Mukaddari Ne Book 1 Complete Hausa Novel
Reading file: MUƘADDARI NE DAGA ALLAH.txt
Chapter 1 of 3
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
MUƘADDARI NE DAGA ALLAH
By
Suhaima Abubakar Shehu
(Sallamar D. A. W. A)
⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡⚡
DASHEN🌲ALLAH
WRITER'S📚ASSOCIATION
TEAM
_*ZAFAFAN🔥DASHEN🌲ALLAH*_
_*بسم الله الر حمن الر حيم*_
_* Yanayin Damuna ne yayiwa Garin rumfa, ga gajimare da har wannan lokacin ya hana rana fitowa. Sakamakon ruwan da aka kwana ana zubawa a daran jiya, hakan ne ya samar da iska mai daɗin shaƙa dake tafaman kaɗawa a tsakanin Bishiyoyin da suka yiwa Dajin ƙawanya, ko'ina kaduba furanni ne shar sun fiffito, wasu sunyi tsayi sosai yayin da wasu ƙananu ne sosai. Ko ina yayi lif-lif gwanin sha'awa da ƙawata kallon mazauna Garin.
Babu abun da kake iyan
juyowa a kaf dajin face kukan Tsutsayen daya ƙarawa yanayin matukar daɗi kasancewar a cikin Dajin babu motsi mai tada hankali, shiyasa dukkan mazauna wajen basa san rabo dashi, musamman ma wanda basa san hayaniya bazasu taɓa so su rabu da wajen ba.
"Sautin Sarewar da wani matashin Saurayi dake zaune akan wani falalin dutse wanda kallo ɗaya zaka masa zaka fahimci matuƙar nishaɗi da wannan busar take bashi, yakuwa haɗa ƙafa ɗaya kan ɗaya yana fuskanta kata faran Dajin da iyakar hangen ka babu abinda zaka iya hange wanda ba kyawawan furanni da bishiyoyi masu matuƙar kyaun kallo da kuma daɗin shaƙa dan ƙanshin su akwai kwantar da hankali, gashi sun ƙawata Dajin fiye da tunanin mai tunani.
Cikin wata yar ƙaramar Rigar saƙi yake data amshi fatar jikinsa sosai ruwan ƙasa ce wadda bata ciza ba sosai ga wani ɗan walki da tsawon sa bai wuce iyakar gwiwarsa ba.
Fari ne sosai duk da irin tarin dattin dake damfare a fatar jikin sa, hakan kuwa bai ɓoye zallar baiwar farin fatar da Allah yayi masa ba. Gashi ko kallo ɗaya kai masa zaka fahimci irin kyawu da kuma sheƙi da sulɓin da fatar take dashi.
Busa Sarewar sa yake har wannan lokacin yana wani rausayar da kai da alama ba kaɗan yake jin daɗin hakan ba.
Ɗif ya tsaya da busar saka makon a bunda idon sa ya hango masa da kuma ƙwa-ƙwalwarsa ke ƙoƙarin gazgata gaskiyar hakan wani sashen ƙwa-ƙwalwar tasa kuma yana kokawar ƙaryata masa mutum ya gani yashe a can ƙasa cikin wani mawuyacin hali domin duda ta zarar dake tsakaninsa da mutumin hakan bai hana ya iya fahimtar halin buƙatar taimakon da mutumin yake ciki ba, sanin cewa lafiya ba zata sa mutum yayi kwance a irin wanan dajin da hakukuwa suka cika ba ko dan tsoron abunda ka iya cutar da lafiyar sa ya saka yake kuma mamaki da kuma tabbatarwa da zuciyar wannan ba lafiya ba.
Dakatawa yayi da tunani da kuma lissafin da kansa ke masa ya kuma kallon Mutumin.
Bai sai lokacin daya furta “Mutum ne nake gani anan fa“ ya faɗa cikin yanayin tabbatarwa da kansa da kuma hasashen da zuciyar sa ke ƙoƙarin karyata masa.
Na dakika ɗaya bai tsaya kara sauraren halin da zuciyar sa ke masa ba ya riƙa kiciniyar saukowa daga dutsen dayake akai bayan ya maƙale sarewar tasa a jikin zaren da yake ɗaure a walkin sa,
Kamar wani ɗan ƙaramin matashin Biri ya riƙa sassarfa cikin ƙwarewa da sabo, yana kamo nan da can har ya dira ƙasa, nan fa ya zura a guje, ya nufi gurin dayaga mutumin nan a kwance.
Yanayin gudun da yake yi cikin matuƙar hanzari yasa bai ɗauki wani dagon lokaci ba saiga shi ya karaso gurin da mutumin yake a yashe kamar wanda rai yayi halin sa mamaki ne fal a zuciyar sa ganin abunda Idanuwan sa ke gane masa, matashi ne yake gani da shekarun sa ba zasu iya haurawa ashirin da uku ba, yanada duhun fatan amma ba za'a ce masa baki ba. Dogo ne amman kuma ba sosai ba sai kuma a yanayin ƙirar jikin sa da ba za'a iya kiranta ta masu ƙarfi ba, ga wata suma himili data karawa kan nasa girma, Da wani maɗaukakin mamaki yake kallon sa ganin suturar dake jikin matashin ko kusa ba irin tasu bace, tsaya yake akan dan matashin har wanan lokacin yana ƙare masa kallon ta'ajibi.
Cikin zuciyar sa kuma bayaga gargadi babu amon dake amsawa, ko ba'a faɗa masa ba yasan wannan mutumin ba irin su bane, domin idan aka cire yanayin halittar sa dake tabbatar masa cewa mutum kalan sa babu wani sauran kamanceceniya da zata karyata gaskiyar cewa ba daga wata duniyar ce yazo ba, ko kuma ma watakila Aljani ne.
Kallonsa ya cigaba dayi yana jin tausayinsa na yaƙar hanin da zuciyar sa ke sake jaddada masa game da taimakowa baƙon halittar da bai sani ba.
Jim yayi kafin nan kamar wanda aka tsikara ya fincikar da duk wani zancen zuci yakai hannayen sa kan matashin yana girgiza sa alamar ya tashi magana ya rika yi masa da yaren su amma ko gezau bai ji matashin yayi ba bare ya farfaɗo
Ganin bazai iya ba shi kaɗai, kuma ga numfashin da matashin yake yi sama-sama cikin matuƙar galabaita dake nuna har wannan lokacin yana raye ne ya bashi tabbacin za'a iya ceto rayuwar sa idan dai yakai sa gurin kakan sa daya kasance babban likitan dake duba mutunen garin nasu da sauri ko ya saɓesa kamar wani kayan wanki ya ɗorasa akafadar sa yabar gurin.
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
_*ASIBITIN MTH SPECIALIST*_
Cikin sassarfa Likitan yake takawa da irin saurin da ba za'a iya kiran sa gudu ba, a bayan sa wasu Nuses ne guda biyu Mata biye dashi har suna dan haɗawa da gudu dan ganin yana ƙoƙarin yi musu nisa, ɗayar Matashiyar Nurse ɗince riƙe da na'urar auna hawan jini sai kuma ɗayar dake rataye da yar na'urar sauraron bugun zuciya a hannayenta ko wani ɗan ƙaramin akwatin allura ne da take ɗauke dashi, dukkansu suna sanye ne cikin fararen kaya irin waƴanda malaman Asibiti suke sanyawa idan ka cire Likitan da sauit ce ajikin sa Amma yar cikin ce kawai da alama ya baro coat ɗin a Ofishin sa.
Wata babbar Mace ce daga ganin yanayin ta kaɗai zai iya fassara maka zallan tashin hankalin dake ɗawainiya da ita, sai faman baza babban Hijabinta kawai take tana gudu kamar wacce aka biyo, da alama dai ita tai kiran Likitan dan a gabansu take kamar itace zata nuna musu ɗakin da yakamata su shiga.
" Intensive care unit (ICU) shine dakin data nufa likitan da sauran nurses ɗin biyu suna take mata baya.
Cikin hanzari ta tura ƙofar ɗakin baki ɗaya bata cikin hayyacin ta, tana nunawa Likitan da sai bayan shigar ta da Ƴan daƙiƙu ne suka ƙara so cikin ɗakin, ko ba'a faɗa ba ganin gado ɗaya tal a katafaren ɗaki irin wannan ya isa bayyana gatan wacce take kwance akan sa.
Wata farar mace ce wadda a ƙiyasi bazata haura shekaru arba'in ba sakama kon rawar ganin da hutu ya taka a fagen shekarun ta, domin dai a zahirin gaskiya tana layin Ƴan shekaru hamsin ne, rashin lafiyar nan ce ma da tsananin tashin hankalin da ya yi wa ahalin su dirar mikiya da rana tsaka ne ya janyo bayyanar tsufan ta kaɗan, ga wanda ya ko ya tsere ta da kallon kurulla ma zai ga tafi hakan.
Yau kwanan ta biyu kenan tun a lokacin da mummunan labarin da ko a mafarki taga faruwar sa saita ƙaryata shi, wannan shine mummunan labarin dake jaddada ikon ubangiji akan bayin sa mummu nan labarin dake tabbatarwa da kowa cewa lallai kaddara makauniya ce, bata duba gurin da ya kamata ta sauka, ko'ina Allah ya ce ta kasance saita kasance dan shine kaɗai mai iko da kuma kum-fayakum akan dukkannin bayinsa.
★★★
Tun yanke jikin da tai a wancan lokacin ta faɗi duk da irin yunkurin da Abba yayi dan hanata kaiwa kasa amma ina saida ta kifo kanta ya daku da centre table din dake tsakiyar falon.
Ga baki ɗaya ahalin ne sukayo kanta dan bata taimakon gaggawa inda ganin irin halin da take ya shallake iyawar su ɓata lokaci Abba ya umarci Aliyu da ya tada moto su wuce Asibiti kawai.
Haka tun bayan zuwa Asibitin da Likitoci sukai kanta Abba, Umma, salim, Aliyu da sauran yaran gida da Umma ta kira ta sanar musu halin da momy take ciki, duk sukai cirko-cirko
Shima ta ɓangaren Abba sosai dangin sa suka zozzo wayar da ya yi dasu ne ɗazun bayan faruwar abun yake shaida musu.
Aiko kafin kace kwabo dangi sun kusan cika Asibiti kowa zazzau ne a kujerarun da aka tanada banda Abba da har wannan lokacin yake rike da hannaye abaya yanata kai kawo.
Ba'a rufa awa ɗaya ba Dr. Harun yafito daga ɗakin, ai kuwa kamar wanda yaci bashin su suka yi kansa da tambayoyi Abba kam har kafaɗar Dr. Harun ɗin ya riƙe yana jero masa tambayoyi.
"Likita tana raye? Wane hali take a yanzu? Zamu iya ganinta?"
Dr. Hurun da har wannan lokacin bai samu damar cewa komai ba sai faman kallon su yake da murmushin daya zamowa fuskar sa Al'ada, cikin kwantar da murya ya ce "Alh ku kwantar da hankalin ku yanzu bata cikin hatsari, sai-dai kuyi haƙuri bazaku iya ganin ta ba yanzu, tana buƙatar hutu"
Dr. Hurun ɗin ne yake faɗawa Abba hakan bayan ya gama sauraren tambayoyin da bazai yuyu ya amsa su duka ba.
Ajiyar zuciya Abba ya sauke tare da furta Alhamdulillahi yanayin Addu'a a cikin ransa.
Dr. Harun ne ya katse musu shurun da cewa
"Alh zanso nayi magana dakai a office"
"To to ai ba damuwa zamu iya tafiya ko" Abba ya faɗa cikin hanzari kafin Dr. Hurun ya wuce gaba Abban ya biyo sa a baya.
Tun bayan tattaunawar Abba da Dr. Haurun inda ya sanar masa ba'a buƙatar duk wayan nan mutanen da saboda irin halin da take ciki da kuma sauran Marasa Lafiya da suke a Asibitin. Dan saboda ba'asan hayaniyar su zata iya ƙara jefa mara lafiyar ne a damuwa.
Saboda haka Abba ya sallame kowa, daga bangaren dangin sa, da kuma ɓangaren su Baba Saminu, sai kuma akabar Umma dan ta kula da ita.
Yauma tun safe yazo duba momyn amma har wannan lokacin dai babu wani sauyi, bayan ƴar jimawa ne ya yi sallama da Umma ya wuce office bayan shaida mata zuwan su Hajia Zuwaira wacce take Ƙanwa ga momy'n
Fitar Abba da kamar awa ɗaya, Umma daketa faman kwashen flask da kofukan da tayi breakfast ne taji kamar motsi a bayanta ta waigo da sauri, itama Mommy cikin sauri ta farfaɗo har tana iya motsa ƴan yatsun ta aikuwa da saurin ta Umma ta ƙaraso gurin tana tambayar ta "Umman Sadauki kin farka, kina iya jina, yatsu nawa ne nan" ta kai hannuta gaban fuskar Momyn tana tambayar ta.
Ito ko Momy'n sai kallon ta kawai take da lumsassun Idanuwanta da suka ƙara bayyana rashin karfin jikin ta ganin Umma tafice da sauri dan kiran Doctor, yasata tabi ƙofar da kallo, aikuwa tana shiga officer ɗinsa tana cikin gaya masa ko rufe baki batai ba aiko ya tafi yana fitowa kamar labarin da yake zaman jira kenan, ita ce ma ta biyo bayansa dan ya rigata fita ma, suna fita Nurses biyu da suke tare alokacin suka rufa masa baya, dan dama yana musu bayani ne akan suje wajen ta.
Kusa da Mommy ya ƙara so da ɗan saurin sa yana nazartar ta kafin ya ce.
"Hajiya ya jikin naki? Ya kike ji a yanzu?"
Bata iya ce masa komai ba sai ido data bisa dashi.
"Hajiya kina iya jina?"
Awanan karon ma dai kallon sa take kafin ta ɗauke idon ta daga kansa ta maida kan Umma wacce ke magana da wani a waya
"Idan kina iya jina kiyi mun wata alama dan na sani, kamar ko idonki ma zaki iya yi mun alama dashi tayadda zamu san abun yi!"
Haka kuwa tayi domin dama can tana iya jin kome, magana ce kawai ta rasa meyasa ta kasa yi.
Idanuwanta ta lumshe sannan ta bude alamar eh ina jinka ƙaramar ajiyar zuciya ya sauke kafin nan ya karɓi ma'aunin gwada hawan jini ya soma daura mata dan auna hawan jini da dai-daiton bugun zuciyar ta.
Haka ya cigaba da yan aune aunen su na likitoci yana wani rubutu a file ɗin daya shigo dashi nata, sallmar da suka jiyo ce ta katse rubutun da yake ya dago domin amsa sallamar.
Abba ne ya shigo kamar wanda aka jefo, Umma ta kirasa take ta shida masa Mommy ta farka, nan take ya tabbatar mata yana kan hanya komai na office ya ajiye a gefe, yakira Habu sakatare ya shaida masa zai tafi wani uzuri bai tsaya jin amsawar Habu bama yayi ficewar sa ko minti shida bai cika ba kuwa sai gashi a MTH HOSPITAL, sakamokon gudun da ya rika yi kamar wani matashin dan tsere.
Kai tsaye Mommy'n yanufa baima lura da gaisuwar da Ummar keyi masa ba, Ummun Khalil yafaɗa yana kai hannusa ya riƙo nata da wani tausayi daya kewaye fuskar sa.
Jin ya ambaci khalil kuwa kamar ya dawo mata da kome sabo ne, Khalil dai ɗanta Namiji ɗaya tilo data mallaka a Duniya, Khalil dai wanda tafi so kaf sama da sauran Ƴaƴan ta, Khalil wannan dai Khalil ɗin da mutuwa ta karbe mata a sanda take cike da so da ƙaunar sa.
Hawaye kaɗai ne abunda tambayoyin Abban ke ƙara bankaɗo mata, ta kasa tsaida Idanuwan ta a fuskar Abban kamar yadda taga abunda yake nema kenan.
So yake ta kalle sa ta faɗa masa ta samu lafiya, sai faman rarraba ido kawai yake a fuskar ta da a yanzu ta soma. Canja launi izuwa ja abun ka da farar fata.
Kuka take son yi mai fitar da duk wata damuwa anan take, amma kamar wacce ana zarewa murya ta kasa fitar da sauti da ko na kusa da ita zai iyi jiyowa bare kuma na ciki dakin.
"Am Alhaji kayi haƙuri ka bata lokaci, bata iya magana har yanzu" Dr. Harun ne yatari numfashin Abba dayake ƙoƙarin ganin momyn ta amsa mishi.
"Bata iya magana kamar ya kenan me yake faruwa da ita ne? Abba ya tambaya cikin alamun ɗaure war kai"
"Abunda muke ƙoƙarin ganowa kenan Alhaji, yanzu dai ga wannan alluran"
Da sauri, ya faɗa yana miƙa masa fallen takardar daya kammala rubutun maganin a ciki, cikin rashin ƙwarin jiki Abban ya karɓa yana jujjuya ta a hunnun sa.
KAUYEN GUMO
Har wanan lokacin khalil baiko motsa ba barema asa ran zai farfaɗo tun bayan da Alili wannan saurayin daya tsinto sa daga cikin daji, sunan sa Aliyu ne amma kowa a garin Alili yake ce masa, sunan da a yanzu ya goge ainihin sunan sa a harsunan mutanen garin kenan.
"Kaka ina so ka taimaki wanan mutumin" Alili ne ya faɗa a sanda ya ƙarasa gidan Kakan nasa cikin tashin hankali, sai maida numfashi yake kamar wanda kuɓuto daga hannun mutuwa.
Kaka kuwa da har a lokacin ya sandare ne a tsaye yana musu kallon rashin fahimta, kalma ɗaya bata yi sa'ar fitowa daga bakin sa ba.
"Kaka zai mutu wlh idan baka taimaka masa ba, jifa irin halin da yake ciki na roƙeka Kaka" Ya ƙarashe maganar kamar zai saka kuka
Kaka kuwa da tsoron abunda kaje ne kadawo ya cika masa ciki sai a sannan ne ya iya ce wa "Ɗannan kana cikin hankalin ka kuwa ka tattalo sa kazo min dashi ashe har yanzu baka da hankali, wanan karon ya ƙarashe zancen ne cikin faɗa-faɗa
"Kenan kada na taimaka masa? Nabarsa acan ya mutu ko Kaka? Hakan kake so nayi iye? Shi kenan Kaka zan koma dashi, zan bar shi a can ya mutun tunda haka kake so. Amma ka sani yanda ba zai ƙara dawowa gida nan ba Kaka, to haka nima da idanuwanka ba zaka ƙara ganina ba" Yana gama faɗar hakan ya juya a fusace.
Ganin dai da gaske Alili zai tafi yasa Kaka yin sauri ya taro jikan sa da wayancewa ya ce "Haba dai Ɗannan, ba nufina ba kenan ina nufin kada mu taimaka masa a ƙarshe hakan ya zama matsala a gare mu."
Alili kuwa da riƙon rigar sa ta baya da k/Kaka ya yi, yasa ya dakata daga tafiyar da ya yi niyya, batare da ya juya ba yake amsa Kakan "Dama taimako na iya janyo wani abun daba Alkhairi ba a rayuwar mutum Kaka" Dariya yake ƙasa-ƙasa a wannan karon, sarai ya gama sanin lagon Kakan nasa, ko abu ya nema a bashi idan ya hana masa to sai ya yi masa barazanar barin gari, shi kuma Kaka ganin bayada kowa a duniya sai Ɗan jikansa a kullum baya shanye rada, duk sanda Alili ya yi barazanar barin Gida atake hankalin Kaka yake tashi ya yi masa abunda ya nema.
"To ka shigo dashi na duba sa ko?" kakan ya faɗa cikin sanyi murya aiko Alili saida ya ƙara turɓune fuska kafin ya juya a fusace yana bin bayan Kakan da ke ƙoƙarin shiga wani ƙaramin ɗaki
Babu ɓata lokaci ya shiga yi masa abubuwan da suka dace dan ceto rayuwar sa.
Abunda babu Alili yake turawa daji ya nemo, ya nemo masa saiwar bishiyu takai biyar, kwana d'aya kenan a ana abun d'aya kullum sai anyi masa turare da shafe jikin sa kaf da magungu nan gargajiya, dan kaka yasa Alili ya rasaba sa da wayan nan kayan na jikin sa an saka masa masu sauki nauyi yar yaloluwar riga ce ma sharara da Alili ke sawa idan yana son fita shan iska sai kuma wani son fita shan iska sai kuma wani karamin walki da suka d'ora masa a kugu,
Sosai kuwa ya fito sak kamar su kamar dama haifaffen garin ne sumar kansa kaka yasa Alili ya aske masa ita da askar da suke yiwa juna aski da ita
Sam idan ka kalli Khalil a yanzu ka had'a da hoton sa a kwana ki uku da suka wuce kafin karuwar wananan al'amari to tsaf zaka wuce ta gaban sa baka gano shine ba yanzu kam ba wannan Khalil din bane dan gayu mai ji da kansa dan kwali sa Khalil din dake gasawa mata aya hannu yanzu ya dawo Khalil dan daji
***
WAYE KHALIL
cikakken sunan sa Khalil Yahaya Chiroma inkiya KYC idan ka cire mahaifan sa kowa da KYC yake kiran sa shi ne babban dan agurin hajia Hafsatu Madaki wacce ake kira momy kuma d'anta guda d'aya tilo namiji tanada wasu yaran kannen Khalil din Khairat ita ke bi masa sai Khalisat Kulthum da Kausar wacce ta kasan ce autar su
Mahaifin sa Alh. Yahaya Ciroma yanada wasu yara da d'aya matar tasa Hajia Rahama Sunusi dake aka cewa umma kuma itace amaryar sa dan haka suka yaranta k'ananu ne sakamakon tsaikon haihuwa data samu dan da farko ma ganin sum shafe shekaru biyar da Alh. Yahaya bata haihu ba har an fara yada jita-jitar cewa juya Alhajin ya daukowa kansa amma da yake haihuwa ta Allah ce sai kuwa ga haihuwa ta rika zuwa mata a duk bayan shekaru biyu da Alhaji Yahaya uku mata sai biyu maza karima itace yarta ta farko wacce taci sunan mahaifiyar Alhaji mai suna Hauwa'u da suke kira Ammu sai Kasim Khalid da kuma Khariyyah sai autar su Khadija dukan su suna amsa KYC ne kamar yadda suka ji ana kiran yayan nasu wato Khalil shekarun Khalil a shirin da biyar zuwa da shida yana karatu a jami'ar bayaro dake kano duda ba itace farko jami'ar daya fara halarta ba zafin rai da zafin zuciya ne ke korar sa a duk inda aka kashi karatu
YALE UNIVERSITY dake kasar Amurka ce jami'a ta karshe ya je ko shekara bai rufe ba suka yi fada da wani dalibi yayi masa dukan tsiya
Bayan karbe lasisin karatun sa da makaranta tasa akayi sakamakon k'in bada hakuri abunda yayi har tsaresa akai wanda da Addu'o'i da matsalar suka bada belinsa daga nan ne kuma Abba yace gaskiya ya gaji
"in dai dai kudina yaro nan zai k'ara tafiya Turai karatu to wlh ya gama daga yau zai ari baki a sanda akayi nasarar sako Khalil din suka dawo Nigeria
Kowa ya taru a falo Abba inda ake jajantawa Khaliln din da mahaifan sa wannan abu daya faru
Momy dake zaune a matukar bacin ran irin halin Khalil na rashin hakuri cewa take "Khalil wlh naran tse da Allah ka kiyaye ni billahillazi zan iya sall....
Kafin ta karasa zance ne Alh. Amadu Chiroma wanda k'ani ne ga Abban yayi saurin katseta da subhanallahi haba Hafsatu yi ashe idan rai ya b'aci hankali ma tafiya yake shima cikin b'acin rai yake mata fad'a abunda take kokarin yi da alama bai ji dadin furucin ta ba " yau Khalil koda bake kika haifesa zaki so wani yayi masa baki? idan lalacewar Khalil tafi haka ai kuwa ba iya kuka zai saka ku ba Allah ya tsare ya kara ko wannan halin ma fata muke Allah ya yaye masa bare kuma wani abu yakaru a kan wannan din Addu'ar nan dai da ake masa za'a cigaba shiriya a hannun Allah take kuma shi kadai za'a iya fadawa ya kawo mana dauki dan idan na ya lalacen dai dole a kirasa da suna zuri'ar Chiroma"
wayannan kalamai na Amadu ba kad'a suka tasirantu a zuciyar momy ba har Abba dake jin kamar ya sallamwa duniya Khalil din ji yayi k'anin sa yafi bukata samada adu'a da farko niyyar Abba shine har anan gida Nigeria bazai biyawa Khalil din ya cigaba da karatun sa ba amma zuwan maganar gurin yayan su gabiki daya yasa ya saussauta daga fushin sa
Yanzu nufin ka Khalil bazai cigaba da karatun sa ba ko anan ma? Baba Abdullahi Chiroma yayan Abba ya tambaya lokacin da yaji hukuncin da Abba ya dauka game da karatun Khalil din yakira shi gidan sa yake tambayar dalili
Shin idan akwai wani wanda yafi kowa sanin muhimmancin ilimi da tagomashin dake cikin sa yakai ka ne? Ina ce ilimi ne ya kawo ka wannan matsayin dakake da kamfani naka kanka shin yanzu idan babu wani babba mai ilimi daga ciki yaran ka da zai rika kula maka da dukiyar ka kana ganin ko da ranka ba za'a cuceka ba bare kuma ka mutu"
Nan ya shiga yi masa nasiha da nusantar dashi irin hadarin dake tattare da fushin mahaifa dake tattare da fushin mahaifa akan y'ay'an su
Sosai nasihar yayan nasa ta karya logon duk wani kudirin sa bai baro gidan sa ba har saida yayi masa alkawarin in sha Allahu zai nemawa Khalil din admisson a BUK
Haka kuwa akayi abokin sa yakira dake karantarwa a jami'ar ya fada masa taimakon dayake nema.
Haba Alhaji ai matsayin ka a gurina ya wuce ka kira ni kana cewa na taimaka maka wlh ko wani yayi karya da sunan ka to sunan ka to sai nayi masa abunda ya nema bare kuma kai kaga ma anyi sa'a ba'a riga an rufe bada gurbin karatu ba in sha Allah har gida zan zo na kawo maka admission farm sai acika.
Sosai Abba yaji dadin wannan karamci irin na Dr. Sani Gusau ba'a rufe wata d'aya ba akayi kome da kome aka kare sakamakon Dr. Sani daya tsaya kan lamarin.
Rananr litinin ta kama ranar da Khalil din zai fara shiga aji tun a ranar lahadi da daddare bayan dawowar Abba yasa akira masa shi dan har wannan lokacin bai gama saukowa daga fushin Khalil din ba wanda da dane dakuwa kansa Abban yafi son Khalil din da son yin hira dashi fiyeda sauran yayan sa ba'a jima ba kuwa Khalil din ya shigo jiki a sanyaye bawai dan yaji fadan da aketa masa bitansa ba tun faruwar wancan al'amarin saida dan tunanin yanzu shi taya zai iya fuskantar bakin da abokan sa musamman ma samir yayi masa
" Khalil ko yaje kasar waje karatu sai ya dawo"
Me yale university kace Billyboy ya fada yana tintsirewa da wata dariya irinta ayi dai mugani samir ko dake duba list din abinci da waitress ta kawo masa dan yi musu order abunda zasu ci cewa yayi dude yale university jami'ar ce mai kyau amma naso ka zabi stanford uni baba Stanford duniya ce yanzu haka na tura musu duk wasu credentials nawa admission kowane lokaci zai iya fita
Khalil da izuwa wannan lokacin ya fara hawa sama da dariyar da Billyboy yake masa girgiza kai yayi alamar No No No ina son yale university ya fad'a adame kafin cikin matukar fusata ya saka kafa ya daki kujerar da Billy saiji yayi yadaki sauran teburan da aka ajiyewa wasu abinci suna ci anan take daga abincin har teburin da kuma kujera ya Billy yake kai suka zube kasa
Ai kuwa hankalin kowa ya dawo. Kan Billy dake kwance a kasa samir kuma wani kallo yake aikawa Khalil din na wannan wane irin banzan wasa ne
Khalil kuwa da har jikin sa wani b'ari yake tsabar fuahi baima ko san kallon da samir din yake masa idon sa akan Billyboy yana jiran ya gani ko zai iya ramawa
Wanan tazarcin da Khalil yayiwa Billy yayi matukar hassala shi musamman ma daya ga yan matan dake me zai wasu ma har dariya suke jefo masa kasa-kasa wannan sosai yayi tasiri gurinnk'ara tunzura Billyboy cikin sauri ya tashi ya nufo Khalil yana cewa kai dan ubanla ni zakaiwa raahin mutumci duda kokarin da samir yayi dan ganin ya dakatar da Billyn amma ina.
Har ya kai ga jikin Khalil din sun kacame da wani sabon fad'a da Khalil gangancin fad'a da khalil kwai yayi domin duda yafi Khalil din karfi amma yasan Khalil yafisa karfin zuciya hannuwa Billy ya murd'e dake kokarin riko wuyan sa yasaka d'aya kafar sa ya kwashe k'afafun Billy ai kuwa saiga Billy kasa tim kafin ma ya gama jin dumin kasa Khalil din ya d'agosa sama ya jefasa cikin wasu teburan cin abincim kamar wani kayan waki bai gama shanye wannan azabar yaji Khalil din sake damko sa ya k'arasa karya kafar teburan da suka kakkarye a guron da nufin banka masa a fuska.
Samir da wasu mutanen suka rirrikesa dak'yar suka iya suka k'waci Billyboy daga rikon da Khalil din yayi masa fuskan Billy kamar wanda yayi karo da bishiya tayi sumtul musamman gefen bakin sa
Wannan wane irin jahilci da dak'ik'anci ne Kyc? Samir ne yake zazzage masa tsantsar bacin ransa da takaicin da zuciyar sa keji game da abinda yayiwa abokin su wlh kyc da dai irin wannan bak'in halin naka bazaka tab'a abokai ba a rayuwar ka saidai ka kare a haka bara kaji kyc ko dabba ya fadi hakan ne yana nuna dan yatsan sa a fuskar Khalil din ko dabba bazata yi irin wannan dabbanci da kayi ba.
Jin wannan kalma ta dabban fa abokin sa ya kirasa dashi yasa cikin fushi ya kira sunan sa SAMIRRR cikin alamar ka kiyaye harshen ka.
Ko nima dukana zaka yi Khalil? cikin d'aga murya shima yake masa maganar fine ka dake ni Kyc wannan karon ya matso daf da Khalil Khalil din ko motsi baiyi ba yasa yayi taku. biyu bayan kafin yakai hannun sa gurin fuskar Khalil din yana k'yasta yatsun sa da cewa da irin wannan zafin zuciyar Khalil babu wata nasara da zaka iya cimmawa a rayuwa ka bi a hankali da zuciya domin kamar yadda ka rasa mu. ayau idon kawai zai kaika Amerika amma ba karatu saboda ba kada hakuri zama a aji yana gama fadar wannan ya juya a fusace yaji Billyboy suka fice daga restaurant din.
Khalil kuwa yafi rabin awa a tsaye a gurin yana maida ajiyar zuciya kafin ya zira hannun sa a aljihun sa ya cire wasu kudin da shi kansa bai san nawa bane yayiwa wata waitress da sukayi cirko-cirko a guri d'aya sauran ma'aikatan gurin suna Allah-Allah kada fushin zuciya ya dawo kansu
Da sauri waitress din daya kira ta k'araso jikinta na bari bai ce mata komai ba ya bata wayannan kudin......
Ku gyara b'arnar da akai muku fuuu ya wuce yabar waitress din nan rike da baki
Ashe yana da mutunci ta fada tana cigaba da kallon sa tafiyar sa har ya fice am burge ni ta k'ara fada wannan karon kam da karfi.
KO BAKAJI BANE maganar Abba ta dawo dashi daga duniyar data aura tunanin sa kamar wanda yayi mummu nan mafarki haka ya d'ago tareda samun kansa yana gyadawa Abba kai "ehh naji Abba in sha Allahu zanyi du abunda kace idan za'a dauki rayuwar sa ko ya fad'i kalma d'aya da Abba ya fada ba zai iya ba amma kuma harda wani bada amsar cewa ya fahimta da yake kuma anyi arashi shima Abban nasiha ce yayi masa akan yazamo mai hakuri da kuma kare martabar gidan su ko kadan bai fahimci cewa bada Khalil yayi magana ba hoton sa ne kawai nnan Abba ya sallamesa.
Nagode Abba saida safe ya fada yana tashi yafita
Abba kuwa binsa da kallo yayi cikin wani yanayin tausayi d'an nasa yana jin kaunar sa aran sa nan ya shige yi masa addu'o'i a bayyane
******
Washi gari ta kama monday kenan ya shirya cikin kananan kaya riga ce mai gajerun hannu launin ja mai d'abbara-d'abbaran bakin wanda jeans ne daya karawa shigar tasa armashi ya taje sumar nan tayi lif-lif kamar bak'in balarane agogon hannun sa ya saka sai takanlmi kirar gucci da ake yayi bayan ya gama feshe kansa da turarrika masu shegen kamshi designers farin glass dinsa kawai yamakala a idon sa jakar laptop dinsa ya rataya kafin ya dauko k'i sallar sa ya lafa aikuwa ya fito ma sha Allah
D'akin umma ya fara zuwa inda ya tadda su karima suna breakfast aikuwa da sauri daga Karima har Khalid Khariyya da Kasim suka shiga gaishe shi dan kada suyi wani laifi dan sosai suke tsoron sa ba dai Karima da ko zaka kwana kana rantse mata kan cewa Khalil baya shaye-shaye bata jin zata iya yarda
Mutumin da akullum neman haryar dazai ci zalin su yake indai yana gida ranar kamar anyi mutuwa kowa shan jinin jikin sa yake ba duka ba zagi amma sai mutum ya sha tsallen kwado kamar ba gobe k'arin abun mamakin ma wai harda su umma da momy kamar suma tsoron nasa suke ji babban abun haushi da takaicin ma irin yadda umma ke nuna tafi son sa fiyeda su.
Ya bude baki zai tambaye su ina umma sai jiyo muryar ta yayi daga bangaren kitchen ta fito rike da flask.
Sadauki haka take kiran sa ka fito kenan ehh umma ya fada fuskar sa ba yabo babu falla sa ya kara da cewa ina kwana umma lpfiya lau Ibrahim ta amsa cikin kulawa kafin ya d'ora da cewa Ibrahim ka zamo mai karbar abunda rayuwa tabaka koda kuwa ba shine zabin daka nema ba kayi hakuri kayiwa mahaifan ka biyayya kaji Ibrahim da wata kulawa ta musamman take masa nasiha kafin tace kayi sauri kaje kada ka makara
Nagode ua kawai ya fada ya nufi kofar fita aran sa yana jin dama ace umma ce ta haife sa dan tafi kowa tausayin da son sa
Ita ko umma da har lokacin take shimasa albarka har ya fice su Karima ta jiyo sun magana kasa-kasa amma da yale da turanci suke yi yasa ta daka musu harara kawai zaku yi sauri ku kammala cin abincin ku wuce makaranta ko sai kun gama gulmar da kuka saba
Gulmar umma kam sun saba dan duk sanda suka ga tana rawar kafa akan Khalil sai sun tattauna zafin da hakan yake musu da junan su amma cikin turanci dan sun san ummar bata ji ko yanzun ma Karima ce tacewa Kasim yanzu bara ka gani albarka zata saka masa aikuwa basu rufe baki ba kuwa umma ta fara zuba masa tuwan albarka yayin da zai fita Kasim ne ya dubi Karima wow kamar kin d'ora a bakin ta kuwa
Hmmm ai dama nasani mune fa kadai bata tokawa albarka ubangiji amma shi da yake dan gwal ne gashi bai nema ba ma ya samu
Jinjina kai kawai Kasim din yayi alamun lallai akwai gyara cikin ramarin umma kafin yayi ajiyar numfashi yace Allah ya kyauta dai-dai sanda umman ta jiyo su
Zaune yake akan kujera mai zaman mutum daya kan sa a kasa yayin da momy keyi masa nasihar sanin ciwon kai sosai ta masa jan kunne akan bin dokokin makaranta da kiyaye fushin zuciya da rike addu'a a duk sanda yaji bacin ran ya taso masa
Ka rika cewa A'uzubillahi mishshaidanirrajim wannan ingantacce maganin sukar fushi ne daga Annabi (saw)
Kwarai ko ya sani amma shi yana rasa abunda yake danne harshen sa daga ambaton Allah a zuciyar sa yana jin rashin kyautawar abubuwan dayake aikatawa amma ya rasa dalilin wanan zafin zuciya irin nasa da kuma k'ank'atar abun zai iya b'ata masa rai
Ganin lokacin yaja momy ta takaita zancen ta da Allah ya kareka daga shrrin mutum da aljanu kaje ka kada ka makara kaji to momy kawai ya fada cikin ladabi kafin ya fice izuwa harabar gidan motar sa kirar GLK da Abba yayi masa kyautar a shagalin bikin zagayowar haifuwar sa da yayi kafin zuwan sa Amerika ita yanufa dan yasa laminu mai kula da fulawoyin gidan ya wanke masa ita tas tun jiya
Key yayi mata ya danyi worming dinta kafin yayi horn mai gadi ya walle masa gate ya fice
" Karar fashewa yaji kuma da alama motor sa ce aka daka sakamakon girgizar daya ji tayi, d'okawar tayi dai-dai da lokacin daya kai hannun sa dan kashe sautin kid'a wacce tayi sanadin zamewar hannun nasa daga madannin daya kama ya danna wohoho kar ku so kuga yanda zuciyar sa tayi baki wani dokawar bacin rai take yi kamar wanda ake doka tanbarin yakin duniya ake doka tambarin yakin duniya na uku cikin ta nan take i danuwan sa suka kada sukayi jajir
Second d'aya bai kara shafewa a cikin motar ba ya fito fuuuu,
Dalibai masu wucewa kuwa tsaitsayawa suka yi suna labartawa wayanda basu ga faruwar abun ba kan kace kwabo an zagaye gurin anata maganganu kowa da abunda yake fadawa abokin sa nan dai aka shiga maida zance,
Shi ko Khalil ganin bumpar motar sa a kasa ga kuma singnals dinsa duk sun tarwatse ne yasa ya manta gurin da yake domin a zuciyar sa kawai hango kansa yake cikin wani masifaffen sansanin yak'i
Cikin daga murya ya dubi daliban da suka taru a gurin ! 𝙐𝘽𝘼𝙉 𝙒𝘼𝙔𝙀 𝙔𝘼 𝘿𝘼𝙆𝘼𝙍 𝙈𝙐𝙉 𝙈𝙊𝙏𝘼? yanda ya fada cikin masifa kai kace da wasu yara yan primary yake magana ba yan jami'a ba.
Babu wanda ya tanka masa saima darewa da akayi a gefe da gefe dan bashi damar ganin motar da tayi masa hakan
ai kuwa kamar an kara ninka bacin ransa ganin wanda yayi bar nar har wannan lokacin bai fito dan ganin abunda ya aikata ba wane shafaffe daman ne haka da zai nuna masa iko a garin kano,
"Ina karya ne wallahi babu wanda ya isa"
Da wanan shawarar da zuciyar sa ta d'ora sa a kaine ya karasa jikin motor inda baka iya ganin komai sakamakon tinted glass da aka zagaye ko ina dashi,
Fuskar nan kamar zata tarwatse irin yanda ya daureta yana mai dukan glass din motar da nufin a bude saboda baya jin akwai sauran saboda baya jin akwai sauran kalmomin da suka rage a bakin sa daga cikin motar kuwa tunda abun ya faru take rike da kunneyen ta cikin matukar tsoro ita kanta sautin bugawar motar ta tsorata ta sosai tasani ko iya wannan sautin kad'ai abun tashin hankali ne balle kuma illar da zata iya biye bayan sa,
Bawai tana jin tsoron fitowa bane daga motar saidai tsawon wannan lokacin tana tariyo yanda abun ne ya faru daki-daki kokarin take ta gano daga inda aka samu matsalar.
Kwarai tasan laifinta ne amma kuma ta yaya? tambayar da tasa komar da tunanin ta tun daga farkon fitowa daga gida bayan tayi wanka ta shirya tsaf fuskar ta tamkar farin wata a daren goma sha hudu
Daga shiga toilet har zuwa kammala shiryawa babu wani kuskure ta fada cikin ranta tana mai kara baza tunaninta a faifai dan samun wata marikar da zata iya alakan ta sanadin da wannan hatsarin
" Bayan na hattama shiryawa Ammi ta kwalo min kira dan yin breakfast na fita da sauri bayan na amsa ina mai nufar dining area inda Ammi da Abi Suhaima Hanan Iman da Imran suka kusan kammalawa na gaishe da su daban-daban sannan na janyo kujera na zauna zan iya tuna tambayar da Abi ya fara min daga zaunawa ta mai sunan mama ya kike jin yau din a matsayin ranar ki ta farko a jami'a?
Murmushi nayi har sai bayan dana hadiye abincin dayake bakin na cikin damuwa sosai nace Abi tsoro nake ji
Haba dai karamar zakanya ta nikam me zai iya tsoratar min dake nifa ba matsoraci bane bansani ba dai ko a gurin Amminki kika dauko tsoro ya fada cikin sigar tsokana
Ammi ko da taga alamar hira na kokarin kacemewa tsakanina da Abi wata maganar ta kawo dan ture wannan
Nace kinyi magana Dan ladi direba kuwa? Ammin ta tambaya
Haba Ammi ba mun riga da mun kai karshen wannan maganar ba ni gaskiya bana so Dan ladi yakai ni ni zan tuka motar zan fashe da kuka
Wanda yasa Abi ya karba zancen da cewa wane irin Dan ladi kuma?
To meye amfanin koyon motar da tayi kenan idan kullum. Dan ladi ne zai rika kai ta makaranta har zuwa yaushe zata jaraba koyan da tayi?
Dama ai kai kullum kana bayanta nifa tsorona kda taje ta bugawa wani motar sa kawai ina laifin suna. zuwa da Dan ladi kafin nan sai. ta rika tukawa da kanta
a'a ban yarda da Dan ladi ya rika kai mamana makaranta Abi ya fada yana mikewa daga gurin alamar ya gama
To ya fada cikin mamakin inda ya jefar da wayar sa sai lulubar jikin sa yake mamana kira min wayata naji da sauri kuwa na laluba number sa nakira
Wayar ce a hannun kujerar tsakiyar falo inda ya fara zaunawa kafin ya karaso gurin dinning din ban katse kiran ba har yaje gurin ya dauka ganin har wannan lokacin ban katse ba yadaga kiran yace ki fadawa maman ki kwalliya ta burge ni kit ya kashe
Babu bukatar sanar da ita domin already na saka a soeaker ne wani kallon zaka sani rayi masa yayin da daga mu har shi muka kwashe da dariyar ta
Ku kuma zaku yi ku kare ne kowa ya wuce makaranta ko kuma sai kun tsaya batawa masu kaiku makaranta lokaci
𝔻𝔸𝕂𝕐𝔸𝕌 ayanzu nagano inda matsalar ta faro Ammi ce silar wannan matsalar kina tsoron na bugawa wani mota kuma ga hakan ya faru ta fada a fili,
" Adai-dai wannan lokacin ne taga tsaya a kan gashin motar ta wanda ko ba'a fada mata ta san wanda tayiwa barna ne saidai hango yanayin masifar datake tattare dashi ya tsorata ta, tana cikin shwarar sauka gashin ko a'a taga ya kara dukan gilashin cikin matukar fusata, aiko ba shiri ta zuga lokaci guda zuwa kasa wanda yabawa Khalil din damar kai hannu dan falla ma ko uba waye wannan lafiyayyen mari kafin kuma ya fito dashi cikin motar yaci masa kaniya,
Cak hannun ya taya kamar wanda aka tsayar da remote, ya kasa karasawa a kyakkyawar fuskar da i danuwan sa sukai masa tozali dasu, wannan fuskar ko ba'a fadawa mutum iya kallonta kadai ya isa shaidar cewa iskar wucewar mari bai taba gigin wucewa ta gefen fuskarta ba,
Sauran daliban da suka yi dafifi dan jiyo sautin kukan wanda ke cikin motar nan ganin irin zafin da Khalil din ya kwaso, ai bazai yuyu bama wanda yayi wannan b'arnan ya sha, dole ayi wacce za'a yi ganin yanda dramar zata kai karshe ne yasa daliban tsayawa dan more kallo bawai dan ba'a fara lectures ba,
Jin shuru har yanzu ba'a alamun kwalla kara ba yasa wasu suka fara lekowa dan ganin abunda ke faruwa musamman wayanda ke daya dashen motar da basa iya hango komai da wani madaukakin mamaki suka kallon sa ya wani saki ido, hanci da baki ga kuma hannun da har wannan lokacin yake sakale a isaka, shi baiyi abunda ya kamata ba kuma ya wani yi tsaye a gurin kamar an dasa shi,
Nan fa kowa ya fara watsewa yana nufar aji, kowa da abunda da yake fada aikin banza kunga yanda ya wani zo kamar jikan iliya dan mai karfi kai kace wata tsiyar zai tsinana amma ji yanda ya kare a tsinkar fure sauran daliban baki daya suka kwashe da dariya,
"A cikin motar kuwa tun bayan data sauka gilashin taga tahowar hannu kan fuskar ta a tsorace ce ta kai hannayen ta ta dafe kumatun ta dan kare su daga saukar wannan azababben farmaki,
Seconds daya, biyu, uku, saida ta kirga seconds har goma ta hanyar amfani da bugawar da zuciyarta keyi cikin da mamaki ta bude i danuwan ta da har wannan lokacin suka a rufe dan tagama sadakarwa fa sai jikinta ya karbi bakon al'amarin da a tarihin rayuwar ta ba'a taba ba,
A hankali ta d'ago i danuwan ta dan ganin abunda ya tare fadowar wannan farmaki, daram kirjin ta ya buga matashi ne kyakkyawa a fuska kamar bazai yi masifa ba, kallon sa tayi sannan tayi kasa da idon ta, saboda kwarjinin da yayi mata, Khalil akwai kwarjini gashi ba daukan rai ni amma yau kamar ba Khalil nima bayi mamakin Khalil wanda mata basa gaban sa, amma bari nayi ahuru🙃
Cikin muryarta dake fita kamar yaro na gangar fashewa da kuka tace kayi hakuri dan Allah, 🙏
Sai a sannan ne yaji ya dawo hayyacin sa cikin second biyu kwakwalwar sa ta rika tariyo masa abun kunyar dayi,
Tofa masu karatu yau Khalil har yasan yayi abun kunya duniya kenan
Nan take haushin kansa ya kamashi, ko arzikin amasata bata ci ba da sauri yabar gurin motar yanufa tasa, bumper sa dake tashe a kasa ya dauka ya saka a boot din motar sa yarufe ya nufi department din su.
Yana mamakin kansa anya shine kuwa maiyake faruwa dashi ne haka,
*******************
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
MHT HOSPITAL
Tsawon mako guda kenan an kasa shawo kan matsalar maganar momy babu irin kokarin da Dr. Harun baiyi ba wanda takai har consultants aka rika kira suna zuwa na musamman domin matsalar momy amma har wannan lokacin abun saidai ma ace cigaba yake wucewar rana zuwa take da wani sabon salon sauyawar rashin lafiyar izuwa wani abun daban domin kan yau dai iya matsalar magana ce kawai take fama dashi, amma a yau cigaban lamarin yakai har ciwon sashe mata fara kamata ada tana iya komai da hannayen ta gurin yin nuni ko yin bayanin abunda take bukata amma a yanzu damar haka ma bata da,
Yanzu momy idan kaga irin halin azabar ciwon da take ciki saika tausaya mata,
Masu zuwa dubiya kuma wasu da hawaye suke barin d'akin Abba kan sa baya iya mallakar kan sa a duk lokacin daya zo dubata sai yayi mata hawaye dan haka ne ma yayi magana da Dr. Harun akan yayi musu duk wani shirye-shirye daya kamata na fitar da ita izuwa manya Asibitocin duniya,
Akwai wata asibiti a Mumbai ta kasa Indiya suna da k'warewa akan matsololi irin wannan ina ganin acan yakamata ku kaita, shawarar da Dr. Harun din yabawa Abba sosai kuma yayi na'am da shawarar domin dama ya yarda kwarewar India a fannin kiwon lafiya,
Yau ya rage saura kwana biyu su cika zuwa India yazo asibitin Umma ce sai su Khairat da Kausar wayanda tun safe da Bala direba ya kawo suke nan har yanzu da agogo ya buga biyar saura kwata suka kawowa su umma tunda momy bata iya cin komai sai duren sa a wani dogon tube ganin Abba ya shigo duka suka gaishe dashi cike da girmamawa shima cikin nuna kulawa da y'anyan sa ya amsa yana jin wani tausayin su na kara danne zuciyar sa musamman ma daya kara kai idon sa yaga halin da momyn su take ciki,
Kausar ne taje gaban gadon tarike hanun momyn ta momy har yanzu baki tashiba momy kinsan saidake nake iya barci akirjin ki yau momy kinki tashi kullum ina nan momy dan Allah kitashi kince komai nake so zakimun momy ina son jin muryan ki najima banji muryan kiba babu yaya Khalil kema baki nan
Kuka takeyi sosai gabaki daya d'akin hawaye ne afuskan su kuka suke sosai,
Khairat ce tazo tarike hannun kausar tana fadin haba autan momy kidai na kuka in momy taji bazata jidadi ba momy in sha Allahu zata samu lafiya oooo auti khairat kullum kice mun momy zata samu lpa amma har yanzu ko magana batayi,
Kuka take sosai gurin Abba ta nufa Abba kowa yaki tashe mun momy na Abba kai katashe ta nasan zata tashi intaji kana magana nasan momy tana jin maganan ka ko yau she kamata magana tanjin maganan ka kuma kullum tanace mana muji maganan ka
Hannayen Abba tarike tana rokon sa akan yatashe masa momyn ta,
Khalisat ma tazo gurin Abba katashe mana momyn mu muna bukatar ta ,
Khairat Khalisat Kulthum Kausar kuka suke sosai
Abba yadube su yace in sha Allahu momyn ku zata samu sauki kucigaba damata Addu'a gobe zamu tafi Indiya insha Allahu momyn ku da kafaffun ta zata dawo gida
Kulthum tace Abba ance duk wanda yabar kasan sa baya dawowa kasan sa darai mu kalm kar afitar mana da momyn mu abarmana ita zamuta mata Addu'a
Abba yace addu'anku take bukata kawai yanzu Bala yana ciran ku awaje kuje kuka Kausar tasa ita agun momyn ta zata zauna da lallashi Abba yabita ta tafi
Bayan tafiyan su Abba ya gadon da momyn ke kwance kamar mai bacci ya wuce kai tsaye ya riko hannunta da irin salon da Abban ne kadai keyi mata yasa ta bude idanuwan ta a hankali cikin nasa daya kafeta dasu ko k'iftawa ba yayi saida suka jima ahaka kowa da abunda yake sakawa aran sa kallon da Abban ke yi mata kallone na cikakken so da kauna wanda tausayin yake kara hura wutar ruruwar su a zuciyar sa.
🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
KAUYE GUMA
Yanayin garin yana matukar dadi wa mazauna garin babu wata hayaniya mai tada hankalin mazauna garin babu wata damuwa acikin zuciyar su farin ciki ne yake tahanikin acikin arayuwar su kowa kagani harkan gaban sayake cikin matukar farin ciki da annashuwa,
"Wata yarinya ce zaune agaban wata bishiya tayi tagumi farace sol bata da kiba sosai kyakyawace sosai ajin farko al-k'alamina bazai musultamuku yadda kyawun ta yake ba duk tayi wani iri gabaki daya babu kwanciyan hankali atattare da ita babu nutsuwa tafada duniyar tunani,
Magana takeyi cikin zuciyar ta shin dagaske ni ba y'ace kamar kowa ba tsinto ni akayi mai yasa inna jummai bata sona kamar su Hauwa da maryam mai yasa kullum nake zama abun musgunawa agun inna jummai bana jindadi agidan sai Baffah yana nan Baffah ne kawai yake sona sai kuma Maryam komai Baffah yayi masu Hauwa yana mun shin dagaske maganan da ake fada bani da kowa ni y'ar tsuntuwace wacce bata san kowa nataba mai yasa ako da yauahe inna sai ta duke ni mai yasa bana samun farin ciki agidan mu sai Baffah yana nan, tunuwa da maganan Baffah tayi alokacin da yashigo gida yasamu Inna jummai tana dukan ta,
Bintu kowa da kika gani akwai tasa kaddaran dan Allah yayi ki yar tsutuwa bashi sai zaki zargir kaddaran kiba ko kuma iyayan ki Bintu ina ji ajiki na iyayan ki suna son ki kuma nasan har yanzu basu fitar da ranganin kiba inkina raye Bintu ina son ki rayu cikin farin ciki, tabbas ina fatan wata rana kiga naki iyayen ki Bintu dukan abunda Jummai zatamiki kiyi hakuri wata rana sai labari in sha Allahu Allah ubangiji zaikawo miki miji nagari wanda zai kula da rayuwar ki,
Bintu ina son kisani aduk inda kike kisani Allah yana tare dake kuma Addu'a ta tana tare dake Bintu
Bintu ina son kisani kimai da al'amuran ki zuwa ga Allah kiyi dogoro na gaskiya gare shi kiyi aiki da bin shar'an sa sababi ki aminta dacewa lallai wanda yake gudanar da al'amura daga sama zuwa kasa masani da abin dayake iyakance dukkan al'amuran ta kowace fusaka ma'abocin cikin abin da yaso yana kewaye dake da ludufi irin na illimin sa da kyautatawa da dudanarwa wanda ba wanda zai iya cikin halitu ko wani haziki ya fahimce karki shgaltu da sha'anin ki kibe dan bautawa ubangijin ki kiyi yakinin cewa dukan wanda yadogara gareshi to fah ya isar masa kuma zai kasance amintattan ce daga hudura kuma yasamu cikekken nutsuwa da kwanciyan hankali kinji Bintu na
Bintu tabbas zakiyi farin ciki arayuwar ki Allah zai kawomi ki miji nagari wanda zai kula dake da rayuwar ki, ubangiji Allah yana sane dake zai kawo miki mafita arayuwar ki kuma in sha Allahu iyayen ki Allah zai hadaku da yarddan sa Allah yamiki Albarka diyar albarka, dukan abun da jummai zatamiki kikasance mai hakuri nasan kina hakuri kikara wata rana sai labari in sha Allahu
Bintu tace nagode Baffah kuma in sha Allahu zankasance mai hakuri aduk indanake ai nika kaine komai na Baffah bani da tamkar ka aduniya nan
Tunani take sosai
Alili tafe yake babu nutsuwa atare da shi a yanzu burin sa shi ne wannan bakon halitan yatashi yau kimanin wata guda kenan amma bai san yadda kan sa yake ba tafiya yake yana magana har yazo zai wuce sai yaci karo da Bintu zaune itama cikin duniyar tunanin da kowa yasan Bintu afagen tunani ako ina kaga Bintu indai batare da maryam ba to cikin tunani take,
Alili ya ambaci sunan ta Bintu Bintu Bintu kamar yana magana da dutse babu alaman taji sa har ta amsa masa tabbas Bintu abun atausaya mata ne duba da yadda rayuwar ta ke tafiya kowa yasan Bintu agarin tun tana yarinya aka tsunto ta akoda yaushe inna Jummai sai tayi mata gori harda duka badun Baffah ba da rayuwar Bintu yajima da tarwatsaiwa duk da rashin gatan da Bintu bata dashi amma Allah yamata farin jini ga sanyi hali uwa uba kyawun ta tabbas Bintu batayi kama da y'an garin ba duk da suma Allah yazuba musu kyau ubangiji Allah yamata ruwan kyau,
Alili yatabata yace Bintu tunanin mai kikeyi haka tun dazo ina magana amma shuru kamar ina magana da dutse
Babu komai ya Alili haba Bintu yazakice babu komai bayan nagan cikin tunani cewar Alili babu komai ya Alili kawai kaina ke mun ciwo bana jin dadi ne
Taya zakiji dadi bayan babu wata nutsuwa atare dake Bintu kaf gari nan kowa yasan babu farin ciki da kike samu a gidan ku Bintu rayuwar ki abun tausayi ne amma kisani kowa da kallan tasa jarabawa da Allah yake daurawa bawan sa arayuwa kici rai damuwa aran ki wata rana sai labari dama ubangiji Allah yana jaraftar bawan sa akan abubuwa da yawa dan ya gwanda imanin ka
Kiduba fa kigani yau wata guda kenan wannan mutumun dana tsunto sa bai san yadda kan sa yake ba Allah yana jarafta bawan sa aduk sanda yaso wani baya gani wani baya ji wani mahaukaci ne wani yana kwance bashi da lafiya to Bintu duk abunda yasame ki kimika lamuran ki zuwa ga mahalincin ki kiroki Allah yashiga cikin lamuran ki kefa kina da lafiyan ki kuma kina cikin haiyacin ki amma kinga shi wannan mutumin dana tsunto bai san yadda kan sa yake ba Bintu rayuwar nan abun tsoro ne amma Allah ne maganin komai arayuwa
Nasani ke mai hakuri ne Bintu tabbas in Allah yasa kinada rabon ganin iyayen ki zaki gan su
Nasiha sosai yamata yace taje gida anjima in sha Allahu zaizo
Maiyasa kowa yace nayi hakuri wata rana sai labari magana Bintu takeyi cikin zuciyar ta
Tabbas Alili tana girmama Alili a rayuwar ta dan bayan Baffah Alili yabata gudumawa sosai arayuwar ta kuma kullum cikin nasiha yake mata akoda yaushe in suka hadu da Alili har bata son su rabu saboda yana ibemata kewa
*Godiya sosai tamasa kuma tamasa alkawarin in sha Allahu zata cire damuwa aran ta kuma zata tayasa da Addu'a mutumin da Alili ya tsunto sa Allah yabashi lafiya
🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
KAUYEN GUMA
"Kauye ne babba wanda kowa harkan gaban sa yake kauye ne wanda kan su ahade yake
" BUSHAR wani matashi ne wanda kafgarin kowa tsoron sa yake babban mutum ne mai jiki sosai amma kyakyawa ne afuska Bushar matashi ne wanda matasan garin tsoran sa yake yagama adaban garin duk abunda yace shi akeyi Bushar atsarin sa baya magana biyu matashi magidanci duk suna tsoron sa saboda yana amfani da sihiri ajikin sa,
Bushar yana matu kar son Bintu, Bintu kyakyawace kuma yarinyace dan shekarun ta bazasu wuce shekara shataraba ko ashirin
Bintu yarinya ce mai farin jini amma babu wanda ya isa yace yana son ta saboda Bushar
Duk abunda inna Jummai takeyi mata bata yarda tayi agunda Bushar zaiji saboda akwai wani rana da yamata rashin mutumci akan tanunawa Bintu yatsa
Alili yakasance yana son Bintu amma tsoron Bushar yahana sa fada mata cewa yana son ta
*******
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
BABBAN BIRNIN TARAYA ABUJA
Anguwar Area one manya-manyan gidaje nagani wanda tsaru wansu bazasu musultuba ina cikin kallon tsarowan gidajen ne idanuwa na suka sauka akan wani kangararran gida wanda tsaruwan sa yasa saida naji kamar zan sume
Kallon gidan nake naka ajikin gidan anyi rubutu da manyan b'ak'i
Abun dana gani anrubuta shine "ZURIYAN MANGA
Zuriyan manga zuriya ce wanda akaf fadin duniya nan kowa yasan da zaman ta Allah yabasu kudi da sukan su ba su san adadin kudin su ba
Babban gida ne mai kyau sosai irin sosai dinan family house ne gida ne kana gani kasan mazauna gidan kudi tazauna agun kaf duniya tasan da zamanta ko wani kamfani akwai hanun jarin su aciki zuriyan manga zuriya ne na masu kudi da mulki masu fada aji hata kasashen waje kowa yasan da zuriyan manga masu kudi ne,
Babban gida ne ya tsaru tsaruwa sosai dinan part-part ne daban-daban agidan
Alhaji Abdulkadir shine kakan gidan Alhaji Abdulkadir babban dan kasuwa ne yana da kamfanuni masuyawa shima kasan sa baisan adadin kudin sa ba,
Alhaji Abdulkadir matan sa biyu ne umma safiyya itace uwar gida y'ay'an ta uku, musa shine babban d'anta kuma shine babba agun mahaifin su sai Abubakar sai autan su majindah
Sai amaryan Alhaji Abudulkadir zulaihat yaron ta daya sadarn
Yaran sunta so cikin girmama junan su inkagan su yadda suke da sadarn bazaka tabacewa ba uwan daya ba
Musa da Abubakar kasuwancin baban su suka dauka sukace su bazasuyi wani dagon karatu ba
Sadarn shukuma tun yana karami yake son yazamo likita dan haka baban sa da yayyun sa suka goya masa baya wajan cikan burin sa
Alh. Musa ya aura matar sa laila yaran ta biyu Abdulkadir sai ummisalm
Sai Abubakar ya aura matan sa Ramlatu yaran su biyu mansoor da sageer
Sadarn kam kasan india yatafi karatun sa yana cikin karatun sa Allah yadashi da sarah jami'an su daya amma ita akasan tane soyayya mai karfi tashiga sakanin su mai karfi har suka fara magan aure
Sadarn yasanarwa yayan sa musa kuma ya goya masa baya kowa yayi na'am da batun da sadarn yakawo musu saboda sadarn d'an laile ne basu sha wahala wajan basu auran sarah ba saboda kowa yasan da zaman zuriyan manga
Sarah macce wacce bata daukan rai ni batashiga tsafgan da banata ba magana ba bata cikayi ba shiyasa su hajia laila suke jin haushin ta akan wai komai za'ayi sai ace sai anji tabakin sarah
Shekaran sarah biyar da auran su Allah bai bata haifuwa ba nan fa su Laila suka fara magana ae juyace ita
Cikin ikon Allah sarah tasamu ciki murna wajan zuriyan manga ba'a magana kamar akanta akafara haifuwa b'akin ciki kamar yakashe hajia Laila
Sarah tahaifu lapiya haifu danta namiji mai kama da ita sak yaron yaci suna siddaharth
Yaro yaci sunan sa Siddahrth kyakyawa ne gashi miskili bai cika son magana ba inkaga Siddarth na magana yana tare da ummin sa ne ko daddyn sa
Yana da shekara biyar a duniya ummin sa tasake haifuwan twins duka maza kyawawa da su masha Allahu Siddarhth yana matukar son su
"Siddarhth ina matukar son aekin soja burin sa kenan yana gama secondery school din sa America karatu domin cikan burin sa
Siddaharth bai son hayaniya dan haka baya shiga cikin ta yana rayuwar sa cikin farin ciki duk da baya Nageria amma akoda yaushe suna tare da daddyn sa awaya haka kawai daddyn sa yana zuwa masa yana rayuwar sa cikin farin ciki da annashuwa daddyn sa ya sakar masa kudi yana abun da yake so
Raj abokin Siddahrth ne, Raj yakalla Siddahrth yace haba haba yanzu abun dakakeyi kana kyauta wa, dan kaga Allah yayi ka kyakyawa ana son ka amma kai ako dayaushe babu abunda ka iya sai wulakanta macce maiye riban hakan yanzu kullum zoey takirani tana kuka wai ka ki kula ta meyasa, again Siddahrth bai kula saba Raj ransa yabaci ai dole kashareni saboda ina fada maka gaskiya
Siddahrth ya dobe sa yace haba Raj nasha fadamaka bana son mace irin zoey sbd zoey bata da aji nifa natsana mace mai tallan kan ta kaima kasani ban son macce da zatace tana son namiji plx kadaina mun maganan zoey banaso
Raj bai sake ce masa komai ba yabar d'akin
"Twins din ummi Arjun da Aaraw kyawawa ne sosai kamanin su daya sak saidai halin su ya banban ta Aaraw shi yana da saukin hali kowa nasane bashi da shariya akoda yauahe murmushi ne kwance akan fuskan sa, amma Arjun komai nasa daban ne akwai uban miskilanci har yafi brothers din Siddahrth baya son magana baya murmushi saidai idan yana tare da y'an uwan sa ne,
Arjun ne sanye cikin k'anan kaya masha Allah yamasa kyau sosai yafito sik india parlo yafito yataran da ummin su wajan ta yanu fa sanda-sanda har ya iso bayan ta bata saniba har ya isa bata saniba rufe mata idanuwa yayi yayi shuru yana son yaji abun da ummin sa zata fada dan d'abi un sune shi da Aaraw idan sunyiwa ummin su haka to sai suyi shuru suna jiran tafada sunan daya daga cikin su
Shuru ummi tayi tana tunanin cikin zuciyar ta wani d'anlelan tane yamata haka daga cikin su, numfasawa tayi can kuma sai tace Arjun yada rufemun idanuwa na, Arjun murmushi yayi yadawo gaban ta yace ummi na fadamun meyasa kullum idan daya daga cikin mu yamiki haka kike gane mu bayan komai namu iri daya ne hata turaran mu komai meysa kike gane mu fad'amun sirrin yadad'a yana daga mata gira' murmushi tayi tace Arjun kenan nice fa mahaifiyar ku daga jiki na kuka fito taya bazan gane kayana ba,
Aaraw ne yafito cikin shiga irin na d'an uwan sa yana fadin afadamun mai ake kullawa babu ni, murmushi ummi tayi tace zo auta na kasan nafi jidakai akan kowa,
Tura baki Aaraw yayi yace haba ummi ai nikam karki sa Arjun yare nani bayan dukan mu rana daya mukazo duniya, murmushi ummi tayi tace kuma haka ne auta na sake wage baki yayi yace kuma kinsake fada Arjun kallon sa yake irin na kafara fusatani fa da shagwaban ka idan Aaraw yana shagwaba wa ummin sa kamar yaro dan shekara uku,
Kama hannu sa tayi tace zo shagwabebe na riko hannun Arjun tayi taman nasu akirjin ta ta fara musu magana da akoda yauahe inzasu fita sai ta musu addu'a tafara zuba musu tana tofa musu cikin kunwan su sai da tagama tafara musu nasiha cikin sanyi muryan ta Arjun tabbas kana da hakuri amma kana da zafin zuciya abun da baidace ace kaji haushin saba sai kaji gashi baka son murmushi acikin mutani hakika murmushi yana da sihiri duk lokacin da ka yiwa masoyin ka sai yaji dadi da farin ciki duk sa'ar da ka yiwa makiyi sai ka sanya shi nadama ga wanda baka san shi ba kuwa in kayi masa murmushi yanzu zai zama masoyin ka sa'anan kuma ga lada da za a samu a wurin Allah dan Allah Arjun ka yawai ta murmushi bakasan yadda rayuw zata kasance ba karka duba daulan dakake ciki abunda nake so dakai kasan yayya zuciyar ka aduk inda kake rayuwar nan babu tabbas acikin ta kowa gani da kalan tasa jarafta duk abun da yasamu mutum to 𝙈𝙐𝙆𝘼𝘿𝘿𝘼𝙍𝙄 𝙉𝙀 𝘿𝘼𝙂𝘼 𝘼𝙇𝙇𝘼𝙃 dan haka kazamo mai sanyaya zuciyar ka,
Kallon Aaraw tayi tace nidai nasan kai mai hakuri ne ako ina dan haka kacigaba da hakuri kaji auta na Allah yashiga cikin lamuran ku y'ay'ana wallahi ina kaunar ku Allah yabaku mata nagari wanda zasu kulamun daku ko bayan rai na
Sosai nasihan ummin su tashige su kama hannaye ta sukayi Arjun yafara magana cikin sanyi muryan sa maidadin saurara yace ummi na kisa banso araina mun hankali ne shiyasa akoda yauahe nake zama fuskana ahade zuciya ta zafi take mun idan aka rai na mun hankali shiyasa bana bada fuska ummi na kijigaba damun addu'an dakika saba sosai suka mata magana maidadi taji dadi sosai hartaji ina da haka kowa yakw da yaran sa ita kam tayi sa'a a rayuwar ta, ruko hannayen ta sukayi suka saka ta atsakiya suka fara tafiya Aara kwantar da kan sa yayi ajikin ummin sa yana zuba mata shagwaba Arjun ko kallon ida yake baiyi ba shifa wannan shagwaban tana bashi haushi sai kace mace har bakin moton su taraka su
𝘗𝘢𝘳𝘵 12
𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘺𝘢 𝘥𝘰𝘣𝘪 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘺𝘢 𝘬𝘢𝘮𝘢𝘵𝘢 𝘧𝘢 𝘮𝘶𝘫𝘦 𝘮𝘶𝘥𝘶𝘣𝘢 𝘶𝘯𝘤𝘭𝘦 𝘮𝘶𝘴𝘢 𝘮𝘶𝘯𝘫𝘪𝘮𝘢 𝘣𝘢 𝘮𝘶𝘫𝘦𝘣𝘢 𝘬𝘶𝘮𝘢 𝘬𝘢𝘴𝘢 𝘢𝘬𝘰𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘶𝘴𝘩𝘦 𝘴𝘢𝘪 𝘺𝘢 𝘵𝘢𝘮𝘣𝘢𝘺𝘢 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘮𝘶 𝘩𝘢𝘳 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘺𝘢𝘨𝘢𝘫𝘪 𝘥𝘢𝘺𝘪 𝘮𝘢𝘯𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘮𝘶𝘫𝘦 𝘩𝘢𝘣𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘻𝘶 𝘥𝘢𝘯 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘮𝘶𝘯 𝘬𝘺𝘢𝘶 𝘵𝘢 𝘬𝘦 𝘯𝘢𝘯 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘸𝘢𝘭𝘭𝘢𝘩𝘪 𝘥𝘶𝘬 𝘭𝘢𝘪𝘧𝘪𝘯 𝘬𝘢 𝘯𝘦 𝘺𝘢𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘬𝘢𝘳𝘢 𝘩𝘢𝘥𝘢 𝘧𝘶𝘴𝘬𝘢 𝘢𝘪 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘣𝘢𝘯𝘴𝘰𝘯 𝘻𝘶𝘸𝘢 𝘨𝘪𝘥𝘢𝘯 𝘥𝘢 𝘻𝘢'𝘢𝘯𝘢 𝘮𝘶𝘯 𝘬𝘢𝘭𝘭𝘰𝘯 𝘥𝘢 𝘣𝘢𝘪 𝘬𝘢𝘮𝘢𝘵𝘢 𝘣𝘢𝘯𝘦, 𝘬𝘰𝘥𝘢𝘪 𝘣𝘢𝘬𝘢 𝘴𝘰𝘯 𝘴𝘶𝘮𝘮𝘢𝘺𝘢 𝘵𝘢 𝘨𝘢𝘯𝘬𝘢 𝘣𝘢 𝘢𝘦 𝘸𝘢𝘭𝘭𝘢𝘩𝘪 𝘬𝘰 𝘺𝘢𝘺𝘢 𝘻𝘢𝘬𝘢𝘺𝘪 𝘚𝘶𝘮𝘮𝘢𝘺𝘢 𝘥𝘢𝘪 𝘺𝘢𝘳 𝘶𝘸𝘢𝘯 𝘬𝘢𝘤𝘦 𝘬𝘶𝘮𝘢 𝘬𝘢𝘯𝘸𝘢𝘳 𝘬𝘢𝘤𝘦 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘺𝘢𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘩𝘢𝘥𝘢 𝘳𝘢𝘪, 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘈𝘶𝘯𝘵𝘺 𝘚𝘢𝘳𝘢𝘩 𝘣𝘢𝘴𝘰𝘯 𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘮𝘶 𝘵𝘢𝘬𝘦𝘣𝘢 𝘮𝘢𝘪𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘴𝘢𝘪 𝘮𝘶𝘯𝘫𝘦 𝘨𝘪𝘥𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘮𝘶 𝘴𝘢 𝘮𝘢𝘪 𝘴𝘢 𝘢 𝘰𝘧𝘧𝘪𝘴 𝘥𝘪𝘯 𝘴𝘢 , 𝘢'𝘢 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘮𝘶𝘫𝘦 𝘩𝘢𝘳 𝘨𝘪𝘥𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘥𝘢𝘯 𝘩𝘢𝘬𝘢 𝘴𝘢𝘪 𝘬𝘢𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘮𝘢𝘯𝘢 𝘳𝘢𝘯𝘥𝘢 𝘻𝘢𝘮𝘶 𝘫𝘦, 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘨𝘢𝘴𝘬𝘪𝘺𝘢 𝘯𝘪 𝘬𝘢𝘮 𝘺𝘢𝘯𝘻𝘶 𝘣𝘢𝘯𝘪 𝘥𝘢 𝘵𝘪𝘮𝘦𝘴 𝘢𝘮𝘮𝘢 𝘬𝘢𝘣𝘢𝘳𝘪 𝘪𝘯 𝘯𝘢𝘴𝘢𝘮𝘶 𝘭𝘰𝘬𝘢𝘤𝘪 𝘴𝘢𝘪 𝘮𝘶𝘫𝘦 𝘺𝘢𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘤𝘪𝘨𝘢𝘣𝘢 𝘥𝘢 𝘥𝘢𝘯𝘯𝘢 𝘭𝘢𝘱𝘵𝘰𝘱 𝘥𝘪𝘯 𝘴𝘢, 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘱𝘭𝘦𝘢𝘴𝘦 𝘮𝘢𝘯𝘢 𝘣𝘳𝘰, 𝘰𝘩𝘩 𝘮𝘺 𝘎𝘰𝘥 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘺𝘢𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘬𝘸𝘢𝘯𝘢𝘯 𝘢𝘪𝘬𝘪 𝘺𝘢 𝘮𝘶𝘯 𝘺𝘢𝘸𝘢 𝘣𝘢𝘯𝘢 𝘴𝘢𝘮𝘶𝘯 𝘭𝘰𝘬𝘢𝘤𝘪𝘯 𝘬𝘢𝘪𝘯𝘢 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘺𝘢𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘮𝘶𝘯 𝘢𝘬𝘢𝘯 𝘴𝘢𝘪 𝘯𝘪𝘯𝘦 𝘻𝘢𝘯 𝘬𝘰𝘮𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘺𝘦 𝘢𝘦𝘬𝘪 𝘬𝘶𝘮𝘢 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘣𝘢𝘴𝘰𝘯 𝘻𝘶𝘸𝘢 𝘯𝘢𝘬𝘦 𝘣𝘢 𝘵𝘰𝘩 𝘢𝘬𝘢𝘪 𝘯𝘢𝘬𝘦 𝘢𝘪𝘬𝘪𝘯 𝘸𝘢𝘯𝘤𝘦𝘯 𝘬𝘢𝘳𝘰𝘮𝘢 𝘣𝘢𝘥𝘢𝘯 𝘮𝘢𝘩𝘦𝘦𝘳 𝘣𝘢 𝘥𝘢 𝘣𝘢𝘣𝘶 𝘢𝘣𝘶𝘯𝘥𝘢 𝘻𝘢𝘯 𝘪𝘺𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘺𝘦𝘯 𝘴𝘶𝘯𝘤𝘪𝘬𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘺𝘢𝘯𝘤𝘪 𝘯𝘦 𝘬𝘶𝘮𝘢 𝘴𝘶𝘯𝘤𝘪𝘬𝘢 𝘬𝘢𝘭𝘭𝘰𝘯 𝘮𝘶𝘵𝘢𝘯𝘪 𝘬𝘢𝘮𝘢𝘳 𝘴𝘶𝘯 𝘴𝘢𝘮𝘶 𝘵𝘷 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘣𝘢𝘥𝘢𝘯 𝘮𝘢𝘩𝘦𝘳𝘳 𝘣𝘢 𝘬𝘰 𝘥𝘢 𝘩𝘢𝘬𝘢 𝘻𝘢𝘯 𝘥𝘢𝘸𝘰 𝘣𝘢𝘣𝘶 𝘸𝘢𝘯𝘪 𝘢𝘣𝘶𝘯 𝘢𝘳𝘻𝘪𝘬𝘪 𝘥𝘢𝘯𝘢𝘺𝘪 𝘺𝘢𝘬𝘢𝘳𝘪𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘺𝘢𝘮𝘶𝘴𝘢 𝘧𝘶𝘴𝘬𝘢 𝘬𝘢𝘮𝘢𝘳 𝘸𝘢𝘯𝘥𝘢 𝘢𝘬𝘢 𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘥𝘰𝘭𝘦 , 𝘈𝘢𝘳𝘸𝘢 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘢𝘪 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘣𝘢 𝘸𝘢𝘯𝘤𝘦𝘯 𝘬𝘢𝘶𝘺𝘦𝘯 𝘻𝘢𝘬𝘶 𝘬𝘰𝘮𝘢 𝘣𝘢 𝘬𝘰 𝘦𝘩𝘩 𝘩𝘢𝘬𝘢 𝘺𝘢𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘢𝘮𝘮𝘢 𝘢𝘪 𝘣𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘣𝘢𝘯𝘦 𝘢𝘮𝘮𝘢 𝘬𝘢𝘪𝘮𝘢 𝘴𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘬𝘢𝘯𝘬𝘢 𝘯𝘦 𝘣𝘢𝘯𝘢 𝘴𝘰𝘯 𝘻𝘶𝘸𝘢 𝘬𝘰 𝘸𝘢𝘵𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘺𝘦 𝘬𝘢𝘸𝘢𝘪 𝘥𝘢𝘯 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘯𝘦 𝘸𝘢𝘭𝘭𝘢𝘩𝘪 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘢𝘳𝘢𝘺𝘶𝘸𝘢 𝘵𝘢 𝘣𝘢𝘣𝘶 𝘢𝘣𝘶𝘯𝘥𝘢 𝘯𝘢𝘵𝘴𝘢𝘯𝘢 𝘬𝘢𝘮𝘢𝘳 𝘻𝘶𝘸𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘺𝘦 𝘢𝘮𝘮𝘢 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘣𝘢𝘣𝘶 𝘸𝘢𝘯𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘬𝘦 𝘵𝘢𝘬𝘶𝘳𝘢𝘸𝘢 𝘥𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘬𝘢𝘮𝘢𝘳 𝘯𝘪 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸𝘢 𝘮𝘶𝘳𝘮𝘶𝘴𝘩𝘪 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘺𝘢𝘮𝘢 𝘴𝘶𝘯𝘢𝘯 𝘬𝘢𝘶𝘺𝘦𝘯 𝘥𝘢 𝘻𝘢𝘬𝘶𝘫𝘦 𝘺𝘢𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘥𝘢𝘨𝘢 𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘨𝘪𝘳𝘢, 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘢𝘬𝘸𝘢𝘪 𝘻𝘰𝘭𝘢𝘺𝘢 𝘢𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢𝘯 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸𝘢 𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘣𝘢𝘪 𝘴𝘢𝘬𝘦 𝘬𝘶𝘭𝘢 𝘴𝘢𝘣𝘢 𝘺𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘥𝘢 𝘧𝘶𝘴𝘬𝘢𝘯 𝘴𝘢, 𝘈𝘢𝘳𝘸𝘢 𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘺𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘥𝘢 𝘧𝘶𝘴𝘬𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘣𝘢𝘪 𝘴𝘢𝘬𝘦 𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘣𝘢 𝘴𝘢𝘣𝘰𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘬𝘰 𝘺𝘢𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘣𝘢𝘻𝘢𝘪 𝘬𝘶𝘭𝘢𝘴𝘢𝘣𝘢 𝘢𝘮𝘮𝘢 𝘢𝘳𝘢𝘯𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘤𝘦𝘸𝘢 𝘸𝘢𝘯𝘯𝘢𝘯 𝘬𝘢𝘳𝘰𝘯 𝘴𝘩𝘪𝘮𝘢 𝘥𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘻𝘢 𝘢𝘵𝘢𝘧𝘪 𝘬𝘢𝘶𝘺𝘢𝘯 𝘯𝘢𝘯,
𝘉𝘢𝘺𝘢𝘯 𝘶𝘮𝘮𝘪 𝘵𝘢𝘬𝘰𝘮𝘢 𝘱𝘢𝘳𝘭𝘰 𝘯𝘦 𝘥'𝘢𝘬𝘪𝘯 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘵𝘢𝘯𝘶𝘧𝘢 𝘴𝘢𝘮𝘶𝘯 𝘴𝘢 𝘵𝘢𝘺𝘪 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘻𝘢𝘶𝘯𝘦 𝘢𝘬𝘢𝘯 𝘨𝘢𝘥'𝘰𝘯 𝘴𝘢 𝘬𝘶𝘴𝘢 𝘥𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘵𝘢 𝘯𝘶𝘧𝘢 𝘵𝘢𝘻𝘢𝘶𝘯𝘢 𝘢𝘨𝘦𝘧𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘬𝘸𝘢𝘯𝘵𝘢𝘳 𝘥𝘢 𝘬𝘢𝘯𝘵𝘢 𝘵𝘢𝘺𝘪 𝘢𝘬𝘢𝘧𝘢𝘥'𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘵𝘢𝘧𝘢𝘳𝘢 𝘤𝘪𝘬𝘪𝘯 𝘴𝘢𝘯𝘺𝘪𝘯 𝘵𝘢 𝘣𝘢𝘳𝘬𝘢 𝘥𝘢 𝘴𝘢𝘱𝘪𝘺𝘢 𝘧𝘢𝘳𝘪𝘯 𝘤𝘪𝘬𝘪𝘯𝘢 𝘫𝘪𝘯𝘫𝘪𝘯𝘢 𝘢𝘨𝘢𝘳𝘦 𝘬𝘢 𝘮𝘪𝘫𝘪𝘯𝘢 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺𝘯 𝘚𝘪𝘥𝘥𝘢𝘳𝘩𝘵𝘩 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺𝘯 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺𝘯 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘩𝘪𝘬𝘪𝘬𝘢 𝘯𝘢 𝘥𝘢𝘥𝘦 𝘪𝘯𝘢 𝘳𝘰𝘬𝘰𝘯 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘳𝘶𝘸𝘢 𝘺𝘢 𝘣𝘢𝘯𝘪 𝘵𝘦𝘬𝘶 𝘯𝘢 𝘳𝘰𝘬𝘦𝘴𝘩𝘪 𝘧𝘶𝘳𝘦 𝘺𝘢𝘣𝘢𝘯𝘪 𝘭𝘢𝘮𝘣𝘶 𝘯𝘢 𝘳𝘰𝘬𝘦𝘴𝘩𝘪 𝘸𝘢𝘯𝘥𝘢 𝘻𝘢𝘯𝘺𝘪 𝘳𝘢𝘺𝘶𝘸𝘢 𝘥𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘴𝘢𝘪 𝘺𝘢𝘣𝘢𝘯𝘪 𝘬𝘢𝘪 𝘩𝘢𝘬𝘪𝘬𝘢 𝘬𝘢𝘪 𝘯𝘦 𝘯𝘢𝘸𝘢 𝘥𝘶𝘬 𝘳𝘪𝘯𝘵𝘴𝘪 𝘥𝘶𝘬 𝘸𝘶𝘺𝘢 𝘬𝘢𝘪 𝘯𝘢𝘬𝘦 𝘴𝘰 𝘥𝘢 𝘥𝘶𝘬𝘬𝘢𝘯 𝘴𝘰𝘺𝘢𝘺𝘺𝘢𝘳 𝘵𝘢𝘩 𝘮𝘪𝘫𝘪𝘯𝘢 𝘢𝘣𝘢𝘳 𝘢𝘭𝘣𝘢𝘩𝘢𝘳𝘪 𝘯𝘢, 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘺𝘢 𝘥𝘶𝘣𝘦𝘵𝘢 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘢𝘬𝘰𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘶𝘴𝘩𝘦 𝘴𝘩𝘪𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘯𝘢𝘬𝘦 𝘬𝘢𝘳𝘢 𝘴𝘰𝘯 𝘬𝘪 𝘥𝘢 𝘬𝘢𝘪𝘯𝘢𝘳 𝘬𝘪 𝘬𝘪𝘯𝘢 𝘧𝘢𝘳𝘢𝘯𝘵𝘢 𝘮𝘶𝘯 𝘳𝘢𝘪𝘯𝘢 𝘥𝘢 𝘬𝘢𝘭𝘭𝘢𝘮𝘢𝘯 𝘬𝘪 𝘥𝘢 𝘣𝘪𝘺𝘢𝘺𝘺𝘢𝘯 𝘬𝘪 𝘢𝘨𝘢𝘳𝘦 𝘯𝘪 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘺𝘢 𝘮𝘪𝘬𝘪 𝘢𝘭𝘣𝘢𝘳𝘬𝘢 𝘪𝘯𝘢 𝘴𝘰𝘯 𝘬𝘪 𝘪𝘳𝘪𝘯 𝘴𝘰𝘴𝘢𝘪 𝘥𝘪𝘯𝘢𝘯 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩𝘶 𝘺𝘢𝘤𝘪𝘬𝘢 𝘳𝘢𝘺𝘶𝘸𝘢𝘳 𝘮𝘶 𝘥𝘢 𝘧𝘢𝘳𝘪𝘯 𝘤𝘪𝘬𝘪 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘺𝘢𝘣𝘢𝘳 𝘮𝘶𝘯 𝘬𝘦 𝘮𝘢𝘵𝘢 𝘵𝘢 𝘪𝘯𝘢 𝘴𝘰𝘯 𝘬𝘪 𝘵𝘢𝘳𝘦 𝘥𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘯𝘢𝘳 𝘬𝘪 𝘣𝘢𝘣𝘺 𝘯𝘢
𝘗𝘢𝘳𝘵 13
𝘒𝘢𝘳𝘢 𝘬𝘸𝘢𝘯𝘵𝘢𝘳 𝘥𝘢 𝘬𝘢𝘯𝘵𝘢 𝘵𝘢𝘺𝘪 𝘢𝘬𝘪𝘳𝘫𝘪𝘯 𝘴𝘢 𝘵𝘢𝘤𝘦 𝘬𝘢𝘪 𝘬𝘢𝘮 𝘩𝘢𝘳 𝘺𝘢𝘯𝘻𝘶 𝘣𝘢𝘻𝘢𝘬𝘢 𝘥𝘢𝘪𝘯𝘢 𝘬𝘪𝘳𝘢𝘯𝘢 𝘥𝘢 𝘣𝘢𝘣𝘺 𝘣𝘢 𝘬𝘰 𝘬𝘢 𝘨𝘪𝘳𝘮𝘢 𝘧𝘢, 𝘮𝘶𝘳𝘮𝘶𝘴𝘩𝘪 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘺 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘢𝘸𝘢𝘫𝘢𝘯 𝘮𝘢𝘵𝘢𝘯𝘢 𝘯𝘪𝘬𝘢𝘮 𝘫𝘢𝘳𝘪𝘳𝘪 𝘯𝘦, 𝘶𝘮𝘮𝘪 𝘵𝘢 𝘥𝘶𝘣𝘦 𝘴𝘢 𝘵𝘢𝘤𝘦 𝘺𝘢𝘶𝘸𝘢 𝘬𝘶𝘯𝘺𝘪 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘥𝘢 𝘚𝘪𝘥𝘥𝘢𝘳𝘩𝘵𝘩 𝘬𝘶𝘸𝘢, 𝘦𝘩𝘩 𝘮𝘶𝘯𝘺𝘪 𝘢𝘦 𝘺𝘢 𝘬𝘢𝘸𝘰 𝘮𝘶𝘯 𝘬𝘢𝘳𝘢𝘯 𝘬𝘪 𝘸𝘢𝘪 𝘣𝘢𝘬𝘪 𝘤𝘪𝘬𝘢 𝘴𝘰𝘯 𝘬𝘶𝘭𝘢 𝘥𝘢𝘴𝘩𝘪𝘣𝘢, 𝘜𝘮𝘮𝘪 𝘵𝘢𝘤𝘦 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘴𝘢𝘳𝘬𝘪 𝘮𝘺 𝘴𝘰𝘯 𝘢𝘦 𝘬𝘶𝘸𝘢 𝘬𝘶𝘭𝘶𝘮 𝘴𝘢𝘪 𝘮𝘶𝘯𝘺𝘪 𝘸𝘢𝘺𝘢 𝘥𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘥𝘢𝘪 𝘺𝘢𝘥𝘢𝘸𝘰 𝘮𝘢𝘯𝘢 𝘥𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘤𝘪𝘬𝘪𝘯 𝘬𝘰𝘴𝘩𝘪𝘯 𝘭𝘢𝘱𝘪𝘺𝘢 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘨𝘢𝘮𝘢 𝘬𝘢𝘳𝘢𝘵𝘶𝘯 𝘴𝘢 𝘭𝘱𝘺,
𝘋𝘢𝘧 𝘮𝘢𝘯𝘨𝘢𝘳𝘪 𝘣𝘢 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘥𝘢 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘴𝘶𝘬𝘢 𝘥𝘢𝘸𝘰 𝘨𝘪𝘥𝘢 𝘬𝘰𝘸𝘢 𝘺𝘢 𝘸𝘶𝘤𝘦 𝘥'𝘢𝘬𝘪𝘯 𝘴𝘢 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘬𝘢𝘪 𝘵𝘢𝘴𝘢𝘺𝘦 𝘵𝘰𝘪𝘭𝘦𝘵 𝘺𝘢 𝘸𝘶𝘤𝘦 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘸𝘢𝘯𝘬𝘢 𝘩𝘢𝘥𝘦 𝘥𝘢 𝘢𝘭𝘰𝘭𝘢 𝘣𝘢𝘺𝘢𝘯 𝘺𝘢 𝘬𝘢𝘮𝘮𝘢𝘭𝘢 𝘺𝘢 𝘧𝘪𝘵𝘰 𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘣𝘢𝘪𝘨𝘢 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘣𝘢 𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘶𝘧𝘪 𝘣𝘦𝘥𝘳𝘰𝘰𝘮 𝘥𝘪𝘯 𝘴𝘢 𝘥𝘢 𝘴𝘢𝘭𝘭𝘢𝘮𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘴𝘩𝘪𝘨𝘢 𝘺𝘢𝘨𝘢 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘢𝘬𝘢𝘯 𝘣𝘦𝘥 𝘥𝘪𝘯 𝘴𝘢 𝘳𝘪𝘬𝘦 𝘥𝘢 𝘮𝘢𝘳𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘫𝘶𝘺𝘢𝘸𝘢 𝘢𝘦 𝘥𝘢 𝘴𝘢𝘶𝘳𝘪 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘺𝘢𝘯𝘶𝘧𝘪 𝘣𝘦𝘥 𝘥𝘪𝘯 𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘩𝘢𝘥𝘪𝘯 𝘥𝘢 𝘥𝘢𝘯 𝘶𝘸𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘬𝘦 𝘤𝘪𝘬𝘪 𝘯𝘦 𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘬𝘢𝘳𝘪𝘴𝘢𝘸𝘢 𝘥𝘢 𝘴𝘢𝘶𝘳𝘪 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘤𝘪𝘸𝘰𝘯 𝘬𝘢 𝘺𝘢𝘵𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘥𝘢 𝘴𝘢𝘶𝘳𝘪 𝘺𝘢 𝘥𝘢𝘶𝘬𝘰 𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘣𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘺𝘢𝘴𝘩𝘢 𝘣𝘢𝘺𝘢𝘯 𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘺𝘢 𝘨𝘺𝘳𝘢𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘬𝘸𝘢𝘯𝘤𝘪 𝘺𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘴𝘩𝘪 𝘬𝘶𝘮𝘢 𝘺𝘢𝘵𝘢𝘧𝘪 𝘮𝘢𝘴𝘢𝘭𝘢𝘤𝘪 𝘥𝘢 𝘵𝘶𝘯𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘥𝘢𝘯 𝘶𝘸𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘣𝘢𝘺𝘢𝘯 𝘢𝘯 𝘪𝘥𝘢𝘳 𝘥𝘢 𝘴𝘢𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘬𝘰 𝘈𝘥𝘥𝘶'𝘢 𝘣𝘢𝘪 𝘵𝘴𝘢𝘺𝘢 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘣𝘢 𝘺𝘢 𝘯𝘶𝘧𝘪 𝘨𝘪𝘥𝘢 𝘬𝘢𝘪 𝘵𝘴𝘢𝘺𝘦 𝘣𝘦𝘥𝘳𝘰𝘰𝘮 𝘥𝘪𝘯 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘺𝘢 𝘯𝘶𝘧𝘢 𝘴𝘢𝘮𝘶𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘢𝘨𝘦𝘧𝘦𝘯 𝘨𝘢𝘥𝘰𝘯 𝘴𝘢 𝘥𝘢 𝘢𝘭𝘢𝘮𝘢 𝘫𝘪𝘬𝘪𝘯 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘴𝘢𝘶𝘬𝘪 𝘥𝘢 𝘴𝘢𝘶𝘳𝘪 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘺𝘢 𝘯𝘶𝘧𝘦 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘧𝘢𝘳𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘺𝘢𝘫𝘪𝘬𝘪𝘯 𝘬𝘢 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘯𝘢𝘴𝘩𝘢 𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘮𝘢𝘬𝘢 𝘬𝘢𝘺𝘪 𝘢𝘶𝘳𝘦 𝘴𝘩𝘪𝘯𝘦 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘥𝘢 𝘮𝘢𝘵𝘴𝘢𝘭𝘢𝘯 𝘬𝘢 𝘬𝘢𝘪𝘮𝘢 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘩𝘢𝘬𝘢, 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘣𝘢𝘪 𝘬𝘶𝘭𝘢 𝘴𝘢𝘣𝘢 𝘺𝘢 𝘸𝘶𝘤𝘦 𝘵𝘰𝘪𝘭𝘦𝘵 𝘸𝘢𝘯𝘬𝘢 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘺𝘢 𝘥𝘢𝘶𝘳𝘢 𝘢𝘭𝘰𝘭𝘢 𝘺𝘢𝘧𝘪𝘵𝘰 𝘺𝘢𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘩𝘢𝘳 𝘺𝘢𝘯𝘻𝘶 𝘣𝘢𝘪 𝘧𝘪𝘵𝘢 𝘣𝘢 𝘺𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘥𝘢 𝘧𝘶𝘴𝘬𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘻𝘶 𝘴𝘢𝘪 𝘺𝘢𝘬𝘢𝘳𝘢 𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘢𝘬𝘢𝘯 𝘢𝘶𝘳𝘦 𝘢𝘦 𝘬𝘶𝘸𝘢 𝘬𝘢𝘳𝘢 𝘮𝘢𝘴𝘰 𝘬𝘶𝘴𝘢 𝘥𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘩𝘢𝘣𝘢 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘥𝘢𝘯 𝘬𝘢𝘨𝘢 𝘯𝘢𝘥𝘢 𝘮𝘶 𝘥𝘢𝘬𝘢𝘪 𝘪𝘯𝘢 𝘮𝘢𝘬𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘴𝘢𝘪 𝘬𝘢𝘮𝘶𝘯 𝘴𝘩𝘶𝘳𝘶 𝘢𝘦 𝘻𝘢𝘬𝘢 𝘴𝘢𝘬𝘦 𝘤𝘪𝘸𝘰 𝘯𝘦 𝘻𝘢𝘬𝘢𝘨𝘢 𝘸𝘢𝘯𝘥𝘢 𝘻𝘢𝘪 𝘣𝘢𝘬𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘪 𝘺𝘢𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘩𝘢𝘥𝘢 𝘳𝘢𝘪 𝘢𝘭𝘢𝘮𝘢 𝘳𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘣𝘢𝘤𝘪 𝘴𝘰𝘴𝘢𝘪 𝘴𝘵𝘪𝘭𝘭 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘣𝘢𝘪 𝘬𝘶𝘭𝘢 𝘴𝘢𝘣𝘢 𝘴𝘢𝘪 𝘮𝘶𝘳𝘮𝘶𝘴𝘩𝘪 𝘥𝘢 𝘺𝘢𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘢𝘪 𝘬𝘶𝘸𝘢 𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘩𝘢𝘬𝘢 𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘧𝘪𝘥𝘢 𝘢𝘥'𝘢𝘬𝘪𝘯, 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘣𝘢𝘪 𝘬𝘶𝘭𝘢 𝘴𝘢𝘣𝘢 𝘺𝘢 𝘴𝘩𝘪𝘮𝘧𝘪𝘥𝘢 𝘥𝘢𝘥𝘥𝘶𝘮𝘢 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘴𝘢𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘣𝘢𝘺𝘢𝘯 𝘺𝘢 𝘪𝘥𝘢𝘳 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘢𝘥𝘶'𝘰𝘪𝘯 𝘴𝘢 𝘱𝘢𝘳𝘭𝘰 𝘺𝘢 𝘯𝘶𝘧𝘢 𝘬𝘢𝘪 𝘵𝘴𝘢𝘺𝘦 𝘥'𝘢𝘬𝘪𝘯 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘺𝘢 𝘯𝘶𝘧𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘴𝘩𝘪𝘨𝘢 𝘢𝘪 𝘬𝘶𝘸𝘢 𝘴𝘶𝘯𝘢 𝘬𝘢𝘭𝘭𝘰𝘯 𝘫𝘶𝘯𝘢 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘺𝘢 𝘩𝘢𝘥𝘢 𝘳𝘢𝘪 𝘺𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘥𝘢 𝘧𝘶𝘴𝘬𝘢 𝘢𝘥𝘰𝘭𝘦 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘧𝘶𝘴𝘩𝘪, 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘧𝘢𝘩𝘪𝘮𝘵𝘢𝘳 𝘩𝘢𝘬𝘢 𝘯𝘦 𝘺𝘢𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘻𝘰 𝘸𝘢𝘫𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢 𝘵𝘴𝘢𝘺𝘢, 𝘴𝘩𝘪𝘬𝘶𝘮𝘢 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘬𝘢𝘳𝘢 𝘬𝘢𝘶𝘥𝘢 𝘧𝘶𝘴𝘬𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘺𝘪, 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘬𝘢𝘳𝘢 𝘮𝘢𝘵𝘴𝘰 𝘬𝘶𝘴𝘢 𝘥𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘺𝘢 𝘵𝘴𝘶𝘨𝘶𝘯𝘢𝘯 𝘺𝘢𝘬𝘢𝘮𝘢 𝘬𝘶𝘯𝘯𝘶𝘸𝘢𝘯 𝘴𝘢 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘯𝘢𝘵𝘶𝘧𝘢 𝘢𝘮𝘶𝘯 𝘢𝘧𝘶𝘸𝘢 𝘣𝘢𝘻𝘢𝘯 𝘬𝘢𝘳𝘢𝘣𝘢, 𝘮𝘶𝘳𝘮𝘶𝘴𝘩𝘪 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘢𝘪 𝘬𝘢𝘪 𝘯𝘦 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘮𝘢𝘵𝘴𝘢𝘭𝘢𝘯 𝘬𝘢 𝘢𝘮𝘮𝘢 𝘬𝘢 𝘬𝘢𝘤𝘦 𝘬𝘢𝘪 𝘣𝘢𝘻𝘢𝘬𝘢 𝘺𝘪 𝘢𝘶𝘳𝘦 𝘣𝘢 𝘣𝘢𝘺𝘢𝘯 𝘢𝘶𝘳𝘦 𝘯𝘦 𝘬𝘢𝘸𝘢𝘪 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘮𝘢𝘵𝘴𝘢𝘭𝘢𝘯 𝘬𝘢, 𝘣𝘢𝘸𝘢𝘪 𝘣𝘢𝘯 𝘴𝘰𝘯 𝘢𝘶𝘳𝘦 𝘣𝘢𝘯𝘦 𝘩𝘢𝘳 𝘺𝘢𝘯𝘻𝘶 𝘣𝘢𝘯𝘨𝘢 𝘸𝘢𝘯𝘥𝘢 𝘯𝘢𝘬𝘦 𝘥𝘢 𝘣𝘶𝘳𝘪𝘯 𝘢𝘶𝘳𝘢 𝘣𝘢 𝘯𝘦 𝘬𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘯𝘢𝘴𝘩𝘢 𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘮𝘢𝘬𝘢 𝘪𝘯𝘢 𝘺𝘢𝘸𝘢𝘯 𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘵𝘢 𝘢𝘮𝘢𝘧𝘢𝘳 𝘬𝘪 𝘯𝘢, 𝘈𝘢𝘳𝘢𝘸 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘦𝘩𝘩 𝘩𝘢𝘬𝘢 𝘯𝘦 𝘢𝘮𝘮𝘢 𝘬𝘶𝘮𝘢 𝘵𝘰 𝘢𝘪 𝘯𝘢 𝘮𝘪𝘫𝘪 𝘮𝘪𝘫𝘪𝘯 𝘮𝘢𝘤𝘤𝘦 𝘩𝘶𝘥𝘶 𝘯𝘦 𝘬𝘢𝘺𝘪 𝘢𝘶𝘳𝘢𝘯 𝘪𝘯𝘺𝘢 𝘴𝘰 𝘥𝘢𝘨𝘢 𝘣𝘢𝘺𝘢 𝘪𝘯𝘬𝘢 𝘴𝘢𝘮𝘶 𝘸𝘢𝘤𝘤𝘦 𝘬𝘢𝘬𝘦 𝘥𝘢 𝘣𝘶𝘳𝘪𝘯 𝘢𝘶𝘳𝘢 𝘣𝘢 𝘴𝘢𝘪 𝘬𝘢 𝘢𝘶𝘳𝘦 𝘵𝘢 𝘣𝘢 , 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘢𝘪 𝘯𝘢𝘴𝘩𝘢 𝘧𝘢𝘥𝘢 𝘮𝘢𝘬𝘢 𝘯𝘪 𝘮𝘪𝘫𝘪𝘯 𝘮𝘢𝘤𝘦 𝘥𝘢𝘺𝘢 𝘯𝘦 𝘥𝘢𝘯 𝘩𝘢𝘬𝘢 𝘢𝘥𝘥𝘶'𝘢 𝘬𝘢𝘸𝘢𝘪 𝘻𝘢𝘬𝘢 𝘵𝘢𝘺𝘢𝘯𝘪 𝘥𝘢𝘴𝘩𝘪 𝘺𝘢𝘬𝘢𝘳𝘪𝘴𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘺𝘢𝘯𝘢 𝘥𝘢𝘨𝘢 𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘨𝘪𝘳𝘢 𝘴𝘩𝘪𝘬𝘦𝘯𝘢𝘯 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘺𝘢𝘬𝘢𝘸𝘰 𝘮𝘢𝘬𝘢 𝘪𝘵𝘢, 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘺𝘢𝘤𝘦 𝘺𝘢𝘶𝘸𝘢 𝘬𝘰 𝘬𝘢𝘪 𝘧𝘢𝘩 𝘩𝘢𝘬𝘢 𝘯𝘢𝘬𝘦 𝘴𝘰𝘯 𝘫𝘪 𝘺𝘢𝘯𝘻𝘶 𝘬𝘢𝘺𝘪 𝘧𝘢𝘳𝘪𝘯 𝘤𝘪𝘬𝘪 𝘥𝘢𝘨𝘢 𝘮𝘢𝘴𝘢 𝘬𝘢𝘪 𝘺𝘢𝘺𝘪 𝘬𝘢𝘮𝘢𝘳 𝘬𝘢𝘳𝘢𝘮𝘪𝘯 𝘺𝘢𝘳𝘰, 𝘮𝘢𝘴𝘩𝘢 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩𝘶 𝘈𝘳𝘫𝘶𝘯 𝘺𝘢𝘤𝘦
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
𝘞𝘈𝘐𝘞𝘈𝘠𝘌 𝘈𝘋𝘖𝘕 𝘛𝘈𝘍𝘐𝘠𝘈
🌲🌲🌲🌲🌲🌲🌲
𝙆𝘼𝙐𝙔𝙀𝙉 𝙂𝙐𝙈𝘼
"Kwance yake akan kati fa babu alaman motsi atattare da shi kakan Alili ya dubi Alili yace nifah ban taba jinya irin wannan ba yau ace wata guda ina jinya mutum amma har yanzu shuru yakarasa magana yana kai duban sa ga majin yacin yacigaba dacewa Alili anya wannan bil adam ne ka tsuto sa acikin daji amma duku maganin da yakamata ace nayi masa nama amma har yanzu shuru gaskiya akwai alaman tambaya yakara sa maganan yana kallon Alili,
Alili yace haba kaka ae zaka zubar da ladan ka nasan kasan sauki na Allah ne ya kamata mukara hakuri, insha Allahu zai farka cikin ikon Allah, kakan Alili yace to shikenan Allahu yasa, ameen Alili yace yacigaba da duban mutum nan da ya tsuto sa,
"Kakan Alili yace Alili ya kamata mu gyra masa k'wanciya saboda da alaman kaman ya gaji da k'wanciya, Alili yace haka ne kaka ae kuwa suka gyrama masa k'wanciyan, fita ad'akin baki dayan su sukayi Alili yace wa kakan sa shiya tafi dandali, adawo lapiya kaka ya masa,
" Dandali kowa ya kama budurwan sa suna fira Alili zuba idanuwan sa yayi yana dube-dube ta ina zaiga Bintu amma bubu ita babu alaman ta aran sa yace inna Jummai tahana Bintu zuwa dandali kenan,
"Dandali yakauce kowa sai rawa yake anata liki, sai kid'an kwarya akeyi ae kuwa ana cikin nishadi sai ga Bushar yazo ai kuwa yayi sit kamar babu mai numfashi acikin su, tsayawa yayi yace ina matana shuru babu wanda ya kula sa saboda abu kad'an zakayi yace kayi laifi, !ba magana nake muku ba kuna jina kunyi mun shuru ae kuwa jikin su ya fara bari am am bamu sanan yadda take ba suka fada cikin barin jiki, dayake kowa yasan wayake nufi da matar sa, Bushar yace ina Hauwa da Maryam, gamu sukace cikin barin jiki duban su yayi yace musu ina matana tana gida suka fada, yace wato ku uwar ku ta turo ku domin nishadin ku amma tabar matana agida dan ta mata bauta ko, bari jikin su yake suna girgiza kai a'a a'a kawai suke cewa yace kumun shuru dan uwar ku saka su yayi agaba suka nufi gida,
Bintu zaune take rike da cikin ta rabon ta da abinci tunda safe da safen ma mairo ne tabata koko tasha, inna jummai ne tazo wajan ta tace tundazo na baki wanke-wanke nan baki karasaba wallahi Allah Bintu kikiyaye ni baizai yayyuba wallahi muciyar da yar tsutuwa amma nasata aiki tana mun ganda, Baffah yana jinta bai isa yayi magana ba tadawo kanta tausayin Bintu yakeyi yasan bataci abinci ba tun safe bazaki yi sauri ki karisa mun ba sai na miki dukan tsiya agida nan gacan awara yana jiran ki wallahi komai dare yau sai kin fita talla nan tafada tana zungurin kanta, kai hanu tayi zata zuba mata fari afuska taji Bushar na magana hanun ki yana kai fuskan ta sai na yanke hanun, ae hanun tsayawa yayi cak kari so gurin Bushar yayi yanausa wanke-wanke , "yace nasan tun safe baki ci komai ba Bintu kin hadu da wanan azaluman matan yakari sa magana yana nunata da yatsa yace wallahi kifita aharka ta inba kina son lahira tayi bako bane yafada yana kai idanuwan sa cikin nata tsire da panta ya bawa Bintu yace taci ta kwanta, yadubi inna jummai yace wallahi wallahi kika sake bataci tsiran nan ba wallahi kinji na rantse da Allah sai na miki abunda baki taba tsammani ba, ya kauce da dariya yace kema kinsa abunda zan iya komai zaki mata daga yanzu zuwa gobe zan gani atafin hanuna yafada yana nuna mata hanun sa, batsa na wuce ko saina bangaje ki ae kuwa babu shiri ta matsa, harya kai kofar gida yaga Baffah dawowa yayi ya tsuguna ya gaishe sa yayi ficewar sa, duk gari Bushar wa Baffah ne kawai yake bashi girma,
"Haka inna jummai tana gani tabar Bintu taci tsiran ta ta kwanta Baffah sai godewa Allah yakeyi, dama akace gaba da gaban ta,
Khalil
"Mutsu-mutsu yafara da alaman dai yafarka, rike kansa yayi yana juyawa akan katafar, hawaye sai zuba sukeyi acikin idanuwan sa, baki daya baya cikin haiyacin sa kuka yake sosai kamar karamin yaro ahaka Alili yashigo yasame sa abirkice Alili ya farama masa magana cikin yaran sa, kafarka ne? Yakake jin jikin ka? yamasa tambaya lokaci guda, dagudu Alili ya juya yanufi kakan sa yana fadama masa, bai karasa maganan ba kakan Alili yatashi suka koma dakin yadda Alili yabar sa haka suka shigo suka samai sa rike da kai hawaye sai fita yake acikin idanuwan sa,
"Rayuwa kenan baka sanin yadda kaddara zata samai ka yau Khalil ne wance akan wata katifar da baitaba ganin irin taba, baima san yadda kansa yake ba"
Da taima kon Allah dana kakan Alili suka samu yabar murkusuwa akan katifa nan,
"Kakan Alili yaduba Alili yace gaskiya jinyan wanan mutumin na asibiti ne kagafa rike kayin sa yake gaskiya yana bukatar likita ya duba sa, Alili yaduba kakan sa yace hakane amma kuma ina zamuga likita har mukai sa ya duba sa mubar sa kawai anan tunda ya farka insha Allahu zai tashi cikin aminci yakarasa magana yana duban mutumin da ya tsuto cikin matukar tausayin sa,
Kakan Alili yace too Allah yasa, " gyra masa kwanciya sukayi kakan Alili yace shi yatafi dayake Alili ad'akin yake kwana"sai da safe Alili ya masa,
"Cikin dare karfe 2:46 daidai Khalil yafara bude idanuwan sa da suka masa nauyi, cikin sauri Alili yatashi yana masa magana kafarka? Ina yake maka ciwo? duk yajera masa tambaya lokaci guda,
!kallon sa kawai Khalil yakeyi baya fahimtar abun da Alili yake fada masa, Alili kuma shi damuwan sa mutumi nan ya masa magana ko zai ji sanyi cikin zuciyar sa .........
"Alili yana ta masa magana damuwan sa wannan mutumin ya masa magana, khalil kallon sa yake kwai baya fahimtar sa, " Alili fita
ad'akin yayi ya nufi d'akin kakan sa dan yasanar masa cewa fah wannan mutumin yafar ka,
"Kaka katashi yafarka fah amma baya magana kaka kana jina kuwa yakarasa maganan kamar zaiyi kuka"
Kaka yace Alili ina jinka fah gani futowa ya karasa magana nan yana mikewa, fitowa yayi suka nufi dakin dan ganin halin da mutum nan yake ciki, shiga cikin daki sukayi yadda Alili ya barsa haka suka zo suka same sa,
"Kaka ya dubi mutumin da har yanzu basu san sunan sa ba magana ya fara masa da yaran su, yawwa bawan Allah ka farka yau kima nin wata guda kenan kana kwance a nan baka san yadda kanka yake ba sai yanzu Allah yayi zaka tashi, yanzu dai katashi kasha koda koko ne dan rabon ka da abinci kajima yakarasa magana nan ya kara kai duban sa ga mutun nan,
"Khalil kallon kaka kawai yakeyi baya fahimtar abunda kaka yake fada masa, idanuwa ya zuba masa sai bin sa da kallo yakeyi, Alili yace kaka anya kuwa yana cikin hankalin sa kuwa sai magana muke yi amma yayi shuru baya ko magana, kamar zai yi kuka ya karasa magana nan,
Kaka yace in sha Allahu zai dawo dai-dai Allah yasa Alili yafada yana kara duba mutun nan
"A haka suka kwana ajikin sa dan kar su tafi kuma yazo yana bukatar wani abu"
Bayan gari ya waye ne kaka yasa Alili yakai masa abun karyawa, kuku da kosai Alili ya kaiwa Khalil
Hmmm rayuwa kenan yau khalil ne aka kai masa kuko da kosai mutumin da shi abinci ma saiya zaba Allah kama maikyau,
"Shiga d'akin Alili yayi ajiye kokon da kosain yayi agefe ya koma wajan khalil, taima ka masa yayi ya dakasa, bayan yadaga sa, ya koma ya dauko kokon nan da kosai dawowa yayi kurin khalil ya mika masa kokon nan, khalil bin hanun yayi da kallo, Alili yace kasha nasan kana jin yanwa dan rabon ka da abinci kaji ma, kallon sa kawai khalil yake yi, Alili ya fahimce wannan mutumin baya jin magana nan sa fah dan haka yakai kokon bakin sa ya nuna masa yadda zaiyi, ae kuwa shima khalil yayi haka, sosai Alili yaji dadi yacigaba da bashi dakan sa,
Bayan ya gama bashi ne sai yameke alaman zai tafi, juyawa yayi da niyan tafiya yaji ancefke hanun sa, ae kuwa da sauri Alili ya juya yana kallon sa, still Khalil baiyi magana ba, girgiza masa kai Khalil yake masa hawaye fal cikin idanuwan sa.........
"Idanuwan sa fal da hawaye, Alili yace mai ya faru kana bukatar wani abu ne? still khalil baiyi masa magana ba sai kallon sa yake, hawaye ne suka zubo daga idanuwan sa, kuka yake sosai kamar karamin yaro, hankalin Alili ya tashi matuka ya rude mai ya faru dashi yakeke kuka kashi ya k'i sake sa bare ya kira kakan sa,
" Kuka sosai Khalil yake kamar kara min yaro duk wanda yaga Khalil a wannan hali sai ya tausaya masa, Alili magana yake ta masa kana bukatar wani abune kodai na maka wani abu ne? bansani ba, shima kuka yasa yana kiran kaka, kaka, kazo kazo yana kuka yana kiran kaka, duk wanda ya gan su sai tausaya musu,
"hawaye ne suka suba acikin idanuwan suhaima tana rubutu tana kuka abun yabata tausayi,
" Bintu zaune ka kasuwa zuba idanuwan ta tayi tana ganin ta yadda Alili zai bulo ako wata safiya sai Alili yazo gun Bintu inta fita talle, yazo sun gai sa amma yau shuru, hankalin Bintu ya fara tashi Alili bai taba mata haka ba kodai ba lapiya yake ba, girgiza kai tayi tace in Allah yadda yaa Alili yana cikin koshin lapiya, bari ko zuwa anjima ne, nasan wani abu ne yari kesa nasan zai zo,
"Har Bintu tagama sai da kokon ta Alili bai zo ba hankalin ta yatashi sosai, addu'a tafara cikin zuciyar ta Allah yasa kar Bushar yazo yau dan ko yaushe sai yazo yarakata gida idan tagama sai da kokon ta "
"Yaso ya hanata amma Bintu tace kar yafara ita tace zatayi badan tana son talle ba a'a saboda tana tausayin Baffah ta saboda aduk lokacin da Bushar yayi ma inna jummai fada akan karya sake ganin Bintu tayi wani abu to fah kan Baffah ta zata koma shiyasa tace ita tace zatayi saboda tasan kullum idan garin Allah yawaye sai tayiwa Baffah fada idan ta tuna Bushar ya hana Bintu talle shiya tace tana so ne, kuma Bushar najin magana nan Bintu sosai,
"Ae kuwa addu'an Bintu ya karbo dan yau Bushar baizo ba, taji dadi sosai,
" Gidan su Alili ta nufa dan ganin ko yana lapiya dan har addu'a takeyi cikin zuciyar ta Allah yasa yayan ta Alili yana lapiya, bayan ta iso kofar gidan tsayawa tayi ta fara tunanin tashiga ne ko kar tashiga, sai kuma tace ae gidan su ya Alili kamar gidan su ne kakan Alili yadauke ni tamkar jikan sa ne, kawai nashiga, bayan tagama yanke shawaran shiga cikin gidan, kafafuwan ta tasaka cikin gidan da sallama acikin bakin ta, ta kusa kai cikin gidan, sallama takeyi atsakar gidan amma shuru babu kowa,
Alili zama yayi kusa da Khalil yana masa magana yana kuka yana cewa kafada mun mai yasa maika kake kuka wani abu ya faru dakai ne, kuka sosai Khalil yakeyi harda shasheka, Alili shima haka kuka yake sosai, kuka sosai sukeyi kamar wanda aka musu mutuwa,
"Bintu tana ta sallama shuru saboda kaka baya gidan tun lokacin da Alili yake kiran kaka akan Khalil na kuka baya gidan yatafi daji dan nimowa wannan mutumin maganin da zaisake samun karfin jikin sa,
Har Bintu tayanke shawaran komawa, " Kawai taji shashekan kuka ad'akin ae kuwa hankalin ta yatashi sosao ita atunanin ta wani abu ya faru da yayanta Alili shiyasa bai zo yau wajan taba ae kuwa bata sanda tashiga cikin dakin ba babu ko sallama gabaki daya bata ma cikin haiya cinta, ya Alili kawai take fada sam bata cikin haiyacin ta Ya Alili mai yasa maika, sam bata lura da abunda ke faruwa acikin dakin ba,
"Alili rike hanun Khalil yayi yana kuka yana masa magiya ya fada masa mai yasa shi kuka haka,
Khalil daugo kan sa yayi ya daura idanuwan sa akan Bintu ae babu shiri yafisge hannun sa daga rukon da Alili yamasa kai tsaye gurin Bintu yayi , yana isa wajan ta yaron gumota ajikin sa sai bari yakeyi yana fadin..........
"Cikin barin jiki Khalil ya rumgume Bintu yana cewa ki boye ni zasu kamani suka she ni, " Kuka yake sosai karamin yaro abu daya yake tafadi, "kiboye ni zasu kamani sukashe ni" Sake rumgumo ta yayi akirjin sa gabaki daya yamata rumfa, k'ankame ta yayi ajikin sa, Bintu tsaban tashi cikin rudani takasa kwace kanta ajikin sa, tashiga bakon yanayi, wanda tunda take acikin rayuwar ta bata taba shiga cikin sa ba, tunda take arayuwar ta namiji bai taba mana haka, tsaban ta rude takasa tabuka komai, shi kuma khalil sai kara cusa kansa yake akirjin ta yana fadin zasu kamani su kashe ni, "
"Alili idanuwa yazuba musu yadae na kuka amma kuma abun yana ta bashi mamaki me hakan ke nufi da wannan bawan Allah kansa kalau kuwa kodai mahaukaci nakawo gidan mu, duniyar tunani yashiga, sai sake-sake yakeyi cikin zuciyar sa, "
"Sumewa Khalil yayi dukan su suka zube akasa anan ne Bintu ta dawo haiyacin ta tunda ga farkon shigo wanta gidan harda shigan ta dakin sai ta tsaya tayi tunani ae kuwa nan, Bintu ta meke tana zare zazzaran idanuwan ta hawaye fal cikin su, sam bata lura da Alili ba tayi da tasanin shigan ta daki baki daya gidan ma tayi da tasani, kokarin ta bar dakin, har tazura kafan ta awaje, taji Alili ya kira sunan ta, Bintu " tsayawa tayi cak ita bata karisa fita ba, ita bata koma ciki ba, "
"Tun lokacin da Khalil yafadi Alili ya dawo daga duniyar da ta aura tunanin sa, yadawo cikin haiyacin sa, "yace Bintu idawo kar kitafi wannan shine mutumin danake fada miki na tsuto sa adaji, tun jiya yafar ka amma baice mana komai ba, sai kuka yake sai da yaganki naga ya fiske hanuna daga rukon da na masa, yaje wajan ki, karki tafi kitsaya dan Allah suma yasake yi nasan dole zai bukace anan gun tanan ne kawai zamu gane mai yafaru dashi, "
"Bintu bazata iya musu wa Alili ba dan haka takoma ciki, mikewa Alili yayi ya fita adakin, randan kasa naga yanufa, yacika kofi da ruwa mai sanyi, komawa dakin yayi kusa da Khalil yanufa, ruwan ya watsa masa akan fuskan sa, doguwar numfashi Khalil ya sauke tare da tashi araza ne yana baza manyan idanuwan sa da suka numshe, sai mutsa bakin sa, yake yi da alama magana yake son yi yana ta baza manya-manya idanuwan sa, daura idanuwan sa yayi akan Bintu ae da sauri yanufa wajan ta, "
"Bintu tana ganin ya nufa wajan ta tafara jada baya tana kokarin boyewa abayan Alili, dan gaskiya bazata bari yanzu yataba taba, "
"Ganin tana kokarin guduwa yasa Khalil tsayawa cak ya fara magana, kema gudu na zakiyi kowa baya sona babu wanda yake kulane sai ke amma kema yanzu guduna kike yi yana magana hawaye suna zuba cikin idanuwan sa,
" Cikin rudani Bintu da Alili suka shiga kamanya daman yasan Bintu ne dama kodai yasamu tabun kwakwalwa ne, "
"Khalil yace inna miki laifi ne na yarda kizane ni amma dan Allah karki kuje ni MiMi, Mimi suka hada baki wajan furtawa baki dayan su da Bintu da Alili,
" Kaka ne yashigo gidan da ganyan maganin da yasamowa wannan mutumin da suke jinyan sa, kai tsaye dakin da yake kwance yanufa, ae yana shiga ya tsinkaya muryan mutumin nan yana magana, tsayawa yayi cak sai da yagama sauraro ya kusa kan sa cikin dakin, "
"Alili kaka ya kalla yace ae nace maka jinyan nan wannan mutumin na asibiti ne, dan haka ya kamata mukai sa asibiti gobe in allah yakai mu
Alili yace.............
Alili yace Allah yakai mu goben insha Allahu zamu kai sa,
"Khalil durku sawa yayi akasa yana kuka yana cewa Mimi dan Allah karki gujeni kamar sauran mutanin, yana kuka yana mata magiya akan karta barshi, daga Kaka har Bintu sunshiga tashin hankali sosai yasan Bintu ne
" Alili ne yanu fah wajan Bintu kama hannun ta yayi ya fara mata magana cikin sanyin jiki, Bintu nasan baki sanwan bawan Allah kamar mu bamu san ko ma haukaci bane amma gashi yana magana ne cikin hankali dan Allah Bintu ina son kimun taimako ki taimaka ki isa wajan wanan bawan Allah kece kawai mafitan mu musa mu kan sa, shifa masoyi abun so ne, makiyan ka kuma abun, kine Bintu tunda yanuna yana bukatar ki kitai maka karyasa ke shiga wani hali dan Allah Bintu Alili yahada hannuwan sa duka biyu alaman yana rokon ta,
"Girkiza kai Bintu tashiga yi tace haba yaa Alili basai ka roke niba insha Allahu idan nice sanadin warakan sa zanyi bakin kokari na ganin yasamu lapiya, takarisa magana nan tana nufar wajan sa,
" Magana tafara masa cikin sanyin muryan ta mai dadin sauraro, tace haba yazan tafi nabar garkuwa na kaima kasan bazan tafi nabar Sadauki na ba kasan ina ji dakai Sadauki, kaine fah abun alfahari na awannan duniya nan kadai na kuka kar kasani nayi nima inkana wannan kukan kana karya mun zuciya ta, kadaina karka sani kuka nima, "
"Kallon ta Khalil yakeyi cikin wani karamin muryan sa mai dadin saurara yace bazaki barki ba ko Mimi, ehh bazan barka ba Sadauki na, sosai Khalil yareke hanunu wanta kamar wani zai kwace masa ita "
*******
"Abba sai shirye-shiryen tafi india sukeyi, gobe ne tafiyan su, Abba ne ya kalla umma yace Rahama gobe ne tafiyan mu insha Allahu sai ki kula da gida, kinga halin da Hafsatu take ciki magana ma batayi babu abun da takeyi saidai adaka akwantar bamu san sanda zamu dawo ba nasan kina da kokari to dan Allah kikara, umma tace insha Allahu zan iya bakin kokari na, kuma samu tamata addu'a Allah yasa atafi asa'a Allah yabata lafiya, amin amin Abba yace yaji dadi sosai da addu'an umma yasanta da kokari sosai, mikewa yayi yace bari nadan je gida nadawo, adawo lafiya umma tace masa,
"Abba yana shiga cikin gida yaji hayani acikin gidan sa, da sauri yashiga cikin parlo amma babu kowa kuma still yana jin hayaniya, kai tsaye sama yayi dan daga gun yake jin hayaniya, ae kuwa yana isa gun yaga su Khairat, da Khalisat, da kuma kulthme, zaune abakin kofan d'akin Kulthme sai kuka suke suna magiya akan Kausar tabude musu kofar dakin tunda zo takulle kanta adakin tana kuka tana cewa ita akaita gun momyn ta babu idan za akai mata momyn ta ae dan sunga babu yaya KYC, ne dama shine mai son ta bayan momyn ta kuka take sosai , Khalisat tace haba autan momy wayace miki muba muson ki ae duk gida nan babu wanda yakai ni son ki, momy fah saboda bata da lapiya ne za aje nima mata magani, addu'an mutake bukata, ba kuka ba haba haba yar autan momy da Abba da umma, ooo nikam ban yarda dake ba to naji momy magani za'a nima mata to yaaa KYC fah kufada mun inda yake kullum kuce mun yayi tafiya kuma haryan zu bai dawo, takari sa magana nan tana kuka mai karya zuciya, Khalisat ce tace babu inda yaa KYC yaje mutuwa yayi kuma idan. bata kari sa magana ba Khairat ta rufe mata baki, ae kuwa Kausar taji komai, sumewa tayi akan gadon, magana Khairat take mata amma shuru ko numfashin tama basuji, "
"Khairat ta dubi Khalisat tace haba mai haka kikayi ita dayace fa adakin kika fada mata wannan magana nan duk tsananin yaa Khalil yana matukar shagwaba Kausar itace kawai take ganin dariyan sa amma zaki fada mata wannan magana nan, "Khalisat tace to kullum zamu ringa boye mata ne bayan idan an mutu ba adawowa, " Khairat tace za afada mata mana amma ba ta hakaba, to acikin haka ne Abba yazo yasame su, "
"Abba ya tambaya abunda yake faruwa Khairat ce ta faiyace masa komai, kai tsaye kufar dakin yayi bugu yakai masa ae kuwa sai ga kofa ta bude, baki dayan su suka shiga cikin dakin kai tsaye gadon da kausar tak kwance akai suka nufa,
" Asume suka same ta babu numfashi atattare da ita gabaki dayan su sunshiga cikin tashin hankali dukan su sun rude sun rasa mai zasuyi, Khalisat kuwa tayi da tasanin fada mata da bata fada mata ba da duk haka bata faru ba, kuka Khalisat da Kulthme suka fashe dashi, "
"Abba ne yayi azancin tura Khairat ta dauko ruwa , ruwa mai sanyi ta dauko akazoba mata, doguwar numfashi ta sauke, idanuwan ta taware akan Abban ta Abba...! tafada arede Abba dagaske yaa KYC ya mutu? Abba yadobe ta yace haba autan momy kina son momy tayi fushi dake ne ko yayan ki Ibrahim ae in sungan ki ahaka baza su jidadi ba haba yar autan yayan ta KYC, ki kwantar da hankalin, kitayiwa yayan ki addu'a shine kawai zai gane kina son sa dan ayanzu yafi bukatar addu an ki, kinji yar auta na,
"Girgiza kai takeyi kafada mun ya mutu ko yana raye kafada mun Abba, Abba yace yanzu nasan kingaji ki kwanta kiyi barci gobe da safe zamuyi magana,
" Dalalabi Abba yasamu yashawo kan Kausar, bayan tayi barcci baki daya Abba ya kira su,
"Ya dubi Khairat yace Khairat kece babba dan haka kita jan su ajiki insha Allahu momy zata dawo lapiya kucigaba da mata addu'a,
" Khairata tace insha Allahu Abba Allah yabawa momy baki dayan su sukace amin,
********
Bari mu koma bangaran Arjun da Aaraw,
Arjun ne zaune a parlo yahada rai sakama kon abunda Abba yafada masa cewa gobe zai tafi KAUYE GUMA sbd ance masa ana bukatar tai makon likita agun saboda akwai majin yata sosai masu bukatar magani, shine daddy yace masa ae yashirya gobe ne tafiyan sa kuma wannna karon bada Maheer zatafi ba shida wani amintattacen daddy ne, shine Arjun yahada rai shifa bai son zuwa KAUYE arayuwar sa amma yazaiyi tunda daddyn sane yace dole sai yaje,
"Arjun ya fada cikin tunani kawai yaji antabashi, dago idanuwan sa yayi saukewa yayi akan ummin sa, haba Arjun sbd zakaje kauye ne kake wannna tunani haka, haba taimako ne fa kuma nasan my son dina mai son taimako ne fada mun maike da munka
'Ummi Allah akwai abunda yake damuna kwana biyu nan inajin gaba na na faduwa, ummi na wallahi ina cikin damuwa zuciya ta tana mun zafi ina jin kamar akwai abunda zan rasa mai mahimmanci acikin rayuwa ta ummi kicigaba da mun addu'a kawai,
"Sosai ummi hankalin ta yatashi tashiga rudani, Arjun fadamun da muwar ka nice mahaifiyan ka babu wanda yakamata yasan sirin ka sama dani fadamun maiyake damunka takari sa magana nan hawaye fal cikin idanuwan ta,
Arjun yace wallahi ummi nima dai bansan mai yake damuna ba amma ina yawan mafarkin wata yarinya, tana fadin intaimaka mata kuma tare da jariri ahannu ta ummi tunban damuwa har nafara damuwa, har yakai ina jin ina matukar kaunar ta ummi wallahi ina matukar son ta, kuma wallahi aduk yaddda nagan ta zan gane ta ummi ina matu kar son ta,
"Ummi taji tausayin yaron ta sosai kuma ta fahimce sa tace insha Allahu zan tayaka da addu'a insha Allahu babu wani mumunan abunda zai faru dakai kaji gaba da addu'a nima zantayaka
"WAYAYE AKACE ADON TAFIYA,"
Bari mukuma can baya wato aeniyin tushin MANGA family, in masu karatu basu manta ba dama nafada muku cewa manga family tana da girma sosai da sosai, kowa yasanta aduniya,
"Alhj Abdulkadir shi ne Granny wato alhaji kaka, alhaji kaka sunkasance su uku ne agurin iyayan su dukan su maza ne Alhaji kaka shine babba sai kuma mai bin sa, malam muhammad sai kuma karamin kanin su, sulaiman, sunta so cikin son junan su da girmama junan su zaman lapiya acikin wanan family ba'a magana nan sa, suna girmama yayan su Abdulkadir shima haka kowa yayi Auran, yayin da Abdulkadir yake da mata biyu safiyya da kuma Zulaihat, sai kuma muhammad matan sa daya Zainab, sai kuma sulaima matan sa daya Hannatu,
Alj. Kaka yaran sa uku musa sai Abubakar sai autan su majidda,
Muhammad kuma yaran sa uku Abdullahi da kuma yahaya sai kanin su Amadu,
Sai sulaiman dan sa daya aduniya Abdulkadir ta kwanran Alhaji kaka
Suna rayuwa cikin farin ciki, akoda yaushe sai sunje sunyi aekin karfi kafun su samu abunda zasukai cikin su gasu da yara kanana, "wata rana Abdulkadir da Muhammad da Sulaiman suna tafiya sukaci karo da wani kwali agaban su, zuciyar su tafara musu sake-sake akan tadauka ko karta dauka, yanke shawa sukayi akan sudauka haka kuwa sukayi suka dauka dan zuciyar su tana basu kamar abu mai mahimnaci ne aciki kai tsaye wajan mahaifin su sukayi da abun, suka sanar masa akan wanan kwalin da suka tsuto sa aciki , ae kuwa suka bude amun mamaki kudine da dalan Amurca da zinare sukaci karo dashi, sunyi murna sosai talauci tayanke musu, Abdulkadir ne wato Alhji kaka yahada rai ya dube su yace wani irin talauci tayanke muku, kudae ce talauci tayenke mun dan nine natsuto wanan abun sunyi mamaki dajin abunda yayan su yafada tofa daga nan rikici takafce tsakanin su har takai da dambe wannan rikicin ne yayi sanadiyan mahaifin su,
"Bayan akai su ne Abdulkadir wato Alhaji kaka yadage fa shi dukiyan sane wannan to daga nan ne kowa yakama gaban sa kowa yadauke matan sa yabar gari batare da waye-wayan junaba sukabar wa Alhji kaka dukiyan sa,
Alhaji kaka ya nufi Abuja nan ne yakafa kasuwancin sa da kaffanuni akasashin waje da yauwa kuma akowata kasa akwai hanun jarin sa, tayadda kowa naduniya tasan da zaman sa yacanza suna ya mai da ita MANGA FAMELY
Wanan kenan,
"Bangaran Muhammad kuma yasha bakar wahalan rayuwar kango suke zaune da matan sa da yaran sa uku wato Abdullahi da Yahaya da kuma Amadu sai sunyi dako suke samun abunda zasuci rayuwa ta musu tsanani haka suke rayuwa da bakar talauci, wata rana Muhammad yana zaune acikin kasuwa wani bawan Allah yazo yana tamasa magana akan yakai masa dako amma shuru baiji saba sai da mutu nan yabatasa tukun na yadawo cikin haiyacin sa, yace inata maka magana amma shuru kashiga cikin tunani, Muhammad yace kayi hkr Alhaji banjika bane mikewa yayi yabi bayan Alhajin yakai masa kayan sa cikin moto,
Alhajin yabukaci Muhammad yabisa ae kuwa yabisa, Alhaji nan ya dubi muhammad, yace suna na Alhaji Iliyasu mai dala nasan kana jin sunan, muhammad yace ehh ina ji, Alhaji Iliyasu mai dala yace kozan iya sanin damuwar ka, girgiza kai muhammad yayi alamun ehh, gabaki daya yabayabasa labarin sa, sosai Alhaji mai dala ya tausaya masa yace masa ae wannan kwalin nine na ajiye sa dan wanda baida karfi yasamu to karka damu zan baka abunda yake cikin kwali nan daga nan kuma sai kafada mun yadda dayan dan uwan ka yake, muhammad yace wallah bansan yadda yake ba dan kowa yayi tafiyan sa ne, shikenan mai dala yafada yace Allah yahada sa da mutumim kirki daga wanan lokacin malam muhammad yadawo mai kudi yakoma muhammad musa churoma yamai da sunan famelyn sa churoma famely, yasaka su Yahaya amakaranta, bakowa bane churoma famely face family Abban Ibrahim Khalil KYC,
Duniya tasan da zaman wa kinan famely sbd kudin su da MANGA FAMELY da kuma CHUROMA FAMELY amma su kuma basu sanna akwai wata alaka atsakanin suba sbd babu wani abunda yataba hada su,
Abdullahi yayi aure matan sa biyu Hajjo Maryam yaran ta biyu Aliyu da Suwaiba, sai kuma amaryan sa Rukaiya yarta daya Khalija,
Alhaji yahaya matan sa biyu ae kun sani Hafsatu momyn Khalil yar sarkin bauchi ne awani taron gama makarantan sa yahadu da ita taje taya yar uwata mur nan gama makaran ta suka hadu har soyayya tashiga tsakanin su akayi aure, Khalil ne babban danta namiji sai Khairat da Khalisat da kuma Kulthme sai autar su Kausar,
Sai kuma matan sa ta biyu Rahama yaran su biyar uku mata biyu maza, Hauwa'u sai kasim sai khalid sai khairiyya sai autan, su Khadija,
Rahama wato umma jakadiyan momy ne sbd tattakun umma ne momy tasa Abba ya auro ta, Abba bai so ba amma kuma momy da tanuna ranta yabaci soasai ne yasa ya aminta wannan kenan,
Su khalil suna kiran da malam Muhammad da malam kaka yayin da suke kiran matar sa da Ammu,
Sulaiman kuma baisha wahalaba Allah yahada sa da wani bature yadauke sa da matan sa da kuma dansa suka wuce Amurca,
WANNAN SHENE LABARIN ALHJI KAKA, MANGA FAMELYFAMELY DA CHUROMA FAMELY AHALI DAYA NE BATARE DA SU YARAN SUNSAN SUNA DA WATA FAMELY BA,
Wannan kenan,
KASAN AMERIKA
Babban parlo ne mai dauke da launin jaa, wata matashiyan yarinya ce zaune gashin kanta duk yarufe mata fuska, riga da wando ne ajikin ta mai launin jaa, danna wayan ta take tana tasake murmushi da alama dai tana cikin inshadi sosai, wani kara naji asama ana magana da karfi, nifah Allah bazan lamun ta abunda akemun acikin gidan ba wannan ae wulakanci ne yazan ajiye lapton dina achager amma ancire mun kuma nasan bakowa zai mun haka ba sai Sana, takari sa magana cikin tsantsan bacin rai, wannan wanda take zaune aparlo nan ne naga tafashe da daria, dani kike zance tafada tana kara zama akan kujera, wallahi indai zaki cigaba da shiga harka ta Suha ta zaki taganin bacin rai takarasa magana nan tana kara fashewa da daria, futowa naga tayi daga dakin ta nufo gun wannan wacce take zaune akan kujera tana karkada kafa da alaman ashirye take ayi duk wacce za ayi, futowan tane yaban daman kallon fuskanta da kyau kyakyawace sosai farace sol gashin kanta duk yazube mata abayan ta,
Nufo parlo tayi kaitsaye wajan wannan yarinyan danaji takirata da Sana tayi tana zuwa naga ta shako wuyan rigan ta anan ne nasamu daman ganin fuskanta kaman su daya sak babu wata babanci atsakanin su saidai babancin hali, magana Suha tafarayi ma Sana nasankece kawai zaki mun abunda akamun wallahi kifita ido na, takari sa magana nan tana mai cilata akan kujeran , dariya Sana tafara tanacewa wallahi indai zaki cigaba da shiga harka ta toni kuma zanta saki bacin rai, takari sa magana nan tana mai fashewa da daria, bakin ciki ne yakama Suha, dakin mom tanufa tana name kwalla mata kira mom mom mom wallahi Allah ina fadamiki kifadawa yarinyar ki tadaina shiga harka ta ban son abunda take mun magana take cikin bacin rai irin an kure mutum dinan,
Mom daga cikin daki tafara magana ooo ni Razia naga takai na ina zansa kaina da rikicin twins dinan kulum cikin fada basa zaman lapiya Suha akwai niman tsokana Sana kuma bata barin ta kwana............
Mom daga ciki dakin tafara magana ooo ni Razia naga takai na ina zansa kaina da riki cikin twins dina kulum cikin fada basa zaman lapiya Suha niman tsokana, Sana kuma bata barin ta kwana da'ace dayan ku nata raye da bansan nata kallan halin taba, takarasa magana nan tana mai jiran shigowan Suha, Suha ne tashigo dakin ranta ahade magana tafara mom mom mom kiyi wa yarinyan ki magana tadaena shiga harka ta haba yariya duk tabi taraina ni nifa basa'ar tabane takari sa magana nan tana mae hada rai da alama ankai ta makura,
Mom tace zoki fada mun mai yahada ku,
Suha tace mom nasa chager lapton dina tacire mun, to mai kika mata tun farko mom babu abunda namata cewar Suha, tooo muje parlo sai muyi shari'an acen,
Duk da harcen turanci suke magana
Parlo suka dawo yayin da suka samu Sana tana shan ice cream tana tande baki idan tasha ice cream sai ta gutsura chocolate, tana ganin Suha yadda ta hada rai ae kuwa tafashi da daria, tana kara kai chocolate din ta baki, ae kuwa da sauri tanufa wajan ta tana mata magana, ina fadamiki tun ba yau ba kifita harka ta amma ke baki jin magana wallahi sukike na biki duka agida nan, Sana tace saidai muduka juna, kafun nafita harkan ki kema kifara fita harka ta mom kallon su take cikin wannna yaran nawa saidae addu'a,
Magana tafara, "hmmm agabana danme kika kirani Suha mai yasa ba kwajin magana tane ku ko yaushe cikin fada haba haba wai yaushe zaku zauna lapiya ne, kuduba kuga yadda su, sukaina suke rayuwar su da brother ta mana shima namiji kenan amma ace kulum fada kamar wanda suke ganin hanjin junan su takari sa magana cikin fada da nuna ranta yabaci,
Ae dukan su suka shiga cikin tashin hankali basu son bacin ran mom su ko kadan, ehh sunsan su yara ne masu gata komai suke so mom din su tana musu suna samun farin ciki awajan ta, mom din su itace abar alfaharin su, tabbas suna da mahaifi mai kudi sanan ne amma basu samun farin ciki agun sa baya musu murmushi baran tana daria kulum cikin hada fuska, inkaga daria yan sa to yana tare da su Sukaina da Sultan, ina matukar nuna musu babbanci, har watarana suka tambaya mom din su shin mom wannan ne ne mahaifin mu, kuwa baya son mu baya kaunar mu yana nuna mana babbanci sai kace bashi yahaife muba,
Mom duban su tayi tace, bani da abunda zance muku saidai ince akoda yaushe kuka sance masu addu'a aduk yadda kuka tsinci kan ku, komai kukaga yasamu bawa to fah kusai MUKADDARI NE DAGA ALLAh, Allah yana jaraftar mu da abubuwa da yawwa dan yagwada imanin mu dan haka kucigaba da addu'a watara sai zakuga riban addu'an ku,
WAYE NE MOM DA SUHA DA KUMA SANA DA SUKE MAGANA NAN MAHAIFIN SU ANYA MAHAIFIN SUNE
KUBIYONI DANJIN YADDA ZATAKASANCE
*********
Abbi shine maihafin Suha da Sana, Alhaji Abdukadir shine sunan sa yakasance yana da mata biyu, Raziya itace matar sa tafar ko sunyi auran soyayya Raziya mahaifin ta mai kudi sosai da sosai alokacin da Abdulkadir suke soyayya da Raziya bashi da komai Raziya yar gatace agun mahifin ta ita kadai ce yarinyan su dan haka da takai Abdulkadir akan shine mijin datake son aura suka amince mata, bayan auran sa da Razia suka shafe shekara biyar batare da tahaifu ba nan ne mahaifin Abdukadir yadage akan sai dan sa yakara aure dan shifa jikan sa yake so Abdukadir yaji tsoro sosai sbd loacin auran sa da Razia iyayan tane suka masa komai suka jasa ajikin sa suka damka masa komai, bayan auran sa da shekara uku iyayan Razia suka shirya tafi saudi aekin ummura, sukayi hatsari baki dayan su suka mutu to wannna yasaka Razia tashiga tashin hankali sosai bayan rasuwan iyayan ta ne aka bata dukiyan ta, gabaki daya ta damkawa mijin ta, shiyake juya mata,
Maihaifin Abdulkadari ne yasaka sa agaba, yana masa fada, ! bani da kowa aduniya nan sai kai yan uwa na danake jida su duk sun guje ni, kai kadai nake gani naji sanyi arai na, dan haka tunda matar ka bata haifuwa ina son ka kara aure, ! Abdukadir yace baba bawai naki taka bane amma ae haifuwa ta Allah ce, Razia tayarda dani komai nata nawaje na, bata da kowa sai mu idan muka mata haka bamu kyauta mata ba,
Fada sosai Baba yarufe sa dashi har yakai yace namaka dan da wata daya idan baka sake aure ba na sallamaka wa matarka, tashi kaban waje,
Mekewayayi yanufa waje cin karo da matar sa yayi hawaye yacika idanuwan ta, juyawa tayi gudu, bin bayan ta yayi yana mata magiya, akan shifa bazai kara aure ba ae haifuwa ta Allah ce
Kallon mijin ta tayi ta soma magana cikin sanyi muryan ta, karkace zaka bijiraiwa mahaifin ka mijina nima bazanji dadin hakan ba tabbas haifuwa ta Allah ce idan inada rabon haifuwa awannan duniyan to fah zan haifu amma yanzu tuda kana da ikon kara aure kuma zakayi adalce atsakanin mu
to kayi, sosai yaji tausayin sa kuma yajinji na mata tabbas ba ko wata macce zata yarda mijin ta ya kara aure, koda kuwa zai bijirewa mahaifan sa ne,
Abdulkadir kallon matar sayayi kuma ya mata alkawarin adalci atsakanin su sosai ya kwantar mata da hankalin ta,
Abbi yakara aure ya aura wata yar kasan india tazo Amurca cirani ya aure ta, tunda tashigo gidan, ta makirci ne sosai, auran ta da shekara daya Allah yabata haifuwa, tasamu danta namiji yaci sunan sa Sultan, Abbi kulum cikin rarrashin matan sa Razia yake yana kara nufar da ita kan takara hkr haifuwa ta Allah ce,
Sultan yana da shekara biyu aduniya tasake samun ciki zoga murna wajan baba kaka, kowa tarerayan ta yake,
Mom Razia kwance akan gadon ta yau kwana uku kenan bata da lafiya, sosai yau jikin yana damun ta, Abbi ne yashigo yasame ta cikin bargo, da sauri ya nufo wajan ta, yana mata magana akan tun jiya nake cemiki mutafi asibiti amma kin ki dan Allah kitashi mutafi,
Babu yadda zatayi haka tashirya suka tafi asibiti,
Bayan angama mata gwaje-gwaje da tambayoyi na likitoci, likita ya dubi su yace Alhaji, congrotulations, ina tayaka murna matan ka tana da juna biyu,
Sosai sukayi murna mom Razia harda sujada godewa Allah, Abbi yasanar wakowa yan gidan, baba kaka yayi murna kowa yana cikin farin ciki amma banda mutum daya
Ninimatar Abbi sosai tashiga tashin hankali, takira kawan ta maro tasheda mata komai, maro tace ki kwantar da hankalin ki kishirya ina zuwa zamuje wajan wani boka shine zai mana maganin ta, wa'iyazubilla Allah katsare mu da aekin shirka,
Nini taji dadi tashirya maro tana zuwa suka wuce, wajan boka, bayan boka ya dube su yace dole sai anhaifa ciki nan amma zan karkatar da hankalin mijin ki zuwa gare ki, Nini bata so haka ba amma datashi mijin ta gabaki daya hankalin sa zai dawo gare ta sai taji dadi kuma tayi na'am da batun wannan kenan
Bangaran mom Razia kuma sosai take raeno cikin ta amma kwana biyu nan tana ganin kamar hankalin mijin ta bai kanta bata wani damuba sosai
Nini ta haifu tasamu macce taci suna Sukaina, tsakanin su da mom Raziya wata uku, mom Razia tahaimu lafiya Allah yabata yaran ta guda uku duka mata kyawawa, masha Allah, amma sai kash Allah ya dauke ran dayan, bayan mom Razia tahaifu Abbi bazo gare taba abun tun baya damun ta harya fara damun ta, yau kwanan ta uku da haifuwa baizo wajan taba, dakin sa taje tasame shi akan ko tamata laifi ne yadaena kulata, babu aebun da kikamun kawai bana bukatar ki ne ayanzu akusa dani dan haka dan Allah bana son ganin ki kifita adaki nan cewar Abbi taso tabashi hkr taji kodai tamasa laifi ne amma hakan bai samu ba, sosai tashiga kuncin rayuwa babu mai kulata agidan,
Rayuwar mom Razia da yaran ta abun tausayi amma duk da hakan mom tana musu abunda suke so ta nan ne suka samu sauki, nufo mom din su suka yi ganin ranta yabaci akan su mom dan Allah kiyi hkr, wallahi bazamu kara ba suka fada cikin raunin murya,
Duban su mom Razia tayi tace, kune wannanda nake gani naji zanyi azuciya ta bani da uwa bani da uba, kunake gani naji sanyi kune sanyin idanuwa ta wallahi ina matukar son ganin kuna zaman lapiya, idan ina ganin ku kuna hayaniya wallahi zuciyata zafi take mun Allah shine shidana bana jin dadin zaman gida nan amma saboda ku nake zaune ku kan ku kunsan gabaki dayan mu babu wanda yake kula da mu amma ku kullum cikin fada, shiyasa akullum nake yawaita muku addu'a,
Sosai jikin su yayi sanyi kama hannaye ta sukayi suka zaunar da ita akan kujera suka fara mata magana, mom mun tufa bazamu karaba insha Allahu wallahi mom bama son ganin bacin ranki dan Allah mom kidai na fushi da mu, sosai suka fadawa mom Razia magana maidadi suka sata farin ciki sosai
Arana nan ma daki daya suka kwana dukan su pillow daya suka kwana cikin farin ciki, washigari da safe mom tace yau zakuje siyayya ae murna ba a magana sosai sukaji dadi suna ta godewa mom din su, gabaki dayan su kaya iri daya suka sa ka shigan riga da wando jaa sun baza gashin kansu abayan su sunyi kyau sosai,
Mom ne tace wow twins dina kyawawa ne sosai Allah yatsare mun ku Allah yakai mu lapiya yadawo mun da ku lapiya sosai tamusu addu'a
BARI MUKOMA BANGARAN SIDDARTH
Siddarth ne zaune shida abokin sa Raj, Raj yace masa wai nikam baka sha'awa ne ko kallon mata bakayi balatana kace kana son ta, Siddarth ya dubi abokin sa yace ina har yanzu ban samu kalan mace danke soba, Raj yace ko zan iya sanin kalal mace dakake so, gyada kae yayi amun ehh zaka sani,
Siddarth yace ina son mace wace take da ra'ayi kalan nawa wace tasan zamantakewar aure wace tasan darajan aure, kasan wasu mutane suna, aure abune na har abadah wasu na kankata girman wanan kalma da har abada wasu da alama ma basu masan mai take nufi ba, bayan ma'anan ta kalman soyayya gurin cewa ina son ki har abadah kafin kayi aure kafara duba wannan kalma ta har abadah zamane da ake so mutuwa ce kadai zata iya shiga tsakani, shin zama ka iya rayuwa ko da dabba ne na har abadah? bare kuma mutum irin ka mai tunani irin naka mai ra'ayi daban da naka mai kalan tsarin rayuwa da ban da nakanaka kuma na tsawon har abadah? Shin zaka iya kafun kafada rijiya mai zurfi kafara tunanin daya fi rijiya zurfi sosai, airin zaman takewa na har abada mai yakamata mufi bukata agurin abokiyar yinta kyawu ne? Ko kyawun hali? Kuma dai soyayya ce ? A irin wannan dogowar tafiyan mai dogon zango mainene abu nafarko da yaka mata mufara kalla agurin abokiyar tafiya nan, ara'ayi na hausawa suna cewa tun za'a ake shiri basai andawoba, ma'ana ba afara niman guziri bayan anfafa tafiya , kafun kafafa tafiya yakamata mutanadi duk wani abun bukata wanda kasan baza ayisamun saba acikin tafiyar, Siddarth yakala abokin sa Raj da ya nutsu yana jin sa yace kana fahimta na ko, girgiza kai yayi amun ehh ina fahimtar ka,
Yadaura dacewa ka aureta dan tana da kyawun hali bawai dan tana da kyawu ko iya kwaliya ba, haka zalika ma ita macen, bawai dan yana da kudi ba, ko kyawun ba, domin kyawu baya rike aure haka ma kudi, haka ma soyayya bata rike aure amma kyawun haleya zasu iya babu kyawu na har abadah haka ma kuma babu soyayya ta har abadah amma kuma anasamun kyawun halaya na har abadah, idan kana son mace sauki zairika azuzuta maka kyawun ta karin ga ganin kamar tafi kowa komai nata zai ringa maka dadi muryan ta, murmushin ta, dariyan ta, dama komai da yashafi ta, karinga jin kamar ita daya ce ta iya komai, rayuwa karigajin bazaka iya hakura da itaba karinga jin zaka iya aura ta kobaka da ko sisi, ae Allah na nan zai hore maka karinga jin zaka iyayi wakowa rashin kunya in yace bazaka aure taba, koda iyaye ne dama sauran su, amma shi tasirin sa yana raguwa ne daga sanda kasame ta dama abunda yake burgemu dan yana nesa ne damu daga sanda muka samai sa to hankalin mu zaidawo dai-dai sauran abubuwa kafu nan kuma sai darajansa zai ringa yin kasa har mukai lokacin da zaman zabi ne kawai mukeyi,
Siddarth ya numfasa yadaura dacewa
Wayan hanka yanzu haka zaman hakuri muke da ita amma kuma idan zaka tuna kafun ka siye ta har wani jindadi kakey
i ayanzu ma idan kasamu kudi nasan akwai wace kake so kacanza ko? to mukala abun haka yadda zamu fi fahimtar sa da kyau zakaji kana son wayan hanun ka kaji ko saurin shiga internt kodai wani abu to mace ma haka ne saidai idan tana da kyawun hali kawai zakaji kana son zama da ita namiji ma saidai idan yana da wannan ne zataji tana son hakurin mace zataji tana son zama dashi,
Siddarth dubi Raj da yakafeahi da idanuwa yadaura dacewa, kada kabanbanta so da kwaya daya ne aduniya shine son mace da muke kira soyayya kuma dai shi so wani abune arayuwar mu m, ina tsoron aure da mace da badan Allah zata aure niba saidan wani abu nawa,
Yanzu kafahimce ba soyayya ake bukata azaman takewar aure ba ba kuma kyawu ake bukata ba asahun farko ba domin kyawu bai rike aure Raj ina son nasamu mace wace zata soni dan Allah
Sosai Raj yake girgiza kai yabude naki zaiyi magana...........
Raj yace wannan gaskiya ne Allah yabamu mata wanda zasu so dan shi,
Yakuma kallon Siddarth yace kamata zamu fita shofing, no banmata ba bari nashirya, mekewa Siddarth yayi toilet yayi wanda bayan yafito, tsayawa yayi cak yana tunanin yau wani shiga zaiyi shi mutum ne me son kasan sa, yau ta kasance friday dan haka shigan manya kaya yayi, yafito sak ba hausa fulani, Siddarth kyakyawa ne ajin farko, yayi kyau sosai, kai tsaye parlo ya nufo wajan Raj, Raj kafesa da idanuwan sa yayi yace masha Allahu amma fa abokina kayi kyau sosai, gaskiya bazaka barni nayi budurwa ba idan ina tare dakai irin wannan kyau haka,
Hararan sa yayi tare da lumshe idanuwan sa woow woow woow Siddarth yakashee ni da idanuwan sa mai rikitar da mata, yace plz bana son surutu mutafi kona fasa yakari sa magana kamar wanda akace dole yayi magana, a'a bazamu fasa ba mutafi cewar Raj,
Suha da Sana sai siyaya suke yi, su dauki wannan sudauki wancan haka suka ringa jabga kayya, masu kyau da tsada, Suha ne ta dubi Sana tace mata too tunda mungama muje can muyi wasa, ae kuwa Sana sarkin wasa tace haka ne fa muje, ajeye kayan acikin moto sukayi, suka nufi wajan wasan kamar wasu kananun yara,
Sana ne tacewa Suha wani kallan wasa zamuyi, tunani Suha tashiga can kuma tace natuna, fuskan ki zan daure, kinga wancan benan zamu haura inkin kamani kinyi nasara, inbaki kamani ba nine nayi nasara kin yarda, Sana tace ehh nayarda,
Daure fuskan Sana Suha tayi suka fara wasa kan benan Suha tayi Sana tana bin bayan ta, Suha dawowa tayi ahankali batare da Sana ta ankara ba ta sauko kasa, ita kuma Sana cigaba da haurawa sama takeyi har ta iso karshen benan,
Tuntube tayi tayi kasa ae kuwa batasan sanda tafuncike abun fuskan taba ganin ta akarshen benan aekuwa tashiga cikin tsoro, da rudani, jada baya take, bata ankaraba kawai jinta tayi tayi kasa, ae kuwa da sauri tarike wani dogon wani abu kamar fanka, wannan abun she kawai yahana ta saukowa kasa gashi benan dogone kuma nakarahe take,
Suha Suha Suha ta kwalla mata kira Suha shikenan karshe na yazo mutuwa zanyi nasan bazan rayuba, Allah sarki mom dina shikenan daga yau bazan kara ganin kiba kuka take sosai tana niman agaji, da farko Suha tazata iskancin Sana ne amma da tadago akan ta zuwa saman benan ae kuwa tashiga rudani, tana ihu tana kiran Sana Sana kire da kyau gani zuwa taimakon ki, saikace zata iya, dan Allah kutaima keta yar uwata ce dan Allah karku bari tafado, ita kadaice yar uwata kuka take sosai, mutani suncika agun sosai ankewaye gun baki daya, Suha ganin babu wanda zai taimaka ma yar uwan ta, gashi kuma Sana sai kuka take hannayen ta da tarike wannan abun da shine kawai maka manta yayi jaa ida nuwanta duk sunyi jaa gashin kanta duk yabazu afuskan ta, Suha yanke shawara tayi tace tacice yar uwan ta, ae kuwa nufanta tayi tana kuka kamar mahaukaciya, mutani suka ankara da ita ae kuwa suka rireke ta, kusake ni kusakeni yar uwatace fa kubarini intaima keta idan ma mutu zamuyi babu ruwan ku, haka kawai Suha take fada, Allah sarki abun tausayi, mutani kuma sai kallon Sana da gabaki daya ta
tafita cikin haiyacin ta,
Adai-dai wannan lokacin kuma moton Siddarth da Raj ta kunno kai, Raj yace maiyake faruwa nan ciki dan mamaki yafo daga cikin moton dan ganin abunda yake faruwa, kallon abunda yake faru cikin mamaki, Siddarth ya daura idanuwan sa akan Sana da gaba ki daya numfashin ta yana dafda daukewa, numshe idanuwan sa yayi yakadaura idanuwan sa akan ta, Sana tana ta sumbatu, Suha kice mom tayafeni nikam nawa yakare, zufa duk ya rufeta ko ina zufa ajikin ta gabaki daya tafita cikin haiyacin ta, murmushin gefen baki yayi, yana numshe idanuwan sa azuciyaya tace sarki numshe idanuwa, Raj yace Allah sarki ina mazan iya ceton ki danayi, Siddarth kafafun sa yasa awaje yafoto daga cikin moton kai tsaye bai tsaya sauraran magana da Raj yake masaba yanufa wannan benan domin ceton wannan yarinya da baisan taba,
Gudu sosai yake kamar ya ara kafa kamar wanda ya ara kafa, gashi manya kayane ajikin sa, yana isa benan yafara kokarin hawa yadda Sana take ae kuwa idanuwan mutane suka dawo kan sa dan babu wanda ya ankara dashi sai ganin sa sukayi asaman benan kawai,
Yana isa gare ta, yana kama wannan abunda yake kama da fankan wanda shine yasa Sana bata fadi ba ita kuma Sana tana sakewa sbd hannaye ta sunyi jaa kuma sunyi tsami tayi kokarma harta kai wannan lokacin,
Ae kuwa yarike ta da dayan hanun sa yayin da dayan ahanun yana rike da wannan abun mai kama da fanka, alokacin da Sana tasake wannan abun ae kuwa Suha tasaka ihu dan tagama sadakarwa yar uwan ta tarasa ta baki daya dan idan mutum yafado dakan wannan benan tabbas bazai yi raiba idan yayi rai to bazai iya tabuka komai ba,
Siddarth rike Sana da hanu daya yayi yayinda wannan hanun sa yana kan wannan abun, sosai yarike ta , soyake yadawo da ita kirjin sa ae kuwa yadawo da ita hannayen ta yasaka abayan wuyan sa, ita kuma alokacin ta sumee sosai ya rike wannan abun da hanu daya dayan hanun kuma yarumgumo ta dashi,.........
Sosai ya rumgumo ta akirjin sa yana rike da wannan abun dashine yarike so dukan su sosai yarike abun kuma yana rumgume da Sana
Raj idanuwa yazubawa Siddarth sbd wannan yana rayawa azuciyar sa shin Siddarth ne da gaske ko a'a Siddarth din da baya son yarike hanun mace bare kuma ya rumgumo ta akirjin sa Siddarth din da adini yagama bin jikin sa Siddarth da babu ruwan sa da ko wata mace wannan dai Siddarth din shine dai wannan yau rumgume da mace,