Deejamah Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Deejamah_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 2 of 19
Page :1️⃣_5⃣🖊️
_DAN DANO_
_________Ihu yakeyi sosai har wani numfashi yake daukewa tsananin azaba,na firgita da ganin katon mutum Mai jini a jika kamar wannan yana ihu haka gashi ko wando Babu a jikinsa da gashi sai wani dan shirt, lamarin ya firgita Ni,cikin sauri na Isa wajen don Jin abinda ke faruwa.........la ilaha'ilallahu abinda nagani yasani firgici matuka.
Wasu kyawawan 'yan mata na gani son kowa kin Wanda yarasa,duk cikansu Babu makusa,sai dai dana lura da kyau na gane acikin su daya tafi kyau,rike Daya take da wandon a hannun ta,wacce tafisu kyan ne naga ta dauki wani Abu a cikin kwanon Sha Yana tururi ta bude kafar sa, dai-dai wajen abin fits*rinsa ta tsiyaye wannan abun dake kwanon,ihu ya saki Mai cike da wahala numfashi yaja a wahale tare da fadi "Innalillahi wa Inna ilaihir raji'un don Allah kuyahakuri wallahi har abada bazan sake ba na tuba wallahi.
Kwanon na duba naga soyayyar mangyada ce tafasashshe suke zuba Mai a joy..*ck nashi.
Bai karisa maganar ba dayar ta daga hannun tabashi punch a mouth,a take anan mouth din yafashe tace"Dalla yimana shiru mutumin banza gaka a fuska sak limami,Amma a cikin zuciya Kai Dan iska ne Lamba daya.
Wani ihun ya yanka jikinshi gabada Banda rawa babu abinda yake,ga zufa na kwaraya masa a jiki.
Duban joy.*ck din nayi gaba daya tatashi tayi sundum ga fatar tayi luhu- luhu ta duru ruwa alamun dai Kuna.
Kyakkyawan cikinsu tasake daukan kwanon Shan ta watsama abun nasa Aiko yasake sakin wani ihun mai firgitarwa,gabadaya sai da namar wajen ya kwashe.
Shikuwa tunda ya saki ihun Nan ya suma a take anan,ganin haka yasa 'yan matan yarda kwanon Shan suka kinkimi rishon su da sukazo dashi don yin wanna aikin,suka fito daga tsohon ginin (kankon),wata hadaddiyar mota kirar benz suka nufa,Shiga sukayi sanya Sanya dariya da tare da fashewa da ihu.
Wani madai daicin gida suka nufa,sauka Daya daga cikinsu tayi tasa key tabude gate din sannan tashiga tacire padlock din ta ciki ta wage gate din.
Shiga da motar sukayi ciki tare da paka ta a inda ta dace,suka fito suka shiga Falon.
Masha Allah Falon dan dai-dai yaji kujeru kirar royal chairs dark blue zallah sai kwalliyar golden tare da troepillows golden Sai Chinese carpet golden,plasma center table set din kujeru sai labulaye dark blue.
Ga badayan su watsewa sukayi a cikin kujerun suna mai da numfashi,mikewa kyakkyawar cikinsu tayi tace"Babie's nifa banyi sallah ba bari naje bedroom dina nayi idan nadawo akwai history.
Amsawa sukayi da "Ok baby,Daya a cikinsu tace"A dade anayiiiiii,gaba Daya suka hada baki wajen furta"Sai gaskiya!!!!!
Dariya suka kyalkyala gaba dayansu,itako ta shige toilet
Washegari karfe 7:30 duke da lectures gashi Mr Right ne keda first period sunan da suka samasa. Wai suwaye 'yan matan nan Shakeerah da Fauzi sai khadee.
Shakeera duk Wanda yaganta yasan 'yar gidan Hutu ne saboda jikinta kawai yanuna ga diri fatan kaman wani butter- butter duk wanda yaganta yaga 'yar hutu da jin dadi,akwai yauki da yanga ga aji,sai dai abinda ya kasheta masifa,masifaffiyace na tashin hankali.
Fauzi ma babaya wajen kyau sai dai duk kyanta batayi ko rabin na shakeera ba,ita Kuma black beauty ce tanada kyanta dai-dai misali, itama akwai ado da kwalliya ga yauki sai dai Kash itama masifa shi ya kasheta.
Sai hajiya khadeeja ita Kuma farace tasss,tana da kyau sai dai zata biyu bayan shakeera,tana kwalliya da ado ga iyayi da feleke,sai dai Kash khadee akwai tsoro na bura uba.
Haduwar makaranta yahadu wato KASU anan suka hadu,halayyarsu ce da tazo guda shine suka hada kai suka sawa kansu daimond ladies,sai dai ko wacce kullum zancen ta shine daukar fansa,ko me yafaru dasu Sai munji a gaba.
Duk cikansu Riga da wando suka Sanya sannan suka dauko hijjabs dinsu babba yadi hur hudu suka Sanya.
Ko breakfast basu hada ba suka zari mukullin mota tare da figarta suka hau kan titi.
Shakeera ta iya tukin gan-gan ci a titi idan tana driving masu mota da daba bata hanya suke,tunda ta sanyo kan motarta cikin school din aka tsaya dubansu samari da 'yan mata kowa kallonsu yake,burin ko wane saurayi da budurwa ace yana hulda da daimond ladies.
A dai-dai inda ake parking motoci suka faka tasu,fitowa sukayi daga cikin motar shakeera ta sama motar key sukuma suka nufi hanyar class din.........
Gaba daya jan birki sukayi a kofar class din,domin Mr Right ya rigasu shiga dafe kai sukayi hannu khadee tafara yarfewa Cike da tsoro tace"wayyo Allah shikenan ya rigamu shiga yanzu ya zamuyi?gashi test akeyi,harara fauzi ta dago ta watsa mata.
Shakeera ce takariso tana fadin "A'ah babies meyafaru na ganku a waje haka?Fauzi tadago tace"kinsan dan rainin wayon Nan ne a ciki gashi bamu taba late ba sai yau,yamana warning akan kada abari yariga shiga to gashinan.
Tsaki shakeera taja tare da shiga cikin class din tana furta"Excuse Sir! Tayi maganar tare da shigewa class din,har takai wajen sit dinta sai dai ta juyo"Oh babies ku shigo mana time yana wucewa gashi test akeyi,daga mr right har student din binsu da kallo sukayi babu Wanda ya Isa yayi magana domin kowa yasan diamond ladies.
Bayan sunga ma test aukayi summit saboda suna da kokari sosai barimma shakeera,direct gida sukayo.
Koda suka dawo shakeera ce da girki don haka kitchen tashiga bayan ta cire hijjab dinta.
Girki tafara,tunanin Dora Abu Mai sauki tayi....a karshe ta yanke shawarar yin taliya da manja da yaji.
Kwala mata Kira fauzi tayi,cikin Sauri tafito daga kitchen din tana fadin"Meye haka fauzi?irin wannan Kira haka,wat hppnd?
Duban ta fauzi take tace"Zauna ki kalli TV kiga meke faruwa.
Sai a lokacin ta maida dubanta kan TV.
Labarai aka fara tare da pic din wani mutumi zai kai 46years,dan jaridar ne yafara magana kamar haka"To jama'a ana dara ga dare yayi,wannan wannan bawan Allahn ne malamin makarantar islamiya da yayiwa dalibarsa fyade 'yar 12years,Wanda aka dade ana nema,to gashi yau ya kawo kansa a dalilin wasu 'yan mata da suka hukuntashi a cewar su kotu ta kasa yanke masa hukunci dai-dai da lefinsa.
An dai sameshi a wani kango ne Rai a hannun Allah domin an Kona masa abin fitsarin sa,a binciken da likitoci ma sukayi da wuya wajen ya sake aiki,sai dai bari muhadaku da bawan Allahn da iftila'in nan ya sameshi.
Fauzi ta saki ihu tare da cewa baka ga komai ba ma kadan akayima.
Nuno shi akayi a gadon asibiti an nannade joyst*ck din nasa da bandeji magana yafara bayan"Assalamu alaikum jama'ah,a yau dole na amsa lefin da na gasgata a kotu, tabbas ni nayiwa wannan yarinyar fyade.
Dan jarida yace"To Allah gafarta malam me yahanaka da amsa lefin ka a kotu?
A jiyar zuciya ya sauke Wanda da ka lura zakasan cewa da kyar yakeyin magana"Saboda inajin kunyar duniya,Ina tsoron mutumcina ya zube a idon duniya,na manta cewa da kunyar lahira gwamma na duniya.
Dan jaridar yace"To Allah gafarta malam Aida an nemeka anrasa ko,ko zaka iya sanar damu inda ka gudu?
Girgiza Kai yayi yace"Sanar daku bashida amfani,nidai abinda nasani wasu 'yan mata suka biyu ni har inda nake suka daukeni suka kaini kango,bayan sun min dukan tsiya shine suka konani,har yau Cike nake da mamaki da tsoro, Ina tunanin Anya su din mutane ne?saboda suna da karfi,sannan kuansu yayi yawa,a tunani na aljanu su suka aikata mun wannan lamarim.
Dariya Dan jarida yayi sannan yace"to masu aikata wannan lamarin da masu niyyar aikatawa,Kila wannan abun fa da yafaru da Allah gafarta ya zame muku ishara a gaba.
Nan dai aka gama labaran aka gama labaran,mikewa shakeera tayi tare da shigewa kitchen,ita kuwa khadeeja banda kuka Babu abinda takeyi saboda ita khadeeja akwai tausayi.
Tsaki Fauzi taja tace"kedai Kika sani Sai kace ba kece mai soya mai a risho ba.....khadeeja batasan sanda ta fashe da dariya ba,don maganar ya bata dariya.
Xahratty ce✍🏽
Lallai Alqalami 🖋️ Yafi takobi🗡️
💕💕
❤️
[7/18, 2:05 PM] Xahratty🥰😘: 💐✨ *DIAMOND LADIES* 💐✨
( Daukar Fansa )
Story& writing
By
PATEEMA ZAHRA LAWAL
______✍🏽______
*TAMBARI WRITER'S ASSOCIATION*
🔱(( Home of Expert and talented writers,da tambarin mu muke tafe domin kawo gyara da cigaban Al'ummah))
*_T.W.A_*
_________________________
https://www.facebook.com/Tambari-writers-Association-106058867819812/
_________________________
Marubuciyar⬇️
_ _A DALILIN 'YAR TSUNTUWA_
*DA*
_ _MIJIN ZAHRA_
*Littafin diamond ladies (Daukar Fansa) na kudi ne duk maiso ya turo katin Naira dari#100 katin waya ta wannan number 08060710719,sai nayi adding din mutum a group din.*
Bismillahir-rahmanir-raheem.
*Da sunan Allah Mai rahama Mai jin Kai....*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.