Best / Popular Hausa Novels

Hamdah Littafi Na Daya Complete Hausa Novel

Reading file: Hamdah Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 1 of 3

[6/1, 3:39 PM] Rasheeda S Director: *🌺HAMDAH🌺*

*NA*

*RASHEEDA S DIRECTOR*

_(Book one)_

*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍�*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*_________________________________*

*Free page*

*Labari mai tsada farashi mai sauki É—arin ki-ka 200 yabiya miki-ka bukata*
*Turo 200 ta wannan asusun bankin 3170524141*
*Rashida Salihu First bank*
*Ko katin waya na MTN 200 ta wannan Number 08034690723*
*tsiyan nagari mai da kuɗi HAMDAH labarine mai tsa da na baku shi a farashi mai rahusa👌🏻*

🅿�1

Karar tsayuwar mota danaji ne yasani saurin wanke kunfar sabulun Dana goga a fuska ta,namike dasauri na Kama jikin karfen window'n bayi nad'ale saman toilet naleka,
karar murna nayi harda d'an tsallena kad'an yarage kafata tawuce cikin toilet,
Naduru da sauri nad'au soso nafara wanke jikina da sauri-sauri wani gunma baisamuba nad'au langar ruwan najuye a jikina dasauri naja zanina nad'aura nafita a bayin hijjab nasaka nafita waje da gudu,
a kofar parlour mukayi Karo da Aunty Rafee'at salle natuma nad'ale jikin ta natukui kuyeta ina fad'in "oyoyo Aunty Rafee'at"
"Ummi dake biye da ita ta ce "ke saketa yadata zakiyi"
Sauka nayi ajikin Aunty Rafee'at nad'ale jikin Ummi "oyoyo Ummi na"
nafad'a Ina dad'a d'alewa jikin ta,
Ummi ta ce "ni da Alla sakeni Sam baki da hankali".
Ganin su Abba da Abbu da Mamie da Aunty Jaleela Ya Masa'ud Nusaiba Fauzan da nayi ne yasani sakin Ummi nayi gurinsu a guje nashe ge cikin su kowa Sai da nad'ale jikinsa harda Fauzan da Nusaiba Sai da na rungumesu muka fad'i kasa, Aunty Rafee'at ce tad'agoni a kansu tana dariya tare da fad'in "Kai Hamdah ai Zaki karyasu kefa bakida girma saina jiki
ko yaushe Zakiyi girman gaskiya oho"
washe baki nayi nace "ai Abba yace saura kad'an nakara girma sai a mai da ni gi da a kawo wa Inna wata kinga yanzu nakusa zama katuwa kamar ke da Aunty Jaleela".
Aunty Jaleela ta harareni ta karasa cikin parlourn tazauna tuni su Ummi sun zazzauna Ina rikeda hannun Aunty Rafee'at muka Isa muka zauna, Ya Masa'ud ya ce "ai kuwa saura kad'an kikamo Jaleela 'yargidan Inna"
Dariya nakuma tunsurewa da shi nace "da gaske Ya Masa'ud?"
Yace "sosai ma"
Aunty Jaleela tace "zamu Sami masala da kai Masa'ud i'dan kasa yarinyar Nan tarai Nani".
Tafad'a tare da gimse fuska Ya Masa'ud kuwa 'yar karamar dariya yy yace "to da nawa kk fi Hamdah'n"
Mamei tace "Kai Masa'ud zaka fara niman ta ko tun amota kk neman ta da sokana kaid'in danawa kagirme tan"
Masa'ud yace "haba Ammi karkisa ma taji dad'i ta da d'a d'aukar kanta wata babba, yarinya shekara shabiyar nabaki dan haka kidaina d'aukar kanki wata babba"

Aunty Rafee'at ta ce "kafad'i kwanakin da ka Bata da kanka kwana shabiyar ba"
Ya ce "Allah Aunty Rafee'at kinga wannan yarinyar ko gyanbo Yabata lfy sabo da tsabar son girman ta in da itace gaba da ni narantse da kullum d'aukar bulala za'tayi tace zatarika yimin duka"
"Yanzuma kayi abun dukan Mana kaga ko bazan ma hukun ciba" Jaleela tafad'a"
Inna ta ce "to jarababbu masu ganin hanjin juna kun iso ba"
Ya Masa'ud ya ce "Eh mun iso Inna'r korafi"
Inna tace Kai Masa'udu kafita a'ido yo shed'anan ci zaka yimin ja'irin yaro kawai"
"Wlh mutum koyayi marmarin yazo yagan kima da zaran yazo da masifa Zaki karb'e shi garama nakoma inda nafito"
Masa'ud yafad'a Yana kokarin mike wa, Inna ta ce "maza ad'au hanya"
Ya ce "ba'inda zani tunda bakisan yadda mukayi muka had'a kud'i da Abdullahi muka gina gidannan ba ganin gari kawai zanyi nadawo nabaje"
Abba ya ce "Kai Masa'ud kaci kaniyar ka uwar tamu kk fad'awa haka"
Ya Masa'ud yy dariya tare da fad'in "Abba wannan tsohuwar tafiye mita daga zuwan mutum koruwa Bata bashiba tafara balbaleshi,garama naje waje abina"
Yafita Yana dariya.

Inna ta ce "yara sai iya bakin magana tun da kuka kwaso Lantai kunshiga uku kud'inama da tamutu dashi Dan siya hargi da tazo takarb'i daddawata girma da arziki harna murtala shida na'ai'ka barb'a tayab'a min banzan magana".
Murmushi Mamie tayi tareda girgiza kai zuwa nannan lokacin Bata da muwa da duk abin da Inna zatace a kan mahaifiyar ta tun kimanin shekaru talatin da suka wuce Inna take nanata wannan maganar harkuma yau Bata fasaba tun tana damuwa harta cire abun aranta.
Abbu najin Inna tafara wannan maganar saiya zaro kud'i a aljuhun sa yamikawa Inna yace "Inna ga kud'in daddawar taki"
Karb'ar kud'in tayi tawurgashi gefen kujerar datake Kai tace "yo anrigada an kuntatawa maishi".
Bb dai Wanda yatan ka Mata.

Bayan gaishe gaishe da ya gudana Hira yabiyo baya,
Ni dai bakina yaki rufuwa sabo da murnar ganin iyayena da 'yan'uwana Ina like a jikin Aunty Rafee'at Dan munfi shiri da ita Aunty Jaleela Kam takame can gefe sai lasar waya take idan nayi magana ta harareni waini nafiye magana Niko namurgud'a mata Baki dan bama shiri da'ita,
Sai da lokacin sallah yy kafin su Abba da Abbu suka fita,
Aunty Rafee'at ta ce "Hamdah zomuje d'akinki nayi sallah a can ina dai bb datti"
dariya nayi na ce "habadai Aunty Rafee'at ai kullum saina gyara d'akina harfa turare nake sawa ko yanzuma muje kiji kamshi"
Najanyo hannun ta
Muka shige d'akin Aunty Rafee'at tace "ah lallai Kam 'yargidan Inna ta'iya gyara"
Dariya nakumayi cikeda Jin dad'in yabawar da Aunty Rafee'at tayimin,
Bayan munyi sallah muka zauna bakin gado Na ce "Aunty Rafee'at wannan zuwan Kam kwana zakuyi ko"
tace "a'a yau zamu koma" b'ata Rai nayi naturo Baki gaba na ce "yanzu tafiya zakuyi to Nima saina biku"
Tace "a'a kibari sai lokacin bikin Ya Salim saikuje da Inna"
Nabud'i Baki zanyi magana sai Aunty Jaleela tashigo tawuce tashiga bayi tayi alawala tafito tahaura kan sallaya.

A can parlour bayan dawowar su Abba daga masallaci a parlour suka tadda Inna su Ummi da Mamie Nusaiba Fauzan kuwa suna d'akin ba'i dake Nan cikin parlourn,su Abbu suka zauna sunad'an tab'a Hira,
Abba yanisa ya ce "Inna adad'a sa Ido a kan Hamdah da kyau kinga yanzu tanakan tasowa Dole akara sanya Mata Ido"
Inna tace "yo kana nufin kace tarbiyya ce ban iyaba ko me? ba Hamdah ba Kai kanka Nan ni na tarbiyan tar dakai"
Abbu ya ce "a'a Inna ba abin da yake nufiba kenan"
Ta ce "to banason iyashegin banza da hofi tarbiyyar danake baiwa yarinyar Nan ko ku baku Isa kubata irin shiba"
Hakuri suka shiga baiwa mahai fiyar tasu harsaida sukaga ta sauko.
Bayan sallar la'asar suka fito domin komawa gi da kamar yadda duk karshen wata suke tattaro iyalen su suzo suwuni wa Inna da yamma sukoma.
Harsai da naga tashinsu kafin nakoma ciki.

Yau lahadi
damisalin karfe 1 narana aka tashemu a islamiya
muka fito da ga cikin makaran tar wata lambun tumaturi da ke gefen makarantar muka nufa aguje Rabi nafad'in "yaukam ni zanfara ban ruwannan tunda ke jiya kk fara"
Na ce "ai baki isaba, Baba na lambu ni zaka fara bani tiyon"
Dai-dai Nan muka shiga cikin lanbun tasaman tumaturin mukarika bi duk muka tattake tumaturin.
Cikin hanzari dattijon dake ban ruwa wa kayan lanbun sa yajuyo kafin yy wata magana tuni muka wafce tiyon da ke hannu sa inaja Rabi naja na ce "garama kisake Dan wlh ni zan fara"
Ganin yadda muketa faffasa masa tumatur yasa Baba na lambu kwatar tiyon da sauri a hannun mu ya ce "ke Rabi'atu barta tafara yau gobe ke Zaki fara"
tsalle nayi ina murna na nad'e hijjab Ina natattareshi narayata shi tabaya na nad'e kafar wando na,
Baba na lambu yamika min tiyo narika bin layi layi inayiwa kayan lambun banruwa inayi Ina d'an salle sabo da hakan bakaramin burgeni yakeba ko agida ne idan naje wanka saina b'ata lokaci Ina wasa da ruwa kafin nayi wankan.
Sai da nazaga d'an madai-daici lanbun tas da ruwa kafin nazo namika Mata tiyon inayima dariya nariga ta.
Itama takarba kamar yadda nazaga lanbun itama Sai da tazaga shi kafin tazo tamikawa Baba na lambu tiyon sa,
Ya ce "to maza a yi gida Kuma saigobe".
Mukace to muka fita tayi hanyar gidan su Nima nayi hanyar namu gi dan,
Tunda nad'au hanyar gi dan nafara Jin kirjina yafara bugawa Dan nasan yanzu karfe 3 tayi mu da aka tashemu tun karfe 1,a bakin get natsaya naleko kaina can nahango Fatu tsaye tana shanya kan igiya da sauri nashigo ganina yasa Fatu bud'e Baki za'tayi maga nayi saurin d'aura hannu na kan baki na nayi Mata alama da tayi shiru
Na karaso in da take
Cikin kasa da murya nace "Fatu Inna tana d'akine ko waje?"
Ta ce "tana d'aki"
Da sauri nawuce ta nanufi kofar da zai sadani da cikin gi dan nanma Sai da naleka natab batar da Bata tsakar gi dan kafin nashiga cikin sand'a, nashige cikin parlour dasauri nashiga d'akina.
Numfashi nasauke Allah yasoni yau da Inna taga shigowa ta da ta taramin jama'a,
Natub'e hajjab Ina nashiga bayi alawala nayi nafito nagabatar da sallar azahar Ina idarwa ko takan abinci banbiba nahaye gado narufe idanuna, nayi hakanne sabo da idan Inna tashigo tayi zaton tuntuni nadawo,har bansan sanda bacci yad'aukeni ba.

"Hamdah Hamdah Hamdah" can cikin bacci nakejin kiranda Inna taketa faman laftamin juyi yanaji cike da Jin da d'in baccin da nake nadad'a gyara Kwan ciyata.
Inna taturo kafa tana fad'in
"Kai Allah wadaren naka yalalace Wai ace yarinya bata da aikin yi sai bacci
dubi uniform in ma ko cireshi batayiba sabo da tsabar lalaci"
Dai-dai Nan Inna ta'iso bakin gadon tad'aka Mata duka
abaya.
Firgigit nafarka namike zaune da sauri Ina mussuke idanu,
Inna tace
"Mike da Allah bakida aikin yi sai bacci taya jiki zaiyi kwari kullum kina tafiya lagwai-lagwai kamar lagwani".
Turo Baki gaba nayi "to mezan Miki idan natashin?"
Tace "ko shara kije kiyi ai dai yafi kwanciyar Nan Kuma gashi almuru ta gabato inba so kk ki kwashi bakaken aljanu ba"
"Kai Inna Dan Allah ni kibarni nayi bacci na baga Fatu ba ai ai kintane basai tayiba ke bakya kaunar kiga mutum nahutawa saikin kwakulo Masa wani aikin."
Inna ta ce "kinci gidan ku yo dan da maiyi saike kizauna bazaki tab'uka komai ba sabo da son jiki irin naku na 'ya'yan yau"
Baki nakuma turowa gaba namike tsaye,
Sam matarna Bata kaunar taga mutum nahutawa kullum tafison tarika ganin mutum tsaye saikace wani soja.
nashige bayi nagara murfin kofar bayin da karfi, Inna tafice ad'akin tana cigaba dafad'in "iya shegen banza dan da maiyi saike kizauna bazakiyi ba"
Tub'e uniform nayi nayi wanka had'eda alawala sannan nad'auro towel nafito, Ina idar da salla namike nasaka Kaya yafito
sakar gida.

Nan na'iske Inna zaune kan tab'arma tana Jan jarbi wuceta nayi naje kicking nazubo a binci nadawo nazauna gefen ta nafara cin a bincin.
Sallama akayi dukan mu muka d'ago Rabi ce takaraso inda muke ta gaida Inna can kasan makoshi Inna ta'amsa gyara zamata nayi na ce
"Rabi zauna muci"
Ta ce "a'a nakoshi dama nazone kirakani kasan layi Mama ce ta'ai keni"
Nace "to Bari nakarisa cin a bincin saimuje"
"Kije gidan uban wa? Ke Rabi tashi kib'ace min da gani
yo nizaki kawo wa iyashege kizo kirika
kwasar yarinya kina kaita layi-layi salon
kiyab'amin kashin kaza a gari a ce ban'iya tarbiyya ba haryakai kunnen ubanta to bb inda zataje tashi maza kitafi"
Inna tafad'a tana nunawa Rabi hanya,
Rabi tamike tafita
Nace "haba Inna meyasa kk yin hakane Dan Allah kawai rakiyar dazan Mata shine yawon?"
"Au nazuba Miki Ido kirika yawo a wannan duniyar da mutanen cikinta suka gurb'ace Ina a nan ubanki yasani gaba yana yimin bita a kan ki kamar shi yahai feni,nifa wannan Rabin datake wurga kafa kamar shamuwar Nan Bata kwan tamin a rai ba, yaran yanzu kasaka musu ido ma ya'aka kare bare kakawar da Kai".

Ture plt in a bincin nayi namike nashige ciki,
Cikin d'aga muyar Inna take fad'in "shashancin banza"

Washegari Monday nagama shirina saf nazuwa makaran ta nad'au jakar makaran tana tafito
A kafa nahaura makaran tar namu saboda bb nisa saka ninmu,
A kofar shiga makaran tar muka had'u da Rabi Dan makaran tar bokon muma d'ayane da ita tare muka shiga,
a natashi muka fito
Har nad'au hanyar gida Rabi tabiyoni da sauri tana Kiran sunana
natsaya takaraso inda nake ta ce "Hamdah Dan Allah kirakani gidan Adda Samira dama can jiya Mama ta'aikeni"
Nace "to muyi sauri muje kinsan Inna tasan lokacin tashin mu yanzu idan taga ban koma gi da a lokacin ba zata biyoni"
Ta ce "tom"
Muka juya dasauri muka d'au hanyar gidan yayarta a kafa mukarika tafiya ga gidan da uban nisa Sai da muka gaji tilis kafin muka Isa gi dan aikuwa mukayi rashin sa'a Bata Nan haushi kamar nayi ya wahalarmu ta banza ko zama ban Bari munyiba nace mukoma Dan gabad'aya hankalina yakoma gida,haka muka Kuma dakawa da kafarmu bakaramar gajiya nayiba saijan kafa nake sabo da tsamin dakafar yy ga cinyoyina dasuke gogar juna sai zugi sukeyimin dakyar muka karasa gida.

Atsakar gida na tadda Inna da mayafi akanta
Baki tabud'e tana Bina da kallo nikuwa nawuceta nashige cikin parlour da sauri tabiyo bayana tana fad'in
"Mezan gani haka ke Hamdah wace irin tafiya naga kkyi" salati tashiga yi tana tafa hannu tare da fad'in "nashiga uku ni A'i wani al gungumin kk had'u dashi yy miki wanna irin zaluncin
Yau yankaki zanyi kafin ubanki yazo yakarasa ki
Ni tunda naga lokacin tashi yy Baki dawoba hankalina yakasa kwanciya ashedai darabon ganin bakin ciki shikenan kinjamana abun fad'a a gari".

Ido naware Ina kallon Inna cikeda mmk
Saikuma nabi jikina da kallo nakuma mai da dubana kan Inna da taketa buga kirji da sharb'e hanci,tana fad'in yankani zanyi,sorone ya lullub'ene lokacin da nagane abin da Inna take nufi,
Inna kuwa kwad'awa Fatu Kira tashiga yi tana fad'in tazo Mata da wuka,
Kara nakwalla tareda tuma tsalle narika zaga cikin parlour Ina fani "Fatu karki kawo wlh Inna banyi iskan ciba karki yankani"

Inna tarikoni tace "fad'amin d'an gidan uwan wayene shi?"
Na ce "wlh Inna babu kowa naraka Rabi ne gidan addan ta akafa shine kafata yakemin zafi"
Numfashi Mai karfi Inna tasauke saita sakeni ai da gudu nashiga d'aki Ina waigen kofa ko Fatu nazuwa da wukar.

Inashiga d'aki nahaye kan gado
shigata baifi da minti 10 ba Inna tashigo d'aukeda plt, nasan za'ayi
haka Inna wata irin mutum ce tanada fad'a yanzu zatayimin fad'an idan taga nab'ata
Rai zata biyoni ta
lallab'ani Amma fa bashi zai Hana anjima
takuma balbalamin masifa ba Kuma Bata son wani yayi min,kullum maganar Inna d'aya ce a duk san da
tatashi yimin fad'a
sai tace narufa Mata asiri ta dankani hannu iyayena ko gidan
mijina lfy,abun da kesa Inna fad'ar haka tun akan wata 'yar makotan mu
da tayi ciki a waje shikenan Inna tasinke kullum a cikin tsaro da
barazanar ta nake.

Plt maid'aukeda a binci ta'aje tazauna gefena tace "tashi kici takwara ta kinsan zama da yunwa bb kyau.........

Mommyn Twins ce
[6/1, 3:39 PM] Rasheeda S Director: *🌺HAMDAH🌺*

*NA*

*RASHEEDA S DIRECTOR*

_(Book one)_

*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍�*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*_________________________________*

*Free page*

*Labari mai tsada farashi mai sauki É—arin ki-ka 200 yabiya miki-ka bukata turo 200 ta wannan asusun bankin 3170524141*
*Rashida Salihu First bank*
*Ko katin waya na MTN 200 ta wannan Number 08034690723*
*tsiyan nagari mai da kuɗi HAMDAH labarine mai tsa da na baku shi a farashi mai rahusa*👌🏻

~wannan page ɗin na sadaukar dashi wa tsohuwa kakata Innar mu tsohuwa mai ran karfe madubin Director family~🥰🤗

🅿�2

Huf namike Dan dama yunwace sur cikina Sai da nafara cin a bincin kafin Inna tafita, Ina gamawa naje nawanko hannuna nadawo nakuma Kwan ciya.
Muryar Inna naji tana rafka
Salati sai kuma
Magana narikaji kasa-kasa da sauri namike zaune Jin muryar goggo Hauwa da a lamun fitar sautin kuka,
Cikin hanzari nadiro a gadon nafito,
Ido naware ganin goggo Hauwa shin fid'e atsakiyar parlour'n sai numfashi take fiddawa d'aya nabin d'aya nakuma Kai dubana takasa inda take kwancen dafe kirji nayi ganin jini nafita tacikin zanin ta, Inna tace
"Subhanallahi mezan gani ni A'i shekenan tayi b'ari"
A binda Inna naji take fad'ane yasani mai da duba na gareta dakyau, "B'ari" nanatata kallamar a raina,
Inna ta dubi Fatu da yanzu shigowar ta ta ce "yimaza kije ki taro Mana Mai a bin hawa mutafi asibiti"
Da sauri Fatu tafita Inna tashiga d'aki tafito da zani a hannu tazo kanta tana kokarin canza mata zanin,
Kara nakwalla lokacinda Inna tamirgina goggo Hauwa ganin yadda jini yakwanta a'inda ta kwanta nayi kan gaggo Hauwa ina fad'in "wayyo Allah goggo Hauwa karki mutu"
Fatu tashigo dasauri tace "Inna nataro Mai abin hawan"
Inna da Fatu su suka d'aga goggo Hauwa suka fita da ita nabi bayansu dasauri Inna ta ce nakoma gida suka haye a bin hawa suka tafi asibiti ina shiga gi da d'aki nawuce Dan gabad'aya ganin jinin Nan yatsora tani.

Sai yamma Inna ta dawo inajin da wowarta nafito Dan tun tafiyar su dana shige d'aki bankuma fitowa ba,
Na ce "Inna inasu goggo Hauwa'n?"
Ta ce "tana gidan ta nabarsu da Fatu zata zauna tayi Mata bakwai kafin tadawo"
Na ce "Inna harciwon b'arin tan yawarke?" Kai kawai tagyd'a min,harna juya zan fita sai nadawo dasauri na ce "Inna kikace Fatu saita kwana bakwai kafin tadawo?to waye zai rikayin wanke-wanke da shara da girkin?"
"Ke Mana bagakiba ke aikin me kk ke Zakiyi tayi kafin tadawo".
Jinayi kamar Inna tasa komin dutsai a ka, shara da wanke-wanken Nan basonsu nakeba garama girkin inason yi kodun nayita motsawa
Nace "Inna duk nikad'ai cap yaushe zan iya". Nafad'a Ina tura Baki,
Ta ce "ai dama ba Wanda a ka haifeshi da iyawa kowa Sai da yazo kafin ya'iya haka Zakiyi har ki iya uwar 'yan sonjiki"
"Ni dai wlh Inna bazan iyaba kice Fatu tadawo kawai tunda kince ciwon b'arin goggo Hauwa'n yawarke"
Dasauri najuya nashige d'aki, "yarinya sai shegen son jiki kullum kina gado kamar Mai kar yaiyen baya". Cewar Inna inajin ta nidai nayi shigewa ta d'aki.

Washegari da safe Inna tashigo d'aki inajin shigowar ta nayi saurin rufe idanuna tazo tashiga bubbugani tana fad'in "ke Hamdah Kin mance kinada makaran tane Baki tashi kinje kin d'aura a bin Kariba gashara da wanke-wanke ma kinsan dai Fatu batanan dai ko"
Da sauri namike zaune "Inna nayi latti fa" tace "yo shine kk kwance dan siya" Huf namike nasauko a gadon nashige bayi Dan gudun kada takuma kawo zancen wanke-wanke da shararnan.
Ina gama shiri nafito a kicking nasami Inna harta had'a a bin karyawa tazubo ta mikamin Ina kammala ci tami komin naira 50 nakarb'a inata murna nayi waje.

Karfe 12:00 muka fito daga aji Ina shiga gida Inna tace nayi maza natub'e nazo nayi shara nasan dai batada lfyr baya bazata iya sun kuyoba, ranar duk wata kiuyata Sai da Inna takure Dan kuwa a kaina tatsaya har Sai da nayi sharar, Ina gamawa naci a binci da sauri nayi Shirin isalamiya natafi tun lokaci zuwa isaliyar Bata yiba,
Gidansu Rabi naje nad'au Kota mukayi lanbun Baba na lambu,a can mukayita wasanmu har Saida mukaji haya niyar d'alibai kafin muka nufi makaran tar
Afilin makaranta tar muka tadda d'alibai,
Bud'e Baki nayi Dan gabad'a namance yauce ranar karb'ar hutun mu, kwata-kwata banji dad'in hutun Nan ba Dan tanan ne kad'ai nake samu nafito nayi wasana haka nakoma gida Raina ajagule.

Ina zuwa kofar gida naga wasu maza su biyo tsaye nazo zan wucesu d'ayan ya ce "am da Allah gidannan Zaki shiga?".
Da kai na'amsa Masa
Ya ce "yauwa kice ana sallama da Saleem". Juyawa nayi zan shige sai d'ayan ya ce "am yasunan ki?"
"na mance saina tanbayo" nafad'a tareda shigewa ciki Ina kunku ni "sun Sani gaba saiwani tanbayo yi sukeyi min sai kace wasu 'yan jaridu toni dasuke cewa nayi musu sallama da Ya Saleem so suke naje Bauchi'n nakira wo musu shine ko me".
Ina sakaina ciki naja natsaya da mmk nake kallon sa ko yaushe yazone oho Yana zaune kan taburma Inna na gefensa kan kujera sai juya invitation card take a hannun ta,
Baki nawashe "la Ya Saleem Ashe kazone shiyasa wad'an can gar da yen sukece na kirawo musu kai"
Da sauri na Isa Inna suke
Nad'au iv Mai d'aukeda sunan Saleem Abdallah and Na'ima, Baki nakuma washewa "la sunan matarka kenan Ya Saleem"
Wani kallo yy min dayasa ni saurin suke bakina,
Inna tace "to Mai sunan Malan madadin kazo da goro karaba wa a bokan ar ziki kazo da wad'an Nan takar dun, yanzu Taya zantu rawa makota ta kardar nan ai sai dai nasai goro na raba musu".

Adakile ya ce "ai dama wanna ba naki bane na jama'an nane"
Yasaka hannu a aljuhu yazaro kud'i yamika mata yad'aura da fad'in "gashi saiki siye goron kiraba wa jama'ar naki"
Da sauri na ce "haba Inna ga abun 'yan gayu kice wani goro ni barima naje gidan su Rabi nanuna mata"
Na a je jakata najuya da sau ri.
"Ke zonan!". A han Kali najuyo nazo d'an nesa da shi hannu yamika min a lamar na ba shi Mika Masa nayi kafin yakar b'a nasake yafad'i kasa najuya cikin tura baki na sallake kafar sa d'aya da ya mikar da shi da sauri Inna ta janye kafar ta ganin namiko kafata nayi bal da jakar makaran ta ta nashige ciki. Inna tabi bayan ta da kallo tana girgiza kai
Yun kurin mikewa yashiga yi Inna ta ce "rabu da ita Mai sunan Malan in dai Hamdah ce bakaga komai ba".
"A rabu da ita kenan tayi a bun da take so waini wanna yarin yar yaushe ne zata gyaru".
Ganin yamike tsaye yasa Inna saurin mike wa
Ta ce "yo Hamdah'n nawa take ai sai hakuri idan tagirma duk wad'an Nan a bubuwan bazata Rika yin suba".
Sun kuyawa yy ya kwashe iv in sa yy gaba Dan yasan idan a kan Hamdah ce komai za a ce bayar da Inna zata yiba.

Uniform in jikina natub'e na shiga bayi,duk kiuya ta ina son wanka sosai kodun nayi wasa da ruwa ina gamawa nafito nasaka Kaya na nufi waje, kamar Inna jira take ta ce na d'au tsintsiya maza nayi shara i'dan nagama Kuma nayi wanke-wanke, kamar na kur ma ihu haka naji.

Tunda dare yy nafara tunanin gofe fa asabar ce bb makaranta gashi an ba da hutun
Islamiya gobe Kam nasan Inna saita kwakulo duk ai kin gidan Nan ta jibgamin.
washegari dasafe inata zuba idon ganin Inna zata shigo shiru yau Kam nasan makara tayi har bacci yad'au keni.
Saida Rana yafito tarr kafin naji motsin ta Jin a lamu zata shigo d'akina sai na yi saurin sauka a gadon nashiga bayi,
Inaji tashigo tayita surutu tafita ina kus na dad'e sosai Sai da nayi wasan ruwa kamar yan da nasaba kafin nafito,
Ta window nale kata nagan ta a kicking,
Hijjab nad'au ka nafito a han Kali nasa kafa zan fita daga cikin parlour sai ganin ta nayi tana kokarin shigo wa "yauwa da ma zanje nataso ki kenan ga wanke-wanke can nahad'a Miki je kiyi".
"Inna kibari sai an Jima Mana nifa sanyi nake ji".
ta ce "wuce da Alla wani sanyi a ke da Zaki ce kinajin sanyi"
Zun b'ura Baki nayi
tawuce gun wanke-wanken na rataye hijjab Ina
a kan igiya nafara wanke-wanke'n Inna sai Karo min wasu
take tana fad'in "kigama maza kiyi shara mace batada
ai kin da ya wuce wannan".
Tana barin gurin da
sauri-sauri nawan ke kwanu kan namike nawan ke kafata, nasau ko da
ga gun wanke-wanken a
han Kali naleka kicking ganin Inna
Bata ciki sai na janyo hijjab Ina natafi cikin sand'a nafice a gidan,
Numfashi nasauke lokacin da nafito kofar gida.

"haba wai mutum bazai hutaba kullum tabi ta ishe shi da wani
maganar wanke-wanke da shara toma ai sai
kin ganni".
Da sauri nad'au hanyar gi dan su Rabi a kofar gi dan su nagan ta rike da roba na ce "Rabi Ina Zaki?"
ta ce "ai kan Mama"
Na ce "nidai lanbun Baba na lanbu zani".
"Muje da ga gurin sai naje wa Mama ai kan ta".
Muka d'au hanyar lanbun.

Da gudu muka shiga cikin lanbun yauma sai da muka faffasa masa tumatur yabamu tiyo muka yita zubawa shukin ruwa duk muka jika jikin mu,
Sai da muka gaji Dan kan mu muka fito muna fita a na Kiran sallah Ido nawaro "nashiga uku yau zan gamu da masifar Inna".
Rabi ta ce "wayyo nikam Mama duka zata min sai da ta ce nayi sauri".

Sauri muka fara yi Rabi tayi hanyar gi dan da Mamar ta ta ai keta, nikuma na Kara sauri,
Ji nayi abun nabin kafata zatona ruwan da na jika zanina ne Sai da naji zubar nashi ya karu ga d'an tsam tsin da nake ji idan cin yoyina suka had'u kamar a bun da ga gun yake sauka,
D'an sassau ta saurin da nake nayi
Na d'an ja zanina sama cak naja natsaya nakuma tattare zanina sama sosai jini nagani nabin kafata jiki nane yakama rawa sai nasaki wani razanannen Kara na tattare zanin da mugun gudu nayi hanyar gi da ina gudun Ina ihu Ina fad'in "wayyo Allah Inna nayi b'ari"
da karfi na tura kofar gi da nashiga a guje Inna na kofar kicking tamike da sauri da gudu nakarasa gun Inna na rirriketa
"Wayyo Allah Inna nayi b'ari wayyo Inna kiga jini Inna nayi b'ari"
Nasaki zanin yafad'i kasa sai na saki Inna nayi cikin parlour dai-dai in da ranar nafito na tadda goggo Hauwa kwan ce lokacin da naji Inna nace wa tayi b'ari nakwan ta narika birgima da ihu Ina fad'in wayyo Allah nayi b'ari.

Da sauri Inna tabiyo bayana tad'agoni "ke Hamdah kanki d'aya kuwa tashi da Alla shashashar banza".
Ta janyo hannu na tashiga da ni d'akin ta
Ban Kuma fasa ihun ba,
Na rirriketa
"Inna Nima kikai ni asibiti wayyo Inna ni dai kikai ni asibiti nayi b'ari".
ta ce "ke Hamdah kinutsu kiji ni girmace yazo Miki irin wanna jinin kowata mace idan takai munzali tanayi wanna jinin shi a ke kirada jinin al'a da ku a islamiyar ku ba'a fad'a mukune?".
Sassau ta kukan nayi "kenan wanna shine jinin haila da malan yake fad'a"
Nayi maganar a rai na, taja hannuna
bayi tashiga da ni ta ce
"cire pant inki ki wan ke jikin ki Sai da taga nafara wanke jikina kafin tafita tadawo rikeda wani pant da wani yankin zani tabani pant in tace nasaka ta nad'e min yankin tagwa da min yan da zan sa, nasaka. ta ce "kisaka dai-dai naje shago nasiyo miki auduga irin Wanda yanzu Mata suke am fani dashi".
Nidai komai ban ce ba zuwa lokacin sai naji duk jikina yy San yi.
Takuma fita takowo min zani nad'au ra natub'e rigar jikina duk nazuba Mata su a cikin bayin nafita,
Natafi d'akina nakwan ta a kan gado na dukun kune guri guda nayi shiru kamar Mara lfy.

Sai da Inna tawan ke kayan kafin tafito Ya Saleem ne yashigo ransa a b'ace Inna ta ce "an shigo ne Mai sunan Malan".
batare da yabata am Saba ya ce "wai ihun me yarin yarnan takewa mutane duk tabi tacikawa mutane kunne".
"Hm wai Hamdah inban da shirme irin nata wai dun girma ya risketa shinefa taketa wannan ihun".
D'an guntun tsaki yaja yajuya yafita "wai mutum yy gudun hayaniya yazonan in ma bai tsiraba"
Yakuma jan tsaki yafita a gidan ma gaba d'aya.

Inna tatura kofa tashigo takaraso tazau na gefe na,nikuwa inanan rakub'e har lokacin haka kawai nakejin wani iri a jikina "Hamdah".
Inna takira sunana Kai nad'ago nakalle ta,
ta ce "kibud'e kunnuwan ki da kyau kijini kinason mutuwa?".
Da sauri nagirgiza Kai cike da jin tso ta ce "to kinga yanzu kin girma a wannan yanayin da kk ciki yanzu idan kika kuskura kk Bari wani namiji yarike hannun ki to shikenan muwa Zakiyi Kuma kafin ki mutu saina Yan kaki da wuka da ganan Kuma shikenan kin mutu,karki yarda wani namiji yarike Koda hannun kine bare har yakaiga tab'a jikin ki Hamdah saina yankaki Kuma ranar Zaki mutu".
Ido na cicciro jikina narawa namike zaune "au mutuwar kk so ko?".
Da sauri nakuma girgiza kaina cikin rawar murya na ce "a'a Inna banaso".
"To duk ran da kk bar wani namiji yatab'a jikin ki ranar Zaki mutu kina jina ko"?.
Kai nashiga gyad'awa ba kakkau tawa.
Inna tamike tafita naja bargo nadukun kune ciki harda kaina nacusa ciki bakaramar tsorata nayi da maganar Inna ba ranar ko parlour ban fita ba.

Tun da ga ranar Konan da kofar gi da bana zuwa,
ganin nake kamar idan nafita wani namiji zai rike hannuna shikenan Inna tayan kani
shikenan Kuma saina mutu,
Makaranta ma na ce bazan jeba
Inna ta ce naje idan dai zan kiyaye maganar ta tofa bazata Yan kani har na mutu ba,
Nan ne nad'an Sami karfin guiwa harnake zuwa makarantar
a na tashi bana tsayuwa ko ina sai a gida,
Ko da muka koma islamiya Rabi tayi-tayi
Dani muje lanbu Baba na lanbu naki
Dan a ce wana ai shima namiji ne,na
gwamma ce na da wo gida nayi wasan
ruwana a bayi.

Yau a ka bamu hutu a makarantar bokon mu hakan kuwa yy dai-dai da saura kwana biyar auren Ya Saleem,
Shiri muka fara yi a na saura kwana biyu muka d'au hanyar Bauchi har kofar gida mota yasau kemu,
a guje nayi cikin gida Ina ihun murna part in Mamie na nufa tunga kofar parlour nake fad'in "Mamie munzu Mamie munzu".
Harna shige ciki ban fasa fad'a ba,da gudu nafad'a kan kafar Mamie da ke zaune kan d'aya da ga cikin kujerun parlour,
Dariya Mamie tayi ta ce "to sannun ku da zuwa".
"Toh 'yar gi dan Inna an bayyano"
Aunty Rafee'at tafad'a tana murmushi namike jikin Mamie nakoma kujerar da Aunty Rafee'at take "la Aunty Rafee'at kema kinzo ne?".
Sai a lokacin na lura da duk family'n mu suna cikin parlour'n har da Ummi na jikin Ummi nakoma sannan nabi kowa na d'ale kijin sa
Sai dari suke suna fad'in 'yar gi Dan Inna kenan.
Da ganan Kuma namike nafita a parlour'n nayi part in Inna Ina shiga naga Ya Saleem zaune kusa da Inna..........

Mommyn Twins ce

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/HZBkGl1rPR14UqBIortjnG

*🌺HAMDAH🌺*

*NA*

*RASHEEDA S DIRECTOR*

_(Book one)_

*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍�*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*_________________________________*

*Free page*

*Labari mai tsada farashi mai sauki É—arin ki-ka 200 yabiya miki-ka bukata turo 200 ta wannan asusun bankin domin mallakar wannan littafin 3170524141*
*Rashida Salihu First bank*
*Ko katin waya na MTN 200 ta wannan Number 08034690723*
*tsiyan nagari mai da kuɗi HAMDAH labarine mai tsa da nabaku shi a farashi mai rahusa*👌🏻

🅿�3

Wuce su nayi nashige d'aki da sauri Dan fitsari ce tamatse ni,Ina gamawa nafito Inna kad'ai nagani zaune nakoma part in Mamie nashige cikin 'yan'uwana mukayi ta Hira.

Yau a ka d'aura auren Abdallah Idris Abdallah da amaryar sa Na'ima,
Anyi biki nagani nafad'a amarya ta tare a d'akin ta.
Bayan bikin Ya Saleem da sati biyu muka koma Dass.

Bayan wani lokaci
Abubuwa sun faru da da ma ciki kuwa har da shigata a ji uku a sakandiri

Kwance nake a kan gado dawo wata kenan da ga makaranta Inna tashigo "Hamdah taso kika mawa Fatu ai ki Dan a gama da wuri kafin mai sunan Malan sudawo ka da Kuma su da wo su samu ba'a gamaba a bin ciba" .
Da d'an murnata namike zaune "la Inna su Ya Saleem in sun zone?".
ta ce "E sunzo d'azu shi da matarsa Basu Jima da fitaba kada Kuma su da wo a binci baiyiba zo ki Kama Mata kuyi da sauri".
Namike nabi bayan Inna,
A kicking na iske Fatu na yankan alaiyahu na Kama Mata muka sun kuya ai kin tuwon farar shinkafa miyar ganye mukayi bamu bar kicking in ba sai wajen karfe 6,
D'aki nakoma nafad'a bayi nayi wanka ban fito ba Saida nad'auro alawala Ina gama Kim sawa a na Kiran sallar magriba nagabatar da sallar kafin nafito a parlour na tarar da Inna zaune nawuce naje kicking nazubo a binci
Na da wo kusa da ita.

Da sallama Ya Saleem yashigo parlour'n Na'ima na biye da shi Inna ta ce "mara banku sai yanzu?". "Eh". Ya am sa a takai ce, Baki nawashe "la Aunty Na'ima sannun ku da zuwa" daga ita har Ya Saleem in bawadda ya am sa ni,
Suka karaso suka zauna kan kujera Inna ta dube ni ta ce "ke Hamdah je ki kawo musu a binci".
"sai nayi wan ka tukun"
Ya Saleem
Yafad'a Yana mikewa "Aunty Na'ima kekam nakawo Miki?". Wani irin kallo ta bini dashi sai tamike tana fad'in "No ai Nima bazan iya cin a bincin ba saina wasa ruwa".
Tana gama fad'a tabi bayan Ya Saleem baki natab'e, bazan man ceba ranar da ta tare washe gari nad'au su Nusaiba da Fauzan mukaje gidan irin wannan kallon wula kancin tayi Mana haka Muka da wo gi da, ko idon Ya Saleem in shima bamu gani
ba.
Baki na kuma tab'ewa naci gaba da cin a bin cina
Inna ta ce "gama ki Kai musu a bin cin can d'akin nashi".
"Inna ai sun koshi ne tun da an ce a kawo musu Nan wani wai sai sun yi wan ka wane kwad'i to ai sai suci wankan".
"A'a ki dai Kai musu kawai". Cewar Inna.
Ina gama wa nad'au plt in na mai da shi kicking na da wo parlour "har kin Kai musun?".
Inna tafad'a tana dubana,
"nifa Inna bacci nakeji idan sun gama wan Kan ai zasuzo suci".
Inna ta ce "hungo naki maza wuce muje kk Kai musu".
kicking muka je Inna tad'au a bin cin su da muka shirya cikin tray ta Mika min
"Maza kikai musu Dan tsiya kyace wani suzo suci ke dai bazaki tab'a dai na kiuya ba."
Karb'a nayi Ina zun b'ura Baki ni gaba d'aya idan ai ka yashafi na Ya Saleem ne bason sa nake ba Dan ba'a yimasa gwanin ta na wuce Ina kun kuni Inna takoma ciki.
nanufi d'akin sa dake tacan gefe.
Da sallama nashiga parlour bb kowa ciki sai karar TV da ke tashi a cikin bedroom na Isa na aje tray'n harna juya zan fita na tuno halin sa wata Rana da yazo Inna tasani nakawo Masa a binci
kamar haka nazo ban samesa a parlour ba na a je a bincin natafi washe gari yarika masifa wai haka yakwana baici a bin ciba sai washe garin da yafito yaga a bincin a parlour ranar kad'an yarage ya bigeni Inna ce ta hatanashi.

Na da wo nad'au tray'n naje kofar bedroom in natura kofar batare da sallama ko niman izini ba na kusa kaina ciki.

Ina kusa kaina ciki idanuna yasau
ka Kan Ya Salim zaune bakin gado bb ko Kaya jikin sa
Cak naja na tsaya jikina ne yakama rawa wani irin tsoro Mai tsanani yarufe ni,
na lura baima San da shigo wata ba sabo da karar TV da ya karad'e cikin d'akin
wani irin Kara na kwalla tare da sakin tray in hannu na yafad'i kasa,
baya nashiga yi.
A razane Ya Saleem yad'ago da matukar mamaki yake kallo na babo ko kakkau tawa da sauri yamike tsaye,
Hannu na biyu nasa narufe fuska ta na juya da mugun gudu nafita a d'akin nanufi shashin mu a guje nashiga parlour nawuce Inna nashige d'akina na haye saman gado can kuyar gado nazauna Ina mai da numfashi, da fe kirji na dake dukan uku-uku nayi narufe idanuna da karfe a fili nafurta
"Kai Ya Saleem ko kunya ma baiji ba kato da shi yazauna bb ko kaya...."

A b'an garen Ya Saleem kuwa ido yakurawa kofar har tab'ace wa ganin sa rasa Mai zaiyi ma yy sai ya koma yazau na bakin gadon ya rumtse ida nunsa da karfe tareda dafe kan sa tsananin b'acin Rai had'eda bakin ciki yahad'u yadun kule masa a zuciya.
Jin karar fad'uwar a bu yasa Na'ima da ke wanka cikin bayi fitowa da sauri tana gyara d'aurin towel in kirjin ta,
Bin kulolin da ya sarwatse cikin d'akin tayi da kallo sai Kuma tamai da duban ta kan Ya Saleem da ya da fe kansa Kuma kallon kwanukar tayi sai takuma maida duban ta kan sa
Ta ce "wannan fa?".
Tafad'a tana nuna kular dasuke watse a gun.
Matsowa tayi kusa dashi tashiga tattab'a jikin sa tana cigaba da fad'in "
ko kaji ciwone?".

Bud'e Idanunsa yy Rai b'ace ya ce "wannan banza shashashar yarin yarce Hamdah itace tashigo da tray Inna ta fasashi a gon Dan sabo da sabar ja kanci tashigo d'aki Kai tatse bb ko sallama".
Da sauri Na'ima ta mike tsawon ta tana binsa da kallo ta ce "ban fahim ta ba kana nufin tashigo cikin d'akin Nan a haka ta same Ka?".
tsaki yaja Ya ce "a haka mana".
Da fe kirji tayi ta ce "what tashigo cikin d'akin Nan takan ka zaune haka!
Wata ta ganka bayan ni!".
Rai b'ace yad'ago yazuba mata ido watoma ita ba ma da muwar ta bakin cikin da 'yarnan ta cusa Masa bane ita da muwar ta da ban na kishin ta take,
Ganin kallon da yake yimata yasa ta saurin suke bakin ta,
Yamike tsaye tareda d'aukar jallabiyar sa yazura ganin na kokarin fita yasa ta masowa da sauri kusa da shi tariko hannun sa cikin muryar buka tuwa ta ce "My love Ina Kuma zakaje Amma fa kasan mun Riga da mun shirya komai yanzu kawai fa Kai nake jira."
Juyowa yy yakalle ta saikuma ya janye hannun sa yajuya yaci gaba da tafi yafita a d'akin parlour yaje yazare igiyar caji,
Bin bayan sa tayi tana fad'in
"Haba Saleem katsaya Mana Amma fa idan kayimin haka baka kyauta min ba yakamata a ce ka ban lokaci na ba kafita ba" .
Ko sau raran ta baiyi ba yy waje a bin sa.

A parlour ya iske Inna zaune tana Jan carbi ya wuce ta da sauri yashige d'akin Hamdah.
Zunbur namike na zauna ganin yadda yafad'o cikin d'akin
Kokarin durowa nake a gadon Dan nagudu yy saurin ruko hannun na yashiga zubamin igiyar caji ihu nashiga zab gawa da iya karfi na Ina tsalle,
Shiko da gewa yy yarika zubamin igiyar cj.
Da sauri Inna ta shigo d'akin har tana had'awa da gudu hannu na da ke rike a hannun sa tashiga ja tana fad'in
"Kai Mai sunan Malan kanka d'aya kuwa saketa me tamaka kk Mata irin wanna duka ha".
Ko sau raran Inna baiyiba yarika shin fid'a min bulalar,
Inna ta dadda ge tashiga saka nin mu ta ce "had'amu ka buga duka"
Tajanyo igiyar cj tad'aura jikin ta ta ce "duke mu Mana Mara kunya gadon Lantai"
Fizge cazar yy Yana huce yanuna ni da hannu ya ce "wlh ban barki ba Allah ya kaimu gobe sai nayi Miki dukar sa'a".
Rab'ewa nayi a gefen Inna Ina rusar kuka idan nakalli hannuna da shatin bulalar yakwan ta sai na da d'a fasa kara.
Inna ta ce "yo ai yanzu ma kamar sa'ar naka kasamu duba kaga yan da ka da ge kk dukar ta kamar kasami sa'ar naka, wlh Mai sunan Malan saidai kahad'a da ni da ita dukan mu kabuga baka'isa kakuma dukan taba mara kunyar banza Mara kunyar hofi Mai zuciya kamar fad'a wuta".
Kwafa yy ya ce "wlh duk san da tasake shiga min cikin d'aki batare da sallama ko niman izini ba saina b'ab'b'alla ta Kuma daga yauma nasa Miki doka har idan nazo ban yarda nasake ganin kafarki a bokar d'akina ba".
"Inna ta ce "kaji Mata ciwo uban ka yy jinya, ko yy dai sai kun nuna halin Lantai a tare da ku kud'inama da taci sai Allah kawai".
Ya ce "wannan Kuma ke kk Sani ni Ina ruwana".
Yajuya yafita fuuu.

Inna tariko hannu na tazaunar da ni bakin gado ta ce
"Yihakuri kinji ai su sun iya karfin hali ba Lantai suka gado ba....."

Lantana wacce Inna take Kira da Lantai kakar su Ya Saleem ce tagurin uwa tun shekaru talatin da d'ori taci bashin daddawar Inna na d'ari da a shirin Bata biya taba har tarasu kullum idan 'ya'yan Mamie suka tab'ota saita goranta musu Mamie Tasha biyan kud'in ba a dadi haka Abbu hatta Abba da Ummi ma a duk san da tatashi maganar idan suna gurin suna bata kud'in da ya ninka kud'in daddawar ta, Amma bashi zaisa gobe tace tana bin Lantai kud'iba,
Tun Mamie tana da muwa har tacire a bun a ranta.
tun bayan rasuwar Lantai da kwana biyu a ke biyan Inna kud'in har Kuma yanzu sai dai idan 'Ya'yan Mamie basu tab'ota ba.

D'akin sa yakoma yahaye gado yakwan ta duk ransa a jagule Na'ima dake zaune tun d'azu a bakin gado ta haura gadon takwanta a bayan sa tasa hannu tana kokarin tab'ashi yabige hannun ta tareda buga Mata tsawa ya ce "matsamin anan!".
Mamaki yakamata Nan take wani muguwar tsanar Hamdah yadirar Mata a zuciya
Tabbas wanna yarin yar itace silar ruguje Mata burin samun Saleem na wannan Rana,
A ranta take fad'in "ni haka kawai nakejin yarinyar Bata kwan tamin a raiba lallai zan d'au mataki a kan ki!".

Washe gari su Ya Saleem suka bar garin ko sallama basuyi wa Inna ba.

Menene a salin wannan family?

Malan Abdullahi Turaki mazaunin cikin garin Dass ne dake jahar Bauchi'n Yakubu,
yanada matarsa d'aya Mai sunan Aisha da yaransu uku Idris Shu'aibu sai Hauwa'u
Idris wato Abbu shine babba sai me bimasa Su'aibu Abba kenan sai kanwar su gogga Hauwa,
Sun taso cikin so da
kaunar junan su
Sun Sami ilimi in gan tacciya wacce yakaisu ga samun ai
kin gamnati Mai tsoka a yanzu Abba da Abbu suna zaune a cikin garin
Bauchi da nasu iyalan ko wannen su na da mata d'ai-d'ai
Abbu da matarsa Hajiya Maryam wato Mamie suna da yara hud'u Abdallah wanda yaci sunan mahaifin
su Abbu a nakiran sa da Saleem shine babba sai Rafee'at Masa'ud sai autarsu
Nusaiba.
Abba da matarsa Hajiya Fatima 'ya'yansu uku sai da ta haifi biyu suka rasu kafin sauran ukun a yanzu dai
Jaleela itace babba sai Hamdah sai Fauzan.
Family'n suna zaune cikin kwan ciyar hankali da lumana, duk da tarin dukiyar
da suka Tara a cikin gi da d'aya suke rayuwa sabo da kauna da a mincin da ke sakanin su.

Bayan wani lokaci Malan Abdullahi Turaki Allah yakarb'i rayuwar sa family ta girgiza ba kad'an ba
bayan ar ba'in su Abbu sukaso d'auko Inna su mai da ta cikin gari fir taki ta ce subarta a in da tasaba cikin 'yan uwan ta,
Haka suka hakura badun sun soba lokacin da su Abba zasu koma gida sai ya yanke hukuncin bariwa Inna Hamdah Dan tad'ebe Mata kewa tareda nema Mata wacce zata Rika yimata ai yukan gida,
Duk karshen wata suke zuwa duba ta harda Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela da suke gidan maza jensu.
Wanna shine takai taccen labarin family'n.

★★★★★★★★★★★★�

Da sauri nafito da ga cikin kicking rikeda kofin kunun da na da mawa Inna nanufi d'akin ta cikin hanzari Jin tana laf tamin Kira,
a kwance na sameta tanata numfarfashi na iso in da take na ce "Inna ga kunun".
Ta ce "um..uhum yarnan wannan ciwo naga a lama bana kare bane kiramin Idris da Shu'aibu"
kiramun su marmaza".
Tafad'a tana turomin 'yar karamar wayar ta kirar TECNO,
D'aukar wayar nayi najuya baya Ina d'an dariya kasa-kasa Yan da takeyin ne yabani dariya saiwani Nishi take nikuma banga wani ciwon kirki ba.
Lanbar Abbu na danna ringing d'a biyu yad'aga tareda yin sallama na ce "inayini Abbu".
Ya ce "lfy lau Hamdah Ina Inna'r take?".
"Gatanan batada lfy ne tace wai nakira ku".
"Subhanallahi meke da munta?".
"Zazzab'i ne" nafad'a Ina Mika Mata wayar kafin ta karb'a ma tuni Abbu yakashi wayar,namika Mata kunu "inna gashi kitashi Kisha".
Tamike ta karb'i kunun tad'an tab'a.

A b'angaren Abbu Yana kashe wayar numbern family Dr su dake cikin Dass yakira batareda b'ata lokaciba yazo wa Inna da magani.
A wa biyu sakani
saiga su Abbu sun iso,
nafito da shirina nazuwa islamiya naji muryarsu a d'akin Inna na nufi d'akin da sauri ina washe baki
"La Abbu Abba kunzone?".
Nafad'a Ina kuma murmushi Abbu yy "mun iso 'yar Inna yau kina inane Baki taromu tun da ga wajeba"
"Ai Abbu ina Shirin makaranta ne Kuma banji shigowar ku ba".
Ya ce "to maza a je makaran ta ka da ki makara".
Na ce "tom".
Najuya nafita Abba dai komai baice ba sai dariyar da ya bini da shi.

Inna tamike zaune da kyar tana Nishi Abba ya ce "sannu Inna jikin neko?".
Gyara zama tayi tanafad'in "hum Shu'aibu jiki Kam haka za'ayi tafama dashi har Allah yakawo wa'a di yanzu ni babban da muwa ta a rayu wa bai wuce Hamdah ba
Itace kad'ai da muwa ta inata fata kafin Allah yad'au rayuwa ta naga auren ta da idanuna".
Sai tashiga Jan hanci tacigaba da fad'in "ina tunanin wanni hannun namiji Hamdah zata fad'a mazajen yanzu basa da rikon a Mana inasowa
Hamdah wan da zai
riketa da gaskiya da a Mana wan da zaiyi hakuri da Jin bakin ta, a Yan zu kuwa samun hakan
sai wan da yasan zafin maishi".
Gefen zanin ta ta Kama tasharb'e hanci sannan ta kalli su Abba ta ce "kuhad'a Hamdah aure da d'an uwan ta Masa'udu inada tabbacin shi zai riketa da a Mana tunda shi yasan zafin ta".
Abbu ya ce "to shikenan Inna insha Allah kamar Yan da kk fad'a za'a had'asu idan suka kammala karatun su".
"Wani karatun? Idris harsai namutu kenan ni ban yar da ba idan Kuma baso kuke ku nunamin kun fini iko da 'ya'yanku bane".
Abba ya ce "a'a Inna ai damu da 'ya'yan mu duk mallakin kine baki dai fahimci abin da yake nufi bane".
"yo wani irin famimta kuke so nayi ai na famim ceku baso kuke saina mutu tukun kuyi ba".
tafad'a tana kokarin mikewa,
Da sauri Abbu ya ce
"Yihakuri Inna ko gobe kika ce a d'aura auren sai a d'aura Amma gawani shawara".
Jin haka yasa Inna gyara zaman ta
Abbu ya ce "kinga yanzu Masa'ud Yana India sai Nan da shekaru uku zai kammala karatunsa ya da wo idan ya da wo sai a d'aura auren ko ya kk ce Inna?"
Shiru Inna tayi zuwacan ta ce "to shikenan in da rabon nagani da numfashi na to................

Mommyn Twins ce

*🌺HAMDAH🌺*

*NA*

*RASHEEDA S DIRECTOR*

_(Book one)_

*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍�*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*_________________________________*

MARUBUCIYAR👇🏻
*BA ABIN DA BAN GANI BA*
*INA SANE DA HAKA*
*AL'FARMA*
*BAZAWARA CE ITA*
AND NOW👇🏻
*HAMDAH*

🅿�4

Tun da Inna tafara ciwon Nan kullum Nike da ma Mata kunu da safe duk da kuwa yanzu tasami lfy Amma Bata fasa ta da ni da sassafe wai na da mamata tunun ba,
ko bacci nake saita sa Fatu ta ta dani haka Ina mita zanje na da ma mata,
Ko yanzu ma motsin Fatu naji tana kokarin shigowa d'akina nayi saurin rufe Ido na.
Ta turo kofa da ga bakin kofar tatsaya ta ce " Hamdah wai kitashi inji Inna ki.."
Huf namike batare da nabari ta tarasa fad'ar a binda zata fad'an ba Fatu naganin haka tayi ficewar ta, nasau ko a gadon da sauri nafito d'akin Inna na nafad'a tana zaune a kan kujera tana Jan jarbi
Hannu nayarfe tare da fad'in
"Inna nifa bani da lfy to tun da ga Fatu basai ta da ma Miki ba ni kenan kullun-kullun da safe sai kin d'agani ni Kam bacci nakeji Yan zu".
Nafad'a Ina tura Baki gaba,
"Yo Mara lfyr haka yake duba fa kiga Yan da kk shigomin d'aki kamar Zaki fad'o min a ka,
To Ina am fanin baccin safen ma in ban da ya kara miki muguwar lalacin Nan naki shiyasa nace a had'aki da d'an uwan ki in ba shid'in ba wazai iya da halinnan naki na son jiki".
Turo Baki nakuma yi najuya Ina buga kafa nafita kicking naje na tad da Fatu harta d'aura ruwa har Yana tafasa,
Kunun na da ma Mata nakai Mata.
Ina gama karyawa wanka nayi nashirya da sauri nad'au mayafi na nafita Dan nasan har idan ina gidan tofa sai Inna ta ce muyi ai ki tare da Fatu,
Gidan su Rabi nanufa a gindin bishiyar kofar gi dan su na isketa zaune
Rike da waya a hannun ta tana kallo Baki na washe
"La Rabi wayan waye a hannun ki?".
Nayi tan bayar Ina zama kusa da ita
Ta ce "wayar Ya Maheer ne".
Kuma washe Baki nayi na ce "la laushe yazu?".
Ta ce "jiya da daddare yanzu yabani nakai masa caji".
Kuma gyara zama ta nayi na da d'a sauke ida nuna a cikin wayar sosai
Yayin da na Mai da han kalina gaba d'aya kan Shirin da a ke a cikin wayar duk da kuwa ba hausa (film) bane
Mace ce da na miji
Suketa ai kin shafa junan su yayin da bakin su ke had'e da juna,
Ido na waro sai na Mai da dubana kan Rabi na ce "Rabi Yan iska nefa".
Dariya Rabi tayi ta ce "hum soyayya sukeyi dai".
"Soyayya".
Na nanata kalmar ta ce "E mana". Nabud'i Baki da zummar Kuma yin magana muka jiyo muryar Ya Maheer wato Yayan Rabi da sauri tamike tayi hanyar shagon caji,
Nikuma nayi hanyar gida.

Tafiya nake yayin da (film)in da na kalla ketayimin yawo a Ido can Kuma cikin kwakwalwa ta kalmar da Rabi ta am Bata na soyya ita keta zirga-zirga cikin ta.
Ina shiga gi da d'aki nawuce nafad'a saman gado har a lokacin kwakwalwa ta da idanuna basu fasa baiyanomin wad'an Nan mace da namijin da na gani da a binda sukeyi da Kuma kalmar soyayyar da
Rabi ta am batamin ba
Juyi nayi a fili na furta
"Wannan shine soyayyar?".
Nayiwa kaina tan bayar Ina maikuma juyi a kan gado.
Ranar haka nawuni cikin tunanin wani a bin da ni kaina ban sanshiba....

Bauchi
Abba ne da Abbu zaune a parlour'n Abbu Kamar Yan da suka Saba a duk San da suka dawo daga gurin ai ki a parlour'n Abbu suke fara ya da zangon su kafin su shiga ciki gun iyalan su.
A cikin hirar da suke ne Abbu ya gyara zaman sa ya dad'a fuskan tar d'an uwan nasa da kyau ya nisa ya ce "Shu'aibu nifa wani a bu na da mina
Tun ranar da Inna tayi Mana magana a kan auren yaran Nan han kalina yakasa kwan ciya,
Idan baka man taba kwatan kwacin haka yatab'a faruwa lokacin daf da rasuwar Baffa kwatan kwacin maganar Inna shi Baffa yayi ya ce mu aurar da Rafee'at da Jaleela tun Yana da numfashin sa bamu d'au maganar da wata girmaba sai bayan rasuwar sa muke ciza yatsa,
To gashi Inna ma nakan maimaita kalmar kada muzamo 'ya'ya marasa biyayya ni nagama yanke hukun ci za'a d'aura wa yarannan aure juma'ar da zatazo Nan da kwana biyar idan shi Masa'ud in ya kammala karatunsa ya da wo sai a yi biki ta tare ko yakagani?".
Abba ya ce "wlh Nima a bunnan Yana Raina wanna hukun cin da kayan ke shine dai-dai Allah yanuna Mana ranar".
Nan suka tsara duk Yan da d'aurin auren zai kasan ce.
Cikin kwanaki uku a ka gama turawa 'yan uwa da a bokan ar ziki katunan gayysta da a ka buga.

Tun da nasami labarin za'a d'aura Mana aure da Ya Masa'ud a cikin satin da muke narika zan Dara ihu sai da natara makota ca
Inna tad'au bulala tabini da shi tana fad'in
"Ina ga halin naki idan ba d'an uwan nakiba wazai iyamiki".
nafita a guje nayi gidan su Rabi har na isa gidan ban fasa ihun danake ba Maman Rabi da ke tsakar gida tana aiki tad'ago cikin han zari tazo inda nake tariko hannuna ta ce "me yafaru *HAMDAH* wayarasu!?".
Tayimin tan bayar hankalin ta a tashi
tsaida ihun da nake nayi naturo Baki gaha na ce "wai ba aure za'ayimin da Ya Masa'ud ba".
Numfashi Maman Rabi tasauke ta ce "wlh harkin tsoratani nad'auka rasuwa akayi to inban da abinki Dan za'ayi Miki aure sai kibi layi kina ihu bakison auren kenan?".
Shiru nayi Dan nikaina bansan dalilin uhu naba bazan iya tantance shin son auren nake ko kinsa ba kawai ihun zuwarmin tayi nakama yinta.
Ganin nayi shiru sai tasaki hannuna tana fad'in "jimin yarinya da tsiya salon d'agawa mutane hankali ca nake mutuwa akai idanun ta babu ko kwalla wai tana ihu".
Ban Kuma bi takantaba nayi gun Rabi dake tsaye bakin kofar d'aki itama Jin ihu nane yafito da ita nawuceta nashige d'akin tabiyo bayana zama nayi bakin katifa itama tazauna
Dad'a gyara zamata nayi tareda washe Baki Kamar banice nagama ihu yanzu ba, cike da zumud'i na ce "yauwa Rabi ina wayar Nan kunnan Mana muga soyayyar Nan wan da ranar muka kalla a can gindin bishiyar kofar gidan ku".
Rabi ta ce "ai wayar Ya Maheer ne ai jiya yakoma birni".
Na ce "ayya yanzu yakoma wlh inso nasake gani
Nima inaso nayi irin soyayyar da naga sukeyi".
Ta ce "ke ance masu aurene kad'ai sukeyi wan da Basu da aure Kuma 'yan iskane".
Shiru nayi Ina nazarin maganar ta "wato masu aurene kad'ai sukeyin hakan?".
Nayi maganar a cikin zuciyata,
Sai Kuma nasheke da dariya harda tafa hannu na ce "la to ai shikenan idan a ka Mana aure da Ya Masa'ud sai muje munayi"
Dariya Rabi tayi ta ce "da gaske zakuje kunayin soyayyan".
Na ce "Eh Mana".
Sai yamma nabaro gidan su Rabi a kofar gida na had'u da Inna da hijabi a kanta Ina ganin ta nasan biyoni tayi hannuna tariko tajanyoni muka shiga cikin gida
tana surfemin masifa wai zaman me nake da almuru a waje.

duk da kuwa cewa aure kawai za'a d'aura banda biki hakan Bai Hana 'yan'uwa zuwaba su Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela tun ranar laraba sukazo kan ranar Alhamis gida yacika Tam da 'yan'uwa washe gari Juma'a bayan an sauka daga sallar juma'a da misalin karfe 2 jama'a ne tam kofar gidan Malan Abdallah Turaki,
tuni aka fara gudanar da aurin aure yayin da hankalin al'umma gabad'aya ya koma kan shaidar d'aurin auren da suke
"Alhamdulillah² munshai da aurin auren *ABDALLAH* Idris Abdallah da *HAMDAH* Shu'aibu Abdallah uban giji Allah yabada zaman lfy".
Wanna kalmar ne ke fita daga bakin manyan limaman dasuka ziyarci d'aurin auren,
A razane yaciro wayar dake kare a kunnen tun isowarsa gurin yaketa amsa Kiran abokan sa wad'an da Basu Sami halartar d'aurin auren ba suna tayasa murnar auren kannensa dazai gudana ayau.
Kamar a mafarki yaji an Dan gantashi da auren da yanzu a ka d'aura cikin hanzari yashiga kusawa cikin jama'ar hankalinsa a matukar tashe ta'in da sautin kefita yanufa hannun wani mutun yarike dake kokarin fita daga gun,
Mutumin yajuyo Yana Masa kallon mamaki ganin yarike Masa hannu
Dad'a rike hannun nasa da kyau yy ya ce "Dan Allah wa akace an d'aura auren sa yanzu?".
Mutumin ya ce "kai da kazo shaidar aure baka ba da hankalin ka wajen karb'ar shaidar ba to *ABDALLAH* Idris.
Da sauri yasaki hannun mutumin batare da yajira yakarasa fad'aba yajuya da sauri.

A can cikin gida kuwa da sauri Aunty Rafee'at tafito daga kichin in da suke rabon abincin ba'i d'akin Inna tanufa da sauri Jaleela tagani tsaye ga dukkan alamu abinda kunnuwar ta suka jiyar Mata suma shi sukaji. Inna kuwa sai tafa hannu take tana fad'in
"Amma ko mutanen nan sunsan abun da suka fad'a kuwa ya za'abasu d'auren auren Masa'udu su d'aura da maisunan Malan maza kirawo min Idris da Shu'aibu".
Tafad'a tana mika musu wayar
Aunty Rafee'at kam kasa karb'ar wayar tayi sabo da tsananin damuwar da tashiga Aunty Jaleela ce takarb'a takira numbern Abbu Yana fara ringing Tamika Mata Inna takara wayar a kunne dai-dai Nan Abbu yad'au wayar da sallama zatayi magana yayi saurin cewa "yihakuri Inna gamunan shigowa cikin gidan".
Batareda b'ata lokaciba su Abbu suka shigo cikin gidan direct d'akin Inna suka shige su Aunty Jaleela suka fita suka Basu guri
Aunty Rafee'at dai gabaki d'aya jikin ta yagama yin sanyi Bata iya komawa kichin in ba sai shigewa tayi d'akin *HAMDAH*.

Su Abbu suka Sami guri suka zauna tunkan su idda zaman Inna tafara fad'in
"menakeji haka ko kunyi mantuwar sunan ne kuka bada na Mai sunan Malan?".
Abbu ya ce "a'a Inna ba mantuwa mukayiba da shi *SALEEM* in aka d'aura auren".
Salati Inna tashiga yi tana tafa hannu ta ce "akan wani dalili zaku sauya daga kan Masa'udu ni dama nasan bason auren Nan kuke ba to kuyi duk Yan da kuke so".
Yunkurin mikewa Inna tashiga yi tana cigaba da fad'in "natara jama'a akan da Masa'udu za'ayi aure kuzo ku canza".
Girgiza Kai Abba yy tareda yin murmushi a b'oye ya ce "Inna kiyi hakuri ki sauraremu".
Abbu ya ce "Inna ke kikace kinason mijin da zai rike Miki *HAMDAH* Yakuma yihakuri da Jin bakin ta shiyasa mukayi nazari idan akace za'a had'a Masa'ud da *HAMDAH* aure to lallai bazaki Sami a binda kikeso ba Dan dukkanin su yarana Masa'ud shekarun sa 24 yanzu Kinga kuwa zaiyi wuya ya'iya rikon *HAMDAH* yanda kkso saboda karancin shekarun sa,shiyasa muka sauya daga kansa zuwa kan d'an uwansa
Kinga shi *SALEEM*
ya mallaki hankalin kansa shi zaifi riketa fiye da Masa'ud in".
Shiru Inna tayi a'lamar nazari zuwa can ta ce
"To wato da Mai sunan Malan in kenan? Amma dai zakuyi Masa kashedi a Nan ma kenan yake bugunta kamar jaka Ina Kuma ga taje gidansa".
"Bai Isa ya tab'a taba Ko da taje gidan nasa".
Cewar Abbu.

Gidan yafad'o baya ko kallon gaban sa tundaga tsakar gida yake kwallawa Inna Kira har ya'iso cikin parlour Bai fasa Kiran nataba yatura kofar d'akin ta yakusa kansa ciki Yana fad'in
"Inna nasan duk Shirin kine Wannan akan me za'a zantar da hukunci batare da saninaba ni nace Miki Ina bukatar karin aure ne to wlh bazai yuwuba!".
tsawan da Abbu yabuga masane yasashi tattaro nutsuwarsa yamai dashi kansa cikin d'aga murya Abbu ya ce "mahaifiyar tamu kk d'agawa murya Kai ka haifemu da har saimun nimi yar darka kafin muzantar da hukunci a kanka!".
Sunnkuyar da kansa yy Dan baiyi zaton dasu Abbu a cikin d'akin ba.
fad'a sosai Abbu yashiga yi Masa Yakuma d'aura dafad'in "yau Kuma zata tare a gidan ka kaje kabud'e d'aya part in da ke gidan ka shine mallakin ta aciki zata zauna".
Abbu na kaiwa Nan yamike yafita Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela yakwad'awa Kira suka fito da sauri, Abbu yadubesu ya ce "kuje yanzu direba yakaiku Bauchi gidan Yayan ku kuje kugyarawa *HAMDAH* d'akinta".
Suka amsa da "tom"
Sannan yakalli Goggo Hauwa ya ce
"Kibisu susaukeki a gida kuje kuyimata siyayyan kayan d'aki ".
Itama "tom"
Ta'amsa da shi, sannan yajuya yafita Yana Mai danna numbern Mamie tana d'agawa ya ce
"Kiyiwa Hajiya Fatima magana Hauwa zatazo sai kunimi wasu daga cikin Dan ginku kuje kuyiwa *HAMDAH* siyayyan kayan d'aki".
Mamie ta ce "to Amma Alhaji dawuri haka ai gara a Bari sai lokacin tarewan nata".
Abbu ya ce "yau zata tare a gidan *SALEEM* Dan dashi aka d'aura ko ba'a gama siyayyan yauba zata tare inyaso daga baya a Kai kauran".
Yasauke wayar a kunnen sa tareda katse kiran..........

_NAGA INGAN TACCEN COMMENTS DA SHARHI IN BA HAKABA NAKUMA D'AUKAR HUTU_

Mommyn Twins ce

*🌺HAMDAH🌺*

*NA*

*RASHEEDA S DIRECTOR*

_(Book one)_

*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍�*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*_________________________________*

MARUBUCIYAR👇🏻
*BA ABIN DA BAN GANI BA*
*INA SANE DA HAKA*
*ALFARMA*
*BAZAWARA CE ITA*
AND NOW👇🏻
*HAMDAH*

Free page

My no 08034690723

🅿�5

Har Abbu yafita *SALEEM* natsaye yakasa Ko da motsawa ne, Abba yamike ya dafa kafad'ar sa ya ce "jeka ai watar da a bin da a ka umur ceka".
Jiki a sab'ule yaja kafar sa yafita a d'akin,
Inna zatai magana Abba ya daddanne ta tahanyar ban hakuri.
Yana fita motarsa yashiga yy Mata ki yad'au hanyar bauchi, su Aunty Rafee'at ma tuni direba yy gaba da su sabo da gudun da yake kusan a tare suka shigo gari,
gidan su Abbu suka fara rasawa Dan sabo da su sauke Goggo Hauwa.
Yana dai-dai ta parking yafito yanufi ciki direct babban parlour yashiga Na'ima yagani tsaye da mayafi a kanta sai Kai kawo take a cikin parlourn yasan za'ayi haka Dan yanada tabbacin zuwa yanzu rahoto ya iso Mata.
Kokarin wuce wa yake
Da sauri ta iso in da yake Tasha gaban sa tazuba Masa idanuwan ta masu d'aukeda zunzurutun matsanan cin kishi ta ce
" *SALEEM* abin da zakamin kenan da irin Wannan mummunar sakayyar zaka sakamin! Amma wlh *SALEEM* kabani mamaki".
Jan yota yy jikin sa yatallafe fuskarta da tafukan hannun sa cikin irin yanayin sa yamosa laɓɓansa yasoma magana.
"bayin kaina bane yin mahai fanane".
Kawar da kanta tayi yayin da zuciyar ta ke kuna takuma Mai da duban ta kansa ta ce
"Meyasa ka Amin ce tun da bayin kan ka bane? wlh bazai tab'a yuwuwa ba Dan ban shirya zama da kishiyaba *SALEEM* Kai nawane ni kad'ai babu wata macen data Isa ta rab'eka kakoma kace musu bakaso".
Cire hannun sa yy daga fuskar ta yajuya yasoma tafiya Yana fad'in
"bazan iya zuwa nafad'a musu Wannan kalmarba yazama dole nayi musu biyayya kuma kema haka".
"Munafurcin banza da ma can kanaso in ba hakaba to kaki Amin cewa Mana wlh-wlh har idan yarinyar nan tatako gidannan masifa da bala'i yanzu yasoma!".
Tafad'a tana wani irin huci Mai d'auke da tsananin kishi.

Bai Kuma juyowa ba yashige cikin d'akin sa
ya Isa gefen gado yaja durowa yad'au makullin d'aya part in da Abbu ya ce yabud'e ta kofar part in San nabaya yafita batare da yabi ta babban parlour ba.
Na'ima kuwa ci gaba tayi da zuba ruwan bala'i da fad'an miyagun kalmomi gaba ki d'aya idanunta sun gama rufewa da sananin kishi.
Yana bud'e kofar part in motar su Aunty Rafee'at yashigo gidan wucesu yy yashige motarsa yabar gidan.
Suna shiga share-share da goge-goge suka sunkuyayi basuwani Sha wahalaba suka gama kasan cewar bawani datatti gurin yy ba Dan duk bayan wata d'aya uban gayyar yakan sa a bud'e part in a share a goge.
bayan la'asar wata jibgegiyar motar kamfanin da su Mamie sukayi odar kayan d'aki tafaka a farfajiyar gidan cikin han zari ma'ai katan kamfanin suka saussauko daga saman motan Nan suka fara sauke kayan Aunty Jaleela ce tafito tayimusu jagora zuwa ciki batare da b'ata lokaciba sukafara shirya kayan a duk in da yakamata yamma lis su Aunty Rafee'at suka koma Dass sukabar ma ai katan suna karasa sauran ai kin.

Da sauri Aunty Rafee'at tayi d'akin HAMDAH Dan tun d'azu take ta so tazo taga halin da take ciki Koda tashiga bb kowa cikin d'akin har tajuya zata fita taji motsin ruwa a bayi da Kuma magana had'e da dariya,
Komawa tayi cikin d'akin tazo jikin marfin bayin karar ruwa sosai takeji alamar dai wasa da shi take sai muryar ta da taji tana fad'in
"Tun da gube ba makaranta gudu zanyi Inna Bata sani ba naje lambun Baba na lambu irin ruwan lambun shi yafi dad'i".
Sai takuma sakin dariya.
Baki Aunty Rafee'at tabud'e tare da girgiza Kai "yarinta dangin hauka".
Tafad'a a fili
Bubbuga kofar bayin Aunty Rafee'at tayi ta ce "ke HAMDAH magana kk a cikin bayi to kiyi maza ki fito".
D'aukar boket in ruwan nayi najuye shi a kaina sannan naja zanina nad'aura nafito.

"La Aunty Rafee'at tun d'azu naketa dubaki ban gankiba"
Hannuna tariko tana fad'in "taho Nan kinje kin zauna cikin bayi kinata surutu maza sa kayanki".
Na ce "tom"
Saita saki hannuna tayi waje zuwa can ta dawo lokacin har nagama sa kayan Ina kokarin fita ta ce "yauwa harma kin shiryan nad'auka ai shiririta kk tsaya yi".
Tariko hannuna mukayi waje d'akin Inna muka shiga tana zaune a bakin gado tana ganina tamiko hannu tana fad'in "toho Nan takwara yau Zaki barni".
Na Isa nazauna kusa da ita bakin zanin ta takama tana share 'yar guntuwar kwallar dake kasan idanunta cikin Jan hanci ta ce
"Kizauna lfy a gidan auren ki kiyi taka san-San da Mai sunan Malam in kk ce zakije kina nuna halin Nan naki dukan tsiya zakisha a hannun shi tun da ba imani yake da Shiba barema yaga bb idon kowa ai sai in da hali yy kawai, dole nakira ubanen ku nakuma jaddada musu Sam ban yar da ba, ban yar da da maganar dukaba".
Ido naware gaba d'aya a kan Inna Kamar Mai nazari nad'aura yatsa kan kumatuna Ina d'an girgiza kai na ce "Inna wa kk ce? Mai sunan Malam kk ce Ya SALEEM fakena".
ta ce "E 'yarnan ai na man ce ne ban sanar mikiba ai auren da shi aka d'aura ba da Masa'udu ba".
Huf na mike tsaye na ce
"Allah Inna ban yar da ba kice da Ya Masa'ud za'ayi Mana aure tukun yanzu kice da Ya SALEEM toma nidai wlh ban yardaba nafasa auren".
Nashiga bubbuga kafa a kasa,
Aunty Rafee'at ta kalleta tareda girgiza kai HAMDAH namatukar Bata tausayi idan tatuna cewa kan kishiya za'a kaita yarin yace Mai cikeda d'in bin kuruciya.
Aunty Jaleela ce tashigo d'akin dasauri rikeda waya a kunnen ta tana fad'in
"To Abbu".
sai tasauke wayar tadubi Aunty Rafee'at ta ce
"Wai mufito ga mota najiran mu inji Abbu".
Aunty Rafee'at tamike tsaye tare dafad'in "tom" takamo hannuna ta ce "toh Inna mudai mun tafi"
Inna ta ce "to HAMDAH kin daiji abin da nafad'a Miki kinutsu kizauna ban da rawan Kai Allah yabaku zaman lfy".
Na ce "cap Allah Inna sati d'aya zanyi nadawo tun da dai bamuyi haka da keba".
Inna dai cigaba da share d'an guntun kwallar ta tayi Bata Kuma cewa komai ba Dan har cikin ranta take Jin rabuwar da zasuyi da HAMDAH.

Muna fita cikin parlour Rabi na shigowa da sauri takaraso In da muke tsaye Aunty Rafee'at suna magana da wata cikin kasa da murya ta ce
"HAMDAH Ya Maheer yazo Kinga wayarsa yanzu naje na anso Masa a gun cj".
Da sauri na ce "haba zo muje d'akina mukalli soyayyar".
Nafad'a Ina kokarin janye hannuna dake rike a hannu Aunty Rafee'at".
Itako tadad'a rikeni gam tareda janyoni mukafita.
Tirjewa nayi na ce "Aunty Rafee'at kutafi kawai nikam kallo zamuyi".
"taho muje in kinje can d'in kyayi kallon".
Tafad'a tana turani cikin mota Baki natura a raina nake fad'in "yanzu shikenan kallon soyayyar Nan yashige ni? yanzu idan Ya Maheer yakoma kafin in dawo A'i na kuma zan sake kollon soyayyar oho, gashi kuma ba Ya Masa'ud bane aka Mana auren da shi bare muje muyi soyayyar".
Murmushi ne yasub'uce min lokacin da zuciyata takawo min wani tunani nakuma gyad'a kaina alamar gaskata a bin da zuciya ta bijiromin da shi "sai muyi da Ya SALEEM in kawai".
Sai kuma na kwab'e fuska Ina tantama akan a binda zuciyata keta sakawa da kwan cewa.
Jin karar tsayuwar motar ce yadawo Dani daga duniyar tunanin danatafi
Da mamaki nake kallon gidan wai yausheni muka taso da har mun iso duk da dai nasan sakanin Dass da Bauchi ba nisa Amma dai tafiyar tayimin sauri.

Motoci uku ne aka taho da su d'aya motar data d'auko mu sai wacce tad'auko 'yan'uwan Ummi da Mamie d'ayan Kuma 'yan'uwan Inna ne had'eda makota.
A tare mukashiga ciki kowa sai San barka yake da tsaruwan part in, duk da ai kin Rabin wuni ne amma Bai Hana part in tsaruwa da d'aukar Ido ba, Dan kwararrun ma ai katane sukayi ai kin cikin kuma kan kanin lokaci suka gama Dan ai kine bana mutun d'aya ko biyuba surai wajan goma ne.
Ko zama mutane basuyi ba diraibobin sukace 'yan Dass sufito sumai dasu a cikin Daren suka juya dasu 'Yan cikin gari ma kowa takama gaban ta mukarage dagani sai Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela.

Wanka Aunty Rafee'at tasani naje nayi Ina fitowa Tamika min Mai nashafa sannan na d'au kayan bacci da ta cire min shi nasaka suna zaune nagama kimsawa tsaf.
Duba a gogo tayi "ta ce Jaleela inaga mukwana kawai kin ga yanzufa karfe 12 ko munfita ma ba lailai bane musami a bin hawa gashi Kuma diraiba yatafi".
Aunty Jaleela ta ce "to shikenan".
Nidai gado nahaye ba jimawa bacci yad'au keni.
Washegari Ina salla nakuma komawa gado su Aunty Rafee'at fita sukayi sukaje suka kikkim sa Mata cikin parlour zuwa kichin da bayin parlour duk da dai baiwani yi datti sosai ba zuwan ba'in jiyane gurin yad'an hargitse
Sannan suka had'a breakfast mafi sauki suna gamawa suka komo d'akin Aunty Jaleela tamaso bakin gadon tad'aka Mata duka.
Firgigit nafarka tareda mikewa zaune Ina shafa inda tabugan,
Baki naturo na ce "Toni menaki?".
Ta ce "banza kin kwanta sai sharar bacci kk kin d'auka Nan d'in gidan Inna ne to Nan bb Mai yimiki Dole ke Zakiyi Koda cewa akwai Mai aiki a gidan yazama dole wani abun kezakiyi".
Aunty Rafee'at ta ce
"kyaleta Jaleela tashi kije kiyi wanka kizo kiyi break".
Namike Ina kunkuni nashige bayi.

Bayan nayi wanka nasa kaya nazauna gefen Aunty Rafee'at nasoma cin breakfast in da ta had'amin Ina gamawa ta ce min nakwashe plt in nakaisu kichin nakwashe nakai Koda nadawo ganin su nayi sanye da mayafi nakaraso in da suke Ina fad'in "Ina Kuma zaku?".
"Zo zaunan Nan".
Aunty Rafee'at tafad'a tana nunamin gefen ta,
Nazauna tadubeni ta ce
"To mu zamu tafi sai in an kwana biyu zamu zo muduba ki HAMDAH".
takuma Kiran sunana na ce "na'am". Ta ce "HAMDAH kirage kiuya idan tayi yawa itake janyo kazan ta da safe kina sallah kada kikoma ki kwanta harsai kin share part inki kin gogeshi kin samasa turare, idan Ya SALEEM anan yake to kitabbata sai kin had'a Masa breakfast tukun idan Zaki kwantan nema saiki kwanta,
Kinsan Ya SALEEM yanada son Shan tea in dare to kidage zan kawo Miki kayan kamshi wad'an da ake girka shayi dasu sai kirika girka Masa dasu".
Shuru nayi Ina kallon ta ni duk tunanina ma yatafi kan shara da goge-gogen data fad'a
"Na ce "Kai Aunty Rafee'at duk ni kad'ai zan Rika sharewa da gogewan tap yaushe zan iya".
"Waye da kk tunanin zaizo yamiki to kada Allah yasa ki'iya Aunty Rafee'at kyaleta kada tayi tasan halin Ya SALEEM ai Sarai Allah yasa kullum yarika nakad'a Miki duka tunda ke idan aka fad'a Miki magana bakyaji tashi mutafi Aunty Rafee'at kada tayi".
Aunty Jaleela tafad'a tana mikewa tsaye,
Murmushi Aunty Rafee'at tayi Dan tasan garunsu baya hawa akwai 'yar tsama na sako da sako sakanin su duk da cewa Jaleela tabaiwa HAMDAH tazaran shekaru dad'an dama.

Aunty Rafee'at Bata Bari sun bar gidan ba harsai Dana Mata alkawarin zanyi duk abin da tasani hardama wad'anda takara d'auramin su akarshe, har bakin get narakasu dafari nace ni zanbisu Aunty Rafee'at tace nazauna ita zatazo gobe Ina tsaye harsai da naga sun shiga nape kafin najuya nakoma ciki, nasa kaina zan shiga parlour sai ganin Aunty Na'ima nayi tsaye cikin parlourn rikeda wuka a hannun ta tana ganina tayi kaina..............

HHHHHH🤔 uhum Bari nayi shiru nafece🏃🏻‍♀�

Mommyn Twins ce

*🌺HAMDAH🌺*

*NA*

*RASHEEDA S DIRECTOR*

_(Book one)_

*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍�*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*_________________________________*

MARUBUCIYAR👇🏻
*BA ABIN DA BAN GANI BA*
*INA SANE DA HAKA*
*ALFARMA*
*BAZAWARA CE ITA*
AND NOW👇🏻
*HAMDAH*

*Free page*

My no 08034690723

🅿�6

Kara nakwalla ganin tayi kaina tana juya wukar,
kafin nayi yunkurin gudu harta isoni tashako kwalata tad'aga wukar takawoshi daf da fuskata,
tana cigaba da juyashi,
tsananin tsoro had'eda firgici su suka dirarmun kad'an yarage nasaki fisari a jikina, duk wani barazanar da Inna takeyimin nazata yankani Bata tab'a d'aukar wukan har takawoshi kusadani irin hakaba.

Wani gigitaccen Kara nasake Mai cike da tsananin tsoro nadaddage narike hannunta data da ta shako wuyata da shi, da ƙyar na iya sun kuyar da kaina na yanka mata cizo a hannun, da sauri tasaki wuyana najuya da mugun gudu nashige d'aki, namai da kofa narufe da karfe namurza key, najin ginu da jikin kofar tareda dafe kirjina da ke dukan uku-uku, sai sauke numfashi nake kamar wacce tayi tsere,
zamewa nayi kasa nazauna har lokacin hannuna nadafe a kirjina.
"Nashigesu yaushe Aunty Na'ima tahaukace?".
Nayiwa kaina tanbayar.
Jin tana dukan kofar yasani mikewa zunbur, sosai take dukan kofar tanafad'in
"Wlh da kin tsaya da sai dai yau uwarki tahaifi wata shegiya munafuka ai ni tun sanda nafara ganin ki nasan bakaramar hatsabibiya za'ayi anan ba, ina zama da mijina kk zab'a to kuwa kin zab'i tarwatsewar rayuwarki!".
Tajuya fuuu tafice.
lekawa nayi tajikin kofar na hangi bayanta tana ficewa daga parlourn, da sauri na Isa bakin gado nazauna Kuma dafe kirjina nayi
"dama ashe Aunty Na'ima tahaukace shine Inna tasa aka kawoni gidan Nan Allah bazan zauna ba ko sati d'ayan ma nafasayi".

Ta babban parlour Na'ima tabi tana shiga Ya SALEEM nafitowa da ga part insa, da sauri taja tatsaya tamai da hannunta dake rike da wukar tabaya,
A sannu yakaraso in da take yatsaya daf da ita, kirjin tane yafara dukan uku-uku tabbas idan yasan a bin da taso ai katawa yau kashin ta yabushe,
Dan tana da tabbacin yaga ta in da tafito, ji tayi zuciyarta tama bushe tashirya
d'aukar koma menene zama da kishiya Kam tad'au alkawari wa kanta sai dai a lahira idan a nayi.

Cikeda karfin hali da bushewar zuciya tad'ago kanta,
Ga mamakin ta
saitaga yatsareta da idanunsa wacce
suka kankace suka Kuma sauya kala,da wannan alamar kawai take iya fahimtar yanayin sa idan yana hannu,
"Jiya bakiga miscall
Ina bane".
Yy tanbayar yyn da ida nunsa yake kafe a kanta,
Numfashi tasauke a kasan zuciyar ta
Dan tafahim ci halin da yake ciki Kuma ta tabbata da
shi yakwana,
ta ce "nagani mana".
Ya ce "to meyasa Baki d'agaba Kuma Baki zoba".
Yy maganar fuskarsa a murtuke
tace "Nazo nayi maka meye bayan ka auro wacce zata maye
maka gurbina ai zuwana baya da
wani am fani
meyasa baka kirata
taje tabiya maka bukatar nakaba".
Tafaɗi maganar ne cikin karfin hali da tsoron a bin da zaije ya dawo dan kuwa karshe ita zai ɓare mata, dan dai tasan koshi waye duk da kasan cewarsa mabukaci yakan iya danne bukatar sa har idan ba ita ta neme shiba, in zasu shekara bazai taɓa neman taba, wani bin takanyi tunani da zargin taya yake iya jure bukatar nasa ko dai yanada mai biya masane a gefe tayi duk wani iya binciken ta daga karshe dai duk amma ɗaya ce babu.👌🏻 kariyarsa shine AZUMI. takan gane zallar bukatarsa ne ta ƙwayar idanunsa.
Had'e Rai Yakuma yi yajanyota jikinsa
yad'an ja da baya
yazauna saman kujera tare da zaunar da ita a gefen sa yakalleta
da kyau ya ce
"Kinsan me kk fad'a
kuwa? HAMDAH d'ince zan kira? Me kike nufi ma tukun?".
Kawar da kanta tayi gefe har lokacin hannunta dake rike da wukar namakale
a bayan ta dad'a mikashi tayi tabaya
sosai,
ta cusa wukar tasakankanin kujerar dasuke Kai ta ce "tun da har
kariga da ka a mince a ka kakaba maka ita to mekuma yarage,tun
da Wannan ya'iya kasan tuwa to meye
bazai iya faruwa ba".
Takarashe cikeda gatsali tayun kura
tana kokarin mikewa,
yaki Bata da ma tahanyar sauke hannun sa a
kafad'arta ya dad'a suke fuska tare da tsareta da ido Yana d'an kyakykyafta su.
kallonsa tayi idanunsa duk sun kankance murmushi tayi a cikin ranta, tace "Dama an faÉ—a min zaka kawo kanka da kanka".
Wannan ma wata kofa ce na mafita a gareta.
Kawar da kanta tayi tamike tsaye tanafad'in
"Kyaleni inada abin yi".
Mikewa yy tareda riko hannun ta yakuma d'aure fuska cikin nuna Isa
da bada umurni ya ce
"Kafin kiyi wani ai kin sai kinyi nawa tukun Dan haka muje".
D'an zabura tayi ta
ce "wa ni?ai Wannan Kuma babushi ai SALEEM tun da kaje ka auro
wata ka ajeta cikin gidan Nan to babu
Wannan maganar sakanina da kai sai
dai karika kunshe abinka kokuma kaje can kasaukeshi cikin mararta".

Kansa yashafa tareda furzar da iska daga bakinsa ransa ya b'aci datake Dan gantashi da kanwarsa, duk jarabarsa bazaije gun HAMDAH da bukatarsa ba to ta inama zai fara 'yarda a ka haifeta a gaban idon sa, yakuma rasa dalilin da yasa yakasa iya danne abinsa har kuma yake kokarin nuna mata halin da yake cikin. Dogon tsaki yaja tare da
Fizgo hannun ta yanufi cikin bedroom in sa, suna
shiga yasaki hannunta yanuna Mata gado yy Mata
alama da tahau.

Wani kuka tasake
Mai cikeda zunzurutun makirci da tsigar Jan hankali tazube bakin gadon har da
Jan sheshsheka cikin muryar kukan takefad'in
"SALEEM tun yanzu
harkafara nunamin cewa kakaro aure A she kaima kana daga cikin mazaje masu irin Wannan halin?,nasan Dan ka
kuntatamin kanunamin ni ba komai bace zaka kwanta Dani,wlh
SALEEM idan ka cutar Dani dan kana tunanin kana da wata Allah sai
yasakamin".
Wani kukan takuma sakewa Wanda duk
Wanda yaganta saiyaji tabashi tausayi.

Kallonta yatsaya yi
hanikam tadage take rusar kukan,
Tabbas yasan ko wata mace irin haka yakasan ce da ita bazato bb sammani a karo Mata abokiyar Zama dole tagirgiza, musamman Na'ima da yasan halinta da kafurin kishi wasu matan sukan iya b'oye kishinsu a wasu lokutan Na'ima kuwa batadaga cikin irin wad'annan matan.
Sai dai a yanzu yanayinta ya banbanta da na sauran lokutan yanayin ta nayanzun yabashi tausayi,
musamman dayaga kishin gauraye da rauni a tattare da ita.

Asannu yamaso in da take yazauna
kusa da ita Yana fuskan tarta ya ce
"Meyasa kk son tada hankalin Ki a kan Wannan?, HAMDAH fa kanwatace kisa a ranki HAMDAH an kawota gidannan ne
Dan ta tayaki wasu ai'kace-ai'kace nagida,
duk wasu a bin da
yakamata ita zata
Rika miki to meye
wani abun tada hankali".

"tabbas Wannan
damace".
tafad'a a kasan zuciyarta
Ganin yadage da lallamin ta gashi
Kuma a bukace yake sai tarika basarwa tana jam
Masa aji.

Rungumota yy yashiga kokarin samarwa kansa nutsuwa Nan ma
Bata bashi dama ba bukatar ta dai yacigaba da fad'ar
magana maraddad'i a kan HAMDAH a hakadai harya samu yabiya bukatarsa.
Bayan komai yalafa
tana kwance a gefen sa hannunta na d'auren saman kirji sa cikin salon yaudara da kirsa da kisisina tanarke
murya tasoma magana.

"My SALEEM ni a ganina ace yarin yarnan tazauna a gidan Nan kawai Dan d'an wani 'yan ayyukan da bazasu gagareniba kuma ga Rufa'ila ma tananan, inaga hakan zai iya zame Mata takura kawai a maidata gida in yaso tarika kawo Mana ziyara lokaci zuwa lokaci, Kar yazamo mun takura mata".

Janye hannunta yy daga kirjinsa yamike zaune ya ce
"hakan
bazai yuwuba bakuma zanso su Abbu su sami wanna
labarin ba, hakan bazai yuwuba tacigaba da zama a
hakan kawai".
D'an shuru tayi zuciyarta na kuna, "dama nasan za'ayi haka shegen wani son biyayya da wani nuna shi Mai iyaye sai yarika nuna shi yafikowa yiwa iyaye biyayya".
Tayi maganar a cikin zuciyarta.
Tabbas tasan abune
Mai wuya ya amince da Wannan kudurin natan Dan SALEEM mutun ne
Mai matukar Jin maganar iyayensa da yimusu biyayya ko da bayason a bu
har idan suka nuna Amin cewarsu a kan
a bun tofa shima ya Amin ta.
Tab'e Baki tayi a je a
haka wataran wanna biyayyar taka sai ta
durkushe.

Saukowa yy daga saman gadon yashige bathroom Dan sarkake jikin sa.

★★★★

Tun bayan fitar
Aunty Na'ima dana koma saman gado ban tashiba saima
kwanciyar da nayi tunani narikayi ta yadda zanyi nafita a
gidan batare da taganni ba, Dan ni banji kamar zan
cigaba da zama watarana ciwon haukanta Yakuma
tashi takasheni babu Wanda yasaniba, gara
kawai nakoma Dass gun Inna.
Mikewa nayi nazauna tare zuro
kafafuna kasa namike tsaye,
gaban wardrobe na Isa da zummar d'iban kayana natafi
Dass, daga in da nake tsaye ina iya hango tajikin window kasan
cewar glass in windown da labulen duk abud'e suke,
Mai da marfin wardrobe in da
nabud'e nayi narufe natako jikin windown, Ido naware hango Mai
baiwa fulawa ruwa yanata zagayi cikin fulawa nazuba musu ruwa,
Washe Baki nayi,
Nan take namance dawani batun tafiya,
Dasauri nabar jikin windown nanufi kofa nafita waje,
da sassarfa na Isa inda
Mai baiwa fulawa ruwa yake banyi wata-wataba na wafci tiyon hannunsa nad'agashi sama
Ina sallen murna, ruwan Yana dawowa jikina,
Na ce "la Salele
Ashe dama kazo garinnan kana irin ai kin da Baba na lambu yakeyine?, ai daga yau kullum
zan Rika tayaka Yasin."

Da sauri Salele yamika hannu Yana kokarin amsar tiyon, nasauke hannuna
nayi baya dashi
ya ce "Æ´ar gidan Inna bani nacigaba da ai kina tun oga
bai fito".
Ban saurareshiba saima watsawa furannin ruwa Dana
soma cikeda Jin dad'in ganin abin kaunata ruwa.

Salele d'an Dass ne
unguwarmu d'aya dashi, ta hannun Inna yabi harya Sami aiki agidan Ya
SALEEM.

Duk yanda yaso
nabashi tiyon fir naki na ce nidai yabari zan tayashi
ne,haka narika d'aga tiyon sama ruwan nasauka a kaina dakuma cikin fulawan tsalle narika yi cikeda Jin
dad'i, karshe dai hakura yy yatsaya Yana kallon ikon
Allah.

Ya SALEEM ne tafe Yana gyara d'aurin tsadadden agogon
dake d'aure a hannun sa, Ga dukkan alamu sauri
yake Dan yanayin tafiyar da yake yanuna hakan.
Da sauri wani dattijo dake share mota yy hanzarin bud'e Masa marfin motar tareda d'an risinawa tun kafin yakaraso in da motar take.

Da sauri Salele yamasa kusa da ni yamiko hannu Yana kokarin amsar tiyon tare da fad'in

"Yargi dan Inna bani Kinga Oga yafito".

Da sauri najuyo Jin ya am baci Oga, dai-dai lokacin Ya SALEEM yakarasa sauka daga saman step in sashin sa, da zai sadaka da farfajiyar gidan.

Idona nasauke kan fuskarsa bb ko alamar rahama a tattare dashi, mayar da dubana nayi jikina daga sama zuwa kasa gaba d'aya najike.

Rai b'ace Ya SALEEM yanufo in da nake Yana maganar zuci,
"Kaduba shashanci irin na yarin yarnan da wannan tsanyin tafito tana jika jikin ta yanzu idan mura yakama ta Ina ni za'abari da damuwar siyan magani tun da an kakabamin da muwa, yarin ya saikace wata mayya
wannan uban sanyi tafito tana zuba ruwan sanyi ajikin ta!".

A zafafe ya dunfaro in da nake.
b'ari jikina yasomayi Dan nasan yau Kam banida wani mafaka bamu tare da Inna bare tahanashi dukana.
Wayar dake rike a hannun sane yafara tashi da wani sassanyan sauti alamar shigowar Kira, batare da ya tsaida tafiyar da yakeba yad'ago wayar tareda kallon fuskar wayan,
Sunan Abbu ne yabayyana kan screen in wayar,
Cikin hanzari yaja yatsaya.

Ganin ya tsaya Da sauri na wurgar da tiyon najuya a guje nayi ciki.

Gyara tsayuwar sa yy da kyau ya Kara wayar a kunne tare da yin sallama ya ce "barka da warhaka
Abbu".
A b'angaren Abbu ya amsa Masa da "yauwa".
Sannan Abbu yad'aura da fad'in "yagidan da iyalin?".
Ya ce "alhmdllh".
"Masha Allah, idan kafita yau kaje kanimawa HAMDAH makaranta tacigaba, Bai kamata ace an dakatar Mata da karatunta ba, kayi Mata duk wani abinda yadace inyaso ko zuwa satin samane saita fara zuwa".
Shuru yy batareda yace komai ba, Abbu ya ce "hello SALEEM kanatare da ni?". Tafiya yasoma sannan ya ce "Eh". Atakai ce,
Abbu yaci gaba da fad'in "Sannan kazuba Mata duk wani abun bukata kamadaga kayan abinci da na Sha da sauran su, duk da nasa an Kai wasu jiya Amma yanada kyau ka Kara mata, kadaiji abinda nafad'a ko?".
"Eh". Yakuma fad'a tare da sauke wayar a kunnen sa Jin Abbu yakatse Kiran.
Dai-dai lokacin ya Isa jikin mota yashige ciki Yana am sa gaisuwar da Malam Sule Mai wankin mota keyimasa,
Salele yakaro jikin motar da sauri yarusuna yashiga gaida shi, Rai b'ace yadubi Salele batare da ya am sa gaisuwar da yake masaba ya ce
"Zaka iya tattarawa kakara gaba tunda ai kin ya isheka!". Kuma durkusawa yy kamar zai zuba goigowonsa kasa ya ce "wlh Oga nace tabari ita taki a gafar ceni".
tsaki yaja yafigi motarsa yy gaba.

Ina shiga d'aki bayi nashige dagudu narufe kofar, Jin karar tashin mota yasani d'ale saman toilet naleka ta window, ganin shine yafita sai naduro daga saman toilet É—in, kayan jikina dasuka gama jikewa yatub'e nawurgasu cikin washing machine,
Najanyo towel dake sakale jikin karfe na silver dake gefen bayin Wanda yake mazaunin igiyar shanya,
Nad'aura,nafito nanufi jikin wardrobe Ina tura Baki had'eda kunkuni
"Shi wanna yafiye takuri baya tab'a barin mutun yasake, Kuma an jima komawa zanyi naje nacigaba".
gajeren tsaki naja naji haushin yadda yakatsemin wasana da yanzu inacan Ina kan zuba ruwa Mai dad'i a jikina.
Kaya nasaka nafito parlour.
Kitchen nanufa, Ina shiga nafara bud'e-bud'e ko zan Sami ragowar breakfast in da Aunty Rafee'at tagirka d'azu, Dan zuwa yanzu nafara Jin yunwa, bb ko alamar abinci agun Dan haka nashiga tunanin mezan girka Dan nasawa cikina.

Jinayi kamar ana buga kofa ido nawaro tareda kasa kunne da kyau,
Tabbas kuwa knocking ake, da karfi kirjina yabuga gaba ki d'aya nagama sinkewa dan nasan Ya SALEEM ne ko wancan mahau kaciyar matar tasa,
Jin an cigaba da knocking in, ahan Kali nafara taku na Isa jikin kofar kitchen, ahan Kali nabud'e kofar Saida naleko na tabbatar da babu kowa cikin parlour'n sannan nafito, Jin an daina buga kofar sai naja natsaya cikin parlour'n,
Nakai minti 5 a tsaye, sai Kuma aka cigaba da knocking in.
Zurunayi Ina kallon kofar a yanzu Kam nasan cewa ba Aunty Na'ima bace Dan ko d'azu da tashigo ai Bata tsaya bugun kofa ba Kai tsaye tashigo,
Saidai banada tabbacin cewa ba Ya SALEEM bane,
Wani numfashi nasauke.

Tabbas inko shine bashakka yau saiya b'allani cikin gidan Nan, Yakuma Hana a d'aurani haka zan cigaba da rayuwa a gurgunce.
Hawayene yasoma gangaromin batare da nasan da zuwan suba,

Ahan Kali nasoma tafiya na Isa jikin kofar, hannuna na rawa nad'aura saman handlle É—in rumtse idanuna nayi naja numfashi da karfi sanda na murd'a handle in, nad'an Masa da baya naja kofar batareda nabud'e idanuna ba,
Baya nakuma yi lokacin Dana gama bud'e kofar nabud'e idanuna dasauri Jin yace b.........

Mommyn Twins ce

*🌺HAMDAH🌺*

*NA*

*RASHEEDA S DIRECTOR*

_(Book one)_

*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍�*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*_________________________________*

MARUBUCIYAR👇🏻
*BA ABIN DA BAN GANI BA*
*INA SANE DA HAKA*
*ALFARMA*
*BAZAWARA CE ITA*
AND NOW👇🏻
*HAMDAH*

*Free page*

My no 08034690723

🅿�7

"Barka da warhaka Hajiya".
Nannauyan ajiyan zuciya nasauke a fili,ganin ba Ya SALEEM d'in da nake zato bane, Kai kawai na iya gyad'a Masa Dan har lokacin jikina Bai daina cirawaba,
Mutumin ya ce "Oga SALEEM ne ya yace nakawo wad'annan".
Yafad'a Yana nuna kayakin abinci daki jibge a gifen sa,bin kayan nayi da Ido, katon-katon in taliya da macaroni Indomie Couscous mangyad'a yello da manja shinkafar dafawa da farar shin kafa da semo buhu d'ai-d'ai, Arish Naman saniya Dana kaza wacce aka gyarata aka yayyanka kwai kiret-kiret sai busashen kifi da d'anye Maggi curry time dadai sauransu, kayan d'and'ano kala-kala.
Sai kayan tea suma komai akwai.

Muryarsa na sinkayo Yana fad'in "Hajiya Bari nashiga dasu ciki".
Kai nakuma gyad'a Masa namasa gefe nabashi hanya, buhun shinkafa yad'auka ya ce "Ina kitchen in yake".
Da hannu nanuna Masa kofar kitchen, asannu nakoma cikin parlour nazauna kan 1str,
Jidan kayakin yasoma Yana shiga dasu ciki tas yakwashe yashiga dasu sannan yakimsa komai in da yakamata kana yafito yymin sallama yafita.

Mikewa nayi nashiga Bedroom Jin sautin Kiran sallah dake tashi cikin masallacin kofar gidan,
Direct bathroom nashige nayi alawala nafito nagabatar da Sallah, Ina idarwa namike nanufi kitchen,
Tsayuwa nayi Ina karewa cikin kitchen É—in kallo yakimsa komai yadda yakamata, a sannu na Isa jikin kofar store da ke Nan cikin kitchen É—in.
Natura nashiga Shima yashirya komai yadda yakamata,

katon É—in macaroni nabud'e naciro laida d'aya, nad'ibi albasa 'yan madai-daita guda uku nakomo kitchen,nad'au 'yar madai-dai ciyar roba namaso jikin Fridge Wanda suke jere subiyu babba da karami,
Nabud'e karamin, Jan namace da kayan ciki sai d'anyen kifi aciki, nad'ibi zallar hanta d'an dai-dai sannan narufe Nazo na aje, nad'au wuka na yayyankashi d'an madai-dai ta nawanke nazuba cikin tukunya, sannan nakunna Gas nad'aura tukunyar,
Nayanka albasa guda biyu cikin ukun dana d'ibo nazuba,na b'are Maggi da curry nad'ibi garin citta da kanumfari sai d'an gishiri d'an kad'an,
duk nahad'a nazuba sannan narufe tukunyar.

Babban Fridge É—in nakuma bud'ewa gefe d'aya kayan ganyene irinsu karas kabeji green beans latas da dai sauransu su,
D'aya gefen Kuma drinks ne kala-kala nad'ibi karas da green beans, na yanka karas sirara sannan nawan kesu natsane guri guda,
Tattasai da taruhu na nikeshi d'an dadai, sannan
Nabud'e tukun Yar hantar tanuna, nasauke,
wata tukunyar nad'aura kan Gas nazuba ruwa cikin sa narufe, batareda b'ata lokaciba ruwan yatafasa kasan cewar ruwan bashida yawa,

Rabin laidar Macaroni nazuba cikin ruwan dake tafasan,
Dan nasan ko wuni zanyi bazan iya cinye laida guda ba,
Bayan 7min nasauke najuye cikin 'yar karamar kwando,nawanke tukunyar Dana tafasa macaroni'n nakuma maidashi kan Gas
nasulala mangyad'a d'an dai-dai yadda nake bukata na yanka albasa cikin sa yana soyuwa najuye kayan miyar Dana rigada na jajjaga minti 4 yy nazuba Masa ruwa d'an kad'an nazuba kayan d'and'ano sannan narufe,Saida yatafa sosai na tabbatar da maggi'n Dake ciki sun narke sannan nazuba tafashashiyar hantan namota nakuma maida marfin narufe,
Zuwa can nabud'e nazuba Macaroni nayuya sosai yadda zasu garwaya da juna,sanin Macaroni da hantan sun d'an nuna tun agun tafashe sai na zuba yankakken karas da girinbins iÉ—in narufe sanna narage wutan namasa gefe Ina sauke numfashi.

Lumshe idanuna nayi Jin daddad'an kamshin Dake fita daga cikin girkin,
Banyi mamakin yadda na'iya had'a girkin batare da yabani wuya wajan iya sarrafa shiba,sanin cewa hakan koyar wace ga Aunty Rafee'at Dan duk Randa taje Dass ita takemana girki harta koma, duk sanda take kitchen Ina tare da ita, hakan ne yasa nau ikan girki iri da kala suke zaune cikin kwakwalwata, duk kiwuyata banayiwa girki Dan Yana burgeni sosai akasin wanke-wanke da shara dasuke cimin tuwo a kwarya.

Numfashi nakuma sauke sanda nakalli inda nab'ata,Baki naturo gaba,tuno maganar da Aunty Rafee'at tayimin d'azu dazasu tafi har narakasu bakin get Bata fasa fad'amin ba,

ta ce
"Duk sanda kikayi ai ki kitabbata kin tsaftace inda Kika b'atan kada kibar jikin ki da datti kada kibar muhallin ki da datti kidage sosai wajen saftar jikin ki da muhallin ki,nasanki da kiwuya HAMDAH Dan Allah kirage".

Asannu namaso nafara
Tarkasa kwanunkan danayi amfani dasu nawanke namaida komai mazau ninsa,
Nashare cikin kitchen in har inda ban b'atan bama nakuma gogeshi tsaf,ni kaina gurin yabani sha'awa tabbas tsafta wata abace Mai girman gaske.

Tuni ruwan cikin macaroni'n yatsane nakashe gas in nasauke tukunyar,
Kula Mai d'an girma nad'auka nakwashe girkin a ciki sannan nazuba Wanda zanci a plate,
Parlour nadawo nazauna nasoma cin abin cin.

Ina gamaci namaida plate in kitchen, Nazo nakulle kofar dazai sadaka da babban parlour'n gidan, wan da tanan ne Aunty Na'ima tabi tashigo,kasan cewar akwai hanya nakowani part dake cikin gidan tacikin babban parlour'n,
Nakuma je namurza key na asalin kofar parlour'n,
Sannan nazo nakunnan TV nakwanta saman doguwar kujera, ba jimawa bacci yad'aukeni.

Ban farkaba sai wajen karfe 6, asannu natashi nashiga Bedroom naje nayi alawala Koda na idar da sallar, ina kan sallayar aka Kira Sallahr magriba namike nagabatar da shi.

Bayan na idar shiru nazauna Kan sallayar, ahan Kali naketa jin tsoron danaketa danneshi natasomin ganin guri yafara duhu,
Ban tashiba Saida nagabatar da Sallah'r Isha,
Tuni guri yagama duhu duk da kuwa hasken wutan lantarkin daya haska ko Ina nacikin gidan,Amma duk da hakan acikin d'ar-d'ar nake, gagurin yatsaya cak bakajin motsin kowa.

asannu namike na ninke sallayar na aje nazauna bakin gado gaba d'aya kewar Inna yacikani,
"Ko yatake?".
Nayi maganar afili, sai Kuma nakwab'e fuska "namasan ita batunani takeba tunda da gangan tasa aka kawoni gidan Nan, ai dafarko da Ya Masa'ud tace za'amana aure shine zatasa a canza da Ya SALEEM,
Kuma sati d'ayan zanyi bazan Kara ko kwana d'ayaba".
Nakareshe maganar tareda yin rau-rau da ido.

Najima sosai zaune agun daga bisani namike naje kitchen nazubo a binci, bedroom in nadawo Ina gama ci naje nawanko bakina, Nazo nahaye gado,
Ganin baccin bazuwa zaiyiba kasancewar ban Jima datashi daga baccin ba, sai nafito parlour nakunnan TV don yad'ebemin kewar Inna, sai wajen karfe 11 nakashe TV'n nashige bedroom lokacin Kam bacci ne Tam idona.

Washegari
Bayan nayi Sallah kwanciya nakumayi bani nafarkaba sai karfe 9,
Nasauko a gadon duk jikina a mace Dan baccin Bai isheniba, nadai tashine kawai saboda hud'ubar da Aunty Rafee'at tayimin na baccin safe,
Har nakai bakin kofar bathroom saikuma najuya na wuce cikin window nazuge labule,
"La harya fara". Nafad'a tareda sakin labulen najuya da sauri nanufi waje.

Da dariya d'auke a bakina nakaraso in'da Salele yake,
Yana ganina yy saurin gyara rikon tiyon hannusa,
Na ce "Salele barka da safiya". Namiko hannu Ina fad'in
"Kawo tiyon natayaka".
Cikin sauri ya ce "a'a 'yargidan Inna kirufamin asiri karkisa narasa ai kina, jiyan nanma bansaniba ko Oga yahakura ko Bai hakura ba, idan yanzu Yakuma fitowa yasameki shikenan nakad'e".

Baki natab'e najuya inafad'in "ohon ku Allah yasa akwai ruwa a bayi".

Ya ce "yauwa yimaza kije na bayin kiyi wasanki hankali kwance".

Nidai ban Kuma kulashiba nawuce a bina,
Ina shiga ciki direct bathroom nashige natub'e kayana nasun kuya zuba ruwa a jikina Saida nagaji Dan kaina kafin nayi wankan soso da sabulu nad'auro towel nafito.

Gaban dressing mirror nazauna,
Mai nashafa sannan nayi simple makeup, namike na isa gaban wardrobe naciro wata doguwar Riga robal material nasaka, sannan nasaka d'an kwalin a kaina batare da na d'aura ba nafito.

Kitchen nashiga na kunna gas nad'aura ruwan zafi, bud'e karamin Fridge nayi nad'au kifi guda d'aya wanda dakyar na'iya ciroshi saboda kankarar da yy duk sun manne da junan su, acikin roba nasaka nabud'e tukunyar Dana d'aura Kan Gas nasaka Kofi nad'ibi ruwan zafi nazuba Kan kifin,
Bayan 10 second duk kankarar jikin sa yazamo ruwa nasiyaye ruwan, sannan nayayyan Kashi gunduwa-gunduwa nakuma wankeshi tsaf nad'au wata tukunyar najuye ciki, d'aya gefen Gas in nakunnan nad'aura tukunyar kifin nazuba Masa ruwa d'an dai-dai.

Nazuba citta na yanka albasa nazuba kana nazuba kayan d'and'ano sannan narufe,
Ganin alamar ruwan zafinnan yafara tafasa ne,nad'auko flakes nazuba ruwan ciki tareda jefamasa Lipton Mai citta narufe flakes É—in na'aje gefe.

Nad'ibi taruhu kwalli uku da albasa 'yar madai-dai ciya na jajjagesu,
Sannan nad'ibi kwai guda hud'u nakad'a na juye jajjagen taruhu da al'basan Nan cikin sa,kayan d'an-d'ano nazuba d'an dai-dai saboda kada yayi yawa, saboda idan yy Masa yawa nasan bazai yi dad'iba.

Bud'e tukunyar kifin nayi, saurin rage gas in nayi ganin yy yadda nakeso yanuna luguf ruwan ciki yakafe, juye kifin nayi cikin wani roba Mai d'an fad'i,
Saida nabarshi yad'an wuce yanda zan iya sa hannuna ciki,kasussuwan kifin nacire gabad'aya sannan najuye kifin cikin kwan Dana kad'a namosa,
Tukunyar tuya nad'aura nasulala Mai Saida yy zafi sannan had'in kwai da kifin Nan nazuba ciki,
Haka narika soyawa kamar waina.

Ina gamawa nakimsa gurin, sannan nakwashi breakfast Ina nakaisu parlour,
Ina Zama cikin parlourn naji ana buga kofar shiga Side in Dake ta babban parlour, Ido nawaro sai Kuma nasauke numfashi tuno cewa kofar a kulle take tun jiya,
Lomar a bincin nakai Baki tare da fad'in "ai kigama yi Allah bazan bud'eba sai kin Sami sauki.

Tun daga wanna ranar kullum side Ina akulle take,
Wasu lokutan zanyi tajin ana bugun kofa ta cikin babban parlour sai dai bantab'a yunkurin bud'ewa ba sanin cewa Aunty Na'ima ce.

Yau kwanana shida a gidan hakan kuwa yy dai-dai da sauran kwana d'aya na koma ayadda nasanyawa kaina iya kwanakin da zanyi a gidan.

Acan cikin garin Dass kuwa,
Zaune Inna take a sakargida bisa Kan tabarba, kwad'awa Fatu Kira tayi, cikin hanzari Fatu tafito daga cikin kitchen, tazo in da take tadurkusa taredafad'in
"Gani Inna". Waya Inna Tamika Mata ta ce
"Ungo maza kiramin Mai sunan Malam yau ace kwana biyu banji halin da 'yarnan ke cikiba, Kullum su Idris surika cemin wai lfyrta Lau,
tana tareda wanna Mai zuciya kamar fad'a wutar, wayasan kalar muguntar dayake shuka Mata".

Murmushi Fatu tayi tareda karb'ar wayar, tun ranar da a kakai HAMDAH Inna ke maganar ko wace hali take ciki, acikin kwana biyun sau uku tana baiwa Fatu waya ta ce takira Mata Abbu da Abba ta tanbayesu wai ya lfyr HAMDA'n, duk San da ta tan bayesu sai suce Mata tana Nan lfy.

Number'n Ya SALEEM ta danwa Kira.

Zaune yake bisa kujerar dining table rike da cup in tea a hannusa yanad'an kurb'a, akai-akai yake kallon gogon Dake d'aure a hannun sa,
Na'ima ko na hakimce a gifen sa yayin da itama breakfast in take, aje cup in yy tareda mikewa tsaye, dai-dai Nan wayarsa tafara tsuwa, Mika hannu yy yad'au wayar dake bisa kan dining in,kamar bazai d'aukaba ganin Mai Kiran nasa, haryau a cike da Inna yake Dan gani yake kamar itace tashirya komai gameda auren, har Kiran takusa katsewa sai Kuma yad'aga.

Jin an d'aga kiranne Fatu tayi saurin mikawa Inna wayar tanafad'i
"Gashi ya d'aga Inna".
Tamiko hannu cikin hanza ta karb'i wayar takaishi kunne.

Ta ce "Assalamu'alaikum Kai Mai Sunan Malam haka ake a gidan ku abaka mata kamar an baka mutuwa, ai dai ni Dana raineta ai kakira kayimin godiya, to baiwa HAMDAH'n waya naji lfyrta".

D'an guntun tsaki yaja a dakile ya ce
"Akan wanna ne zakiwani kirani da sassafen Nan to kikirata Mana kiji lfyrtan saini Zaki Kira".

Ta ce "Dan gidan ku in da tanada wayar da zan tan bayeka lfyrtane, kasiya Mata wayar Mana kaga ko zan Rika kiran naka, iye shegen banza Mai bakar zuciya, kada kakawomin shed'ananci yanzu nahayo mota Nazo Bauchi'n".

Tab'e Baki yy tare da fad'in
"Inko ni zan siya Mata waya to lallai bazata rike wayar ba, yaran yanzu ba'a barsu sun rike wayar bama yasuka kare bare an barsu".

Salati Inna tayi ta ce "yo Mata agidan auren ta harwani dokar rike waya za'ayi Mata? Ai dai duk wani tarbiyyar daya kamata ayimata a gida duk ammata, yanzukam tarbiyyar shizata bazashi wajen yin biyayyar aure,maza Bata wayar ko Kuma in d'ago ubanka Dana Isa da shi yakawo Mata".

Kashe wayar yy yajefata cikin aljuhu yajuya yafara sauka daga step in dining in,
Na'ima da tun farin wayar tabaza kunne tana Jin dagar dasuke, wani murmushi najin dad'i tasake ko ba komai hakan ma yy Mata, takuma gas kata cewa SALEEM natane ita d'aya Dan tanada kyakkyawar tabbaci akan hakan, Dan saboda sanin ko waye SALEEM in da Kuma yanda akayi harta sameshi.
Mikewa tayi cikin kirsa da nufin yimasa rakiya kafin ta an Kara sai ganin fitarsa tayi.

Yana fita motarsa yashiga Yana dai-daita zamansa Kiran Abbu yashigo wayarsa, yad'auka tare da yin sallama,
Abbu ya amsa tare da fad'in
"Akan me Inna zatace kabaiwa HAMDAH waya kk to maza ka kirata ka had'asu".

Numfashi yaja kana ya ce
"Abbu bana gidane idan nadawo zan had'asu".
Ya ce "kana dawowa ka tabbata ka had'asu".
"To".harzai sauke wayar yaji Abbu nafad'in
"Kadai gama shirya Mata komai ko Monday Mai zuwannan yakamata tafara zuwa makaranta".
Dafe kansa yy shi gaba d'ayama yagama mancewa da wanna zance, "Eh". yace sanna yakatse Kiran yaja motarsa yabar gidan, tsaki yarika saukewa akai-akai yajuya akalar tafiyar tasa izuwa wata makaranta dake Nan cikin unguwar tasu, sai dai da d'an rata sakanin su,
Yab'ata lokaci sosai acikin makaran tar Dan Saida yagama Mata komai kafin yafita ransa a b'ace Dan yy lettin zuwa Office.

A hanya yakira Jamilu wani tela ne Wanda yake Bababa plaza Dake cikin kasuwar winti, bayan sun gaisa ya ce
"D'inki nakeso daga Nan zuwa yamma".
Jamilu ya ce "an gama kakawosu yanzu za a fara".
Ya ce "Uniform ne Kai zakaje kasiyo". Yafad'a Masa Sunan makaran tar yace yagane kalar uniform É—in su,sannan yace
"To ai ma bawani d'inki Mai wahala bane awa 3 yy yawa, to Amma bansan girman jikin wacce za'ayiwa d'inkin ba".
Ya ce "bawata babba bace 'yar kimanin shekaru Sha hud'u zuwa Sha biyar ce,batada kiba sosai Kuma ba arame takeba, tanada d'an tsawo dai ba can sosai ba".
Tuni Jamilu yad'auki komai da yafad'a Masa na yanayin girman jikin ta a kwakwalwar sa, kasan cewar kwararran telane, suna gama wayar yatura Masa kud'i wanda zasu ishesa harda saura Mai yawa.

Da misalin karfe 6 yataso daga Office Saida yabiya shagon Jamilu ya amshi d'inkin kafin yanufo gida, Yana shiga gida part in ta yanufa, saboda Kiran da Abbu yy tamasa bayan wayan dasukayi da safe, Kuma yasan fitinar Inna ce kesa Abbu Kiran nashi.

Tura kofar yy yajishi gam, akufule yashiga bubbuga kofar Rai b'ace yakwaso gajiya kamata yy ace Side É—in sa yanufa yawatsa ruwa yahuta, Amma fitinar 'yar tsohuwar nan yasashi dolenshi sai yazo Nan gashi Dan sabar rainin wayo takulle kofar ko mayune cikin gidan ba mutaneba.

Ina tsaye gaban mirror bayan fitowata daga wanka,Jin kakar bugun kofar da ake yasani saurin karasa saka doguwar rigar baccin nada soma sata a jikina,
Nayi saurin bud'e wardrobe na d'au wata Yar karamar gyale nasaka a kaina, duk abin da nake cikin rawan jiki nake,
Gaba d'aya na firgita da kalar bugun kofar da ake,
Sorona d'aya kada ace Aunty Na'ima ce ke kokarin b'alla kofarnan tashigo ta kasheni, sabar firgici ban San San da nafito cikin parlourn ba,
Shiru nayi Jin bata kofar babban parlour ake bugawa ba, ta asalin takofar Side in ce, ahan Kali nasoma taku duk da kuwa kwab'e ni da zuciyata take Kan cewa Na'ima'n ce tazo ta wanna kofar Dan nabud'e tasamu tashigo, tsayuwa nayi daf da jikin kofar Jin shiru an daina bugawa,
D'an d'aga muryata nayi na ce

"wanene?".

Cikin tsawa ya ce "Zaki bud'e kofarne ko ya!".

Wani irin kad'awa anjin cikina yy da sauri na murza key in tareda murd'a handle, turo kofar yy da karfi kasan cewar Ina daf da kofar Kuma nad'an sun kuyo da kaina yasa kofar yabigi goshina, baya nayi luuu tareda saka Kara nadafe goshina,
Natafi da baya luuu nagaru da gijin garu still kaina yakuma garuwa da jikin garun, wani Karan nakuma sakewa tare da rike kaina da hannuna biyu Ina jujjuya Kan Jin wani irin azabar zafi da sarawar da Kan keyi, shigowa cikin parlour'n yy cikin d'aga murya ya ce "I...........

Mommyn Twins ce

*🌺HAMDAH🌺*

*NA*

*RASHEEDA S DIRECTOR*

_(Book one)_

*_________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍�*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻

https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association

*_________________________________*

MARUBUCIYAR👇🏻
*BA ABIN DA BAN GANI BA*
*INA SANE DA HAKA*
*ALFARMA*
*BAZAWARA CE ITA*
AND NOW👇🏻
*HAMDAH*

*Fee page*

My no 08034690723

🅿�8

"Idan Baki rufamin bakiba saina Kuma had'a Kan naki da garu yarab'e gida biyu!".
Cikin hanzari nakai hannu Kan Baki na hawaye yasoma zarya Kan fuskata.

Cikin Jin azaba da sarawar da kaina keyi Dan bakaramin buguwa Kan yy ba,nakai hannu tabayan keyana takasan mayafin kaina nacusa hannu nashafo gun, tareda Ciro hannuna nawaro Ido Ina kallon hannun Dan ganin ko gun yayi jini, Dan irin rad'ad'in da gun yake min yafimin kamada Kan fashewa yayi,
Na yarfe hannu hawaye nazuba na ce
"Wayyo Allah kaina".

Harara yawatsa min lokacin da yakarasa Zama Kan kujera 2str, Niko matsawa nayi na Jin Gina da jikin garun Ina ci gaba da masar kwalla.

Wayarsa ya Ciro yadaddanna
Fuska a murtuke yakalleni tare da fad'in.

"Zonan! Kuma kafin ki iso Nan kishare wad'annan hawayen gulmar tun Kan in samo Miki nagaske".

Tafin hannuna nakai fuskata nashare hawayen natako a hankali Nazo in da yake, a kasa nazauna dirshen a gaban sa,
Wayar yamikamin batare da yy magana ba,
Mika hannu nayi na amsa ido natsurawa wayar araina nace
"To nikuma me zan yi dashi".
D'ago kaina nayi nakallesa,
Ganin yatsareni da nashi idon kana yakuma kalli wayar,
cikin hanzari namayar da ido na Kan wayar ganin yadad'a tamke fuska,hannuna na rawa Dan bansan me yake nufi da bani wayarsa ba,Niko gyara rikon danayiwa wayar nayi da kyau ganin kamar zai fad'i saboda rawar da hannuna keyi,
Sanadin haka kuwa sai hannuna yad'an matse gefen wayar Nan fuskar wayar takawo haske.

Da mamaki nake kallon Number Mai d'auke da sunan Inna, 20 second shine adad'in dad'ewar d'aga Kiran da Inna tayi,cikin sauri nakai wayar kunne cike da zakuwa da son Jin muryar Inna ta,
Jiyo muryarta nayi tana fad'in
"Yo d'annan ka Kira waya Ina magana kayi burus Dani, wannan irin bahagon halin nakadai Allah shigyara".

"Laa Inna nicefa".
Nafad'a Ina washe Baki,
Inna tace "yo kema kyayi shiru kinaji nayita b'ab'atu ni kad'ai, yagidan kinadai lfy ko? tun yaushe nakesa akawo Miki waya naji lfyarki Abu yagagara,shikuma wanna Mai bakar zuciyar tun farar safiya nace yabani ke yatsaya yimin halin NASA sai yanzu yaga dama kenan".

"Ayya Inna ai da bakisa an kawomin bama nida gobe zan koma ko kin mance gobene zancika sati d'ayan,dama ai cemiki nayi sati d'aya zanyi nadawo".

Cikin tsigar kwantar da hankali da lallami
Inna ta ce
"A'a HAMDAH kada kizo kinji?' kibari ni zanzo".

"Nidai Allah Inna bazan zauna ba gari na wayewa zan dawo garama kisani Kuma n."

Fizge wayar yy batare da yabari nakarasa abin da zan fad'an ba, ya ce "ko yanzuma kihau mota ki koma, akan shirmen banza kuka tsaya batamin Kati".

Mikewa nayi tsaye naturo Baki tare da yin magana cikin zuciya
"Mugu ai ko baka cebama komawa yazama Dole yaushe zan zauna Kai da matarka kukasheni bb wan da yasani".

tsaki yaja tare da jefa wayar cikin aljuhu.

Niko mayafin kaina daya zamo saman kafad'a ta nagyara, kasan cewar bb d'ankwali kaina ga Kuma gashina dayake atsefe najuya Ina kokarin barin parlour'n.

Kallon laidar dake gefensa yy wan da yashigo rike da shi a hannunsa, ya ce
"D'auka kib'ace min da gani Monday me zuwa Zaki fara zuwa makaran ta Allah yasa naga wani abinda ba dai-dai ba kiga abinda zan Miki".

Da sauri nad'ago kwayar idona nasauke kanshi Jin abinda yafad'a, saurin cire idan nayi akansa ganin yadda yawasomin wani kallo, Baki nakuma turawa nasun kuyo nad'au laidar irin na shopping innan ne Mai d'an girma najuya nayi hanyar bedroom Ina kunkuni kasa-kasa.

"Cap nida ba fita nayi amakarantar danake ba mekuma zai sani Kuma shiga wata makarantar, nida gobe zan koma ma babu wata makaran tar da zanje".

Tura kofar bedroom nayi Ina shiga nayi wurgi da laidar a Kan gado,wasu daga cikin kayan ciki suka fita suka zube Kan gadon,
Nahayo gadon tareda janyo laidar nafidda sauran kayakin ciki.

Uniform ne kala hud'u biyu iri d'aya biyu iri d'aya d'agosu nayi Ina dubawa
"Wato na islamiya da boko kenan".
Tab'e Baki nayi nawurgasu can gefe, sauran kayan ma kamarsu sandal da safa da dai sauran kayan bukata na makaran ta duk nakwashe natura cikin laidar nawur gashi can gefe, sauka nayi a Kan gadon nazaro akwati guda d'aya cikin set in akwatunan dasuke jere saman wardrobe,kana na bud'e wardrobe in nasoma jidar kayana Ina sasu ciki, Saida nacika cikin akwatin dam sannan naja zip narufe na aje gefe.

Bathroom nashiga nayi alawala Nazo nagabatar da Sallar magriba.

A b'angaren Inna Jin HAMDAH tayi shiru yasata fad'in "ke HAMDAH kinajina ko? kizauna ni zanzo".
Jin shirun yy yawa saita ciro wayar a kunnan ta tana fad'in
"Fatu dubamin naji tayi shiru".
Karb'ar wayar Fatu tayi tace "Inna an kashe ne".
Gyara Zama tayi ta ce "maza sake kiramin shi".
Tom tace Nan takuma maida Kiran yayita ringing harya yanke ba'a d'agaba takuma Kira har sau uku Bai d'agaba.

Shiko Ya SALEEM shigowar Kiran nafarko wayar tana hannun sa Yana kallo Kiran har ta yanke,aje wayar yy kan bedside yanaji wasu Kiran sukata shigowa akai-akai, yamike yashige bathroom dan dama Shirin wanka yake.

Fatu takuma duban Inna tace "Inna har yanzu ba'a d'agaba".

"Toyi maza ki kiramin Shu'aibu nasan halin 'yarnan Sarai tun da tace zata dawo tofa sai ta dawon".
To tace kana ta talalub'o Number'n Abba ta danna mishi kira,aka ko yi rashin sa'a numbern Bai shigaba da alama duk in da yake to akwai karancin network agon,
Nan tasanar wa Inna Shima Bai shigaba,ta ce "to kira Idris".
Tana dannan Numbern Abbu kuwa yashiga bugu d'aya anabiyu yad'aga Tamika Mata wayar, ta amsa tare da gyara Zama takai wayar kunnen ta.

A b'angaren Abbu sallama yy yad'aura da fad'in "barka da da dare Inna".

Ta ce "yauwa".

Wani gaisuwar yake kokarin Mata tace "Idris bar gaisuwar Nan, yanzu mukayi waya da yarin yarnan HAMDAH tace wai gobe zata dawo nasan halinta kaje kahanata zuwa ni zan zo daga baya".

To Abbu yace yasauke wayar Yana murmushi afili yace "HAMDAH kenan 'yargidan Inna".

Washegari Ina idar da sallar asuba namike Kan sallayar daniyyar in d'anyi bacci kafin gari yy haske natafi Dan nasan har idan nahau gado naji laushi tofa bazan tashi da wuriba,
Ina kwan ciya kuwa bacci Mai dad'i yad'au keni,ban farkaba sai wajen karfe 11 da sauri namike Ina mamakin tsawon lokacin danayi Ina baccin, bathroom nashiga yau ko tsayuwa wasa da ruwan banyiba nayi wankan nafito,
Mai nashafa sai 'yar pauda da man Baki,
Naje nad'au Kaya da tun jiya nashirya Kaya cikin akwatin nacireshi na aje saman bedside drower,riga da zanine na atamfa atamfar Reed and blue ne sai d'an rasin black and white ajiki rigar 'yarcas da ita,
Nasaka rigar wacce tazaunamin d'amas ajiki nad'aura zanin, sannan nad'au d'an kwali da gyale, nakoma gaban mirror nad'aura d'an kwalin tare da fesa turare, nayafa gyalen a kaina kallon agogon dake like ajikin garun d'akin nayi karfe 12,na Isa inda akwatin yake na janyoshi nanufi parlour.

tsayuwa nayi a tsakiyar parlour'n nakai hannu Kan cikina dake tad'an murd'amin tun sanda nashiga wanna har nafito nasoma Shirin kasan cewar kad'an-kad'an yakemin a lokacin nasa araina bazan tsaya cin abinciba saina Isa Dass,
Yanzu Kuma jinayi cikin yanad'an murd'amin sosai.

Aje akwatin nayi nanufi kitchen ruwan Lipton nad'aura Kan gas sannan nafasa kwai guda uku nasoya, cikin sauri nakamla had'a breakfast in kasan cewar bawani mai wuya bane,na tattaro nakoma parlour.

Motar Abbu ne yy parking a farfajiyar gidan, da sauri Ya SALEEM dake zaune cikin babban parlour yamike yanufi waje sanin yasan da zuwan Abbu'n shiyasa Bai tafi office ba,tun ajiyan da Abbu sukayi waya da Inna yasanar masa cewa Inna ta aikeshi gun HAMDAH Yana zuwa gobe in Sha Allah, Kai Ya SALEEM ya girgiza tare da tab'e Baki Wai ace babba kamar Abbu Wai shine Inna zata aika wannan Æ´ar tsohuwa da fitina.

Cikin hanzari yakarasa in da Abbu yake tsaye suna gaisawa da ma ai katan gidan, ritsinawa yy cikeda girmamawa yashiga gai dashi tareda yimasa barka da zuwa,kana yamike tsaye ya ce "Bismillah Abbu".
Yafad'a tare da nuna Masa hanya,Yana gaba Abbu na biye dashi suka nufi Side in HAMDAH, suna Isa bakin kofar part in yad'aura hannunsa Kan handle ya murd'a tare da tura kofar.

Da sauri nad'ago nazubawa kofar Ido Jin karar bud'e kofar dai-dai lokacin yasanya kafarsa yashigo,
baya yaÉ—anyi sai Yakuma jawo kofar yadaÉ—a bud'eshi sosai yakuma ja da baya cikin girmamawa yace
"Bismillah shigo Abbu".
daallama Abbu yasanyo kansa cikin parlour'n, da sauri namike tsaye ganin
Wanda suke tare da shi Baki nawashe na ce "laa Abbu sannu da zuwa".
Murmushi yy suka karaso cikin parlour'n yazauna saman kujera,shiko Ya SALEEM kasa yazauna gefen Daman shi,cike da Jin dad'in ganin sa namaso nazauna kasa gefen hagunsa.

D'an matsowa na kumayi tare da gyara Zama nace

"Ina kawana Abbu ya su Mamie da Ummi'na".

Murmushi Mai fad'i yy ya ce "duk suna lfy sunce nagaidaki".

Kai na gyad'a nace "to su Nusaiba da Fauzan su basuce a gaida niba?". Nakareshe maganar tare da d'an langwab'ar da kana gefe.
Yace "na mance ne su suka Fara cewa nagaida ki kafin su Ummin ku".
Murmushi nayi cike da Jin dad'i da kewar Æ´an kannena.

Kallon a kwatin dake a je tsakiyar parlour'n Abbu sai kuma ya jinjina kai akasan zuciyar sa kuwa yakefad'in
"Ƴar gidan Inna kenan yarinta a kwai dad'i in ban da yarinta waza a Kai gidan aure yace sati
guda zaiyi yakoma gida".
Afile Yakuma murmushi yayi kana yamai da kallon sa kaina ya ce "HAMDAH wannan jakar Kuma meyasa a ka fito dashi Nan ki kaishi d'aki Mana".

Muskutawa nayi na É—an kalli a kwatin turo baki gaba nayi nace " Abbu Dass zan tafifa".
Gyara zama yy cikin dabara da hikima irin tasu ta manya yace
"To yanzu tafiyar zakiyi kenan?".
Kai nagyaÉ—a alamar Eh kana na É—aura dafaÉ—in "Amma sai katafi kafin natafi".
É—an shiru yayi tare da É—an tsuramin ido sannan
Yace "to meyasa zaki tafin?".
da sauri nace "Abbu ni kawai tafiya zanyi gun Inna, ni É—aya kawai kamar mayya ni dai tsoro nakeji, da daddare sai na rufe idona da karfi kafin nayi bacci, kuma ma ai sati É—aya nace wa Inna zanyi kuma yaune satina É—ayan".

Kallonsa ya maida kan Ya SALEEM da yayi kicin-kicin da fuska yana ai kamin harara kamar zai kai min bugu na tabbata in badun Abbu na gunba bb abin da zai sa bai kai min hannun ba.
"Meye ke in ba mayyar ba".
Yayi maganar a kasan zuciyarsa,tare da É—an jan guntun tsaki a file.
Niko baki naturo tare da É—an murguÉ—a shi ganin yan da yawani murtuke fuska.

Gyaran murya Abbu yy kana yazura hannunsa cikin aljuhun rigarsa yazaro waya yami kamin yana faɗin "Ungo karɓi nakine duk san da kkson jin muryar Inna sai ki kirata duk Number'n ƴan uwan ki yana ciki, wayar ita zata rika tayaki hira basai kin tafi ba kin jiko? Inna'r ma tana zuwa kuzauna a nan tare".
Da sauri na karɓi wayar cike da tsananin jin daɗi narika juya wayar a hannuna cikin muryar dariya nace
"Ngd Abbu".
Wata Æ´ar karamar laida yamikomin mai É—auke da kwalin wayar da i'giyar cj, na amsa.
Yace "to tashi ki É—au jakarnan kimai dashi ciki".
Tun kafin yakarasa namike da sauri yayin da ida nuna ke kan wayar ina ta lallatsa shi bakina kuwa yakasa rufuwa naja a kwatin nanufi bedroom cike da farin ciki.

Numfashi Abbu yasauke kana ya maida hankalinsa kan Ya SALEEM yace
"Shi yaro ɗan lallamine idan kace zaka tan ƙwasashi da karfi sai yakarye batare da yayi yan da kakeso ɗin ba, idan kabishi cikin dabara da lallami to fa bazaka taɓa shan wuya wajen sai tashi kan hanya ba".
Shidai Ya SALEEM kan sa yaÉ—an dukar kasa batare da yace komai ba.
Abbu yaci gaba da faÉ—in
"Gidan dai lfy babu komai ko ya ita É—ayan iyalin taka?".
"Lfy lau tana ciki batasan kashigo ba".
YafaÉ—a yana mikewa tsaye
Abbu yace "ƙyaleta in bacci take ka gai data in tatashi."
Kofar babban parlour da ke nan cikin parlour'n yanufa yana faÉ—in
"Ba bacci takeba".

Ina aje akwatin najuya nakoma parlour'n ina jin wani irin daÉ—i a raina bakaramin daÉ—i naji da Abbu yabani wayar nan ba har na mance da batun tafiya Dass can gefe nazauna saman 1str ina cigaba da latsa wayar,
Zamana baifi da 4min ba su Ya SALEEM suka shigo yana gaba Na'ima na biye da shi sai wani yamusa fuska take da kaga yanayin yan da take tafiyar da yamusa fuskar da take zaka san dole a kayi mata,a kasa gefen Abbu in da É—azu ya zauna nan yakuma zama,itama ta zauna gefen sa.

ÆŠan sun kuyar da kai tayi cikin yamusa fuskar da take tace
"Ina kwana". tafaÉ—a a gajarce.

Abbu da bai ma fahimci yanayin taba ya amsa cikin sakin fuska kana ya É—aura da faÉ—in
"Kuna lfy ya gidan da bakuwar taku?". "Lfy lau". tafaÉ—a can kasa.

gyara zama Abbu yy kana yace
"Masha Allah".
sai kuma ya É—an yi gyaran murya yaci gaba da faÉ—in
"To madalla acigaba da hakuri dai dan yanzu kece babba ga HAMDAH nan kanwar kuce sai kunyi hakuri da wasu lamuran ta,
mu samman ke da kullum kuna tare da ita a gida dole wasu
a bubuwan ke zaki rika É—aurata kan hanya,
ki ɗau keta tamkar kanwarki idan kinga tayi wani a bin da ba dai-dai ba ki nuna mata rashin dacewar shi, ita bakuwace a wannan ɓangare dole sai an nuna mata wasu abubuwan, sannan HAMDAH yarin yace sai kunyi hakuri da ita,
Allah yabaku zaman lafiya da hakuri da juna".

"Amin". Ya SALEEM yace.

Itako wani irin kallon shekeke tabi Abbu da shi sai kuma tayi wani irin shu'umin murmushi.

akasan ranta kuwa faÉ—i take
"Uhum dole kace yarin yace ita naga yarin yarce kaɗauko ta ka kawo ta gidan nan a matsayin mata, wai ni za'a kife bai-bai kuma ai kanwata bazata taɓa shigowa gidan nan a matsayin da nake ba, kishiya-kishiya ce Allah yasa wake tazamo kanwata".

Shiru tayi da zan cen zucin da take ganin Abbu ya mike yana faÉ—in

"To nabarku lfy a kula a daÉ—a yin hakuri da juna".

Murmushin yake tayi tace
"To Abbu mungode Allah yatsare a gai da gi da".
tafaÉ—a tare da mikewa tsaye tanufi kofa.

Ni duk a bin da suke ma sama-sama nake jinsu gaba É—aya hankalina nakan game in da nake bugawa a wayar, ganin Abbu yamike ne yasani mikewa da sauri na a je wayar nace
"Abbu tafiya zakayi?"
Nayi maganar a marairaice.

Murmushi yy kana yace
"Eh zan tafi daga nan office zan wuce".
Nace "to kagai da su Ummi dasu Fauzan".
Yace "zasuji, ranar juma'a su Fauzan in zasuzo suyi miki kwana biyu ranar Lahadi su koma sabo da makaranta".
To. nace cike da jin daÉ—i, yayimin sallama suka fita.

Suna fita na koma nazauna na ɗau wayar Game in da naketa bugawa tun ɗazu nakashe, nashiga contact numbers in ciki nafara bi ina dubawa duk lambobin mutanen gidan mu yana ciki Number'n Inna nashiga laluɓowa cike da zakuwar jin muryarta na dannawa Number'n nata kira.
Bugu É—aya a nabi taÉ—aga da tare da yin sallama
ko sallamar da take ban amsaba cikin zakuwa da É—onkin jin muryarta nace
"Inna nice Abbu ya siyamin waya".
NafaÉ—a cike da zallar jin daÉ—i.

Washe Baki Inna tayi tana dariya tace
"Kai to madalla gaskiya Abbu ya ƙyauta kuwa, yauwa kinga yanzu zan rika jin muryar ki batare da na kira wancan mai bakar zuciyar ba, dama nima nace yau zan zo to yanzu kam hankalina ya ƙwanta yanzu dai sai nakuma sa rana zan zo".

Da sauri nace
"Inna kizofa".tace
"Zan zo"
Hira muka buÉ—e sosai.

A can waje
har jikin mota Ya SALEEM yaraka Abbu,
Abbu ya buÉ—e marfin motar yashiga yana dai-dai ta zaman sa yakalli gefen sa, numfashi yasauke tare da mika hannu yaÉ—au wata laida dake kan sit É—in gefensa yamikowa SALEEM yace
"Ungo kaiwa HAMDAH Mamei'n kuce tabani na bata kaga na mance sai yanzu da nagani". To yace tare da
Karɓar laidar, Abbu yatada motar yy masa sallama mai gadi yabuɗe masa get yafita,har sai da motar Abbu yafice a gidan kafin yajuya
part in sa ya nufa rike da laidar yana shiga bedroom ya aje laidar saman bedside drowar yashiga bayi wan ka yayi a É—an gaggauce kana yafito ya shiriya cikin wani danda tsatstsiyar yadi kalar lemon grind wan da tasha ai ki da farin zare da É—an ratsin red a jiki kaÉ—an.

Yasaka hula kalar kayan yaÉ—aura wata tsadaddiyar a gogo a hannunsa, sai bakar takallimi feshe jikinsa yy da turaruka masu daÉ—in kamshi da kasha,
wayo yinsa yaÉ—iba dasuke kan mirror yazura É—aya cikin aljuhu É—aya kuma yarike a hannunsa,
Ya É—au jakar system É—in sa yarataye a kafaÉ—ar sa kana yaÉ—au makullin mota yafita,

Direct parking lot yanufa da É—an sauri kasan cewar yaÉ—an makara da zuwa offece É—in, yashige motar yafice a gidan.

Bayan mun gama waya da Inna
Number'n Aunty Jalela dake kusa da nata na dannawa kira sai da yakusa katsewa kafin ta É—aga.

Jin ta É—aga yasani faÉ—in
"Hello Aunty Jalela nice HAMDAH ce".
tace "nasani ai ya akayi ya rashin jin magana?".
Baki na turo gaba cikin murguÉ—a bakin nace
"Nidai inajin magana dan nakiraki na faÉ—a miki abbu yasiya min waya shine zakice min haka, ko Ummi na ban kira ba ina gama waya da Inna naga Number'n ki kusa da nata shinefa na kira".
Nakarasa cikin É—an É—aga murya da gatsali kamar dai yanda kullum idan muka haÉ—u sai munyi faÉ—a.

Tace "To an ji Æ´ar masu baki ko yaushe ne zaki nutsu? Allah yasa ma kina tare da wan da zai gyara miki maza Allah yasa kiyi masa halin ya nakaÉ—a miki duka".
Baki nakuma turowa nace
"Daga kiran ki sai ki kama yimin sururu toma bazan sake Kiran kiba".
nakatse kiran ina ci gaba da mitar.

Cikin tsananin zakuwa da begen Aunty Rafee'at na danna Number'n ta
bai daÉ—e yana ringing ba ta É—aga
sinkayo muryarta nayi daga cikin wayar tana faÉ—in
"Ah Æ´argidan Inna kice dai har wayar tashi hannunki".
Dariya nayi nace
"La Aunty Rafee'at dama kinsan nice?".
Aunty Rafee'at tayi murmushi mai sauti kana tace
"Nasani mana ai É—azu Abbu yakirani da layin yace min nakine".
dariya nakuma yi dafaÉ—in
"Ai É—an É—azu kaÉ—an Abbu yakawomin wayar".
tace "Kinji daÉ—i kenan?" nace "Naji daÉ—i sosai Aunty Rafee'at".
tace "Ah to madalla lallai yaukam kice waya zatasha danne-danne".
dariya mukayi gaba É—ayanmu.
Cikin dariyar nace
"Aunty Rafee'at kince zakizo kuma bakizoba".
"Zanzo a cikin satin nan, ina fata dai duk abin da nace kirika yin nan kinayi".
É—an shiru nayi tace
"Iye HAMDAH kinayi kuwa?".
nace "Eh". tace "An ya kuwa?". nace "Allah da gaske"
tace "To har da girkawa Ya SALEEM tea in da nace".
É—an shiru na kuma yi sai kuma nace
"To zan yi idan yazo zan girka masa".
"Yauwa ko kefa ko bai zobama ki girka ki kai masa É—akinsa kuma É—an abin makulashe idan kika girka shima kiÉ—an rika kai masa ko bai cibama watarana zai ci".

Nace
"Kai Aunty Rafee'at Aunty Na'ima cefa ke yimasa girki"
Tace "Ina ruwan ki da Na'ima ai bata isa ta hanaki girka masa ba kafin ya santa ai ke yafara sani kin fita kusan ci da shi ke dai kiyi abin da nace miki".
To nace.

nan muka ɗan taɓa hira daga bisani mukayi sallama jin an tada salla a masallaci yasani mikewa nanufi bedroom.

Ina shiga na a je wayar saman mirror sannan na nashige bayi ruwa na kunna yafara sauka cikin bath kana nasoma tuɓe kayan jikina ina gamawa nashige cikin bath ɗin da sauri dan na zaku najini cikin wuwan wan da yacika cikin bath ɗin tam.
zama nayi cikin ruwan naɗan ƙwantar da bayana na ɗago kaina nayi pillow da bakin bath ɗin ruwan yakawo min har haɓana.

Lamo nayi a cikin ruwan inajin daÉ—in yan da ruwan yake ratsa ko ina na jikina wutsilwutsil haka narika yi kamar mai yin iyo cikin kogi, nakai minti 30 a cikin ruwan kana namike na É—au soso da sabulu wanke jikina koda nagama wanke lungu da sako najikina ruwa na sakarwa kai na daga tsayen da nake ya wanke kunfar sabulun, kana nafito daga cikin ruwan bawai dan nagaji da ruwan ba sai dun ganin lokacin salla natafiya,
nazaro towel naÉ—aura a kirjina al'wala nayi kana nafita a cikin bayin.

Gaban wardrobe na isa na buÉ—e naciro zani na kunce towel É—in naÉ—aura zanin sannan na mai da towel É—in bayi nashanya na dawo É—akin nazura hijabi na shin fiÉ—a sallaya na tada sallah.

Koda na idar nacire hijabin tare da naÉ—e sallayar na ajesu ma ajin su,
gaban mirror na isa nazauna,
mai na shafa naÉ—an murza pauda a fuskata tare da É—an goga man baki kan lip ina kana namike naje naciro wata doguwar riga robal material mara nauyi nazura bayan nasaka pan da bra,
gaban mirror'n na dawo na feshe jikina da turare kana naÉ—au wayata wan da duk abin da nake ida nuna na kansa naje bakin gado nazauna naja pillow nakwan ta,
nan nafara latsa wayar.

Number'n Ya Masa'ud na laluɓo nakai wayar kunne na gyara ƙwanciya ta lokacin da naji layin tashiga,
har kiran ta katse ba'a É—aga ba, kuma mai da kiran nayi harna cire rai da É—aukar wayar nasa jin wannan kiran ma na kokarin katsewa.

Acan kasar India
Masa'ud ne zaune cikin É—an ma dai-dai ciyar parlour'n wan da yake masau kinsa,
littattafai ne a gaban sa ya mai da hankalin sa kansu sai dubasu yake,daga can cikin bedroom yarika jiyo sautin ringing É—in wayar sa,
ture littafan yy gefe yamike tsaye yanufi bedroom
yatako gaban bedside drowar in da wayoyin sa ke É—aure a kai,
É—au kar wayar yy tare da zama saman bedside É—in yy saurin É—aga kiran yaka wayar a kunne.
fuska É—auke da murmushi yace
"Kaji manya Æ´ar gidan Inna".
Baki nawashe jin abin da yafaÉ—a cike da mamakin yan da akayi yagane nice na kirasa tun banyi magana ba.
nace
"La Ya Masa'ud kai ma kasan nice?".
ya ce "Eh ai Abbu faÉ—amin wannan layin nakine".

Baki nakuma washewa kana nace
"To ykk ya India da mutanen garin".
Dariya yaÉ—anyi mai sauti kana yace
"Suna lfy zance kina gai dasu".
YafaÉ—a da yanayin zulaya
"To". nace cike da jin daÉ—i tare da cewa
"Ya Masa'ud har yanzu baka kusa da wowa ba?".
Yace
"Nakusa in Allah ya yarda".
Nace to kakawo min tsaraba".
"Bakida matsala jaka guda zan ciko miki na tsaraba amarya to ya Yayan namu yake?".
Baki natura nace
"Nidai kabar cemin a marya ba kai ne kaki da wowa ba ai da ma Inna tace da kai za'a mana aure gashi kaki zuwa ammana da Ya SALEEM".

Dariya yy kana yace
"to ai dani da Ya SALEEM É—in duk É—aya ne"

Da sauri nace
"A'a kam ai kai kana dariya shikuma bayayi kullum yayita É—aure fuska kamar dodo nidai idan ka dawo zancewa Inna amana auren da kai kawai".

Kai ya jinjina tare da mikewa yazo bakin gado yazauna
yana mai cigaba da dariya haÉ—e da zallar shauki da jin-jina shiririta irin na HAMDAH kodaga maganar ta zaka gane É—in bin yarin ta tattare da ita,
yace
"To ai mace bata auren maza biyu a lokaci guda kuma nan gaba zakiga yana miki dariyar, ina dai baya dukan ki?".

Kai na gyaÉ—a kamar ina gaban shi kana nace
"Eh ai Inna tace duk ran da yabigeni sai tasa Abbu yabigeshi shima".

Yace "to kin ga bazai ma faraba tun da yasan idan yabigeki shima dukan shi za'ayi".

Dariya nayi har da buga cinya sai kuma na rike haɓa naɗan waro ido ina ɗan girgiza kai nace
"Cab Kato dashi ai sai dai Abbu yaÉ—au katon bulala in ba haka ba bazai ji zafi ba ko Ya Masa'ud?".

Yace "ai dama babban bulala zai É—auka yan da zaiji zafi sosai".

Kai na jinjina alamar gamsuwa
Hira sosai mukayi da Ya Masa'ud sai dariya muke dan shi Ya Masa'ud bashida É—aurewa.
Nan yace min yana karatu ne idan yagama zai kirana mukayi sallama na sauke wayar.

Yau kowa sai da yasan an siyamin waya dan ina katse kiran Ya Masa'ud Ummi na kira muka gaisa har da Fauzan.
Sannan na kira Mamei ita ma muka gaisa nasa tabawa Nusaiba.
Abba ne kiran karshe daganan na aje wayar gefe na gyara ƙwanciya ba jimawa bacci ya ɗaukeni.

Ban far kaba sai wajen karfe 5 alawala nayi nazo nayi sallar la'asar koda na idar nafito parlour na nufi kitchen, abinci mai saukin dahuwa na girka taliya ce miyar jajjage
ina gamawa nazuba wan da zan iya ci cikin plt sannan nafito parlour, TV na kunna kana nazauna nan tsakiyar parlour'n Ina cikin cin a bincin a ka kira sallar magriba, bayan na gama naÉ—au plt É—in na kai kitchen nawan keshi kana na Mai dashi mazau ninsa sannan nafita na koma É—aki.
Wanka nashiga ban wani jima cikin bayin ba nafito dan ban tsaya wasan ruwa ba yanzu, wata riga da wandon bacci na ciro nasaka rigar takai min har guiwa wandon kuwa dogone har kasa, sai hula mai raga dana murza a kaina.

Kasan cewar nayi alawala sai na shinfiÉ—a sallaya nazura hijabi nagabatar da sallar magriba ban tashi kan sallayar ba har sai da nagabatar da sallar Isha.

A ɓangaren Ya SALEEM karfe 6 yadawo daga offece koda yashiga bedroom in sa rage kayan jikin sa yy yafaɗa bathroom wan ka saosai yy da ɗan ruwa mai zafi dan son cire gajiyar daya ƙwaso.
Na'ima ta turo kofar tashigo jin motsintsa a bayi sai tafi takoma É—akin ta dan dama waya take da wata a miniyarta jin da wowarsa ne yasa akatse wayar nan suka ci gaba da wayar su.

Shiko SALEEM ko da yafito wata farar tattausar jallabi yazura yanufi masallaci da sauri jin an tada salla,
da misalin karfe 8 yashigo gidan ta kofar side in sa ta baya yashiga batare da yabi ta babban parlour ba, yana shiga É—aki ida nunsa suka sauka kan laidar da Abbu yabasa É—azu zuwan sa yace yabawa HAMDAH,
É—an guntun tsaki yaje har ya juya zai haye gado sai kuma yakuma juyowa ya isa in da ya aje laidar yaÉ—auka tare da kuma jan wani tsakin yanufi kofa,
takofar da yashigo tanan yafita yanufi kofar side É—in ta dake tanan parfajiyar gidan.

Yatura kofar yashiga asannu yatako cikin parlour'n babu kowa sai tv dake tafaman ai ki shi kaÉ—ai,
É—an tsurawa tv'n ido yayi ganin wani Amirican Film in da a ke haskowa.

Mikewa nayi zaune jin karar buÉ—e kofar da akayi a sannu nazuro kafafuna kasa namike tsaye natako bakin kofa buÉ—e kofar nayi a hankali naÉ—an leko kaina ganin shine a tsaye saina karasa buÉ—e kofar nafito na tsaya nan bakin kofar.
É—an juyowa yy yakalleni sai kuma ya mai da idanunsa kan tv'n,
a hankali na juya zan koma ciki na najiyo muryarsa cikin faÉ—a
"Ok komawa zaki kibarni rike dashi sabo da ni É—an ai kenki niko".
cak natsaya tare da juyowa na kalle shi sai kuma na kalli hannunsa jin ya ambaci rikewa
"To in banda abin shi taya zanyi nasan wani abune tafe dashi tun da ba faÉ—a yayiba ko Allan musuru gareni da zan sani".
Baki na turo "shidai kullum a masifa zai kare".
Nafaɗa can kasan makoshi ina takowa in da yake,hannu na mika na rike lai dar da nagani rike a hannunsa, wan da nafi tunani shi yake nufi nabarshi da shi rike, ina rike lai dar yasake da sauri na daɗa rikewa dan tun kan na ida rikewa yasake kaɗan yarage yasuɓuce kasa,najuya nanufi ɗaki.

Shiko gyara tsayuwar sa yy yayin da ida nunsa ke kan tv,sai kuma yaÉ—anyi baya kaÉ—an yazauna saman kujerar dake bayan sa sosai ya mai da hankalin sa kan suburbuÉ—ar da a ke da bindiga a cikin TV'n.

Ina shiga na isa bakin gado nazauna nafara buɗe laidar wani ɗan ma dai-dai cin ƙyaƙƙyawar kwano ce mai murfin glass a ciki,
naciro shi daga jikin murfin ina iya hango abin da ke cikin ƙwanon,
da É—an saurina nabuÉ—e marfin wani kamshine yabigi hancina na haÉ—iye miyau daya taru cikin bakina,
Lafiyayyiyar dambun namace wan da yaji kayan kamshi da É—an-É—ano sai fidda wani kamshi na musamman yake,
É—ebuwa nayi nakai baki dan na gama zakuwa najishi cikin bakina a sannu nashiga tauna shi yayin da da É—in ha É—eÉ—É—iyar danbun naman ya gauraye cikin bakina,
Ko ba'a faÉ—a min ba nasan wannan haÉ—in na Mamei ce.
Aje ƙwanon nayi gefe na mike da sauri nafita dan naje kitchen na ɗauko plt.

Ina fita naɗanyi turus a bakin kofa hangoshi zaune kan kujera yaɗan ƙwanto da bayansa ya jingina da jikin kujerar hannayen sa kuma suna sakale a bayan keyarsa yayi pillow da su.
Mayar da dubana nayi kan TV'n daya kafe da ido sai ai kin harbe-harbe da naushe-naushe suke.
Asannu nanufi kitchen har na É—au plt É—in zan juya sai kuma na tsaya tare da É—aura yatsata kan kumatu alaman nazari
"Yauwa tun da gashi yazo bari na girka masa shayin da Aunty Rafee'at tace".
gaɗa kai nayi alamar gamsuwa da zancen zucin da bake Nan take na ɗaura tukunya nazuba ruwa kofi ɗaya da ɗan kaɗan naɗibi ganyen na'ana'a nazuba sai ƙwayan citta guda biyu da ɗan kanumfari shima baisfi silli huɗu ba nawa ciki na kunna wuta.
Ina nan tsaye ruwan ya tafasa kasan cewar ruwan bashida wani yawa É—an barinsa nayi yakara tafasa saboda kayakin da ke cikin sa suÉ—an nuna,
Zuwa can na kashe wutar nasauke na tacesa cikin cup ƙwalbar zuma na ɗauko na siyaya cikin cup ɗin kana nasa spoon na mosa, naɗau ƴar karamar tray na ɗaura cup haɗe da spoon akai kana naɗauka nanufi parlour'n.

In da na barshi a haka na taddashi a sannu natako in da yake naɗan sun kuya na aje tray'n saman table in dake gefe da kujerar da yake kai,naɗago da niyyar ce masa ga tea na kawo masa, sai kuma nayi shiru ido naɗan tsura masa ganin yan da yabaje kan kujerar ƙafarsa ɗaya yana kan kujerar yatan ƙwashe sa ɗayan kuma yana kasa har lokacin hannunsa nanan in da yy pillow da shi ta bayan keyar sa.

Sosai na zuba masa ido nan take zuciya ta tafara tunano min Film É—in damuka kakalla ni da Rabi a wayan Ya Maheer wato yayan Rabi'n.
Ahan kali na lumshe ida nuna sai gashi kamar yanzu ne nake kallon, murmushi ne yasuɓuce min
"Ai sai na gwa da yan da ake soyayyar nan".
nafaÉ—a a hankali saman lip É—ina,
Ido na buÉ—e kansa sai kawai nafaÉ—a jikin sa nasau ke hannuna kan.........

*Sai kunyi hakuri nasan zakuga typing error ban sami damar editing ba*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.