Complete Hausa Novels

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Nakasa_Ba_Kasawa_Bace_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 4 of 27

*PAGE 4*

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Free page

*Wannan page É—in kuma nakunw Æ´an Hukuncin Allah fans two, ina al'fahari daku,*

*Ga masu son saya turo katin Mtn na 300 ta nan 09097853276 ko ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa*

Yaji An d'an matso kusa dashi har jikin wanda ya matso kusa da shid'in na gogan nashi jikin hakan ya sashi juyowa a hankali ya d'an kalli matashin da bazai zarta sa'anshi ba,
ganin d'an saurayin yana murmushi ya sashi d'an murmusawa,
shi kuwa saurayin cikin fara'a ya mik'a mishi hannu ganin haka shima Saifuddeen ya bashi hannu, fuska cike da fara matashin ya fara mgna cikin bagwariyar larabcin, dan a zatonsa Saifuddeen balarabene,
sosai Saifuddeen ya zuba mishi ido tare da mmki dan ya gane zaton saurayin, haka yasashi k'ara tsurawa bakin matashin ido lokacin daya kuma ci gaba da mgna cikin larabcin shuwa'arab yace.
"Barka da zuwa, shigo daga ciki, me kake so?."
kai kawai Saifuddeen yake jujjuya mishi alamun a a ba abinda zai saya,
shi kuwa saurayin murmishi ya kumayi dan a zatonsa Saifuddeen baya gane irin nashi larabcin ne haka ya sashi juya harshe eh zuwa hausa yece.
"Kai wannan balarabe ba dai kyauba Masha Allah, ko me kakeso ne oho."
wani dake cikin shagon ne yace.
"Jabeer wai me yake sone, jiya mafa na ganshi a bakin shagon Alhaj ishaq."
murmushi wanda aka kira da Jabeer yayi kana yace.
"Ai bai gane larabcina."
cikin zuba mishi ido wancan din yace.
"To yaje gaba wala Allah a samu mai iya mishi irin yarenshi."
daga nan ya juya yaci gaba da sabgogin jera kayayyakin.
Shi kuwa Saifuddeen gane abinda suka cene ya sashi juyawa ya ci gaba da tafiya.
daga nan yayi ta bulayi har azahar koda yaga ana al'wala shima ya zaro goma ya sai pure water yayi al'wala kana ya nufi inda ya hango ana jam'i yana zuwa ana tada ik'a.
Bayan an idar da salla ya d'an jima a zaune yana addu'oi saida yaga an fara nannad'e taburman sai ya mik'e yaci gaba da yawatawa.
kanshi ya kule ya rasa ya zaiyi dan sam cikin kasuwar babu mai kula kowa kowa sabgar gabanshi keyi, kana duk bakin shagon da yaje ya tsaya sai ai ta mishi gwarancin larabci, duk da yana ganewa to amman dame zai basu amsa tunda shi kurmane,
haka yasa ake zaton bai gane larabcin ne tunda yawanci yan koyone ke gwada iyawarsu.
jin ya gaji da yawone yasashi shiga layin masu kayan kitchen nan ya samu inuwa dai dai bakin wani babban shago ya tsaya bencin dake gefe yaja ya zauna,
yana kallon yadda ma'aikatan keta cinikaiya da masu sayyya kasan cewar ramadan ya kusa baifi wata biyu ya rageba shiyasa kasuwan masu kayan kitchen ke gudu,
sabida mata kan sabunta ababen aiki dan samun yalwatuwarsu.
d'aya daga cikin yaran shagon ne ya kalleshi da kyau kana yace.
"Mai gida Allah yasa dai kana jin hausa?."
da sauri ya gyad'a mishi kai alamar. "Eh inaji."
shi kuwa murmushi yayi sannan yace.
"To me kakeso?." da sauri ya jujjuya mishi kai alamar.
"Ba abinda nakeso."
gane abinda yake nufi yasa yaron shagon yace.
"Hutawa kakeyi kenan?." still kai ya gyad'a mishi alamar eh.
ganin kamar baison mgnane yasa yaron ya shareshi yaci gaba da sabgoginshi.
Shiko Saifuddeen gyara zamanshi yayi tare jingina da jikin k'ofar shagon.
mata nata shiga da fita,
sai ya kuma tsargu ganin yadda aketa kallonshi,
har ya mik'e zai tafi sai ya kuma tsayawa ganin wani kekyawan Dottijo fari k'al dashi dake bisa keke bayan keken wani k'aton kwaline dake cike da lododi manya-manya irin k'atti sosai d'innan wanda in kayi sayayya mai yawa ake saka maka kayanka ciki,
sai kuma tsaka-tsakiya sai yan saffa-saffa sai k'anana kana sai masu layi-layin nan sai kuma k'ananu irin mai gida ya kasa d'inna.
hannu ya mik'a ganin wannan kekyawan dottijon yana mik'o mishi kullunan lododin yana ce mishi.
"Tai maka min mana yarona mik'a musu lododin,
ka amso min kud'in na jiya, ba sai na sauk'a bisa motar tawa ba".
ya k'arishe mgnar cikin fara'a,
shima murmushi yayi kana ya amshi ledodin ya juya cikin shagon inda yagga babban ogansu ya zaro kud'i ya irga gudan dubu guda uku kana da d'ari biyar,
yana mik'owa Saifuddeen d'in yana kuma kallon Dottijon tare da cewa.
"Barka da yamma baba Bello, kaga ko kamar kasan lododinmu sun k'are."
cikin sakin fuska dottijon yace.
"Kace nazo a dai-dai kenan?."
shiko mai shagon bayan ya karb'i lododin da Saifuddeen yake mik'o mishi sai ya kuma kalleshi kana ya kalli Dottijon tare da cewa.
"Kai Baba yau kam inaga a bamu na dubu biyar,
sabida kar muzo gobe bakazo da wuriba su gaza mana."
da sauri tsohon yace.
"To ba matsala."
bayan ya amshi kud'in da Saifuddeen yake mik'o mishi ne sai ya kuma bashi wasu banduran lododin,
da sauri ya amsa kana ya bawa mai shagon.
ganin alamun bakin mai shagon yana cewa.
"To Baba bello Allah bada kasuwa sai gobe kuma."
da sauri ya juya, ganin Dottijon na ce mishi.
"Ngd ko d'an saurayi."
kai ya gyad'a mishi tare da zura mushi ido ganin yaja keke nai ya tafi.

A hankali ya juya yaci gaba da tafiya bai jima da fara bulayinba yaga anata shirin Sallan la'asar daga nan shima yayi harama.
Bayan an idarne ya koma layin masu robobi nan yayi ta yawatawa,
hardai aka kira magrib ganin anata rurrufe shaguna ya sashi fitowa, inda yayi sallan magrib jiya anan yauma yayi salla yana dawowa kuma ya samu Salisu ya iso.

Daga nan bakin kasuwan bakin General hospital sukana nufa,
inda daga bakin titin ta d'aya gefen akwai wata mai saida abinci sanin tanada tsabta ne yasa Salisu kawosu nan,
amman Saifuddeen k'in ci yayi,
sai dai Salisu yaci kana ya nuna mishi wani shagon fura da nono,
gane yana sone yasa Salisu shiga ya seyo mishi k'aramar roba saida yasha sukayi sallan isha kafin suka d'auki hanyar dukku.

Bayan sun isa shi Salisu yayi gidansu da machine d'in shi kuwa, Saifuddeen kai tsaye cikin gida ya nufa a tsakar gida ya samesu zaune,
gefen Umminshi ya zauna kasan cewar akwai wuta duk suna ganin juna,
da sauri Rahma ta kawo mishi abinci kana ta kunce bakin zaninta ta kunto 50 sannan ta kalli Hayatuddeen dake tsaye alamar zai fita ganin Saifuddeen dinne ya hanashi fita,
hamtsin d'in ta mik'a mishi tare da cewa.
"Ingo jeka gidansu Ya Adnan ka seyo mishi ruwan sanyi."
da sauri ya amsa tare ficewa.
Ummi kuwa cikin kula tace.
"Ya kasuwa?."
kai ya jinjina mata cikin son boye yanayin da yake wuni a cikin kasuwar.
Rahma kuwa ido ta zuba mishi tare da cewa.
"Saifuddeen gobema zakaje ne?."
da sauri ya gyad'a mata kai dan baya son su karaya.
Raihana kuwa cikin karya wuya tace.
"Hamma Saif me kake sayarwa ne to?."
ido ya zuba mata cikin rashin son yi musu k'arya ya girgiza mata kai alamar babu
da sauri Raliyya tace.
"To me kakeyi?."
sai ya kuma juyo ya kalli Ummi ba tare daya amsawa Raliyya ba,
cikin sanyi take ce mishi.
"To Babana me amfanin zuwan, kalli jiya da yau duk baka wuni damu ka tafi har Gombe kuma kaje ba wani abu kakeyi ba ai gwara ka hak'ura ko?."
murmushin k'arfin hali yayi kana ya fara rubutu a k'asa.
"Ummi wai har kin karaya ne? To ki aro jarumta ki yafa ai komai a hankali yake zuwa,
ai mai nema baya fushi, yoh su masu shagunan da kansu wata rana zasu bud'e ko asi basuyiba kuma haka bazaisa gobe su k'i zuwaba, kedai kiyi ta min addu'a in sha Allah, Allah bazai hanani abin yiba."
sai ya kuma kalli Rahma dasu Raihana yace.
"kuyi tamin addu'a in sha Allah dukkan tsanani tare yake da sauk'i."
cikin samun k'warin guiwa, sukayi mishi addu'a.

Bayan yaga sun saki Randi sunata hirane sai ya mik'e yad'auki bokiti ya debi ruwa a randa kana shiga d'anshi wanda da shida Nuruddeen ne,
farar jallabiyarshi ya d'auka da boxer inshi kana ya fito hannunshi rik'e da kondon wonkanshi ban d'aki ya nufa yaje ya shiga wonka.
Ya jima kafin ya fito daga cikin d'an madaidacin bayan gidan nasu da aka lailayeshi da fulo d'in siminti,
shaddan na can gefe kana wurin wonkan anyishi da mazaunin siminti da kuma inda zaka ajiye sawunka.

A hankali yake tafi bisa dukkan alamu baison kasa ya bud'e mishi sawune,
d'akin nashi ya shiga,
inda yake gyare tsab sai k'amshin turare yakeyi wanda ishaq ne ke saya musu tare,
ko ina a kimtse kodan babu tarkece sosaine,
leda carpet ne a malale a tsakiyar d'akin wanda sai Shek'i yakeyi alamun ya wadatu da tsabta sai katifarshi shimfid'e a gefe wanda yasha gyara sai pillows biyu a
gefen katifar.
can daga k'asa kuma wata yar madaidaciyar durowa ce,
inda gefe d'aya ya jera kayayyakinshi dake wonke a goge, sai d'aya side in kuma littafanshi ne a jere daga sama har k'asa kama dana boko na islamiya dana allonsu wanda wasu tun na kakansu ne, sai wani dogon madubi dake lik'e a jikin ginin daga sama har zuwa k'asa dan zaka iya kallon tsawonka duk ta cikin madubin
sai wani dan abun aje takalma kana sai fankar k'asa da kuma wani d'an k'aramin randar tabo da sai naso yakeyi alamun ruwan ciki da sanyi
sai butarshi a gefe kana can gefen durowar kuma sallayanshi ne ke shimfid'e.
Mai ya shafa sannan ya fito tsakar gidan tuni Hayatuddeen ya dawo har yayi bacci hakama su Faruq.

Gefen Umminshi ya zauna tare da tonk'oshe sawunshi abincin da Rahma ta ajiye mishi ya jawo,
bud'ewa yayi sai ya kuma yi murmushi ganin tuk'ek'k'en tuwan shinkafa da miyar busasshen zogale wanda yasha kifi, gyada, attaruhu, da albasa, wanda aka had'esu da kifi,
kana ga wake dasu kayan d'and'ano
miyar sai k'amshi take, Allah ya sani Saifuddeen nason miyar zogale shiyasa Umminshi ke yawan yin miyar in dai tanada halin yinta da yake miyar tanada cin kud'i.
ledan ruwa d'aya ya d'auka tare da b'ulawa kana ya wonke hannunshi ya fara ci,
ita kuwa Ummi ido ta zuba mishi tare da cewa.
"Yayanka Adnan yazo ya sallameni d'azu wai zai tafi karatu har Zaria."
kanshi ya d'an jinjina alamar Ayyah,
sai ya kuma yi mata alamun Allah ya kaishi lfy.
Amin Amin tace,
bayan ya d'an ci abincin ne ya wonke hannunshi Raihana ta kwashe kwanukan kana ta dawo sukaci gaba da hira.
Suna nan a zaune Bappa Ali da Aunty Nina ma suka shigo yi mishi barka da dawowa nan sukayi ta hira.

Washe gari da sassafe Rahma ta hura wuta tayi d'umame kamar yadda suka saba,
da sauri ta d'auko pillet ganin Saifuddeen ya fito cikin shirin tafiya,
yau k'ananun kaya yasa wanda sukayi masifar yi mishi kyau blue Jeans ne a jikinshi sai bak'ar riga mai farin rubutu a jiki,
kanshi ba hula hakan ba k'aramin haskashi yayiba,
yana shiga d'akin Umminsu tana binshi a baya,
bisa kujerarta irin zauna kaci doya nan ne ya zauna,
ita kuwa Rahma mik'o mishi fillet d'in tayi kana ta jawo kolban man shanun da suke sawa in sunyi d'umame,
bud'ewa tayi tare da tsiyaya mishi kana ta mik'e ta koma kitchen robar dakekken yajin borkono ta d'auko sannan ta dawo barbad'a mishi tayi,
sannan ta d'auki kofi ta nufi d'akinshi ruwa ta d'ebo mishi a wannan randar tashi,
sannan ta kawo mishi tare da cewa.
"Kaci kafin ku tafi."
kai ya gyad'a mata kana ya kalli Umminshi dake shirya Hayatuddeen yanata zumbura baki, murmushi yayi tare da jawo hannun Hayatuddeen yana mishi tambaya irin tasu ta kurame ya tambayeshi me ya sashi fushin.
Bakin ya kuma turawa kana ya rab'a jikin Saifyddeen d'in tare da cewa.
"Hamma Saif ba Adda Rahma bace tayi d'umame kua tasan ni bana cin d'umame hakama Faruq da Adda Raliyya."
murmushi yayi kana ya jawoshi ya ajiyeshi gefenshi,
a hankali yasa cokalin da Rahma ta mik'i mishi ya gutsuri gayan kana ya dandalo miyar da taketa k'amshin man shanu,
bakin Hayatuddeen ya kai,
tura baki yayi tare kwabe fuska kana yace.
"Na k'os. "
bai k'arisa mgnar tashiba yayi shiru,
jin ya sa mishi loman a bakinshi, lumshe ido yayi tare da fara sarrafa abincin,
saida ya had'iye kana ya bud'e idanunshi tare da cewa.
"Dad'i wlh miyar tayi dad'i Faruq zo kaci."
Ummi kam da Raihana dake shirya Faruq tuni dariya sukeyi, shima Saifuddeen dariya yakeyi har saida dimples nashi suka lotse sosai kana fararen hak'oranshi suka baiyana manyan idanunshi ya lumshe tare daci gaba da basu abincin a baki,
aifa sukaci sukayi nak, sannan suka tafi makaranta,
ita kuwa Raihana da sauri ta fita tace.
"Adda Rahma ki samishi wani abincin su Faruq sun cinye wannan,
harda santinsu."
dariya sukayi kana Rahma ta samishi wani yana cikin cine Salisu ya shigo nan sukaci tare kafin suka fita suka tafi.

Yauma kamar kullum Saifuddeen wuni yayi yana yawo da bulayi a kasuwa,
sai da magrib tayi ya fito, kana yayi salla kafin Salisu yazo ya d'aukeshi yau ma fura da nono yasha da zasu tafi.

Haka dai Saifuddeen yayi ta fama yawo da wahala a cikin kasuwar Gombe har tsawon kwana bakwai,
to a ranan ne kuma Salisu ya basu balance ensu kamar yadda sukayi duk sati zaike basu dubu biyar.

Koda ya karbi kud'in Bappa Ali ya kaiwa su,
shi kuwa Bappa Ali k'in amsarsu yayi yace ya kaiwa Ummi kud'in zasu samu abinda zasuke sarrafa cefenen abincin.
da yake har yanzu sunada sauran abincin da baban Arabi ya kawo musu.

Shi kuwa Saifuddeen sai ya zare dubu biyu ya bawa bappan nashi, amman sam yak'i karb'a acewarsa ai da yanada hali shine ya kamata ya basu,
to dai ganin Saifuddeen ya b'ata rai ya sashi amsar 1k yasanya al'barka.
Shiko yaje ya bawa Ummi dubu uku sannan ya d'auki dubu d'aya.
Ummi kam sai sanya mishi al'barka takeyi.

Washe gari kamar kullum suka shirya suka tafi cikin. Gombe a inda ya saba sauk'eshi yau ma nan ya sauk'eshin, bayan Salisun ya tafi shi kuma Saifuddeen sai ya d'anyi tattaki zuwa bakin mashigar kasuwar, addu'a yayi kamar kullum kana ya shiga da k'afar dama,
yauma bakin shagunan yayi tabi har kusa k'arfe shad'aya lokacin rana ta tsala zafi ya fara,
sai ya nufi layin masu robobi,
yana zuwa shagon wani bayerbe sai ya tsaya,
bokatin kand'e tsirara ya saya wanda wasu ke cemai ganta sarai,
bayan sun gama ciniki cikin mgnar kurame ya bashi dubu d'ayannan,
kana bayerben ya bashi canjinshi,
daga nan ya nufi wani layin tafiya kad'an yayi sai gashi a wani babban shago da yake cike da d'ima-d'ima firiji masu tsawo da masu fad'i.

Yana zuwa d'aya daga cikin yaran shagon yace mishi. "Kana son ruwane?."
da sauri ya gyad'a mishi alamar eh.
shi kuwa yaro bud'e wani k'aton firiji yayi kana ya juyo ya kalleshi, sannan yace.
"Leda nawa kake so?."
hannunshi ya d'ago kana ya had'a yatsunshi biyu yayi mishi alama da leda biyu yakeso.
cikin mmki yaro ya kalleshi kana ya kawo mishi leda biyun sannan yace mushi.
"Kai kurmane?."
murmushi Saifuddeen yayi kana ya gyad'a mishi kai tare da mik'a mishi d'ari biyun,
amsa yayi tare da bashi canjinshi kana yace.
"Kuma naga kamar kana gane abinda nake fad'i ko?."
still kai ya gyad'a tare dasa lododin ruwan cikin bokatin daya saya d'in,
a take botikin yayi sanyi sabida ruwan yanada tsananin sanyi wasu har sun fara yin k'ank'ara,
shi kuwa yaron shagon ashirin ya kuma zarowa a al'jihunshi kana ya mik'a mishi tare da cewa.
"Gashi nayi maka ragin naira 10 cikin ko wanne leda akan yadda muke sararwa Allah ya baka sa'a inka k'arema kazo zan ajiye maka mai sanyi."
cikin murmushi Saifuddeen ya jujjuya mishi kai alamun baya son ragin, kana ya juya ya nuna mishi sauran yaran ya mishi alamun da sai dai in suma duk za'ayi musu ragin,
cikin sauk'e numfashi yaro yace.
"To sadaka na baka."
fuska ya had'e kana ya tsuguna gefe tare da rubuta mishi.
"Bara nazo makane da zakace sadaka ka bani? in sadaka kakeson badawa kaje gidan marayu da gajiyayyu, ni karka kashe min zuciya,
ka dai ajemin mai sanyi in wannan ya k'are zan kuma zuwa."
hannu yaron ya bashi sukayi musabaha lokacin daya karanta rubutun kana yace.
"To kayi hak'uri abokina sai ka dawo d'in."
kai ya jinjina kana ya juya hannunshi rik'e da botikin.
ya fara bin layi-layi yana yawo,
amman babu wanda yace mishi kawo,
har ruwan ya fara rage sanyi.
cikin gajiya ya dawo bakin shagon masu kayan kitchen inda ya huta jiyan nan, inda ya zauna jiyan yauma nan ya zauna ya tasa batikin a gabanshi.
yaron jiyan ne ya kula dashi cikin fara'a yace.
"Balarabe yauma ka zone?."
cikin gajiya ya lumshe mishi idanu alamar eh,
shi kuwa yaron shagon cikin karantar yanayinshi yace.
"To yau ma hutawa kazo yine ko zaka sayi abune?."
da ido ya nuna mishi botikin pure water enshin,
cikin sauri ya zaro ido tare da cewa.
"Wai kai dama tallan ruwa kakeyi ne?".
Kai ya gyad'a mishi tare gyara zamanshi,
cikin sanyi yace.
"To wai kai kurmane naga jiyama har ka tafi body language kakeyi min."
still sai ya d'aga mishi gira duka biyu alamun eh shi kurmane.
da sauri yaron ya kalli alajin shagon cikin tausayawa yace.
"Abba kalli wai wannan Balaraben kurmane kuma wai ruwa yake saidawa."
sai ya kuma kalli Saifuddeen tare da yin rau-rau kamar idanunshi zasu zubda hawaye,
ganin haka da sauri Saifuddeen ya jujjuya mishi kai sannan yasa hannunshi bisa idanunshi alamun kar yayi kuka.
still shima wanda ya kira da Abba sai ya zuba musu ido tare da cewa.
"To Hisham kafi ubangijin daya halicceshi a haka sonshi ne?
kada kayi kuka kasa mishi rauni,
ai ita Nakasa ba kasawa bace,
bare wannan mai nagartane Kaga dai jiya kun dad'e tare amman duk bamu gane kurma bane kuma kaga yana gane duk abinda muke cewa.
So shi bai sa nakasar jikinsa ta zamar mishi na zuciya ba."
Jin haka sai Hisham ya sharshe hawayenshi kana yayi murmushi tare da bawa Saifuddeen hannu yace.
"Daga yau kai aboki nane."
shima Saifuddeen murmushi yayi,
shi kuwa Alhaji Ibrahim al'barka ya samusu.
Sai ya kuma kalli costumers insu da suke cike da shagon inda d'aya daga cikinsu ta kalli botikin ruwa tare da cewa.
"Yauwa mai ruwa bani biyu, wlh tun d'azu nakeji k'ishin kamar zai karni."
gane abinda tace yasa Saifuddeen d'auko guda biyu ya mik'a mata,
amsa tayi tare da bashi ashirin d'in,
shi kuwa Alhaji Ibrahim cikin iya kula da bak'inshi yace.
"A a Hajia bar kud'in."
sai ya kuma kalli Saifudddeen tare da cewa.
"Basu ruwan kowa ya d'auki yadda zai isheshi."
ai nan matan nan kowa ta d'auka wasu bibbiyu wasu d'addaya wasuma cikin hand bags nasu suke ajiye ruwan,
tuni sun d'auke yafi rabi.
lissafi akayi don lokacin ne forko-forkon da pure water ya tashi daga d'aya biyar ya koma d'aya goma,
to nanfa had'a lissafi inda kud'inshi ya kama d'ari da hamtsin.
aifa sai yaji k'arfin guiwa ya mik'e yabi layin masu saida gonjo wanda kusan a rana suke,
cikin k'udurar ubangiji ya saida ruwan tsab,
ba tare da yin k'asa a guiwaba yaje ya kuma saro leda biyu,
nan sai ya fito bakin kasuwa nanfa 'yan acab'a suka rink'a saya wani a take yake shanye leda biyu wani har leda uku ya saya bar masu sayan d'ad'd'aya,
kana masu taxi ma wasu sai su sayi lada hud'u su aje cikin yar durowar motar nasu.
Cikin awa d'aya wannan leda biyun suka k'are,
ai da sauri ya kuma komawa ganin azahar tayi sai ya amso leda d'aya,
kafin kace kobo ya k'are dan masuyin Al'walene sukayi ta kiranshi suna saya,
ganin saura d'aya sai yayi Al'wala dashi ganin a layin shagonsu Jabeer yake sai yaje ya ajiye botikin a barandar shagunsun gefen gadajen jarirai,
sahun salla ya shiga,
bayan an idarne ya yi addu'o'inshi sannan yaje d'aukan botikin nashi, Jabeer na ganinshi yace.
"Aboki balarabe dama har yanzu kana k'asar tamu ne?."
hararan wasa Saifuddeen ya cilla mishi dan ya gaya mishi shi bafullatanine ba balarabeba, so da yake Jabeer yanada far-far da jama da wasa da dariya sai yace shi dai yasan sai in satoshi akayi daga saudia.
botikin ya d'auka kana ya d'an harari Jabeer tare da tsuke fuska irin na abokai sannan ya bashi hannu.
da sauri Jabeer ya kamo hannunshi tare da cewa.
"Yoh ai dole ma in baka hannu ko zan samu ka rab'a min farinka da laushin hannunka."
dariya yaran shagon sukayi baki d'aya,
kana sai ogansun yace.
"Gashi dai duk muna inuwa fanka na kad'awa muci abinda mukeso, shi kuma gararamba kawai yake a kasuwa amman in ka ganshi sai kace daga fadar masarautar saudia ya fito."
cikin had'e fuska Saifuddeen ya zaro biron dake aljihun rigar Jabeer kana ya fara rubutu a tafin hannunshi yana gamawa ya nunawa ogan nasu tafin hannun nashi,
kusan a tare suka lek'o da idanunsu bisa tafin hannunshi cikin mmki suke karanta rubutun da yayi da fillanci.
"Oga ba gararamba nakeyiba fa inada sa'a ta nima ba yawon banza nake a kasuwarba pure water nike saidawa."
cikin mmki suka kalli juna tare da had'a baki wurin cewa.
"Ikon Allah kunga wlh da gaskene fa bafillacene."
shi kuwa ogan nasu murmushi yayi tare da cewa.
"Eh gskyarka ba gararamba kakeyiba ai shi mai sana'a ba matsiyaci ba,
yanzu je ka kawo mana ruwan dan yanzu zamuci abinci."
aifa da jin haka ya juya ya fita su kuwa sai Al'ajabi sukeyi,
yanzu dai sun tabbatar shi kurmane kuma bafillatanine kana yana gane abinda ake fad'i in yana ganin bakin mutun.

Leda biyu ya kuma sarowa cikin sa'a kafinma ya isa wurinsu rabin ledane ya rage,
nan suka d'auka to ganin bai ishesu bane sai ya kuma komawa ya dauko leda biyu.
kai tsaye wurinsu ya nufa
nan suka k'ara guda uku.
sun bashi kud'inshi ya juya zai tafi kenan sai yaga wannan dottijon mai keke wanda suka tab'a had'u a shagonsu Hisham kusan tsawon sati d'aya daya gabata kenan,
still yauma kamar ranar dottijon ya kalleshi tare da mik'o mishi banduran leda guda hud'u irin kitika-kitikan ledojin da in an sayi koda katifan jarirai zai iya shiga ciki kai hatta gadon jariran zai iya shiga cikin ledan,
kana in zaka sai setin kayan sanyi dana abin goyo dasu rigunan yara dasu setin mayukansu da takalma duk leda d'aya zata iya d'aukansu dan irin manyan ledodi bak'ak'ennan ne,
sai kuma masu binsu sai masu zane bak'i da yellow nan,
cikin alamun gajiya dottijon yace.
"Yauwa yarona dan Allah mik'a musu."
da sauri ya ajiye botikin nashi kana ya amshi ledodin ya juya ya mik'awa Jabeer dake kusa dashi,
sai kuma ya kalli ogan nasu ganin yanayiwa dottijon mgna.
"Yauwa Baba bello ya a bamu ledodin na dubu hud'u dan na dubu ukun basa isanmu sabida yanzu iyayen yara sun fara sayayyan kayan sallan yaransu ga masu haihuwa nan nata zuwa ga yan mata da samari masu sayan kayan aure."
murmushi dottijon yayi kana yace.
"Masha Allah ai haka mukeso domin cini kinku shine namu,
domin sai kunyi ciniki da muyi tunda mu duk kasuwa abin mune k'arshen saya dole sai an gama sayyaya ake tuna sayan leda."
Jabber ne ya murmusa tare da cewa.
"Gashi kuma kasuwar taku da yawan al'barka take duk mai saida abu dole sai ya sai naku."
murmushi sukayi baki d'aya kana Alhaji Adamu ya mik'owa Saifuddeen 4k d'in sannan shi kuma ya mik'awa dottijon amsa yayi tare da sasu a aljihu sannan ya kalli Saifuddeen da kyau kana yace.
"Ngd matuk'a yarona Allah ya maka al'barka."
Amin Amin duk suka amsa harda Saifuddeen daya amsa a zuciya,
Jabeer kuwa cikin tsokana yace.
"Kai Baba bello wannan fa balarabene."
ba tare da mmkiba Dottijon yace.
"Yoh ai ba musu in akace hakanma."
Tahir ne dake gefe ya d'an bugi k'eyan Jabeer kana ya kalli Dottijon yace.
"K'aryafa yakeyi maka baba bello shi ba fulatanine kawai dai kurmane."
da sauri Baba bello ya kuma kallonsa cikin tausayawa yace.
"Allah sarki bawan Allah dama ance ko wani d'an adam tara yake bai cika gomba, wato kai kuma nan tawayar ka take."
sai ya kuma kalli Saifuddeen da kyau sai ya sauk'o bisa keken nashi.
hannunshi yasa ya jawo wuyan Saifuddeen yadda zai iya ganin tsakiyar kanshi ido ya zura mishi tsawon 38 minutes shi kuwa Saifuddeen shiru kawai yayi ya bashi kai d'in,
bayan ya gama dubawa yace.
"Masha Allah lallai kam wannan kan naka zai d'auki nauyin abu da yawa,
domin magergerar gashi tushe ukune a kanka wanda ba kowa Allah ke yiwa wannan halittarba."
shiru sukayi yayinda shi kuwa Dottijon ya kalli Alhaji Adamu tare da hawa kekenshi kana yace.
"Akwai al'khairi cikin yin mak'otaka dashi."
daga nan yaja kekenshi ya tafi,
shi kuwa Saifuddeen d'aukan botikinshi yayi tare da bin bayanshi,
yana ganinshi ya nufi shagon masu d'inka hijabannan da alamun suma a wurinshi suke sayan leda. Har zaibi bayanshi sai kuma yaga ana kiranshi a shagon alhaji ishaq haka yasa ya nufi can.
Pure water suka sassaya bayan sun bashi kud'in ya juyo kenan sai yaga Dottijon nan tuni ya bar wurin,
to sai kawai yaci ga da zageye da ruwan,
amman sai cinikin yayi d'ib tun bayan azahar ya d'aukosu amman har la'asar basu k'areba,
to saida aka kira sallan la'asarne sai kuma akayi ta saya ana al'wala nan ya samu wannan leda biyun suka k'are.
To koda aka idar da salla ya gaji sai ya koma layin shagon ba mishkila ya zauna ya zuba musu idanu yana ganin yadda aketa seye da sayarwa yana kallon yadda suke ink'anta awunsu.
Ya d'an jima a wurin sai biyar dai-dai ya mik'e a ranshi yake cewa.
"Uhmm Saif tashi kaje ko leda d'aya ka samu ka saida kafin magrib ai yafi zaman mutuwar jiki da zuciyan."
daga nan yaje ya k'aro leda d'aya,
to kuma lokacin rana tayi sanyi ba ciniki sosai,
ya jima yana yawo kafin ya samu aka sayi gwara shida na arba'in kenan daga nan yaita zagayawa,
tuni ya gaji dan yau kusan wuni yayi bisa sawunshi,
saida magrib ta gabatone akayi ta saya nan ya saida kab sai gwara d'aya da ya bari na al'walanshi. Bayan yayi alwalan ne ya bawa Jabeer botikin ya ajiye mishi a shagonsu,
sannan ya fito bakin gate d'in fita kasuwar yana lissafin bag nawa ya saida a cikin ranshi yace.
"Alhamdulillahi leda goma cib na saida, ya rabbil izzati kayiwa wannan kasuwa tawa al'barka ya Allah ka jib'anci lamurana ka fad'ad'amin hanyar samu in samu damar tallafawa k'annena marayuwa da mahaifiyata da yayata da marayun yaranta,
bayan anyi sallan magrib d'inne ya dawo inda Salisu zaizo ya sameshi yana ko zuwa Salisu na isa,
yauma kamar jiya shi dai fura da nono yasha shi kuwa Salisu ya sai nama yaci.
daga nan sukayi sallan isha kafin suka kama hanyar Dukku.

Bayan sun isa wonka yayi ya canza kaya kana yazo yaci abinci,
sannan ya fita woje sugar ya seyo da madara da Lipton sai biredi d'aya.
kafin ya dawo duk sunyi bacci sai Ummi da Rahma.
Rahma ya mik'awa ledan kana ya zauna gefen Ummi data zuba mishi ido,
cikin kula tace.
"To kuma d'an dubu d'aya daka amsa d'inne zaka kasheshi a kanmu? buk'atunka zakayi dashi ba namuba ai dubu ukun nan zasuyi min sati ina cefene kullum d'aribiyar zata isheni cefenen dere da rana, tunda munada gari da shinkafa harda sauran taliya da mai da manja."
mik'e sawunshi yayi kana ya fara rubutu a k'asa yana bata lbrin ai ya fara sana'ar saida ruwa kuma Alhamdulillahi sana'ar tana gudu dan ya samu ribar 700 a wunin yau kawai.
Cikin tausayawa Ummi tace.
"To Babana ka dai nuna kai sana'ar tayi maka, amman ni tausayinka nikeji kaje kayita wuni a rana kana yawo da robar ruwa, amman Allah ya baka sa'a yanzu asusu zan saya zaka rink'a tara kudin in ka samu jari dai ka fara wata sana'ar kabar wannan."
cikin girmamawa da shak'uwa da tsantsar biyayya ya gyad'a mata kai tare da fara rubutu a k'asa yace.
"To Ummi na yadda kikeso haka za'ayi."
sai ya kuma kalli Hayatuddeen dake konce yayi pillow da cinyar Ummi ture kanshi yayi kad'an kana ya zame ya konta tare dasa kanshi gefen na Hayatuddeen da nufin wai zasuyi hira.
Amman ina tsananin gajiyar yawon daya wuni yanayi ne yasa tuni yayi bacci.
ganin baccin zai nisane yasa Rahma sa hannu ta d'an mari kumatunshi a hankali ya bud'e ido,
sai ya kuma kalli Ummi dake shafa suman kanshi da alamun bacci a idanunta.
cikin sanyi ya mik'e kana ya musu saida safe sannan ya kamo hannun Hayatuddeen da nufin suje d'akinshi su fara kwana tare amman sai k'ara mak'ale Ummi yakeyi hakan yasa ya barshi, yaje ya shiga kana suma suka shiga.

Still yauma kamar jiya cikin ikon Allah ya saida leda goma kamar jiya.
Koda ya koma ya samu tuni Ummi ta sai asusu ta zura mishi d'aribar din jiya dan ya sai musu kayan tea na d'ari da biredin d'ari kana ya bata sauran d'aribar d'in duk cikin ribarshi 700 d'in jiyan,
kana jarinshi kuma na nan. To Alhamdulillahi yauma haka ya samu kamar na jiya,
toh sai ya bawa Ummi duka kud'in tasa 500 a asusu 200 kuma ta d'auka ta ajiye dan 'yan buk'atunsu irinsu omo ko kud'in break d'insu Hayatuddeen da Faruq
haka dai lokaci yaita shud'ewa.

Duk randa Salisu ya basu kud'in balance kuma zai bawa bappa Ali 1k kana ya damk'awa Ummi 4k d'in.

Alhamdulillahi rayuwafa ta fara juyawa kasuwa na tafiya tuni Saifuddeen ya saba da mutane da dama,
wani lokacin har leda 14 yake saidawa inda yake samun riba kusan 900,
sosai yayi abokai sa'anninshi manyan mutane kuma na son mgnanshi sabida yanada dad'in zama ga tsabta da girmama na gaba dashi.
Abu gaba-gaba yanzu harda robobin Faro, yake sara dasu Fanta, Coca-Cola, molt etc. Wanda yawanci matasa shi kan seya.

Yanzu ya saba da wahalar da yawon da ranar saidai ya d'anyi duhu farinshi ya disashe sabida rana da yake shiga.
Yana yawan had'uwa da Dottijon nan baba bello, mafi akasari shike mik'awa mutane leda su bashi kud'i ya bawa baba bello,
Alhamdulillahi yanzu littafi da biro yake yawo dasu a aljihu duk mgnar da kai mishi zai baka amsa,
wasu da dama dan suga rubutunshi suke son Magna dashi sabida Allah ya mishi baiwar iya rubutu in yayi tamkar na'urace tayi.
da yawa da Balarabe suke kiranshi wasu kuma suce Saifuddeen balarabe.

Azumi nata gaba towa dan yanzu baifi 8 days ya rage Ramadan ba,
Yayinda dukkan Al'ummar musulmai keta shirye-shiryen azumi.
kuma zuwa yanzu kusan tsawon kwana 46 da kafa asusun Saifuddeen.
To ga azumi yana zuwa gaba d'aya ya rasa sana'ar da zai kama dan yasan cikin azumi cinikin ruwa bazaiyi guduba tunda duk musulmai baki a rufe yake.
Yana dai ta nazarin abin yi amman har zuwa azumi saura kwana uku bai tsaida sana'ar da zaiba da fari yayi niyar ko zai koma saida dabino dasu kwakwane sai ya kuma ga sana'ar yawoce kuma ga azumi so yasan zai wahala,
a haka dai yau kam yayi niyar yin shawara da abokinshi Jabeer ko Hisham, duk da yaso ace da is'haq zai shawarar to is'haq kuma yanzu ya fi kwana 36 da tafiya Abuja wurin yayanshi Rabi'u kuma acan zaiyi azumi dan shida Ummarsu ne suka tafi,
dan bayan ya fara zuwa kasuwar da sati d'aya ne yaje gidansu Is'haq sai ya samu ranar sukayi sammakon tafiya Abuja.

Yau tunda yaje yaketa sintirin saida ruwanshi dasu Fantan har sai bayan la'asar ya je shagonsu Hisham da niyan zai tattauna dashi sai ya samu tuni ya tafi gida ya kai cefenen dare.
haka yasa ya wuce shagonsu Jabeer yana zuwa suka zauna dan lokacin mata sun d'an tsagaita,
rubutu yayi na neman shawarar sana'ar da zai fara saida ya gama rubutawa kana ya mik'awa Jabeer takardar dai-dai lokacin daya karb'a dai-dai lokacin kuma baba Bello ya iso wannan dottijon.
karantawa Jabber yayi kana ya kalli Saifuddeen da yake mik'o mishi banduran ledodin daya amsa a hannun Dottijon cikin yanayinshi na wasa da dariya yace.
"Yoh balarabe ga sana'ar da zakayi a hannunka ai kawai ka fara saida leda, gashi dama Baba bello bai saida leda a Ramadan kaga sai ka karb'eshi bayan salla in an dawo sai ka bashi sana'arshi kai ka koma pure waternka ko?."
Ido suka zuba mishi baki d'aya,
shi kuwa ba tare daya bi ta kan kallon da duk suke mishiba ya matso kusa da Dottijon cikin nitsuwa yace.
"Kana ji ko baba Bello shi Balarabe ruwa yake sedawa da kayan zak'i irin namu na yara,
to kuma kaga ga Ramadan yana zuwa to duk abin saidawa in dai na cine cinikinshi ya mutu da rana sai dai in darene,
to kaga ita kuma kasuwa da rana takeci,
shi kuma d'an dukkune kullum zuwa yake da safe bayan sallan isha yake komawa,
toh shine yaketa nazarin wani abu zai fara saidawa cikin azumin,
da yayi zaton zaike saida dabino da kwakwa to gsky itana sana'ar yawace kuma kada yaje garin talla ya tsalli dabino ya afa a baki."
Ya k'arishe mgnar cikin tsokana da wasa,
k'eyarshi Saifuddeen ya bugi tare zare mishi irin yadda akewa yara masu surutu,
dariya sukayi baki d'aya ganin yadda Jabeer ya tura baki tare da cewa.
"To nayi shiru."
shi kuwa ogansu Jabeer gyara zama yayi tare da cewa.
"Baba Bello bananma da wuri zaka shiga itikafin ne?."
cikin kauda zancen Dottijon yace.
"Waya ce da kai itikafi nake shiga,
kawai dai ina ajiye kasuwancin ne da ramadan sabida tsufa yazo kuma azumi na wahaldani."
Murmushi kawai Alhaji Adamu yayi sabida yasa Baba Bello itikafi yake shiga shi kuma yana b'oyewa sabida gudun riya,
shiyasa yake ce musu hutun Ramadan kawai yakeyi.
shiko Dottijon cikin kulla ya kalli Saifuddeen kana murya a tausashe yace.
"Yaro na zaka iya yawon bin shago layi-layi kana raba musu ledodi, suna yi maka biyan bashin daddawan k'auye?."
murmushi yayi tare da gyad'a mishi kai alamar zai iya.
Shiko Dottijon sauk'owa yayi daga kan keken nashi kana ya zauna kusa da Saifuddeen cikin tattausan lafazi yace.
"Kullum in azumi yayi ina barin kasuwa duk costomomina sai dai suyi ta kame-kamen sayan leda wurin wasu,
anayin salla kuma da kwana biyu zan dawo to duk masu kawo musu sai su bari inci gaba da kawo musu kamar kullum to amman tunda gashi bana Allah ya had'ani da kai, in dai ka amince kayi al'k'awarin rik'e amana to zan kaika wurin babban dilanmu da yake bamu talla bisa farashi mai sauk'i,
zaike baka kaya ba tare da ka bashi ko asiba,
sai kai kuma ka tallata ka d'ora ribarka,
misali yau in ka kawo bazasu baka kud'iba sai gobe in ka kawo musu sai su baka kud'in na yau,
na yau kuma sai ka kawo musu na gobe.
to wasu ba ruwansu kana kai musu zasu biyaka,
wasu kuma dole sai goben,
to anan amanar da nakeso ka rik'e zan kaika gaban dilanmu amatsayin kai jikanane dan in baisan wani nakaba bazai bakaba,
in ya amince zai baka kuma zan had'aka da costomomina baki d'aya, nasan duk masu amana da gsky ne, suma kuma zan basu amanarka kada su ganka bakaji su cuceka, nasan zaka iya kasuwancin kam tunda kayi karatu zaku rink'ayin komai a rubuce."
cikin lumshe ido Saifuddeen ya had'e hannunsu wuri d'aya kana ya jinjina mishi sannan ya zaro biro ya fara rubutu a tafin hannunshi saida ya gama kana ya nunawa Jabeer nan Jabeer ya fara karanta abinda ya rubutan.
"In sha Allah Baba bazan kasance mara gsky ba a cikin had'akarmu,
nayi alk'awarin rik'oda gsky da amana bazan kunyataka ba,
ga Oga Adamu da abokina Jabeer da sauran maikatan shagon nan su zama shaida, Allah kuma ya bamu sa'a ngd matuk'a Allah ya k'ara lfy da wadata."
Murmushi sukayi baki d'aya,
daga nan Dottijon nan yayi gaba Saifuddeen na binshi a baya har shagon babban dilansu na leda,
nan ya gabatar dashi ga Alhaji Babayo,
ba wani dogon bincike Alhaji Babayo ya aminta da Saifuddeen sabida ganin Baba Bello ne ya kawoshi Dottijon da sunfi shekaru 20 suna tare a harkar leda.
shi kuwa Baba Bello ya musu bayanin Saifuddeen kurmane amman yana gane duk abinda ake cewa in yana ganin bakin mutun.
an yarda tuni an rattaba sunan Saifuddeen a jerin sunayen masu amsar talla,
yasa hannu shaidu sun saka hannu.
daga nan suka juya Baba Bello ya tasa Saifuddeen a gaba duk inda yasan yana kai ledodi saida ya nuna musu Saifuddeen yana ce musu jikanshi ne, kuma shi zai rink'a kawo musu Leda cikin azumi har sai bayan sallah shi zai dawo,
to dama duk kostomominshi sun san da baya kawo musu leda cikin azumi to sai sukaji dad'in wannan ci gaban koda sukaje shagon Alhaji Ibrahim baban Hisham yaji dad'in abun sosai ya sanya albarka haka dai duk wunin wannan ranar kam sukayi shi ranar bag d'in pure water takwas kawai ya saida sai dai ya saida su Coca-Cola sosai.
Sun bari akan sai ana gobe azumi zai fara tallan ledan tunda ranar Baba Bello zayi zuwan k'arshe sai kuma bayan sallah.

Anayin sallan magrib Salisu yazo ya d'aukeshi kamar kullum,
yau wurin mai shayi sukaje kwai aka soya musu da indomi kana sai ruwan tea,
bayan sunci ne sukayi sallan isha, kana suka kama hanyar Dukku.

Koda suka isa Saifuddeen na sauk'a Salisu ya zaro dubu biyar d'in balance ya mik'ashi,
amsa yayi kana ya zare 2k ya bashi yace yaje ya sayawa Mamanshi sugar da Lipton baiso karb'a amman dole ya amsa,
shi kuwa Saifuddeen yana shiga gida kai tsaye d'akin Umminshi ya shiga inda ya sameta ita da Aunty Nina suna hirarsu.
Bayan sun gaisane ya mik'e tare da yiwa Ummi alamun bari yaje yayi wonka.
To tace mishi kana sukaci gaba da hira,
shi kuwa solle jikinshi yayi suk'al kana ya shafa mai tare da fesa turare,
canza kaya yayi sannan ya nufi tsank'aya wurin Bappa Ali duk da yasan yau al'hamis ne ba karatu so ya kuma san canne wurin zaman Bappa Ali ko yaushe bayan sun gaisane ya mishi bayanin canjin sana'ar da zaiyi da tsarin kasuwancin da dokokinshi,
sosai Bappa Ali ya gamsu da hakan addu'a yayi da fatan al'khairi.
Koda ya tashi tafiya sai ya kwaso cinikinsa na yau duka da riban da jarin duk dubu 3 ne.
sai ya kuma zaro da sauran dubu ukun balance d'in ya had'asu inda suka bashi dubu shida kenan.
Cikin nitsuwa ya mik'awa bappa Ali.
Cikin tsuke fuska da fad'a bappa Ali yace.
"Me zanyi dasu? shin ba nacema Ka dena bani kud'iba in dai ban bakaba to ai baici ka baniba,
fatana Allah ya bud'a maka yadda zakayi kaci gaba da rik'e marayun k'annenka dani bappanku na gaza rik'ewa."
da sauri ya girgiza mishi kai kana ya rubuta mishi.
"Dan Allah Bappa Ali ka amshi kud'innan in dai ba rainawa kayiba, meyasa kullum in na baka abu baka amsa,
to in ban makaba waye zanyiwa kainefa uba a garemu ka sanya al'barka a lamarinmu in bani dashi zan baka ne?."
to ganin ranshi ya b'acine yasa Bappa Alin amsar tare da samishi al'barka.

Har ya tashi sai ya kuma zauna ganin Bappa Alin ya rik'o hannunshi bayan ya zaunane yake shaida mishi wannan mutumin daya kad'e Nuruddeen ya kawo musu kayan azumin.
Kama daga shinkafa, taliya, doya, Couscous, indomi, mai, manja, magi, gishiri, onga, kwai madara da Milo sugar Lipton, da kud'i 10k.
wani irin tsuke fuska Saifuddeen yayi tare had'e rai sai ya kuma yiwa bappa Ali alamun tambayar sun karb'ane?.
kai bappa Ali ya gyad'a mishi alamar eh sun amshi kayan,
cikin takaici ya...

By
*GARKUWAR FULANI*
8/

*NAKASA BA KASAWA BACE*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.