna da radadi, dafa zuciyar shi yayi,yana mai fadin, ba zata mutu ts barni bah, insha Allahu babu abunda zai faru da ita, na aikata kuskure, tabbas na aikata babban kuskure, dole na nemo tah, domin ce to rayuwar ?i, nima na yarda dana bada rayuwa ta,indai zan ceci taki rayuwar.

Yana kaiwa nan ya fice daga parlour, su Sadiq na ganin akan,yasa suka bi bayan sa da sauri, shiga mota sukayi gaba-daya, yayin da "Kabeer ya tada mota, suka fice daga gidan.

Saida su Kabeer, suka kewaye garin Abuja ba?i daya, amma basu ga Amriya bah.

Kallon Kabir Sadiq yayi, yana mai fadin, Kabeer me zai hana muje gidan radio mu sanar da batan tah, Khalid ya ce, kwarai kuwa Kabir, maganar Sadiq gaskiya ce, ya kama ta muje gidan radio ka sanar da batar ta, tunda dai itadin matar kace.

Shikenen Kabeer ya fada, tare da fadin muje gidan radion, bah bata lokaci suka nufi hanyar gidan radio.

Cikin kankanin lokaci suka isa wajan, fitowa suka yi baki ?aya yayin da suka shiga wajan

Gaisawa da mutane wajan suka yi, inda Kabir ke sanar musu cewa, wani muhimmin abune ya kawo su, Kuma suna bu?atar su sanar da mutane.

Tashi ?an jaridan yayi, tare da bawa Kabir kujera ya zauna, zama Kabir ya yi, tare da ri?e speaker ya fara magana kamar aka.

Assalamu alaikum jama'a wannan garin, barkan ku da wannan lokacin, fatan kowa na cikin koshin lafiya, sunana Kabir Muhammad yunusa, kamar yadda mutane suka sani, nine mai Company fishes production na Abuja, nazo wannan gidan radio ne badan komai bah,sai ?an na sanar da wata muhimmiyar magana, hana cigiyar wata budurwa wacce a kalla zata kai shekaru ashirin da haihuwa, kuma duk wanda yayi ?o?arin gano inda take yana da kyautar million ?aya, za'a buga hotunan ta yanzu kuma inason a ya?a, zan hajiye number na, duk wanda ya ganta sai ya kirani, 07045421451, wannan shine number na.
Ina fatan za'a ganta.

Kabeer na hajiye speaker,wata kira ta shigo wayar sa, cikin rawar jiki Kabir ya yi saurin ?aukan wayar, ?aga wa yayi, tare da fadin Hello!, daga ?ayan ?angare naji ance, shin ina magana da Kabir",

Kabir ya bashi amsa da cewar, eh nine, waye akan layi? daga ?ayan ?angare akace sunana Sani, tambaya ce a ba?i na akan yasa na kira ka, bawai naga budurwar bah.

Kabir yace, ina jin ka fada min, Sani yace, shin budurwar da kake nema itadin wacece a wajan kah?, mene ne ha?in ka da ita?,

Murmushi Kabir yayi, yace zan fa?a muku wacece ita, kashe wayan yayi, ya saita ba?in sa dai-dai wajan speaker yace, itadin matata ce kuma kan wata, Kuma tabbas itadin rayuwa tace, idan har bangan ta bah, bana tunanin zan iya cigaba da kasan cewa a raye.

Share hawaye da ke ?o?arin zubo masa yayi, yace tabbas nasan da cewa kina jina, na ro?eki, ki dawo rayuwa ta, ba zan taba iya rayuwa in babu ke.

Kin yi min komai a rayuwa, inason nima na saka miki da abinda kika aikata a gareni, Amriya ki sani cewa ba iya sonki ka?ai nake bah, zan iya bada rayuwa ta, saboda ke da kuma ?ana na cikin ki, mahaifyar ki tana bukatar ki a kusa da ita, ki taimaka ki dawo, zamu nuna miki kulawa wacce ba?i ta?a tsammani bah. Ina fatan zaki dawo gare mu.. Yana kaiwa nan, ya kashe speaker, sannan ya fuce daga wajan da sauri, tareda nufan cikin mota,

Kuka ne yaci karfin sa, saida yayi mai isarsa,ganin su Khalid suna nufo inda yake,yasa yayi saurin share hawayen sa, tareda goge fuskan shi da handkerchief.

Shi ga cikin motan suka yi, suka tarar da Kabeer yayi jugum, hajiyan zuciya suka yi, Sadiq yayi karfin halin fa?in, Kabir why are thinking?, kwanakin baya idan ba zaka manta bah,me muka ce maka?

Lokacin da kake wulakanta ta, kayi mata duk abunda ranka yaso, duka, zagi, cin mutun cin, babu Wanda baka yiwa Amriya bah, so now tell me are you not regretting of all what you did to that innocent girl, who's suffering now between you and Amriya?.

Tagumi Kabir yayi, yayin da ya nemi kuka ya rasa, cikin kasala ya motsa leben sa, tareda fadin, lokacin rashin sani ne, tabbas dana san cewa, Amriya ita ce ta ceci rayuwa ta a teku daban aikata mata akan bah,duk abunda kuka ga nayi,duk acikin rashin sani ne, kuma ina fatan ta yafe mun kura kurai na.

Khalid yace yanzu solution muke nema,bah labari muka ce ka fada mana bah, mu tada mota muje a buga photon ta cikin jarida a ya?a, saboda a ganta, if not, am sorry to say, Ba zamu ganta bah,

Kabeer yace, na ruga dana aikata akan tuntuni, an ruga da an ya?a photon ta,kuma nayi al?awarin cewa,duk wanda yayi nasaran ganin ta, yana da kyautar million ?aya.

Khalid ya ce, Kabir bani motan na tuka,saboda yadda nake ganin ka ?in nan, bah lallai ka iya yin driving bah. Okay Kabir ya fa?a, tare da bawa Khalid driver sit ya zauna. Tada motan Khalid yayi suka bar harabar wajan.

Babu abinda kake ji a gari, sai maganar batar Amriya, gaba-daya garin Photon Amriya ne kawai ke yawo, inda gaba-daya maganar batar ta kawai ake yi a gari,yayin da mutane na ?aukan Photon a waya suna ya ?awa a kasassen sada zumunta, irinsu facebook, twitter, Instagram dadai sauran su............

Kwance take a gefen bishiya, tayi ta gumi, yayin da gaba daya fuskan ta, ya Ku kumbura, idanuwan ta, sunyi jajir, hawaye ta, ta share da bayan hannun ta, sannan tace,

Makaryaci, mugu, azzalumi, wato ni zaka nuna a idanuwan duniya ksce kana so, saboda na koma, ka cigaba da galla zamin azaba kamar yadda ka saba.

Na tsane ka Kabir,bana qaunar ganin ka, bana fatan na sake hada idanuwa dakai har tsawon numfashi na, na karshe.

Shafa cikin ta Amriya tayi, tana mai fa?in, kada ka damu ?ana, zan Kula dakai Kamar yadda kowacce mahaifiya zata kula da ?an cikin ta, bazan ta?a barin wani abu na cutar wa ya same ka bah, mundin ina raye, babu wanda ya isa ya taba ka.
Tana kaiwa nan ta mi?e tsaye, ta cigaba da tafiya.

Bayan isarsu Kabir gidan Ammi, suka tarar da kowa na parlour yayi ta gumi,
Kallon su, Sadiq yayi yace, me yasa Kuma naga kowanne ku acikin damuwa, bai kamata ace mun zauna aka bah, mafita ya kama ta , ace mun nema, ba wai kowa ya zauna yayi tagumi bah, indai akan batar Amriya ne, insha Allahu zamu ganta.

Yanzu ku taso mu koma gida kunji, insha Allahu, Allah zai bayyana mana ita. ?an jimmm Aunty amarya tayi, tareda kallo su Ammar tace, triplets Inason gobe goben nan, ki harhada kayayyakin ku, ku koma kasar Turkish.

Abdul yace, Amma umma tayaya zamu tafi bayan ba'a ga Amriya bah, damuwar ku shine damuwar mu, tayaya zamu iyayin abunda ya kaimu, bayan bamu ganku cikin walwala bah kafin mu tafi, gaskiya babu inda zamu je, in mah mutuwar ce , mu mutu tare , amma babu inda zamu je.

Daka mai tsawa Kabeer yayi! yace, Abdul Hope you are not out of your senses, Hana nuna muku hanyar daya dace, kuna yi wa mutane iska ci, toh Wallahi ksda kabari na saku a jeri mutanen da nake taming,

Maza ku tashi mu koma gida, tashi ba?i ?aya su, suka yi tare da ficewa daga parlour,suka nufi inda mototcin su ke a fake, suka shiga, yayin da su Aunty amarya,da maman Kabir suka yi sallama da juna, daga bi sani suka fice daga gidan.

Haahaha! Mom da Zainab suka kwashe da dariya, Zainab tace, ai ki min daidai karima, gwanda da kika azabtar dasu, hmmm wannan mah kadan su kaga gani.

Mom tace ke dai bari, Zainab ai ina fada maki, ina kashe su baki daya zamu kwashe dukiyar, sannan mu more duniyar mu da tsinke.

Zainab tace wallahi kamm, amma Karima, shin harda Kabir zaki kashe?,
Mom ta bata amsa da fa?in eh mana hai shi zan fara kashe wa.

Mike wa Zainab tayi tsaye tace, ba zai yiyu ba, ba zaki kashe Kabir bah, kinsan da cewa ina matukar sonsa shine zaki ce wai shi zaki fara kashe, toh gaskiya bazan yarda bah.

Mom ji tayi kamar ta kurms ihuu saboda takaici, murmushi mugun ta tayi, sannan tayi ?asa da murya tace, ana dai Zainab, ke dadi na dake bakya kwashe wa, ai bah kashe kabir zanyi bah, ina nufin shi zamu fara kwamushe wa, na saka shi ya aure ki,koh yana so koh baya so.

Murmushi Zainab tayi sa'annan tace, yanzu naji magana, amma dazu da kika ce shi za'a fara kashe wa, hankali na bah karamin tashi yayi bah.

Mom tace shikenen dai,nidai na samu matsuguni, daga yau a gidan nan zan dunga zama, har zuwa wasu kwanaki, dariya Zainab ta kwashe dashi!, sannan tace, kada ki samu damuwa shugaba, ki dauka cewa nan gidan ki ne, kiyi duk abunda ranki yake so.

Tashi Mom tayi tare da shigewa cikin ?aki,
Zainab na ganin aka ta bi bayan ta da sauri.

Zuwan su Kabir gida keda wuya, suka tarar Mom da sauran yan qungiyan ta basua nan.

Cikin gidan suka shiga, yayin da Kabir ya tura keyan su triplets gaba, yasa suka fara har hada kayayyakin su.

A ranar babu wanda yayi bacci kirki a cikin su, washe gari da sassafe, su triplets suka wuce ?asar Turkish, yayin da su kabir suka kuma koma wa gidan radio domin jin shin wani ya gano masani inda Amriya take, amma cikin rashin sa'a kuwa su kaje ba'a ji wani labari akan Amriya bah.

Aka su Kabir suka dunga zaryar zuwa gidan radio harna tsawon wata guda, saboda yadda suke zuwa akai akai, yasa mutanen wajan suka gane su.....................

Tafiya ta ke yi batare da tasan inda take nufa bah, gaba-daya ta rame tayi ba?i, fatar ta ya fara komawa ruwan tarwa?a. Yayin da gefe guda kuma cikin jikin ta ya soma girma. Wani karamin matsuguni ta samu acikin wannan jejin ta zauna, tare da share hawaye dake zubo mata.

Kallon yadda farin wata ya haska dajin tayi, ta saki dan ?aramin murmushi, tare da shafa cikin ta tace, wai yaushe zaka iso duniya domin ganin yadda take da matukar kyau, gwanin ban sha'awa.

Zan so ace a gaban idona zaka girma, amma akan bazai yihu ba, Saboda ni mutuwa zanyi na barka, amma ?ana zan roke wa wata alfarma ,

Indan Allah yayi kazo duniya da rai da lafiya, kuma ka girma, dan Allah kada kayo halin mahaifin ka, kaji koh, tsam banason ka dauko halin baban ka. Tana kaiwa nan ta jingina ajikin bishiyar tare da lumshe idonta...........

Shin kai yanzu misali idan ka samu million ?aya, me zaka yi dashi?, dariya na kusa da shi yayi, sannan yace, kaii abubuwa da dama, farko zanje ne na biya kudin makarantun yaran na , sannan na siyi kayan abinci na gida , sauran kudaden da suka yi ragowa kuma, na dora wa kaina jari.

Saurin dafa shi abokin nasa yayi yace, sani kaga mai na gani kuwa?, Sani ya bashi amsa da cewa, ni banga komai bah, menene ya faru?

Nuna yatsan shi abokin nasa yayi, yayin da Sani yabi ?an yatsan nasa da ido, abunda ya gani ne yayi matu?ar bashi mamaki, dafa abokin sa Sani yayi yace, Wannan bah ita akace hana nema bah, wata ?aya daya wuce, tabbas babu makawa itace,

Yanzu zan kira Sir Kabir na sanar masa,kaga mu kuma sai a bamu kyautar million ?aya. ?aukan wayar wacce take keypad yayi, tare da dialling number Kabir.

Kabir dake kwance kan gado gaba-daya yayi wani iri, yayi sanyi bah kamar daba, ganin hana kira shi, yasa ya bi wayar da kallo, ganin sunan Sani ne bayyane akan screen din wayar sa, akai yasa shi jan tsaki, sannan ya koma ya kwanta...

Wai me yasa mutumin nan baya ?aga wa ne , koh baya kusa da wayar tasa ne. Abokin nasa yace masa, ka kara kiran sa, wallahi million ?aya bah wasa bane.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.