Trending Hausa Novels

Gidan Aunty Book 2 Complete Hausa Novel

Reading file: GIDAN AUNTY BOOK 2.txt

Chapter 5 of 13

Page 7&8💖

Kai tsaye khaleed yana fita daga part d’in dada part d’in ummey ya nufa itama ya mata sallama bayn gift d’in da ta basa ya kaiwa zahra, mahma ma da dada gabaki d’aya sai da suka bawa zahra gift, king baya gida shiyasa basuyi sallama sea ta waya, lokacin da zai tafi sai kallan part d’insu ilham yake ko zai ganta amma babu ita babu alamarta, murmushi ya saki lokacin da ya tuna kunyarta, ji yake kamar ya je part d’insu ya dubata amma yasan hakan ba meyuwa bane . 2:30pm na rana jirginsa ya tashi zuwa Abuja, 1hour 15mins ne ya kawosa Abuja , yana fitowa harabar Airport ya tarar da zahra na jiransa, hannu ta mi’ka masa kamar wasu friends sukayi shaking , fuskarta cike da farinciki ta furta “ Nayi missing d’inka yaya”. Nima nayi missing d’inki cewar khaleed , suna zuwa gida ya tarar da oumma ta had’a masa favorite food d’insa wato dambu da kuma zo’bo da yake matukar so, sun d’an ta’ba hira kad’an bayn ya bawa zahra gift d’inta kai tsaye d’akinsa ya nufa ya watsa ruwa, so yake ya runtsa amma kuma ya kasa Sabida muryarta da yake san ji, phone d’insa ya d’auka kamar zaiyi dialing wata number da yayi saving da MINE 💞 sai kuma ya fasa , sau biyu yana ‘ko’karin kiran wayar , daga karshe ajje wayan Kawai yayi yana lumshe ido , shi kad’ai yana sakin murmushi abunsa.

*******Ilham ko data gudu, kai tsaye part d’insu ta wuce har mamy na tanbayarta lapiya amma bata amsa musu ba sai faman sakin murmushi take ita kad’ai , tana shiga d’aki ta kulle ‘kofar tare da kallan d’an ‘karamin box din brown colour meshegen kyau, yana bud’e wata sarki ce aciki sai faman walwali take yi ita kadai, zaro idanuwa ilham tayi sosai sarkar tayi mata kyau musamman Heart d’in da ke jikin sarkar ya fi komai d’aukan hankalinta, gaban mudubinta ta’karasa har Zata saka sarkan sai ta fasa , yar ‘karamar letter d’in dake jikin box d’in ta bud’e , wasu ‘kananan flowers ne Suka fara fitowa daga jikin paper ne me design din flower a jiki, kan gadanta ilham ta koma tana sakin ajiyar zuciya , letter d’in ta soma karantawa cikin zuciyar ta, daka ‘karshe ma pillow d’inta ta d’auka taba boye fuskarta ita kadai sai faman sakin murmushi take, lokaci zuwa lokaci tana kallan sarkar da ya bata da kuma letter d’in, gabaki d’aya yinin ranar da tunanin khaleed ta yini , ko me zatayi sai ya fad’o mata arai musamman lokacin da yake furta “ ki kulamun da kanki”, rufe idanuwanta tayi gabaki d’aya tana tuno abunda ya faru d’azu, sai taji kamar bata kyauta ba, amma wani zuciyar na fad’a mata Daidai ne abunda tayi.

✨✨✨✨

karfe 9:00pm na dare gabaki d’aya familyn Nahyan suna falon dada banda king da gabaki d’aya ynxu baya shigowa part d’in ko wannan su, a wannan karan har da Ammeey a falon, duk Wanda ya kalli fuskarta zai san tana cikin damuwa, amma babu Wanda ya kawo wani abune yake damunta sai canzawar king da kowa yasan tafi kusan ci dashi, hatta part d’in ta yanxu baya shigowa , abunda ya ‘kara tayar mata da hankali sabida ‘kullun maganin da bokansu ya bata, indea ba a cikin abinci tabasa ba nan da sati d’aya toh komai zai iya lallacewa, a binciken da tasa ayi mata akan tahee kuwa , hatta bokansu baya iya ganin komai a duk lokacin da yake bincike a kanta cikin abun tsafinsu, sai hasken da yake kashe masa idanuwa da tsoratar dasu, bakomai ne yafi d’aga mata hankali ba musamman dawowar tahee da boka ya tabbatar masu, sannan a wannan karan tabbas idan ta bari tahee tashigo cikin gidan komai nata data d’au shekaru tana ginawa zai rushe rushewar da bazea ta’ba gyaruwa, duk da maganar boka ya girgizata sosai amma duk da hakan bata karaya ba , sannan tayi Al’kawarin bazata ta’ba barin tahee ta cikin familyn nan ba , yanxu burunta kawai king yaci gubar da bakan tsafinsu ya bata, shiyasa ta fakaice da had’a wa duka family d’in dinner , sannan ta had’awa king favorite kunun a yarta da ta zuye duka gubar a ciki yanda ci d’aya zai tsinka masa komai na jijiyoyin jikinsa. Amma gabaki d’aya babu king babu alamar sa gashi ta hana kowa ta’ba zoban da tayi masa, sau hud’u Ammeey tana gwada kiransa a wayrta , amma ko sau d’aya be d’aga mata kiran ba, hakan ba ‘karamin ‘bata mata rai yayi ba , har wajan 9:30 king ne shigowa , kowa ya damu da’kin shigowarsa Amma duk sun masa uziri, gumine ya soma gesowa Ammeey ganin saura mintu na kudun ayar data sawa magani ya canza zuwa launin’baki,rai a’bace Ammey ta d’auki kunun ayar zata tafi, gabaki d’aya mutanan falon kallanta sukai, murmushi tasakar musu cikin rarrabewar murya ta furta “ zan sa masa a fridge ne kafun ya dawo”, girgiza Mata kai abeey yyi, “ no karki damu ki dawo kawai kiyi zamanki “, a rud’e Ammey ta kallesa “ Dama akwai abunda nakeso na saka a ciki sai yanxu ya fad’o mun”, ki barshi kawai, cikin zuciyar Ammey kamar taje ta sha’kesa ta furta bazan dad’e ba yanxu zan dawo ai, gudun kar ya sake magana tayi saurin juyawa , lokaci d’aya momy da ummey suka bita da kallo, hakanan kawai ummey take jin kamar akwai abunda ya kamata ta sani , amma kasan cewar ta mace me ‘boye komai sai ta ajje zancen a gefe, wayar ilham ce ta soma ‘kara gabaki d’aya sai hankalin kowa ya koma kanta, ganin number ba suna ne yasa ta d’an mi’kewa “ Dama husna ce ta kira ni”, gida mta kai sukayi kafun ta wuce , kallan juna sumayya da firdausi sukai, da ido suke nunata Suma ‘kunshe dariyarsu.

Saida ta tabbatar ta shiga d’akinsu ta rufe , alokacin kiran farko har ya katse, kafun wani ya sake shigowa kamar bazata d’auka ba , sai kuma ta d’auka bakinta d’auke da sallah, ajiyar zuciya taji an sauke ajiyar zuciya, gabantane ya soma fad’uwa jin anyi shirune yasata cire wayan a kunnan , still ba ayi magana ba , ‘karamin tsaki taja zata kashe taji ance mata “sorry “, da Sauri ta ri’ke wayarta dake neman fad’uwa ‘kasa dan sam batayi zatan shi bane , da ‘kyar bakinta ya iya furta “ yaya khaleed barka da dare ya hanya “, shiru be amsa ba, kara maimaita tayi nan ma be amsaba,hararar wayar tayi kamar ta kashe sai taji saukar muryarsa kuma “ I missed you “, shiru ilham tayi tana saurarar bugun zuciyarta, me yake nufi da maganganunsa,” Ba’amsa?” Ya tanbaya nan ma shiru tayi ta kasa amsa masa murmushi yasaki kad’an kafin ya furta “ shikenan, kula mun da kanki kinji? Good deary “ sea Kuma kit ya kashe kiran , bin wayar tayi da kallo kamar me jira ya ‘kara kira , ita kadai sai tsaki take ga wani irin feeling dataji yana tasoma ta tunda ‘kafarta har zuwa saman kanta, a gefe ta ajje wayar lokaci zuwa lokaci tana dubawa, a haka bacci ya d’auketa tare da wayar a hannunta.

A ‘bangaran Ammey kuwa wani bakin cikine ya tokare mata ma’koshi , tana komawa part d’inta a zuciye ta jefarda jug d’in take a wajan ya fashe gabaki d’aya kunun ayar ya zube a’kasa , ko cikakken muntuna biyu be ba daga kalar kunun ya koma ba’ki ‘kirin dashi, sai a lokacin ta ankara da abunda tayi, cikin mummunan ta shin hankali ta d’ora hannayenta aka tana kwarara ihu ko damuwa da Ajiyata batayi, gabaki d’aya ta fita hayyacinta, zoban hannunta ta murza take a wajan ta ‘bace battttt.

YOLA

Cikin matsanan ciyar tashin hankali Ammeey ta bayyana cikin babban falonsu dake cike da kayan shirka , sabida tashin hankalin da ta shiga a wannan karan ko damu da kulle fuskarta batayi ba kamar yadda ta saba ,ragowar abokanan shirkar tata ko wannansu na zaune cikin jajan ‘kyalle daga cikin su zuwa ‘kaurinsu ko kaya babu a ciki, cikin kururuwa Abar kauna take kiran sunan gunkinsu, kusan sau uku be amsa ba kuma babu Wanda yayi magana cikin mutanan wajan, a na hud’in ne data kara kiran sunanta taji saukar tsawar da tunda Tashi ga cikin kungiyar ba a ta’ba yi mata ba Sabida ita d’in kullun me nasara a fagen aikinsu.
Cikin kausash shiyar muryarta mara dad’in ji ta daka wa Abar ‘kauna tsawa da har saida tayi suman wucin gani, cikin muryarta mara dad’in sauraro rai a’bache ta kalli Abar’kauna “ kinyi sake , kinyi sake , kin yi saken da damar ki ta kubuce miki, tabbas kisaka aranki daga rana irin ta yau , ginin ma sarautar da kike ‘ko’karin kammala lawa ta rushe, rushewar da bazata sake tashi ba har sai kin dawo da yarinyar ta kikayi sanadiyyar barin ta gidan, tabbas Abar ‘kauna kina cikin tsaka , Sabida lalatawa dodan tsafi aikin sa, idan baki kashe sa nan da kwana bakwai ba , to tabbas yayi miki nisa hakan na nufin lokacin tonuwar asirin ki ya bude, dama d’aya kike da ita , ki dawo da yarinyar cikin gidan sannan ki bawa dodan tsafi Jinin ta dana cikinta,
Idan ta dawo kuma zaki iya shiga kasada komai zakiyi kuma baze kara tasiri akanta ba , sabida tana tare da Jini guda hudu da kikayi kokarin rusawa, dawowarta kamar tonuwan asirinkine,ta ‘karasa tana sakin wata yar iskar dariya mara dad’in ji, lokaci d’aya wani ‘bakin hayaki ya cika falon tsawan mintuna kafun ya washe babu wannan Matar, wata iriyar kururuwa Ammeey ta fara a haukace kamar ta ‘babbiya, sam ta fita cikin hayyacinta, fad’i take sai na kashe ka , sai na ka she ka, gabaki d’aya bata jikin hayyacinsa , suma sauran mutanan zagayeta suka somayi suna wani irin surutai kafin lokaci taya gabaki d’ayansu su bace duka .

✨✨✨✨

A ‘bangaran king gabaki ya ‘kara sauyawa sama da ydda aka sansa a baya , kwata kwata baya murmushi , baya fara’a sannan baya yiwa kowa magana sai dai ya zuba maka narkakkun kyawawan idanuwansa masu ladaftar da mutum,gabaki d’aya ya sauya ya zama wani irin Miskili na bugawa a jarida , ga saurin zuciya da ya koya , hatta abinci yanxu baya sai ummey ko samreen sun soma kusa sannan da d’ar zaici spoon kad’an , yana shiga sabgar kowa a gidan shiyasa kowa ya kara shiga taitayinsa, lokacin da Amray ta samu labarin farfad’owarsa da murnarta ta dawo gidan, alokacin dada ta sa masa kukan sai yasha furar da ta dama masa ganin baya cin komai hatta furar da yake mugunso, cikin iyayi Amrah ta shiga cikin falon,sabida tsananin farincikin da ta shiga lokacin da taji labarin ‘batan Tahee , shiyasa tazo da confidence d’inta bayan kwallin da mamanta ta bata acewarta Indai suka had’a ido da king daga lokacin ta mallakeshi komai zata iya sasa, tana shigo wa kai tsaye ta sauke idanuwanta da suka ji kwalli , Daidai lokacin da yake d’ago idanuwansa, cikin sa’ a idanuwanta suka shiga cikin nasa , da Sauri ta d’auke nata idanuwan sabida wani irin abu daji ya shigeta, lokaci d’aya farin ciki ya kamata ganin sun had’a idanuwa dashi, cike da kwarkwasa ta ‘karaso inda yake mo motsawa beyi ba , kai tsaye kan kujerar da Yake ta nufa tare da zama daga gefensa, be ce mata komai ba , har ta rangwafo daniyar ta’basa , bata Ankara ba sai saukar gigitaccen marin da yasaka kunnuwanta toshe wa lokaci guda , ga wani jiri jiri da ya soma d’i barta bashiri ta saki wani gigitaccen ihu Sabida azabar marin da taji, bata gama jin zafin marin ba ta sake jin saukar wani lafiyayyen marin dama da hagu , a wannan karan ihun da tayi saida mahma da dada sukaji, da sauri suka fito alokacin da ya ‘kara dagewa ya tsinka mata mari, d’an kwalin kanta ya dam’ka da karfi dayasa attachment dinta Fito wa , wani irin ball king yayi da ita , mahma da ya fara bata tsoro da sauri tazo zata ri’keshi yanda yake a zuciyen nan bai san lokacin da ya hankad’ata ba itama , a rude dada ta la’be bayan kujera cikin tashin hankali ta fara danna wayar ta da’kyar ta lalubo number abeey sabida rud’ewa, lokacin yana falonsa shi da ummey, da sauri suka nufi part d’in dada , lokacin da king ya ‘kara saukewa amrah kyakkyawan marin da se da hannunsa ya Fito a fuskarta, cikin ‘bacin rai da kausash shiyar murya dake firgita mutum ya daka mata tsawa “ minti biyar na baki daki bar gidan nan, wallahi ko me kama da ke na ‘kara gani a cikin gidan nan , sai dai uwarki ta sake Haifo wata, Tashi kiban waje “ cikin azaba da fitar hayyaci amrah ta mike da kyar ga hawaye da majina dasuka ‘bata mata fuska, ko bin takan jakarta batayi ba ta arta a guje ko tunanin inda zataje batayi , cikin tashin hankali ta fita daga cikin gidan tayi tafiya me dogon zango rai a bace ta d’auko coccine me tafawa zuga, tun tana tuni har ta soma ganin biyu biyu amma bata hakura ba , ta cigaba da shaye shayenta tana tu’ki , bata Ankara ba wata mota tazo ta bangajeta, sai motar tata ta soma kifawa kanta ya bugu Sabida abun shaye shayen da ta Shaka me ‘karfi d’aya sata yin accident d’in.

***** Abeeey na zuwa falon dada rai a ‘bace ya wanke fuskar king da mari, ummey ba hatta dada da mahma saida sukayi suman tsaye shima king a zuciye ya d’ago fuskarsa ya kana kallan abeey “ Ni ? Mari?” Shima sai alokacin abeey ya kula da abunda yayi, amma be nuna ba sai ma had’e fuskarsa da yayi , cikin sama sama da murya ya furta “ Ina iliminka yake da zaka saka hannu ka mari mace? Akan Wana dalili zakace karta kuskura ta ‘kara dawowa cikin gidan nan, kar ka manta wannan gidan gidanane da kudina na Gina sa , baka da hurumin da zakace kar Wanda yafita “, murmushi king ya saki da ya bawa kowa mamaki, “ really? Gidan ka ko? Toh kasani zan bar maka gidan naka inyaso ko wa kake so sai ya shiga “, zamewa ummey tayi a kasa ta kasa cewa komai, mahma ce tayi saurin shan gabansa ganin yana kokarin tafiya hankali a tashe “ No son , please ka kwantar da hankalin ka , let’s talk”, gabaki d’aya idanuwansa ya rufe ransa yayi mugun baci, cikin murmushi da bekai har zuciya ba ya furta “ why ? Me zan zauna nayi? I lost my beloved brother ? I lost my wife ? My baby ? And mahaifina yana fad’a mun gidan sane , to ki fad’a masa zan bar masa gida, long time ago na rasa farin cikine ? Menene yayi saura?nothing”, yana kai zancensa ya soma tafiya , mahma zata dakatar dashi abeey shima cikin daka tsawa yace ya rabu dashi ya tafi, tashin hankalin da ba ‘a sa masa date , sai a lokacin dada da tayi suman tsaye ta saka sallallami , ganin king yanar part d’in, cikin kuka ta furta “ yanxu zayyadu baka da imani? Duk halin da yaran nan yake cike bazama lalla’basa ba shine zaka kore sa ? Toh wallahi bari na fad’a maka , idan har tahanuni na yabar gidan toh Nima na barshi kenan “, da mugun shock abeey ya kalli dada da ranta ya baci itama cikin daka tsawa tace wa mahma ta d’auko mata mayafinta , dole mahma ta d’auko ganin yadda ran dada ya baci, Allah sarki ummey abun tausayi ta kasa cewa komai sai binsu da kallo da take . Kafun Abeey yasa a dakatar da king har ya fice daga gidan a zuciye, hakuri ya fara bawa dada da tace itama tafiya zatayi, da ‘kyar suka samu suka shawo kan dada har da ummey dake bata hakuri, akan cewa ran sane ya ‘baci Amma zai dawo insha Allah.

Gabaki d’aya a cikin gidan babu Wanda y samu labarin futar king har Ammey data ci alwashin ganin bayansa a yau, har dare kuma king ne dawo ba hakan ne yasa kowa yaji abunda ya faru, hatta Ammey sai a lokacin ta Samu labari take a Wajan wani irin zazzafan zazzabi ya kamata da ko motsi bata iyayi Sabida bakinciki da yake kokarin kashe ta .

***** king kuwa rai a mugun bace ya bar gidan cikin mugun speed ko zaki be d’aukaba, kai tsaye airport ya nufa cikin jirginsa , ba ‘bata lokaci jirginsa ya Dashi zuwa America.

AMRAH

Da kar aka samu wasu suka kira police station Sabida hatsarin da ya faru , suma suna zuwa aka dauki amrah sai asibiti, likitocin ne suka bukaci ganawa da yan uwan Amrahn amma aka sanar musu basu san kowa nata bai wayarta da ita mata lallace , Take a wajan likitoci suka tabbatar musu da matsalar kwakwalwa da amrah ta samu sabida mugayen kwayoyin da take ta ammali dasu .

Har washe gari babu king babu alamarsa sai a lokacin hankalin abeey ya kara tashi, d’aya daga cikin masu kula da jirginsu ya kira , abakinsa yaji labarin tashin jirgin king , kuma babu Wanda yasan wata kasa ya tafi, take a Wajan shima Abeeey ya yanke jiki ya fad’i.
Sau da yayi 2 days yana jinya , tun suna sa ran dawowar king harkowa yashiga damuwa , lokacin da khaleed ya kira ilham , kuka ta fashe masa dashi cikin tashin hankali ya tanbayeta me yafaru gabaki d’aya ta kwashe ta fad’a masa da ‘kyar ya kwantar mata da hankali akan cewa zai ne mosa. Babu inda khaleeed be duba ba da binciken da yasa ayi masa ko akwai Wanda yaga king amma kowa ce masa yake ya dad’e basa king a cikin idanunsa ba .
Kowa da abunda yake sakawa cikin zuciyarsa ummey Sosai ta shiga cikin damuwa , samreen ce kawai me kwantar musu da hankali dukda natan ma a tashe yake . Ammeey tun tana irga kwanaki ko zai zawo har sati d’aya ya zago hakan yasa har ciwo sai datayi kowa ya d’auka sabida barin king gida amma tsantsan tashin hankali ne ya kwantar da ita .

Saida amrah tayi 2weeks a hospital kafun mamanta ta samu labarin hatsarin da tayi cikin tashin hankali da doctor yace dole sai ankai amrah asibitin mahaukata sabida anan za afi kulawa da ita , ba ydda mommynta ta iya dole haka ta hakura aka kai amrah asibitin mahaukata, suma lokacin da familyn NAHYAN suka samu labari gabaki d’aya sai da Suka je dubata banda Ammeey da ynxu ta zama shiru shiru abun duniya ya dameta.

Haka rayuwa ta cigaba da kansancewa cikin familyn , kusan kullum sai khaleed ya kira ilham , tun yana boye mata feelings dinsa har ya fito ya furta yana santa. Sosai suke zuba soyayyarsu wani lokaci har hira suke da zahra idan ya kirata har maganar taje kunnan dadi, sosai kuwa sukai farinciki da hakan

Watanni sun cigaba da shud’ewa har lokacin king be dawo gida ba , sai 5 month suka san yana America dukda kome suke ciki yana sane amma ya sharesu, ba yadda ba ayi dashi ya dawo ba Amma yaki , a cikin wannan lokacin ne Abeey yasan da soyayyarsu ilham shima sukai hakan yayi masa dadi.

✨✨✨✨✨✨

4 YEARS LATER

💖💖GIDAN AUNTY 💖💖

07041879581
Mss Lee 💖

BOOK 2
Page 9 💖

4 YEARS LATER

Abubuwa da dama sun fara cikin tsawan wannan lokaci , har zuwa lokacin kuma babu Wanda ya ‘kara samun labarin Tahee sai addua da kullum ake mata, gidan sai ya ‘karayin shiru babu Tahee babu king,Amrah da king ya Koreta sai da tayi good 2 years a gidan mahaukata kafun Allah ya bata lapiya amma duk da hakan ta d’an tabu , lokuta zuwa lokuta tana abu kamar na marasa hankali, yan kiran sunan king akai shiga taitayin take har lokacin kuma bata ‘kara kuskuran koda tako ‘kafarta gidan ba ,ga wani irin abu da take ji lokaci zuwa lokaci a ‘kasan ta na mata zutt zutt Amma babu Wanda ta ta’ba fad’awa sai ma harkar less da ta koma ita da wata friend d’inta ,kullum suna manne da juna ko basa waje d’aya toh kullum suna cikin yin vidoe call. Cikin Shawan shekarun nan wani irin soyayya khaleed yake yi shida ilham da basa kwana d’aya basuji muryar zunansuba , tun ana d’auka abun da wasa har saida khaleed ya nufi dady da cewar a Aura masa ilham . Dady ba ‘karamin farinciki da mamaki yashiga ba , sosai kuma yayi farincikin hakan . Zarah ma yanxu an zama big girl duk wannan surutun da rashin jin ta dena su da wuya kaji surutun ta inva a wajan oummey da ta zame musu tamkar uwa ba , me share Masu hawaye , sau da dama idan aka gansu tare sai a yi tunanin oumma ce ta haifeta musamman gogewa da oumma ta ‘karayi sosai ta zama babbar hajiya , ayanxu bayan mall din da take Dashi ta ‘kara gida guda biyu da gida guda uku dayake duk mallakinta,sai kuma filayen da take siyarwa, babu Wanda zai ga oumma yanxu yace Itace a baya sabida yadda kudi da kwanciyar hankali ya zauna mata dukda har yanxu tana yiwa ‘ya’yanta addua kuma batacire rai a sake ganinsuba, lokaci zuwa lokaci tana zuwa bunkure kuma , yanxu wani irin zumunta suke yi abunsu kamar babu abunda ya ta’ba faruwa a tsakaninsu , lokaci zuwa kuma suma suna kawo mata ziyara har Abuja sannan tasa a mayar dasu gida, ynxu gabaki d’aya sun sauya suma kamar basu ba , iya rufin asiri yanxu Allah ya basu sai faman cikawa da Imani , gabaki day sun mata da Dije ko wata bintalo da dad’ewa sun kira sabuwar rayuwar da oumma ta zama sanadin farin cikinsu.Ganin yadda khaleed yake bawa oumma labarin ilham kullum Yasa oumma tanbayar dadi akan auransu , shima yayi na’am da barin alokacin har ya samu Abeey da zancan, ba ‘karamin farinciki Abeey yayi da hakan ba , amma duk da hakan be yanke hukunci ba saida yakira uncle musaddiq da har da kukan sa Sabida farinciki, babu dad’ewa aka saka auren 7 month , a yanxu gabaki d’aya biyan saura 3month, duk lokacin da sukai waya da ilham sai yace mata lokacin yayi tsawa zaije ya zamu Abeey yace a rage , da ‘Kyar ta lallashe sa akan saura ‘kan’kanin lokaci Amma dukda hakan baya hana gobe ya ‘kara ce mata lokaci baya sauri.

A ‘bangaran king tun bayar ‘batan Tahee gabaki d’aya ya ‘kara sauyawa kwata kwata baya zama a gida , saida yayi 3 years be je ko da Nigeria ba ,babu Wanda be kira ya lallashe saba Amma gabaki d’aya ya sharesu hatta small mom dake Dubai itama sai da takira sa amma babu abunda ya canza ganin ummey da dada na ‘kara shiga cikin damuwa yasa Abeey da kansa yaje U.S.A ya lallashesa akan ya dawo gida , still dukda ya dena fushin amma yace bazai iya zama babu matarsaba idan ba haka ba zai iya samun ciwan zuciya , sosai abeeey ya tausayawa son d’in nasa shiyasa be takura masa akan sai ya dawo ba , shima koda ya koma gida kwantar musu da hankali Abeey yayi , amma kusan kullum sai sun kira sa , dukda rashin magana da ya koya hakan baya hana in yana free ya kira ummey ko abeey, wani lokacin kuma ya kira dada da kullum sai tayi masa adduar Allah ya bayyana tahura .

AMMEEY
Cikin kwana bakwai d’in da abun bautar su ya bata ba ‘karamin shiga damuwa da rud’ani Ammey tayi ba , ganin har lokacin king be dawo ba , sosai ta shiga matsanan ciyar damuwa , da ‘kyar ta iya dannewa take kiran sa ko dan tace masa ya dawo amma itama amsarsa kamar ta sauran ce , “ he can’t, bazai iya rayuwa babu matar saba “, wannan kalla tasa ba ‘karamin sosa ran Ammeey yayi ba Amma cikin bariki itama ta nuna damuwarsa tare da baza goyan baya . Sosai ta saka ayi mata binciken a nemo mata tahee cikin SIRRI yadda zata kammala aikinta na ‘karshe amma duk magana d’aya ce ba a gantaba. Tun Ammeey na sa ran dawowar tahee har ta cire gabaki d’aya tare da shinfid’a sabuwar rayuwa acewarta abunbauta ya Mata ‘karya may be taheen ta dad’e da zama Matacciya shiyasa sosai ta saki ranta, kwarton ta da yake kulle fuska kuwa kusan kullum sai yayi sex da ita, ita kuma ko a jikinta ganin ta salwartar da mutanan da sukeso su zama cikas a rayuwarta, yanxu buri d’aya ne yayi saura ta cika, su kwashe gabaki d’aya dukiyar Abbey hatta ta king da ummey da suke hari sai kuma bayan Abeey da yafi komai tsaya mata arai da takeso ta kawar.

****************
UNITED KINGDOM 🇬🇧

A wata mata shiyar budurwace so classy sanye cikin doguwar rigar material, farace kyakkyawa , hannunta na d’auke da siririyar fashion pose red colour , kantamemiyar tsadar wayarta ma pod d’in ta ma red colour ,cikin taku irin na wayayyiyar budurwa meji da kanta ta soma sakko wa cikin heels dinta shima red , agogon hannunta take dubawa tun d’azu, tana sakkowa daga steps ta soma kwalla kiran sunan “ momy kuna ina lokacin na tafi , nasan sister tana can tana jiran mu”, wani kyakkyawar baturan yaro ne ya fita daga wata ‘kofa cikin gudu gudu, yake furta “ My love , junior is hear “, kallan inda yaran yake tayi, tubarkalla Masha Allah , wani kyakkyawan yaro ne , sosai yake da kyau fari tass kamar a ‘bula Jini ya fita , sanye take cikin Red suit na yara da ya ‘kara yi wa kyakkyawar fuskarsa kyau, gashin kansa kuwa wani irin gyara akayi masa ne shegen kyau da ya kwanto masa har wajan goshinsa, d’an mitsitsin bakinsa pink colour sai faman shining yake , da Sauri itama matashiyar budurwar ta ‘karasa Wajansa, lokaci d’aya sukai hugging d’in juna , duk da hills d’in dake kafarta Hakan be hanata juyasa ba sai faman dariya yake , dimples dinsa na both side na lotsawa, fararan jerarrun hakoransa tass dasu. “Mimi?” Da Sauri matar shiyar budurwa ta juya , sai yanxu na ganeta sabida wani irin kyau da tayi gabaki d’aya ta canza ta zama so classy, yaron naganin guy din daya kira mimi yayi saurin sauka daga Wajan Mimi ya ruga a guje zuwa wajan guy d’in , shima hugging d’insa yayi cikin turanci ya furta “ Big Dady”, sai yanxu fuskar mutumin ta fito, bakowa bane face Yah moh , shima sosai ya canza ya zama wani kyakkyawan guy , sanye yake cikin wasu ‘kananan kaya shima , sosai kayan sukayi masa kyau . Murmushi ya sakar wa boy d’in “ you look so wow sweetheart “, kashe masa ido d’aya yaran yayi kafun ya ja masa kumatunsa “ and also you my Big dady”,suna tsaye momy da dady da Hutu ya kara rutsa jikinsu fitowa , gabaki d’aya ko wannansu tashi kalar d’aukan wankan , a wannan karan ma kyakkyawan boy d’innan wajan su momy da dady ya nufa cikin hausarsa da bata fitowa sosai ya furta “grandparents kun dad’e tun dazu muna jiran ku”, jan hancinsa momy tayi “ toh ai gamu mun fito sai mutafi ko ?” Kanshi ya jinjina mata kafun ya kama both hannunta dana Dady suka fito baban harabar gidan , motoci biyu kawai suka d’auka d’aya yah moh da Mimi , d’ayar kuma dady ne da kanshi zaiyi driving din sai momy da junior a gefenta. A hankali cikin tafiyar nutsuwa a mota suka hau kan babban titin da zai kaisu **The inner temple ** lokacin da Suka je mutane sai fuffuto wa suke daka ciki zuwa harabar filin Inda kowa zai had’u da family d’insa , da yawa daga cikin mutanan sanye suke da suit a jikinsu sai wig and gown na lawyers da ko wanne ya saka, fara dudduba sukai suna jiran Suga ta Inda zata fito tun suna sa ranganinta har Mimi tayi *kokarin kiranta a waya “daga bayansu sukaji wata daddad’ar siririyar murya ta furta “‘momy”, gabaki d’aya su lokaci guda suka juya zuwa inda muryar ta fito , kyakkyawar matashiyar budurwace ta a jikin karshe fara sol da ita , tsabar farin ta har yellow yellow jikinta yake , sanye take cikin suit ita ba’ka sai wig and gown dinta da ta ri’ke a left hand dinsa , fashion swag bag dinta ma nakegen hannunta na hagu black colour , sosai hill din data saka yafito da kyawun ‘kafarta , idanuwanta sanye yake cikin farin glass da kemar medical, siririyar cute lips dinta ya ‘kara fito tas dashi, duk da suit ne a jikinta hakan be nuna sura ko wani Shati na baiwar da Allah ya bata ba, da Sauri junior ya saki hannunta su momy yaruga wajan matashiyar budurwannan da kudi da jin dadi suka gama zama a jikinta, yana zuwa wajanta yayi saurin hugging d’inta, “ My love ! I missed you “, kyakkyawan murmushi ta sakar masa da ya ‘kara mata kyau lokaci guda both dimples dinta suka lo’ba, “ missed you too” cewar matashiyar budurwar tana sakar masa peck a goshi, inda su momy suke ta nufa cikin ta kunya na d’aukan hankali , tana zuwa ta rungume momy kafun ta koma kan mimi itama ta rungumeta , cikin jin dadi mimi ta furta “ Congratulations sis tahee , you’re now a barrister “, wacce aka kira da tahee da kalla da mugun shock , tabbas Itace Amma gabaki d’aya ta canza ta zama wata babbar mace meji da aji ga baiwar karatun da Allah ya bata na zama babbar Barrister, itama momy congratulations dinta tayi kafun yah moh da dady kowa yayi congratulations dinta, cikin farin ciki suka fara d’aukar hoto gabaki d’ayan su , junior ya ta’ba tahee kadan , kallan sa tayi da dara daran idanuwanta da suka ‘kara haske da kyau , alama yayi mata data matso, d’an rankwafo tayi batayi auneba taji saukar kiss a goshinta , cikin harshen turanci ya furta “ I love you mom”.

💖💖GIDAN AUNTY 💖💖

07041879581
Mss Lee 💖

BOOK 2
Page 10

Da Sauri na ‘kara maida hankali na kan junior , daga nesa idan ka kallesa sak zaka ga tsantsan asalin balarabe, sai da ya matso da fuskarsa daidai inda tata yake kafun kamanninsa ya kara fitowa dukda kasan cewarsa yaro , amma sosai zaka hango tsantsan kamannin king, sosai suke kama , kamar tasu hartaso baci , banbancin shi junior har yanxu yaro ne , hatta yadda king yake kallan mutum haka shima junior yake , sosai suka d’auki pictures, sun d’anjima a Wajan kafun su kama hanyar komawa gidan bayan siyayyar da yah moh ya kaisu. Tahee na shigowa direct dakin ta tanufa sabida ba ‘karamin gajiya tayi ba , tana shiga wanka tayi kawai ta kwanta , amaimakon tayi bacci sai kawai ta fashe da kuka, Kukane take yinsa tundaga ‘kasan zuciyar ta , diamond ring d’inta da abun hannunta shima diamond da king ya bata take bi da kallo, lokaci d’aya kuma ta saki murmushin da dimples dinta suka lo’ba “ Ammi kin cucenii, kin rabani da farin cikina , why ? , me yasa “, ita kadai take tanbayar kanta,sosai take jin ‘kuna cikin ranta, yau ta kasance mata ranar farinciki da bakin ciki,sosai take sa’ke sa’ke cikin ranta , hannun da taji a kuma tunta ana share mata hawaye ta kalla , junior ne fuskarshi shi kamar zaiyi kuka “ Ammu me yasa kike kuka ?” Girgiza masa kai kawai taheee tayi wasu hawayen na ‘kara sakko mata , duk lokacin da ta kalli fuskar junior fuskar mijinta take gani, he’s eyes , mouth , cute face,he’s everything sak irin na king ne ,” Tohm ki dena kuka kinji “, ynxu ma kanta ta jinjina masa ta kasa magana , rungumeta yayi a jikinsa shima a hankali ya furta “ I love you!!!!!! Ammu”, a hankali ta furta “ Love you more and more my baby“. Kusan 3 minutes suna rungume da suna kafun da Sauri junior ya kalleta “ Ammu na manta, abinci fa zamuci grandpa yace na kira ki”, girgiza masa kai tayi “ Allah ya shiryeka son , bari na wanke fuskata sai mutafi”, tana kai karshen zancantawta wanke face d’inta tare da daukar junior kamar wani baby suka fito down stairs, gabaki d’aya kowa da kowa ya hallara tahee da junior kawai ake jira , kallan fuskarta Dady da momy sukai, duk da alamu ya nuna kuka tayi babu Wanda yayi magana , daman ta sabayin kukan , yau da kanta Mimi tayi serving d’insu abinci, tunda suka soma ci babu Wanda yayi magana sai junior da lokaci zuwa lokaci yake magana , suna kammalawa kowa ya bawa tahee gift ta zamowarta barrister , a nan d’in ma wani saban kuka ta fashe da shi, sun d’an jima a Wajan kafun dady ya mike , momy ta bi bayansa , yayi saura tahee da Mimi, daman yah moh shiya fara futa da junior.

*********
***************
**********
***************

FLASH BACK

Tun lokacin da tahee ta dawo Uk wajan Alhaji isma’il suka cigaba da kula da ita, tun tana kin sakewa dasu har ta fara sabida yadda ko wannan su yake janta a jiki, A bangaran momy ma sosai take bawa tahee kulawa kamar ‘yar da ta haifa da cikinta kome zatayi wa mimi shi zatayiwa tahee, sosai suke bata kulawa babu me nuna mata banbanci, kullum momy cikin dubata take kasan tuwarta kwararriyar Doctor . Shima yah moh kullum cikin siyo mata kayan kwad’ayi suke shi da dady. Gabaki d’aya family sai suke bata kulawa ta musamman. Lokacin da dady yakezo sa tahee a makaranta ta wayarta da baba Malam ya basa yayi anfani ya Fito da soft copy din makaranta dake cikin wayar, duk da yar hanzu be fad’a mata wayar na hannunsa ba . Koda sukaje school sabida kokarin ta yasa aka za tayi iya tafiya university, sosai tahee tayi farinciki da hakan, take a Wajan ta cike ‘bangaran law department, mimi ta cike nursing, haka rayuwa ta cigaba da tafiya cikin ahalin kullum tahee da tunanin a halinta take kwanciya take tashi , fatan ta Allah yasa suna cikin ‘koshin lapiya. A haka rayuwa tacigaba da tafiya da tahee tana samun kyakkyawar kulawa daga mutanan gidan , mimi ma sosai take janta a jikinta har soyayyar da suke wa juna tayi ‘karfi, lokacin da tahee ta fara labour gabaki d’aya family babu Wanda hankalinsa be tashi ba amma cikin iko na ubangiji ta sum’bulo d’anta kyakkyawan gaske fari tass dashi kamar ka ta’basa Jini ya zuba sabida kyansa, hatta Doctor d’in kowa ya gansa sai ya furta “ the baby is so beautiful” basu wani dad’e a asibitin ba aka basu sallama suka koma gida , gabaki d’aya familyn momy saida sukazo hatta wata sister d’in momy Itace tayiwa tahee wanka sabida yanda suke ‘kaunarta suma musamman da momy ta basu labarinta . Sosai dady da yah moh suka nuna bajintarsu ranar sunan kamar d’ansune ya haihu haka akayi tafi nagani na fad’a , baby da maman baby sosai suka tara gift sbd yaro yayi goshi sai san barka . Hatta friends d’inta na school wasu duk sunzo mata , ranar suna yaro yaci suna mohammad , Sabida shine sunan da kullum king yakece mata yanaso ya sa wa babynsu, sai suke masa la’kabi da junior .kullum momy da mimi ne suke kula da junior , har yaro yayi wayo sabida baiwar saurin fahimta da yake dashi, a haka tahee taci gaba da karatunta har zuwa ynxu da ta kammala karatunta amatsayin barrister.

✨✨✨✨✨✨

BACK TO STORY

Karfe 9:30 na dare dady yabu ‘kaci ganawa da kowa da kowa na cikin family d’in, gabaki d’aya taruwa sukai cikin babban falon dady, lokacin junior na jikin momy yana bacci , taro dady ya bud’e da addua bayan salatin annabi da sukayi, shiru dady yayi yana juya maganar da zaiyi , itama momy shiru kawai tayi batace komai ba , gyaran murya dady yayi kafun ya soma magana , “Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah , ina ‘kara gode wa Allah da ya bani ikon ganin ranar nan, ha’ki’ka nayi farincikin kammaluwar karatunku, ina ‘kara gode wa Allah, sannan ko wannan ku gift d’insa da na basa yana wajan momy a Wajan ta zaku karba , abi na biyu kuma maganata akankine tahee,” lokaci d’aya zuciyar tahee ta buga jin ya ambaci sunanta, amma bata ce komai ba sai ‘kasa da ta ‘karayi da kanta.Ba sai na maimaita abunda suka faru shekaru bayaba, amma yanxu lokaci yayi da za’a wuce wannan ga’bar, lokaci yayi da tabon mutanan da suke cikin‘kuncin ya goge, ko ba’a fad’a ba nasan kinsani junior ya fara wayo, yana bu’katar sanin mahaifinsa, yana bu’katar salin ahlinsa, ke matar aurece na tabbata Indai mijinki na raye to tabbas yana cikin kuncin rayuwa, mahaifiyarki tana cikin bakin cikin rayuwa haka ma d’an uwanki, lokaci yayi da zamu koma Nigeria gabaki d’ayan mu. Ba tahee data d’ago kanta ba hatta yah moh a mugun firgice ya kalli dady kansa na sara masa , cikin zuciyar sa ya maimaita “Nigeria ?”, kamar dady yasan me yake fad’a ya ‘kara maimaitawa “ eh Nigeria, Nan da 2 weeks duk Wanda yasan yana da abunyi yayi kafun nan da 2 weeks dan tafiya ba fashi “, idanuwan ya moh har sun fara yin ja, itama tahee da wani irin shock take maimaita Nigeria cikin zuciyarta. Wata waya ya ciro daga cikin aljihunsa tare da wani ‘karamin hoto da ya fad’i batare da sanin saba , wayar ya mi’kowa tahee “ Nasan bazaki manta da wannan wayar ba ko? Sabida tare da ita aka sameta cikin aljihunta”, ita tahee kuwa gabaki d’aya bata san me yake cewa ba , hankalinta yana kan hotan da ya fad’i a kasa , hakanan zuciyar ta take san ganin hotan, saida dady ya ‘kara kiran sunan ta kafun ta saka hannu zata kar’ba wayan ya su’buce mata a hannu sabida bud’ewar da hotan yayi ita kuma wayar ta gangara inda yah moh yake, da Sauri tahee ta d’auki hotan zuciyar ta na bugawa da sauri da sauri , gabaki d’aya sai suka maida hankalinsu kanta, kallan Alhaji isma’il tahee tayi kafun ta mayar da hankalinta kan hotan, shima a Daidai lokacin da yah moh ya d’auki wayar tahee da ta fad’i, cikin wani irin zabura tahee ta furta “Oumma?”, da sauri Alhaji isma’il ya mi’ke tsaye yana ‘ko’karin yin magana wayar tahee tayi haske, cikin wani irin shock yah moh ya mi’ke take a wajan ya soma ganin jiri jiri na d’ibarsa , babu abunda yake maimaitawa sai “ Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un”, nuna wayar tahee kawai yake yana ja da baya ga juwar da take ‘ko’karin kayar dashi , mimi har ta soma kuka babu abunda take fad’i sai yaya moh , meke damunka” . Ga baki d’aya sai abubuwan yaso d’aurewa dady kai musamman Wayar tahee da yah moh yake nunawa, kamar daka sama ya furta “ King” da ‘karfi, take a wajan kuma ya sulale ‘kasa . Da sauri dady da su momy suka nufa inda yake, tahee kuwa kasa ‘karasawa inda yake sai fuskarsa da ta tsurawa ido, kusan 2 minutes tana kallan fuskarsa kafin cikin shock ta mayar da kallanta kan junior dake bacci, sosai tashiga rud’ani kanta itama ya soma juyawa take a Wajan itama ta sulale. Tashin hankalin da ba’a sa masa date, sai suka rasa kan wa zasu tahee data suma ko yah Moh daya suma , babu abunda dady yake furtawa sai “ruwa ! Ruwa !” Da Sauri mimi ta nufi kitchen , cikin ‘kan’kanin lokaci ta dawo d’auke da bottle d’in ruwa guda biyu, momy ta karbi d’aya shima dady ya karbi, ruwan suka shafamusu gabaki d’aya suma sun rikice ganin abunda yake shirin faruwa . Tahee ce ta soma ajiyar zuciya har yanxu hotan data d’auka yana hannunta ta ru’keshi gagam. Yah moh kuwa har yanxu baya motsi abunda ya ‘kara tayar da hankalinsu, abunda ya bawa kowa mamaki, tahee tana farkawa inda yah moh yake a kwance ta zube tana fashewa da wani saban kuka , cikin murya kuka take furta “ Na ro’keka katashi, katashi dan Allah”, kasa magana dady yayi ganin irin kukan da tahee take ,sai abu yaso had’e masa ga momy data tayar da hankalinta ga mimi itama da take masa kuka, a ‘bangaran tahee ma gashi tana bashi tsoro ganin yadda take kuka akan Moh ya Tashi. Yana kara fesawa yah moh ruwa , ya fara motsi a hankali, bakinsa babu abunda ya ke am bata sai “Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un, Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un “. Temaka masa dady yayi ya zauna sosai , da sauri tahee ta d’auki wayar tata tana nunawa yah moh, cikin rawar murya take nuna masa wayar , da ‘kyar ta samu bakinta ya furta “ yaya king” sannan ta nunasa a hankali kamar tana tsoran magana ta furta “ Akhieee?” Shima
Fuskarsa gabaki d’aya tayi jawur bakinsa yayi nauyi ya kasa cewa komai sai d’an motsa mata kai da yayi alamar eh , murmushi da hawaye tahee ta fara lokaci d’aya sai momy da dady da kuma mimi suka zuba musu idanu gabaki d’aya sun kasa magana , maganar yah moh ne ya ‘kara rikitasu da ‘kyar ya kalli tahee kafun ya nuna junior dake kwance yana bacci, sai kuma ya nuna wayar hannunta “ junior !? Is my son”,murmushi tahee ta sakar masa tana d’aga masa kai , duk da haka sai da ya ‘kara furta “ junior is my brother’s son? ‘Dana ne ? ‘Dan king d’ina ? My dearest brother is now a father ?finally zan ‘kara ganin king d’ina ? Ummey? Abeey?Samreen? Dada?” Kai kawai tahee ta d’aga masa dan gabaki d’aya ta kasa magana , Sabida farincikin da ta shiga “ her lovely husband zai ‘kara samun farinciki? Wana irin farin ciki zai shiga idan ya ga brother d’insa , together with his wife and his baby?” Duka wad’an nan tanbayoyin kanta tahee take yiwa . Dakatar dasu momy tayi kafun ta furta “ kunsa mu cikin duhu, daman kun san junane?” Lokaci d’aya suka girgiza mata kai alamar a’ah . A sanyaye , dady ya furta “ kuyi mana bayani yadda zamu gane amma kafun nan inaso na tanbayeki tahee, naji kinkira matar cikin wannan photon da oumma ko kinsan me kama da ita ne?”. Sai yanxu hankalin tahee ya dawo kan hoton tana sakin murmushi, Oumma tace tare da brother d’inta da ya ‘bata “ da Sauri dady ya kalleta tare da nuna hotan “ oumman ki? “ yanxu ma kai tahee ta jinjina masa murmushi kwance a kan fuskarta. “ Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un” cewar dady, hotan hannunta ya nuna sannan ya nunata , a hankali ya furta “ ke.. ke yar maryam ce ?”, dukda tahee tayi mamakin yadda yasan sunan oummanta hakan be hana ta amsawa da “eh” wani irin farin cikine ya kama dady har ya kasa ‘boyuwa akan fuskarsa “ Alhamdulillah!!! Alhamdulillah!!” Kawai yake furtawa , kallan momy dady yayi itama da take murmushi “ ina tare da Jinina tsawan lokaci Amma ban sani ba ?” Da Sauri Mimi ta furta Dady wacce ?”, farin cikin da ya dad’e beyi bane kwance a fuskar dady , amsawa Mimi ba sai ‘kara kallan tahee da yayi sosai , tabbas tana kama da maryam d’insa , alama yayi mata data matso, ba musu kuwa ta matso d’in hotan hannunta ya kar’ba kafun ya nuna mata oummanta , “ Maryam ‘kan wa tace , nine nan a kusa da ita “, yanxu ma su mimi zubawa sarautar Allah ido sukai har yah moh kallansu yake lokaci zuwa lokaci yana sakin murmushi idan ya kalli junior . Nunasa tahee tayi kafin ta nuna hotan , a hankali ta furta “ uncle isma’il?”, murmushi ya sakar mata sosai yana jinjina mata kai , cikin farin ciki ya furta “ Allah ya ‘kaddara zan ‘kara ganin ahalin Maryam Alhamdulillah, yanxu dare yayi zamu tattauna gobe da safe “, badan sun soba duk suka mi’ke dan gabaki d’aya baccin ya gudu sabida farinciki, kallan tahee ya moh yayi , kafun ya kalli junior “ please ki barshi yau a waje na “, dariya yaso bata kamar yau ne suka soma kwana tare kanta kawai ta d’aga masa , itama fuskarta cike da murmushi ta furta “ bari na d’auko kayan baccin sa “, kafun ta ‘karasa ma Mimi har ta hau sama taje d’auko masa , d’aukan junior yah moh yayi , Daidai lokacin da Mimi ta dawo d’auke da kayan sa, mi’kawa yah moh da yake binta da d’an kallo kawai tayi, har yanxu kanta a tushe yake , ganin komai take kamar a mafarki , jira take kawai gobe tayi . Gabaki d’ayansu kowa goodnight yayi wa junansa kafun su nufa d’akunansu, yau Mimi d’akin tahee ta nufa , lokacin da suka kwanta Mimi sai kallan tahee take har hakan yasa ta tsargu , d’akawa Mimi duka tayi “ wannan kallanfa?” Murmushi Mimi tayi kafin ta sha gefan fuskar tahee , a mai makon ta amsawa tahee tanbayarta “ ban ta’ba ganin farin ciki sosia haka a fuskar dady ba , ya dad’e yana neman ku, da ya samu free time zaice zai tafi Nigeria , wani lokacin har kishi nake , sai na dunga tunanin ko dady yafi sansu akan mune ? Amma yanxu sosai nake farinciki, finally Nima naga familyn dady na “d’an harararta tahee tayi wato da mu kike kishi?” Murmushi kawai Mimi tayi mata , shiru tahee tayi kamar me tunani kafun ta furta “ Yah moh fa”, juya mata baya Mimi tayi tare da kashe light d’in dakin kafun ta furta “ good night, ni bacci nake ji”, dariya ce ta so su’buce wa tahee Amma tayi ‘ko’karin dannewa so take washe gari Kawai tayi, “ one side d’an uwan mijinta da kowa yayi tunanin ya mutu, the other side yayan mamanta.”, a hankali yadda Mimi bazata ji ba ta furta “ ya Allah ! Allah ka bayyana mun su , ko zan ‘kara ganin farincikinsu. Gabaki d’aya ahalin gidan sai kowa ya kasa rintsawa kowa da abunda yake sa’kawa aransa , yah moh tunda suka kwanta yake bin fuskar junior da kallo lokaci zuwa lokaci yana kissing forehead d’insa.

✨✨✨✨✨✨✨✨
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨

BUNKURE

💖💖GIDAN AUNTY 💖💖

07041879581
MSS LEE 💖

LEESHARH DATA HUB

BUY DATA AT AFFORDABLE PRICE:

MTN AIRTEL
500mb-120. 500mb-140
1gb-240. 1gb-300
2gb-440. 2gb-600
3gb-620. 3gb-900
5gb-1200. 4gb-1200
10gb-2200. 5gb- 1500

Validity : 30 days

ACCOUNT DETAILS :
2681892316
AISHA UMAR , ZENITH BANK .

For more information contact me through my phone number: 07041879581.

BOOK 2

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.