Complete Hausa Novels

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Nakasa_Ba_Kasawa_Bace_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 6 of 27

*PAGE 6*

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

```Hukuncin Allah fans one ku na musamman ne a gareni fatana, Allah ya bar zumunci da ƙauna a tsakaninmu```

_Littafinga na kuɗine nairanki ɗari uku kacal ya biya miki buƙata ,turo katin mtn na 300 ta wannan number 09097853276 ko transfer ta 0005388578 jaiz bank Aisha Garkuwa Aliyu, sai ka/ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276_

free page

Suna isa harabar masallacin suka d'an k'ara sauri sabida tuni liman ya kabbarta.
Bayan anyi salla an idar duk sai kowa ya firfito dan a d'anci wani abu, wasu kuma zafine yasa suka fito sabida babu wuta kuma basu da gen kana in mutun ya wuni da azumi tofa lokacin da kasha ruwa zufa na iya keto maka.

To hakane ta kasance dasu d'in.
da yawa cikin gida suka shisshiga,
haka ma su Saifuddeen da Salisu tare da Mudassir da suka samu a masallacin,
suna shiga Ummi suka gaida kana suka wuce d'akin Saifuddeen inda suna shiga wuta ta dawo,
dan haka cikin farin ciki suka zauna Rahma da kanta ta kawo musu abincin suma tea sukace zasu sha dan haka ta kawo musu kana ta aika musu ruwan sanyi soyayyan doya da kwan sukaci suna korawa da ruwan tea da yaketa k'amshi,
daga nan kuma cikinsu ya cika,
suna cikin hira sukaji an kira sallan isha,
kusan a tare suka mik'e sukaje suka sabunta al'wala a tsakar gidan kana suka nufi woje suna fita suka shiga sahu, bayan anyi isha sai kuma aka fara yin sallan asham.
Suma su Ummi suka sabunta al'wala kana suka fara sallan.

Bayan an idar duk an fiffito ne sai Bappa Ali yacewa Saifuddeen zasufa tafi masallacin fada yanzu zasu fara tafsir d'in dan takwas ta kusa.
Mudassir ne ya kalllesu kana yace,
"Bari inje in cewa Ummi tafa ajiye mana jolof d'innan in mun taso tabsir zamuci dan ni in nazo konciya sai naci abinci."
dariya sukayi mishi kana Warisu dake bayansu yace.
"Anya ko kai bafullatanine Mudassir dan gaskiya fulani basu da yawanci."
Ahmad ne da shima yanzu ya iso yace.
"Yoh ai shi iyamburi ne bakaga yadda yayi k'atoba."
shiko Mudassir shafa cikinsa yayi tare da cewa.
"Me yafi raina."
dariya suka kumayi sai Saifuddeen da yaketa murmushi sai kuma Warisu ya kalli Saifuddeen kana ya kallesu tare da cewa.
"Ni ai ko dan kar inyi k'aton ciki zan yiwa kaina k'aidar ci abinci,
wlh da nasan yadda zanyi in koma kamar Saifuddeen da nayi na koma,
kalleshi komai na jikinshi dai-dai da shekarunsa,
shiyasa yake tafiya da kenshi da k'uruciyarshi,
wlh koda namiji d'an uwanshi in ya ganshi sai ya kuma kallonshi in ka ganshi kamar balarabe ko ba indiye."
cikin kauda kai Saifuddeen ya d'an shafa suman kanshi tare da mishi alamar.
"Kai Warisu in naga wani kyau."
daga nan suka shiga cikin gida bisa taburmar da Ummi ke zaune suka zauna bayan sun gaisane ta kallesu cikin kula tace.
"Ya kamata ace iwar haka kuna wurin tafsir, ku rage yawon dare kun san wannan wata ta musammance ga musulmai."
mik'ewa sukayi da sauri sai kuma Mudassir yace.
"Yauwa Ummi a ajiye mana taliyar nanfa in mun taso zamuci."
cikin jin dad'in had'in kan yaran tace.
"Ba matsala sai kun dawo."
daga nan suka juya har sunje bakin k'ofa tace.
"Ahmad kwana zamuyi ko."
cikin tsiya wasu Salisu yace.
"No Ummi ba kwana zanyiba ai inada yan rakiya."
yana fad'in haka sukayi ca a kanshi wai bazasu rakashi ba.
ita kam Ummi da murmushi ta rakasu.

Bayan sunje suka samu anata taruwa manya da yara da dottab'ai duk an cika can ta wojen gidan sarki kuma wani rumfane da mata ke taruwa a ciki.

Suna shiga duk sukayi gefen da aka ajiye mazaunin malam,
wuri d'aya suka zauna yayinda tuni,
Saifuddeen kuma ya zagaya bayan Bappa Ali da alarammanshi Abdurahman gyara tsayuwarshi yayi gefen d'an agajin dake bayansu Bappa Alin.
shi kuwa Bappa Ali da alarammanshi gyara abin sautin mgnar dake gabansu sukayi tare da d'an sunkuyawa kan Qur'anen dake bud'e a gansu inda bana zasuyi tabsir d'in ```suratul Maedah.```
shi kuwa Saifuddeen ta cikin glass d'in table d'in gabansu yake ganin fuskar Bappa Ali ras har yadda zai gane motsin bakinshi da abinda yake fad'in.
dan haka ya maida hankalinshi bisa bakin bappan nashi.

Bayan anyi addu'a an bud'e taro kana ya kuma jero addu'o'i. gyara zamanshi yayi kana cikin sakekken sauti yace.
"Alhamdulillahi Allah ya kawomu watan Ramadan tun kafin mu shiga cikin tafsirin namu zan d'anyi tsokaci ga yan kasuwanmu."
sai ya kuma d'ago kanshi ya d'an kalli taron jama'ar dake cike da masallacin ido ya d'an zuba musu tare da ci gaba da cewa.
"Shi watan Ramadan wotan rahama ne da jink'ai da kuma tausayin juna. Amman abin takaici abin haushi tun gabanin zuwan watan zakaga wasu musulman suna k'arawa kayayyakin sana'arsu kud'i domin suyi tsada, maimakon su rage musu k'ud'in domin tausayawa juna da tallafawa tallakawa."
sai ya kuma tsagaita. shi kuwa Saifuddeen tuni yake fassara abinda yake fad'in da body language yadda masu matsalar ji zasu iya gane komai a sau k'ak'e.
cikin nitsuwa Bappa Ali yaci gaba da sharan fage akan bayanin Ramadan inda yake cewa.
"Yana daga cikin fa'idojin azumi,
Azumi na sanya bawa godewa ni'imomin Allah mad'aukaki.
Azumi na taimaka wa bawa gurin barin abinda Allah ya haramta.
A cikin azumi akwai tsanani ga shaid'an da raunatashi.
Sannan Azumi na karya k'arfin sha'awa mu samman ga matasanmu.
Azumi na gadar da samin rahamar Allah da jin k'ansa.
Azumi na koyarwa bawa tsoron Allah, da tausayin na k'asa dashi.
Azumi na tafe da wasu falaloli na musamman,
da yawa sai a azumi suke samun dama da k'arfin guiwar shiga itikafi.
Itikafi shine keb'ewa ko zama cikin masallaci domin ibada.
Mafi falalan itikafi lokacin goman k'arshe, yin itikafi sunnace mai k'arfi
yin itikafi a masallacin jumma'a idan kwanakin da za'ayi sun had'a da jumma.
Idan zaka shiga itikafi zaka shiga kafin fad'uwar rana a daren da kake son fara itikafin.
Mustahabbi ne ga maiyin itikafi ya keb'ance da ibadu yawan salloli, zhikiri, addu'a, karatun Qur'an, tuba, istik'afari, salatin annabi, da dai sauransu domin nemar kusanci da yardar Allah.
Mai itikafi idan ya gama kwanakin da yayi niya zai fitane bayan fad'uwan rana.
Baya halatta ga mai yin itikafi ya fita zuwa duba mara lfy da kusantar iyali.
Amman mai itikafi zai iya fita domin abinda ya zama dole kamar buk'atu irin na d'an adam,
kamarsu zagayawa bayan gida da neman abinda zaici.
Idan rashin lfy ko jinin haila suka zowa mai itikafi,
zasu fita idan ya samu sauk'i ko ta samu tsarki sai a dawo."
gaba d'aya wurin anyi tsit ana sauraron bayanin malam Alin.
daga nan ya d'anyi k'arin bayani game da azumin kanshi inda yake cewa.
"Abubuwan k'i ga mai azumi,
Kaiwa matuk'a gurin kurkuran baki da shak'a ruwa.
Sumbatar iyali da makamancin haka ga wanda baya iya mallakar kanshi.
D'andanon abinci badon buk'ata ba.
B'ata lokaci kawai wasannin banza da surutai marasa amfani.
Zarcewa da azumi kwana biyu zuwa sama."
A k'arshe yace a tak'aice abinda ya kamata ga mai azumi ya kiyaye harshensa daga dukkan maganganun banza zagi annamimanci giba isgilanci da sauransu kodako a social media ne.
Daga nan suka shiga cikin tafsir d'in nasu gadan-gadan,
mutane sun nitsu wurin jin fad'in allahu subahanahu wata ala.

K'arfe tara dai-dai aka tashi, Saifuddeen ne ya karb'i d'an jakar Quran d'in bappan nashi kana suka wuce gida da abo kanshi,
suna shiga su suka wuce d'akinshi shi kuwa ya bi bayan bappa Ali da jakarshi saida suka shiga ya bashi sannan ya juyo ya nufi side insu,
murmushi yayi ganin suna fito daga d'akinshi suna zuwa tsakar gida Ummi kuwa taburma ta shimfid'a musu kana ta zuba musu zazzafan colof d'inan a tire tare da basu forks Mudassir ne ya amshi cokulan ya raba musu kana suka fara ci,
Raliyya kuwa babban kofi ta d'auka ta d'ebo musu ruwan randar d'akinshi ta kawo musu,
shi kam bai kula abincinba suma basubi ta kanshiba dan sun sanshi sam baida cin abinci,
Warisu ma kad'an yaci ya ajiye spoon d'in sabida baison yayi teb'a
suna gamawa suka sha ruwa kana suka fita suka raka Ahmad har shabewa sannan suka dawo,
tuni sha d'aya tayi shiyasa kowa ya nufi gida.

Yauma da dare kamar jiya haka Ummi ta tashi yaranta,
sai k'arfe uku Rahma ta tuk'a musu tuwon shinkafa dama kuma Raihana tayi musu miyar zogale tun da dare.
to yau Saifuddeen ya d'anci mai d'an yawa kana yasha tea,
suna gama sahur din ya shiga wonka kafin ya fito anyi assalatu,
so alwala yayi tasa Hayatudden a a gaba suka tafi,
su Ummi kuma sukayi nasu a gida.
Ana idar da salla ya fara azkar nashi sai da ya gama sannan ya shiga suka gaisa da Ummi kana ya bata 5k d'innan yace ta sama musu asusu na daban ta rink'a sasu,
ita kam Ummi tayi mmkin yawan kudin to ganin yana sauri Salisu na jiranshi yasa ta barshi ya tafi sai ya dawo suyi mgna.

Suna isa Salisu ya sauk'eshi a bakin masallacin bakin kasuwan,
shi kuma ya wuce kabo-kabonshi.
shi kuwa Saifuddeen cikin masallacin ya shiga kamar jiya yayi baccin awa d'aya da rabi kana yana farkawa yayi Al'wala yayi walaha raka'a biyu sannan yayi addu'o'inshi kafin ya fito ya nufi cikin kad'uwa.

Yana shiga kai tsaye dilansu na leda ya shiga inda ya samu mutun biyu a gabanshi dole yabi layi,
bayan an basu shima aka bashi na 60k Lamar na jiya kenan k'arfe 10:00 Am dai-dai suka bashi nashin,
with full confidence ya fara bin layi-layi shago-shago lungu da sak'o yana raba musu suna bashi kud'in na jiya, 1:35 pm ya gama rabawa da yake kusan fiye da rabin kasuwar duk a wurin baba bello suke sayan ledan to shiyasa yake dad'ewa yana yawata kasuwan da k'afa tunda shi bashi da keke kamar baba bello,
yana gamawa yazo ya had'a lissafin kud'in ya samu dubu settin da bakwai da dari biyu, cikin aminci ya basu 60k d'insu sannan ya adana ribarshi a jikinshi godiya yayi musu bayan an rubuta ya dawo da kud'in na jiya,
tafiya yake yana nazari shifa gani yakeyi kamar kyauta suke bashi kud'in duk da ko azabar nauyin kwalin da yake azawa a k'afad'anshi na dama aikine mai matuk'ar wuya ga yawo cikin rana har ji yake k'afafunshi suna yum-yum dan azaban rana da nauyin kayan da yake azawa a kafad'anshi.

Ganin azahar ta kawo kai yasa ya zauna ya d'an huta dan yana jin kafad'arshi na mishi ciwo ga zafin ranan da yabi sai yake jin wani irin azabebben k'ishi ,
ganin an kira salla yasa ya mik'e yaje yayi al'wala kana ya shiga sahu,
bayan an idar ne ya mik'e a gajiye yana tafiya a hankali yaje ya karb'i omo dasu sabulu,
sai kuma ya zage da talla dan yanada burin ya maida Raihana da Raliyya makaranta in kes dai ace sun gama koda d'an Secondary school,
yana kuma fatan ya ink'anta karatun Hayatuddeen da Faruq da Adam kuma yana fatan Allah ya hanasu sake tsammatan abinda zasuci daga wurin wani.

Da wannan tunanin ya zage yaketa yawa tawa cikin ikon Allah ranar ribar 1,200 ya samu.
Ganin ya fara ganin jirine ya sashi neman inuwa ya zauna saida ya huta sannan ya maida sauran omon.

ganin hud'u da rabi tayi sai yaje shagon ba mishkila gero ya auna mudu shida sai wake mudu shida sai sugar mudu d'aya da rabi,
daga nan yaje ya sayi mai k'aramin galam sai ya saya musu lemu da ayaba da kankana,

A tak'aice dai ya kashe dubu uku d'ari biyun nan sai dubu biyar ya bari su kuma na sawa a asusune.

Biyar na cika Salisu yazo nan suka kama hanyar Dukku, cikin sa'a suka isa da sauran rana.
Yauma kamar jiya tare da abokanshi sukayi bud'a baki.
ana idar da sallan asham suka tafi tabsir.
koda suka dawo suka ci abinci sannan suka raka Ahmad.

Yana dawowa ya sumu Ummi a tsakar gida,
bisa taburma Rahma na gefenta tana bacci yayinda take ruggume da Adam.
gefenta ya zauna ita kuwa Ummi tea ta had'a mishi sannan ta bashi,
yana sha ne taje ta d'auko asusun duka biyu yana ganinta da asusun ya d'an kaikaice tare da cusa hannunshi a aljihun wondon Jeans d'in jikinshi zaro kud'in yayi tare da mik'a mata,
cikin kula ta amsa kana ta irgasu ganin dubu biyar ne sai ta fuskanci da kyau cikin maganar kurame tace mishi.
"Kud'in waye ne."
kurb'an tea d'in ya d'anyi bayan ya had'iye ne sai ya nuna mata kanta.
fidda numfashi tayi tare da gyara zama dan tasan in abu nashine in ta tambayeshi na waye ne sai yace mata natane haka yasa ta gane kud'in nashine cikin tsoro da tuhuna da gudun masifun zamani wanda dole in kaga d'anka da kud'i ka bincikeshi ina ya samesu a hankali tace mishi.
"Ina ka samesu? Me kayi aka baka su? Ya jiya ka samu da yawa yauma kuma gasu da yawa gashi harda su gero naga ka seyo Babana ina tsoro duk da tabbas nasan halinka amman kud'in sunyi yawa."
Allah sarki Saifuddeen ganin firgici a fuskarta ya sashi ajiye kofin tea d'in kana ya juyo suka fuskanci juna da kyau,
a hankali yasa hannu ya kamo nata hannun cikin sama mata nitsuwa ya mata bayanin komai yadda ya samu kud'in duk da body language yakeyi so Ummi tana bala'i gane body language shiyasa wasu lokutan takanyi mgna dashi cikin mutane ba mai ganewa sai Rahma,
sai kuma yanzu sun lura Hayatuddeen ma yana ganewa kad'an-kad'an ajiyan zuciya ta sauk'e lokacin daya gama yi mata bayi,
sai tayi murmushi tare da hamdala kana ta godewa Allah,
sai kuma ya fara rubutu a gefensu kamar haka.
"Yauwa my Ummi ko kefa kada kiji tsoro Saif d'inki da halal zai cigar daku ya shayar daku ya tufatar daku da guminshi."
kanshi ta shafa tare da samishi al'barka shi kuwa rubutun ya kumayi.
"Amin Amin ya rabbil izzati.
Yauwa Ummi batun gero da wake da sugar kuma,
a jik'a geron sai a markad'a ayi kamu a rink'a dama kunu kullum da yamma sannan d'auki wake mudu d'aya kullum a surfa ayi k'osai da yamma sai asa a manyan kwanuka a rink'a kaiwa bakin masallaci sadaka,
gobe zan sayi dabino a rink'a had'awa da dabinon."
Allah sarki Ummi ji tayi tamkar ta ruggumeshi sai kuma taji wasu zafafan hawayen farin ciki,
cikin raman murya tace.
"Ya Allah ya yimaka al'barka babana Allah ya k'ara maka imani da tausayi ya Allah ya bud'a maka k'ofofin samu mai al'barka in sha Allahu nida kaina zan rink'a wannan aikin har zuwa k'arshen Ramadan su Rahma da Raihana kuma suyi na gida."
Wani irin farin ciki yaji yana ratsashi sabida ganin yasa mahaifiyarshi farin ciki.
ita kuma cikin bada shawara ko ince neman izininshi a matsayinshi namiji kuma babba tace.
"Goggonku Dada ta aiko Ahmad d'azu yake cemin wai dan Allah a bata Raliyya mana taje suyi azumi acan zata d'an taimaka mata da aiki."
cikin sanin makamar girma ya rubuta mata.
"Ummi in dai kin yarda ba matsala dan na yarda da tarbiyar Goggo Dada, amman ki gayawa Bappa Ali in ya amince ai sai taje."
kai ta jinjina kana tace.
"Shi na fara gayawa kasan ai bazai hanaba yace taje ba matsala."
gyara zamanshi yayi ya kalli Rahma data zuba musu ido,
sai kuma tayi maza ta rufe ido wai ita bacci takeyi.
Jin sautin murmushin sane ya sata tashi zaune kana tace.
"Yoh tun d'azu na farka sai naga kamar hirran sirri uwa da d'an lelenta sukeyi shine nayi likimo ai, kai kuma da yake ka shahara da body language ko kallonka akeyi jikinka ke gaya maka kawai sai naga ka zuba min wannan fararen idanun naka."
dariya suka d'anyi baki d'aya kana ta zauna sukaci gaba da hira,
inda itace ta amshi kud'in ta cusasu a asusun babban goggonin milo.

Daga nan sukaci gaba da hirarsu tasu ta rayuwarsu sai shad'aya suka shiga.

Shi kam Saifuddeen saida yayi wonka sannan ya yayi al'wala kana yazo ya shafa mai tare da fesa turare wanda wannan al'adar rayuwarsa ce domin Saifuddeen mutunne mai tsananin tsabta sam baya son k'azanta ko kad'a shiyasa yakeda kenkeyani over.

Washe gari kamar kullum yayi suka tafi gombe da kafin bakwai na safema sun isa,
baccinshi ya d'anyi na awa d'aya da rabi kana daya tashi yayi walahan shi kamar yadda ya saba,
sannan ya shiga cikin kasuwa ya fara rarraba ledodinshi ana bashi kud'in na jiya yana bada wani, cikin awa hud'u da kad'an ya gama rabawa ya had'a kud'insu 60k sannan ya ware ribanshi dubu bakwai da d'ari biyu,
yaso yayi ragin d'ari bibbiyun saman to kuma sai ya shawarci Jabeer sai yake ce mishi kada ya rage dan kar ya zama yayi azarb'ab'i a kasuwar ledan tunda du du du a wata d'aya ne zaiyi sana'ar kar yayiwa baba Bella shisshigi to da wannan
shawarar ya hak'ura.

Daga shagonsu Jabeer wucewa yayi yaje ya amso omo aifa nan ya samu sa'an shiga layin masu wonki da guga sukayi ta kwasan sabulun kamaru da omon ranar ribar 2k ya samu a omon ma,
da zai koma ya saya musu naman miya da kuma fruits.

********

Rayuwa ta ja yau da gobe asarar mai rai,
kwanaki sun tafi tuni azumi ya shigi jikin al'ummar annabi
anyi dibi-dibin goma na marmari gashi har an shiga goma na wuya inji hausawa da fad'i.
Cikin izinin Allah an gama na wuyan ma yau, gobe dai na d'okin sallah za'a fara.
Iyaye da yan uwa da masu wadata dama talaka kowa na hidimar d'inkunan sallah.

Saifuddeen ya k'ara sabawa da mutane sosai ko ta ina an sanshi a kasuwar sabida dalilai uku sana'arsa ta yawoce dole yana ratsa ko wanne lungu,
sannan shi kurmane da hakane duk wanda ya had'u dashi baya manceshi kana shi mai gsky da amanane da yawan ibada to sai Allah ya sanya soyayyarsa a zuk'atan bani adam.
Uwa uba Allah ya yalwata mishi surarshi da kyau mai d'aukar hankali yana da muhibba, kima, daraja, kamala, haiba, da cikar zati,
so wadannan abubuwan sukasa ya sanu tako ina.
Alhamdulillahi kasuwarshi kuwa sai son barka dashi dama Ummi da Rahma sai godewa Allah suke suna k'arawa sabida sune kad'ai suka san kullum sai yasa dubu buyer a asusunshi, sauran na saman kuma da balance d'in machine dasu sukeyi buk'atun yau da kullum,
ribar omo kuma yaci gaba da zurawa a asusun ribar pure water.

Abota tsakanin shi da Jabeer da Hisham da Kabir kuwa sai gaba-gaba sun shak'u sosai yanzu ya saba da wani yaron shagon Alhaji ishaq Ibrahim shima yaron yana sonshi, sosai hakama wani shagon ba miskila Bello sun saba over amman shi ya girmi Saifuddeen sosai so da yake Saifuddeen ya gaya mishi sunan Abbanshi gareshi shiyasa yana kiran Saifuddeen da Bingel am d'ana kenan.

Rayuwa ta mik'a d'aura kwalin ledodi a kafad'a da Saifuddeen yake yawan yi sai ya d'an canza mishi salon tafiya
sai ya d'an karkace ka d'an mu samman ta samanshi karkacewar da bafa zaka ganeba sai in ka zuba mishi ido sosai baranma in ka sanshi kafin ya fara tallan ledan ne zaka gane hakan sosai,
wannan 'yar karkacewar sai ta zama wani abu da yake jan hankalin mutane a gareshi domin daga saman wuyanshi zakaga time to time yana tonk'oshe wuyarshi irin yadda manyan sara kuna keyi sabida nauyin rawani da k'asaita,
da yawa kuma cewa sukeyi kyanshi ne yasa yake hakan wai a zatonsu rigimace da izza,
sabida in dai ka kalli yadda yake tafiya to sai kayi zaton d'an sarkine ko matashin d'awisu domin dama a nitse yake sai tafiyarshi da tsarinshi suka koma tamkar na jarumI R.K na seris film d'in Madubalah wanda aka tab'a nunawa a Bollywood
in ka ganshi sai kayi zaton tsantsar izzace da gadara da tak'ama kasan cewarsa karma ba ko yaushe yake mgna ba sai wasu suke zaton miskilanci ne.

Yakan je gidansu Is'haq time to time musamman in yaji zafi ya matsa mishi sai ya ajiye omonshi yaje yayi wonka ya canza kayan inda zaisa na is'haq sabida bashi da shamaki a gidansu is'haq so yawan tsabtarshi yasa kawai wasu ke masa kallon tabbas rigimace tunda gashi a wuni d'aya a kasuwa sai a ganshi da kaya kala biyu,
in yaje gidansu is'haq yakan amshi wayar step mother in is'haq din su gaisa ta hanyar rubutawa juna text.

Kullum duk bayan kwana uku zai sayi wakenshi mudu shida geroma haka sannan sugar mudu d'aya da rabi sai mai k'aramin galam da dabino mudu d'aya.
Umminshi ta dama koko ta toya kosan a kai masallacin k'ofar gidansu.

Yau jumma'a kana ana tsula zafin rana kowa ido yayi zuru-zuru sabida k'ishi da yunwa mazauna inuwama suna shan zafin azumin bare masu k'ananan sana'o'i irin Saifuddeen mai sai da leda da yan dako da yan garuwa da masu gonjo da kafintocin sama da kuma 'yan acab'a da direbobi.
Gashi yau shine azumi na 20,
Sosai Saifuddeen ke azabar jin k'ishi hakane yasa k'arfe hud'u dai-dai ya maida omo inda yauma ya samu riba sosai,
dama ya gama had'a ribar leda wanda yanzu masu sayan sun d'an k'ara sabida karatowan salla yasa cini kaiya k'aruwa.
Shagon ba miskila yaje yana isa Bello ya kalleshi cikin kula yace.
"Bingel yau ba omon ne?."
cikin gajiya ya lumshe ido tare da sharte zufar da yakeji da hankicib d'inshi cikin gajiya ya lumshe ido tare da mishi alamun akwai ya gajine yasa ya maida.
cikin kalato yawu Bello yace.
"Gsky kam bingel am azumin yau yanada dad'i."
murmushi sukayi baki d'aya kana Saifuddeen ya nunawa Bella d'anyar shinkafa da fulawa da sugar da geron
sai yaga kuma kamar bai fahimtaba hanne yasa shi zaro biro ya rubuta mishi cewa yana son d'anyar shinkafa da fulawa da sugar.
cikin kula ya auna mishi kana ya bashi kud'inshi shi kuma ya bashi ledodin daya zuba shinkafar a ciki.
Karb'a yayi sannan ya wuce ya sayo mai dasu yis, dan yana son a rink'a had'awa da masa a sadakan da ake kaiwa masallacin.
Sai kuma ya sai kayan marmarin daya saba saya, sannan yaje layin masu nama,
zabbi ya saya guda uku aka yanka aka fige aka gyarasu.
sannan ya fito bakin inda Salisu zai sameshi nan ya irga sauran kud'in inda ya samu ya shigesu sosai yau dubu uku zaisa a asusunshi,
yana zama ba jimawa Salisu yazo sauk'e wota mata kuma lokacin biyar saura aifa yace kawai su tafi gida,
to dama shima Salisu ya gaji kawai sai suka kama hanyar dukku.

Suna isa gida Hayatuddeen da Faruq suka tarbeshi,
da murnarsu bayan ya ajiye ledidin yayiwa Ummi alamun tayi musu ferfesun zabbin da asuba suci ko da biredi da tea
ai kam Raihana murna ta rink'a wai zata huta yin miyan asuba.
Shi kuwa gefen Rahma ya zauna sai ya kuma manna kanshi a kafad'arta cikin nuna tsantsar alamun gajiya domin Saifuddeen yana da tsoron wahala to kuma Allah ya jarab ceshi da ita,
cikin tausayawa ta shafa fuskarshi dan gaba d'aya jikinshi rawa yakeyi,
cikin tausayawa tace.
"D'an uwana sannu yau azumin da wuya anyi rana."
ido ya lumshe yana mai jin azabebben k'ishi,
a hankali ta kalli Ummi da tuni idonta sun cicciko da hawaye,
sai ta kuma kalli Raihana cikin sanyin murya tace.
"Raihana kai mishi ruwan wonka."
da sauri ta mik'e duk da tana jin wahalan azumi amman tasan dole ya fita shan zafin rana,
a randar tab'onsu ta d'iba saida ta cika mishi botiki sannan ta kai mishi bayan gida wanda yana wonke stab dan shi kad'ai ke amfani da bayan gidan tunda Nuruddeen da Abba suka rasu Hayatuddeen har yanzu bayan gidansu Ummi yake zuwa.
Tana kai ruwan taje ta d'auko mishi kondon sosonshi ta kai mishi sannan tace.
"Hamma na kai ruwan."
kai kawai ya iya gyad'a mata kana ya k'ara lafewa jikin Adda Rahmanshi,
jin hannun Ummi a kan gishinsa ne ya sashi d'ago kai ya zuba mata idanu,
ganin alamun zatayi kuka sai ya yunk'ura ya mik'e jiki na rawa,
cikin sanyi tace.
"Babana baka da lfy ko."
kai ya jujjuya mata a hankali kana yasa hannunshi kan cikinshi da yake a d'akale bafa irin d'akalellen cikin maceba a a irin nasu na maza,
sai ya kuma nuna mata mak'oshin sa alum k'ishi yakeji,
cikin kula tace.
"Je kayi wonka zakaji sanyi Babana."
Kai ya gyad'a mata sannan ya juya a hankali ya shiga kayan da zai sa ya d'auka sannan ya shiga bandakin,
yana shiga ya zare kayan jikinshi duka sannan yaje ya zauna bisa dutsen wonkan da yaketa shek'i da yake a inuwa yake baiyi zafiba,
surarshi ya k'arewa kallo idon ya zuba kan mararshi a ranshi yace.
"Hmmm yau kam kaji haza bayan baccinma har b'uya kayi ka koma cikin cikina ko?."
sai kuma ya fara watsa ruwan.

To Alhamdulillahi da yayi wonkan ya ji dama-dama gashi yana fitowa ana kiran salla,
al'wala yayi wanda tuni Ummi na gabanshi rik'e da dabino da surki mai d'umi,
dabinon ya amsa addu'a yayi kafin yaci guda uku,
da sauri ya jujjuya kanshi alamun shi bazai sha surkinba.
infa da sabo Ummi ta saba don haka yake ba komai yake ciba kuma zai tace maka yana jin yunwa kana kawo mishi abinci in ya tsakuri kad'an sai ya cire hannu wai ya k'oshi.
da sauri Hayatuddeen ya mik'o mishi pilet d'in su kankana to nan ya amshi fork a hannun Raihana sannan ya fara sokawa jikin kankanan da Rahma ta zuba mishi madara da sugar kad'an sabida ta sanshi da son zak'i,
ido kawai Ummi ta lumshe tana kallonshi sai yana tuno mata k'uruciyar Abbanshi,
bai shanye rabinshi bama yayi wani sassanyan gyatsa tare da mik'ewa wai ya k'oshi kenan,

jin ana tada kabbarane yasa Ummi bata hanashi fitaba,
shi kuwa kama hannun Hayatuddeen yayi suka fita zuwa masallacin.

Suma su Ummi sukayi haramar yin sallan.

Bayan an idar da salla, suna fitowa, Mudassir, Warisu, Salisu.
Suka nufi cikin gidansu Saifuddeen kai tsaye a babbar taburmar da Ummi ta saba shimfid'a musu suka zauna.
Rahma mace ta mik'e a hankali ta fara jero musu abin motsa baki, kankana da ayaba da dabinon suka fara ci, sunaci suna hira Rahma kuwa ita da kanta ta matso gefensu zama tayi tare da yi musu harara sannan ta jawo kulan dake gabanta cikin fidda numfashi tace.
"Daga yau bazan sake biye mukuba,
kun sani yi muku yambos wallahi ba k'aramar wuya na shaba kirba doyan nan wuya gareshi, gashi Raihana k'in tayani tayi wai ai nike biye muku."
Saminu da yanzu ya shigo tare da Saifuddeen ne ya harari Raihana tare da cewa.
"Yan ubanci zatayi mana shareta Adda Rahma ran salla ke kad'ai zamu bawa barka da salla."
tab'e baki Raihana tayi tare da cewa.
"Kada ku bani mana ni dama ban rok'aba."
Muddassir ne yayi d'an gyaran murya kana ya kalleta cikin tsuke fuska da bada umarni yace.
"Ni bazanma ci wannan yambos d'inba, yanzu ki d'an soya min dankali."
tura baki tayi tare da mik'ewa tana cewa.
"Ni wlh na gaji kuma yunwa nakeji."
Ummi ce ta d'anyi dariya kana tace.
"Zo Raihana taho nan ga dankalin dama na soyawa Bappa Alinku na kuma d'iba musu zoki basu nasan Mudassir so yake ya wahal min dake."
da sauri Saminu yace.
"To ni kuma indomi nakeso mai ruwa-ruwa yaji yaji da al'basa."
dariya sukayi baki d'aya dan sun san bazata iya musa mishiba,
sai kuma suka zuba musu ido jin tana ce mishi.
"Yanzu ne kakeso ko sai kun taso daga tabsir ne zan maka?."
ido ya lumshe kana ya zuba mata ido cikin sanyi yace.
"Ki huta sai mun dawo zamuyi aikin tare."
Ummi kam kauda ido tayi Warisu kuwa da Salisu tuni suketa hirarsu,
Mudassir kuma tuni ya zuba musu yambos d'in har ya fara ci Adda Rahma kuma tea tai ta had'a musu, nan suka fara ci sunaci suna hira.
Shi kuwa Saifuddeen gefen Ummin shi ya rab'a a hankali ya konta tare da d'ora kanshi a cinyarta, gyara zamanta tayi dan yaji dad'in konciyar,
kanshi ta d'an shafa cikin ido ta zuba mishi ganin sosai fa ya rame hancin shi zuwet har bisa baki idanunshi sun k'ara fitowa,
farinshi ya k'ara baiyana cikin kula ta kalleshi ganin ita yake kallo tace.
"Tashi mana Babana kaje kaci abinci da yan uwanka ai zakafi jin dad'in cin."
sanin in bai ciba hankalin ta bazai konta bane ya sashi yunk'urawa ya tashi zaune sannan ya amshi cup d'in da Adda Rahma ta cika da zazzafan tea mai k'auri sai k'amshi yake, gyara zamanshi yayi kana ya mik'awa Warisu hannunshi alamun ya bashi abinda suke ci d'in,
ganin Warisu zai kwatso mishi da yawane ya sashi nuna mishi yatsa d'aya alamun guda d'aya zai bashi,
kauda kai wWrisu yayi kana ya mik'o mishi guda biyu,
fuska ya d'an had'e dan shi cikinshi ya cika da ruwan da yaketa sha, ya kuma san Ummi zata sashi dole ya cinye biyun da ya sako mishi,
haka kuwa akayi dole ta sashi yaci sannan ta samishi soyayyan dankalin turawa, nanma yanaci yana d'an korawa da tea d'in a haka dai yaci kad'an.

Jin an fara kiran sallan isha yasa suka mik'e duka dan yin al'wala, dai-dai lokacin kuma Ahmad ya shigo shida Raliyya,
da sauri Rahma tace.
"Ke Raliyya meya kawoki a daren nan?."
kai ta d'an rausayar tare da gaida su Saifuddeen sannan ta zauna gaban Ummi cikin sanyi tace.
"Kai Adda Rahma ai nida Ya Ahmad ne muka zo nayi kewanku ne especially Hamma Saifuddeen, shiyasa nace yau mu taho tare kuma tare zamu koma."
Cikin fad'a Saifuddeen ya mata alamun da kada ta sake biyoshi gwara tazo da rana.
kai ta gyad'a mishi kana itama ta d'auki buta dan yin al'wala.

Su kuwa suna gamawa suka nufi masallaci koda akayi insha akayi asham, suna fitowa suka shiga cikin gida ruwa suka sha sannan suka nufi hanyar fita dan tafiya wurin tabsir kamar kullum,
har sunje bakin k'ofar fita Ummi tace.
"Ahmad ka dawo da wurifa ku tafi kasan Raliyya yanzu zatayi bacci anan."
juyawa yayi ya d'an kalli Raliyya cikin lumshe ido yace.
"Shike nan in tayi bacci sai in goyata mu tafi gida abinmu."
Warisu ne ya d'an bugeshi tare dayin k'asa da murya yace.
"Kai a gaban Ummin kake mata wannan kallon kamar wani tsohon maye."
ita kuwa Ummi cewa tai.
"Asheko yau sai dai ku kwana anan."
dariya sukayi kana suka fita,
Raihana kuwa da sauri ta isa gaban Saminu da shi yanzu yake shan ruwan,
cikin kauda kai ta mik'o mishi dabinon data ciko hannunta dashi guga bakwai ya tsinta kana yace.
"Ya isa sai mun dawo."
"To". tace dashi a sanyaye.

Daga nan suka fita suka tafi masallacin fad'an Dukku.

Ita kuwa Ummi ita da kanta ta shiga kitchen dan k'arisa aikin ferfesun zabbin data fara dan tasan yau Rahma ta gaji sosai,
Raliyya kuwa k'ofan bappa Ali ta nufa wurin Aunty Nina,
Raihana kuwa Attaruhu da al'basa ta d'auko tazo ta zauna gefen Rahma da keyiwa su Hayatuddeen homework shida Faruq, d'an k'aramin bilandan dake hannunta ta had'a kana ta yayyanka su ta jajjagasu sannan ta juye a roba mai marfi,
Hayatuddeen kuma saura su kankana da ayaban da akaci ya d'an rage guntayen yake ci shifa a dole baya son cin abu mai nauyi a rayuwarshi.

Ummi kuwa a kitchen tuni gidan ya cika da k'amshi dan zabbin sunji kayan had'i bayan ta gama zuba komai ne sai ta rufeshi bisa rushin yaci gaba da bararraka,
tea ta kuma tafasawa ta d'ura a filas sannan ta fito gudan dubu ta bawa Hayatuddeen ya sayo musu sabon biredi, guda biyu,
da sauri ya mik'e ya amshi kud'in yana zuwa ya kwaso biredi har guda hud'u.

Yana shigowa ganinshi da ledodi har biyu yasa Rahma cewa.
"Kai amman dai kai kam Hayatuddeen kaga ta kanka shin ba biyu aka aikeka ba?."
da sauri Ummi tace.
"Barshi ai bazai b'aciba nida nakeda samari yanzuma sun kusa dawowa."
Raihana ce ta d'an harareshi kana tace.
"Ai shiyasa yake komai na sakalci sabida yasan ba abinda za'ayi mishi ana tab'ashi kad'an Ummi da Hamma Saifuddeen zasuyi ta fad'a."
sai ta kuma kalli Rahma daketa dariya tace.
"Baga irinta nanba ai harda ke ake sakaltashi."
dariya sukayi baki d'aya ganin yana yiwa Raihana gwalo, Raliyya kuma da yanzu ta shigo dungure k'enyashi tayi nan suka fara 'yar tsamarsu ta sak'o da sak'o.

Daga bisani suka zauna suna hira cikin nitsuwa Raliyya ta gyara zamanta sannan ta fuskanci Ummi a hankali tace.
"Ummi Ya Ahmad yamin d'inki kala biyu ya kuma sayamin takalmi da mayafi ya kuma yiwa Faruq da Adam ma,
sai ya kuma yiwa Hayatuddeen dashi da Hamma Saifuddeen iri d'aya."
cikin mamaki Ummi tace.
"To shi Ahmad duk samunshi a kanku zai k'are ne, yayi ta zaman d'inki yana shan wuya ya kuma k'arar da samunshi a kanku ai wannan d'awainiya tayi yawa."
cikin sanyi tace.
"Wlh yana wahala kam Ummi kwana fa yakeyi yana d'inki, to amman kuma yana samun kud'i kinsan ya iya d'inki wasu ma daga bajoga da Ngalda duk shi suke kawowa d'inki gashi nan dukku duk ba wani tela daya fishi iya d'inki kinga fa duk zuriyar gidan sarki shi suke bawa d'inki tunda Ya Saminu ya hadasu dashi."
sai ta kuma kalli Raihana tare da cewa.
"Ai naga kema Ya Saminu ya bada aiyi miki dunkuna har kala uku, d'aya atampa ce d'aya kuma lace d'aya kuma shadda ce kedashi iri d'aya."
shiru tayi kamar bataji ba dan kunya takeji bata son a gane Ya Saminun sonta yakeyi tunda yace mata sai ya gama karatunshi, dan yanzu yana level 2 a G.S.U kunsan duk abokan Saifuddeen sun wuceshi da shekaru biyu sanadin nakasar daya samu ta sashi tsagaitawa da karatunshi sai daga baya da Nurudden ya kawo shawarar ya fara zuwa gombe dashi yana kaishi makarantar kuramen.
so shi Saminu shiyasa bai fiye zaman Dukku ba Salisu kuma kusan shine ya rik'e kakarshi inna shatu,
Mudassir kuwa yanzu iyayensu hankalinsu na kan karatun Ya Adnan da yake karatun likita yakeyi shiyasa basu bi ta kan mudassir ba tukun tunda sunaga shi Adnan ya kusa gamawa ason ransu sai sun gama da Adnan sannan su dawo kan Mudassir.
Warisu kuma yak'i ya nemi sana'a sai dogon buri to shima mudassir ai da yanada sana'a da duk sun d'auki nauyin karatunsu tunda su ba nauyin ciyar da wasu a kansu, to Saminu kuma da yake d'an gatane dan sarki kuma shalelenshi shiyasa tuni yayi nisa a karatunshi shiyasa ma yakeda damar yiwa Raihana hidima

Ganin Raihana tayi kamar bata jisu bane yasa suka kauda zancen.

Suna cikin haka suka jiyo hayaniyarsu Ahmad alamun sun dawo daga wurin tabsir d'in.

Bayan sun shigo duk suka zauna bisa taburma
sunata hirarsu ta abokai matasa,
ganin Ahmad ya sake ko a jikinshi kamar ba har Shabewa zasu komaba ne yasa Ummi ce mishi.
"Kaida zaku tafi kuma shine harda konciya kallifa har tara da kwata tayi."
sai ta kuma juyo ta kalli Raliyya dake konce kanta bisa sallayar da aka ninnenke.
"Ke maza tashi ku tafi."
cikin alamun bacci tace to,
Saifuddeen kuwa gyara zama yayi tare fuskantarsu cikin body language yace dasu.
"Ba inda fa zaku tafi a daren nan ku bari gobe kwa tafi da safe."
ido Ahmad ya zaro tare da cewa.
"To uban wa zaimin d'inkunan da na yanka na ajiye da kake cemin mu kwana."
hararan shi Saifuddeen yayi tare da rubuta mishi.
"Uban uwarka ne zai maka d'inkin."
dariya Ahmad yayi sosai yayinda Ummi taketa hararansu tare da ce musu.
"Kada ku sake samin kawuna a shirmenku kuyi da iyayenku banda salihan iyayenmu kam da suka bar duniya da dadewa."
cikin dariya Ahmad yace.
"Yoh dama wa zaice iyayenshi ba salihaiba mu nan gani muke duk duniya ba salihai kamarku."
shi dai Saifuddeen murmushi yayi had'i da shafa k'eyanshi da Ummi ta d'an dungura.
kana sai ya kuma tsuke fuska sannan ya musu alamun, dolefa su Ahmad su kwana da shi kad'ai yazo kamar kullum da zasu rakashi so tunda ya taho da Raliyya kuma dole su kwana,
ita kam Raliyya tuni ta b'ink'ire,
shi kuwa Ahmad tsaki yaja tare da cewa.
"Yaseen d'inku nanka sai bayan salla zan maka su, tunda dama gashi har yanzu baka kawosuba kuma kasan tun kafin azumi nake rufe karb'an d'inki amman da yake kai d'an gadarane da can da saya maka akeyi ma kullum wai sai ishirin da d'aya ga watan kake mik'o min dinkin ka kakuma samin naci dole in d'inka maka."
Tab'e baki yayi tare da d'aga mishi girarshi duka biyu alamun dolenka ai,
Warisu da su Salisu kuwa kanshi sukayi da cewa kadafa yayi musu al'k'awarin teloli.
mik'ewa yayi ya nufi d'akin Saifuddeen tare da ce musu.
"Kunga kada ku d'aura min jakar tsaba kaji su bini su tsatstsageni ni tuni na gama dinkunan maza yanzu na mata nakeyi, sai irin nasu Saifuddeen da basu badaba.
Saminu kuwa shi tuni yana bakin k'ofar kitchen ta woje yayinda Raihana keta ciki inda take dafa musu indomin,
sunata yar hirarsu,
nan ta dafa musu ta gama komai a wani babban tire ta juye musu kana ta jera musu fork sannan ta fito yana binta a baya suka isa a tsakiyar su ta ajiye musu tiren zazzafan indomin da yaketa k'amshin sai dafaffan kwai da tasa guda shida kowa daddaya kenan,
tana ajiyewa Ahmad daya canza kaya yasa jallabiyar Saifuddeen ya fito nan suka yiwa tiren zobe sunaci suna hira,
shi kuwa Saifuddeen kwan kawai ya fasa yake d'anci kana ya kalli Ummi data yunk'ura ta mik'e cikin body language yace mata ta zubo musu ferfesun in gama kai ta gyad'a tare da mishi alamun dama abinda ya tada ita kenan,
kai tsaye kitchen ta nufa kasan cewar zabbin guga ukune shiyasa ta zuba musu d'aya da rabi sannan ta d'auko biredi biyu kana tazo ta ajiye a gabansu aifa tuni Mudassir yayi gyaran murya tare da cewa.
"To yaseen ni dai na k'oshi da indomi ferfesun zansha."
dariya Ahmad yayi tare da cewa.
"Ni kuma dama mura nakeyi."
nanfa suka ture tiren indomin wanda dama kad'an ya rage,
nan suka fara cin tab'arb'ashin naman zabin da biredi,
duk sun nitsu sunaci shi kuwa Saifuddeen kad'an yaci sannan ya juyo ga Adda Rahma da Raihana Raliyya da suke ci a tare ido ya d'an lumshe ya musu alamun.....!

BY
*GARKUWAR FULANI*

*NAKASA BA KASAWA BACE*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.