Trending Hausa Novels

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel

Reading file: Asanadin_Makwabtaka_Part_3_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 1 of 4

*ASM 073*

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*

.......bayan ta gama warware takardar, zuba ma content d'in ciki ido tay tana Karantawa, lokacin data gama a matuk'ar razane ta d'ago idanunta a waje ta kalli Hajiyar kawae sai taga tana mata dariya, kai idon ta tay kan Haisam shima taga yayi mata d'an guntun murmushi tare da lumshe ido, rud'ewa tay ta kasa Fahimtar komai hakan yasa ta k'ara maida idon ta kan takardar ta k'ara karanta abunda aka rubuta a ciki kamar haka,

_WE ARE SO HAPPY TO WELCOME YOU INTO OUR FAMILY ZARAH_

_It's such a joy to be with u, We hope your presence will brightens up our days. You're a Wonderful person Zarah, we are so lucky to know u._

*We look forward to all the Wonderful things you'll bring to our lives. We love u so much Zaraah.*

Lokacin data gama d'agowa
tay ta waro idanu ta kalli Fanan dake tsaye a gabanta har lokacin kawai sai gani tay itama tay mata d'an murmushi, gaba d'aya sun rud'ata har Fuskarta ta bayyanar da hakan, d'age mata gira Fanan tayi Calmly ta furta "Nima na rama halin da Message d'in ki ya sani Zaraah" ta6e baki ta fara kawae sai ta fashe da Kuka Fanan ta kai hannu ta rungumo ta a jikinta a hankali take furta mata is okey, d'agota tayi bayan wani lokaci ta kama hannunta suka nufi ciki har lokacin Fatuu kuka take tasa gefen gyalenta tana ta goge k'wallan dake zubo mata, Kujerar data taso ta nufa da ita ta Zaunar da ita itama ta zauna a gefenta ta yadda suka saka Fatun a tsakiya har lokacin tanata sharar k'walla da gyalenta, Hannu Fanan ta kai ta dafa Shoulder d'inta tana ce mata ya isa haka kada tayi ciwon kai tayi mata wasa ne, Hajiya itama ta fara bata hak'uri tace mata sune suka shirya mata haka ita ba ruwan ta, daina yin kukan tayi ta sadda kanta k'asa har lokacin gabanta na d'an fad'uwa ganin komai take kamar a Mafarki don bata ta6a zaton haka daga Fanan d'in ba, a hankali ta d'an juyar da kanta ta saci kallon Haisam dake gefenta karaf suka had'a ido dashi ya kafeta da idanun shi dake a d'an lumshe da sauri ta maida kanta k'asa, Hajiya ce tayi d'an gyaran murya tace masu suyi ma Annabi salati (SAW), bayan sun gama ta fara masu Nasiha gaba d'aya kan zaman tare da kuma hak'uri da juna daga baya ta fara ma Haisam shi kadae kan rike amanar matan shi da kuma yin Adalci a tsakanin su, bayan ta gama dashi ta koma kan Fanan ta nuna mata kada ta dauki duk abunda ake fad'a akan kishiya ta d'auka ita d'in Alkhairi ce sai taga ta zame mata Alkhairin ta rufe idanunta ta kuma toshe kunnuwan ta daga dukkan wata zuga da za'ai mata kan Fateema, kada ta goyi bayan a cutar da ita domin tasan Allah baya barin cuta, tace ta ci gaba da yi mata kallon k'anwarta kamar yadda take yi mata a da, a matsayinta na babba ta zamo mai hak'uri sosae akan komai in taga tayi ba daidai ba ta nusar da ita...Sosae tayi mata Nasiha itama Fanan d'in dake jingina da kujera tana ta d'an jinjina mata kai, a k'arshe ta yaba mata sosae akan Namijin kokarin da tayi wurin yak'i da zuciyarta ta danne kishinta don Farincikin su ta nuna samun matan da zasu iya yin hakan yanada matuk'ar wahala ta nuna mata kar ta d'auki hakan gazawa face jarumta wurin yin abunda yake daidai, ta nuna more ma rayuwa shine ka sanya farinciki a zukatan mutane ba ka za6i ka saka kanka kad'ai ba hakan zai saya maka soyayya da k'ima a idon mutane, haka kuma ko bayan ba ranka za'a ji rashin ka baza kuma a manta da kai ba riba biyu kenan sa6anin ka za6i Farincikin kanka kai kad'ai ka cuta ma mutane su rink'a k'in ka k'arshe ka mutu aita murna tunawa ma da kai yayi wuya,

Kallon Haisam tay dake kishingid'e yana sauraran ta tace "ina son ka sani Fanan masoyiyar ka ce ta hak'ika tunda har ta za6i Farincikin ka fiye da nata don haka indai ka wulakanta ta wllh sai Allah ya saka mata duk da bani da haufi a kan ka kawai tuni nake maka" jinjina mata kai yay a lokacin Fanan tasa hannu ta d'an dafe goshinta jin kuka na niyyar taho mata ita kad'ai tasan abunda take going through don ma tana ta yin Addu'oi a cikin ranta, komawa Hajiya tayi kan Fatuu da kanta ke a sadde tace ta dawo gareta, farko maraba da shigowa cikin Family d'in su ta k'ara yi mata tace tasan halinta itama bata da shakku a kanta don haka kada ta sake ta canza daga yadda ta santa ga Fanan nan taci gaba da d'aukar ta matsayin Yayarta kar ta sake daidai da rana d'aya tace zata mata kallon kishiya, in tana da matsala ta sanar da ita tana da yak'inin zata bata shawarar kirki sannan ta taimaka ma mijin su wurin ganin yayi masu Adalci hakan shine son gaskiya, in Fanan tana yi mata abunda bata jin dad'i ta fad'i mata idan bata gyara ba ita ta fad'i mata duk da tasan in sha Allahu hakan bazata faru ba, daga k'arshe bayan ta gama yi masu nasihohin da suka tsuma masu jiki sosae tayi masu Addu'oi tasa Haisam shima yayi duk suka d'aga hannuwa suna amsawa har ya gama gaba d'aya suka shafa, shiru ta biyo baya duk suka cigaba da yin kallo saidai kowa da abunda ke kai kawo cikin Zuciyar shi, gaba d'aya Fatuu ta kasa sakewa don jikinta na bata Haisam kallon ta yake hakan yasa duk ta takura ga kuma yanayin Fanan data lura tana a cikin damuwa k'arfin hali kawai take hakan yasa duk ta sha jinin jikinta, kiran sallar Magrib da aka fara yi yasa Haisam mik'ewa hannunshi ruk'e da rigar shi ta sama daya d'auka yace ma Hajiya zai je salla tai mashi a dawo lpy, d'an d'aga ido Fatuu tayi tana kallon bayan shi har ya kusa fita sannan ta maido shi k'asa, zuciyarta ce ta shiga raya mata wani abu game da shi, bayan fitar shi Hajiya ta mik'e tace masu suje suyi salla, Fanan ce ta fara mik'ewa da d'an murmushi ta kalli Fatuu data d'ago tana kallonta ta mik'a mata hannu, a sanyaye ta kama hannun ta mik'e suka nufi ciki.

Yadda hakan ta faru, bayan Haisam sun gama Magana da Fanan kan zuwa Nigeria ranar talata, da yamma Hajiya Maryam ta kirata don ta ji halin da ake ciki game da tahowarta nan take sanar mata yadda sukai da Haisam kan zuwa Nigeria ta yi ma Hajiyar Magana da kanta, nan Hajiya Maryam taji dad'i sosae don tasan da wuya in Hajiyar bata bari an saki Fatun ba Saboda su duka sun nuna basu so kuma tasan yadda take ji dasu gaba d'aya, hakan ne yasa washe gari da Hajiya ta kira Hajiya Maryam game da zancen dawowar Farha da Maganar data yi mata sam bata damu ba, tun bayan da suka yanke zuwa Nigeria Haisam ya kasa samun natsuwa, damuwa tayi mashi yawa don yasan shi dae ba iya sakin Zaraah zai yi ba yadai biye mata ne don ya kwantar mata da hankali k'arshe kuma yasan indae suka zo Nigeria yak'i sakin Fatuu to abun zai k'ara kwa6ewa ne, hakan yasa ya yanke tunkararta akan hakan, Ranar Alhamis da daddare ya isketa a d'aki lokacin tana zaune akan gado tana latsa wayarta, tana ganin shi ta d'ago tana mashi dariya ya nufi bakin gadon ya zauna shima yana mata murmushi, aje wayar tayi ta matso inda yake ta kwanta a bayan shi ta yadda yay kaman ya goyata ta sak'alo hannuwanta a wuyan shi nan ta shiga fad'a mashi kalaman soyayya, sosae yaji fargabar sanar da ita abunda ya kawo shi k'arshe dai yay k'arfin hali yace mata magana yake so zasu yi, tana jin hakan ta sake shi ta dawo daga gefe tana kallon shi, d'an jimm yay ta kafe shi da ido daga baya ya fara magana gently, ce mata yay Alfarma yake son ya nema a wurinta for the first time a zaman su, jinjina mashi kai tay gaba d'aya ta maida hankalinta akan shi, ce mata yay ya zauna yayi dogon tunani gaskiya idan ya saki Zarah bai mata Adalci ba zai zama ya cuce ta ne Saboda shi ya fara saninta sannan tayi k'arama ace ta zama bazawara, wani kallo take bin shi dashi yanayin fuskar ta ya canza da alamun d'aurewar kai tace to mi yake nufi kenan, kauda idon shi yay tana ta kallon shi can ya juyo ya kalleta yace "I can't divorce her......" waro ido tay hankali tashe take kallon shi, hannu ya kai zai kama hannunta da sauri ta janye ta fara k'ok'arin nufar can d'ayan 6angaren gadon ta sauka, da sauri ya idasa hayewa saman gadon ya cafkota, rungume ta yay k'am ta fara kokowar kwacewa amman ta kasa kawae sai ta fashe da matsanancin kuka ta fara fad'in ita zai yaudara bacin sun gama Magana shine zai zo yace bazai saketa ba dama tasan yana sonta ne shiyasa ya aureta yanzu kuma daya san ita tana haihuwa shine zai ce bai iya rabuwa da ita to indai ya za6i zama da ita ita Allah bazata cigaba da zama da shi ba, sosae ta tashi hankalin ta sai k'ok'arin k'wace kanta take k'arshe kawai sai ya had'e bakunan su ya fara kissing d'inta deeply don yasan hakan zai iya calming nata, ya d'an d'auki lokaci yana mata hakan kafin ya saki bakin nata jikinta sai kerma yake tana sheshsheka, kwantar da kanshi yay saman kanta cikin sigar rarrashi ya fara magana yace mata yasan ita ba mai son kai bace tayi tunani, in ya saki Zarah zai cuceta ne yasan bazata so hakan gareta ba ko kuma sister d'inta Farha tayi aiki da Hadisin manzo SAW da yace love for ur brother what you love for urself, a yadda yasani tana son Zarah sosae miyasa bazata tausaya mata ba, sai huci take ta hau girgiza mashi kai tace ita dai bazata iya zama da ita matsayin kishiya ba, miyasa zai saka mata rai yayi mata alk'awarin zasu zauna su biyu, ce mata yay ya gaya mata already da aure a tsakanin su amman yanzu zai iya yi mata wani daga Zarah bazai k'ara Auren wata ba su biyu zasu zama matan shi har k'arshen rayuwar shi, shiru tay kaman mai nazarin wani abu can ta d'ago ta kalle shi idanunta sharkaf da hawaye tace "Tell me the truth, do you love Zarah?" Shiru ya d'an yi yana kallonta can ya jinjina mata kai kawai sai ta fashe da kuka ta fad'a jikin shi tana fad'in ita daman tasan son Zarah yake shiyasa tun farko ya auretan in ba haka ba miyasa bai sa Abbas ya aureta ba daga baya ya saketa sai shi daga baya kuma yazo ya kwanta da ita, tasan itace First love d'in shi dama ita ba son ta yake ba kawai tausayinta ne yasa ya aureta don haka zata bar shi sai suji dad'in zama da juna, sosae take kuka yana rungume da ita cikin kwantar da murya yace mata wayace mata bai sonta, da farko da akai mashi Maganar aurenta Saboda yasan ba soyayya suke ba shiyasa ya nuna bazai aureta ba don bai d'auka Maganar da ta yi mashi ta zai aureta ba da gaske take Saboda lokacin a wurin shi tayi k'arama da wannan Maganar, amman daga baya daya nuna ya amince Saboda yana son ta ne, kuma da bai sonta a zaman da sukai ai ya isa ta gane, tambayarta yay a zaman su tare ya ta6a cutar da ita ko hantarar ta ko dai yi mata wani abu na rashin so, d'an girgiza mashi kai tay yace to ta daina cewa haka he truly loves her kuma yana rokonta tayi mashi wannan alfarmar Saboda son da take mashi koda kuwa daga ita bazata k'ara mashi wata ba har k'arshen rayuwar su ya amince, gaba d'aya ya kashe mata jiki ganin haka yasa yaci gaba da rarrashinta, wai akace tsakanin mata da miji sai Allah d'agowa tay tace "Shikenan na Amince but don't break the promise u have made now kuma kayi man Alk'awarin zaka yi mana Adalci" sosae ta bashi tausayi don yasan Saboda son da take mashi ne yasa tayi saurin Amincewa, ce mata yay in sha Allahu zai yi masu Adalci tace ita bata yarda ba sai yayi mata Alk'awari da d'an murmushi yace to ya yi mata. Koda suna a jirgi saida ta jaddada mashi ya dai ce zaiyi Adalci a tsakanin su ko yana murmushi yace mata eh, Bayan sun iso a Bedroom d'in Hajiya suka sauka dama tun kafin su zo Haisam d'in ya fad'i mata game da amincewar da tayi itama Hajiya taji dad'i sosae, bayan sun gama gaisawa tayi masu Maganar Abinci duk suka ce mata basu jin yunwa a lokacin nan ta k'ara yi ma Fanan Nasiha sosae ta nuna mata ta d'auki abun a matsayin Alkhairi ta shiga bata misalai kan irin hakan sosae Fanan ta d'auki Nasihar Hajiyar daga baya ta tambayi Fatun Hajiya tace bata dad'e da barin Part d'in ba, ita da kanta ta tambayi Hajiya takarda ta rubuta abun ciki taba Haisam d'in tace zata mata wasa ne Hajiya na dariya tace ta dai tada mata hankali dama yar'uwarta da Mahaifiyarta sun gama nasu da alamun rashin fahimta Fanan d'in ta tambayi mi sukai mata nan Hajiya ta kwashe komai da Hajiya Maryam da Farha sukai ma Fatun, sosae ta bata tausayi har fuskarta ta bayyana, daga baya suka koma Parlor nan Hajiya ta kirata saidae ita bata san da Maganar sak'on da Fatuu ta tura ma Haisam ba saida tazo Fanan na mata Maganar ta fahimci ita ta tura mashi sak'o Fanan d'in ta gani.

Sai bayan da aka yi isha sannan Haisam ya dawo lokacin suma sun dawo cikin parlon, Fatuu na ganin shi ta gane yaje part d'in su don har ya canzo kaya, har ya k'araso idon shi na akan Fatuu da tunda ta kalle shi ta maida idon ta akan Tv, Fanan ce tay mashi sannu da zuwa da murmushi ya amsa mata Fatuu tay d'an jimm zuciyar ta ta raya mata itama tace mashi mana, da k'yar ta d'an kalle shi da yake Facing d'in su yake murya na d'an rawa tace mashi sannu da zuwan ya jinjina mata kai kawae ya zuba mata ido da sauri ta maida nata kan Tv, wani abu take ji mai kamar haushin shi a ranta, bai dad'e da zama ba Saude tazo ta sanar dasu ta shirya Table, Hajiya ce ta fara mik'ewa tace masu su taso, bayan duk sun zauna Saude na niyyar Serving nasu bayan ta gama da Hajiya tace mata taje kawae, kallon Fatuu tay tace ta tashi tay Serving bak'inta ta d'aga mata kai, Haisam ta fara zuba mawa tana yi tana tambayar shi in yayi ya kafeta da kaifafan idanuwan shi da suke a d'an lumshe dasu yake bata amsa ko da kai gaba d'aya yana neman rikita ta, bayan ta gama ta juya kan Fanan itama ta zuba mata saidae d'an kad'an tasa ta zuba mata, zubawa itama tayi bada yawa sosae ba duk suka fara ci a nutse, baka jin komai sai k'arar cokulla, duk in ta saci kallon Haisam sai taga ita yake kallo yanayin fuskarta kamar a d'aure, tana lura da Fanan sam bata wani cin Abincin juya cokali ya fi yawa sai an d'auki lokaci take d'an d'iba ta kai baki tay ta taunar shi sai kaga kaman tana ci, duk Fatuu sai taji ba dad'i don gani take itace silar damuwar ta, can dae tay k'arfin hali murya na d'an rawa tace "A...unty Fanan baki ci sosae" da sauri Fanan d'in ta kalleta tay mata murmushi murya k'asa k'asa tace mata tana ci mana, Hajiya da ta d'ago ta kalli Fanan d'in da d'an murmushi tace an sha tafiya ko gajiya ce tasa ta kasa ci sosae in tana son wani abu ta fad'i sai a had'a mata, d'an girgiza ma Hajiyar kai tay tace wannan ma lafiya lou, kad'an ta k'ara ta mik'e duk suka kalleta tana murmushi tace ta k'oshi bata da appetite ne zata k'ara da tea daga haka ta fita daga cikin Kujerar ta nufi hanyar Bedroom idon Haisam a kanta ita kuma Fatuu lokacin ta samu damar kallonshi sosae bata Ankara ba ya juyo suka had'a ido, kayataccen murmushi taga ya sakar mata ta bishi da ido kawae, kaman daga sama suka ji muryar Hajiya tana fad'in suyi sauri su gama ba sai suje suji dad'in kallon Junan ba, sosae kunya ta kama Fatuu ta sunkuyar da kai, da k'yar ta cinye Abincin ta mik'e tace ma Hajiya saida safe ta kalleta tace to Allah ya basu Alkhairi,

bayan ta fita daga cikin Kujerun Hajiya ta tsaida ita tace taje suyi sallama da Yayar ta tace to ta nufi hanyar Corridor tana tafiya kamar wadda k'wai ya fashe mawa a ciki, d'an jimm tay a bakin kopar visitor room d'in gabanta na d'an fad'uwa hakanan fargabar shiga take ji, can dai ta tura kopar a hankali tare da yin yar sallama, a kwance ta hangota ta kife fuska a jikin pillow kai da gani kasan da wuya in ba kuka take ba, bugun k'irjin Fatuu ne ya k'aru da sauri ta juya zata fita don ta lura kaman bata ji sallamar data yi ba, har zata fita taji Muryar ta ta kira Sunanta, juyowa Fatuu tay ta kalle ta taga ta tashi zaune, a sanyaye ta nufi gadon ta nuna mata gefen ta alamar ta zauna Fatuu na kallon idonta ta gane kuka take duk da goge idon da ta yi, shiru suka d'an yi kafin Fanan d'in tace mata har ta gama cin Abincin ta d'aga mata kai ta jinjina nata itama, shiru suka k'ara yi idanun Fatuu a k'asa wani irin tausayin Fanan d'in take ji can ta d'ago ta kalleta idanunta sun ciko da k'walla cikin karyayyar murya tace "Aunty Fanan don Allah kiyi hak'uri wllh ban ta6a nuna mashi ina son shi ba, ko wannan sak'on da kika gani bani na tura mashi ba wllh k'awata ce kuma sai da na nuna mata ban ji dad'i ba daga baya ma na goge shi ko tambayar shi zaki ko ki duba zaki ga an goge" idanun Fanan d'in suma cike tabb da k'walla take kallon ta harda Murmushin k'arfin hali har ta gama sannan ta kai hannu ta janyota ta kwantar da kanta a saman shoulder d'inta cikin sanyin murya tace 'its okey Zaraah I understand everything, kema bake kika d'aura ma kan ki ba, komai da yake Faruwa akan mutum was already written, Allah ya bamu ikon ruk'e Amanar juna and am sorry for what u'r going through itama Friend d'in tak'i taga kina wahala ne yasa ta yanke turo sak'on" shiru Fatuu tay wani irin tausayin Fanan ya mamaye mata zuciya, can ta d'ago daga kan kafad'ar tata ta kalleta a sanyaye tace mata to don Allah ta daina yin kuka bata jin dad'in ganin ta haka sai taita ganin kaman Saboda ita ne, da sauri ta girgiza mata kai tace ta bar sama ranta hakan kawai abunne gaba d'aya yazo mata a bazata so dole sai a hankali zata washe nan ta sanar mata da bata san komai ba sai da aka turo sak'on ita ta fara gani, sosae Fatuu taji ba dad'i Fuskarta a yamutse take kallonta can Fanan d'in tace mata ta k'ara girma sosae tana murmushi harda tambayar ta ta kai 20yrs ne yanzu, Fatun tace mata a'a 19 take ta jinjina kai tace tana da jiki mai kyau ita dai d'an murmushi kawai tayi sai kuma tace mata itama ai tana da kyaun jiki ga tsawo ita kuwa gajera ce har saida tasa Fanan d'in yar dariya,

tambayarta karatun ta tayi tace ta kusa gamawa ko, ta bata amsa da yanzu zasu kama nursing 2 sai su shiga 3 daga nan zasu gama, jinjina kai tayi tace Allah ya basu sa'a bayan Fatuu ta amsa tace "in kika gama nasan U.S zaki dawo sai kiyi Medicine ki zama likita da kike buri" yar dariya Fatun tayi kawai, suna haka aka turo kopar d'akin duk suka kai idanunsa wurin, Haisam ne ya shigo hannun shi ruk'e da tea cup asaman saucer, har saida gaban Fatuu ya d'an fad'i ganin shi, ciki ya shigo ya nufo wurin su,a gaban Fanan ya tsaya idonta akan shi da d'an murmushi ya mik'a mata cup d'in tea d'in ta amsa a hankali ta furta mashi thanks Fuskar shi a sake ya jinjina mata kai, d'agowa yay idon shi akan Fatuu da ke kallon k'asa sai taji duk ta takura, mik'ewa tay ta kalli Fanan tace mata saida safe tace ta tsaya su sha tea d'in mana da d'an murmushi ta girgiza mata kai tace taci Abinci sosae dama saida safen ta shigo yi mata, godiya tayi mata tace sai sun had'u da safe daga haka Fatun ta juya ba tare data kalli inda yake ba ta nufi k'opa ta fuce. Tana tafiya tana ta zancen zuci har ta k'araso part d'in su, tun a parlor ta gasgata Haisam ya shigo jin k'amshin turaren shi,

Bedroom ta wuce tana shiga ta nufi bakin gado ta zauna tay zuru tana cigaba da zancen zucinta, sosae Fanan take bata tausayi tasan itama ba K'aramin so take ma Ya Haisam d'in ba yanzu kuma ace ya auri wata tasan dole ta shiga matsananciyar damuwa, mamakin ta yadda akai tay saurin amincewa ba kamar data ce mata saida aka tura sak'on nan ta sani duka kuma ba'a fi kwana shidda ba, wata zuciyar ce ta raya mata wato da ya kasa fad'a mata saida asiri ya tonu ta amince shine suka taho da hakan bata faru ba tasan baida niyyar zuwa, wani abu taji mai kaman 6acin rai ta raya yanzu dai ta tabbatar ba son ta yake ba tunda saida Matar shi ta amince zai waiwaye ta dama kuma tasan Saboda Hajiya yake zaune da ita, rayawa tayi to miye amfanin zaman ta dashi wai tunda bai son ta kawai ya saketa ya huta Aunty Fanan ma ta huta da damuwa, tunanin ta nemi ya saketa ta shiga yi, wata zuciyar ta raya mata tana tunanin a yanzu zai saketa bacin yasan sirrin zuciyarta ita kanta Fanan ai don ta nuna tana son shi ya aure ta, sosae taji bata ji dad'in sak'on da ya gani ba amman duk da haka ta sama ranta zata ce ya sake ta kawai, ta d'auki lokaci a zaunen kafin ta mik'e don taje tayi wanka, bayan ta aje gyalen ta gaban mirror ta tsaya tana kallon kanta ta kai hannu tana cire yan kunnan ta fashion bayan ta cire su ta cire agogon hannunta ta d'aura su akan dressing mirror, daidai ta juyo aka turo kopar Bedroom d'in har saida gaban ta ya fad'i, shi ne ya shigo idon shi akanta yasa hannu d'aya ya tura kopar, a wurin ya tsaya suka kafe juna da ido fuskar shi a sake kaman zai yi murmushi ita kuwa yanayin tata kaman a d'aure, kauda idon ta tayi gefe zuciyarta ta raya mata tsayuwar mi take ta tafi tay wankan ta, nufar hanyar Laundry room tay idon ta a k'asa har tazo daidai inda yake a tsayen, tana niyyar wuce shi kawai taji ya kamo hannun ta na gefen da yake, yamutsa fuska tay fuskarta na kallon gefe wurin gado kirjinta ya hau bugu da sauri da sauri, wani irin haushin shi taji ya kamata wato sai yanzu da aka amince mashi ne zai yi lokacinta ta raya hakan, kaman daga sama taji ya furta "Zaraah" wani kalan murmushin takaici ta yi nan take ta fara k'ok'arin k'wace hannunta, k'ara kiran sunanta yay aikuwa a fusace ta juya idanunta har sun ciko da k'walla tace "ba suna na haka ba sunana Fatuu ka kira ni da hakan" cikin yanayin muryar kuka tayi Maganar tana rufe baki k'walla suka zubo mata sharr da sauri ta juyar da fuskar inda take kallo da, still yay yan kallonta don ya gane dalilin daya sa ta fad'i hakan, k'ok'arin matso da ita ya fara nan take ta fahimci rungume ta zaiyi aikuwa ta tirje ta fara jan hannunta sai ga abu ya zama kaman kokowa, da dai taga ta kasa kwace hannun sai ta fashe mashi da kuka ta fara fad'in ita ya sakar mata hannu, janyota yay ya had'a jikinsu ta kafe tak'i yarda ya mannata da k'irjin shi ta hau girgiza kan ta cikin k'araji take fad'in ita ya k'yaleta, sosae take kuka tana girgiza kai idonta a rufe gaba d'aya ta fara rud'a shi fuska a yamutse yake kallon tata fuskar, da k'yar ya manna ta da k'irjin nashi ya rungumeta gam sai faman kuka take, d'aura ha6ar shi yay a saman sumar ta mai santsi da tuni kallabin dake sama ya fad'i, lumshe idanunshi yay underneath his breath yake furta "am sorry for hurting u Zaraah, it was never my intention" shiru tay tana cigaba da kukan saidae sautin kukan ya d'an ragu sai sheshsheka take ga fitinannan k'amshin jikin shi duk ya cika mata hanci hakan ne yasa natsuwarta ta d'an daidaita, Moving yay da ita zuwa bakin gado ya zauna da ita ta kasance a saman cinyoyin shi har lokacin kuma yana rungume da ita gam, maida ha6ar shi yay saman kan nata breathing d'in shi na fita slowly idanun shi a d'an lumshe shi kad'ai yasan abunda yake ji a cikin ran shi ganin ta cikin halin nan, ganin kaman ta d'an natsu yasa shi janye beard d'in shi ya maida fuskar shi saitin kunnanta whispering in to her ear ya furta "I came all because of you" da sauri ta girgiza mashi kai ta d'ago idanunta sharkaf da hawaye ta juyar da fuskar ta gefe cikin fushi tace "ni ban son Auren ka sake ni!" jimm yay yana kallon ta can yay sigh calmly ya furta "Zarah kina fad'a man haka a matsayi na na mijin ki ba kyau fa" sheshshekar kukan ta ce ta k'aru, ji tay yace "Kin daina sona ne??" Kaman tana jira da sauri ta d'aga mashi kai alamar eh har saida ya d'an runtse idon shi kafin slowly ya bud'e sai kuma ya d'an cize le6en shi na k'asa, nisawa yay yace "are u serious Zarah?"da sauri ta k'ara d'aga mashi kai alamar eh wannan karon har saida yaji gaban shi ya d'an fad'i, shiru yay idon shi a kan gefen fuskar ta, mutsu mutsu ta fara yi tana son ta k'wace daga jikin shi saidae ta kasa a hasale tace ita ya k'yaleta, still shiru yay bai kuma sake tankawa ba sai dae zuciyar shi ta fara gasgata mashi abun da take fad'an, muryarta ce ta k'ara ziyartar kunnan shi tace ya saketa, sigh yay Slowly ya furta "Ok, I want you to look into my eyes and tell that u don't love me sai in maki abunda kike so in hakan zai saki farinciki" yana rufe baki ta juyo ta kalle shi cikin idon da k'arfi gaban shi ya fad'i don yana ganin fad'in zata yi, bin juna sukai da ido tana d'an huci wani irin kallo yake bin ta da shi sai motsa baki take ta kasa furta mashi Maganar gaba d'ayan su gaban su fad'uwa yake bai ta6a jin zullumin magana ba sosae irin haka, da k'yar ta fara bud'e baki tace "ba.......n......." Zuciyarta ce ta fara tariyo mata Alkhairan shi a gareta ta shiga raya mata yanzu duk son da take mashi da wahalar da tasha Saboda shi ta za6i ta rabu dashi, kawai sai gani yay ta fashe da matsanancin kuka ta fad'a mashi, wani irin lumshe ido Haisam yay sosae yaji sanyi a ran shi, Kuka take sosae ta had'e fuskar ta da k'irjin shi, daga jin yadda sautin kukan ke fita yasan ba K'aramin K'ona ranta ke mata ba zuciyar shi ce ta shiga tunano sak'on data tura mashi irin wahalar data bayyana mashi ta sha Saboda son shi, wani irin tausayin ta ne ke ratsa shi sam bai jin dad'in yadda take kukan har Fuskar shi ta nuna fararen idanuwan shi sun d'an yi ja, hannun shi d'aya ya d'ago ya d'aura a saman kan ta ya fara shafa gashin ta alamar lallashi cikin breaking voice ya fara magana "am very sorry Wife, am not happy I caused u pain, kiyi hak'uri don Allah, bansan komai ba game da haka" cigaba da shafa kan yayi a hankali sautin kukan nata ya fara raguwa, sun d'an d'auki lokaci a haka saida yaji tayi shiru sai ajiyar zuciya da take ta faman yi ya d'ago da kanta suka fara kallon juna idanunta sun yi luhu luhu sunyi ja har lokacin ajiyar zuciyar take ta saki,

"Forgive your Husband pls, bana jin dad'in ganin ki haka Wife, ba kamar in na tuna duk Saboda ni ne, ki manta komai ya wuce pls" yana Maganar d'umin numfashin shi na sauka akan Fuskar ta, shiru kawae tay tana kallon shi ba alamun zata tanka, fuskar shi a sake kaman zai murmushi yace mata tayi mashi magana pls sai lokacin ta d'an juyar da fuskar ta, hannu ya kai ya juyo da Fuskar ta sake kallonshi ya lumshe mata ido nan take ta gane Magana yake nufin tayi, da k'yar ta bud'e baki cikin muryar kuka da yar in ina tace "t...to ai kai baka sona ko shiyasa gara a bar Auren" d'an murmushi yayi yace mata in sun rabu to ya zatayi da son nashi,

"A...ai dama baka sani ba ko na 6oye sai in yi hak'uri kuma nasan zan daina daga baya, d...dama ai har na hak'ura za'a min Aure ko" tana Maganar ya zuba ma bakinta ido Fuskar shi kaman zai murmushi har ta gama ta d'an tura baki, murmushi yay ya d'an d'age gira yace "in kuma ni ban son rabuwa dake fa Saboda nima ina son ki" ba shiri ta waro ido bakinta ya d'an bud'e, sosae taji Al'ajabin Maganar don ta gama yanke bai sonta, hannu ya kai ya rufe mata bakinta da ta bud'e ta tura mashi bakin had'i da d'an juyar da fuskar ta, ji tayi yace bata bashi amsa ba sannan ta maido idon ta kanshi a sanyaye tace ai tasan da wasa yake tunda da yana son ta ai da ya nuna mata, murmushi yay kawae suka zuba ma juna ido Fatuu sai d'an kikkafta ido take idan tace bata jin sabon son shi na ratsa zuciyar ta to ta shirga babbar k'arya, ganin bai da niyyar cewa komai gashi ta k'osa taji da gaske yana son ta yasa ta d'an yamutsa mashi Fuska, d'age mata gira yay yace "What?" a d'an shagwabe tace he should tell her da gaske abunda ya fad'a, Sigh yay kafin a nutse ya fara Magana,

"Lokacin da Hajiya ta kira ni tay informing nawa game da Auren da za'ai maki na shiga damuwa because nasan miye burin ki kina son kiyi karatu, hakan yasa naji ba dad'i sosae har nayi mata magana kan bai kamata ayi maki Aure ba kuma ma wannan Auren dole ne I asked her to do something tunda hakan ya shafi aikinta na NGO but sai ta nuna man haka al'adan ku yake in ta shiga Maganar har ta hana ayi maki auren zai zama wani seriou issue Dad d'in ki zai shiga matsala sosae a lokacin ta fad'a man a halin da yake ciki kuma kema kin amince, karshe I have no option dole na bari suyi maki yadda suke so din, abun ya dame ni sosae bayan na kira ki kin sanar man kema baki so Saboda Dad d'inki kika amince haka nayi ta tuna Maganar ki da kukan da kike yi a lokacin, I thought damuwan nawa zai ragu tunda kin nuna man kin amince da Auren but sai abun yay ta gaba thinking of u all the time, nayi tunanin don na damu da halin da kike ciki ne a Lokacin amman abun sai yay ta k'aruwa damuwan yayi man yawa ko yaushe Zarah ce a raina abun har ya fara affecting bacci na bana samun enough ko ya d'auke ni it's Zarah gaba d'aya cikin shi, while eating, while driving ko mi nike Zarah ce abun har ya kaini ga hullicinations da naga yar baturiya daidai girman ki sai inta ganin ke ce inna zauna shiru sai inta jin muryar ki kina magana ko kuma in wata tayi magana naji kaman voice d'inki....." Dakatawa yay dama Maganar yana yi yana d'an tsayawa yake yin ta, idon su cikin na juna Fatuu tayi k'uri tana saurarar shi cike da Al'ajabi, d'an yamutsa mata fuska yay yace "kin man nauyi" wani kallo tay mashi ta d'an tura baki, K'ok'arin sauka daga saman jikin nashi ta fara ya maidota yay wrapping nata sosae, kai Fuskar shi yay gefen kunnanta whispering into her ear ya furta "just kidding wife, bana jin nauyin ki in ma kina da shi" yadda Maganar ke sauka acikin kunnanta har saida ta runtse ido fuskar ta d'auke da murmushi, shiru suka d'anyi can ta d'ago da fuskarta taga ita yake kallo, ganin baida niyyar cigaba yasa ta d'an yamutsa mashi Fuska tare da d'an motsa kai, murmushi yay don ya fahimci mi hakan ke nufi slowly ya kai bakin sa saman goshinta yay pecking wurin har saida ta d'an lumshe ido tana bud'ewa suka shiga cikin nashi kunya ce ta kamata da sauri ta kife fuskarta a broad chest d'in shi, hannu ya kai ya cigaba da shafa sumar ta mai santsi da laushi,

"I don't know what's happening to me a lokacin,but I know am not alright don ban ta6a fuskantar irin hakan ga wani ba besides ni ban sa damuwa a raina, in dai abu naga zai zaman man damuwa da wuri nike maganin shi, a lokacin Fanan ta gane abu na damuna ta fara tambayana farko na nuna mata kawai banjin dad'i ne amman daga baya ta fara nuna man damuwarta kan sai na fad'i mata abunda ke damuna don ta ganni abnormal, na rasa mi zance mata yana damuna na barshi a banjin dad'i ne tace to muje Asibiti na nuna mata ba wani ciwo nike ba itace take ganin kaman ban lafiya, nasan kawai ta k'yale ni ne ba don ta yarda ba daga lokacin na fara k'ok'arin 6oye abunda ke damuna Saboda ita sai kuma na fara samun sleepless nights don sai damuwan ya dame ni in dare yayi hakan ke sa in kasa bacci, daga k'arshe na yanke zuwa inga Doctor, banje Asibitin su Fanan ba sai na je wani daban naga likita, bayan nayi mashi duk bayanin abunda ke damuna ban 6oye mashi komai ba shine yay assuring nawa cewa.....Na fad'a Son ki ne....." dakatawa ya k'ara yi suka k'ura ma juna ido cike da k'auna yayin da numfashin su ke had'uwa dana juna, kasa jurewa Fatuu tay ta sauke idanunta don wani irin kallo mai saukar da kasala yake mata,

"Nayi mamakin jin hakan sosae Saboda tunda nike dake ban ta6a ji ko yi maki kallon hakan ba, ina d'aukar ki a matsayin blood sis tawa, kallon da nike maki kenan Zarah, saidae ban k'aryata Maganar shi ba na yarda da hakan, nan ya bani shawarwari saidae wadda yafi bani itace in mallake ki shine solution kawai a lokacin, jin hakan har saida na d'an yi murmushi sanin it's impossible, daga lokacin na dage kan sai na cire son naki a raina na dage da rok'on Allah akan hakan sosae nike yak'i da zuciyana, ban gane son ki yamun mugun kamu ba sai bayan na tafi wani Seminar da Company d'in mu suka tura ni, ina cikin yin bayani na rink'a ambaton sunan ki saida aka man magana sannan na gane shirmen da nike tafkawa, k'arshe dai ranar a gadon Asibiti na kwana don wani duhu na fara gani har ya kai na fad'i......",

dakatawa ya k'ara yi ya d'age mata gira yace "tunda kike ciwon sona kin ta6a koda shan drug ne Saboda hakan?" d'an jimm tay alamar tunani kafin a sanyaye tace mashi a'a saidae maganin bacci da Kawu Amadu ya ta6a amso mata data kasa yin bacci, d'an murmushi yay yace "kin ga ni nasha drugs, na kar6i injections k'arshe harda drip all because u" wani irin tausayin shi ne ya mamaye mata zuciya nan da nan idanuwanta suka ciko da k'walla yana ganin haka ya girgiza mata kai da sauri alamar kar tayi kukan ta hau kikkafta idanu, cikin karyayyar murya tace mashi yaci gaba, d'an tura mata baki yay irin yadda take yi slowly yace mata ya gaji da Magana har saida yasa ta d'an yi yar dariya dama don ta washe kada tayi kukan yayi Mata hakan,

"Kwana na d'aya a asibitin na nuna gida zan koma aka matsa man kan in bari in k'ara samun sauk'i, bayan nayi kwana biyu lokacin na warware sosai na dawo gida ba tare dana k'arasa abunda naje yi ba...., wani iko na ubangiji ranar Abbas ya kirani yake sanar dani ai gaki kin gudo wai baki son Auren da za'a maki na tambaye shi dalili nan ya sanar dani irin mijin da ake son Aura maki, lokacin na tambaye shi to miye mafita sai yace man ai ya yanke zuwa garin shida Grandma d'inki nace mashi Shikenan duk abunda ake ciki sai ya sanar man, a next wayan da mukai da Abbas lokacin yay man Maganar Auren ki, bazan 6oye maki ba lokacin duk da halin da nike ciki ban ji zan amince ba don ina ganin ba abu bane mai yuwuwa, ban dad'e da nayi Aure ba so nasan Matana da iyaye na bazasu amince ba, k'arshe da yake Allah ya k'addaro Aure tsakanin mu Abbas yay convincing ena ya tsara yadda za'ai, I guess you know everything about dat" kai ta jinjina mashi wani irin kallon tausayi mai had'e da tsantsar kauna take mashi, shima fuskar shi da d'an murmushi idanun shi a d'an lumshe yake kallonta shi kad'ai yasan irin nishad'in da yake ji a cikin zuciyar shi jin Zarah a jikin shi, cikin karyayyar murya tace mashi to miyasa bai saketa ba kaman yadda suka tsara, bin bakinta yay da kallo tana furta Maganar har ta gama yay d'an jimm yana ta kallonta hakan yasa Fatuu d'an motsa jikinta cike da shagwa6a tace yayi Magana mana, Slowly ya matsa da Fuskar shi ya had'e goshin su nan take yanayin fitar numfashin Fatuu ya canza ya koma fita da d'an k'arfi ta lumshe ido, shima nashi idon a lumshe yake kusan ma sun rufe wani irin yanayi mai dad'i suke ciki son junansu na sake sabuntuwa a cikin zuciyoyin su, sun d'an d'auki lokaci a haka suna inhaling sweet scent d'in juna, sai after some few minutes sannan ya d'ago da fuskar a hankali itama a hankali ta fara bud'e idanuwanta saidai ta kasa bud'e su gaba d'aya sun lumshe kaman yadda nashi ma suke a a d'an lumshen gashi sun k'ara cizawa, murya k'asa k'asa ya fara magana "after the marriage naji ban iya sakin ki and to my surprise tunda nasan kin zama tawa sai kawai na nemi ciwon da nike na rasa....." Dakatawa yay yana sakar mata wani k'ayataccen murmushi, itama murmushin take mashi, cigaba yay "if u can remember, akwae wani rana da muna Video call da kika ce ko kinga kaman face dina ya canza na tambaye ki mi yayi kika ce ya fad'a ko ban lafiya nace maki eh but na samu sauk'i, lokacin ina Tunanin bai fi 2 days dana dawo daga inda naje Seminar ba harna kwanta Medical bed" d'an jimm Fatuu tay alamar tunani nan take ta tuno lokacin bayan su gwaggo sun dawo ne tare da su yadikko har ta shiga d'akin Kawu Amadu suna cikin yin Vedio call d'in bacci ya d'auketa, da sauri ta maida idanunta cikin nashi tace "kenan lokacin ni Matar ka ce?" Ido ya lumshe mata still da murmushi akan Face d'in shi, murmushi tayi mashi ya kai hannu ya rungumota ta kwantar da kanta a chest d'in shi, shima kwantar da gefen fuskar shi yay suna kallon side guda,

"Lokacin dana maido Hajiya that's why I can't take my eyes off u, sosae nike jin dad'i a zuciyana in ina kallon ki, akwae wani lokaci da nayi maki Maganar ko zaki bini U.S a cikin Mota bansan ko zaki tuna ba....." Kai ta d'aga mashi alamar ta tuna, ce mata yay lokacin da gaske yake data amince zai tafi da itan alokacin ya yanke ya sanar ma Hajiya game da Auran, jin tana k'ok'arin d'ago kanta ta kalle shi yasa shi janye face d'in shi,

"To da na amincen ka tafi dani Aunty Fanan fa tunda nasan bata sani ba" a sanyaye tayi Maganar tana kallon shi, sigh yay yace zai kai ta wani wuri ne da bazata sani ba tunda lokacin ya fahimci bata son zuwa can Saboda Fanan d'in don akwae wani lokaci a baya sun ta6a Maganar yace ko zataje can taci gaba da karatu tace mashi Fanan d'in koro ta zata yi tace ta lik'e ma mijin ta,
daga baya in ya yi mata bayanin komai sai ta koma gidan su, ce mashi tay to karatun ta fa bacin tayi nisa yana murmushi yace mata acan ma ai ana karatun sai tayi kuma bai d'aukar lokaci kamar na nan, shiru kawai tay suna cigaba da kallon juna can ya d'age mata gira yace "Are u satisfied now that I love you?" Lumshe mashi ido tay irin yadda yake mata nan take ya gane kwaikwayon shi tay, murmushi yay slowly ya kai bakin shi saitin nata ya manna mata kiss, da sauri ta kauda fuskarta alamar kunya, Hannu ya kai ya juyo da Fuskar tata ya furta "is dat all u want know ko da wani abu?" had'e lips dinta tayi ta d'an d'age ido alamar tunani, kallon shi tay cike da shagwaba tace "to amman miyasa kake gudu na?" kafeta da ido yay yana mata wani kallo ba tare da yace komai ba, ganin haka yasa ta fara nazarin Maganar da tayin a d'an rud'e tace mashi tana nufin miyasa bai sake mata bayan ta tare in kuma don abunda tayi ne ai ta bashi hak'uri kuma yace ya hak'ura, wani irin murmushi taga ya saki aikuwa ta fad'a mashi ta cusa fuskarta cikin broad chest d'inshi tana fad'in itafa ba wani abu take nufi ba wllh, rungume ta yay tightly yana ji a ranshi kaman su dawwama a haka bayan ya kwantar da Fuskar shi saman gashinta a nutse ya furta "ba gudun ki nike ba Wife, I always need u badly, abunda ya faru a G.r.a nasan nima inada laifi duk da ban kai ki can ba don hakan Allah ne ya kaddara hakan zai faru, banyi fushi da ke ba kawai abu biyu ne ban ji dad'in su ba, farko yadda nayi maki nasan na cutar dake sannan kuma da kika zo sanar man u'r pregnant duk abunda kika fad'a man banji komai ba don nasan nayi maki ba daidai ba kawae abunda banji dad'in shi ba yadda nayi k'ok'arin dakatar dake amman kika k'i saurarana bazan 6oye maki ba banji dad'i ba kaman yadda na fad'a maki da kika zo bani hak'uri, hankali na ya tashi a lokacin ba kuma don rasa cikin ba sai don tsoron abunda zai iya faruwa dake I might lose u i thought to myself, hakan yasa na je na fad'i ma Hajiya duk da dama ina niyyar inje in fad'a matan Saboda abunda nayi maki.....Tun bayan da abu ya shiga tsakanin mu...Sai na sha drug nike iya bacci peacefully" lamo Fatuu tay cikin ranta ta shiga tunanin ashe Maganin data gani kenan Saboda haka yake shan shi, kai bakin shi yay saitin kunnanta cikin magana mai kaman rad'a yace mata yana gudun ta k'ara samun ciki ne yafi son sai dangin shi sun sani komai ya daidaita don yasan dole farko za'a iya samun matsala hakan kuma na iya sata a damuwa wanda ba'ason mai ciki tana damuwa k'arshe ma cikin zai iya k'ara zubewa wannan ne dalilinshi duk da yana cutuwa amman in itama ta cutu sai yafi jin ciwo, nan ya bata hakurin abunda su Hajiya Maryam suka mata ya nuna bai ji dad'i ba sosae amman insha Allah hakan ya wuce ba wanda zai k'ara mata, k'ank'ame shi Fatuu tay lokaci guda yaji sheshshekar kukan ta a cikin kukan ta fara bashi hak'uri kan tunanin da tayi ba daidai ba a kan shi da kuma wahalar daya sha saboda ita, gaba d'aya ta gama kashe mashi jiki, d'ago Fuskarta yay har tayi jage jage da hawaye, idanun shi a lumshe yake kallon ta sai kukan take itama tana kallon shi, girgiza mata kai ya fara kafin ya kai bakin shi ya fara kissing hawayen, jin tayi shiru yasa shi dakatawa ya d'ago hannu yana share mata fuskar, bayan ya gama yana murmushi ya tambaye ta ya akai ta fara son shi itada yasan ba komai a ranta sai son karatu ta zama Doctor, cikin muryar kuka ta fara bashi labari tana yi tana yar ajiyar zuciya, bata 6oye mashi komai ba tun daga kan yadda Haulat ta nuna mata son ta yake shiyasa yake hidima da ita har ranar ta tuna mashi daya tambayi Haulat d'in ko yau sun samu kud'i ne a school yaga tana cikin farin ciki tace mashi tun daga nan ta fara jin son shi, ta sanar mashi tun ranar da Aunty Fanan tazo ta gane abunda ke tsakanin su ta fara wahala akan son shi, a shagwabe ta furta "Wllh Ya Haisam nasha wahala....maimakon tunda nasan kana da wadda zaka aura in daina jin son kan amman zuciyata taita k'ara man son ka gashi kuma tasan ba samun ka zan yi ba....." Fuskarta sharkaf take Maganar, wani irin tausayin ta ne ke ratsa shi har idanun shi sun k'ara sauyawa, cigaba da goge mata kwallan yay yana fadin "I promise you that this is the last time you will ever have to cry because of me" bayan ya gama goge mata rungumeta yay, suna haka yake ce mata ai da ta sani daya kirata ya tambayeta abunda ke damunta ta fad'i mashi tace mashi to ai tasan k'arshen ta ya bata hak'uri kaman yadda ta fad'i mashi su Kawu Amadu da Haulat sun ce mata a labarin data bashi kuma shima ba gashi yace lokacin da Abbas yay mashi Maganar aurenta duk da yana sonta da farko bai amince ba" shiru yay yasan kusan hakan ne zai faru, shafa bayanta ya shiga yi ana fadin she should forget about d pass, saida yaji ta samu natsuwa sosae sannan ya d'ago fuskar ta yana murmushi ya d'an dage mata gira yace yanzu yaushe zata biya shi abunda tasa ya rasa kaman yadda ta fad'a, kunya ce ta kamata ta fara mutsu mutsun son 6oye fuskar ta amman ya hana sai dariya yake hakanan sai ta kasa ce mashi ba ita ta tura sak'on ba, k'ara maimaita mata tambayar yay da k'yar tace mashi yana so ne, kai ya jinjina mata idonta a d'an runtse tace to miyasa Aunty Fanan bata haihun mashi ba tunda dai yana so, d'an jimm yay yana kallon ta har saida tasha jinin jikinta, saida ya d'an d'auki lokaci sannan ya sanar da ita tana da problem ne daya hana hakan amman tana cikin shan Magani, wani iri Fatuu taji sai taji dama bata yi Maganar ba, a sanyaye tayi Addu'ar Allah ya bata lafiya ya amsa sai kuma yace "in bata haihun ba zaki bata kyauta cikin naki?" Da sauri ta jinjina mashi kai tace "dana haifi na farko ma zan bata" d'an bud'a ido yay yace mata to yaushe zata biya shin aikuwa da sauri ta kife fuskarta k'ok'arin d'agota ya fara amman ta k'ank'ame shi sosae sai yar dariya yake yi, tsit kake ji zuciyoyin su sai bugawa suke a tare kowanne ya rufe ido, sun dauki lokaci a haka kafin taji ya tambayi mi zata yi a cikin Laundry room daya ga d'azun ta nufi can, ce mashi tay wanka take son yi ba tare data d'ago ba, k'ok'arin d'agota ya fara yi yace "Ok, let me help u take the bath" da sauri ta k'arasa d'agowa ta waro ido tana kallon shi ya d'age mata gira aikuwa da sauri ta fara k'ok'arin sauka daga jikin shi nan take ya gane guduwa take son yi ko kafin ta ankare gaba d'aya ya mik'e tare da ita ya sa6ata a kan kafad'ar shi ya nufi Laundry d'in da ita sai faman wuwwuntsila k'afafu take tana fad'in don Allah ya bari zata yi da kanta shi abunma dariya yake bashi yana zuwa da k'afa ya tura kopar ta bud'e ya shige da ita..............(Wayyo! An yi magani na ina niyyar sa kai don d'aukko rahoto aka bugo man k'opa a goshi, maganina kenan mai son ganin sirrin ma'aurata)

....In zauna a bakin gado in jira su su fito, amman dai goshina ya bugu dama k'opar bata wasa bace.........Ina zaunen Fanan ta fad'o man arai, ko awane hali take baiwar Allah.

*ASM 074*

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*

........... After some minutes sai gashi ya fito da ita yayi mata irin d'aukar jarirai gaba d'aya ta duk'unk'une a cikin bathrobe,gado ya nufa da ita ya d'aurata aikuwa kaman tana jira da sauri ta jawo duvet ta lullube, zama yay a bakin gadon idon shi a kanta fuskar shi d'auke da k'ayataccen murmushi tunawa da yadda akai wankan, shi ganin hakan yake bak'on abu don koda Fanan tana Amarya bata yi mashi haka ba saidae kuma sosae yadda take nuna kunyar ke burge shi, jin shiru bata ji yayi Magana ba yasa tayi tunanin ko da ya ajeta tafiya yayi, a hankali ta sa hannu ta d'an janye bargon da nufin ta d'an lek'o taga ko tafiyar yay, karaf suka had'a ido aikuwa da sauri ta ja bargon ta maida Fuskar, Murmushi kawae yake saki can taji ya kira ta "Baby" runtse ido tayi tana dariya ta cikin bargon, dama tunda yana mata wankan taji ya fara kiran ta da haka, ji tay ya k'ara kiranta still idanunta a runtse suke ta amsa mashi, taji yace yanzu shi bazata taya shi yay wankan ba, dama tun a toilet d'in yaso suyi tare tak'i yarda harda yi mashi magiya kan hakan, ya lura sosae take jin kunya don da k'yar yayi mata wankan hakan yasa shi k'yaleta, k'ara yi mata magana yayi ta cikin lullubar ta girgiza mashi kai, sigh yay yace mata Ok shi ya saba sai an taimaka mashi yake yin wanka bari yaje wurin Fanan in tayi mashi sai ya dawo, wani abu taji a ranta jin motsin mik'ewar shi yasa ta raya da gaske yake kenan aikuwa da sauri ta d'ago dama yana tsaye bai tafi ba, inda yake tazo still tana kudundunan kawai sai ji yay ta kamo mashi riga, gaba d'aya ta cure a guri guda shi yadda tayi ma sai ya bashi dariya har jerarrun fararen hak'oran shi suka d'an bayyana,

"I will be back ai da an gama wankan" taji ya fad'a, da sauri ta girgiza mashi kai, d'an bud'a ido yay yace "kar in je?" Kai ta d'aga mashi, "Ok zaki taimaka man in yi kenan?" jimm ta d'an yi kafin a shagwabe tace "n...ni wllh Kunya nike ji" still dariyar yake dama wasa yake mata kawai komai nata nishad'i yake bashi ne, komawa yay ya zauna ya kai hannu ya janye duvet d'in Sumarta ta bayyana don ta kife fuskar a jikin mattress, bin ta yay da kallo cike da k'auna yana jin kaman don ita zuciyar shi ke beating, kiran ta yay ta amsa ba tare da ta d'ago ba yace tunda tana jin kunya zai k'yaleta yaje yayi amman har sai yaushe zata daina jin kunyar ta fara taimaka mashi wurin yin wanka, d'an jimm tay sai murmushi take zuciyarta ce ta tuno mata da zancen zuwa wurin Fanan da yayi kan tayi mashi wanka bata san lokacin data furta mashi gobe ba, jinjina kai yay yace promise ta d'aga mashi nata kan, ce mata yay to ta tashi ya taimaka mata ta shirya, girgiza mashi kai tayi murya can k'asa tace yaje yayi wankan zata shirya, hannu ya kai ya shafi sumar ta ya furta "Ok My Baby" daga haka ya mik'e, ta ji lokacin da ya tashi saida ta d'an bashi lokaci sannan ta d'ago ganin bata gan shi ba yasa ta tashi zaune ta juya hanyar laundry ta d'aga kai daidai zai tura kopar kawai sai gani tay ya d'ago mata hannu alamar yasan tana kallon shi, dariya ta saki ta maido kan ta k'asa,

tana jin k'arar rufe kopar shi cike da Farinciki ta runtse idanunta tana d'an k'ank'ame hannunta, wani irin dad'i take ji tamkar ta saki ihu haka take ji sai d'an rawa rawa take da jikinta, idanunta a runtse ta shiga tariyo yadda akai wankan, a laundry ya cire mata rigar jikinta da k'yar lokacin da ya zo kan bra d'inta k'ank'ame jikinta tay idanunta a rufe ta hau yi mashi magiya kan basai an cire su ba ayi wankan da su, ganin bazata bari ya cire su ta dad'i ba yasa shi had'e lips d'in su ya fara kissing nata deeply nan take jikinta ya saki a haka ya cire bra d'in, lokacin daya raba mouth d'in nasu ai ko ido bata iya bud'ewa nan ya cire sauran undies d'in hankali kwance sai sakin murmushi yake, saida ya cire mata komai sannan ya sa6eta yay cikin toilet d'in da ita, cigaba da imagination na abunda ya faru bayan sun shiga cikin toilet d'in tay har zuwa fara yin wankan......., da sauri ta bud'e idanunta ta dawo daga tunanin da take yi jin kaman a lokacin hakan ke faruwa, k'ayataccen murmushi ta shiga saki tana haka Mino ta fad'o mata a rai, ita sham ta manta da wata Mino ta raya a ranta har saida tay yar dariya, tunanin ko lafiya bata zo ba ta shiga yi zuciyarta ta bata k'ilan zata zo sai kuma tay tunanin ai bata kaiwa haka bata zo ba, tun tana a part d'in Hajiya tara saura tayi yanzu kuma tasan karfe goma bata rasa wucewa, to ko dai bata lafiya amman kuma fa d'azun suka rabu, wata zuciyar ta ayyana mata to ai yanzu yanzu sai Allah ko, yin wannan tunanin yasa ta mik'e tasa hannu ta ruk'e gaban bathrobe d'in, gaban dressing mirror ta nufa ta d'aukko wayarta ta dawo bakin gado ta zauna, Kawu Amadu tayi tunanin kira tasan yanzu yana shago, bayan ta fara ringing yay picking, gaida shi tay ya amsa tace mashi dama so take ta tambayi ko lafiya Mino bata zo ba, cikin d'an fad'a fad'a yace mata to ba mijinta ya dawo ba zuwa kwanan mi zata yi kuma, d'an jimm Fatuu tay a ranta tana mamakin ashe sun san ya dawo, kaman yasan tunanin da take taji yace d'azun yana shago yaga zuwan su Tk ya d'aukko su har tsayawa yay suka gaisa, amsa mashi tayi da to tay mashi saida safe, saman bedside ta d'aura wayar tay shiru, zuciyar ta ce ta raya mata to bazata tashi ta shiryan ba sai ya fito kuma yaga bata shirya ba tace mashi zata shirya da kanta, mik'ewa tay ta nufi gaban mirror cikin fargabar kar ya fito ta fara yin shafa, bayan ta gama mulke jikinta da mai ta d'aukko wata yar sauran Humra da ta rage mata ta fara shafawa cike da takaicin sauran da Farha ta fasa mata tana ta so ma tayi ma Aunty Mareeya Magana kan tana son wasu don Hajiya tace tayi magana a fad'i kud'in, bayan ta gama shafe shafen wardrobe ta nufa, bayan ta bud'e wurin kayan bacci ta kai hannu har zata d'aukko wasu zuciyarta ta raya mata ta sa cikin wanda Aunty Mareeya ta bata ko ajiyar su zatai tayi, can k'asa ta kai hannu ta jawo su, tunanin wadda zata saka ta fara zuciyarta ta sake bata ta saka pink d'in, d'an jimm tay tana kallon rigar a ranta ta raya anya Ya kamata ta saka karfa yayi mata kallon yar iska, zuciyarta ta sake raya mata taya zai mata wannan kallon tunda dai shima yasan rigar bacci ce kuma Aunty Fanan bata rasa saka irin su kuma su Aunty Mareeyar ba sun ce ta cire kunya ba, da wannan tunanin ta d'auki rigar ta nufi bakin gado, gaban ta sai fad'uwa yake don kar ya fito ya ganta, hannunta sai d'an rawa yake ta fara saka rigar bayan ta gama gaban Mirror ta nufa, koda taga kanta ba shiri ta kai hannu ta rufe bakinta alamar Al'ajabin ganin yadda rigar tayi mata don ba abunda ba'a gani na jikinta gashi ta bi jikin ta lafe da kad'an ta wuce mazaunanta don da zata duk'a ma sai an gan su, amman fa tayi mata kyau Over yadda daga wurin k'ugunta ya bud'e, d'an juyi tay tana murmushi ganinta take kaman ba yar Nigeria ba, ranta ne ya bata ta kwance gashinta ta gyara, gaba d'aya ta shagala da alama ma k'ilan ta manta da Maganar fitowar Haisam d'in, gaba d'aya gashin yayi mata rumfa ya saukko har kusan tsakiyar bayanta tasa Comb tana sharcewa, tana haka taji k'arar bud'e k'opa da sauri ta juya ta kai idonta kan Haisam da ke fitowa daga cikin Laundry, rud'ewa tay gaba d'aya da sauri ta nufi wurin wardrobe da nufin ta d'aukko abu ta rufe jikinta kafin ta k'arasa ta tuno duvet d'in dake akan gado aikuwa da gudu ta juyo ta nufi gadon tana zuwa ta haye taja Duvet d'in ta lullu6e, shigowa yay ciki yana yar dariyar ganin yadda ta dabarbarce k'ugun shi d'aure da farin towel ga wani short rataye a wuyan shi, gaban dressing mirror ya tsaya yana goge lemar wurin kan shi da sauran jikin, juyowa yay ya nufi hanyar k'opar fita idanun shi akan Fatuu data duk'unk'une guri guda, fita yay ba tare da ya kulle kopar ba, jin k'arar bud'e kopar yasa ta d'an bud'e fuskar ta lek'o, bai dad'e ba sai gashi ya dawo da sauri ta maida kan ta rufe, Wani babban trolley ya shigo dashi yana ja dama yana ajiye a cikin Corridor d'azun da ya baro part d'in Hajiya zaije sallar Magrib yasa Tk ya kawo shi, bakin wardrobe ya kai shi bayan ya bud'e wardrobe d'in ya fara fiddo kayan ciki yana jerawa ciki, bayan ya gama ya fiddo wasu mayuka da turarurruka ya kai su kan dressing mirror, cikin mayukan ya bud'e wani ya fara shafawa, a hankali Fatuu ke bud'e duvet d'in tana d'an lek'en shi, da taga kaman zai juyo sai tay sauri ta maida kan, bayan ya gama turare ya fara fesawa ya d'aukko roll on ya shafa a armpit, wani mai ya matso a tafin hannun shi ya kai shi jikin kwantacciyar sumar chest d'in shi ya shafe nan da nan ta k'ara kwanciya luff duk abun nan Fatuu na kallon shi, bayan ya gama data chest d'in ta saman kan itama ya matso man ya fara shafe ta da shi saida ya shafa kala biyu sannan ya d'auki comb yana sharce ta bayan ya gama Hair spray ya d'aukko ya hau feshe ta da ita, sakin baki Fatuu tay tana kallon ikon Allah ko ita batai shafe shafen da yake ba, bayan duk ya gama ya matsa man tafin hannu ya murza sannan ya juya ya nufi wardrobe ta zuba ma bayan shi ido gaba d'aya a murde yake, rigar bacci kimono ya fiddo ruwan Madara itama sabuwa ce dal tana ganin zai juyo ta maida kan, a gefen gadon ya d'aura rigar yana k'ok'arin kwance towel d'in ta lek'o karaf suka had'a ido a sukwane ta koma ya d'an girgiza kai yana murmushi, bayan ya gama saka rigar ya d'aure, d'aukar towels d'in yay ya had'a da bathrobe d'inta data cire ya nufi hanyar laundry, bada Jimawa ba taji k'arar fitowar shi, side d'in da take ya zagayo ya zauna a bakin gadon idon shi akanta, kiran sunanta da ya fara kiranta dashi wato Baby yayi tay shiru saida ya k'ara kiran sannan ta amsa mashi, hannu ya kai zai janye duvet d'in ta k'ank'ame shi, Dariyar naki wasa ne yay ja d'aya yay mashi ya janyo shi, sosae ta k'ank'ame jikinta idanunta a runtse tana kallon gefe, hannu ya kai ya kamo hannunta guda ya d'ago da ita still idanunta a rufe suke, zuba mata ido yay yana bin jikinta da komai yake a bayyane da kallo kafin ya tsaida idon shi akan boobs d'inta dat look firm and pointed, kiran sunan ta yay da k'yar ta amsa yace ta bud'e ido ta kalle shi kaman bazata bud'en ba sai kuma ta dan bud'a su d'an kad'an har saida ta bashi dariya, d'age mata gira yay yace "didn't u wear it for me to see?" d'an jinjina mashi kai tay yace "then why are u hiding it from me?" yamutsa fuska tay da ido tay mashi nuni da fitila alamar haske, still yar dariya yake ganin da tsiya ta maida kanta kaman yar makauniya, sakin hannunta yay ya mik'e da sauri ta koma ta kwanta taja duvet d'in, wurin Switch ya nufa ya latsa hasken fitilun d'akin suka d'auke, dawowa yay side d'in da take kwance ya kashe lamp d'in wurin kafin ya juya ya zagaya d'ayan side d'in, bai kashe lamp d'in wurin ba ya barta a kunne amman ya rage haskenta ta yadda ta d'an haska d'akin, tana jin ya hawo saman gadon gabanta ya d'an fad'i ta runtse idonta, kwanciya yay ya d'aura kan shi saman pillow idon shi a kanta yana kallonta Fuskar shi d'auke da Murmushi, tsit kake ji ba mai motsi a cikin su saida aka d'an d'auki lokaci sannan ya matsa tsakiyar gadon, hannu ya kai ya janye duvet d'in kafin yay pulling d'inta ya had'e ta da jikinshi ta yadda Fuskarta na a saitin wuyan shi, sosae gaban Fatuu ya shiga fad'uwa sai kace wannan ne karo na farko da hakan zai kasance a tsakanin su, duk'o da Fuskar shi yay ta had'e da tata breathing d'in su ya shiga had'uwa, sun d'an d'auki lokaci a haka sai shak'ar daddad'an k'amshin juna suke can taji muryar shi k'asa k'asa yace "Baby, are u ready to make ur husband happy" k'ara runtse idanunta tayi sosae jin saukar hucin Maganar akan Fuskarta ga wani irin k'amshi da bakin nashi ke saki na Mouth freshener daya fesa acikin Laundry, da k'yar ta jinjina mashi kai, foreplay ya fara yi mata cike da salon gwanancewa nan take Fatuu ta fara losing mind dinta idanunta a runtse gam gasping heavily for breath sai d'an jan yar ajiyar zuciya, gaba d'aya jikinta ya saki sosae take savouring every bit of abunda yake mata, da kan shi ya fara nuna mata abunda yake son tayi mashi da k'yar ta fara maida mashi martanin ganin yana nuna mata yana enjoying sosae yasa ta d'an k'ara k'aimi nan take ya fara rasa control har ta kai ya zame hannuwan rigar jikinta ya saukko da ita wurin k'ugunta, a wannan lokaci gaba d'aya Fatuu d'imaucewa tay cikin fitar hayyaci take maida mashi martani hakan yasa shi rikicewa suka kacame ma juna and he got her all wet, sun d'auki tsawon lokaci suna faranta ma juna cike da tsantsar k'auna, daga baya ya fara kokarin getting in to her bayan ya karanto Addu'ar yin hakan, runtse idanu Fatuu tay sosae jikinta ya hau kerma ta fara jan numfashi duk da isn't the First time sosae take jin zafi shi kanshi Haisam d'in saida yayi Mamaki a hakan ma don akwae wetness sosae, gaba d'aya Fatuu gigicewa tay tun tana breathing rapidly da sakin nannauyar ajiyar zuciya har ta koma kiran sunan shi cikin fitar hayyaci ita kanta bata san mi zata ce mashi ba gaba d'aya Al'amarin yana nema yafi k'arfin kanta she's feeling like her heart is about to burst with joy k'arshe ma sai ta fashe da kuka, shima dae uban gayyar idon shi a runtse yake gam breathing heavily, he completely lost his mind har ta kai ya fara sakin layi.........,

Lokacin da suka samu natsuwa kife face d'in shi yay a saman tata ba tare daya raba jikinsu ba both of them were breathing rapidly, jikin Fatuu sai kerma yake don ba k'aramar jigatuwa tayi ba, cikin wata irin murya da bata san shi da ita ba taji ya fara fad'in "Thank u...thank u so much wife, thank u for coming in to my life Zarah.....I'm very proud of u, You have been a blessing...." Sai faman nishi yake, ba sosae take comprehending nashi ba idanunta a runtse gam, ji tay abu mai d'umi na d'iga akan Fuskar ta kaman ruwa, tunanin miye ta shiga yi da k'yar ta bud'e idanunta da sukai mata nauyi don ba K'aramin kuka tasha ba, lokacin ta fahimci kaman k'walla ne ta d'ago hannunta da ba k'wari ta sak'a shi tsakanin Fuskokin su ta ta6a fuskar Haisam nan take ta tabbatar da k'wallan shi ne duk da halin da take ciki saida ta d'an rud'e don abu ne da bata ta6a gani ba, murya a disashe ta fara ce mashi "Ya Haisam pls stop crying...." Shiru bata ji yace komai ba hakan yasa ta cigaba da yin kukan itama, d'ago Fuskar shi yay can k'asan mak'oshi ya furta mata ya bari, ya fara k'ok'arin raba jikin su har saida Fatuu ta d'an gantsare ya mirgina gefe, hannu ya kai ya matso da ita they were both nicked yay wrapping nata a jikin shi ta yadda ha6ar shi ke akan sumarta da ta gama fita hayyacin ta itama, shiru kake ji kowa da abunda yake rayawa a cikin mind d'in shi har lokacin da d'an k'arfi suke breathing, Haisam sai sakin k'ayataccen murmushi yake shi kad'ai yasan irin nishad'in da yake ciki, Zarah ta kai shi wata duniya da bai ta6a zuwa ba sai yau, mutsu mutsu yaji ta fara yi ya d'ago kanshi ya kai bakin shi saitin kunnanta ya tambayi miye ko tana son wani abu ne cike da tsantsar k'auna ya furta Maganar, juyo da Fuskar ta tayi suka had'a ido da sauri ta maida kan k'asa k'asa tace mashi fitsari take ji, Ok ya furta da sauri ya tashi da yake akwae d'an haske bai sha wahalar gano rigar shi ba, bayan ya saka ya saukko daga saman gadon ta bangaren da take har lokacin tana kwance kunyar tashi take, hannu ya kai zai d'agota cike da shagwa6a tace mashi bafa kaya a jikinta, murmushi kawai yay ba tare daya ce komae ba ya d'aukko ta ya nufi hanyar laundry da ita duk ta k'ank'ame shi, sun d'an d'auki lokaci kafin ya fito da ita jikinta d'aure da towel kanta ma an yafa wani short ta rufe fuskarta dashi, a bakin gadon ya ajeta ganin tana yar kerma ya juya yaje ya rage Ac tare da kunne d'ayar lamp d'in d'akin ya k'ara haske, dressing mirror ya nufa ya d'aukko man da yake amfani da shi ya dawo, a gefenta ya zauna ya kai hannu ya curo towel d'in saman kanta ya fara goge mata jikinta duk da ma ba wata lema Saboda bayan an yi wankan sun tsaya a Laundry ya d'an mata drying gashinta da hand dryer, gaba d'aya ta kasa had'a ido dashi saidae wani irin dad'i take ji a cikin ranta sosae take ta mamaki, who thought hakan zata kasance tsakanin ta da ya Haisam gaba d'aya ta fidda ran samun shi sai gashi cikin iko na ubangiji bada jimawa ba ta mallake shi sun zama abu d'aya ita da shi Allah mai yadda yaso a lokacin da ya so, ana ta ce mata tayi hak'uri tayi hak'uri zata ci riba sai gashi har taci ribar ba tare da an d'auki dogon lokaci ba, sai faman sakin murmushi take tana juyar da fuska bata san duk yana ganin ta ba shi kan shi murmushin yake, bayan ya gama da kan shi ya shiga shafa mata mai a jiki, mik'ewa yay ya nufi dressing mirror don ya maida mai ta juyo tana kallon bayan shi abubuwa na dawo mata da suka faru lately, bayan ya aje wardrobe ya nufa ya bud'e a wurin kayan ta ya fiddo wata doguwar riga tare da gyalenta ya dawo ta kauda idon ta gefe, bayan ya koma ya zauna yana k'ok'arin zura mata ta d'an kalle shi tace ya bari ta saka, yana ta kallonta tasa ta d'aure kallabin bayan ta gama ta maida kanta gefe, hannu ya kai yay tapping shoulder d'inta ta juyo ta kalle shi idanun ta adan lumshe d'age mata gira yay yace "bacci ko" kai ta d'aga mashi ya matsa ya rungumota jikinshi ta lumshe ido, shima nashi a d'an lumshen suke fuskar shi d'auke da d'an murmushi, Slowly taji ya fara magana in whispering "Baby na wahalar dake ko?" Kai ta d'an girgiza mashi, still da murmushi akan fuskar shi yasan ta fad'a ne kawae yace "am so sorry it was never my intention, I just wanted to make u forget about all the pain I caused you" shiru tayi sai kuma cikin disasshiyar murya yaji tace ai ba laifin shi bane yana murmushi yace amman ai dalilin shi ne, shiru suka d'an yi can ya tambayeta to yayi nasarar yin hakan nan ma kai ta d'aga mashi kafin tace ai tun d'azu ma daya bayyana mata yana sonta ta manta da komai, daga jin yadda tayi Maganar bacci ya fara cin k'arfinta, jin saukar numfashinta a hankali yasa shi kiran sunanta shiru bata amsa ba, d'ago Fuskarta yay yaga tayi bacci, bin Face d'in yayi da kallo, tunda yake bai ta6a ganin mutumin da komai nashi ke burge shi ba irin ta, tun farkon sanin shi da ita abubuwa da yawa a tattare da ita ke burge shi, kai bakin shi yay ya manna mata kiss akan lips d'in ta ya Furta "I love u so much Zaraah" yana rufe baki kawai sai gani yay ta d'an bud'e idanun ta cikin muryar bacci ta furta "I... love you...so much Ya Handsome" daga haka idanun suka rufe bakinta a d'an bude, faffad'an murmushi yay da alama acikin baccin taji Maganar da yayi sama sama shine itama ta maida mashi ta kuma kira shi da Handsome, Kwantar da ita yayi yaja duvet ya rufe mata jiki, saida ya yi pecking gefen fuskar ta sannan ya mik'e ya nufi toilet, bayan ya fito wardrobe ya nufa ya fiddo wasu kayan baccin riga da wando masu taushi ya saka, bayan ya gama ya nufi side d'in da take ya kashe fitilar daya kunna sannan ya nufo d'ayan bangaren gadon, bayan ya hau matsawa yay kusa da ita ya janyo ta yay cuddling nata sosae kaunarta na ratsa ko ina na jikin shi idanun shi a lumshe ya shiga tariyo abunda ya faru tsakanin su haka yay ta sakin murmushi kaman wani zautacce. Kiran sallar Asuban farko ya farka duk da baccin bai ishe shi ba saidae ya riga ya saba da lokacin yayi yake tashi, bayan yayo Alwala ya fito Wardrobe ya nufa ya d'aukko jallabiya ya canza kayan jikin shi, prayer mat ya d'aukko ya shimfid'a ya kabbara raka'atanil fajr, bayan ya gama mik'ewa yay yaje ya d'aukko Al'qur'ani ya dawo ya shiga karantawa, har saida lokacin salla yayi sannan ya mik'e ya maida Al'qur'anin, kallon Fatuu dake ta shan bacci yay da murmushi yasan dole tayi bacci sosae, saida ya duk'a yay pecking kumatun ta sannan ya tafi. Har ya dawo ko juyawa bata yi ba tana a yadda ya barta, gefen da take ya nufa ya zauna idon shi akanta yana jin kamar kar ya tasheta to amman lokacin ya dace tayi sallar, bayan ya tashe ta da k'yar ta bud'e ido tana kallon shi yace mata ta tashi tayi sallar saita koma ta d'aga mashi kai, sosae taga safiyar tayi saurin yi, saida ya rakata har toilet tayo Alwala sannan suka dawo, a gefen gado yasa ta zauna ya tambayi inda Hijabs d'in ta suke ta fad'i mashi ya nufi wardrobe d'in tana ta kallon shi sosae kulawar da yake nuna mata ke k'ara dulmiyar da ita acikin k'aunar shi, bayan ya kawo mata Hijab d'in tasa ta kabbara sallar ya juya ya fita daga d'akin, har ta gama bai dawo ba ta mik'e ta d'auke abun sallar, gado ta nufa ta haye taja Duvet ta lullube, shiru tay ta fara tunanin ko ina ya tafi da sassafe zuciyar ta ce ta raya mata k'ilan wurin Fanan ya tafi, shiru kawai tay ita kanta bazata iya fad'in mi take ji ba, bata dad'e da kwanciya ba idanunta a rufe taji an bud'e kopar da sauri ta bud'e idon tana ganin shi ta d'an ji wani sanyi a ranta, shigowa yay hannun shi ruk'e da d'an Babban try ya nufi gadon, aje tray d'in yayi a k'asa ya zauna bakin gadon yana kallonta itama ta juyo tana kallon shi, hannu ya mik'a mata yace ta tashi taci Abinci yasan dole tana jin yunwa yanzu, kama hannun tayi ta tashi ya matso da ita gefen shi, cup d'in tea ya d'aukko ya mik'a mata ta amsa ya d'ago da plate mai d'auke da wainar kwai ya aje a tsakiyar su, da kan shi ya 6allo wainar ya kai bakinta ta bud'e ya saka mata ta d'an kur6i tea din, bayan ta cinye na bakin ta ya 6allo wata zai saka mata tace "did u made it for me?" Fuskar shi a sake ya lumshe mata ido, bayan ta cinye ta bakinta daya saka mata ta furta mashi "thanks, I appreciate" d'an bud'a ido yay yana murmushi yace "I appreciate too" da d'an alamun mamaki tace What, shiru kaman bazai ce komai ba ya k'ara bata wainar, ganin tana ta kallon shi ya d'age gira ya furta "Yesternight" da sauri ta d'an juyar da fuskar ta, har mamaki take a cikin ranta yadda shi kwata kwata bai jin kunyar ta sai kace ba itace hakan ke faruwa tsakanin su ba, itama fara bashi tay yace ai ita kad'ai ya had'a mawa shi bai cin Abinci da sassafe ta tura mashi baki a shagwabe tace to ai shima tasan yana jin yunwa ko, bin ta kawae yake da ido gaba d'aya in tana shagwabe melting heart d'in shi take tun ba yanzu ba, dole ya bud'e baki ta rink'a bashi har suka cinye, mik'ewa tay don ta kai kayan Kitchen yace ta bari ya kai ta mak'e mashi kafad'a yay yar dariya, juyawa yay yana kallonta ta nufi hanyar fita tana kaiwa k'opa ta juyo suka had'a ido ta sakar mashi murmushi k'asa k'asa ta furta "I love u" ta fuce da sauri, mik'ewa yay ya nufi Laundry don ya wanko hannuwan shi yana ta sakin k'ayataccen murmushi, lokacin daya fito daidai ta shigo don saida ta wanke kayan, tsayawa tay daga bakin kopar tana kallon shi ya k'araso wurinta ba zato kawae taga yayi mata d'aukar jarirai har saida ta saki yar k'ara don abun yazo mata a bazata, a kan gado ya d'aurata ya dawo ya rufe k'opar, hawa yay saman gadon ya matsa kusa da ita ya jawota jikin shi, bin juna sukai da kallo da d'an murmushi na wani lokaci fuskokin su na a saitin na juna inhaling each others breathe, can ta fara motsa baki kaman tana son cewa wani abu, ya lura yace mata mi take son ce mashi ne, a hankali tace so take ta tambaye shi bai yin mamaki, murmushi yay ya d'age gira yace mamakin mi, tace "wai mune muka zama ma'aurata" da k'yar tayi Maganar yay yar dariya kafin ya d'an girgiza mata kai yace "ai ba abun mamaki bane baby, a rayuwa there is reason for everything, Allah ya k'addaro dama zamu zama married couple shine dalilin had'uwar mu and I blessed it" lumshe ido tay, slowly ya had'e face d'in su ya kai lips d'in shi kan nata he started kissing her deeply, sosae ta bashi had'in kai suka shiga ba juna hot romances a haka bacci yay awon gaba dasu.......

Jama'a ina Baiwar Allah Fanan🤔

*ASM 075*

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*

............Sosae suka sha Bacci Haisam ne ya fara tashi wurin k'arfe goma, toilet ya wuce yayo wanka, bayan ya fito ya shirya cikin k'ananun kaya wanda da gani sababbi ne sai baza k'amshi yake, bayan ya gama shiryawa ya koma bakin gadon yana kallon Fatuu dake ta shan bacci gashinta duk ya tarwatse har ya d'an rufe mata fuska, murmushi yay ya juya ya nufi k'opa ya fita,

Fanan kwance akan gado ta lullu6e da bargo tana bacci, she spent almost the whole Yesternight pacing up and down acikin d'akin, gaba d'aya zuciyarta ta hana mata zaman lafiya wani irin zafin rad'ad'i ta rink'a mata, she wept until there were no tears left, haka tay ta kai da kawowa kota kwanta tana son tayi bacci sai tay ta imaginations kan Haisam da Fatuu dole ta tashi, sosae ta jigata baiwar Allah har salla taso tayi amman ta kasa k'arshe a fili ta rink'a d'aga hannu tana rok'on Allah da ya sauk'ak'a mata abunda take ji fuskarta a yamutse, saida akai sallar Asuba bayan ta gama tayi Addu'oi sosae ta koma gado ta kwanta, ta d'an d'auki lokaci kafin cikin sa'a baccin ya d'auketa. Part d'in Hajiya ya zo lokacin da ya shigo ba kowa a parlon ya wuce hanyar corridor, Bedroom d'in Hajiyar ya nufa lokacin da ya shiga tana zaune a bakin gado tana shafa mai jikinta sanye da doguwar riga bata dad'e da fitowa daga wanka ba, bayan ta amsa mashi sallamar da yayi ya nufi inda take, a gefenta ya zauna Fuskar shi cike da annuri ga wani fitinannan k'amshi da yake saki, gaisawa sukai tayi mashi an tashi lpy ya amsa daga baya ta tambayi Fateema yace mata tana bacci, yar hira sukai sama sama kafin ya tashi yace bari ya ga Fanan tace to,

A hankali ya tura k'opar d'akin da take ya shiga, a kan gado ya hangota ta duk'unk'une a cikin bargo, saida ya k'arasa gaban gadon yaga Fuskarta a d'an bude idanunta a rufe alamar bacci take, tsaye yay yana kallonta tun daga yanayin fuskar ya fahimci she isn't alright don Fuskar ta yi wani ja, ta cikin baccin k'amshin turaren shi ya fara kai mata, motsi ta fara yi ta fara bud'e idanunta a hankali, bayan ta bud'en bin juna sukai da kallo her eyes were red and swollen yana gani ya fahimci ba K'aramin kuka ta sha ba, yunk'urawa tayi ta tashi zaune ta kasa d'auke idanunta akan shi zuciyarta sai sak'a mata abubuwa da ke k'ara mata rad'ad'i take, wasu k'walla ne masu zafi suka taho mata jin zasu zubo yasa tay saurin sauke idanunta k'asa, gefenta ya matso ya zauna ya kai hannu ya matso da kanta saman kafad'ar shi sai sheshsheka take a hankali, shiru Haisam yay ya d'an rufe ido can ya bud'e ya juya yana kallon saman kanta, gently yace mata miyasa zata sa damuwa haka a ranta sai tayi causing mata wani ciwo, da damuwa akan fuskar shi yay Maganar don ba K'aramin tausayi ta bashi ba, cikin muryar kuka tace ita kanta ba yadda bata yi ba don kar ta damu amman zuciyanta ta takura mata ko bacci bata yi ba sai da Safe nan ta d'an samu ya d'auketa, daga jin yadda take futar da Maganar zaka Fahimci she's in serious grief, shiru yay he wished he could remove all the pain from her heart, a hankali ya kwantar da gefen fuskar shi a saman kanta cikin nuna damuwa yace "Am very sorry Sweetheart am not happy I caused you so much pain" d'an girgiza mashi kai tay suka yi shiru kowa yana kallon wuri guda can yay sigh ya d'ago itama ta d'aga kai tana kallon shi, tambayar ta yay tayi breakfast ta d'an girgiza mashi kai ya furta Ok bari ya kawo mata, yana k'ok'arin tashi ta kama hannun shi a marairaice tace mashi wanka take so tayi ko zata ji dad'in jikinta, mik'a mata hannu yay ta saukko daga saman gadon suka nufi Toilet. Bayan wani lokaci suka fito yana tallafe da ita k'irjinta d'aure da towel, taimaka mata yayi ta shirya cikin doguwar riga da hula ta zauna a bakin gado yace mata yana zuwa ya juya ya nufi k'opa ta bi bayan shi da kallo Zuciyar ta na raya mata abu game da shi da Zarah, k'walla ne suka shiga gangaro mata ta d'age kai sama, yana fita cikin parlor ya had'u da Hajiya ta fito yin Breakfast yay mata Magana kan yana son breakfast zai kai ma Fanan kai kawae ta d'aga mashi ta nufi Dining ya bita, bayan Saude ta zuba mashi ya juya ya koma, Magana Hajiya tay ma Saude kan ta had'a ta kai masu nasu can part d'in su tace to, bayan ta gama Serving nata ta juya Kitchen don ta had'a masu.

A hankali Fatuu ta fara motsi kafin ta fara bud'e idanunta, hannu tasa ta janye gashin daya rufe mata fuska har saida ta d'an ji mamaki ganin ba Haisam kaman yadda suka kwanta tare, tunani tay k'ilan yana toilet tay shiru tana kallon wuri guda sai faman zabga murmushi take da gani tana cikin tsananin farinciki, can ta yunk'ura ta tashi Zaune ta jingina da Headboard, memory d'in rayuwar su ya shiga dawo mata sai faman sakin murmushi take, sosae take mamakin yadda komai ya kasance a tsakanin su, ta d'an d'auki lokaci a haka ganin shiru bai fito ba yasa ta fara tunanin ko dai bai cikin toilet d'in ne, saukkowa tayi ta nufi hanyar laundry tana gab da isa k'opar taji anyi knocking kopar Bedroom d'in, juyowa tayi ta nufi kopar ta tsaya a bakin ta, tambayar waye tayi ta jiyo Muryar Saude da sauri ta kai hannu tana tattare gashinta bayan ta d'aure ta kai hannu ta bud'e kopar, da d'an murmushi ta gaidata itama murmushin take mata ta amsa tace "Amaryar mu an tashi lpy, dama Breakfast na kawo ba kowa a parlon to da yake naga shi yalla6ai d'in a can shine nace bari in fad'i maki" still Murmushin take tace mata to kafin tayi mata godiya sukai sallama, bayan ta dawo cikin d'akin a gefen gado ta Zauna tay shiru kaman mai tunanin wani abu, ta dan d'auki lokaci can ta mik'e sukuku da ita ta nufi hanyar laundry, after some minutes ta fito jikinta sanye da bathrobe ta nufo cikin d'akin, shiryawa ta shiga yi bayan ta gama yin shafa ta nufi Wardrobe, saida ta d'an yi ruwan idon kafin ta fiddo wata doguwar rigar shadda kalar butter an yi mata red aiki, bayan ta gama shiryawa gaban mirror ta koma ta fiddo jewellery da suka hau da kayan ta saka, k'ara gyara fuskarta tayi ta goga jan jambaki ta goga maskara a gashin idonta ya k'ara mik'ewa gazar gazar kaman ta saka eyelashes, bata yi ja gira ba sai kawai ta gyara gashin don tana dashi da d'an yawa, ita kanta taga kyaun da tayi tana Fesa turare tana k'are ma kanta kallo da d'an murmushi, bayan ta gama komai komawa tay bakin gado ta zauna bata yi tunanin zuwa tayi breakfast d'in ba don ba wata yunwa take ji ba,

Bayan ya kai mata Breakfast d'in da kanshi ya shiga bata a baki sai gashi ba laifi ta d'an ci da yawa kafin ta ce mashi ta k'oshi, kokarin mik'ewa tay tace bari ta fidda kayan ya rigata tashi yace ta zauna tana murmushi ta furta mashi thanks ya d'an lumshe mata ido, har ya kusa k'opa tace don Allah ya tambayi Hajiya in akwae paracetamol ya d'aga mata kai, bai jima ba ya dawo hannun shi ruk'e da glass of water ya nufi wurinta, da kan shi ya 6allo mata Maganin ya bata ta sha bayan ya d'aura glass cup d'in akan bedside drawer da Maganin ya d'aura idon shi akan ta cikin nuna kulawa yace "Your sacrifice means the world to me, it's the most generous thing anyone has ever done for me" daka kalli idanuwan shi zaka tabbatar da abunda yake fad'i, d'an murmushi tayi ta d'aura kan ta a saman shoulder d'in shi slowly ta furta "I can do anything for you my husband" lumshe ido yay fuskar shi d'auke da Murmushi, gyara zaman shi yay ya hau gadon sosae ya kwantar da kanta a saman cinyoyin shi fuskar ta na kallon shi tana mashi murmushi ya fara d'an shafa kumatunta can yaji tace "I love u so much babe, don Allah kar canza man zan iya mutuwa wllh" idanunta raurau tayi Maganar, lumshe mata ido yay ya furta " I will never forget how much you have done for me sweetheart" lumshe ido tay still da murmushi daga yanayin fuskar ta zaka fahimci ta samu sauk'in abunda take ji a cikin zuciyar ta, cigaba da shafa fuskar tata yay can ya d'an d'age kan shi sama ya lumshe ido nan take memory d'in shi da Fatuu ya shiga dawo mashi fuskar shi d'auke da d'an murmushi yayin da Fanan ta fara yin gyangyad'i daga baya bacci ya d'auketa.

Tana ta zaune a bakin gadon ji take kaman taje part d'in Hajiyar saidae wata irin kunya take ji, tunanin gyara d'akin tayi ta mik'e, wani sabon Bedsheet taje ta d'aukko a cikin Wardrobe ta dawo ta cire na saman gadon da na pillows d'in ta fara shimfid'a wanda ta d'aukko, bayan ta gama laundry ta nufa ta d'aukko floor wiper tazo ta fara share dakin, data gama ta maida ta d'aukko bucket d'in Mopping ta dawo, tana cikin yin Mopping d'in har ta kusa gamawa taji an turo k'opar Bedroom d'in ta kai idonta da sauri, shine ya shigo suka had'a ido nan take zuciyarta ta shiga raya mata daga wurin Fanan yake, ganin yana mata murmushi yasa ta d'an yi murmushin itama, rufe kopar yay ya nufo inda take tsaye hannunta ruk'e da mop, a gabanta ya tsaya ya kai hannu ya ruk'o mop d'in ta sakar mashi, janye bucket d'in yay gefe ya kai duka hannuwan shi ya matso da ita gaban shi idonta a kanshi, ganin ta d'an yi mashi k'asa yasa shi rankwafawa ya had'e goshin su slowly yace mata waya sata yin wannan aikin yanzu, shiru bata ce mashi komai ba ya d'ago da fuskar shi yana kallon ta ya d'an d'age mata gira, da d'an murmushi tace mashi taga bata yin komai ne kuma d'akin na buk'atar a gyara shi shiyasa, tunda ta fara Maganar ya maida idon shi akan bakin ta daya sha jan jambaki har ta gama, ganin yadda ya kafe ta da ido ba tare daya ce komai ba yasa ta d'an tura mashi baki ya saki murmushi, juyawa yay da ita suka nufi wurin gado, shi ya fara zama sannan ya zaunar da ita kan cinyoyin shi ta yadda fuskokin su suka kusa yin saiti, shiru sukai gazing lovingly into each other's eyes kowa kokarin nuna ma d'an uwanshi yadda yake k'aunar shi suke ta cikin idanun, kasa jurewa Fatuu tay tana murmushi ta kwanta a jikin shi idanunta a d'an lumshe tana shak'ar daddad'an k'amshin da jikin na shi ke saki, hannuwan shi yasa ya rungumeta sosae ha6arshi a saman kanta taji ya furta tayi kyau sosae still Murmushi take ta furta mashi ta gode shima yayi kyau, shiru suka k'ara yi tayi lamo idanunta a rufe she felt safe in his embrace, suna haka taji Muryar shi yana tambayar tayi Breakfast ne ta d'an girgiza mashi kai alamar a'a, d'agota yay gaba d'ayan su idanuwan su sun d'an lumshe yace "miyasa zaki zauna da yunwa ko kina so ulcer ya kama man ke?" yay Maganar tare da d'age mata gira, yar dariya tayi don ta gane abunda take ce mashi ne yace mata da sigar shagwa6a tace to ba shi take jira ba, "Ok, kiyi hak'uri na bar ki da yunwa naje gaida Hajiya da Auntie d'in ki" jinjina mashi kai tayi ya kai bakin shi saitin nata ya manna ma lips dinta kiss, yana d'agowa ta d'an waro ido sai kuma ta saki dariya tambayar ta yay miye tace ya gogi jan bakin ta ganin abun ya saka ta nishad'i yasa shi kai hannu ya matso da kanta ya kad'e lips din nasu giving her a deep kiss, sun d'an d'auki lokaci kafin ya saki kan da k'yar take bud'e ido koda taga yadda bakin nashi yayi da jan bakin sosae ta sa dariya harda k'yak'yatawa sai kallonta yake yana yar dariyar shima sosae take burge shi, can ta kai hannu ta fara goge mashi tana yi tana k'ara sakin dariyar suna cikin haka ya mik'e da ita yay mata d'aukar jarirai har lokacin tana goge mashi bakin ya nufi hanyar k'opa da ita don suje suyi breakfast.

Bayan sun gama yace su je ta gaida su Hajiya tace to, Bedroom ta koma ta d'aukko gyale bayan ta fito a corridor ta tsaya tasa takalma sannan ta dawo yana zaune a cikin parlor yana ganin ta ya mik'e yana mata murmushi ya kama hannunta suka tafi, suna zuwa k'arshen hanyar da zasu shigo cikin harabar gidan ta zame hannunta ya juya ya kalleta ta d'an yamutsa mashi Fuska, murmushi kawai yay baice komai ba don ya fahimci dalilin daya sa tayi hakan, lokacin da suka shiga cikin parlon Hajiya na zaune suka nufe ta idonta akan su tana murmushi, Haisam d'in ya nuna mata wuri ganin tayi tsaye ta zauna shima ya zauna a gefenta duk sai taji wani iri, da k'yar ta gaishe da Hajiya don duk ta sha jinin jikinta gani take kaman duk ansan abunda ya faru tsakanin su, bayan d'an wani lokaci ta mik'e tace bari su gaisa da Aunty Fanan Hajiya tace mata to, bata dad'e ba ta dawo idon Haisam a kanta ta koma ta zauna tun kafin tayi Magana Hajiya tace halan bacci take tace mata eh, kallo suka d'an yi daga baya Haisam d'in ya mik'e yace zai je ya dawo Hajiya tayi mashi a dawo lafiya ya nufi hanyar fita idon Fatuu a kan shi sai kuma ta juyo ta kalli Hajiya ganin ta maida idon ta akan Tv yasa ta mik'e sumi sumi ta bi bayan shi, lokacin da ta fita har ya nufi hanyar parking space ta kira shi da d'an d'aga murya ya dakata ya juyo, tana k'arasowa ta tsaya a gaban shi tana murmushi yace ai ya zata bazai ai mashi rakiyan ba, bata ce komai ba ya kai hannu ya kamo hannunta har saida ta d'an waiga bayanta suka nufi parking space, bakin Motar da zai hau suka tsaya ya tambayi ko tana son wani abu ta girgiza mashi kai ya furta Ok, saida yay kissing hannun nata sannan ya saki ya bud'e Motar ya shiga ganin tayi tsaye yace mata ta koma ta d'aga mashi kai alamar to amman bata da niyyar tafiyar, Maganar Hajiya ce ta fad'o mata a rai ta kwanaki data ce in itace abunda ya gani k'arshe to zaita tunaninta a waje har yay ta sakin murmushi kamar zautacce, k'ara ce mata yay koda wani abu dai ta d'aga mashi kai alamar eh yace to miye ko ya fito ne, da sauri ta girgiza mashi kai ta fara matsawa, tsaye tay gaba dashi tana ta faman murmushi, d'age mata gira yay ya d'an k'ank'ance ido yace "What do you want?" tsuke baki tay sai kuma ta runtse ido da hannu tay mashi nuni da kumatun ta, lokaci guda ya gane mi hakan ke nufi yace "Do you want to kiss me?" ba tare data bud'e idon ba ta d'aga mashi kai kawai sai ji tay ya kamo ta ya shigo da ita cikin Motar yana k'ok'arin zaunar da ita akan cinyar shi da sauri ta fara k'ok'arin kwacewa yak'i sakin ta ganin haka yasa a marairaice tace mashi wani fa zai iya ganin su ya d'age mata gira yace to shine mi, k'arshe ba yadda zata yi dole ta zauna idanun shi a lumshe yace tay kissing nashi iya yadda take so a kuma duk inda take so........

Bayan ta koma parlor duk ta bi ta kama kanta Hajiya tace ya tafi ta ce eh, bata dad'e da komawa ba Mino tazo jikinta sanye da Uniform d'in islamiyya taje can part d'in bata isketa ba, tana murmushi ta gaishe da Hajiya itama da fara'a ta amsa tace mata an dawo tace mata eh Fatuu ta nuna mata gefen ta alamar tazo ta zauna, bayan ta zauna Hajiya tace jiya bata zo tayin kwana ba maigida ya dawo, ita dai Minon murmushi kawae take yi cike da wasa ta sake ce mata ai da tazo ta taya ta ita duk suka d'an yi dariya, bata dad'e ba sosae ta mik'e zata tafi, bayan ta masu sallama Fatuu tace ta gaida mata da gwaggo, daga baya itama Fatun mik'ewa tay tace bari taje ta taya Aunty Saude aiki a Kitchen, Lokacin da akai Azahar sun gama komai ta wuce d'akin Aunty Sauden don tayi salla, bayan ta gama sallar ne ta fito ta nufi d'akin da Fanan take, da sallama ta tura kopar ta shiga, a saman abun salla ta hangota daga gaban gado tana jingine dashi ta juyo tana amsa mata sallamar da d'an murmushi, sosae gaban Fatuu ya fad'i da ta k'arasa wurinta taga idanunta a haka ma wai don ta samu bacci sun rage, gabanta ne ya shiga fad'uwa Fanan d'in ta nuna mata gefen gado tace ta zauna mana tayi tsaye, bayan ta zauna a sanyaye ta gaida ita ta amsa kafin tace taso taje ai can part d'in nata su gaisa bata tashi da wuri bane, cikin kama kai Fatuu ta d'an yi murmushin yak'e tace mata ai tun d'azu itama tazo ta shigo ta gaida ita ta iske tana bacci, sama sama suke d'an yin hira yawanci ma Fanan d'in ce ke kawo zance anan har take tambayar ta gwaggo tace zata shiga su gaisa in sha Allah, suna haka Haisam ya shigo duk suka yi mashi sannu da zuwa fuskar shi a sake ya amsa ya nufi mirror ya d'aukko stool ya dawo daga gefen gadon ya zauna, gaba d'aya Fatuu ta takura Saboda yawon kallon da yake mata har fakar idon Fanan tay ta d'an mashi alamar ya daina sai kawai taga yayi d'an murmushi, gaba d'aya su biyu ke yin hiran sama sama sai ta kama sannan Fatuu ta saka masu baki, daga baya Saude tazo tayi masu Maganar an shirya table bayan ta fita Fatuu ce ta fara mik'ewa dama duk a takure take cikin wasa Haisam d'in yace mata acici bazata jira su tafi tare ba sai kuma kunya ta kamata tana niyyar komawa ta zauna ya mik'e yana yar dariya Fanan ma yar dariyar tay ganin bata tashi ba yayi mata magana ta d'an yamutsa fuska tace gaba d'aya bata da appetite ne yace ta dai daure kar ta zauna da yunwa, mik'a mashi hannu tayi alamar ya taimaka mata ya kama hannun ya mik'ar da ita, bayan ta mik'e ta fara k'ok'arin cire Hijab din jikinta Haisam ya kai idon shi kan Fatuu dake kallon su suna had'a ido da sauri ta maida kan ta gefe, moving yay zuwa inda take yace su je ba tare data kalle shi ba ta wuce yana biye da ita Fanan kuma na gefen shi. Bayan sun fara cin Abincin Haisam na lura da Fanan bata wani ci kaman dai jiya can ya d'ebo ya kai spoon d'in bakinta da yake tana a gefen shi, kallon shi tay da murmushi yay mata alamun ta ci ta bud'e bakin ya bata, ci gaba yay da bata tunda Fatuu taga haka ta daina kallon su, sai gashi taci sosae, gaba d'aya Fatuu jin ta take wani iri hakan yasa taji Abincin ma ya fitar mata a rai hakanan take d'an tsakura gudun kada ta tashi ai tunanin wani abu, can bayan an k'ara lokaci ta mik'e duk suka kalleta da k'yar ta k'ak'alo murmushi tace ta k'oshi, Fanan ce tace mata amman ai kaman fa bata ci da yawa ba still da murmushin tace ai bata dad'e da yin Breakfast ba tazo ta d'aga mata kai alamar gamsuwa, idon Haisam a kanta ita dai Hajiya d'an murmushi kawae take a ranta ta raya aiki ya ga Haisam don tasan dama dole Fateema bata rasa jin wani abu a ranta a kan Abincin da yake ba Fanan d'in a baki, d'akin Saude ta wuce don acan ta aje gyalen ta, lokacin da ta shiga ba kowa a d'akin don Sauden na can baya ta nufi katifa ta Zauna tay shiru tana kallon wuri guda kaman mai tunanin wani abu, daga baya ma sai ta kwanta kawae,

Bayan su Fanan sun gama cin Abincin Parlor suka wuce Suna kallo saidae gaba d'aya hankalin Haisam na a wurin Fatuu tunani abunda take a cikin d'aki yake ta yi, ana fara kiran sallar la'asar ya mik'e yace zai je Masallaci, bayan ya fito tsayawa yay cikin harabar yana kiran Fatuu a waya saida ya kira har sau biyu amman bata yi picking ba ya juya ya nufi part d'in su a ranshi yana wani tunani, bayan ya shiga Bedroom ne yaga wayar ajiye akan bedside ashe bada ita ta tafi ba ya wuce toilet don yin Alwala, bayan fitar shi Hajiya ma ta tashi itama Fanan d'in ta mik'e suka tafi suma su yi sallar, har Hajiya zata shiga d'aki tayi tunanin Fatuu tace ma Fanan ta duba Fateema a d'akin Saude watak'il bacci take tace to, bayan ta shiga taje ta tasheta tace lokacin salla yayi Fatun tay mata godiya ta mik'e ita kuma ta juyo ta fito, d'aukar gyalenta tayi ta fito daga cikin d'akin lokacin data shigo parlon ba kowa ta nufi hanyar fita ta wuce part d'in su, tana shiga Bedroom ta cire gyalenta a gefen gado ta wuce laundry, bayan ta fito ta yo Alwala ta shimfid'a prayer mat ta kabbara salla.

Tun bayan data gama tayi zaune a wurin tay shiru k'arshe ma sai ta jingina da gado ta kwantar da kanta, Fauzy ce ta fad'o mata a rai ta raya yakamata ta kira ta sanar da ita Ya Haisam ya dawo bata samu ta hau online bane shiyasa data fad'a mata tuni, tana ta zaune can taji an turo k'opar ta kai idon ta, shine ya shigo suka had'a ido bayan ya rufe kopar ya nufota ta d'ago tana kallon shi, tayi tunanin saman gadon zai zauna amman ga mamakinta sai gani tayi ya zauna k'asa a gaban ta ya d'age kafa d'aya d'ayar kuma ya mik'ar da ita tana dai ta kallon shi fuskar ta a d'an sake, kallon ta yake shima saidai yanayin kallon kaman na mai nazarinta ganin haka yasa ta sunkuyar da Fuskar ta ta koma kallon k'asa, tana haka taji Muryar shi calmly yana fad'in "I want to try my possible best to be equitable to you, but I understand it would not be as easy as I think" jin abunda yace yasa a hankali ta d'ago ta kalle shi yanayin damuwa ya bayyana akan fuskar shi, bin shi tay da ido ta fahimci dalilin da ya sa yayi Maganar k'ilan yayi tunanin ko tayi fushi ne Saboda abubuwan da suka faru tsakanin shi da Fanan d'azun, d'an murmushi yaga tayi ta kai hannu ta ta6a gefen fuskar shi da turanci itama tace mashi kar ya damu zata taimaka mashi ya cimma hakan a tsakanin su, d'age gira yay ya tambayi da gaske ta d'aga mashi kai yace kenan bata yi fushi ba, tana yar dariya ta girgiza mashi kai tace fushin mi zatayi ya d'an kashe mata ido guda ya furta kishi, sosae ya bata dariya yadda taga yayi ta fad'a jikin shi a shagwa6e tace to yau ta fara gani ya ba Aunty Fanan Abinci a baki ai tasan yana bata dama, d'age mata gira yay ya tambayi a yaushe tasan hakan tace "a can baya mana lokacin ranar nazo nan gidan har na kawo mata wainar fulawa daga baya da aka ce an shirya table ta matsa man sai munje an ci Abincin da ni, koda naje ma kasa wani ci nayi na taso na dawo parlor, dama ranar da k'yar nazo sai da gwaggo ta ce ya kamata in zo ita ta damu dani tana ta zuwa" a shagwa6e take Maganar gaba d'aya ya zuba ma bakinta ido har ta gama sannan ya k'ara d'age mata gira yace "lokacin kina ciwon so na?" wani kallo tay mashi ta d'an tura baki ya ce ta bashi amsa kawae sai tasa hijab ta rufe fuskarta tana dariya, k'ok'arin bud'e Fuskar ya fara ta bi ta k'ank'ame ta, wani abu ya fara mata yana cigaba da k'ok'arin bud'e Fuskar sai ta ji yanayin yadda take jin abunda yake matan yayi mata kaman cakulkulo ai kuwa cikin d'an k'araji ta fara fad'in "Ya Haisam!....don Allah ka bari.... Wayyo Allah zan bud'e wllh, ka bari don Allah......" ba Arzik'i ta bud'e Fuskar tana haki da dariya, shima dariyar abunda ta rink'a yi yake, ce mata yay to ta fad'i mashi still tana a jikin shi saidai ta zame ta kwanta sosae, d'aga mashi gira tay irin yadda yake mata yace ta bud'e baki a shagwa6e tace "Ehhhhh" d'an bud'a mata ido yay yace "Eh What?" tura baki tay "kai Ya Haisam ba ka gane ba" d'an girgiza mata kai yay alamar bai gane ba ta tura baki, kawai taga ya d'ago hannu aikuwa da sauri ta tare hannun tana dariya tace "Ehh lokacin ina ciwon son ka" sosae yadda tayi Maganar ya bashi dariya sukai tayi a tare saidae ita tafi shi yi,

bayan ya tsagaita yin dariyar yace "ni yaushe za'a canza man suna ne" d'age mashi gira tay "kana so ne?" da murmushi ya d'aga mata kai, tace "to wane suna kake so?" wani kallo yay mata mai kaman harara yace shi zai fad'i mata shi da ya canza mata ita ta fad'i mashi, d'an jimm tay ta kanne ido guda alamar tunani can tace "To Sweetheart?" shiru ya d'an yi sai kuma ya girgiza mata kai yace bai son shi ai dama tana ce mashi haka tace to ai da hakanan take ce mashi ko yanzu kuma da dalili yace to ai shiyasa yake son a canza, jimm ta k'ara yi tace to tunda shi yana da jinin larabawa bari ta rink'a ce mashi Habiby waro ido yay jin irin sunan da Mom d'in shi ke fad'a mashi ne ya girgiza mata kai yace a canza wani tace to Honey, wannan karon yar dariya yay yace to ai duk kusan d'aya ne da Sweetheart d'in, d'an yamutsa fuska tay ta d'an Jujjuya jiki cike da shagwaba tace to ita ta rud'e ta rasa wanda zata za6o yay shiru dae yana bin ta da ido da murmushi can tace "Yauwa to Hubby" Dariya yay kawai bata san shi yadda take mashi Maganar bane yake burgeshi shiyasa yake ta jan abun, tambayar shi tay yayi ya d'aga mata kai harda d'an d'aga hannuwa ta jinjina su alamar jin dad'i, shiru sukai suna ta kallon juna kowanne face d'in shi d'auke da Murmushi can yace mata mi ta zauna yi k'asa ne bata je Parlor ba ko ta hau gado tace mashi Sallah tayi da ta gama Addu'a sai kuma tayi zaune, tambayar ta yay Addu'ar mi tayi tace da yawa, hannu ya kai ya kama hannunta ya d'agata ta zauna sosae suna kallon juna yace to ta fad'a mashi Addu'o'in da ta yi,

"Nayi ma mamana na rok'i Allah ya jaddada rahama a gare ta da sauran wanda suka rasu...." jinjina kai yay Slowly ya furta "Ameen" cigaba tayi "Sai Baffana da gwaggo harda Hajiya na rok'i Allah ya k'ara masu lafiya da nisan kwana mai Albarka" lumshe ido yay, ta sake cewa "Aunty Fanan ma nayi mata Allah ya bata lafiya ya kuma had'a kan mu, sai su Kawu Amadu da sauran yan'uwa harda k'awaye na su Fauzy na rok'i Allah itama ya bata Miji na gari wanda zai sota tsakani da Allah ya riketa da Amana harda su Mino ma" jinjina mata kai yay a hankali yace Allah ya amsa, shiru tay yace Shikenan ta d'aga mashi kai, wani kallo yay mata mai kaman harara tana ganin haka tasa dariya tace "to ai kai fa na fara yi mawa Allah, na rok'i Allah ya k'ara ma rayuwar ka Albarka yasa ka gama da iyayen ka lafiya ya k'ara maka lafiya da Arziki mai Albarka ya biya maka dukkan bukatunka na Alkhairi yasa ka dawwama a cikin farinciki ya kuma bani ikon yi maka biyayya" lumshe ido yay ya saki k'ayataccen murmushi sosae yaji dadin Addu'oin ya amsa mata da Amin, ce mata yay ita bata ma kanta bane tace tayi yace to ta fad'i mashi wacce tayi ma kanta wani kallo tay mashi tana dariya da alamun kunyar fad'i take ji yace yana jin ta, cikin jin kunya tace "Na rok'i Allah yasa....in samu ciki in haiho yaro mai kama da kai sak" da k'yar ta k'arasa Maganar tana rufe fuskarta da hannunta d'aya, yana murmushi yace bata son mai kama da ita ta d'aga mashi kai, tambayar ta yay miyasa take son mai kama da shi tace "Saboda nasan ba kowane lokaci zamu kasan ce a tare ba kaga in na haifi mai kama da kai ko baka nan zan rage kewar ka in ta kallon fuskar shi" tana yar dariya ta k'arasa Maganar, jinjina kai yay ya d'an kalli gefe alamar tunani kafin ya juyo yace mata to taji wani alama, ta d'an bud'a ido tace alamar mi, wani kallo yay mata da sauri ta maida fuskarta gefe, ce mata yay ta bashi amsa ba tare data kalle shi ba a shagwabe tace ita ya za'ai ta gane,

"But, did you feel anything last time?" Yay tambayar ya kafeta da ido, d'an jimm tay sai kuma ta yarfa hannu cike da kunya tace itafa bata fahimci komai ba lokacin, yace "Ok I forgot, u were in severe pain lokacin ba zaki fahimta ba" ita dai shiru tayi taga ya mik'e, Hijab d'in jikinta ya cire da kan shi ya kaita wardrobe tana ta kallon bayan shi, dawowa yayi ya duk'a a gabanta yasa hannu ya duk'o da kanta saman chest din shi ya kai hannu ya cire mata necklace d'inta bayan ya dagota ya had'a da earrings d'in gaba d'aya jewellery d'in ya cire ya kai saman dressing mirror, saida yaje ya sa ma kopar Bedroom d'in key sannan ya dawo wurinta gaba d'aya ya ciccibo ta yana fad'in Let them try their luck now.........

*ASM 076*

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*

.........Gab da kiran sallar Magrib Haisam tsaye a gaban mirror ya gama shiryawa cikin jallabiya, bai dad'e da ya fito daga wanka ba bayan ya tashi bacci, gado ya nufa ya hau ya matsa kusa da Fatuu dake lullu6e da duvet tana ta shan bacci, hannu ya kai ya shafi fuskarta tare da kiran sunanta, ganin tak'i tashi yasa shi d'an bubbuga fuskar a hankali yadda bazata ji zafi ba, motsi ta fara yi kafin ta fara bud'e idanun tana yi tana lumshe su har ta bud'e su gaba d'aya sun d'an yi ja, bin juna sukai da kallo Haisam na d'an murmushi yace "My Lazy Wife" jin haka yasa ta tura mashi baki a shagwabe tace itace lazy d'in ya d'aga mata gira alamar eh, k'ok'arin rufe fuskarta da duvet ta shiga yi ta d'an d'aure ta ita ala dole tayi fushi, da sauri ya ruk'e Duvet d'in yace mata wasa yake mata ita ba lazy bace shi shaida ne, ganin irin kallon da yake mata yasa ta d'an juyar da fuskar ta tana yar dariya, ce mata yay ta tashi taje tayi wanka lokacin salla ya yi ta d'aga mashi kai, hannu ya kai zai d'ago da ita da sauri ta k'ank'ame duvet d'in tace yaje zata tashi yanzu, murmushi kawai yay ya juya ya saukko daga kan gadon, tanata kallon bayan shi har ya bud'e k'opa ya fita, lumshe ido tay tana ta sakin k'ayataccen murmushi da alama itama ta zaucen, daga baya ta saukko ta nufi toilet.

Bayan ta gama sallar Magrib mik'ewa tay ta d'aukko wayarta ta dawo kan prayer mat d'in ta zauna ta shiga kiran Fauzy, tana fara ringing ta d'auka suka gaisa tace mata ya School Fauzyn tace ta manta Weekend ne tana gida ai, d'an shiru Fatun tayi jin haka yasa Fauzy tambayar ta lafiya, tace "kin san Fauzy Ya Haisam fa ya dawo" da alamun mamaki tace mata da gaske Fatun tace mata "Eh, kuma harda Aunty Fanan ma, ashe wannan sak'on da kika tura sun gani kuma lokacin daya shiga ma ita ta fara gani wayar na a hannunta" wani uban salati Fauzy ta buga har saida ta kusa sa Fatuu fashewa da dariya don a matuk'ar razane ta yi shi, a rud'e ta shiga tambayar ta yanzu ya akai, mi ya faru, da alamun damuwa Fatun tace mata bata yarda ba rigima tasa wai sai an sake ta shine suka taho, wani salatin Fauzy ta k'ara saki, a iya muryarta zaka shaida ba K'aramin tashi hankalinta yay ba, a kid'ime tace ma Fatun to shi ya Haisam d'in miya ce, don kada taci gaba da tada mata da hankali tasan hakan bashi da kyau yasa ta saki dariya tace "sorry k'awata ina tsokanar ki ne amman da gaske ya dawo kuma taren suka zo sannan da gaske ita ta fara ganin sak'on" da sauri Fauzy tace "to yanzu miya faru don Allah??" Fatuu na murmushi tace mata Alkhairi, nan ta kwashe yadda komai ya faru harda bayyana mata da ya Haisam yayi yana son ta shima, wata uwar k'arar murna Fauzy ta saki Fatuu nata dariya tana jiyo ta tana k'wala ma Aunty Mareeya kira tana fad'in the long expected day has come, d'akin Aunty Mareeyar ta nufa dama tare suke suna kallo a parlor ta tashi taje ta dawo, a daidai bakin k'opar bedroom d'in nata sukai kacibus don ta jiyo k'wala mata kiran da take, cike da farinciki ta hau bata labarin abunda ya faru tun kafin ta k'arasa ta mik'a hannu ta amshi wayar dama duk Fatun na jin su, tana amsa cike da Farinciki harta kasa rufe baki ta kira sunan Fatun itama tanata murmushi ta amsa mata kafin ta gaishe da ita, Cike da tsantsar farinciki tace "ashe wai haka abu ya kasance, shima bawan Allah ashe ashe yana ta gurzuwa" yar dariya Fatun tay tace mata eh,

"Kai jama'a! Wannan cutar kai har ina kana son abu kuma abun nan ya zama mallakin ka Saboda tsabar cutar miskilanci ka tauye ma kan ka hakki" cike da jin kunya Fatun ta fad'i mata dalilin shi na yana son sai dangin shi sun sani, cikin washe baki tace "duk da yana da dalili amman ai da sai ya maki bayani ko yanzu da yasa zuciyar ki ta buga fa d'an bantan uba da yafi kowa shiga hali kuwa k'ilan ma tashi itama ta buga don na lura irin soyayyar laila da majnun kuke ma juna an sha yan ciwoce ciwoce" dariya Fatuun take ta yi Aunty Mareeyar ta shiga taya ta murna ta kuma yaba ma Fanan tace gaskiya tayi namijin k'ok'arin da ba kowace mace zata iya ba don ita kanta Maganar gaskiya bazata iya ba, daga baya kuma tace to kuma irin haka in har mutum ya fito ya bayyana maka in baka amince ba kai kanka ba samun kwanciyar hankali zaka yi ba, k'arshe kuma tace Allah ma kada ya kawo wacce zata siye mata zuciyar miji haka Fatuu dai sai dariya take, yar Nasiha ta d'an yi mata ta kuma ja hankalinta kan kula da miji dasu kwalliya tace sai sun had'u zata mata karatu sosae,

"Yanzu Zarah nace sai in maido magungunan aro ko, dama shekaran jiya tayi promo jiya aka kawo man wanda na siya" shiru ta d'an yi kafin cikin jin kunya tace mata eh to tunda akwae, dariya Aunty Mareeya tasa tace "ja'ira da ba kince in ma kwashe duka ba, in ce dai na farkon sun yi maki aiki yadda nike ta fata Allah yasa ya magantu iya magantuwa" k'asa k'asa Fatun tace mata eh, kafin da k'yar tace mata harda kuka ma, wani irin ihu da Aunty Mareeya ta saki har saida Fatun ta cire wayar daga kunnanta tana dariya Fauzy ce ta taso da sauri tana tambayar Auntyn wai mi akai tay mata alamun ta tafi da hannu tace mata Maganar manya ce wannan, ce mata tay zata bada in zata je Makaranta gobe sai Fauzy ta tafin mata da su tace eh zata je, daga baya sukai sallama sai farinciki Aunty Mareeya ke yi, bayan Fauzy ta amshi wayar itama sukai sallama tace mata sai sun had'u School gobe, Fauzyn tace ita da ke shan Amarci ta bari ta gama, Fatuu na yar dariya tace yadda in jarabawa tazo zata rubuta hakan ko, duk suka yi dariya nan tayi ma Fauzy godiyar sak'on da ta tura tace dama koda ta nuna bata ji dad'i ba Saboda gudun abun da zaije ya dawo ne, Fauzyn na dariya tace mata haba ba komai ai tun lokacin ta fahimceta tayi mata Addu'ar Allah ya sanya Alkhairi ya basu zaman lpy yasa nan da nine months su sha suna Fatuu dai nata dariya daga baya sukai sallama. Cikin parlon Fauzy ta koma ta zauna kusa da Aunty Mareeya nan suka dasa hirar farinciki Fauzy na fad'in ita wllh dama ranta ya bata shima yana son Zarah bawan Allah ashe ma ya fita shiga hali.

Saida aka gama sallar isha Haisam ya dawo yace mata ta shirya suje part d'in Hajiya suci Abinci tace to, k'ananun kaya skinny jeans da riga wadda ta hau da shi ta fiddo, yana kwance saman gado ya jingina da headboard yana kallonta ta fara shiryawa, tana yi suna sakar ma juna murmushi in tazo kan abunda take jin kunya sai ta duk'e k'asa a haka har ta gama sakawa ta nufi gaban mirror tana gyara parking d'in gashinta, kasa jurewa Haisam yayi ya saukko daga gadon Slowly ya nufe ta, ba zato taji ya rungumota ta baya har saida ta d'an yi firgit, hannu ya kai ya janye gashinta data baza shi tana sharcewa fuskar shi da ya d'aura akan shoulder d'inta ta bayyana, murmushi suka shiga sakar ma juna ya d'an lumshe ido ya furta mata "Baby you're very beautiful" itama Lumshe mashi ido tay itama ta furta "Hubby you're very Handsome man" gaba d'aya sukai murmushi, hannuwan shi yasa yana bin shape d'in jikinta tamkar yana zana ta, d'an runtse ido da mak'e kafad'a Fatuu ta shiga yi, ganin bai da niyyar dainawa yasa tace mashi zai hanata ta gama shiryawa su tafi, juyota yay ya kai hannu ya fara k'ok'arin yi mata parking d'in gashin, suna haka take ce mashi wai a da can da ya fara saninta yana ganin kyaun ta, shiru yay yana d'an murmushi kafin yace bazai iya ganewa ba kawai dai yasan komai nata na burge shi, bayan ya gama d'aure mata gashin d'ago da ita yay ya d'aura ta akan k'afafun shi yadda ta d'an k'ara tsawo hannuwan shi tallafe da waist d'in ta itama ta zagayo da nata hannuwan ta bayan shi, bin juna sukai da wani irin azababben kallo kowa K'ok'arin nuna irin k'aunar dayake ma d'an uwan shi yake ta cikin kallon, As they held each other close, their bodies seemed to melt together like two puzzle pieces that were made for each other, Fatuu ce ta sare ta rufe fuskar ta a jikinshi idonta a lumshe can k'asan mak'oshi taji ya furta yana son ta itace best thing d'aya ta6a faruwa dashi tana mak'ale dashi ta furta mashi itama haka, d'agota yay suna sakar ma juna murmushi yace suje tace bari ta d'aura After dress, bayan ta d'aukko ta saka tayi rolling veil d'in ya kama hannunta suka tafi.

Wuraren k'arfe goma da rabi lokacin basu dad'e da dawowa ba suna zaune a parlorn su suna kallon American film Fatuu ta cire after dress d'in tana mak'ale jikinshi kamar yar mage sai shak'ar k'amshin juna suke, d'aga kai tayi ta kalle shi tace mashi gobe zata je school, shiru ya d'an yi yana kallonta kafin yace bazata bari ta huta ba, a d'an shagwabe tace mashi Exams d'in su ta taho fa Upper week zasu fara bata son ayi wani abun bata nan kuma ma test ake ta masu, jinjina mata kai yay suka cigaba da kallon, bayan wani d'an lokaci taji ya fara magana ta k'ara d'aga kai tana kallon shi, shima kallon ta yake yace mata jibi Fanan zata tafi Lagos yana son zasu rakata, jimm Fatuu tay tana kallon shi ba tare data ce mashi komai ba hakanan sai taji bata son zuwa duk da bazata so ya tafi ya barta ba, ganin tayi shiru yasa shi tambayarta ko bazata rakata ba, da alamun yar damuwa tace ba wai bata son zuwa ba kawae dai bata son wani abu ya faru in taje gidan su, shiru ya d'an yi yana nazarin Maganar tata can yace mata Shikenan sai su sauka a Hotel kawai, bin shi da ido Fatuu tayi don hakan ma bata ji ya kwanta mata ba gani tay in suka yi haka kuma ai kaman ba'a kyauta ma Fanan d'in ba anan suna tare kuma acan ma su ware duk da bata san ya suka tsara da ita ba game da kwanakin da zaiyi da ita ba,

tambayar shi tay kwana nawa zasu yi yace just 2 days, sauke idanunta tayi ta shiga tunanin tunda ba dad'ewa zai yi ba kodai ta k'i bin shi don k'arshen ta hakan ba komai zai k'ara mata ba face bak'in jini a wurin su Hajiya Maryam in dai suka san da ita yaje kuma ya sauka da ita a Hotel tunda dai tasan ai k'ilan duk in suka je da Fanan a gidansu suke sauka, tana haka taji ya tambayi koda wani matsalan ne, kallon shi tay ta d'an girgiza mashi kai kafin a sanyaye tace tana jin saidai yaje ya dawo don a jibin tana da test, shiru ya d'an yi sai kuma yace Ok bari a d'aga tafiyar sai bata da test d'in da sauri tace "Ai Hubby daga jibin fa kusan kullum sai munyi don upper Wednesday zamu fara exam, tunda just 2 days ne ka rakata kawai" shiru yay yana kallonta sai d'an yamutsa fuska take, sam ba haka ya so ba don a yadda ya tsara tare zasu, ganin yanayin shi yasa ta kai hannu tana shafa kwantacciyar sumar sajen shi cikin nuna damuwa tace "You shouldn't worry pls" d'an murmushi yay ya lumshe mata ido, cigaba da shafa beard d'in tayi shi kuma yaci gaba da kallon yana yi yana maido idon kanta, k'arfe 11 na yi yace suje su kwanta tunda zata school suka mik'e a tare yana ruk'e da hannunta sai kace k'anwar shi, bayan ya kashe kayan kallon ya rage hasken Parlon suka nufi Bedroom yana tallafe da ita.

Washe gari bayan ta gama shiryawa tare suka fito da shi zai kaita, saida suka tsaya suka d'auki Mino sannan suka wuce, Mino aka fara ajewa suka wuce, a inda ya saba ajeta nan yayi packing ta kalle shi tana murmushi tayi mashi godiya tana niyyar juyawa ta bud'e kopar taji ya ruk'o hannunta ta juyo ta kalle shi, idanun shi a d'an lumshe ya jingina kanshi jikin headrest, tana kallon shi ta fahimci ruk'on kona miye tay mashi nuni da lip glow d'in da ta shafa ya ida lumshe idon, matsawa tay wurin shi ta kai baki ta manna mashi kiss a kumatun shi tana niyyar janye fuskar ya ruk'o kan, lokacin daya saketa gaba d'aya ba lip glow d'in, komawa tay ta zauna itama ta jingina kanta da kujerar tana breathing rapidly haka shima, bayan sun natsu ya tambayi tana tare da Atm d'inta ta d'aga mashi kai yace ok zai tura mata kud'i ta tabbatar taci Abinci mai kyau ta k'oshi nan ma kai ta d'aga mashi suna kallon cikin idanun juna, har zata juya taji yace ko ya kawo mata Abincin da break, da sauri ta girgiza mashi kai tace a'a ai anan akwae Abinci mai kyau zata ci.

A class ta iske Fauzy don da wuri tazo Saboda zumud'in ganin Fatun, tana shiga ta taso da gudu tazo ta rungume ta cike da Farinciki itama Fatun sai dariya take, bayan sun je sun zauna gaba d'aya Fauzy ta kafeta da ido tana ta washe baki sai kace wadda aka ma Albishir mai dad'i tama kasa Magana, Fatuu na dariya tace "wai sai kallo na kike sai kace yau kika fara ganina" yarfa hannu tay tace "bazaki gane irin farincikin da nike ji ba wllh don abu ne da ban yi zaton shi kusa ba, kinga wai yadda kika canza cikin kwana biyu kacal har fa wani glowing kike wllh ga k'amshin amarci, koda yake dama fa irin su Ya Haisam ba dai iya zuba ruwan love ba wllh kina ganin su shiru shiru sai hum....." dariya kawae Fatuu take ta kasa cewa komai itama Fauzyn dariyar take can tace "k'awata kukan ya Haisam bai damu da ni ba bai sona ya k'are ko" bugu Fatuu ta kai mata tana fad'in "leave me alone Fauzy" gaba d'aya dariya suke a haka malamin su ya shigo, tun bayan da malamin ya fara masu bayani Fauzy na lura da Fatuu sai faman sakin murmushi take da gani ba K'aramin nishad'i take ciki ba, sai da akai break sun fito take ce mata ita wannan Amarcin anya ma zai bari tayi wani karatun Exams Malam na explanation tana sakin murmushi inaga in jarabawar tazo kar ta kai fa in aka tambayi zane ta zana Ya Haisam, sosae Fatuu ke dariya suka nufi inda zasu ci Abinci.

Da yamma wurin sallar la'asar Fatuu ta fito daga wanka, bayan ta zura doguwar riga ta kabbara salla, tana gamawa ta nufi gaban dressing mirror ta fara shirin zuwa part d'in Hajiya, tun bayan daya d'aukkota daga school suna dawowa suka ci Abinci ko wanka bai bari tayi ba suka kwanta bacci, sai da aka fara kiran sallar la'asar ya farka yaje yayi wanka bayan ya fito ya shirya ne ya tasheta ya sanar da ita time d'in salla yayi, tana cikin yin shafan aka yi knocking k'opar Bedroom d'in ta juya ta nufi kopar, tana bud'ewa suka had'a ido da Fanan ta sakar mata murmushi tana sanye da fitted gown ta lace dark blue fuskarta ba wani makeup sai lip glow data shafa a baki sai kuma yanayin fuskar bata rasa shafa powder yar kad'an ta yafa mayafi mahad'in kayan a saman kafad'ar ta, murmushi itama Fatun tayi mata ta kira Sunanta kafin ta gaishe da ita, ce mata tayi ta shigo mana tace a'a bari ta jirata a parlor dama tana son zata rakata wurin gwaggo ne da sauri tace mata to, komawa ray cikin d'akin cike da zumud'i ta d'auki waya ta kira Haisam bayan yayi picking ta sanar dashi zancen fitar yace ai Fanan dama tayi mashi magana sai sun dawo sukai sallama cike da nuna k'auna, ba 6ata lokaci ta k'arasa shiryawa bata canza kaya ba sai kawae ta yafa mayafin rigar jikinta ta d'aukki wayarta ta fita.

A parlor suka zauna gwaggo nata faman sakin murmushin yak'e dama tun lokacin da suka zo tayi arba da Fanan saida gabanta ya fad'i, wani irin nauyi da kunyar Fanan d'in ne suka kamata duk ta bi ta kama kanta a haka suka gaisa tayi mata an zo lafiya da tambayar yan gidan su, lokacin Mino ta tafi islamiyya Amadu kuma yana a shago saida ma suka tsaya ya gaisa da Fanan kafin su shigo, Fatuu ce ta mik'e taje ta d'aukko mata ruwa da lemu don ta lura da yanayin gwaggon, bayan ta zuba mata cup ta mik'a mata ta fara sha, da k'yar gwaggo ta mik'e tace bari a kawo mata Abinci, da sauri Fanan d'in tace "No gwaggo ban dad'e dana ci Abinci bana jin yunwa" still murmushin yak'e gwaggo ke tayi tace "amman d'iyata Fanan ai a d'an ci na zumunci ko Yaya ne tunda yaushe rabon da acin" tana Murmushi tace mata kar ta damu ai tasha ruwa da lemu sai kuma tace "Da dai akwae dambu da na ci"

da sauri gwaggo tace "ah in shi kike so sai in yi maki yanzun nan" girgiza kai Fanan tayi tace ba sai tayi wahala ba tunda babu, da sauri gwaggon ta k'ara cewa "ai ba wani abun wahala tunda komai akwae bari kiga yanzun nan a yi" tana rufe baki ta juya ba tare data jira cewar Fanan d'in ba,

tun bayan data fara aikin girkin dambun take ta faman sambatu ita kad'ai, wani lokacin ta girgiza kai duk ta bi ta damu, Kallo suka cigaba da yi sai dai Fanan ba wani kallon take ba tafi yawan d'aga kai ta kalli sama kaman mai yin tunani sai jefi jefi take sauke idon ta kalli Tv, gaba d'aya Fatuu duk ta damu da yanayin ta don akwae alamun damuwa a tattare da ita hakan yasa bunu bunu sai ta kalleta, suna haka can ta kalli Fanan d'in suka had'a ido ta k'ak'alo d'an murmushi itama Fanan d'in fuskarta a d'an sake tace mata "Sis Zarah kinata kallo na tun d'azun da wani abu ne?" da sauri Fatuu ta girgiza mata kai ta maida idon ta k'asa , kaman daga sama taji tace "ko ina baki tausayi ne?" da sauri ta d'ago ta kalleta idon Fanan d'in akanta da alama amsa take jira da k'yar Fatuu ta d'an d'aga mata kai alamar eh kawai sai gani tay ta mata wani kallo mai kaman harara tace tunda ta k'wace mata miji ba dole taji tausayin ta ba, a rud'e Fatuu tace "a...a Aunty Fanan don Allah ki yi hak'uri.... " idanun ta har sun ciko da k'walla sai kawae gani tay Fanan d'in ta yi dariya tace tana tsokanarta ne, cigaba da kallon sukai saidae duk Fatuu jin ta take wani iri don tasan dama damuwar Fanan d'in bata wuce kan Haisam, ba'a d'au wani dogon lokaci ba gwaggo ta gama yin dambun yasha zogale da gyad'a da albasa sai uban k'amshi ke tashi, saida tazo ta tambayi Fanan d'in da k'uli take so ko yaji tana murmushi tace a kawo duka sai tasa taji wanda yafi dad'i gwaggon tace to, a d'an babban plate ta zubo mata bayan ta aje ta kalli Fatuu da d'an murmushi tace itama zata ci ne ta d'an tura baki tace eh mana, tana niyyar fita Fanan tace ta bari su ci tare in basu k'oshi ba sai a k'aro masu gwaggo ta washe baki tace to, suna cikin cin Abincin Mino ta dawo daga islamiyya ta shigo tana ta fara'a ta duk'a ta gaida Fanan itama tana murmushi ta amsa mata daga baya ta gaishe da Fatuu kafin ta mik'e don taje ta cire Uniform, anan sukai sallar Magrib bayan sun gama suka fara shirin tafiya Fatuu taje ta sanar ma gwaggo zasu tafi, tana sanye da hijab da tayi salla tazo parlon lokacin Fanan na zaune a kan kujera itama ta zauna tana murmushi cike da k'arfin hali ta fara Magana "Y'ata Fanan inata so in baki hak'uri kan yadda abu ya faru tun d'azun nauyin ki yasa na kasa, nasan dole an maki ba daidai ba dole kuma hakan ya jefa ki a halin matsananciyar damuwa, don Allah kiyi hak'uri, duk ta wani bayani ba shi bane tunda mai faruwa ta faru" d'an murmushi tayi tace "No gwaggo ba komai, ni musulma ne na yarda da k'addara mai kyau da mara kyau and I hope wannan ya zama mai kyau, kawae ina son ki ma Zarah magana taci gaba da d'aukana matsayin sister nata ba kishiya ba, kuma duk abunda take so ma kanta ni ma ta so man....." Kuka ne ya taho mata da sauri tasa hannu ta rufe idanunta a rud'e gwaggo ta hau lallashinta kafin ta juya kan Fatuu ta fara mata Nasiha can ta maida Maganar da harshen fulatanci ta ce mata kar ta sake ta canza mata ta rink'a kyautata mata sosae samun abokiyar zama irinta a yanzu zai matuk'ar wahala idan ma tayi mata wani abu da bata ji dad'i ba ita ta fad'i mata zata bata shawara, haka tay mata fad'a sosae Fatun nata k'walla tana d'aga mata kai, daga baya ta had'a su gaba d'aya tayi masu Nasiha, sosae tayi ma Fanan godiya da Addu'oi tana ta amsawa a hankali, ce masu tayi bari ta zuba masu dambun su kai ma Hajiya, lokacin data zubo ta fito har sun fito tsakar gida Mino ma ta fito daga cikin d'akin Fatuu na da yanzu ita ce a ciki, har waje bakin shagon Amadu suka rako su Fatuu ta amshi kular dambun Amadu ma ya fito sukai sallama cike da nuna jin dad'i, jikin gwaggo ba K'aramin sanyi yay ba sai dai kuma yanzu hankalin ta ya fara kwanciya sosae.

Bayan sun koma gidan part d'in Hajiya suka wuce, lokacin da suka shiga ba kowa a cikin parlon dama Hajiya sai tayi sallar isha take fitowa, d'akin da Fanan d'in ta sauka suka wuce bayan Fatuu ta je Kitchen ta aje dambun, yar hira suka shiga yi suna haka aka kira sallar isha. Bayan sun gama sallar Parlor suka fito suka zauna suna yin kallo, basu dad'e da zama ba Hajiya ta fito ta nufo cikin parlon, bayan ta zauna gaba d'aya suka gaishe da ita ta amsa tace masu an dawo ya Dijen, amsa mata sukai da tana lafiya tana gaishe da ita Fanan ta sanar da ita an bada dambu ma a kawo mata tace dambu Dijen tayi kenan aikuwa zata ci don ta kwana biyu bata ci shi ba, Fanan tace ita aka mawa, jinjina kai Hajiya tayi tana murmushi tace lallai Dije na ji da ita, Fatuu ma murmushi take ta mik'e don ta d'aukko mata, A plate ta zubo mata ta sako mata spoon ta dawo cikin parlon, tana niyyar d'aurawa saman sofa table ta kinkimo mata shi Hajiyar tace mata ta barshi ta bata, tambayarta tayi lemun da zata d'aukko tace ta bata ruwa kawae, juyawa tay ta koma hanyar Dining don ta d'aukko, sosae taji dad'in dambun tana ta yabawa Fanan na yar dariya tana fad'in kodai santi take, suna haka Haisam ya shigo cikin parlon hannuwan shi ruk'e da manyan ledoji, kusan a tare Fanan da Fatuu suka mik'e suka nufe shi kowa ya amshi leda guda tare da yi mashi sannu da zuwa yana murmushi ya amsa, Hajiya na yar dariya tace sun hutar da ita ita Uwargida duk sukai yar dariya, bud'e wadda Fanan ta amsa tayi taga su ice cream ne da snacks ta hannun Fatuu kuma Fruit ne, ce ma Fatuu tay taje ta zubo a plate sai ta taho da wasu a zuba snacks d'in ta amsa da to tana niyyar juyawa suka had'a ido da Haisam ya lumshe mata idanu tay d'an murmushi kawae ta wuce, bayan ta dawo kowa aka zuba mashi su shawarma suka d'auki ice cream Hajiya tace bazata sha shi ba Fanan d'in tace mata to akwae Fura a bata tace eh, k'arshe dai basu ci Abincin dare ba don duk sun k'oshi da abubuwan daga baya wurin k'arfe goma Haisam da Fatuu sukai masu sallama Fanan harda yi masu rakiya bakin k'opa bayan sun tafi ta dawo.

Washe gari tun da Fatuu ta tashi take jin ta wani iri sanin yau Haisam d'in zasu tafi Lagos duk tayi wani sukuku da ita, Lokacin da zai kaita Makaranta bayan sun aje Mino sun wuce ganin yanayin ta yasa ya kai hannu ya kamo hannunta ya tambayi mike damunta ta d'an girgiza mashi kai kawai alamar ba komai, shiru yay kawai don ya fahimci dalilin canzawar tata yaci gaba da driving squeezing her hand lovingly. Bayan sun tashi ya d'aukko su saida aka aje Mino gida sannan suka wuce, Abinci suka fara ci kafin suka shiga faranta ran junansu, tare sukai wanka bayan sun fito ya fara taimaka mata ta shirya cikin doguwar riga kafin shima ya fara shiryawa tana zaune a bakin gado tana kallon shi, bayan ya gama shafe shafen jikin shi sanye da bathrobe ya nufo inda take zaune, zama yay daga gefenta cike da nuna damuwa ya kai hannu ya ruk'o hannunta yana ce mata karta damu kanta haka sosae is just 2 days ai zai dawo shima ba son tafiya yake ya barta ba shiyasa ma tun farkon yace a jira sai bata da test to kuma tace kusan kullum zasu yi gashi ya riga yace ma Fanan d'in zasu je tare, kuka ta saka mashi dama dannewa take ta yi, hannu ya kai ya jawo ta jikin shi, sosae ya shiga rarrashinta yana nuna mata ai zasu rink'a yin Vedio call kafin ya dawo, sai kace yana zugata sai k'ara sautin kukan take gaba d'aya ta fara rikita shi a da ma bai son kukan ta balle kuma yanzu, haka yay ta aikin rarrashi cikin salon k'auna, har aka kira la'asar suna abu d'aya k'arshe dai sai a d'aki yayi Sallah tare da ita bayan ya samu tayi shiru sai sakin ajiyar zuciya take, bayan sun gama ya fara shiryawa cikin shadda light blue itama d'aukko mata riga da skirt na atampa yay don doguwar rigar jikinta duk ta yamutse, kusan a tare suka sa kayan ya taimaka mata, bayan an gama saka kayan gaban dressing mirror suka nufa da kanshi ya shafa mata powder yanata mata murmushi itama tana d'an maida mashi, jambaki ya d'aukko zai shafa mata ta tare hannun ta d'an girgiza mashi kai yace bata so a hankali tace mashi bashi ba, yace Ok wanne ta nuna mashi lip glow ya d'aukko ya shafa mata, kai fuskar shi wurin tata yay ta d'aga ido ta kalle kawai sai gani tai ya kai bakin shi ya manna ma lips d'in ta kiss, yana d'agowa taga ya gogi lip glow d'in hakan yasa ta saki faffad'an murmushi, yar dariya yay dama so yake yaga ta saki fuskar yasa yayi mata hakan tunawa da yadda sukai na jambaki, bayan ya gama yi mata komai kama hannunta yay suka nufi bakin gado shi ya fara zama ya d'aurata akan laps d'in shi idon su cikin na juna, da d'an murmushi yace "za'a rakani Airport?" shiru tay ta kafeshi da ido sai da taga ya d'age mata gira alamar amsa yake jira sannan murya a disashe tace "kana so?" Lumshe mata ido yay ta d'aga ma shi kai alamar to, hannuwan shi ya kai ya rungumota jikin shi ya duk'a da kanshi saitin nata whispering in to her ear ya furta "promise me bazaki k'ara kukan ba har in dawo?" jimm tay ta kasa cewa tayi alk'awarin don ita kanta kawae ji taje kukan na zuwa, k'ara ce mata yay tayi mashi alk'awarin cikin karyayyar murya tace "ai shine ke zuwa da kan shi" k'ara matseta yay yace Ok amman ta daure ta daina yi hankalin shi ba zai kwanta ba in ya tafi ya barta tana kukan ta d'aga mashi kai alamar to, shiru suka d'an yi ha6arshi a saman kanta can taji yace mi take so ya siyo mata, d'an girgiza mashi kai tayi alamar ba komai yace bai yarda ba kullum sai tace ba abunda take so yanzu dai ta fad'a komi take so zai kawo mata,

murya a disashe tace mashi da gaske ba abunda take so kawai sai ji tay yace "Ok I will buy you a teddy bear" ba shiri ta d'ago ta kalle shi da alamun mamaki akan fuskar ta, idanun shi a d'an lumshe yana d'an murmushi ganin kallon da take mashi ya d'age gira yace "or a Barbie doll wanne kike so ko duka?" tura mashi baki tay a shagwabe tace "to ni k'aramar yarinya ce da zaka siyo man wannan" still idanunshi a lumshe suke ya furta "Yes u'r my baby",

murmushi tayi tace "to ni ban son su in ma abun wasan zaka siyo man to kan ka zaka siyo man" yana murmushi yace shi ai ta riga da ta mallake shi tuni, itama murmushin take tace to tana jira ya dawo sai tayi wasan da shi shine teddy d'in nata sukai yar dariya, wayarshi ce ta fara ringing ta sauka daga jikin shi tace bari ta d'aukko mashi, wurin mirror taje ta d'aukko ba tare data duba mai kiran ba ta kai mashi, sunan Fanan ya gani alamar ita ke kira bayan yayi picking ba tare da ya bari tayi magana ba yace gashi nan fitowa yanzu, yana gama wayar ya mik'e tana tsaye daga gefe ya kama hannunta suka nufi Wardrobe, bayan ya fiddo mata gyale da kan shi ya yafa mata shi suka tafi bai d'auki komai na kayan shi ba anan abunda ya ke son d'auka d'azun ya d'aukko a G.r.a da ya aje ta school harda jakar computer d'in shi, koda suka zo shiga harabar gidan ba yadda bata yi ba ya sake mata hannu amman ya k'iya haka da suka zo shiga part d'in Hajiya ma k'in sakin hannun yay suka shiga haka duk kunya ta kamata, a cikin parlon suka samu Hajiyar da Fanan ta shirya dama shi kad'ai take jira, zama sukai Fatuu ta gaishe dasu duka shima ya gaisa da Hajiya daga haka suka yi sallama duk suka mik'e don lokaci na neman k'urewa Hajiya na k'ok'arin mik'ewa tayi masu rakiya Haisam d'in yace tayi zaman ta kawae tayi masu Allah ya tsare, a parking space suka iske Tk a gefen Motar da zasu hau, ita da Fanan suka shiga baya shi kuma ya zauna a gaba Tk ya zauna a driver seat bayan ya rufe ya tashi Motar suka fito daga cikin wurin kafin yaja suka tunkari gate.

Ba K'aramin k'ok'ari Fatuu tayi ba wurin hana idanunta zubar da k'walla har suka raka su suka dawo, gaba d'aya jinta take wani iri duk tayi sukuku da ita, suna zuwa kusa da gidan su tace mashi ya ajeta a gidan, lokacin data shiga Mino bata nan tana islamiyya sai gwaggo kawai ta iske a cikin d'akin ta tana zaune a saman gado tana linkin kaya, a saman kujera ta zauna bayan sun gaisa ta tambaye ta daga ina da d'an murmushi ta fad'i mata ta raka su Aunty Fanan ne nan gwaggon tayi masu Allah ya tsare, daga baya tsohon dakinta ta koma ta kwanta tayi lamo tana ta tunanin Masoyinta har Mino ta dawo ta isketa anan, tana a gidan har aka yi sallar isha lokacin har Haisam ya kirata ya sanar da ita sun sauka, bayan sun ci Abinci suka tafi tare da Mino zata taya ta kwana.

Tun bayan da suka sauka Driver d'in gidan su Fanan ne yazo ya d'auke su, lokacin da suka isa gidan kusan ba kowa Hajiya Maryam bata nan ta d'an fita ta dawo haka sauran yara ma basu kaiga dawowa daga Islamic school ba Dad d'in su kuma na Asibiti wurin aiki sai Farha kad'ai tazo tayi masu sannu da zuwa, part d'in da suka saba sauka suka nufa, bayan Fanan ta aje masu kayan su kwanciya sukai don su huta har lokacin Magrib yayi sannan Haisam ya tashi don zuwa Masallaci itama ta tashi tayi sallar, ana gama salla Hajiya Maryam ta dawo, part d'in nasu tazo ganin ba kowa a cikin parlon yasa ta kira Fanan d'in a waya ta sanar mata tana a parlor, fitowa tay da murmushi itama Mom d'in nata d'an murmushin take mata tana zuwa ta rungumeta tana fad'in tayi missing nata itama tace tayi nata, bayan ta d'ago bin ta da ido Mom d'in tayi kaman mai nazarin wani abu can tace mata bata lafiya ne taga idanunta sun fad'a, har saida gaban Fanan ya d'an fad'i, tana murmushin yak'e tace mata tundai halin data shiga ne acan Us na sanin zancen Auren da Haisam d'in yayi a 6oye shiyasata har ta rame, jinjina kai tay cike da gamsuwa ta kama hannunta tace suje part d'in ta, Bedroom d'inta suka wuce suka zauna a bakin gado gaba d'aya ta maida hankalinta akan Fanan d'in ta tambaye ta ya suka k'are da Hajiya to, jimm tay tana tunanin abunda zata ce mata, tasan muddin ta fad'a mata ta amince to tabbas ran kowa sai ya 6aci har Haisam d'in ba k'yale shi zatai ba ita kuma bazata so hakan ba, d'an yamutsa fuska tay tace "Mom ki bari in huta sai mu yi Maganar we didn't arrive long ko Abinci bamu ci ba" wani kallo ta bita dashi tace to miyasa basu ci Abincin ba bacin already table a shirye yake tace mata sun bari su huta ne kuma basu jin yunwa sosae, tambayar ta Haisam tay tace yaje Masallaci daga baya gudun karta matsa mata kan Maganar ta mik'e tana fad'in bari taga in ya dawo sai su ci Abincin ta nufi hanyar fita Mom d'in ta bita da ido, tana komawa part d'in su ta shige Bedroom tay kwanciyarta a ranta tana raya ko zata fad'i mata sai Haisam ya bar gidan,

sai bayan sallar isha ya dawo Fanan tace mashi suje suci Abinci, kusan gaba d'aya suka ci Abincin harda Farha da Hajiya Maryam da ba laifi ta sakar mashi fuska da suka gaisa, sai can wurin k'arfe goma na daren Dad d'in su ya dawo har part d'in nasu yazo suka gaisa Fanan ta rungume shi tana mashi shagwa6ar tayi missing nashi sosae shima yana fad'i mata yayi nata Haisam dai sai murmushi yake daga baya ya tafi, tun daga lokacin Fanan ta fara zille ma Mom d'in nata bata bari su zauna tare su dad'e don karta yi mata zancen, Sosae Haisam yake k'ok'arin faranta mata duk suka kasance tare, haka Fatuu ma yana yawan kiranta a waya tay ta zuba mashi shagwa6a,

Ranar Alhamis da yamma ya shirya zai koma saidae a ranar da safe Mom d'in shi ta kira shi ta sanar dashi tana son ganin shi yaje Abuja kafin ya koma don tasan yana Lagos d'in, lokacin daya kira Fatuu ya sanar da ita yayi tunanin zata nuna damuwa amman ga mamakin shi bata nuna ba tana murmushi tace mashi ba komai Allah ya dawo dashi lpy sosae yaji dad'i dama duk itace damuwar shi, a ranar da yamma yayi sallama da Hajiya Maryam Fanan ce ta tafi kai shi Airport, ita ke driving Motar yana gefe hannun shi ruk'e da nata, cike da k'auna sukai sallama da shi ta dawo cike da jin kewar mijinta, bayan ta parker Motar a parking space, tana shigowa cikin parlor ta iske Hajiya Maryam zaune da Farha suna kallo a Tv, nufar su tay tana sanye da jallabiya tayi rolling veil ta tsaya a bakin kujerun tay mata sannu tana kallon ta tace har ya tafi tace eh, shiru suka d'an yi kafin ta juya zata tafi d'aki taji muryar ta tace "Wait I want to talk to you" daramm gaban Fanan ya fad'i, dakatawa tayi ta kai idonta akan Mom d'in su ta nuna mata sofa d'in gefen ta tace ta zauna,

"Yanzu dai ai nasan kin huta sosae so am all ears ya kukai da Hajjaju ta amince an saki yarinyar nan?" Shiru Fanan tayi idonta a kan had'add'an carpet d'in k'asan parlon, maimaita mata tambayar tayi sannan ta d'ago ta kalleta gaba d'aya sun kafeta da ido harda Farha itama tana son taji amsar da zata bada, Sigh tay a sanyaye tace mata Hajiya ta k'i amincewa tace tayi hak'uri su zauna tare da ita, tun kan ta k'arasa Hajiya Maryam ta yamutsa fuska tana kallon ta har ta gama sannan cikin d'aga murya tace "You're telling a lie Fanan, daga yanayin face d'in ki nagane ba gaskiya kike fad'a man ba, kar ki manta ni na tsugunna na haife ki, so zan iya gane in kina 6oye man abu, dama tun da kika zo na fara zargin wani abu k'in tsayawa muyi magana ya k'ara k'arfafa zargin nawa, Now tell me the truth, else, ranki zai yi mummunan 6aci!" A fusace tay Maganar, abu Fanan ta had'iya kafin murya na rawa tace Ok zata fad'i mata gaskiyar, nan ta fara fad'i mata yadda sukai da Haisam ya nuna mata in ya saki Yarinyar za'a cuceta ne tunda shi ya fara saninta ya san hakan ne ma yasa Hajiya tun farko ta hana ya saketa, tun kafin ta gama ta katseta da tambayar "sai kika amince yaci gaba da zaman da ita???"

Cikin yar in ina tace mata yayi mata alk'awarin zai masu Adalci kuma daga ita bazai k'ara Auren wata ba shiyasa ta amince don tasan ko sun zo wurin Hajiyar ba amincewa zata yi ba tunda shima ya nuna zai cigaba da zama da ita.....,

Buga hannun kujera Hajiya Maryam tayi tare da mik'ewa tsaye cikin daka tsawa tace "Enough Fanan! I never knew you were such a fool until Today, ba a iya sakarci ko wawanci kika tsaya ba har hankali baki da shi, yanzu ke ashe dama baki da wayau har haka, wato ya zauna yayi maki dad'in baki shine kika hau kika zauna ke gaki shashasha har ki ka kasa gane cewa son yarinyar yake shiyasa ya fake da hakan, in don abunda ya shiga tsakanin su ne ba sadaki ya biya ba to miye abun cuta ko wani cin zali a ciki......!" Sosae take fad'a ta inda take shiga ba tanan take fita ba a k'arshe tace sam bata yarda da amincewar da tayi ba don haka dole ta canza ra'ayi ta nuna mashi bata amince ba, shiru Fanan d'in tayi kanta a k'asa, ganin yadda ta d'auki zafi yasa ta d'ago kai idanunta cike da k'walla tace ma Mom d'in nasu ita gaskiya ta riga ta amince bazata canza ra'ayin ta ba tunda ya nuna yana son cigaba da zama da itan kuma Hajiya ma na so ita ta hak'uri sannan ita yarinyar sam bata da wata matsala zasu zauna lafiya,

rai a tsananin 6ace Hajiya Maryam ta nuna kanta tace "Fanan! Ni kike fad'a ma haka! ni kike k'ok'arin nuna ma kin za6i faranta ma mijin ki fiye da ni duk da komai nike ina yi ne don ki dawwama cikin Farinciki, don in ga rayuwar ki baki shiga cikin matsala ba!" Girgiza kai Fanan ta fara yi k'wallan da suka taru suka fara zubo mata cikin karyayyar murya tace "No Mom ba haka bane wllh, is just dat in life Sometimes we must sacrifice our own happiness for the sake of those we love, yanzu in na za6i farinciki na kad'ai zan bak'an ta ma mutane da yawa, Hajiya bata so, shima baya so sannan ita kanta Zarah bazata so ta zama bazawara ba, sannan yan'uwanta ma bazasu so ace an sake ta ba that's why na hak'ura kuma nasan in sha Allah zan ci riba tunda Allah yace yana tare da mai hak'uri" wani kalan murmushin takaici Hajiya Maryam tay tana jinjina kai da alama ta kashe bakinta ta kasa ma magana, ganin yanayinta yasa Fanan sauka daga saman kujerar ta duk'a saman knees d'inta ta shiga bata hak'uri tana fad'in don Allah ta fahimce ta, can ta sauke nannauyar ajiyar zuciya tace "Ok, kiyi yadda duk kika ga yayi maki Fanan rayuwar ki ce ba tawa ba, dama katsalandan ne irin nawa yasa na zaqe, amman ki sani ba baki nayi maki ba indai Namiji ne gaki ga shi zaki nadama ne, ina zaune wataran zaki kira ni kina kuka tunda har kika za6i farincikin shi fiye da naki farincikin ma na k'arfafa mashi ya zauna da wadda yake so, uhmmm harna tausaya maki Fanan, duk da a lokacin bazan ji tausayin ba ko misk'ala zarratin!!!" A kausashe tayi Maganar tana huci ta na gamawa ta nufi hanyar Bedroom a fusace Fanan ta fashe da kuka tana bata hak'uri tana fad'in ta Fahimce ta don Allah hakan kaddarar ta ne.......

*ASM 077*

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*

.........Sosae Fanan ke kuka maganganun Hajiya Maryam sun ta6a mata zuciya sosae hakan ya k'ara tado mata rad'ad'in da take ji dangane da Auran Haisam d'in, dama ko a can Katsina ba K'aramin k'ok'ari take ba ta na dannewa, gaba d'aya abun yayi mata yawa a zuciya sosae take ta Kuka cikin kukan ta fara fad'in ita ya zata yi ne, tasan ko ta nuna bata so in dai hakan kaddarar ta ce dole sai yaci gaba da zama da Zarah k'arshe zata tada hankalin ta ne a banza, duk wannan abun Farha na zaune a inda take idon ta akan Fanan d'in dake a durk'ushe tana kuka bazaka gane yanayin da ke akan fuskar ta ba, mik'ewa Farhar tayi tana sanye da doguwar riga roba da ta kamata, wurin Fanan d'in tazo ta kai hannu tana k'ok'arin d'ago da ita Fanan d'in ta kalleta idanunta har sun yi ja fuskar jage jage da hawaye, ce mata tay ta tashi Fanan d'in ta mik'e ta koma kan kujera ta zauna itama Farhar ta zauna daga gefen ta idanunta akan ta, itama Fanan d'in kallonta take tana cigaba da zubar da hawaye can Farhar tace mata tayi shiru karta yi ciwo fuskarta a d'an yamutse tayi Maganar, hannu Fanan ta kai ta kamo hannunta guda cikin Muryar kuka ta fara Magana "Farha kema na baki haushi ko?" shiru tayi fuskarta kamar a d'aure dama ita yanayin fuskar ta a koda yaushe haka yake can tace a'a ita bata ji haushinta ba tunda taji zata iya kawae dai tayi mamakin yadda ta amince ta zauna da wannan yar talakawan a matsayin kishiyanta dama wadda suke the same level ne da sauki, hannu d'aya Fanan ta kai tana share hawayen fuskarta bayan ta gama a nutse ta fara ma Farha magana da sautin kuka tace "I want u to understand wacece Zarah ba yadda kike tunanin ta ba take, she's a very nice person bata da matsala wllh, kuma don ita talaka ce hakan ba yana nufin tana da illa ba Saboda da mai kud'i da talaka we're all the same a wurin Allah kuma in yaso zai iya canza rayuwar su suma su zama masu kud'in da baki ta6a zato ba, muma da kike ganin muna dasu bafa fin su muka yi ba ya bamu, kawai hikiman sa ne yasa ya raba don kowa yay benefiting da kowa, in ya bamu kud'i so yake muyi amfani da su wurin taimaka ma wanda bai ba bawai mu ci mu kad'ai ba kuma mu kyamace su, kinga kenan kamata yay mu rink'a girmama wanda bashi dashi tunda ta silar shi Allah zai k'ara bud'a mana because whenyou give you always get back more in return, sannan ta silar yi masu Alkhairi zai kai ka har Aljanna, Farha i advise u, stop hating the poor pls ki rink'a kyautata masu I assure u zaki ji dad'in rayuwar ki don kema Allah zai rink'a kyautata rayuwar ki zai rink'a baki way out a dukkan matsalolin ki....." Dakatawa tay tana numfasawa ita dai Farhar bin ta da ido kawae take still da yanayin da fuskar ta take tun farko,

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.