Trending Hausa Novels

Tubali Book 2 Complete Hausa Novel

Reading file: TUBALI book 2.txt

Chapter 1 of 2

22/12/2021, 07:01 - Messages and calls are end-to-end encrypted. No one outside of this chat, not even WhatsApp, can read or listen to them. Tap to learn more.
22/12/2021, 19:45 - 🥰🥰: A Jikinta ya manna kanshi da cikinta kana kuma ya cusa fuskarshi acikin jikin nata.
Tare dasa hannunshi na dama ya damƙe mararshi.
Gaba É—aya jikinshi rawa yakeyi tamkar mazari, wani irin ciwo cikinnasa keyi masa, wanda har hakan yasa numfashinsa, ke kokarin kwacewa.
Hannunshi na hagu yasa abayanta ya zagayeta, tare da riƙe ta gam-gam cikin gigitan ciwo da fitan hayyaci.

Hakan kuwa yayi masifar gigita Jannart, wanda gaba daya jikinta ya d’auki rawa, kamar yadda nashi jikin ke rawa.
Kana ya kwakumeta ya kanainayeta ya hanata ƙwaƙƙwaran motsi.

Jannart kuwa Ganin hakan yasa cikin firgici ta buÉ—e baki, murya na rawa ta fara cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun Mamy! Mamy!! Mamy!!! Kalli yadda yakeyi fa!!!!�.
Yayinda ita kuwa Mamy cikin tsananin tashin hankali da kidima, ta fara juyawa tsakiyar falon cikin rashin sanin abinyi taketa rabkawa Ramadan kira.
“Ramadan! Ramadan!!! Kazo!!! Rayyern ba lfy�.

Dr. Sulaiman ne wanda shi ya dawo da Rayyern din, ya turo ƙofar da hanzari,
baishigo da wuri bane kuma, saboda ya tsaya fadawa Baba MauÉ—o cewar ciwon Rayyern ne ya tashi.
A hanzarce ya faÉ—o cikin falon,
Baba MauÉ—o na biye dashi a baya.
Yayinda sukabar Hadi da Ari mai gadi kuwa tsaye a harabar gidan, sunyi jugum-jugum domin duk mai imani, muddin yasan yadda ciwon Rayyern ke yi in ya tashi tamkar zai tafi da ransa to tabbas zai cika da fargaba.

Hakan ne ma yasa Hadi zaro wayarshi ya kira Abba, yana É—agawa cikin yanayin tashin hankali yace.

“Alhaji jikin Rayyern fa ya tashi�.

Cikin kidima Abba ya kalli mutanen da yake tare dasu tare da miƙewa tsaye yace.
“Rayyern ba lfy�.
Yana faÉ—in haka ya fita daga falon da bisa alamu duk mgnar sirri yakeyi.

Yana katse kiran Hadi ya kira Ramadan yana É—agawa yace.
“Kai Ramadan kana ina�.
Da sauri yace.
“Abba ina Minjibir ne. Lfy kuwa?�.
Cikin bada umarni da tashin hankali yace.
“Maza ka wuce kayi gida yau kuma cikin Rayyern ya tashi�.

Cikin tsananin tashin hankali Ramadan ya mike tare, da barin duk wani abu da yakeyi, hankalinsa amatukar tashe yace.

“innalillahi wa innailaihi rajiun! Jikin Hamma Rayyern ya tashi? Yanzu Abba Hamma Rayyern din yana ina?�

Abba dake tsaye, cikin alhini da fargaba yace.
“Yana gida, kayi sauri kaje.�
Yana gama fad’in haka ya katse kiran.
Kana yaci gaba da tuƙin da yakeyi.

Shi kuwa Ramadan a kidime ya kalli Riyyam-nsra dake cewa.
“Hamma Ramadan meya faru�.
Ya ƙare .mgnar yana firfito da idanunsa.

Idanu Ramadan din ya rumtse da karfi, cike da alhinin abunda Abban ya gaya masa, ya kamo hannun Riyyam-nsra tare da jansa, suka nufi parking lot, hankalinsa atashe yace.

“Riyyam mu tafi gida yau kuma ciwon cikin Hamma Rayyern ya tashi,
abunda yafi shekara biyu ya kusa shekara uku bai tashi ba, amma yau gashi ya sake tashi mishi.�

“Innalillahi!�
shine abinda Riyyam-nsra ke ta maimaitawa.
Dai-dai lokacin da suka shiga mota.
A 360 Radaman ya figi motar yana cewa.
“Yah Rabbi, Yah Allah ka bawa Hamma na lfy, gaba ɗaya mun sakankance, da cewar ya worke tunda mukaga yayi shekaru bai tashiba�.

A nan gidan kuwa.
Cikin yanayi tashin hankali Mamy ta kamo hannun Dr Sulaiman, a gigice ta jawoshi zuwa gaban Jannart da Rayyern ke kwance kanta, irin kwanciyar nan ta rubda ciki.

Murya na rawa Mamy tace.
“Sulaiman duba min Rayyern yana raye kuwa duba minshi kaga fa baya motsi�.
Ta ƙare mgnar wasu irin masifaffun hawaye na kwaranyo mata.
Yayinda sai a lokacin kuma Jannart ta sunkuyo da kanta, ta zuba mishi ido tabbas kuwa ya daina motsi, duk rawa da karkarwar da jikinshi keyi ya bari.
Wani irin zaro ido tayi tana kallon Mamy dake cewa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun Sulaiman ka duba min Rayyern, kada ya tafi ya barmu akwai nauyinshi da bamu sauke a kanmu ba."

Shi kuwa Dr Sulaiman kamo hannunta yakeyi, yana son zaunar da ita amman ina, gaba daya ta gama gigicewa, ga hawayen dake ta Kwarara acikin Idanunta.

Baba MauÉ—o kuwa da sauri ya matso gaban Jannart ya tsuguna, cikin kuma tashin hankali yasa hannunshi, akan wuyan RAYYERN sabida a kife yake, murya na rawa dattijon ya fara kiran sunanshi.
“Rayyern! Rayyern!! RAYYANU!!! Muhammad Muhammadu tashi.
Buɗe idanunka Mauɗona!!!�.

Ya ƙare mgnar hawaye na kwaranyo mishi.
Wanda ganinsu ne kuma yasa hawayen idanun Jannart tsinkowa.

Tausayin tsohon da Mamy ne sukayi masifar raunata mata zuciya.
A fili zaka gano tsananin tashin hankali da kidimar da suke ciki, kana da tsananin sonshi dake cikin kwayar idanunsu.

Shi kuwa Rayyern da yakejin kansa acikin wata duniya, mai dauke da tsananin azaba gami da radadi, sama-sama haka yake jiyo muryarsu.
Saidai kuma bazai taba iya amsawa ba, duk da yana jiyo kiran sunansa da Baba MauÉ—o keyi, saidai baya da hakikanin cewa, ko yan siraran labban bakinsa zai iya motsawa, saboda tsananin ciwon da yakeji.

Dr Sulaiman kuwa cikin samar da kwanciyar hankali wa Mamy, ya samu ya ajiyeta bisa kujera kana a hankali yace.
“Mamy Rayyern yana numfashi fa, babu abunda ya samesa, Dan Allah ki kwantar da hankalin ki, Insha Allah zai samu lfy, na mishi allura tun a asibiti, yanzu haka ciwon ya fara lafawa, Insha Allah gaba daya zai daina�.

Dr. Sulaiman din ya kare maganar cikin, kwantar da murya da kuma son samawa Mamyn nutsuwa.

Dai-dai lokacin ne kuma Abba ya shigo.
Da sauri ya iso tsakiyar falon.
Sai kuma ya iso gefen Baba MauÉ—o a kidime ya fara kiransa.
“Rayyern�.
Sai kuma ya juyo da sauri jin Dr Sulaiman na cewa.
“Abba dan Allah ku kwantar da hankalinku, ku barshi zuwa anjima kaɗan zai iya amsa muku, nayi masa allura Insha Allah zai samu sauki�.

Wani irin dogon numfashi Abba ya sauke, kana ya koma ya zauna bisa kujerar dake gefensa.

Yayinda Mamy kuwa har yanzu ta gaza tsaida hawayenta.
Gaba daya hankalinta yaki kwanciya, tsoro takeji kada wani abu ya samu Rayyern din, badon komai ba kuwa saidan sanin da tayi, cewar ciwon cikin baya tab’a yi masa da sauki idan ya tashi.

Jannart kuwa da tayi k’asa da kanta, tana jin yadda Rayyern din ke kwakume da ita da masifar ƙarfi, yanayin rikon da yayi mata, dinne kuma yasa kugunta ya soma sarawa, saboda ba wai riko ne na wasa yayi mata ba riƙone na neman mafita.

Ramadan da Riyyam-nsra kuwa kusan a jere da sassarfa suka shigo cikin falon, kowannensu hankalinsa amatukar tashe.
More especially Ramadan da yasan irin yanda ciwon, keyiwa Hamman nasu idan ya tashi.

Da sauri suka nufi kanshi, saidai basu k’arasa ba kuma suka tsaya, saboda ganin su Abba duk suna zaune.

Baba MauÉ—o na zubda hawaye, Mamy ma haka kana Jannart da yake kwance lib a cinyarta kamar matacce, itama hawayen take tsiyayarwa.

Abba kuwa habarsa ya tallafe, saidai kallo daya zakayi masa, ka karanto tsananin tashin hankalin dake kwance akan fuskarsa.

Ganin hakanne kuma yasa, zuciyar Ramadan wani irin harbawa, lokaci daya kuma gaba É—aya jikinsa ya fara tsuman tashin hankali, dan su a zatonsu Rayyern din ya rasu ne.

Cikin wani irin tashin hankali rauni gigita da kuma kidima.
Riyyam-nsra ya saki wani irin raunataccen kuka, tare da zamewa ya zauna aƙasa ya kife kansa bisa sawun Rayyern, cikin rauni murya na rawa kuka na danne abinda yake faɗa yake cewa.
“Innallahi wa innailaihi rajiun Mammy mutuwa zata hanani cika miki burinki,
Wayyoooooooo Allah na Mammy na inama kina kusa kizo kiga halin da tsatsonki yake ciki, Mammy wlh shine wlh sune�.

Su Abba kuwa, tsananin tashin hankalin da suke ciki, yasa gaba É—aya basa iya fahimtar kalaman Riyyam-nsra, asalima basa jin me yake faÉ—a da kyau.
Sai dai shi kuwa Rayyern da tunaninsa ke kokarin gushewa, a sama sama yake jiyo kukan yaron, da kuma abinda yake faÉ—i.
Duk da bawai yana fahimtar kalaman sosai bane, amma yaji wasu daga cikin maganganun, wanda ayanzu baya cikin Lfy da kuma hayyacin da zai iya nazari ko hasashen kalaman.

Dr Sulaiman ne ya matso kusa da Riyyam-nsra, ya jawoshi jikinsa ya zaunar dashi tare da cewa.

“Kai Riyyam-nsra kabar kuka bafa rasuwa yayi ba, ciwon ne ya fara lafawa kaga Abbanku ma yayi shiru�.

Sai alokacin Ramadan ya sauke wani irin numfashin daya, sakar masa da wani nannauyan abu mai kama da dutse daya tsaya a ƙirjinsa.
Sabida gaba É—aya ya fara rasa numfashin sa.

Shi kuwa Riyyam-nsra cikin kasa danne kukan sa yace.
“Yah Sulaiman, da gaske kake Hamma Rayyern dina, yana numfashi?�.

Kai Dr. Sulaiman ya jinjina, kana cikin sauri yace.
“Eh Riyyam-nsra bai rasuba gashi yana numfashi, nanda y’an mintuna zai tashi insha Allah.�

Ajiyan zuciya suka sauƙe baki ɗayansu.

Sai lokacinne kuma Mamy ta iya tsaida hawayenta.
Yayinda Baba MauÉ—o Kuwa sam hawayen shi ya gaza tsayuwa.
Hakan kuwa shi yasa Jannart ta gaza tsaida hawayenta, saboda acikin rayuwar ta akwai rauni sosai, matukar zata ga hawayen Babba, To Lallai zuciyarta saita karye, ba kuma zata iya lallashin kanta ba.

Ganin duk sun d’an nutsu ne kuma yasa, cikin sanyi Dr. Sulaiman ya samu ya zauna, tare da d’go kansa ahankali yayi gyaran murya kana anutse yace.

“Kwata kwata abun bai wuce 30mnt da fara mishi ba, domin tun da ya fara mishi na fahimta, saboda naga yana ta haɗa zufa, kasancewar alokacin muna cikin meeting ne da sauran Doctor's din mu,
Akan wani course da muke son wasu daga cikin Doctor's É—in namu suje suyi a Mascow,
So dana fahimci cewa, ciwon cikin nasa nason tashi ne, sai na bukaci da mu tashi taron, amma sai yaki bani dama, to kafin mu gama ma abin har ya fara tsanan ta.�

Idanu duk suka tsurawa Dr. Sulaiman din, saboda Jin abunda yake fad’a.

Shikuwa Dr. Sulaeman gyara zamansa yayi, tare da fuskantarsu, cike da son sake samar musu nutsuwa yace.

“Insha Allah Rayyern zaiji sauk’i, domin muna fita a meeting din nayi masa allura, saidai kafun nan ma tuni abin ya gama tashi, shiyasa ya ɗan wahal dashi amman Alhamdulillah, bayan 50mn idan alluran ta fara aiki zai dan ji sauƙi, wanda kuma zuwa yanzu inada yakinin, fara aikin allurar Dan shiyasa ma kukaga yayi shiru jikin ya daina bari.�

Cikin gamsuwa Ramadan da Abba suka gyaÉ—a kai, saboda wannan bayanine da likitocin suka saba yi musu, sudai fatansu shine samun saukin Rayyern din.

Baba MauÉ—o dake zaune kuwa, ahankali yasa hannunshi ya shafa kan Rayyern din zuwa wuyansa.
Kana ya miƙe tsaye.
Tare da sharce hawayen sa.
Cikin tausayawa yace.

“Toh Alhamdulillah Allah ya bashi lfy yasa zakkan jikine, Allah ya daga kafadunsa.�
Ya ƙare mgnar yana nufar hanyar fita.

Cikin sauƙe numfashi Riyyam-nsra da Ramadan suka bishi da ido, da kuma wani kallo mai cike da wani irin so na musamman.
Abba da Mamy kuwa.
Numfashi suka fesar tare da cewa.
“Amin ya Allah baba Mauɗo�.

Shi kuwa Baba MauÉ—o yana fita
Hadi da Ari sukayi kanshi, cikin girmamawa da kwarjinin dattijon suka hada baki wurin cewa.

“Allah rene ya jikin nasa?�.
A hankali yace.
“Alhamdulillah jiki da sauƙi.�

“Allah ya kara sauki.�
suka had’a baki wajen fad’a.

Shikuwa Baba Maud’o.
“Amin ya Allah�.
Yace yana mai wucewa cikin É—an side É—insu.
Kai tsaye Bathroom ya wuce al'wala yayi kana yazo.
Ya dauki Kur'ani ya fara karatu wai ko zaiji sanyin zuciyarshi, da wani nauyi daya danne mishi ƙahon zuciyarshi.
Amma ina hakan ya gagara,
Hawaye kuwa tamkar an bude bakin famfo.
Allah ya sani yana jin wani irin azabebben son yaran a zuciyarshi,
Baya son gani ko jin duk wani abu da zai cutar dasu duk kankantarshi da yanada hali da ko kuda bazata sauka kan Rayyern ba.

Da ya dauka kawai dan kyautata mishi da sukeyi ne, kuma dan kasan cewarsu yaran uban gidansa.
Toh amman zuwan Riyyam-nsra yasa ya fahimci, kawai yana son duk wani abinda ya shafesu ne.
Wasu lokutan yakanyi tunanin ko dan kamar da Riyyam-nsra din, yakeyi da Rayyern ne yasa yake masifar sonshi ma din.

Hannun shi ya daga sama yana mai yiwa yaran addu'a.

A nan cikin falon kuwa.
Shiru Jannart tayi ta sunkuyar da kanta ƙasa.
Yayinda hawayenta keta kwaranya ba ƙaƙƙautawa.
Tana ciwo amman bata taɓa ganin irin wannan tashin hankali a fuskar Daddy, kamar yadda ta gani a fuskar Baba Mauɗo da Abba ba.
Bata taɓa ganin makamancin gigitar da Mamy tayi a fuskar Mom ba.
Duk da tasan mom tana masifar sonta.
Wannan kawai ya isa shaidar son uwa da banne a duniya.
Mamy kuwa numfashi take ta saukewa kawai.
Riyyam-nsra kuwa miƙewa yayi ya haura sama.
Yana shiga kuwa ya kira Mammyn sa.

Abba kuwa cikin sauƙe numfashi ya tallabe haba.
Tare da cewa.
“Ramadan dagashi a kanta.
Sai ka gyara mishi kwanciyarsa�.

Cikin sauri Dr Sulaiman yace.
“A'a Abba barshi shida kanshi zai tashi in allurar ta gama ratsashi.�

Cikin sanyi Mamy tace.
“Ai kuma Jannart din zata gaji�.

Kai ya dan juya tare da cewa.
“Bazai dadeba zai tashi�.

Shiru sukayi.
Kana shi kuma Dr. Sulaiman miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
“Toh Abba ni bari in wuce gida anjima zan dawo.�

“Toh mun gode Dakta�.
Abba ya faÉ—a yana mai gyara zamanshi.

Shi kuwa Dr Sulaiman Ramadan ya kalla tare da cewa.
“Kasan idan ya tashi zai tashi ba ƙarfi illar alurar kenan, shiyasa ba'a cika son yawaita yiwa mutum itaba.
Zaijishi duk ba ƙarfi, so dole sai an taimaka mishi ka sani�.

Kai Ramadan ya jinjina tare da cewa.
“Eh na sani�.
Daga nan ya sallamesu ya tafi.

Su kuwa, shiru sukayi suka zauna jugum-jugum.
Ganin kuma yamma lokacin daura girki yayine, yasa Mamy miƙewa a hankali ta nufi Kitchen.
Bayan ta cire lallenta ne kuma ta fara aiki.

Ita kuwa Jannart gaba É—aya ta kasa kwakwaran motsi.
Sabida masifar kunya da nauyin Abba da takeji, kana ga kuma nauyin zaratan namiji dake kanta.
Wanda agaba daya rayuwarta bata taɓa fuskantar makamancin hakan ba ga wani irin masifeffen ƙamshin jikinsa dake narkar da jikinta, tattausan sumar kansa da sajensa ta zuwa idanu.

Yanzu kusan 50 minutes kenan suke a hakan.
Yayinda kuma har yanzu hawayenta ked’an disowa kadan-kadan.
Suna mannewa ajikin gashin idanunta.
Shi kuwa Rayyern dake kwance a hankali ya É—an ja numfashin wahala tare da fesar dashi.
Kana ya rumtse idanunshi da ƙarfi tare da taune lips ɗinshi, duka biyu saboda so yake ya tashi, amman gaba ɗaya jikinshi daga kugunsa zuwa sawun takawarsa sunyi lakwas.
Wannan abun shiyasa baya son allurar.
Dan muddin akayi mishi ita sai yayi kusan mako guda karfinsa bai dawo dai-dai ba.

Da sauri Ramadan ya matso kusa dashi.
Dai-dai lokacin kuma Riyyam-nsra shima ya sauko ƙasa.

A tare suka É—an sunkuyo kanshi, ahankali ya buÉ—e idanunshi jin muryar Abba nakiran sunansa.
“Rayyern! Rayyern!!�.
Cikin wata iriyar sassanyar murya can ƙasan maƙoshi yace.
“Na'am Abba�.

Jin Rayyern din ya amsa ne kuma, yasa Abba cikin jin daÉ—i yace.
“Alhamdulillah! Alhamdulillah!!�

Rayyern kuwa cikin ƙarfin hali da jarunta ya tattaro ragowar kuzarin sa baki ɗaya.
Ya yunƙura alamun zai tashi.
Da sauri Ramadan yasa hannunsa zai tallabeshi.
Cikin sanyin murya yace.
“Barni zan iya�.
Cike da rauni Ramadan yace.
“Hamma Rayyern bazaka iyaba�.

Kar-kar haka jikinsa ke rawa.
Lokacin da ya samu ya juyo ya É—ago kanshi.
Da sauri ya rumtse idanunshi ganin kamar kan Jannart yake.
Haka yasa ya miƙawa Ramadan hannunsa.
Da sauri ya kamoshi kana ya yunƙura ya zauna.
Lokacin Mamy ma ta iso cikin jin daÉ—i tace.
“Alhamdulillah sannu ko Babana�.
Kanshi ya gyada mata.
Ita kuwa Jannart a hankali ta miƙe tsaye.
Cikin son tsaida hawayenta ta nufi Kitchen.

Tashinta ne yasa Abba matsowa kusa dashi.
Hakama Mamy nanfa sukayi ta mishi sannu.

Ita kuwa Jannart tana shiga Kitchen aikin da Mamy ta fara taci gaba da yinsa.

Su kuwa A falon cikin ƙarfin hali ya maida kansa ya jingina da jikin kujera, kana a hankali ya fara yunƙurin tashi tsaye.
Da sauri Abba ya tallabeshi gefen damanshi.
Kana Riyyam-nsra ya tallabe gefen hagunshi.

Ramadan kuwa da Mamy ido suka zuba musu, sunaga yadda yake taka kafafunsa da suke karkarwa.

A hankali suka fara take steps din da taimakon su Abba ya samu.
Suka haura.
Kai tsaye Bedroom dinsa suka wuce dashi.
Suna shiga suka kwantar dashi.
Sanin kuma allurar zata sashi bacci ne yasa Abba juyawa ya fita.

Shi kuwa Riyyam-nsra gefensa ya zauna.
Yana gyara masa pillow.

Rayyern din kuwa yana kwanciya, lokacin É—aya bacci ya fara fuzgarshi.

Ramadan ko ganin sun haura sama ne, ya sashi fita kaitsaye kuma Mai-nasara pharmacy ya nufa, inda yaje ya d’auko magungunan da Rayyern din Kesha Idan ciwon ya tashi.

Ita kuwa Mamy Kitchen ta koma nan sukaci gaba da aikinsu ita da Jannart.

Bayan sallan isha'i.

A hankali Jannart ta dan juyo tana kallon kofar babban falon,
daga nan cikin falonta.
Da sauri kuma ta miƙe jin muryar mutumin nan da taji ana kiransa da Baba Mauɗo yana sallama.

Da alamun kuma babu kowa a main falon.
Da sauri ta mike ta nufo falon.
Baba Mauɗo Kuma tsaye yake bakin ƙofar, ya ɗan turota yana sallama da ɗan buga kofar.
A hankali tace.
“Wa alaikassalam Baba ka shigo mana�.
Dai-dai lokacin kuma Mamy ta fito daga side É—insu.
Cikin girmamawa tace.
“A'a Baba Mauɗo ka shigo mana�.
Cikin kamala yace.
“Toh�.
Kana ya shigo.
A hankali Jannart ta dan rusuna tare da cewa.
“Barka da dare Baba�.
Juyawa yayi ya kalleta cikin wani irin mamaki da nazarin fuska da kammanin muryar yarinyar yace.
“Barka dai, Ya mai gidan naki da jikin?�.
Cike da girmamawa tace.
“Alhamdulillah jiki da sauƙi�.

“Masha Allah. Allah ya ƙara mana sauki�.
Ya faÉ—a yana mai juyowa yana kallon Mamy dake cewa.
“Bismillah mu isa yana sama, Abbansu ma yana can�.
Hakan ne yasa ya nufi saman.

Ita kuwa Mamy juyowa tayi ta kalli Jannart, da idanunta suka dan yi ja cikin kulawa tace.
“Kinyi salla ko?�.
Kai ta gyaÉ—a mata alaman eh.
Ita kuwa Mamy.
Ba tare da tace mata komaiba ta nufi Dinning area.
Foodflask ta É—auko wanda tasa mata,
Abincin da sukayi sakwara ce, da miyar agushi.
Miƙa mata tayi tare da plate da spoon tace.
“Gashi ki zauna kici abinci, ki kuma bar zubda hawayen nan haka kinji ko Mamana�.
Cikin sanyi tace to.
Kana ta amshi kular ta wuce É—akinta.

Ita kuwa Mamy Kitchen ta koma tazo ta shiryawa su Ramadan nasu ta kai musu falon sama.
Anan ta samesu.

Baba MauÉ—o da Abba Kuma suna cikin dakin Rayyern É—in.
Ganin har yanzu bacci yakeyi ne, yasa suka fito.

Ita kuwa Jannart ajiye kular tayi a falon.
Ba tare da tayi niyar ciba, ta kwanta a ƙasa bisa carpet din, tana rike da wayarta.
Sam ta rasa me take tunawa,
saidai kawai ta fahimci cewa yau gidan babu daÉ—i dan ciwon Rayyern É—in.
Sabida su Ramadan masu É—ebe mata kewa da Riyyam-nsra mai sata farin ciki duk yau basa da Gud Mood.

Tana nan kwance ahaka har tayi bacci.

A folon kuwa suna fitowa suka samu Dr Sulaiman ya iso.
Nan Abba ya koma dashi ya ɗan ƙara dudduba shi.
Kana ya sallamesu ya tafi.

Haka dai su Ramadan suka tafi dakinsu.

Mamy kuwa falon Jannart ta leƙa ganin tana bacci ne yasa ta wuce side ɗinsu.
Dan tasan yau Abba a dakin Rayyern zai kwana.

Haka
Hakan kuwa akayi.
Rayyern kuwa baccin yayi mai zurfi sai karfe uku da rabi ya farka.
Abba da kanshi ya hada masa ruwa yayi wonka,
Kana yayi al'wala.
Yana fitowa yayi ramuwar sallan magriba da isha'i, sannan ya dan sha tea É—in da Abba ya hada masa da kansa.

Toh kuma daga nan sai idonsa ya É—an bushe.

Sai da akayi sallan asuba.
Kafin ya koma wani baccin.

Koda Abba suka dawo masallacin sun sameshi yana bacci.

Nan suka fito.

Mamy da Jannart kuwa Kitchen suka shiga dan haÉ—a breakfast.

Kasan cewar yau É—in asabar ce ba aiki.
Yasa Riyyam-nsra da Ramadan ma basu tashi da wuriba.

Sai karfe tara suka fito,
d’akin Rayyern suka shiga.
Zaune suka sameshi bisa carpet ya jingina jikinsa da gado.

Mamy da Abba ne zaune agabanshi.
Mamy na haÉ—a mishi tea.
Abba Kuma da kanshi yake zuba mishi ferfesun jan nama da Jannart tayi mishi yayi laushi tibis.

A hankali ya É—an juyo ya kalli Radaman dake cewa.
“Hamma ya jikin naka?�.
Cikin sauƙe numfashi yace.
“Alhamdulillah�.

Riyyam-nsra kuwa matsoshi yayi da kyau tare da cewa.
“Hamma Rayyern Mammy ta gaishe ka da jiki.
Zaiton ma tace in gaisheka da jiki�.
Cikin sanyi yace.

“Ngd".
Ganin kuma alamun bai son surutune.
Yasa suka sauƙo ƙasa.

Abba kuwa cikin kulawa yace.
“Rayyern kaci abincin tunda ɗuminsa kaji�.
Cikin sanyi yace.
“Abba na gaji bazan iya cin nama da sassafen nan ba�.
Da sauri Mamy tace.
“Rayyern yayi laushi sosai fa�.
Cikin narke fuska yace.
“Bani tea ɗin kawai is okay".
Haka suka hakura suka barshi.
Tea É—in yasha.
Kana Abba ya kuma hada masa ruwan wonka yayi.

Koda ya fito daga wankan, wasu tausassun riga da wondo yasa wanda Abban ya fito masa dasu.

Mamy kuwa tuni ta sauko k’asa,
aƙasan ta samu su Ramadan da Riyyam nsra a dining area suna zaune, Yayinda Jannart ke zuba musu abinci.
Da sauri Mamy tace.

“Kai kun kai abincin su Baba Mauɗo kuwa?�
Kai Riyyam-nsra ya gyaÉ—a tare da cewa.
“Eh Mamy nakai musu, yanzu ma na dawo�.

“To yayi.�
Mamyn tace tare da zama gefensu, nan sukayi Karin kumallon.

Wunin ranar dai haka sukayi shi a gida gaba dayansu.

Alhamdulillah kuma jikin Rayyern da sauki, sai dai rashin karfi da rashin cin abinci, dama kuma da rashin son mgn da bayayi, dama kuma shi ba gwanin surutu bane, balle kuma yanzu ga halin ciwo.

Washe gari ranar lahadi ma
Haka suka wuni.
Duk da surutun Riyyam-nsra ya rage,
saboda jikin Hamman nasa.
Da yamma kuma Nasir Ahmad yazo ya duba Rayyern din da jiki.

Bayan sun d’an taba hira shida Riyyam nsra ne kuma, yayi musu sallama daga nan kuma gidan Malam Mai-nasara ya wuce.
Nan yake sanar masa abinda ke faruwa...

Jannart kuwa tun ranar tun lokacin kuma bata sake ganinsa ba ko jin muryarsa.
Yayinda Mamy kuwa duk a zatonta Jannart din, duk safiya tana zuwa duba jikin Rayyern din.

Washe gari Ranar Monday Alhamdulillah jikin da sauki sosai, domin karfinsa ma ya É—an fara dawowa.

Bayan sunyi breakfast ne kuma Ramadan ya tafi asibiti.

Hakan yasa Jannart da kuma Riyyam-nsra, sai kuma Mamy ne ke zaune afalon.

D’ago kai Riyyam nsra din yayi, tare da kallon Jannart dake riƙe da wayarsa, tana kallon comments ɗin followers ɗinsa akan wata wakar fullancin daya bibiya.

jin wayar tasa tana ringing ne kuma yasashi kallonta, tare da d’an gyara zamansa yace.
“Aunty Jannart Waye�.

“Mammy ce�.
Ta bashi amsa tana miƙo masa wayar.
Da sauri ya amshi wayar tare da amsa kiran

“Assalamu alaikum yah Mammy�.
Jim ya ɗanyi na tsawon kusan daƙiƙu 2, kana a hankali ya miƙe tsaye tare da fara haurawa sama yana cewa.

“Afwan Mamma wlh shine baya son surutu, ko wayarsa bai amsa kira, tun ranar nake son hadaku toh ganin baida lfyarne yasa nai shiru�.

Ya ƙare mgnar yana ida hawa saman.
Kai tsaye dakin Rayyern É—in ya nufa da sallama a bakinsa.

A falon kuwa cike da mamaki Mamy ta bishi da ido.
Zuwa yanzu ta fara tsoron wani al'amarin, to wai ma ya akayi bata taɓa tunanin Riyyam-nsra ya nuna mata hoton Mammansa ba?.
Tayi wannan tunanin.

Jannart kuwa da sauri ta juyo ta kalli wayarta dake gefenta, cikin mamaki ta zubawa wayar ido ganin number dake kiranta...

Shi kuwa Riyyam-nsra a hankali ya isa gaban Rayyern dake zaune bisa kujera.
Yasa system É—in shi a gaba da alamun aiki zaiyi dan yanzu ya buÉ—e ta.
Idonshi ya É—ago ya zubawa Riyyam-nsra su.
Shi kuwa Riyyam-nsra cikin karya wuya.
Da rauni ya iso garesa, murya a raunace yace.
“Ayyah Hamma Rayyern, dan Allah ga waya kayi mgna da Mammy na, tun shekaran jiya take cemin in hadaku ta gaidaka da jiki taji muryarka�.

Ya ƙarashe mgnar yana karya wuya.

Ga mamakin Rayyern kuwa sai ga hawaye na zubowa a fuskar yaron.

Shi kuwa Riyyam-nsra cikin yin rau-rau da ido.
Ya miƙa masa wayar tare da cewa.
“Dan Allah Hamma Rayyern kada kace a'a�.
Ya rigada ya gama karya mishi zuciya da hawayensa.
Duk da ko mgnar yayi sai yaji ya gaji shiyasa baya son yawan mgn.
A hankali yasa hannunshin ya amshi wayar.
Cikin nitsuwa ya manna wayar a kunneshi tare dasa kafaÉ—arsa ya makale wayar.
Murya a sanyaye yace.
“Assalamu alaikum�.

A can ƙasar Ethiopia kuwa.
Wani irin lumshe ido Mamma tayi, tare da jan wani irin dogon numfashi, kana cikin tsananin harbawar da zuciyarta keyi tace.
“Wa alaikassalam Mauɗo am!!!�.

Wani irin rumtse idanu Rayyern yayi da azaban ƙarfi tare dasa hannunshi y...!

*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.

Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuÉ—i gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*

By
*GARKUWAR FULANI*
22/12/2021, 19:45 - 🥰🥰: Ya dafe ƙahon zuciyarshi sabida wani irin masifeffen harbawa da yaji tayi da azaban ƙarfi.
“Yah salam�.
Shine abinda ya iya fada cikin zuciyarsa.

Yayinda Riyyam-nsra kuwa ya zauna a kasa, a gabanshi tare dasa hannunshi duka biyu ya tallabe Fuskarsa, kana ya zubawa Rayyern É—in idanu kamar mai kallon madubi ko TV.

Shi kuwa Rayyern wani irin sakewa yaji jijiyoyin kanshi zuwa zuciyarsa sunayi.
Suna bada sautin
Ras-ras, yayinda duk kofofin gargasar jikinsa suka fara amsa amon muryar baiwar Allah nan.

Yayinda can wurin Mammy ma haka abin yake.
Dan Tuni ita wasu hawaye na ke tsiyayo mata, Yayinda takejin zuciyarta nayi mata ani irin duka.

Cikin rumtse idanunta tace.
“Maudo ya jikin naka?�.

Idanunsa ya dan lumshe, cikin kuma jin wani sabon bugun zuciya yace.
“Mammmmmy jiki da sauƙi Alhamdulillah.�

Riyyam nsra kuwa dake gefe, wasu irin zafafan hawaye ne suka zubo, daga cikin idanunsa, wanda sukafi kama da hawayen farin ciki.

Yayinda shikuwa Rayyern meda kanshi yayi ya jingine, jikin kujerar yana mai amsar saƙon da jijiyoyin jikinsa suke bashi.
Cikin kasala kuma ya motsa lips É—insa tare da cewa.
“Amin Mammy.�
Ya fad’i hakanne kuma saboda, addu’ar da Mammyn tayi masa.

Mammy kuwa Idanunta ta lumshe, cikin kuma danne abunda takeji, yayi tsaye acikin zuciyarta, ta soma yi mishi addu’an samun lafiya, tare da sa mishi al'barka.

Sai kuma ta daura da cewa.
“Ina Ramadan?�

Cikin sauƙe numfashi Rayyern din yace.
“Ya tafi wurin aiki�.

Daga can b’angaren Mammy kuwa Kai ta jinjina, tare da soma tambayan shi, akan sauran ahlin gidan nasu.

Shikuwa Rayyern duk yanda yakejin, mood d’insa na sanjawa, amma anutse yake amsa mata, kana kuma
Cikin girmamawa.
Kamar da wasa kuwa, shida Mammyn saida sukayi mgnar mituna shida kana sukayi sallama.
Bayan ya zare wayar akan kunnensa ne kuma, ya mikawa Riyyam nsra.

Cikin sauri kuwa Riyyam ya karb’i wayan, tare da mikewa tsaye, direct ya koma dakin Ramadan.

Ganin fitan Riyyam dinne kuma yasa, Rayyern jingine kansa da jikin kujera, tare da rumtse idanunshi.

Asanyaye kuma cikin tausasshiyar muryarsa, yake fad’in.
“Yah ilahi ya mujibadda'awati.
Ya salam�.
Sune abunda yake fad’a yana mejin
tamkar kanshi zai juye, abubuwa da yawa keyi masa yawo acikin tunanin sa.
“Maudona!!�
Ya maimaita kalmar da yaji ya tsaya mai arai, dan sai yakejin tamkar ya tab’a jinta.
Idanunshi ya buÉ—e kana a hankali yace.
“Toh ko dai Baba Mauɗon da nake jine yasa naji kamar nasan kalmar ada can baya?�

Saurin girgiza kanshi yayi, tare dasa hakwaransa ya cije lips d’insa.

Take kuma ya fad’a dogon nazari, wanda hakan yasa ya gaza ci gaba da aikin da yake son yin.

A can falon kuwa, cike da mamaki Jannart ta zubawa wayarta ta ido
Taki amsawa.

“Jannart ba kiranki akeyi ba ki amsa mana�.
Mamy ta fada tana kallonta cikin kulawa.

Jannart din kuwa cikin yanayin nazari tace.
“Mamy number’n ba suna, ban san waye bane�.
Ta ida mgnar tana jawo wayar jin da tayi sako ya shigo mata.

“Toh ki amsa mana ai zakiji waye ne�.
Cewar Mamy.

Jannart din kuwa kai ta É—ago daga duba sakon tare da cewa.

“Lah ashe ma Aunty Dijat ce�.

Ganin kiran ya kuma shigowa ne yasa ta amsa kiran.
Tare da kara wayar a kunne.
Da sauri tace.
“Abba kaine�.

Gyara zama Barrister Kabir yayi tare da cewa.
“Eh nine dai Jannart, na fahimci.
Daddynki yana iya zargar wayata da bin diddiginta ne, yasa na kiraki da wayan Khadija."

Cikin gamsuwa tace.
“Ayyah Daddy na�.
Miƙewa Mamy tayi ta bar wurin.
Sabida ta barta ta É—an sake.

Ta sake din kuwa ganin Mamyn ta tafi cikin nitsuwa tace.
“Abba ya lbrin su Daddyn ya Mom tayi, ina Yah Azeez na?�.

Da sauri yace.
“Me ruwanki dasu�.
Shiru tayi cikin sanyi jiki ta miƙe ta nufi falon ta.
shi kuwa Barrister Kabir cikin kulawa yace.
“Kina lfy ko".

“Lfy lau Alhamdulillah Abba�.
Ta bashi amsa tana zama.

“Gaba ɗaya jiya ke nai ta tunawa da sanyin nan, ki kula da kanki sosai kin san irin wannan sanyin ƙarshen hunturun yafi miki illa da tada ciwonki, kiyaye shan ruwan sanyi da AC, sannan kike rufe Windows ɗinki duka sabida hazo kinji ko?".

Cikin nitsuwa tace.
“Toh Abba�.

Juyowa yayi ya kalli Dijat dake ta son ya Bata wayar suyi magana da Jannart din, kauda kanshi yayi daga kallonta tare da cewa.
“Gidan naku duk lfy ko?�.

Gyara labulen window dake kusa da ita tayi kana a hankali tace.
“Uhumm shine dai baida lfy, tun ran jumma'a, wai ciwon cikinsa ya tashi, sai ka gani Abba kamar zai mutu fa�.

Ta k’are maganan cikin dan nuna tausayawa.

Abba Kabir kuwa da sauri yace.
“Subahanallah Rayyern din?�.

Kai ta gyaÉ—a kamar tana gabanshi.
Sai kuma ta daura da cewa.
“Eh Mamynsa nata kuka da Baba Mauɗo�.

“Innalillahi Jannart meyasa baki gaya min ba�.
Cikin sanyi tace.
“Abba na manta ne�.
Cikin faÉ—a yace.
“Jannart ki mance ciwo da lfyar mijinki? Kada ki sake yin haka kul kinji ko?".
Cikin biyayya tace.
“Toh Abba"

Barrister Kabir din kuwa dan gyara zamansa yayi, tare da cewa.
“In sha Allah da yamma zan zo, akwai wani abu da kike buk’ata ne?�

Kai Jannart din ta jinjina, kana cikin sanyin murya tace.
“A’a Abba babu abunda nake buk’ata.�

“To shikenan sai nazo.�
Daga haka sukayi sallama.

Bayan ya katse wayarne kuma ta mik’e, tare da fitowa waje suka shiga Kitchen da Mamy.

Da yamma misalin ƙarfe biyar da da rabi na yamma.
Abba da Barrister Kabir din Suka shigo a jere.
Kasancewar shigowar Barrister’n ya samu Abban a wurin Baba Mauɗo ne.

Ganinsu ne kuma yasa, Mamy yin murmushi, fuska asake tace.
“Sannu da zuwa Barrister".

Shidin ma Barrister Kabir din murmushi yayi, kana cikin mutuntaka yace.
“Yauwa sannu Hajiya, fatan na sameku lafiya ya mai jiki?�

“Lafiya k’alau Barrister, jiki kuma Alhamdulillah dan yana ta samun sauki, ya iyalai?�

“Masha Allah Iyalai Alhamdulillah.�
Ya fad’a adaidai lokacin da yake zama akan kujera.

Yayinda ita kuwa Mamy juyawa tayi kaitsaye ta nufi, d’akin Jannart tana cewa.
“Jannart ga Abbanki yazo�.

Jin abunda Mamyn ke fad’ane yasa Jannart dake zaune, saurin mikewa tsaye tare da nufo falon tana gyara mayafin doguwar rigar jikinta.
Murmushi Mamy tayi tare da juyowa.
Ta nufi falon ita kuwa ta rufa mata baya.

Suna fitowa ta nufi kusa da Abban tana murmushi.
“Abba sannu da zuwa�.
Tace tana zama agefenshi.

Yayinda ta hango Abban Rayyern kuma yana haurawa sama.

Mamy kuwa Dinning area ta nufa.
Goran Ruwan sanyi dana Nutri milk tasa a É—an ma dai-dai-cin tray da cup, kana Akan santer table É—in dake gabanshi, ta ajiye tray tare da zama bisa kujera.
“Sannu Barrister Bismillah ga ruwa�.
Ta faÉ—a cikin kulawa.

“To nagode.�
Barrister Kabir ya amsa.
Tare da daukan ruwan ya d’ansha kadan.

Jiyo alamun ana sauƙowa ne kuma, yasa Mamy maida kallonta ga stairs din.
Ganin kuma Rayyern ne yake takowa a hankali, yana sanye da wata tattausar jallabiya baƙa mai masifar sheƙi.
Irin mai guntun hannu ne jallabiyar,
gabanta kuma ta sama ank’awatasa da aninaye.

Abba na biye dashi a baya.

Sosai ya É—an rame duk da jallabiya ce a jikinsa, kuwa amma ramarsa ta É—an fito, sai wani irin fari da yayi yayinda sajenshi yake É—an hargitse.

Cikin jin daÉ—i Mamy tace.
“Alhamdullahi lallai yau kam jiki da sauƙi, tunda har Babana zai sauƙo ƙasa."
Jin hakane yasa Barrister Kabir juyowa, ya kalli gefen damanshi ganin Rayyern ne, da yadda yake tafiya a kasalance alamun ba isashen ƙarfi ajikinsa ya sashi cewa.
“Ayyah Alhaji da ka barshi ai, Idan yaso ni saina haura in ganshi, gaskiya yaji jiki�.
Dai-dai lokacin kuma suka iso kan steps ɗin ƙarshe.
Cikin yanayin gajiya da maida nufashi ya zame, ya zauna kan step na biyu tare da jingina kansa, da jikin ƙarafunan gefe da gefen steps din, cikin lumshe ido yace.
“Abba na gaji.�

Ya ƙare mgnar yana kallon tsakiyar falon.

Ita kuwa Jannart jin muryarsa ne, da kuma abinda Mamy da Abbanta suka fadane, yasa ta ɗago kanta tare da ware manyan idanunta,ta kalli hanyar sauƙowan.
Wanda yanzu kusan satinta uku a gidan, amman bata taɓa zuwa ko kusa da wurinba.
Ido cikin ido sukayi dashi,
Wanda hakan yasa tayi maza tayi ƙasa da kanta.
Tare da lumshe idanunta tabbas ya rame sosai fuskarshi tayi wani irin haske.
Sajenshi ya hargitse kaɗan alamun babu isasshen ƙarfin jiki da nitsuwar lfya.

Dib-dab-dib-dab haka taji bugun zuciyarta na harbawa.

Shi kuwa Rayyern fuskarshi ya tsuke tare dayin mgnar zuci.
“Eh dole mana a Barka ka haura sama, tunda gaka ubana, kasan da ka gani ka karanta duk bai isheka ba ai, sai kaga makwancina".
Mtswwww yaja É—an gajeren tsaki cikin bakinsa.

Mamy kuwa cikin jin daÉ—i tace.
“Sannu ko Babana.�
Kai ya gyaÉ—a mata cikin sanyin jiki.

Abba kuwa gefenshi ya É—an ratsa tare da cewa.
“Toh huta sai ka ƙaraso ko�.

Kai ya kuma gyaÉ—awa.

Barrister Kabir kuwa gyara zamansa yayi tare da cewa.
“Rayyern ya jikin naka?�.
Da sauri yace.
“Alhamdulillahi ni nama worke.�
Murmushi Barrister yayi domin ya gane cewar.
Har yanzu Dr.Rayyern bai yarda dashi ba, asalima zarginsa yakeyi.
Cikin kulawa yace.
“Masha Allah. Haka ake so.
Allah ya ƙara lfy da karfin jiki.�
A takaice yace.
“Amin.�

Shi kuwa Abban Rayyern da Mamy cikin jin daÉ—i sukace.
“Amin Amin Barrister mun gode matuƙa, Allah ya bar zumunci.�
Amin yace yana mai kallon Jannart data sunkuyar da kanta ƙasa, tana wasa da wayar hannun ta.

Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
“Toh Alhaji bari in wuce gida, Allah ya ƙara sauƙi.�

Miƙewa shima Abban yayi tare da cewa.
"Amin Amin Barrister mun gode sosai�

Daga nan suka fita tare.

Suna fita itama Jannart ta miƙe ta nufi ɗakinta.

Da wani irin masifeffen kallo Rayyern ya bita dashi, kallon da yafi kama da harara.

Mamy kuwa shi ɗin ta zubawa ido, Jin ana kallonsa ne kuma, yasa ya ɗan juyo ya kalli Mamy ganin yadda ta tsareshi da ido ne, yasashi kwaɓe fuskarsa tare da miƙewa ya dawo kan doguwar kujera.
A hankali ya kwanta tare da É—aura kafa É—aya kan É—aya kana
Yace.
“Mamy Riyyim fa?�
Numfashi ta sauke tare da cewa.
“Ya tafi yi mana cefene shida Hadi.�

Kai ya gyaÉ—a tare da fuskantar TV.

Ita kuwa Jannart tana shiga part dinta.
Wonka tayi tare da al'wala kana ta fito dan magriba ta gabato.

A falon kuma a tare Ramadan da Riyyam-nsra da Abba suka shigo.
Gaba ɗayansu riƙe da manyan ledodi.
Kitchen suka wuce.
Kasan cewar kayan miyane.
Yasa duk suka diresu nan.
Kana duk suka je sukayi al'wala.
Shi kuwa Rayyern dama ya koma É—akinsa dan yin wonka.

Bazai iya zuwa masallaci ba, dan d’an haurowan da yayi duk jikinsa rawa yakeyi.
Haka yasa yayi salla a É—akinsa.
Su kuma suka wuce masallacin.

Basu dawoba saida sukayi isha'i.

A haka dai Rayyern yayi jinyar É—an motsawa kaÉ—an da ciwon cikinsa yayi.
Cikin ikon Allah cikin mako ɗaya ya samu lfy, sosai yanzu ƙarfin jikinsa ya dawo.
Yau Monday har asibiti yaje sai dai sam bakinsa ba daÉ—i shi yasa bai iya cin abinci.

Jannart kuma bata wani ganinsa bare wata mgn ta haÉ—a su.

A can sashin Alhaji idi Saleh Dakata kuwa.
Duk yadda Barrister Kabir ya zaci takun yayan nasa ya wuce zatonsa.
Hakan yasa ya tsananta matakan irin bi diddigi.
Da taimakon Baba Ado da Ashiru.

Duk yadda yaso gano ainihin zuciyar yayan nashi ya gaza ganewa.

Yah Azeez kuwa sosai ya shiga tashin hankali.
Wanda saida yayi jinyar ciwon da tashin hankalin yasakar masa.

Mom da Abdul kuwa gaba É—aya gidan ya juye musu.
Domin abun ya musu yawa, ga Daddy da hawanjininsa ke yawan tashi, bini-bini ciwon kai an tafi asibiti.

A can tashar Arewa 24 TV kuwa.
Gaba ɗaya Aisha Lawal da Aunty Fauziyya D Sulaiman da Hajia Rabi'ah, dama sauran ma'aikatan hankalinsu yayi matuƙar tashi, da jin labarin ɓacewar Jannart.

Musamman Salman da gaba É—aya ya gigice ya É—imauce.
Dan abun ya daki zuciyarsa sosai, hakan yasa ko aiki yanzu ya dena zuwa, dan shi a zatonsa akan shirinsu aka sace ta sai yake gani shine next target din masatan.
Ganin tashin hankalin da yake cikine kuma yasa.
MD neman Barrister Kabir yayi mishi bayani.
Dole yazo har gidansu shida MD.
Nan sukayi mishi duk bayanin abinda ke faruwa.
Toh Alhamdulillah ya samu nitsuwa sai dai kuma ya shiga ruÉ—ani.
Nan MD ya gyara zamanshi tare da cewa.
“Yanzu dai sai ka kwantar da hankalin ka.
Ka fara zuwa aiki�.
Da sauri yace.
“Toh Ni da waye zamuyi aikin?".
Cikin sauƙe numfashi MD yace.
“Yanzu zamu bawa Asiya riƙon kwaryar shirin zuwa, lokacin da komai zai dai-dai-ta.�
Cikin tarin ruÉ—ani yace.
“Toh ita Jannart fa?�
Da sauri Barrister Kabir yace.
“Kada ka damu da mgnar Jannart komai zai dai-dai-ta da izinin ubangiji.�
A hankali yace.
“Toh Allah ya yarda.�
Amin Amin sukace kana suka sallameshi suka tafi.

A gajiye ya dawo cikin gidan.
Ko yanzun fitowarsa kenan daga cikin mota, Yayinda Usman PA ke riƙe da marfin motar.
Cikin kulawa yace.
“Sannu�.
Kanshi kawai ya gyaɗa kana ya raɓa ta gefen Usman ya wuce.

Shi kuwa Usman binshi a baya yayi, riƙe da jakar laptop dinsa da ɗaya wayarsa, sai wasu files dake hannunsa.
A hankali ya kalli Baba MauÉ—o dake yi masa ya jiki, fuska ya É—an sake tare da cewa.
“Jiki da sauki Baba Mauɗo�.

“Masha Allah. Allah ya ƙara sauki�.

“Amin Amin.�
yace tare da wucewa.

PA na biye dashi a baya.

“Wa alaikassalam�.
Mamy tace lokacin da suka shigo tare da sallama a bakinsu.

“Masha Allah Babana sannu da dawowa ya Office�.
Mamyn ta Kuma faÉ—a.

Shikuwa Rayyern numfashi ya É—an fesar tare da cewa.
“ALHAMDULILLAH Mamy�.
Juyowa tayi ta kalli PA dake gaidata tare da, ajiye kayan uban gidan nasa agefenta.
“Lfy lau Usman ya Umma da jiki�.
Mamyn ta amsa masa tana d’an murmushi.

“Jiki da sauƙi, tace ma in gaidaki�.
Ya faÉ—a yana kallon Rayyern É—in daya nufi Dinning area.

Kai ya É—an juyo tare da cewa.
“Riyyam fa, nasan Ramadan kam mun barshi a asibiti�.

“Riyyam yana sama yanayi musu gyare-gyare.�
Murmushi Usman yayi tare da cewa.
“Toh wai sai yaushe zai koma ne, yanzu fa yafi wata ɗaya da zuwa har ya shiga na biyu, kuma banga yana wani aikinba.�

Da sauri ya kalli Riyyam-nsra dake saukowa yana cewa.
“Toh P.A ko dai korata zakayi ne, wai dan Allah ma me na tare maka ne, nafa gane tun a jirgi ba sona kakeyi ba, to yawo nazo ko kana da mgna?".
Ya ida mgnar yana turo baki.

Dariya sosai PA yayi domin dama akwai yar tsama tsakaninsu cikin dariya yace.
“A'a ni kuma in koreka, to a kaina kake ne?"

Cikin taɓe bakinsa da salon ƴan samarin TIKTOK da sukafi kama dana ƴan daudu yace.
“Toh waya sani�.
Murmushi Usman ya kumayi tare da cewa.
“Mamy ni bari in wuce gida�.

“Toh ka gaida Umma ko Usman�.
“In Sha Allah zataji�
Ya bata amsa.
Har yaje bakin ƙofar fita kuma ya juyo tare da cewa Riyyam-nsra.
“Nest week fa zamu wuce China, dan haka ka shirya mu sauƙeka a ƙasarku.�
Ya ƙare mgnar cikin tsokana.

Shi kuwa Riyyam-nsra murmushi yayi tare da cewa.
“Ayyah to dan Allah ka bari in zamewa Hamma Rayyern PA'nsa mu tafi tare�.

Dariya Usman yayi kana ya juya ya fita.
Shi dai Dr Rayyern bai kulasu bama,

Shi kuwa Riyyam-nsra System É—in da wayar ya É—auka ya koma sama dasu.

Mamy kuwa shiru tayi ta kasa kunneta can kitchine, dan tasan Jannart na ciki taga kuma Rayyern ya nufi can.

A hankali ya sako ƙafarsa ka step ɗin Dinning area.
Ƙamshin da yake jin ya ɗan shaƙa.
Ba tare da tunanin komai ba ya kutsa kai cikin Kitchen din.

Ita kuwa Jannart dake tsaye miyar taushe da man shanu take haɗawa, Yayinda tamaida gaba d’aya nutsuwarta, ga aikin da takeyi din, wanda hakan yasa ita sam bata ma lura da shiba.

Shi kuwa Rayyern yana shigowa cikin kitchine din, idanunsa suka sauk’a akan bayanta.
Wanda dogon gashin kanta ya sauk’o har tsakiyan gadon bayan ta, kasancewar kuma turkish gown ne ajikinta, shiyasa tayi kyau sosai yaudin, duk wani kuruciya da yarintar ta, I mean innocent dinta ya bayyana.

Kallo d’aya yayi mata ya d’auke kansa, tare da tab’e bakinsa, batare kuma da ya aiwatar da abunda ya shigo dashi cikin kitchine dinba, ya juya tare da ficewa, Kai tsaye ya nufi falon Abbansa.

Da sallama a bakinsa ya shiga.
Gefen Abban nasa ya zauna.
Bayan sun gaisane kuma ya É—an gyara zamanshi, kana cikin nitsuwa yace.
“Abba batun tafiya ta China fa na gama komai, Insha Allah Ranar Monday mai zuwa zamu tafi.�

Cikin zuba mishi ido Abba yace.
“Rayyern baza’a bariba kuma, sai ka kara samun lfyar jikinka?�

Dan guntun murmushi Rayyern din yayi tare da gyara zamansa yace.
“Abba ba komai nayi sauki ai zan iya zuwa, kaga in mun je ɗin ma ba dadewa zamuyi ba, dududu bazan fi kwana ashirin ba zuwa da biyar zan dawo�.

D’an jim Abban yayi, kana cikin shakka yace.
“Kai gsky ni dai ban gamsuba.�

Da sauri yace.
“In sha Allah Abba ba komai fa, zanje lafiya nadawo lafiya.�

Kai Abban ya É—an jinjina tare da cewa.
“Kayi shirin tafiyar ne?"
Da sauri yace.
“Ai na gama komai ma, nida Usman zamu je.�
Akaro na barkatai Abban ya sauke numfashi tare da cewa.
“Toh Allah ya kaimu, ya kuma bada sa’a.�

“Amin Amin.� yace.
Jin an fara kiran sallan magriba ne kuma, yasa duk suka mike sukayo al'wala suka wuce masallaci.

Yau jumma'a. Bayan an taso sallan jumma'a ne, kuma suna zazzaune a falon suna cin abinci.
Dan duk basu ci abincin rana ba.
Sabida gudun kada su makara.

A nitse ya turo ƙofar falon ya shigo.
Tare da sallama a saman lips É—inshi, yayinda Usman PA kuwa, ke biye dashi a baya.

Riyyam-nsra ne ya fara mgn ba tare da ya haÉ—iye danwaken da yasa a bakinshi ba yace.
“Hamma Rayyern Mammy tace in gaisheka da jiki.�
Cikin alamun gajiya da É—an yunwa ya gyaÉ—a kai.
Yana mai kallon Mamy da Usman da suke gaisawa.
Kana Mamy na sawa Usman din danwaken a plate.

Shi kuwa Usman kanshi ya É—an juyo ya kalli Jannart dake bare dafeffen kwai.
“Hajia Barka da yamma.�

k’asa ta d’anyi da kanta, batare kuma da ta d’ago ta kalleshi ba, cikin mutumtawa tace.
“Barka dai PA ya gida.�
Tayi maganan tana bare kwan tana sawa a plate din da Mamyn ta turo mata.
Kana ta miƙa mishi.

Ramadan kuwa baki ya É—an bude tare da É—an yin shishitan yaji yace.
“Kai yajin nada zafi my Aunty ƙara min salat da tumatur da kwai ɗin zai ɗan kashe yajin.�
Ya ƙare mgnar yana turo mata plate din, murmurshi tayi tare da cewa.

“Toh sha ruwa kafin nan�.
Ba musu ya É—auki cup din ruwa dan suna masifar tsoron yaji.

Riyyam-nsra kuwa sai ci yake yana tande baki kamar ɓera a gari.

Shi kuwa Rayyern a hankali ya ɗan muskuta tare da kwaɓe fuska.
Ido Mamy ta zuba mishi.
A hankali yasa hannunshin ya shafa cikinsa kana yace.
“Yunwa.�
Yayi mgnar can ƙasan makoshin sa.
Kai ta jinjina tare da jawo plate alamun zata zuba mishi.
Da sauri ya jujjuya kanshi tare da nuna mata Ramadan daketa shishitan.
“Abu sai kace cimar Mayu,mutun yanaci yana gigicewa.
Ai ni in nasa wannan a bakina suma zanyi Mamy.�
Yayi mgnar yana miƙewa tsaye.

Murmushi Mamy tayi.
Ita kuwa Jannart lips É—inta duka biyu ta haÉ—e ta ciza.
Saboda yayi mgnar da ƙarfi kuma da gayya.
hakan yasa acikin ranta tace.
“Uhum ni dai ba mayya bace ato.�

Shi kuwa fara haurawa sama yayi tare da cewa Mamy.
“Please Mamy abu mai ɗan ruwa-ruwa.�
Ba tare da ta kulashi ba.
Ta kalli Jannart tare da cewa.
“Kici mana Jannart.�

Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa.
“Na koshi Mamy sai anjima.�

Juyowa sukayi suka kalli ƙofar ɗakin.
Jin ana bubbugawa.
Da sauri Riyyam-nsra dake ta hanyar kofar ya mike tare da zuwa ya buÉ—e.
Fahad ne telan Mamy da ta bawa kayan Jannart.
Cikin sauri Riyyam-nsra yasa hannunsa ya amsar masa jaka É—aya tare da cewa.
“Bismilla shigo ciki, Mamy Fahad ne.�
Yayi mgnar yana shigowa Fahad na biye dashi a baya, yana dariya tare da rufe ido.
Da sauri Mamy ta juyo tana kallon Fahad tare da cewa.
“A Allah mai iko al'ƙawarin tela bai zuwa masallaci, nanfa ace min mako, biyu, har zance yayi yawa ma, amma nai shiru sai gashi kuma sai yau ka bullo.�
Dariya mai sauti Fahad din yayi tare da ajiye jakar hannunshi.
Kusa da inda Riyyam-nsra ya aje na hannunsa.
Kanshi ya É—an shafa tare da zama gabanta kana anutse yace.

“Wlh akasi aka samu zazzaɓi ne ya...�

Da sauri Ramadan ya katseshi da cewa.
“Dan Allah kada ka daurawa kanka ciwo Fahad kai dai kawai kayi shiru.�

Dariya yayi tare da cewa.
“Toh Hajia buɗesu ki ganima zaki sha, mamakin kyansu da tsarinsu.�

Murmushi Mamyn tayi tare da cewa.
“Toh Jannart tattare plates din nan.�

Murmushi Jannart din tayi tare da fara tattare wurin.
Ita kuwa Mamy Fahad din ta zu bawa danwaken tare da sa mishi duk kayan haÉ—i.
Gyaran zamanshi yayi tare da fara ci.
Yayinda Jannart kuwa ta gyara wurin.

Riyyam-nsra kuwa kayan ya fara jawowa da sauri Fahad yace.

“A kai malam dakata ya kake figosu haka? a dinke a goge suke da ko wanne yana haɗe da ɗan uwansa cikin leda.�
Ya ƙare mgnar yana matsar da plate din gabanshi ya matso.
Kana ya fara fito dasu daya bayan daya saida ya fiddasu kab, kala ashirin da biyar.
Shadda biyar lace biyar atampa biyar material biyar shadda lace biyar.
A hankali ya fara ware É—inkin wata shadda pink color, wacce akayiwa É—inkin fent wok mai masifar kyau dan doguwar rigace.
“Masha Allah gsky ɗinki yayi kyau�.
mamy ta faÉ—a tana kallon rigar atamfar da ya kuma warewa.
Irin É—in kin nanne na duwatsun shuwariski masu masifar kyau da akabi da kelleyen kolliyar.
Kasan cewar atampar koriyace sosai take daukar ido.
Medata yayi ya ninke tare da jawo wani shadda lace, mai azabar kyau pink and purple mai É—an karen tsada.
Sai wani lace ya kuma fiddasa kalan yellow and orange, anyi masa É—inkin gariyar mata mai masifar kyau.

Ita kanta Jannart kai ta jinjina dan ta gamsu da kalar kayyakin, da zafafan É—inkuna na zamanin da suka samu.

Cikin jin daÉ—i Mamy tace.
“Kai sannu da aiki Fahad na huce, dan gaskiya kamana dinki mai kyau, ninkesu kawai medasu leda, dama
nasan ɗinkinka ai babu haifi�.

Murmushi yayi cikin jin daÉ—i kana ya medasu cikin leda.
Tare da ci gaba da cin danwaken.

Cikin jin daÉ—i Jannart tace.
“Gsky ɗinkuna sunyi kyau.
Allah ya saka da al'khairi Mamy.�
Amin Amin tace tare da kallon Riyyam-nsra tace.
“Yauwa ɗauki kayan kai matasu Bedroom in ta shigo sai ta kimtsasu.�
Da sauri yace.
“To.�
Kana ya fara jidansu.

Ita kuwa Mamy cikin kula tace.
“Nawane sauran kuɗinka Fahad?�

Gyara zama Fahad din yayi, tare da jinjina kansa yace.
“Ba ranan Hadi ya kai min 70k ba da fari kuma kin bani 50k
Yanzu saura 30k kenan Hajjajo.�

Cikin dariya Mamy tace.
“A'a fa Fahad kuke jin tausayin mutane mana kana nufin dubu dari da hamsin kenan a ɗinki kala ashirin da biyar.�
Da sauri yace.
“Allah ko Hajjajo ɗan ma kece kuma nasan ba adawo dasu da wuriba.�

Kai ta jinjina tare da cewa.
“Toh ba matsala Ramadan yi mishi transfer.�
Cikin sauran É—an shishitan yace to.
Kana shi kuma Fahad ya fara gaya mishi ac no dinsa.

Haka dai yayi mishi send 30k din kana yaci yayi haniƙan kafin ya sallamesu ya tafi.

Usman ma tare suka fita.
Shi kuwa Ramadan anan ya miƙa sai bacci.

Mamy kuwa cikin alamun baccin itama tace.
“Yauwa Jannart jeki kimtsa kayanki.
Sai kizo ki samawa mijinki wani ɗan abu mai sauƙi.�
Kai ta jinnina kana ta miƙe.
Riyyam-nsra na cewa.
“Yauwa kiyi ki fito my Aunty zan tayaki.�
To tace kana ta wuce daki.
Itama Mamy dakin ta wuce.

Shi kuwa Riyyam-nsra nan ya zauna tare da fara sana'ar tasa.

Bayan ta gama kimtsa kayan nata kab da shiryasu cin drawer ne.
Ta fito a falon ta samu Riyyam-nsra.

Cikin alamun gajiya itama tace.
“Muje mu dama masa kunu.�
Tayi mgnar tana gaba.
A ranta kuwa tana cewa.
“Mutumin da ba'ayin masa gwaninta, zanyi mgninka ne kunu zan dama maka, idan kaga dama kasha in kaga dama ka bari cikinka ko nawa.�

Shi kuwa Riyyam-nsra yana biye da ita, har cikin store.
Shinkafa danya ta É—iba gongoni biyu.
Ta miƙa mishi tare da cewa.
“Yauwa wonke wannan ka jiƙa min shi�.
Toh yace tare da amsa.

Manyan Robobin dake jere a wurin ta É—an fara budewa.
Tana buÉ—e na forko ta samu tankadedden garin kunune, da alama ya dade É—an har ya fara yin zare-zare.
Tana buÉ—e na biyu kuma ta samu markadedden gyada ne mai kyau, sai nason mai yakeyi.
Cikin jin daÉ—i tace.
“Lah markadedden gyaɗa ai ban saniba,In sha Allah kwannan zan mana miyar kase zan matse man inyi tunkuza.�
A roba ta ukune kuma ta samu barerren ɗanyen gyaɗa, ɗan ƙasa irin jajayen nan.
Ɗan ɗago kanta tayi ta ɗauki roba, gyad’an a diba gongoni huɗu.
Kana ta fito cikin Kitchen din, inda ta samu Riyyam-nsra tsaye ya wonke shinkafar ya jiƙata.

Sa gyadan tayi a tray'n roba ta bushesa tare da tsince duk wani É—an daÉ—i.
Kana tasa ruwa ta wonkesu.
Sannan ta haÉ—esa da shinka fan.

Kujerar É—an table É—in dake tsakiyar Kitchen din Riyyam-nsra yaja ya zauna.
Ita kuma store ta koma, ta É—an dudduba tsamiya, saidai kuma bata samuba.
Da sauri ta fito kitchine É—in.
Fridge ta bude É—an tuno akwai lemun tsami.
Guda biyar ta dauko manya, ta miƙawa Riyyam-nsra tare da cewa.
“Yauwa ga wannan matse min ruwansu.�
Aje wayarsa yayi tare da cewa.
“Toh bani cup.�
Miƙa mishi cup da wukawa tayi,
kana ta koma gaban Fridge din.
Kwakwa kwaya biyu da dabino ta É—ebo, mai É—an yawa sai citta kwaya biyu rak, sai kanamfari cokali É—aya,
tazo ta baresu tare da cire kwallayen dabinon da bawan kwakwan.
Kana ta watsasu cikin shinkafar da gyaÉ—an data jika.
Blender ta É—auko tare da lallatsashi.
Kana tazo ta zuba kayan haɗin duka da yake kofin blender’n, babbane ruwa ta ɗan tarfa ciki,
rufewa tayi tare da kunnawa, ta markadeshi lukui.

Bayan tagama ne kuma ta É—auko tukunya number uku.
Ta lallaye sannan ta dauki rariyar tatan koko.
Shina ta lalleyeshi.
Kana ta juye cikin tare dasa ruwa ta lallaye kofin blendern mai dan yawa ta lallaye ta meda shi wurin zamanshi.
Ta tace markaden.
Yayi wani irin fari tas tamkar madaran shanu.
Gas din ta kunna kana ta ɗan rage ruwan kunun a kofi, sannan ta ɗaura kan wuta, tare da dauko ɗan ƙaramin muciyarsu.
Ta matso kusa tasa cikin tukunyar, tana É—an motsashi a hankali wutan naci, tana nan tsaye tana gaurayashi kuwa har ya fara kauri.
Tana motsashi tana tarfa wannan ruwan data diba tare da ruwan lemun tsamin.
Lokaci ɗaya ya fara wani irin masifeffen ƙamshi yayi kauri yayi fari tas, in ka gani zakace kinɗirmo ne aka burge.
Kashe wutan tayi tare da sauƙe tukunyar.

Riyyam-nsra kuwa aje wayarsa yayi tare da cewa.
“Har kin gama.�
Sai kuma ya matso ganin yadda kunun yake da sauri yace.
“Kai my Aunty wannan ko nono ne kikayi?�

Murmushi ta É—anyi tare da cewa.
“Kunun Gombawa kenan.�
Kai ya jinjina tare da miƙo ƙaramin cup yace.
“Samin in mana dandanel".
Murmushi tayi tare da sa mishi.
Kana ta É—auko wani roba mai kyau ta juyeshi ciki.
Kana ta rage kaɗan tasa a ƙaramin flaks.
Tasa bisa tray'n tasa mug da spoon kana sai madarar gari a roba mai haÉ—e da set din flaks din.
ÆŠayan kuma tasa zumar a ciki.
Kana ta mikawa Riyyam-nsra.
“Ajiye kam table a Dinning.�
To yace ya amsa.
Ita kuma ta jawo nashi kofin kunun, madarar ta saka mishi tare da zuma ta motsa da kyau.
Kana ta miƙo mishi tana cewa.
“Biri in sa wannan kuma a Fridge don in yayi sanyi yafi daɗin sha.�
Kai ya jinjina tare da amsa ya fita.
Ita kuwa ta buÉ—e Fridge ta sashi ciki.
Kana ta wonke komai ta fito.

(Gareku masu karatu.
Kunun yana sauko da ni'ima a jikin mace sosai kana da ruwan nono ga mai shayarwa, ga maza kuma yana sasu feelings yana kuma mgnin ciwon ciki in kin yawaita zuma da dabinon yana kuma gyara fatan jiki.)

Da sauri ta fito falon jin Riyyam-nsra na cewa.
“Wow masha ALLAH kai my Aunty wannan kunun duniya ne, yaseen yayi masifar daɗi.�
Yadda yayi mgnar da ƙarfine yasa Ramadan buɗe idonshi tare da yin tsaki.
Cikin murmushi Jannart tace.
“Kadama ka sake rufe ido la'asar tayi.
Tashi kawai.�
Miƙa yayi tare da cewa.
“Wallahi yajin nanne ya sani bacci.�

Juyowa sukayi jiyo takun.
Rayyern yana sauƙowa.

Kanta ta kauda daga kallonshi tare da nufar É—akinta.
Shi kuwa Riyyam-nsra ya kalla tare da cewa.
“ku tashi kuyi al'wala mu tafi masallaci.�

“To.� Sukace kana duk suka miƙe sukayi al'wala suka mara mishi baya.

Ita kuwa Jannart tana shiga bathroom ta faÉ—a wanka.
Wonka tayi da ruwan sanyi dan cikin kwana biyun nan.
Duk zafi ake É—anyi, alamun sanyi na tattara kayansa zai tafi ya bawa zafi wuri.

Al'wala tayi kana ta fito.

Bayan ta idar da salla ne, ta mike ta isa gaban dreesing mirror'nta, mai ta É—an shafawa jikinta.
Kana ta É—an murza yar fauda tare dasa kwalli sai man baki, da ta É—an goga akan lips dinta, tare kuma da gyara gashin giranta.

Takowa tayi zuwa gaban durowar ta, Ido ta zubawa jerin kayan bayan ta buÉ—e durowar, ahankali tasa hannunta ta jawo ledar da taga wata tattausar atamfa, Black and green color sai ratsin red, wanda akayiwa dinkin riga da zani.
Underwear ta zaro fari ƙal da pant shima fari.
Bayan ta rufe drawern ne kuma, ta dawo bakin gadon ta tsaya, kana anutse ta zura kayan.

Cas kuwa suka zauna mata a jikinta, Musamman rigar da tayi cib-cib da jikinta, breast cup din da aka yiwa rigar tamkar an gwada mamanta ne.

“Kai tela maye ne.�

Ta faɗa lokacin da ta dawo gaban dreesing mirror'nta, ganin yadda ƙirjinta yayi cib-cib a cikin rigar.

ÆŠaurin É—an kwali ta murza tare da fito da jelan gashinta gefe.

Turare mai sanyin ƙamshi ta fesa ajikinta, kana ta zaro gyale red color ta yafa a kafad’anta kana ta fito.

Kitchine ta nufa, sabida jiyo motsin Mamy da tayi.

“Kai Masha Allah diya kinyi kyau".
Mamy tace lokacin da tayi arba da ita.
Murmushi tayi tare da cewa.
“Ngd Mamy".
Ta ida mgnar tana shigowa ciki tare da cewa.
“Mamy ga kunu a fridge.�
Kai Mamy ta gyaÉ—a tare da cewa.
“Au kunu ne ni ai nayi zaton kimdirmo ne.�
miƙowa Mamy hannu tayi alamun ta bata aikin, suyan kayan miyan da takeyi tace.
“Haka Riyyam-nsra ma yace.�

Kai Mamyn ta jinjina tare da cewa.
“Ato bari in na gama zan sha,yanzu bar wannan ɗauko semolina kizo ki tuƙa mana tuwo, yau miyar kuɓewa da bandan kifi zamuyi da tuwo bayanshi bazamu ƙara komai ba mun gaji".
Toh tace kana ta É—auki garin tazo ta fara tukawa.
Ita kuwa Mamy ruwan nama tasa a suyan kayan miyar nata, kana tasa tafasheshshen nama da kifi banda, da É—an dakakken daddawa da citta da kanamfari.

Ita kuwa Jannart bayan ta gama tuka tuwon ta rufeshi yana turara.
Tace.
“Mamy kubewar fa."

“A gata can na gogata.�

Dai-dai lokacin Rayyern ya shigo cikin falon, da sallama a bakinshi tare da daurawa da kira
“Mamy! Mamy!!.�
“Na'am Rayyern gani nan fa�.
Tace tana juyowa tana kallon ƙofar Kitchine ɗin.

Shi kuwa cikin alamun gajiya ya shigo.

Kauda kanshi yayi daga kallon inda take.
Kujera yaja ya zauna tare da cewa.

“Kai Mamy daddawa yayi yawa a miyar nan, ji yadda duk Kitchine din ya dibke.�
Rufe tukunyar Mamy tayi tare da cewa.
“In ta tafasa zai ragu.�

“Mamy yunwa.�
Yace yana mai ajiye wayarsa gefensa.

“Jannart bashi abinda zaici.�

“Toh".
Tace tare da juyawa ta fita.

A hankali ya É—an juyo kwayar idanunsa.
Jin motsin ta ajiye tray'n gefensa.

Yatsunta ya É—an kalla kana ya kauda kanshi.
Ita kuwa bud’e flaks din tayi ta zuba mishi kunun a cikin mug mai dan girma.
Saida ta kusan cikashi, kana a hankali ta ajiye tare da sa spoon ta debi garin madara, cokali uku ta saka mishi, kana ta É—aga robar zuma ta sulala mishi, tare da motsashi kana ta ajiye mishi a gabanshi.
Da sauri ya É—an sunkuyo ido ya zubawa kunun ba tare daya fahimci menene ba.
Cikin kwaɓe fuska yace.
“Mamy me wannan kuma?�
Tana mai fita Kitchen din tace.
“Taɓa kaji.�
Sai kuma ta kalli Jannart tare da cewa.
“Kwashe abin cinnan haka.�

“Toh Mamy.�
Jannart din tace tana mai juyawa ta nufi wurin tukunyar.

Shi kuwa Rayyern idonshi ya lumshe sabida ƙugin yunwa da cikinsa keyi,
ahankali yasa hannunshi ya É—auki spoon din.
Motsa kunun ya farayi wanda yake masu kallon nono, sai dai ganin yana tururine yasashi fahimtar ba nono bane.
A hankali ya É—an ja guntun tsaki.

Sai kuma ya É—an É—ebo cikin cokalin ya É—an É—ago sama ya zubawa kunun ido,
sunkuyowa ya É—an yi harshensa, ya É—an zaro ya É—an laso kunun.

Zir haka yaji yawun bakinsa ya tsinko kunsan Dakta da son zaki da gardi.
Da sauri yasa spoon din a bakinsa ya zuƙe kunun.
Idonsa ya lumshe sabida dandanon kwakwa da zaƙin dabino da zuma da gyadar da yaji sun gigita masa harshe.
Gyara zamansa yayi tare da d’ago mug din ya kai bakinshi.
Kasan cewar madara da zumar sun sa zafin kunun ya koma dai-dai misali.
Kafa kanshi yayi yana mai lumshe idonshi ya fara zukan kunun.
Yana mai jin garɗinsa, saboda d’umin kunun ya wadaci hanjin cikinsa.
A hankali ya É—an janye mug din, yana mai jin dandanon lemun tsamin ya, gyara mishi bakinsa Kunsan bakin mara lfy.

Numfashi ya É—an fesar tare da juyowa ya kalleta tana aikinta kamar bata Kitchine din.
Kafa kai yayi ya shanye sauran kana ya aje mug din, gyatsa yayi mai sanyi kana ya miƙe ya fita yana jin cikinsa tib-tib.

A falon ya zauna bayan ya kara karfin Ac sabida zufan data karyo masa.

Ita kuwa Jannart tana gama kwashe tuwon ta ida miyar, tuni kuma an fara kiran sallan magriba, tana gamawa ta fito.
Yayinda Ita kuwa Mamy tana can wurin Abba.

Washe gari da safe.
Kasan cewar asabar ce tuni u Ramadan sun shiga gari.

Rayyern kuwa sai karfe goma saura ya sauko cikin shigar tattausar jallabiya blue mai guntun hannun.

Kai tsaye wurin Abbansa ya wuce, bayan sun gaisa ne kuma ya tafi wurin Baba MauÉ—o.
Ya dan jima a nan kafin ya dawo ciki.

A falo ya samu Mamy kwance tana kallon tv tuni sha ɗaya ta gota lokacin, gefenta ya zauna a ƙasa tare da jawo system dinsa da ya ajiye kafin ya wuce.
A hankali yace.
“Mamy me aka dafa?.�
Ba tare da ta kalleshi ba tace.
“Dumame mukayi na tuwon jiya dan bai ciwuba, kasan mu kuma muna son ɗumamen dasu Baba Mauɗo duka.�

Kai ya gyaÉ—a dan yasan time to time suna É—umamen duk da shi dai ba ci yakeyi ba.

“Me su Riyyam-nsra sukaci?".
Ya kuma tambayarta.

“Waya san musu ni dai naji Ramadan yanata kwarwa da mita, wai Riyyam-nsra ya cika musu yaji, ina zaton indomie suka soya da kwai.�

Kai ya É—an juyo ya kalleta tare da cewa.

“Toh Mamy yunwan da nakeji ni me zan samu?�
Cikin kauda kai tace.

“Tambayi matarka.�

Da mamaki ya kalleta ganin ita bashi take kallo bane ma, yasa shi yin kwaffa tare da jingina kansa.
Dai-dai lokacin kuma Jannart ta fito daga Kitchen din riƙe da roba da markadedden gyada a ciki, ta ɗan sa ruwa da yar ƙaramar muciya alamun matsan mai zatayi.

Ido Mamy ta zuba mata, ita kuwa Jannart zama tayi gefe a ƙasa.
Kana ta kuma kallon Mamy ganin har lau ita take kallo.
Da sauri tayi ƙasa da kanta ganin Mamyn ta meda kallonta ga Rayyern ɗin.
A hankali ta É—an É—ago ta kalleshi cikin lumshe ido tace.
“Ina kwana?�

A hankali ya É—ago kanshi ya juyo gareta.
Ido cikin ido sukayi, haka nan ba zato ba tsammani bare niya, kawai sai yaji lips É—inshi sun furta.
“B...!

By
*GARKUWAR FULANI*
22/12/2021, 19:45 - 🥰🥰: “Ba abinda za'a bani kenan Mamy.�

Yayi mgnar yana sunkuyar da kanshi, ita kuwa Mamy murmushin dake son subce mata ta danne tare da cewa.

“Gaka ga matarka nan.
Rayyern ka fita idonafa ka dena damuna, ka tambayeta ita mana, ya zaka zo ka tsareni da mita kamar ɗan yaye.�
Kanshi ya juyo ya kalleta cikin kwaɓe fuska ya kontar da kai bisa kujerar.
Cikin sanyi yace.
“Shike nan Mamy na barki.�
Miƙewa tsaye Mamy tayi tare da nufar side ɗinta tana cewa.
“Bari ma in bar maka wurin.�

Ita dai Jannart jujjuya yar muciyar takeyi, tana haÉ—e markadedden gyadan.

Tuni kuma ya fara haduwa ya fara nason mai.
Shi kuwa Rayyern cikin haɗe fuska ya kalleta, kana yayi mgnar can ƙasan maƙoshinsa.
“Ke wai ce miki akayi ni bani da rabone a gidan nan?�.

Juyowa tayi ta É—an kalleshi a fakaice kana ta meda kanta.
Dan bata jishi ba sosaiba ta dai ji alamun yayi mgn kam.

Shikuwa ganin hakanne yasa shi, jan tsaki tare da dan buÉ—e murya yace.
“Ba dake nake mgna ba? Kina jina kinyi shiru.�

Da sauri ta É—ago kanta tare da cewa.
“Ban jiba?"
A kufule yace.
“Kada Allah yasa kiji, idan kunu na na jiya yana nan, ai sai ki kawo min tunda ba ke kika dama minba.�

Jin abunda ya fad’a dinne kuma, yasa ta satan kallonsa, ta gefen Idanunta, batare kuma da tace masa komai ba, ta miƙe tsaye da robar a hannunta.

Kaitsaye dining ta nufa ta ajiye robar,
sannan anutse ta wuce cikin Kitchen,
mug ta ɗauƙa da spoon kana ta buɗe fridge, sassayan kunun ta tsiyaya mishi.
Kana tasa madara da zuma ta motsa, sannan ta É—aura a dan tray.

Anutse ta fito daga cikin kitchine din, hannunta dauke da tray din, ta nufo inda yake.

Isowarta ne kuma yasa shi d’ago kanshi ya kalleta.

Jannart kuwa batare da ta kalleshi ba, ta d’an rusuna agabanshi, tare da ajiye try’n, cikin tafiyarta na nutsuwa kuma ta juya ta tafi.

Shi kuwa Rayyern baki ya taɓe tare da cewa.
“Aniyarku zata koma kanki, wato irin bari ki fara kasheni da yunwa dinan ko, dan kin samu an sake miki ragamar gidan.�
Ya ida mgnar nasa yana kai mug din bakinsa.
A zatonsa mai dumine sai kuma ya jishi mai É—an karen sanyi harda É—an kankara, da sauri ya lumshe idonshi dan sai yaji kamar yafi daÉ—i a hakan, sai yakeji kamar masoyinsa milkybar Chocolate dinsa yakeci, dan wani rin gardi yaji kunun yayi mishi.

Jannart kuwa komawa tayi ta ci gaba da aikinta, dan sosai ta tuka tukunzan nan saida ya haÉ—e da kyau mansa ya fito.
Tsiyaye man tayi a cikin kaskon mai, kana taja kujera ta zauna, tunkuzan ta fara gutsura tana mulmulasu ƴan ƙanana tana sasu kan tray mai ɗan girma.

Yayinda busan doyan da ta daura yake ta tururi alamun ya dahu.

Da sauri ta ida gama mulmula tunkuzan.
Kana ta miƙe ta kaishi cikin store ta ɗaurashi sama tare dasa rariya a kai yadda zaisha iska.

Tana fitowa ta sauke tukunyar ta kwashe doyar cikin, kula biyu manya daya nasu Baba Mauɗo daya nasu sai ƙaramar kuma ta Abba.

Dakakken yajin k’arakon da yasha kayan hadi tasa musu a robobi, kana tasa plates, sannan ta ɗaura wannan man data matse yanzu ta soya, ta sawa kowa.

Ganin kusan ƙarfe ɗaya ne yasa tasa kadan a plate, tare dasa yaji da mai, kana ta fito da salat da dafaffen kwai.

Inda ta barshi a nan ta sameshi ya dukufa kan system É—in nashi.

A nitse ta wuce shi, shi kuwa yatsun ƙafarta ya ɗan bi da ido har saida ta ɓacewa ganinsa.

Bayan sallan azahar ne duk suna zaune a Dinning table.

Cikin zuba musu ido yace.
“Wlh za'a kasheku da yaji sai Ulcer tayi muku mugun illa, Ramadan kafa san illan yaji, jiya war haka kake cin danwake har kana kuka dan yaji, amma yanzu kazo kanacin wani abu daban kuma.�

Da sauri Ramadan yace.
“Wato harda kuka nayi jiyanko, to amman dai gsky wannan ba yaji, kuma wlh yamin daɗi yama fi min a soya doyan da kwai.�
Riyyam-nsra ne ya ɗan kalleshi yana sa farar doya da yajin k’arago, da yankekken kwai da ƴar al'basa da man gyaɗan a baki yace.

“Gsky nima yamin daɗi wlh, dan Mammy na yawan yi mana shi.�
Kai ya jinjina tare da cewa.

“Okay aci daɗi lfy.�
Sai lokacin Mamy ta kalleshi a fakaice tace.
“Kai har zaka cewa wani yasan illar wani abu kuma yake ci, kaida kasan ciwonka kuma kake meda zaki abokin rayuwarka.�

Da sauri yace.
“No Mamy ciwo na bashi da alaƙa da zaƙin.�

Kai kawai ta gyaÉ—a tare da zuba mishi ido irin na tuhuma.
Ganin hakane yasa ya juyawa yayi ya nufi sama...

Haka dai al'amarin zaman gidan yayi ta tafiya.
Cikin kwanakin sosai Rayyern ya samu lfy ya koma kamar da.

A can tashar Arewa kuwa sosai Asiya tayi farin cikin jin lbrin bacewar Jannart daya zo mata da wani nasarar rayuwa.
Tunda gashi aikin da take son din ya dawo hannunta.

A gidan Barrister Kabir kuwa sosai hankalinsa ya kwanta yanzu, ya duƙufa kan fuskantar karar da zai shigar ka'in da na’in, nason tono tsohon zalumcin da aka binne, shekara da shekaru.

Alhaji idi Saleh Dakata kuwa sosai ɓacewar Jannart, ya gigita mishi lamuran rayuwa, wannan yasa ya dade rabonsa dasu Dr.Lukman ma.

Sai dai yau tun safe yake gidan Alhaji Bala Tambari.
Kasan cewar yayi tafiya ne, kusan na wata daya yasa suka jima basu gana ba.

Cikin tsananin takaicin abubuwan da suka faru,Alhaji idi Saleh Dakata ya kalli Alhaji Bala Tambari tare da cewa.

“Toh kaji dai duk abinda ya faru, ni kuwa kaji matakin dana ɗauka, da kuma kalubale da nasarorin dake cikin al'amarin, dole inyi wani abu dan tabbatar da abinda zai kiyaye min ahlina da mutuncina.�

Murmushi Alhaji Bala Tambari yayi kana yace.

“Wannan shirin naka yayi, kaga duk kulafacin mutun da nacinsa bazai cimma manufarka ba, amman inada shawara ta musamman da zan baka, ka bari sai na ɗan huta, zuwa jibi zanzo har gidanka, sai muyi maganan.�

Cikin jin daÉ—i da dukkan yarda Alhaji idi Saleh Dakata yace.
“Toh ngd matuƙa sai na ganka, ni bari in wuce Tababa Company.�

Daga nan sukayi sallama.

Kasancewar yau É—in Lahadi ne, ya kama kuma gobe Monday Dr.Rayyern Mai-nasara da PA'nsa zasu tashi zuwa China.

Yau tun safe daya fita bai dawo gidaba.
Shida Abbansa dan suna Mai-nasara campany'n su da aketa kafa injinun kayan aiki.
Suna dudduba duk wata inji ko ƙarfen dakeda matsala.
Bisa jagoranci Engineer Bello, dan su san me-da-me suke da buƙatar sayan sabo, in yaje China.

Gaba ɗaya wurin masarrafin nasu, suketa dudddubawa yayinda PA ke biye dasu a baya, yana riƙe da woyoyin uban gidan nasa.
Shi kuwa Rayyern rike da system nashi yake.
Yana wasu ƴan rubuce-rubuce da alamu bayanan Engineer bello yake adanawa na abubuwan da suke buƙata.

“Wannan shine babbar matsalar data dakatar da komai, badon shiba da tun tuni an fara sarrafa al'kama zuwa fulawa, kana a medata macaroni indomie, da dai sauransu, ganan Cerelac ma da yayi k’aranci, kuma akwai buk’atar lallai muyisa.�

Engr bello ya faɗa yana nunawa, Dr Rayyern wani ɗan ƙaramin ƙarfen da bai taka kara ya karyaba.

Hannu Rayyern yasa ya amshi ƙarfe
Tare da duba numbers din jiki yace.
“Number 2%�.
Da sauri Engr bello yace.
“Eh to 3% ake bukata dan wannan campany'n ai yafi sauran baki ɗayansu girma da manyan kayan aiki,
na manta ne san da zaka tafi ban cema kada ka sayi kamar na wanda ka saba saya ba�.

Kai Rayyern din ya jinjina tare da cewa.
“Ba matsala a ajiyeshi zaiyi amfani, dan na campany'n Jigawa ya fara samun matsala aturashi can. PA."
Ya faÉ—a yana kallon Usman.

Da sauri Usman PA yace.
“Ok Sir".
Haka dai sukayi ta zazzagayawa.

A gida kuwa Jannart ce tsaye gefen Mamy dake kokarin shiga falonta.
“Mamy zaki shiga ne?".
“Eh.�
tace tare da juyowa tana kallonta.

“Toh me zamuyi abincin dare?�

Cikin bada ishashshen matsayi Mamyn tace.
“Ki dafa duk abinda kike son muci.�

Murmushi Jannart din tayi, kana cikin sauri tace.
“Yauwa to Mamy tukekken tuwon shinkafa da miyar kase kuna ci ko?.�

ÆŠan jim Mamy tayi kana a hankali tace.
“Ba matsala kiyi, ni dai bansan miyarba amman nasan zan iya ci�.
Da sauri tace.
Toh kana ta fada Kitchine ita kuwa Mamy ta wuce falonta.

Tana shiga Kitchine din.
Ta É—auko tukunyar yar madaidaiciya number biyu kenan.
*(Tun bayan gamakarantan littafin GARKUWA anata damuna wai yadda ake miyar kase, shiyasa Jannart zatayita daki-daki Hajia ki kula miyar tana da masifar daÉ—i)*
Lalabe tukunyar tayi kana tasa ruwa fiye da rabin tukunyar kusan cikawa ta É—aura kan gas bayan ta kunna wutan.
Dai-dai-ta wutan tayi Dai-dai misali.

Kana ta debi kayan miyanta masu É—an dama tattasai al'basa, tumatur kaÉ—an duk da tasan basa son yaji ta É—an É—ebi taruhu kaÉ—an sabida miyar kase tana raina yaji ainun.

Jajjagesu tayi, kana ta adanasu gefe ta rufe.

Ganin tukunyar ta fara Bararraka ne, yasa ta wuce store.
Wannan tunkuzan data aje ta É—auko
Ya É—an bushe ya kama jikinsa yayi kam.
Haka yasa ta juyeshi a roba,
kana ta buÉ—e tukunyar ta É—an É—ebi ruwan zafin ta zuba a ciki,
Sannan ta É—auko bushesshen yakwanta, mai kyau ta wonkeshi kana ta sa cikin tukinyar tuni ya fara tafasa,
Sai kuma ta jawo robar tunkuzar da ta zuba tafasasshen ruwan a kai, sauri-sauri ta É—an motsashi ta lallayeshi mgnin É—an kura in akwai.
Kana ta watsasu cikin tukunyar tare da rufewa, ta kuma ɗan ƙara wutan.
Yadda zasuyi ta watsal-watsal da kyau gudun cakudewa shiyasa ba'asa tunkuzar sai ruwan ya tafasa da yakuwar a ciki,
Rufewa tayi.
In a take kika mulmula tunƙuzarki ba sai kin lallabeta ba,
Yakuwar anfi son bushesshe dan zaifi É—an tsami.
Amman in ba busashen zakisa É—anyen ma ba matsalar komai.

Tukunyar ta buÉ—e kai ta jinjina ganin, yana ta watsal-watsal mulmulayen tunkuzar nan suna ta jujjuyawa.
Yayinda tuni man jikinsu kuma ya tsastsafo sosai kai kace tasa mai.

Juyawa tayi jikin Fridge.
Soyayyan naman miyan da suke ajiyewa, ta ɗibo mai yawa, tare dasa ƙasusuwan tantakwashi, kana ta zo da plate din kan table ɗin, kara yayyanka naman tayi kanana.

Sannan ta buÉ—e tukunyar ta watsashi ciki ta rufe.
Watsa-watsa haka yake tafasa, ruwan naman yana tsastsafowa yana gaureyewa.
Tuni kuma tunkuzar ta kame jikinta, ta fara komawa tamkar hanta ga ganyen yakuwan yayi shar gwanin kyau, karamar tukunya ta ɗauka a gefen, man gyaɗan hannu tasa kadan, Kana ta juye kayan miyar nan, ta ɗan soyasu sama-sama kana ta sauƙesu.

Bandan kifi tarwad‘a ta ɗauki guda huɗu cikin kwalin da kifin suke a store.
Baresu tayi kana ta gyarasu ta fito da tsokokin ras.
Guntun ruwan dumin data bari ta juye kan kifin.

Kana ta debo al'basa ta yanka mai yawa, irin ƙananan yankan nan.
Citta da kanamfari ta É—an daka.
Kana ta buÉ—e tukunyar ta saka su.
Lokaci ɗaya suka fara zuba ƙamshi.
Rage wutan tayi Dai-dai misali.
Kana ta kimtsa komai.
Ganin la'asar tayi ta fita ta wuce É—akinta dan yin salla.

A hankali ta fito daga cikin Bathroom din bayan tayi al'wala.

Miƙewa tayi kan sallayar bayan ta idar da sallan.
Sabida sanin miyar tana buƙatar wuta sosai.
Wuta kuma nitsetstsen wuta, ba wurrururun nan ba, an gane ko?

Mamy kuwa bayan tayi sallan bacci ne ya saceta bisa sallayan.

Ita kuwa Jannart huɗu da kwata dai-dai ta miƙe tsaye.
Ninke sallayar tayi kana ta fito ta nufi Kitchen din.

Shiru gidan alamun babu kowa, hakan ne yasa ta kunna tv, tasharsu ta kunna dai-dai lokacin kuma aka sako tallar cekiyanta da akeyi.

Da sauri ta koma da baya ta zauna bisa kujera.
“Allah sarki Daddy na bawan Allah na sashi a tashin hankali, Allah na tuba, Astagafirullah Allah ka yafe min sa mahaifina da nayi a damuwa, Allah ya isa tsakanina da kai, Yah Junaid tunda sanadin ka ne komai ya faru.�.
Cikin rauni a fili yace.
“Anya kuwa Abba Kabir yayi abinda ya dace kuwa, raba uba da yarsa ?�

Ta ƙare mgnar hawaye masu zafi na tsilalo mata.
Haka nan bege da kewar mahaifinta ya dawo mata sabo, sosai idonta ke zubda hawaye, haka ta nufi Kitchine din.

Hannunta tasa ta sharce hawayenta sabida idonta bai gani da kyau, saboda ruwan hawayen daya cikasu, wanke hannunta tayi, kana ta juya zuwa kan tukunyar miyar nata.

BuÉ—ewa tayi tare da dauko ludeyi ta É—an motsashi, tare da É—aukan mulmullen tunkuza É—aya ta matseshi ta fasashi, kai ta jinnina ganin ya nuna, yayinda kuma har yanzu hawayen ke tsastsafo mata.
Tunkuzar ta nuna tayi dir-dir da ita ta dahu ta koma tamkar hanta.
Naman nan kuwa gaba É—aya yayi ligib ya diddige.
Tantakwashin kuwa yayi taushi.
meda marfin tayi ta rufe, Kana ta matsa gefe.
Su maggi Curry da dai sauran kayan ɗandanon ta ɗibo dai-dai yadda take buƙata ta ajesu a plate.
Kana ta É—auki tukunyar tuwo number biyar tasa ruwa, kana ta hura wutan É—aya gefen gas din ta daura tukunyar tuwon.

Yankekken albasan nan ta dauko ta watsa a ciki.
Kana ta É—auki kifi bandan nan ta saka,
Tare da debo wani tafasheshen nama da ruwan tafashen kadan ta saka
Kana ta rufe su.

Shinkafar tuwon ta debo,
tazo ta ajiye a gefe.

Kana ta buÉ—e tukunyar miyar ta juye soyayyan kayan miyan nan nata duka aciki.

Sannan tasa duk kayan dandano dana ƙamshi, kana ta meda marfin ta rufe sannan ta ɗan rage wutan.

Ahaha gaba É—aya gidan ya É—auki kamshi, yayinda miyar kuwa taketa
Bul-bul mai yana ta tsastsafowa komai yayi dai-dai miyar tayi masifar kyau.

(Tsokaci ba dole sai da nama ko kifi ba, ana iya yinta haka nanma ita É—aya kuma tana daÉ—i matuka gaya.
Tana son wuta sosai a wurarenmu fulani masuyinta a tukunyar ƙasa mukan ɗaurata tun safe ko azahar in zamuci tuwon dare da ita.)

Kai ta jinjina jin yadda miyar ke zuba ƙamshi, sai yanzu ta samu kuma hawayenta ya tsaya.

Shinkafar ta wonke wacce take mudu É—aya kwanon sha, dan suna da É—an yawa, gidan duk da ma dai tasan masu cikashi sosai.
So tana son É—umamen miyar kase tasan kuma ba mamaki su Mamy ma su so.
Duk da shi miyar kase in kana cin tuwo malmala biyu to in itace malmala É—aya ma zata isheki.

BuÉ—e tukunyar ta kumayi tare da motsa miyar ganin komai yayi yadda take sone yasa ta meda ta rufe, tare da kashe wannan wutan.

Dai-dai lokacin Mamy ta shigo Kitchen din tana mai cewa.
“Kai-kai Jannart yau me kike dafa mana haka gidan yaketa baza ƙamshi�.
Ta ida mgnar tana buɗe tukunyar miyar da sauri ta shaƙi daddaɗan kamshi tare da cewa.
“Masha Allah, tab lallai yau Ramadan akwai kwasar gara, irin wannan dege-dege haka, gashi dama gwanin son nama�.
Tayi mgnar a zatonta duk namane,
fahimtar hakanne kuma yasa Jannart É—an yin murmushi tare da cewa.
“Ato in ya gani kam zaiyi zaton duk nama ne ba kasenba�.

Da sauri Mamy tasa ludeyi tana É—an juya miyar kana ta juyo ta kalleta tare da cewa.
“Yoh ai nima nayi zaton duk namane".
Tana mai rage wutan tuwon ganin tsanewane ya rage mishi tace.

“Akwai naman ma kam, miyar tana son nama sosai�.
Murmushi Mamy tayi cikin jin daÉ—i tace.
"kai masha ALLAH.Yanzu bari in ƙarasa tuwon tunda kinyi mai wuyar, je kiyi wonka ga magriba ta gabato�.

Cikin yanayin gajiya tace
“Toh Mamy.�

Kana ta fita ta tafi.

Ita kuwa Mamy matso da foodflask guda uku tayi, biyu yan madai-daita daya karami.
Miyar ta zuba da zafinta cikin na miyansu Baba Mauɗo saida ta cika musu kular, kana tasa a ƙaramar na Abba kenan.
Sannan tasa a dayar tasu kenan, kowanne ta zuba namomin da tsokokin kifi bandan kana da kasen da kyau, rufe tukunyar tayi kana ta buɗe ƙasan gas din ta ajiye sauran miyar.

Muciya ta ɗauko ta tuka tuwon da kyau tana tarfa garin fulawa kaɗan, hakan yasa tuwon ya tuku yayi dank’o mai kyau, y’ar kwaryar da suke malmala ta ɗauko ta rinka malmalawa tana sawa a kulolin.

Kwaya biyu ta sawa Abba dan tasan cikin mijinta.

Su Baba Mauɗo kuwa kwaya tara ta saka musu, sannan auran kuma da zasu kai goma sha ta juye a kularsu, kana ta tattare wurin ta wonke duk abinda suka ɓata.
Sannan ta dauki tray'n na Abba ta kai falonsa, sannan ta dawo ta shirya nasu kan Dinning table, Bayan tasa plate biyar da dan na miyarsu da spoons.

Sai kuma nasu Baba Mauɗo ta aje kular akan Fridge sannan ta hada musu plate da sauran abin buƙata.

Komawa tayi É—akinta dan yin alwala.

Jannart kuwa tsaye take agaban dreesing mirror'nta.
Da alamun tayi wonkanta da al'wala, wani zazzafan lace ne ta saka mai orange, pink, and yellow color É—innan,
dinkin ayi masifar yi mata kyau.

Gashin kanta take tajewa, tana gamawa kuwa ta tubkeshi a keyarta, Kana ta ninke É—an kwalin tayi É—aurin da shi kaÉ—ai tafi iyawa, sabida ita dama tafi ta'ammali da kananan kaya.

Banda hoda ba abinda ta sawa fuskarta, ko man baki bata saba tabar natural pink lips É—inta.

Turare ta fesa kana ta gyara É—aurin.
Yayinda ta tubke gashin a ƙeya hakan ya taimakawa ɗaurin yayi ras.

Hijabi tasa jin an kabbarta sallah a masallatai.

Bayan ta idar da sallan ma bata tashi ba.
Sai da akayi isha'i, tana idarwa ta yafa É—an siririn mayafi pink color kasan cewar akwai ratsin pink a lace din.

A falon ta samu Mamy ita É—aya.
Gefenta ta zauna tare da cewa.
“Mamy ke ɗaya?�.
Juyowa tayi ta kalleta cikin kulawa tace.
“Wlh kuwa kinga yau har yanzu Abbanku da Rayyern basu dawo ba.
Gashi su Ramadan ma shiru...�
Ta ƙare mgnar tana kallon himilin gashin Jannart ɗin.
Ita kuwa Jannart cewa tayi.
“Mamy ki kirasu mana to�.
Miƙewa zaune tayi tare da cewa.
“Toh".
Sai kuma ta É—ora da cewa.
“Jannart ko dai inyi miki kitso ne? Naga tunda kikazo kan a tsefe�.
Da sauri tace.
“Ai kuwa ina son kitso Mamy�.
Murmushi tayi tare da cewa.

“Toh ba matsala bari muci abinci sai inyi miki koda cukune, tunda naga bakya son barinshi a sake, kinga sai ki tubke abinki�.
Kai ta gyaÉ—a kana ita kuma Mamy wayarta ta É—auka tare da cewa.
“Bari dai in kira s..�
Bata ida rufe bakinta ba Rayyern ya turo ƙofar ya shigo da sallama, kana PA na biye dashi abaya.

“Masha Allah kinga ɗan halal yaki ambato.�
Mamy ta fada.

Shikuwa Rayyern din cikin yanayin tarin gajiya da yunwa, ya zauna gefen Mamy tare da fesar da numfashi kana a hankali yace.
“Wash Allah na Mamy na gaji, kishi da yunwa kamar zasu karni.�

Da sauri Mamy ta miƙe tare da cewa.
“Toh Jannart kinji shi, ni nayi can nasan Abbanshi ma a gajiye ya dawo."
Ta ida mgnar tare da kallon PA kana tace.
“PA kada ma ka zauna a nan ku iso kan Dinning table kawai�.
Ai kuwa murmushi PA yayi tare da biyo bayanta yana cewa.
“Hajia azo a bamu abinci.�
Yayi mgnar yana kallon Jannart.

Ita kuwa Jannart miƙewa tayi a hankali ta ɗan saci kallonsa cikin sanyi tace.
“In kawo maka nanne?�.

Da alamun tarin gajiya da kuma fitinenneyar yunwar, daya kashe masa jiki ya kad’a kai kawai.

Ganin hakanne kuma ya sata juyawa ta nufi dining area.
“PA ya dai kana tsaye zauna mana�.
Ta fadi haka, saboda ganin Usman PA da tayi a tsaye.

Da alamun sauri yace.
“Kai inaga ni bani abincin zan wuce gida dashi naci ko a mota.�

Cikin mamaki tace.
“Saurin me kakeyi haka?�
Tayi mgnar tana shigewa kitchine.

Wani dan kyakkyawan kula ta dauko mai haÉ—e da na miya.
Kana ta dawo shi kuwa PA fridge dake gefensa ya buÉ—e tare da cewa.
“Wlh banyi shiri bane kuma gobe da sassafe zamu wuce Abuja, saboda bayan azahar zamu wuce china.�

Kai Jannart din ta jinjina mishi, tare dasa mishi miyar bayan ta sa mishi tuwo malmala uku.

Amsar kular yayi kana ya sauka da sauri, ya sallami uban gidan nasa ya tafi.

Ita kuwa Jannart tray'n ma dai-dai-ci ta ɗauka, plate ta ajiye akai, kana tasa tuwo malmala biyu, tare dasa wani plate din ta rufeshi, sannan tasa miyar acikin wani dan bowl na glass k’arami mai kyaun gaske, Koda tazo diba masa miyar kuwa, sosai ta sa mishi nama da kifin, bayan ta kammala ne kuma, ta saka murfin bowl din ta rufe,
kana ta É—auko goran faro mai sanyi da cup.
A hankali ta ɗauki tray'n tare da sauƙowa akan steps din.

System ɗinshi ne ke bisa cinyarsa, wanda hakan yasa bai kalleta ba, santer table ɗin baƙin Glass din,ta jawo gabanshi bayan ta aje tray'n a kai.

Batare kuma da tace masa komai ba, ta juya ta koma cikin Kitchine din.

Wani É—an roba mai kyau ta É—auka tasa ruwa a ciki kana ta koma ta ajiye a gefen tray'n.

Dai-dai lokacin ne kuma Mamy ta futo, hannunta riƙe da kum da kifiya.
Kan kujerar dake fuskantar wacce yake kai Mamyn ta zauna tare dace wa.
“Yauwa Jannart kin gama masa ko, to zo mu fara kitson kawai.�

Da sauri Jannart din tace
“To.�
kana ta matso gabanta ta zauna a ƙasa bisa carpet din.

Tare da ture É—an kwalin kanta.
Ita kuwa Mamy dan matsowa tayi gaba kaÉ—an tasa hannunta.
Ta fara warware gashin Jannart din dake tubke.

“Wai-wai Masha Allah, Jannart gashin naki ya cika santsi anya zan iya kitsashi kuwa ga yawa ga tsawo�.
Mamy ta faÉ—a lokacin da ta gama warware jelar gashin.

A hankali tace.
“Yana da wuyan kitso kam Mamy, ko zamu bari saida safe.�

A hankali ya É—ago kansa ya kallesu,
Idonshi ya tsaida kan tarin gashinta dake kwance bisa kafadunta.
Fuskarshi ya É—an ya mutsa kana a hankali yace.
“Mamy kitso kuma anan ga abinci na�.

Ba tare da ta kalleshi ba ta fara tattare gashin dan taga a taje yake.
“Ga can wurin cin abinci kaje can�.
Ta faÉ—a tana nuna mishi Dinning area.

Cikin gajiya yace.
“Wlh na gaji ne Mamy�.

“Toh zauna kana can muna nan, kuma ba taje kan zamuyi ba, me hadinmu da kai�.

Fuskarshi ya kwaɓe tare da aje system ɗin nashi.
Kana ya gyara zamanshi tare dasa hannunshi cikin roban wonke hannun yana mai cewa.
“Kiyi hakuri bari inci da sauri-sauri sai kuyi�.

BuÉ—e plate din yayi kana ya buÉ—e miyar.

Ido ya É—an zubawa miyar tare da cewa.
“Mamy wannan fa miyar menene�.

Tana mai tsaga tsakiyar suman tace.
“Ka dan-da na mana ita kaji yadda take�.
Shiru yayi kamar ya maida ya rufe.
Toh kuma yunwar dake zakularshi kara kaimi tayi ganin abincin.
Hannunshi yasa bisa tuwon ya ɗan gutsuro ƙarami.
“Gaba ɗaya ni ba son cin tuwo da dare nakeyi ba, sabida sa katon ciki yakeyi�.
Ya faÉ—a yana mai É—an yago miyar ya haÉ—a da gayan tare da yin bismillah.
Ya nufi bakinsa da loman yana mai kallon miyar.

A hankali yasa loman a baki.
Da sauri ya murza harshensa yayi gefe dashi tare É—aukan gayan da miyar.
GarÉ—in miyar ne ya sashi jan nannauyan numfashin kana ya lumshe idonshi.

Zamanshi ya gyara tare da kai hannunshi ya gutsuro loma ta biyu.
Yana mai jin wani irin tsinkewa da yawun bakinshi sukayi.
Ga É—an-danon Nama, kifi, kasen.
Kana ga wani É—an tsami-tsami mai shegen daÉ—i more Especially ga bakin mara lfy.

Miyar ya diba da É—an yawa ya haÉ—a da gayan kana yasa a baki.
Yan kananan tsokokin naman da kifin, ne da diddigin naman ya tauna cikin jin marmarin cin abincin.

Mamy kuwa ido ta zuba mishi.
Sabida taji yadda Abba yayi ta santin miyar har ya cinyeta tsab.
Har yana cewa gobe É—umamen zaici, ya shiga wonkane ta fiton.

Sunkuyar da kanta tayi ta fara yiwa Jannart É—in kitson.

Shi kuwa Rayyern matsowa yayi bakin kujerar da kyau.
Yaci gaba da cin abinci.

“Bari kawai inyi miki manyan ibra zasuyi miki kyau�.
Mamy ta faÉ—a tana fara kitson.
Dago kanshi yayi ya kallesu.
Yatsun Mamy ya É—an kalla ganin yadda take sasu cikin tattausar sumar mai É—an karen sulbi.
Haka nan sai ya gaza É—auke idonshi kan gashin.

Wuyanta ya ɗan kalla fatar fara ƙal kana wuyan yayi wani rin zane kamar guru-guru haka.

Ta goshinta kuma gashin ne ya kwanta lib-lib Mamy na janshi yana suɓalewa.
A hankali ya rumtse idanunshi sabida sun gaza daina kallon.
A fizge ya sunkuyar da kanshi yaci gaba da cin abincin.
Yayinda idanunshi kuma suka sauka akan.
Tattausan tafin kafafunta da suke a naÉ—e.

Sosai yaci abincin yana mai kallon himilin gashin.

A hankali yayi wani sassanyan gyatsa, tare da aje goran ruwan daya sha.
Kana ya É—an ture tray'n gefe tare da É—aura sawunshi kan table É—in ya samu yayi balance domin cikinsa yayi masa nauyi.
Dan kab tuwon ya cinye.
A hankali yace.
“Alhamdulillah".
Sai kuma yayi wani sassanyan gyatsa

Kana ya É—an kallesu.

“Kai tray'n Kitchen kizo muci gaba�.
Mamy ta faÉ—a tare da sake kan Jannart.
Ita kuwa miƙewa tayi tare da isowa gareshi ba tare da tasa dankwali ba.
Sunkuyowan da tayi ne kuma yasa gashin tahowa.
Har yana taɓa yatsun ƙafarsa.
Wani irin masifeffen taushi da tsulbin gashin ne yasashi jin tsikar jikin sa mimmiƙewa,
Kauda kanshi yayi tare da miƙewa.
Ya nufi sama.
Ita kuma ta kai tray'n kana ta dawo sukaci gaba.

Suna gamawa su Ramadan na shigowa.
Haka yasa suka wuce Dinning area.
Sosai sukaci abinci fiye da zatonsu sunaci suna zuba santi.

“Kai gsky nima gobe d‘umame zanci Mamy�.
Ramadan ya faÉ—a yana taunar tattausan sokan nama.
Riyyam-nsra kuwa cewa yayi.

“Ni gsky bazanci dumameba amman a ajiye mana miyar gobe da rana amana tuwo.�
Dariya Mamy tayi tare da cewa.
“Gsky dai miyar tayi daɗi, kamar za'a iya cinta da shinkafa fara ko?�.

Dariya sosai Ramadan yayi tare da cewa.
“Jama'a waiji yaseen Mamy kema yau kin shiga motar santi�.

Cikin danne dariya Jannart tace.
“Ba wani santi Mamy ana iya cinta da farar shinkafa madadin miyar stew ko mai da yaji".

Haka dai sukayi ta hira sai kusan karfe goma da rabi suka watse.

Washe gari da Asuba, bayan sun dawo masallacin.

Zaune suke a falon baki É—ayansu.
Yayinda PA ma shigowarsa kenan

A hankali yake takowa yana saukowa.
PA ne ya nufi inda yake yana kallon agogon hannunsa.
Shida da rabi kuma bakwai dai-dai jirginsu zai tashi.

Yana gama saukowa yazo ya zauna kusa da Abba tare da cewa.

“Toh Abba zamu tafi.�

Cikin tsananin kulawa Abba yace.
“Toh Rayyern Allah ya bada sa'a ya kaiku lfy ya dawo daku lfy ya tsareka da sharrin abin ƙi�.

Da “Amin.� suka amsa baki ɗayansu.
Kana ya kalli Mamy.

Mamy ko gane me yake nufi ne yasa tace.
“Allah ya kaiku lfy babana ya dawo daku lfy, PA ka kular min dashi da kyau musamman kan cin abinci.�

Kai Usman PA ya gyaÉ—a bayan sunce Amin.
Shi kuwa juyowa yayi ya kalli Riyyam-nsra tare da cewa.
“Zan dawo in sameka ko?"
Da sauri ya gyaÉ—a mishi kai yana mai yin rau-rau da ido yace.

“Yesss Hamma Rayyern zan jiraka sai ka dawo, duk da Mammy tana matsawa in koma".

Kanshi ya jinjina tare da cewa.
“Toh banda yawon banza, da shashanci, kai kuma Ramadan ka kula da aikinka, kasan ganinka zaisa sauran Doctor's din karsashi.�

Cikin gamsuwa Ramadan yace.
“Toh Hamma Rayyern Allah ya kiyaye hanya, Insha Allah kuma zan kula.�

“Amin.� Yace yana mai miƙewa tsaye.

PA kuwa tuni ya fita, yayinda Ramadan da Riyyam-nsra suka mara mishi baya.
Kana shima Rayyern ya bisu a baya.

“Rayyern!!�.
Yaji muryar Abbanshi da sauri ya É—an juyo.
Ƙofar ɗakin Jannart ya nuna mishi tare da cewa.
“Dan Allah ka shiga ka sallameta, na roƙeka da girman Allah.�

Wani irin abu mai nauyi yaji ya danne masa zuciya.
“Ya salam".
Ya fadi a ransa jin Abban yace ya hadasa da girman Allah wato badon shiba.
Wani rauni, da damuwa ne suka rufesa, sabida ganin da yayi suna gab da sashi a sahun ya'ya marassa biyayya.

A hankali ya juya nufi ƙofar dakin.

Ita kuwa Jannart kasan cewar bakonta (al'ada) ya dawo daren jiya ne, yasa yanzu ta fito daga wonka daga ita sai towel ajikinta, take zaune agaban dreesing mirror'nta.

Rayyern kuwa ahankali ya tura ƙofar falon ya shigo, tare kuma da maida kofar ya rufe.
Ahankali kuma ya tako zuwa tsakiyar falon.
Murya a dakile yace.
“Salamu alaikum.�

Jannart dake zaune kuwa shiru tayi, tare da aje goran man da take shafawa, dan jin kamar mgnar mutum, Jin shiru babu alaman wani motsinne kuma yasa ta cigaba da shafa mai dinta.

Still tana cikin shafa maidin ne kuma tasake jiyo kamar sautin muryar mutum.
Da sauri ta mik’e tsaye tare da nufar kofar fita, ahankali ta bud’e k’ofar tare da d’an lek’o kanta tace.
“Waye?�

Shiru yayi ba tare daya bata amsaba.

Jannart kuwa hakanne yasa ta sake leƙo da kanta, sai dai bata ganshiba.

Jin kaman da gaske ba kowa acikin falonne kuma yasa ta fito gaba É—ayanta.
Inda tayi taku É—aya ana biyu ta ganshi tsaye.
Cikin wasu irin fitinannun Suit bakake masu masifar kyau da sheƙi.

Da wani irin sauri ta juya ta koma cikin labule.

Shi kuwa Rayyern dauke kansa yayi gefe, kamar bai ganta ba murya a dakile yace.
“Na tafi.�

Da sauri, kuma cikin muryarta dake rawan fargaban ganinsa da tayi, da kuma ganinta da yayi ahaka tace.
“Allah ya tsare ya kiyaye hanya�.

A takaice yace.
“Amin, idan da zuciya ɗaya kika fada�.
Yana faÉ—in haka ya juya ya fita.

Jin alamun fitansa ne kuma yasa ta fitowa, daga inda ta boye cikin sauri ta koma cikin bedroom din, tana nanata mgnar sa ta karshe, da taji ya fada.

Shi kuwa yana fita, kai tsaye Airport suka wuce.

Su Ramadan kuwa basu dawo ba, saida sukaga jirginsu ya tashi suka dawo tare dasu Hadi.

Su Rayyern din kuwa a Abuja sukayi breakfast.
Kana sai ƙarfe huɗu dai-dai na yamma jirgin da zai kaisu China ya tashi.

Acan gidan kuwa Ramadan na dawowa ya tafi aiki, Yayinda Riyyam-nsra kuma kofar gida ya fita wurin Baba MauÉ—o.

Su kuwa su Dr.Rayyern Mai-nasara dare ya fara nisa sosai jirginsu ya sauka a.
Beijing Capital International Airport China.

Suna fitowa a jirgi.
PA yace.
“Yah Subahanallahi, tsarki ya tabbata ga Ubangijin talikai mai duniya da ƙiyama.�

Rayyern kuwa limshe idanun sa yayi.
Duk da yazo wurin nan a ƙalla sau biyar.
Amman idanunsa kullum a sabo suke ganin Airport É—in, sabida masifar kyau da tsananin haÉ—uwa.
Duk da tsakar dare ne kai kace tsakar ranace, sabida yadda wurin yake da masifar kyau da ƙawatuwa.
Ina in an haÉ—a Airport's dinmu na Nigeria da nasu tofa ai namu jujine.

Da dan sassarfa suka fito inda zasu samu taxi.

Bayan sun shigane PA yace ya kaisu hotel mafi kusa da Airport É—in.
Dan campany'n injinun da suke da akalar kasuwancin yana kusa.

Kai PA ya jinjina cikin takaicin Yaren masu idanun kwadin nan wato China sam basu cika gane turanci ba.

Saida Rayyern yayi masa karin bayani da kyau kana ya gane.

Tafiya mai É—an nisa kaÉ—an sukayi sai gasu a wani tamfatsetsen hotel.
China world hotel beijing.

Bayan sun sallameshi ne, suka shiga.

Bayan sun kama daki sun, haura wonka sukayi kana sukayi ramuwar sallan magriba da isha'i, kasancewar sunci abinci a jirgi ba yunwa ba kishi ne, yasa kawai suka kwanta dan yin baccin gajiya, saboda tafiya dai ko ya take tafiya ce.

A nan gida kuwa Riyyam-nsra ne zaune gefen Baba MauÉ—o yana masa gugan kayanshi.
Yayinda shi kuma yake can gefe,
wayarsa dake kusa da Riyyam-nsra ne ta fara ringing.
Juyowa yayi ya kalli Riyyam-nsra tare da cewa.
“Wake kirana?�

Ido Riyyam-nsra É—in ya zubawa fuskar wayar cike da mamaki, ya juyo ya kalli Baba MauÉ—o kana ya Kuma juyowa ya kalli fuskar wayar.
Hakan yasa Baba Mauɗo yun ƙurowa da sauri, cikin rawan jiki ya jawo wayar tasa.
Da sauri kuma ya juyo ya kalli Riyyam-nsra.
Shi kuwa Riyyam-nsra cikin wani irin kallo mai cike da mamaki yace.
“in...!

*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*

NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.

Wannan ita ce mace. Ina da wata saukakkar hanyar da zaki zama abar so da kulawa da soyayya a wajan mijinki ta hanya mafi sauki, 09097853276 hanyar ita ce ki gwada amfani da kayana na gyara ki gani, ina mai tabbatar miki da in sha Allahu sai kin dara da murna sai kuma kin gode min. Kayana kaya ne da aka yi shi da zallan itacanmu na gado marasa illa a cikin jikin dan adam musamman mace, kaya ne da suke taimakawa (sex hormones 😍) dinki.
Misali kina kallon India😘, hollywood, Asian film🥰 kina ganin yanda mazansu ke nunawa matansu tsananin soyayya kamar su ba su kyautar ransu!?
Saboda me hakan? Saboda suna sadaukar da lokacinsu wajan gyara jikinsu da kayan da ke tsattsafo da ni’ima cike da tsukewa, kayan nan kuma ana yinsu ne zallar magungunan gargajiya wanda ba su da illa domin haɗine na ingantattun itatuwa da yayansu.
Ina baiwar Allahn da miji ke daure mata fuska babu hirar arziki?
Zo ki ji yar’uwa zan baki gumbata da zallar gari wanda aka yi su da nagartattun itacen da ke da matukar amfani a jikin mace. Gubar ciko, gumbar tsalle dole, gubar da ba'a baiwa mai kishiya, garin maɗi, garin mallaka, tsumin goron tula, tsumin tsartai, tsumin maratsi, pala-pala butar sirri, kwanon k’asaitacciyar mace, furar mata madararta gareki Hajia takenta sha yanzu mgni yanzu,
Ina mata masu fama da sanyi? Sanyin mara ki zo na hadaki da magani na na sanyi wanda yake wanke mara ya fitar da duk wata cuta da ke samun mazauni a wajan.
Ina da ciccibi mai kyau. Ina da hadin amare mai kyau wanda zai gyara yarinya ya kankaro mata kimarta akwai hadin mai jego wanda muke yinsa na asali inada kekkyawan Hadi maida tsohuwa yarinya.

Akwai daya bangaren wato *KAMSHI*
Kimarki gyaranki da kamshinki. Matan da suka gane suka san yanda za su kankaro da mutunci su ne masu amfani da kayan gyara da kuma sanyaya jikinsu da kamshi, ina da turaren wanka da na bandaki na daki na jiki da na kaya dana tsuguno kamshin turarena na dabam ne mai sanyaya zuciyar wanda ya shaka ina da kayan kamshi na amarya da na maijego da na uwargida da dukkan macen da take kokarin mayar da kanta mai daraja a idon kowa ta zamo sarauni a idon mijinta, akwai shu'umar humra, sayan na gari maida kuÉ—i gida, banda karanta yayin gyara Hajia.

Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.

🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*

By
*GARKUWAR FULANI*
22/12/2021, 19:45 - 🥰🥰: “information�.
Riyyam-nsra ya faɗa yana kallon Baba Mauɗo da ya miƙe tsaye, tare da amsa kiran wayar ya liƙa a kunne.
Ba tare daya kalleshi ba, kuma ya fita parlon.

Yana gab da fitan ne kuma Riyyam-nsra ya kuma zura mishi ido jin yana cewa.
“I always pray for wisdom, domin saida hikima zan iya warware zare da abawan da ake sakawa tsawon shekaru dole saida hiki zan warware, in kuma gano bakin zaren, kana inyiwa ahalin GARKUWA daga ruftawa bisa gadar zaren da magauta ke sakawa.�

Sai kuma ya É—anyi shiru yana mai jinjina kai.
A ƙalla tsawon daƙiƙu 4 kana cikin yanayin zak’uwa da kaɗuwa yace.
“What are you saying?�

Sai kuma yayi dan jim yana mai gyaÉ—a kai alamun gamsuwa kana yace.
“You can see me at anytime, saboda mgnar zatafi kyau gani gaka.�

Zare soket ɗin dutsen gugan Riyyam-nsra yayi tare, da juyowa ya fuskanci ƙofar dakin
Kana kuma ya kasa kunnensa da kyau, Yana mai jiyo muryar Baba Maud’on can ƙasa, dan a hankali yake mgnar alamun baya son wani yaji.
Sai dai mamaki mai tarin yawa ne ya rufe Riyyam-nsra, sabida jin yadda Baba Mauɗo yake sarrafa harshensa da ingantaccen turancin da bai taɓa zaton yanajin koda kawo min wuƙa in yanka kabane sabida yanayin shigarsa harcensa suturarsa.

Kana ya gaza gane ina manufar mgnanganun da yake jiyowa, domin daga kan sunan da ya sawa mai kiran ma ya sashi a tunani sannan kuma a take ya tuno hirar da suka tabayi da Ramadan akan Baba MauÉ—on.

Shi kuwa Baba MauÉ—o, sosai yake mangantuwa.
Har kusan rabin awa yana mgn kana daga bisani ya katse kiran.

Yana shigowa dakin ya kalli Riyyam-nsra da ya ƙarasa gugan yanzu ya tattare wurin.
Cikin yanayin tsare fuska kada yaron yayi mishi wata tambayar, dan ya sanshi surataccen yarone na ƙarshe fuska a ɗan tsare yace.

“Sannu ko Riyyam-nsra Allah yayi maka al'barka.�

Juyawa Riyyam nsra din yayi ya É—an kalleshi kana yace.
“Amin Baba Mauɗo.�

Ya ida mgnar yana miƙewa da kayan a hannunsa, cikin ɗan madaidacin wordrobe ya shirya mishi su kana ya juyo yana mai cewa.
“Bari inje inyi wonka.�

“Toh sai ka fito ngd ko�
Cewar Baba Maud’o.

Shikuwa Riyyam kai ya gyaÉ—a kana ya juya ya fita.

Washe gari da dare suna kwance bisa gado shida Ramadan.
Juyowa yayi ya fuskanci Ramadan da kyau.
Tsaki ya É—an ja ganin har yanzu Ramadan na ruggume da waya, yayi tsit ya nitsu alamun yana jin abinda Rayhanarsa ke zanta mishi.

Ganin hakane ya miƙe ya fita.
A falon ya zauna kana ya danddanan wayarsa, ya kira Mammy tana É—agawa tace.
“Riyyam lfy kuwa?�

Riyyam-nsra kuwa jin muryarta da alamun bacci takeyi ne, yasa ya ɗan kwaɓe fuska kana a hankali yace.

“Mammy kaina yana kullewafa da lamarin ahlin na.
Akwai fa abinda ke ɓoye fa,
ina son Baba Mauɗo kuma, ina ganin wasu abubuwa daga gareshi, shin baki da wani ƙarin bayani a kan makusantan baya ne!? naji ina mamaki amman fa babu mummunan zatoa kanshi.�

Cikin sauƙe numfashi tace.
“Ka haɗani video call dashi.�
Da sauri yace.
“Toh Mammy zan hadaku in ya yarda.�

Har zata katse kiran kuma yace.
“Ina Zayton?�
“Gata tana bacci�.
Mammy Ta fadi a takaice tare da katse kiran.

Da safe zaune suke a Dinning area,
Jannart na kusa da Mamy suna karyawa.
“Ramadan kayi waya da Rayyern kuwa tunda suka tafi?�.
Mamy ta tambaya.

Tea ya dan kurba kana yace.
“Eh tun ranar da sukaje washe gari, mukayi waya dashi, dazuma kuma muna dawowa masallaci ya kira Abba.�
Kai Mamyn ta gyaÉ—a tare da cewa.
“Eh haka yace min, Amman ni bai kirani ba yayi kyau ai.�

Riyyam-nsra ne ya É—an kalli Jannart da tayi kamar bata wurin.

“My Aunty idan kunyi waya kice masa, Allah yasa mutuwa ta manta dani da Mamy, fiye da yanda ya mance damu, tunda mu bazai kiramuba.�

Dariya sukayi baki É—ayansu hatta Jannart, saida ta dara tare da cewa.
“Uhum kishi ko Riyyam-nsra".
A ranta kuma cewa tayi.
“Waya san dani nima�.
A zahiri kuwa ido ta zuba Riyyam.
Baki ya tura tare da cewa.
“Ba wani kishi fisabilillahi Mamy ya mana adalci kenan, yaufa kwanansa biyu fa ace bai neme mu ba.�

Dariyar tsokana Ramadan yayi tare da cewa.
“Toh ku kirashi mana.�
Ya ida mgnar yana miƙewa tsaye tare da kallon agogon hannunsa.

Ganin lokaci ya tafine yasa ya nufi waje, shi ma Riyyam-nsra da sauri ya miƙe yana cewa.
“Yauwa Hamma Ramadan muje ka sauƙeni, a gidan Malam Mai-nasara mana, munyi da Nasir zamu hadu a can.�

“Toh taho mu tafi.�
Ramadan yace
Daga nan suka fita.
Suna gab da fita agidanne kuma, Ramadan ya ɗan leƙo ta cikin motar ya kalli Ari, tare da cewa.
“Baba Mauɗo fa?�.

Ari yana mai ida buÉ—e musu gate din yace.
“Yau tun sassafe ya fita har yanzu bai dawo ba.�

Da sauri Ramadan yace.
“Ina yaje, meyasa Hadi bai kaishi ba?�

Da sauri Hadi dake gefe yace.
“Wllh nace zan kaishi yace, a'a in bari ba dadewa zaiba, toh kuma gashi har yanzu bai dawoba.�

“Yayi breakfast ne kafin ya fita.�
Ramadan ya kuma tambaya.

“A'a baiyiba".
Ari ya faÉ—a.

Kai Ramadan din ya gyaÉ—a tare dajan motar suka fice daga cikin gidan.
Wayarshi ya miƙa wa Riyyam-nsra tare da cewa.
“Kira min shi.�
Toh yace tare da duba number kana ya kira.
Miƙa masa wayar yayi jin an amsa kiran.
“Assalamu alaimun Barka da safiya Baba Mauɗo.�

“Wa alaikassalam Barka dai Ramadan�.

“Baba ina ka tafine yau shiru ban ganka ba.�

Da sauri Baba Maud’o yace.
“Ah gani nan zuwa nazo nan wurin wani ɗan ƙasarmu ne Niger ne zai je gida Agadaz gobe shine zan aikeshi.�

Yana mai taka motar yace.
“Toh sai ka dawo nima na wuce wurin aiki amman ai da ka gaya min da na kaika.�

“A'a ba komai Allah ya bada sa'a.� Baba Maud’on ya fad’a.

Ramadan kuwa da
“Amin.� Ya amsa kana ya katse kiran.

Shi kuwa Baba MauÉ—o juyowa yayi ya fuskanci mutanen da yake mgnar da Allah ne kadai yasan kan me suke tattaunawa cikin killace kai sukaci gaba da mgn.

A cikin gidan kuwa, tattare wurin Jannart ta fara.
Mamy kuwa miƙewa tayi ta koma side ɗinsu dan sanin Abba na tsumayin ta.

Tana gama kimtsa wurin ta wuce Bedroom É—inta dan, bacci takeji kasan cewar in tana cikin halin larura tana yawan jin kasala da bacci.

Bayan Ramadan ya sauke Riyyam agidan Malam Mai-nasara, bai shigaba ya wuce sabida lokacin ya kure masa.

Zaune suke gaban malam Mai-nasara.
Cikin muryar girma yace.
“Zakariyya ya jikin ya'yan naka?"
Kai Riyyam ya d’aga ya ɗan kallesu tare da cewa.
“Jiki da sauki har yayi tafiya ma, zuwa China.�
Da sauri Uncle Mustapha yace.
“Eh lallai haka akayi ai naje dubasa a asibitinsa, da yake ban san gidan nakuba, nan yake cemin zaiyi tafiya in ya dawo zaizo ya duba ka da jiki Malam.�

“Masha allah. Toh Allah ya dawo dashi lfy.�

Cewar Malam da Amin suka amsa.
Nasir ne ya ɗan miƙe tare da cewa.
“Riyyam mu tafi ko.�

Inna ce ta kalleshi cikin tuhuma tace.
“Ku kam baku da aikin yine kullum sai yawo da latse-latsen waya?�

Da sauri Nasir yace.
“Kinfi kowa sanin karatu nakeyi kuma ina gab da hada degree dina, shi kuma Riyyam-nsra yama gama wannan shekarar, kuma aikine yake nema tukun.�
Ya ida mgnar yana haÉ—e fuska.

Uncle Mustapha kuwa murmushi yayi hakama Malam.

Sukuwa su Riyyam nsra daga nan rijiyar zaki suka nufa gidansu Nasir É—in.

A falo suka samu babban ya'yan Nasir.
Yah Marwan kasan cewarsa filot ne kwana biyu yana gida.

Marwan yana da sauƙin kai sosai haka yasa suke sakewa dashi,
Bayan Riyyam ya gaida Marwan da Ummansu ne, suka roƙeshi mota.
Miƙawa Riyyam car key din yayi tare da cewa.
“Ku kula da kanku, banda tuƙin ganganci.�
Da sauri suka amsa tare da miƙewa.
Kana suka fita suna cewa.
“Umma sai mun dawo.�

Murmushi tayi tare da cewa.
“Allah ya kiyaye.�
Amin sukace kana suka fice.

Dr.Rayyern Mai-nasara kuwa a ƙasar masu ƙananan idanu, komai yana tafiya bisa tsari yadda yakeso.

Yau kwanansu tara a garin, ya sayi dukkan abun da yake buƙata na campany'nsa.

Sai kuma Engineer bello ya kirashi ya shaida masa suna son wannan karfen 3%, ya zama biyu suka samu domin aje sefiya.
So hakane yasa tashi da shirin zuwa sayansa cikin ingantacen kamfanin kayan ƙarafunan.

Tsaye yake cikin shirin fita PA na tsaye agefensa.
Kiran Mamy ne ya shigo wayarsa da sauri PA yace.
“Mamy ce.�
Yayi mgnar yana miƙo masa wayar.
Amsa yayi tare da karawa a kunne
“Barka da safiya Mamy.�
Ya fad’a cikin kulawa.

A dakile tace.
“Barka dai.�
Ba tare da ta bari yayi mgn ba ta daura da cewa.

“Ka kira Jannart kuwa tunda ka tafi?�

Idonshi ya É—an jujjuya alamun nazari kana a hankali yace.
“Mamy waye kuma hakan?�

Fuska ta kuma tsukewa kamar yana gabanta tace.
“Ok bari in kaiwa Abbanku wayar sai ya gaya maka waye ita.�

Da sauri yace.
“Dan Allah Mamy ki saki ranki kimin bayani, wlh ban fahimci mgnar kiba,
niba sai kin haɗani da Abba ba, ɗazu ma munyi mgna dashi.�

Murmushi ta É—anyi a ranta tace.
“Uhum Rayyern halinka sai kai.�
A zahiri kuwa cewa tayi.
“Matarka ce baka saniba yanzu tunda ka tafi sau nawa ka kirata?�

A takaice ba tare da yaja mgnar ba cikin kare kai yace.
“Mamy banda number ta.�
Sai kuma yace.
“Dan Allah Mamy kiyi haƙuri ina zuwa zan kiraki anjima yanzu wani aiki nakeyi.�
Bai jira me zata ceba ya katse kiran wayar, kana ya miƙa wa Usman ita, daga nan suka fito d’aya daga cikin taxi ɗin hotel ɗin, nasu suka shiga kamar koda yaushe.

Kai tsaye Chinese Construction Engineering company suka nufa,
koda suka shiga basu fitoba sai gab da sallan azahar dinsu.

Suna fitowa sukayi salla kana suka shiga taxi É—in da suka zo dashi dan yana jiransu, tunda batu ne dai na kuÉ—i daga nan Rayyern yace ya kaisu halal Restaurant.

Tafiyar mai yar tazara sukayi kana suka tsaya, wani babban wuri inda daga can sama aka rubuta HALAL Restaurant's da manyan baki.
Kai RAYYERN ya É—an juya ya kalli gefen hagunshi kana ya juyo damanshi.
Bottega ya faɗa a hankali kana ya ɗan kaikace ya zaro katinshi, ya miƙawa PA tare da cewa.
“Shiga ka saya mana, ni pizza ma ya isheni,kai kuma ka sai abinda kakeso, ka sayawa wannan ma.�
Ya ida mgnar yana nuna masa Driver'n'sun.

Toh yace, ya amsa kana ya bude ya fita.

Jim kaɗan ya dawo riƙe da ledodi.
Kana ya shiga suka tafi.

Bayan kwana biyar ya gama har had’a komai, ya kimtsa kayansa kana ya kaisu Airport, dan yana son kayan su rigasu tasowa.

Yau ta kama satinsu biyu cur da zuwa.
Yau ne kuma jirgin kayansu ya tashi sai dai ta Lagos zai sauƙa.
Daga can kuma ya wuce Kano.

Kasan cewar yau É—in Lahadi ne, shine a.lissafi kuma sunyi kwana goma sha huÉ—u.

Tunda safe yayi musu order’n abinci ta online a Frongji Restaurant, kasan cewar komai nasu da tsari, yasa Delivery available ne ko yaushe.
Kuma free delivery ne, cikin abinda baifi 40 minutes ba sai gashi sun kawo musu har ƙofar dakinsu.

Jin ana buga ƙofar ne yasa.
Ya ɗanyi miƙa daga kwancen da yake, ido ya ɗan rumtse sabida kartawar da yakeji cikinsa nayi masa tun daren jiya.
A hankali ya yunƙura ya taso jin anci gaba da bugawar, ya sani bazai iya cin komai ba, sai dai yayi musu order ne sabida PA.

A hankali ya miƙe tsaye sai dai ya kasa ida miƙewa zat, sabida yadda yaji cikinsa na tsananta ciwon in ya gwada tsayuwar, hannunshi yasa ya dafe cikin, kana ya fara taku a hankali.

PA kuwa dake falon kasan cewar ya fara yin bacci ne, yasa toh sai yanzu yaji bugun da sauri.
Ya miƙe tare da nufar ƙofar yana buɗe wa.
Ma'akkacin Halal Frongji restaurant, din ya miƙa masa ledodin hannunsa kana ya juya ya fita.
Sabida dama yayi musu transfer'n kuÉ—in su.

Yana juyowa ne kuma ya hango Rayyern É—in yana fitowa daga cikin Bedroom din.

Ido ya zuba mishi ganin a É—an sunkuye yake tafiya, kana yana dafe da cikinsa da hannun damanshi, da sauri ya nufo gareshi, cikin kulawa da fargaba yace.
“Sir lfy kuwa?"
Cikin rumtse idanunshi ya zauna bisa kujerar dake gefenshi.
Ba tare daya buÉ—e idonba murya a hankali yace.
“Usman ƙara gudun AC'nnan�.
Da sauri Usman ya juya, ya ƙara gudun ACn kana ya dawo inda yake.

Cikin kulawa yace.
“Sir cikin ne?�
Lip ɗinsa na ƙasa ya taune,
tare da ƙara rumtse idanunshi kana a hankali ya miƙe kan kujerar,
baya son yin mgn sabida ko numfashin ya fesar sai yaji wani irin masifeffen ciwon cikin ya karu.
Ido P.A ya zuba mishi ganin lokaci É—aya wata iriyar fitinenneyar zufa ta keto mishi tako wanne hudan gashin jikinsa.
Duk da sanyin garin da kuma na'urar take busawa.

Gaba É—aya hankalin Usman ya tashi sunkuyowa yayi kansa cikin tsananin tsoron kada dai ciwon cikin nasa ne zai tashi yace.
“Hamma Rayyern ko zamu tafi asibiti ne?�.
Cikin sanyi murya can ƙasa yace.
“P.A kaci abinci�.
Ya ƙare mgnar da ɗan ƙarfi alamun baya son mgnar.
Shi kuwa P.A a hankali ya É—an ja da baya cikin taraddadi yace.
“Toh tashi muci.�

Da sauri ya buÉ—e idanunsa da tuni sun gama rinewa sunyi jazir sabida ciwo.
A faÉ—ace yace.
“Dan Allah ka zauna kaci abinci.�

Jin hakane yasa P.A aje ledodin kana shima ya zame ya zauna a wurin.

Shi kuwa Rayyern juyawa yayi ya kwanta a kife.
Tare dasa hannunsa duka biyu ya dafe cikinsa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil, la'ila ha illa'anta subahanaka innikuntu minazzalumin�.
WaÉ—annan sune yaketa maimaitawa a hankali, yadda P.A ma bayaji kana ya matse cikin yayi shiru.

Hakan ne yasa hankalin P.A ya É—an kwanta,
har ya samu yaja abincin ya fara ci.
Yanaci yana juyowa yana É—an kallonsa.
Haka dai har ya gama ci.
Kana ya tattare wurin.

Sannan ya wuce É—akin kwanansa ya É—auko wayarsa, kana ya fito falon.
Dakin Rayyern É—in ya wuce,
Woyoyinsa ya dauko duka biyu kana yazo ya zauna kusa dashi.

Zuwa lokacin kuma cikin ya É—an lafa,
hakan yasa Ya buÉ—e idonshi ya kalleshi a hankali yace.
“Me zakayi da waya?�
Da sauri ya kalleshi tare da cewa.
“Dama zan kira Ramadan ne ko Dr Sulaiman in gaya musu halin da ake ciki.�
Tsareshi da ido yayi, hakan yasa yayi shiru.
Hannun ya miƙa masa ya amshi woyoyin kana a hankali yace.
“Kada ka faɗa musu domin zaka tada musu hankali, kuma in nayi Sa'a haka zai keyi yana lafawa har ya bari, so kada ka gaya musu�.
Cikin yanayin rashin gamsuwa yace.
“Okay Sir�.
Shi kuwa a hankali ya miƙa ya tsaya tsakiyar tamfatsetsen falon na al'farma.
Kana ya nufi É—akinsa.
Kai tsaye Bathroom ya wuce.
Wonka yayi kana ya fito.

Wasu tattausan riga da wondo yasa Pink panther masu sheƙi.

Kana ya gyara labulayen sannan ya ƙara ac sannan ya kashe wutan ɗakin ya dawo ya kwanta.

A nan gida Nigeria kuwa.

Bayan sallan isha'i Abba ne
Zaune bisa kujera, Ramadan na gabansh, Yayinda Mamy ke gefensu.

Jannart da Riyyam-nsra kuwa suna can main falon suna kallon wani India'n Film a zee world.

A Karo na barka tai Ramadan ya kuma gyara zamanshi,
Abba kuwa ido ya zubawa TV kamar yana gane me sukeyi.
Yayinda Mamy kuwa ta zuba musu ido.
Cikin kwaɓe fuska da shogobe fuska Ramadan yace.
“Uhum Abba dama..�
Sai kuma yayi shiru.
“Dama me?�
Abba ya tambaya ba tare da ya kalleshi ba.

Cikin sanyi yace.
“Eh dama gidansu Rayhana ce, sukace in tura�

A fakaice Abba ya kalleshi tare da cewa.
“Ka tura me?�
Kamar zaiyi kuka yace.
“Wai in tura manya na ayi mgnar aure in da gaske nakeyi, dan su gidansu daga yarinya ta gama Secondary School bazataci gaba ba, sai an aurar da ita taci gaba a gidan mijinta, to gashi ita Rayhana har taci gaba sabida, batun Hamma Rayyern baiyi aureba, shine sukace toh ai yanzu dai yayi auren sai ayi batun namun ko?�

Ya ƙare mgnar yana kallon iyayen nasu.
Mamy kam kai ta kauda tana mamakin zalama, irin ta Ramadan sam baya iya ɓoye maitarsa akan san aure.
“Wannan dai anyi jarabebben yaro�
Ta faÉ—a cikin ranta
Abba kuwa numfashi ya É—an fesar tare da cewa.
“Toh su sukace ko dai kai kace?"
Da sauri yace.
“Su�
Kallonshi yayi tare da cewa.
“Banbancinka da Rayyern kenan Ramadan, kai kakan ɗan taɓa ƙarya shi kuwa duk ɗacin gsky zai faɗeta, yanzu da shine cewa zaiyi shine ya faɗa�
Da sauri yace.
“Toh Abba nine na faɗan.�
Mamy kam dariyar dake cintane ta dan subuce mata.
Ido ya É—an zuba mishi kana yace.
“Wato kai dai ayi maka aure kake so ko?�
Da sauri yayi ƙasa da kansa.

“Toh ba damuwa tashi kaje zamuyi mgn da Baba Mauɗo.�

Wayyo Ramadan kamar ya mutu dan daÉ—i ai da sassarfa ya fito.
A falo ya tsaya kusa da Jannart cikin happy yace.
“My Aunty ki shirya kun kusa kai kayan aure.�
Da sauri Jannnart din tace.
“Kai haba dai iye, lallai kam abin nema ya samu kenan matar ma tsunci ta haifi kogi.�

Riyyam nsra kuwa Jujjuyawa yayi tare da cewa.
“Eh matar falke ta haifi sanda,
kai lallai akwai casu a ƙasar Kano�
Sai kuma suka bishi da ido jin ya kira Rayhana ya fara mgn da ita ya haura sama.
Murmushi Jannart tayi tare da cewa.
“Kai Riyyam wai kai baka gajiya da rawane?�
Dariya mai sauti yayi tare da cewa.
“Nida Hamma Rayyern duka ƙugunmu kamar roba yake Bama gajiya da karairayashi�
Harara ta É—an cilla mishi tare da cewa.
“Ji sharri�.
Da sauri yace.
“Wallahi kuwa my Aunty�.
Cikin hararan wasa tace.
“A'a wlh kada kayi mishi sharri, wannan kuma da son jiki ma abu kaɗan ya kama raki yaushe zai iya jujjuyawa kamar yadda kake�

Dariyar Mamy da suka jine yasa, Jannart miƙewa da sauri ta nufi ɗakinta cike da kunya.
Ita kuwa Mamy tafiya takeyi tare da cewa.
“Gskyarki dai kare mijinki diyata�

Shima Riyyam dariya yayi tare da cewa.
“Aifa kam tana kareshi.�

Nan dai sukaci gaba da hira.

A can China kuwa gaba É—aya wunin ranar a daki Rayyern yayi shi.
Koda ruwa bai sa a bakinsa ba,
sabida matsa mishi da cikinsa yayi duk bayan 10mnt sai ya lafa na tsawon 10mnt É—in kana ya sake tashi.
Salla kwai ke tadashi, shima sai in ya samu ya lafa.

P.A kuwa haka ya wuni zirga-zirga a kansa.

Dare nayi kuwa ciwo yace Assalamu alaikum.
Ya tashi gadan-gadan.

Shi kuwa P.A yayi baccin gajiyan zirga-zirgan, da yayi yau din.

“Ya ilahi ya mujibadda'awati.�

Sune kalaman da bakinshi ke iya furta wa, yayinda gaba É—aya jikinshi ke wani irin masifeffen karkarwa,
zuface take keto mishi tako ina tamkar wanda ake watsawa ruwa.

Juyi yakeyi a kan gadon yana mai yin duk wata addu'ar da tazo bakinsa.

“Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Yayi addu'ar cikin wani irin azabebben numfashin, da yake ja tamkar ransa zai bar gangar jikinsa.
Kar-kar haka jikinsa ke rawa, so yake ya jawo wayarshi ya kira asibiti, amman ina ya kasa hakan sabida ko numfashinsa, in yaja kamar zai suma haka yakeji, cikin ya kulle yayi wani irin tauri da zafi.

A hankali ya mirgino dan matsowa zai jawo wayarsa, cikin akasi ya ture woyoyin duka biyu suka fadi ƙasa daga kan bedside drower.

Dai-dai lokacin kuma yaji cikin nasa yayi wani irin damƙa mai cike da azaba.
Wani irin duhune ya rufewa ganinsa.
A hankali yaji kamar gadon na jujjuyawa dashi...

P.A kuwa yanata baccinsa, sai asuba ya tashi, alwala yayi bayan ya fito yayi sallan asuba.
Sabida ganin kamar ya É—an makara yasa Rayyern yayi ta tadashi kenan bai tashi ba.

Yana idawar ya fito falo.

Shiru ya tsaya tsakiyar falon.
“Bai tashi ba, ko ya fitane, bari in duba dai?�
Yayi mgnar zuciya yana mai nufar dakin.

A hankali ya dan ƙonƙosa kofar.
Shiru ba alamun mgn haka yasa ya kuma bubbugawa yana mai kiransa still shiru.

Dan tura ƙofar yayi tare da sallama a bakinsa.

Cikin yanayin firgici ya zaro ido tare da nufo kan gadon, sabida hango Rayyern É—in da yayi a yashe bisa gadon tamkar matacce.
Cikin kidima ya haura gadon tare da ruggumeshi yana jijjigashi da kiran sunanshi da ɗan ƙarfi.
“Sir! Sir!! Sirrrrrr!!!!".
Ya ida kiran da ƙarfi cikin tsananin tashin hankali, domin gaba d’aya jikinsa ya sake yayi sanyi tamkar wanda ya mutu, sai iya cikinsa ne yake da ɗumi.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil Hamma Rayyern tashi".
Gaba É—aya jikinsa rawa da karkarwar yakeyi.
Cikin tsananin tashin hankali ya debo ruwa ya yayyafa mishi amman ina.
Haka yasa ya buɗe ƙofar ɗakin ya fita da gudu.
Sauka kasa yayi.

Jim kaÉ—an sai gashi ya dawo da ma'aikatan hotel É—in.
Kana da Driver'n' taxi.
ID card din Rayyern ya nuna musu.
Tare da Receipt's din kayayyakin da suka saya da kuma takardun Campany da matsayin nasa companies din da kasan cewarsa likita.
Haka yasa da sauri sukasa hannu suka ciccibeshi suka sauƙo aka sashi a mota, P.A ya shiga tare da jan marfin ya rufe kana Driver'n yaja.

Daga nan kai tsaye
Puhua International Hospital and clinic (PIH) Suka nufa.

A cikin motar kuwa cikin tashin hankali P.A ya kira. Dr Sulaiman yana É—agawa yace.
“Dr Usman P.A ke mgna�.
Cikin kaÉ—uwa Sulaiman yace.
“Yesss na gane meke faruwa ne Usman�.
Murya a karye yayi mishi bayanin abinda ya faru ya É—aura da cewa.
“Yanzu haka yana sume gamu a hanyar zuwa asibiti, yauwa gashi ma mun iso�
Yayi mgnar ganin sun shiga cikin asibitin.

Suna yin parking nurses Suka nufosu.
Da irin wannan gadajen ganin Ambulance ce kuma da tambarin hotel É—in a jiki.
Suna isa driver'n na buÉ—e musu.
Da sauri P.A ya fito yayinda Sulaiman ke ce mishi.
Ina kun isa ka haɗani da Doctor ko nurse, duk wanda ka samu kana kada ka gayawa su Abba sai ya farfaɗo kaji ko Usman�.
Da sauri yace to kana ya fito.

Daurasa sukayi a kan gadon kana suka nufi Emergency room.
Yayinda tuni likitoci suka rufawa Nurses din dake tura gadon baya.

Da sauri P.A ya miƙawa daya daga cikin Nurses din wayarsa.
Ƙarawa a kunne tayi.
Kai take ta jinjinawa jin cikekken bayanin matsalarsa, haka yasa da sauri ta miƙa babban Doctor'nsu wayar.

Sosai Sulaiman yayi mishi duk bayani, wannan yasa suka fara bin matakan bashi taimakon gaggawa.
Bayan ya bawa nurse din wayar ta dawowa P.A da ita.

Wasa-wasa kusan awa uku ba'a fito da shiba,
hankali P.A yayi matuƙar tashi.
Sulaiman kuwa ya kirashi yafi sau goma.
Sosai shima ya karaya jin shiru ba'a fito da shi bane.
Yasa yace.
“P.A kira Ramadan ka gaya masa halin da ake ci, ni gsky abin ya bani tsoro�.

Cikin karaya P.A yace.
“To.� kana ya katse kiran.

Number Ramadan ya kira.
Shi kuwa Ramadan lokacin duk suna falon, sun gama karyawa kenan.
Kasan cewar jiya a asibiti ya kwana shiyasa yau zai wuni a gida duk da Monday ne.

Jin wayarsa na ringing ne ya kalli Jannart, dake kusa da wayar inda ya sakalata a caji.
“Waye ne�. Ya tambaya.

Dan leƙa fuskar wayar tayi tare da cewa.
“P.A ne�
Haka nan sai yaji zuciyarsa ta tsinke.
Mamy ma haka abin yake gareta.
Sai suka zubawa wayar ido gaba dayansu.
Riyyam-nsra ne ya É—an jujjuya ya kallesu.
Yayinda sai kuma yace.
“Hamma Ramadan ka amsa mana�.

“Miƙo min wayar�.
Yace yana kalloshi
Da sauri ya miƙo masa wayar bayan ya amsa kira na biyu.
“Hello P.A ya akayi ne?�
Cewar Ramadan.

P.A kuwa Murya a sanyaye yace.
“Ramadan Hamma Rayyern ba lfy ciwon cikinsa ya tash...�

Da sauri duk suka juyo suna kallon Ramadan din daya miƙe tsaye yana cewa.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun, hasbunallahiwani'imanwakil,
P.A, ina yake? Wanne hali yake ciki? Kuna ina yanzu? Bashi wayar!"

Gaba daya Ramadan din ya gigice.

Jin abinda yake faɗa ne kuma yasa Mamy miƙewa, jiki na rawa take cewa.

“Menene Ramadan meya faru da Rayyern? Ina yake bani wayar�.

Juyawa yayi cikin yanayi tashin hankali jin P.A na cewa.
“Muna asibitine Ramadan, a sume muka kawoshi tun safe, kuma har yanzu bai farfad’oba, nima kaina ban san halin da yake cikiba�

“Yah ilahi ya mujibadda'awati�.
Ramadan ya faÉ—a murya na rawa.
Mamy kuwa da sauri ta nufi side É—insu tana cewa.
“Abban Rayyern, Rayyern! Rayyern!!!�.
Da sauri Abba ya miƙe ya nufo kofar falon su.

Riyyam-nsra kuwa a main falon.
Gaba É—aya jikinshi rawa ya fara.
Yayinda Jannart kuwa take binsu da kallo.
Shi kuwa Ramadan bin bayan Mamy yayi yana cewa.
“Abba Hamma Rayyern ciwon cikinsa ya tashi, tun jiya da dare yana sume har yanzu bai farfadoba, Abba ya zamuyi.�
Da sauri duk suka tsaya cirko-cirko a tsakiyar falon.

“Kira min P.A maza bani wayar�

Cewar Abba haka yasa Ramadan sake kiran P.A.
Bayanin da yayiwa Ramadan din shi yayiwa Abba.

Tashin hankalin da ba'a sa masa rana.
Jannart kuwa shiru tayi tana kallon Riyyam-nsra daya kira Mammy a waya yana gaya mata abinda ke faruwa yadaura da cewa.
“Mammy kiyi masa addu'a'n samun lfy kin san addu'arki gareshi bata da hijabi, Mammy yana cikin tsananin hali wuya bakiga yadda ciwon ke wahal dashi ba kamar zai ɗauke mana ransa�.
Ya ƙare mgnar murya na rawa hawaye na zuba.

Ita kam Jannart abubuwan sun raunata-ta.
Domin ganin hawayen Riyyam.
Dan ita haka Allah yayi idonta muddin taga hawaye idon wani to nata zai zubo, dan irin idon GARKUWA ne fareta.
Haka kuma tana da rauni abu kaÉ—an ke sata hawaye.
Bare kuma wannan al'amarin da tasan yana masifar sasu cikin tsananin tashin hankali.
Sautin muryar Abba tajiyo cikin rauni yana cewa.
“Rukayya ki dena yi mishi kuka, addu'arki yafi buƙata, Ramadan tashi maza dauki E-passport dinmu, Ka fara mana shirin tafiya.�
Ya ƙare mgnar suna fitowa main falon a jere.
Yayinda shima idanunsa sunyi jazir alamun tashin hankali.

Waje ya nufa.

Mamy kuwa zamewa tayi ta zauna bisa kujera hawaye na shatata tace.
“Yah Allah kaji tausayin wannan bawa naka, ka jikanshi ka yaye masa wannan azabar ka bashi lfy.
Ya Allah ka zama gatansa a kasar da ba ta saba bashi da kowa sai kai ya Allah�
Cikin raunin murya da sanyi ido na ciko da hawaye Jannart tace.
“Amin ya Allah, Mamy ki dena kuka kici gaba da yimishi addu'a�.

Riyyam ya kalli Ramadan da ya sauƙo yanzu da E passport a hannunsa.
Da sauri Riyyam yace.
“Hamma Ramadan bazakayi muku booking ta online ba ai yafi sauki.
Ka duba ka gani ina za’afi samun jirgin China da wuri Abuja ko Lagos kaga baka da nitsuwar yin tuƙi�.
Da sauri Jannart tace.
“Eh hakanfa zaifi�.

Hakan kuwa shi yasa Ramadan komawa zaune jiki, a mace ya fara bincike kan sifirin jiragen sama na kasa da kasa.
Cikin sa'a kuwa ya samu akwai jirgin zuwa China ta Abuja nanda kwana biyu.

Haka yasa ya fara hidimar neman visa nan take a wurin yayi komai.
Sabida yanzu duniya ta zama a tafin hannu.

A can harabar gidan kuwa.
Gaba É—aya hankalin Baba MauÉ—o yayi matukar tashi da jin wannan lbrin.
Hadi da Ari ma jikinsu yayi sanyi.

Suna nan Sulaiman ya shigo.
Bayan sun gaisane ya kalli Baba MauÉ—o cikin kulawa yace.
“Ba komai fa, ya farfaɗo P.A ya ganshi ma, sai dai sun hanashi shiga dakin da yake�.
Toh abunka da nesa in kaji baka gamsuwa in ba gani kayi ba.

Koda suka shiga cikin gida.
Nan yayi ta kwantar musu da hankali.
Haka dai suka wuni a ranar da zulumi bini-bini su kira P.A.

Washe gari ma hakan suka wuni.
Toh da Yamma Ramadan ya tafi Abuja.
Dan Sulaiman da P.A sunce ba sai Abban yaje ba.
Tafiyar Ramadan yasan gidan ya ƙara zama shiru kamar ba mutane.

P.A kuwa shima har yau bai ganshi ba.
Sai da dare ne da ya sake zuwa asibitin sai gobe da safe yazo.
sunce ya koma masauƙinsu ne a cewarsu ma'aikatansu ke kula da maralafiya.

Ranar da Ramadan yazo Abuja da dare washe gari da safe.
Jirginsu ya daga zuwa kasar China.

Gab da magriba jirginsu Ramadan ya sauƙa.
Daga Airport É—in kai tsaye Puhua International Hospital din yace mai taxi ya wuce dashi.
Cikin sa'a kuwa suna zuwa bakin gate din P.A na fitowa.
Nan ya sallami mai taxi shida PA Suka nufi ciki.
“Kayi sauri P.A ta ina zamu bi? Ya jikin nasa? Yana mgn?�.
Ramadan ya jerowa Usman tambayoyin.
Cikin sanyi Usman yace.
“Ko munje bazasu barka ka ganshi ba, amman sunce gobe da safe zamu ganshi. Sai dai in nuna maka dakin da yake ciki kawai."
Hakan kuwa akayi duk da kasancewar Ramadan likita basu barshi ya shigaba sabida wai ƙare a gidansa zakine.

Dole suka koma masauƙinsu.
Usman din yayi musu order'n abinci.
Bayan sunyi wonka sunyi sallane.
Suna cin abinci Ramadan ya kira Abba wanda lokacin suna tare da Baba Mauɗo nan ya ɗan ƙarfafa musu guiwa.
Kana ya kira Riyyam yace ya bawa Mamy waya.
Toh sun danji sanyi dai.

Washegari

Ƙarfe takwas dai-dai ta samesu tsaye a bakin dakin da Rayyern ɗin ke ciki.
Wanda yau kwana shi uju kenan a na hudu.
Bayan Doctor ya fitone.
Ya kalli Ramadan tare da cewa ya biyosa Office nasa.
Haka kuwa akayi.

P.A kuma yana tsaye a wurin
Tsawon kusan ,35mnt kafin Ramadan ya dawo jiki a mace.
A hankali yace.
“P.A mu shiga�.
Da sauri P.A ya mara masa baya.

Suna shiga suka hangoshi can kwance kan gado.
Lumshe ido Ramadan yayi sai ga wasu hawaye masu zafi sun zubo mishi.
Sabida tausayin Hamman nashi.
Shi kuwa Rayyern cikin yanayin mamaki yake kallon Ramadan tare da buÉ—e baki a hankali yace.
“Ramadan yaushe kazo�.
Hawaye na zuba yace.
“Jiya nazo Hamma Rayyern�.
Cikin tausayawa P.A yace.
“Sir ya jikin?�.

A hankali yace.
“Alhamdulillah�.
Ina hawaye Ramadan sun gaza tsayuwa, sabida ganin wani irin masifeffen rama da Hamman nashi yayi.
Cikin nan a É—akale tamkar babu hanji a ciki.
Ya rame yayi fiyau.
Yayi wani irin sanyi ko mgn a hankali yakeyi.
“Abba ya gaisheka da jiki Baba Mauɗo yace inyi maka sannu in shafa masa kanka, Riyyam yanata kuka.
Mamy ma tanata kuka.
Aunty Jannart tace in gaisheka da jikin�.
Idonshi ya lumshe tare da cewa.
“Ayyah na samu sauƙi ai�.
A raunace.
P.A yace.
“Sir a hakan ne ka samu sauƙin?�.
Kai ya É—an jinjina dan baida kuzarin komai.

Cikin sanyi yace.
“Visa'n mu ya kusa karewa ko.
Dama kwana ashirin da uku ne ko P.A?�.
Da sauri ya gyaÉ—a kai.
Cikin sanyi yace.
“Kaifa Ramadan?�.
Yana gyara masa pillow yace.
“Ƙafarka kafata ai�.

Kwanansu biyu a asibitin bayan zuwan Ramadan aka sallamesu.
Nan suka fara shirin dawowa.
Sun dai kashe kudi kam dan yanke kwanakin Ramadan.

Cikin sa'a kuwa suka samu jirgin Lagos.

Haka yasa suna sauƙa suka haɗo da kayansu da ya kai kwana bakwai da isowa.

Ƙarfe takwas na dare suka sauka a Lagos.

Sha É—aya da rabi kuma jirgi ya debesu zuwa kanon dabo jallabar hausa.

A gida kuwa Abba da Baba MauÉ—o.
Hadi da Riyyam mota É—aya ne suka tafi Airport daukosu.

Jannart kuwa tun bayan sallan isha'i da ta fito.
Bata samu kowa a falonba ta koma dakinta

Ta kwanta tana Game har bacci ya kwasheta.

Sha biyu da rabi dai-dai suka iso gida.
Da sauri Ari ya buÉ—e musu gate.
Cikin kulawa Baba MauÉ—o ya fito tare da matsawa gefe.
Kasan cewar dama a tsakiya sukasa Rayyern É—in shida Abba.
Tallabeshi yayi sabida ganin kamar jiri na dibansa.
Cikin sanyi yace.
“Baba Maud’o zan iya dai�.

Da kulawa yace.
“A'a Rayyanu kaga yadda ka dawo kuwa cikin sati ɗaya�.
Isowar Ramadan ne yasa ya É—an matsa yace.
“Ramadan tallabeshi.�
Cikin ƙarfin hali yace.
“Ka barni zan iya�.

Dole tasa aka barshi.
P.A da Riyyam kuma dama sunyi gaba da kaya tuni sun haura sama.
Ganinsu ne yasa Mamy fitowa da sauri.

Dai-dai lokacin su kuma suka iso kan barandar.
A hankali ya zauna bisa kujera tare da sauke nannauyan numfashi dan gajiya.
Cikin tsananin so Mamy ta matsoshi tare da jera mishi sannu.

“Sannu Babana. Ramadan meyasa bazaka taimaka mishi ba, kasan yadda allurar nan take mishi fa�.

A hankali ya fesar da numfashi tare da miƙewa tsaye yace.
“Mamy ba'amin allurar ba�.
Ya ƙare mgnar yana shigewa ciki.
Abba da Ramadan na biye dashi a baya.
Baba MauÉ—o Kuma dasu Hadi sukayi baya.

A hankali ya fara take matakalan yana layi.
Ganin hakane yasa Abba rikoshi ya tallabeshi suka fara takawa
Fuska ya ɗan kwaɓe yana cewa.
“Zan iyafa�.

“Kaci gidanku Rayyern, bana son wannan taurin kan da ƙarfin halin dolen nan�.
Abba ya faÉ—a suna takawa.
Dole yayi shiru.

Suna shiga kai tsaye É—akinsa suka shiga.
“Zan kwanta bacci nakeji�.
Ya faÉ—a yana kwanciya.

“Kada kayi bacci bari in kawo ma abinci�.
Cewar Mamy kai ya jujjuya tare da lumshe ido.

“Ku barshi sabida akwai mgnin dake ɗan sa bacci a magungunanshi.�
Cewar Ramadan.
Haka yasa suka fita suka bar Ramadan.
Abba da Mamy suka sauƙo.
P.A da Riyyam suka kwana dakin Ramadan.

Abba kuwa da Mamy a falonsu suka zauna suka fara tattauna wasu, mahimman abubuwan wanda dagasu sai mahalicci su suka san menene.

Washegari da safe.
Misalin ƙarfe shida Jannart ta fito.
Cikin wani tattausan material mai masifar kyau.
ÆŠinkin doguwar riga yabi jikinta ya lafe.
Kasan cewarsa Royal blue, pink, yellow, and green sai ya zama kamar zanen dawisu kana yasa farar fatarta kara fitowa ras hips É—inta sukayi cib-cib da rigar gwanin kyau.
Ta tubke jelan gashinta daya konta kan wuyanta.
ÆŠan sisirin mayafi pink color ta yafa.
Sai ƙamshi take bazawa gwanin daɗi.

A hankali ta turo ƙofar falon.
Da sauri ta rusuna ganin Abba na saukowa daga sama.
“Abba ina kwana?�.
Cikin kulawa yace.
“Lfya lau Alhamdulillah ya gajiyan aiyuka".

Alhamdulillah tace kanta a sunkuye.
Kofar fita ya nufa.
Ita kuwa da sauri ta nufi.
Kitchine jin gidan ya kacame da kanshi Mamy nata hidima.

“Barka da safiya Mamy�.
Ta faÉ—a tana shigowa Kitchen din.

Da sauri Mamy ta juyo tare da cewa.
“Barka dai Jannart kin fito�.

Matsowa tayi tana cewa.
“Eh Mamy kawo in karɓa miki aikin�.
Ta ida mgnar tana son amsar ludayen.
Da sauri Mamy tace.
“A'a bari ma ai na gama ma�.

Toh tace tana É—an matsawa tare da cewa.
“Mamy ya lbrin mai jiki?�.
Da sauri ta juyo tare da cewa.
“A'a na mancema ai sun iso jiya da dare.
Maza haura yana ɗakinsa jeki dubashi da jikin ko�.
Cikin yin ƙasa da kai tace.
“Ayyah ashe sun dawo�.

”Eh wlh kusan ƙarfe ɗaya suka shigo shiyasa ban gaya miki ba.�
Cewar Mamy.
Ita kuwa Jannart
“Ayyah�. Tace tare da tsayuwa.
Ramadan ne ya leƙo Kitchen din tare da cewa.
“Mamy Hamma Rayyern yace tea yake so. Akai mishi tun ɗazu ya gayawa Abba�.

Da sauri Mamyn tace.
“Toh ban saniba, Abbanku woje yayi da sauri�.

“Toh kawo in kai mishi, inaga ya mantane�.

“A'a bari ga matarsa zata kai mishi�
Mamy ta faÉ—a tana hada kayan tea É—in akan tray'n.

Shi kuwa Ramadan juyawa yayi tare da cewa.
“Toh bari inje wurin Abba da P.A zamu wuce kai kayan campany�.

Sai kun dawo tayi musu tana mai mikowa Jannart É—an madaidicin tray'n datasa komai a kai.

Amsar tray'n tayi cikin sanyi tace.
“Mamy ban san dakin shiba ai�.
Ta faÉ—a tanajin zuciyarta na harbawa.

Ita kuwa Mamy ba tare da ta kalleta ba tace.
“Kina haurawa sama na gefen dama shine ɗakinsa na hagu na Ramadan.
Kiyi maza ki kai mishi�.
Ta ƙare mgnar tana kallonta hakan ne yasa.
Ta juya a hankali ta fita Kitchen.

Tsakiyar falon ta fito tare da nufan steps din a hankali take daga kafafunta.
Haka nan taji zuciyarta na harbawa da sauri-sauri, lokacin da ta daura ƙafarta kan step din forko.
Tunda tazo gidan yanzu kusan kimanin watanni biyu cur harda kwanaki, ƙafarta bai taɓa taka wurinba.
Bare ta haura saman, da sauri ta juyo jin muryar Mamy na cewa.

“A'a Jannart me kike jira, kiyi maza ki kaimashi.�
Da sauri tace.
“Toh�.
Kana ta fara tattakawan a hankali.

Shi kuwa Rayyern fitowar shi daga wonka kenan.
Dan Abba ya hada masa ruwan wonka kenan ya fita.

A hankali ya matso gaban gadon shi.
Kayan da yasa Ramadan ya ciro mishi ya kalla.
Wani singlet ne mai faɗin hannu fara ƙal mai masifar taushi.
Daga gefen damanta kan kirjin da al'jihun.
Sai kuma wondonshi wanda bazai wuce masa iya guiwa ba.
A hankali ya É—an sunkuyo ya zauna sabida yar tafiyar da yayin yaji ya gaji.

A hankali ya ware wondon tare dasa kafafunsa yana daga zaunen.

Cikin tattaro sauran ƙarfinshi ya yunƙura ya taso.
Tare dasa hannunsa daya ya ware towel din dake daure, a kugunsa ya fadi ƙasa, hakan yasa yatsaya ba komai a jikinsa.
Sai gajeren wondon da yake dai-dai kan guiwarsa, bai jawoshi zuwa sama ya suturce shi ba.
Dai-dai lokacin kuma Jannart ta turo Æ™...!

*GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA

By
*GARKUWAR FULANI*
22/12/2021, 19:45 - 🥰🥰: *GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

GARKUWAR MA'AURATA

K’ofar falon ta tura ahankali tare dasa k’afarta na dama ta d’an shigo cikin falon, bakinta d’auke da siririyar sallama, wanda ba kowane zai iya jin amo da kuma sautin muryar natan ba.

Ahankali tad’an sake kofar, tare da k’arasa shigowa, wanda hakan ya bawa kofar daman rufewa.

Shiru ta d’anyi na y’an wasu sakanni, kafun daga bisani ta soma yawo da Idanunta acikin, had’add’en falon wanda kaitsaye za’a iya k’iransa da suna Aljannar duniya, badon komai ba kuwa face saboda tsananin had’uwarsa, duk da cewar babu wani tarkace aciki, amma falone daya amsa sunansa falo.

Ahankali ta d’an lumshe Idanunta, tare da shak’an daddad’an k’amshin dake tashi acikin falon, wanda ya had’u da sanyin A/C da kuma, fitinannen turaren air conditioner mai k’amshin strawberry.

Daddad’an k’amshin da d’adinsa kan iya saka mutum jin bacci ta zuk’a, tare kuma da d’an bud’e lumsassun Idanunta, b’angaren dama da kuma hagunta ta kalla, inda taga d’akuna guda biyu, sai kuma kitchine dake can gefe guda, gefe dashi kuwa wani had’adden dining table ne, mai kyaun gaske.

Gefen damanta ta kuma kallo, kasancewar ance mata bedroom din nasa, ab’angaren dama yake.

Ahankali kuma Cikin nutsuwa ta nufi, kekkyawan kofar da take da tabbacin cewa, nanne d’akinsa, hannunta rike da tray.
Kowani taku zatayi kuwa sai tafukan k’afafunta sun amsa, da wani irin sanyi da kuma taushin dake tashi ak’asan tiles din dake malale acikin falon.

Acan b’angaren Rayyern kuwa, akasalance yaja wandon nasa sama, cikin yanayin gajiya da kuma kosawa da tsayuwan da yayi.

Idanunsa yadan lumshe Ahankali adai-dai sanda ya kawo wandon saman kugunsa, duk da cewar bai gama jan wandon ya haura masa can sama ba, hakan kuwa shiyasa duk shatin saman mararsa ya bayyana.

Akasalance ya jawo short sleeve ya saka ajikinsa, saboda yanayin da yake ciki ne kuma, yasa ko gama had’e bottum din rigar baiyi ba, hakan kuwa shiya saka kwantattun gargasan dake kwance akan kirjinsa suka Dan bayyana.
Haka ma gargasan k’afarsa saboda wandon daya saka din, ya tsaya iyaka guiwarsa ne, wannan shi yasa duk wani lallausan bakin gashin dake kwance a jikinsa suka bayyana.

Duk da cewar akwai rama ajikinsa, kuwa amma hakan baihana kyawunsa bayyana ba, musamman ayanzu daya saka kayan da suka k’ara fito masa da kyaun surarsa.

Ahankali ya sauke wani irin numfashi mai dauke da ‘alamar gajiya, cikin kosawa da tsayuwar da yakeyi din kuma, ya d’an juya tare da jawo wata had’add’iyar kujera dake gefen gadonsa.

Zama yayi akan kujera tare da fesar da numfashi mai dumi, Jin kansa yake ya gaji sosai, wanda kuma yasan hakan bai rasa na saba, da rashin karfin jiki da bashi dashi sosai.

Idanunsa ya lumshe tare da maida kansa ya daura ajikin kujeran, akai akai haka yake fitar da numfashi.

A dai-dai lokacin kuwa Jannart ta k’ara masowa jikin k’ofar d’akinnasa, tsayawa tayi ajikin k’ofar tare dayin shiru, zuciyarta cike da tunanin yanda zatayi ta shiga cikin dakin.

Sake gyara rikon tray din dake hannunta tayi, kana Ahankali ta d’an matso, hannunta na dama tasa ajikin kofar tare da soma knocking, cikin kuma tattausan muryarta tace.

“Assalamu Alaikum!�

Shiru taji babu alaman za’a amsa mata, gashi kuma ta kasa ci gaba da knocking din.

Daga can b’angaren kuwa sam Rayyern baima jita ba, saboda tunaninsa daya tafi izuwa wani waje na daban.

Itakuwa Jannart sanin da tayi cewar tana da raunin ji, ba lallaine ma taji koda ya amsa mata ba, hakan yasa Ahankali ta d’an murd’a handle din kofar.

Cikin sa’a kuwa kofar ta bud’e, wanda hakan ya bata daman d’an tura kanta ciki ta shigo ciki bakinta dauke da sallama.

Rayyern kuwa Jin alamun bude kofar ne yasa shi dan bud’e idanunsa Ahankali, inda ya sauke ganinsa akanta, ganin ita dinne kuma yasa shi maida idanun nasa ya lumshe, ba tare da ya bari sunyi ido hudu ba.

Jannart kuwa sauk’e idanunta da tayi akansa ne yasa ta d’an tsaya, tare da sauk’e ganinta akan kyakkyawar fuskarsa, Ahankali ta dan soma yawo da idanun nata akansa, har dai ta sauke ganinta akan lallausan sajen dake kwance agefen fuskar tasa, sajen nasa da kuma wuyansa ta d’an k’urawa ido, saboda yanda taga tsaruwa da kuma k’awatuwarsa, ga kuma wani irin haske da taga cikin jikin nasa ke dashi.

Sak ayanayin nasa da mai bacci yayi mata kama, domin hakanne ma yasa ta d’an tsaya kallonsa na d’an wasu sakanni.

Ahankali kuwa ta kauda kanta tare da janye Idanunta daga garesa.

Cikin sanyi da nutsuwa ta k’arasa shigowa cikin d’akin, tare kuma da nufo inda yake.

Anutse ta d’an rusuna adai-dai gabansa, inda wani glass stull ke aje anan gefensa, sunkuyawa tayi tare da soma kokarin ajiye tray din dake hannunta.

Batare kuma da takai ga ajiye tray dinba, ta d’an d’ago da kanta ta kuma Kallon fuskarsa.

“Ina kwana.�
Ta fad’a asanyaye, duk da kuwa bata da yakinin cewar zai amsa mata.

Hakan kuwa akayi domin shiru yayi bai amsa mata ba, saidai taga kwayan idanunsa sun d’an motsa, wanda kuma hakan shiya tabbatar mata da cewar ba bacci yake yi ba.

D’agowa tayi daga ajiye tray din, still kuma cikin muryarta dake bayyana sautin nutsuwa tace.

“Sannu Ya jiki?�

Akaro na biyu kenan daya d’an motsa, tare kuma da jan wani dogon numfashi, kana ya bud’e maraitattun idanunsa, masu cike da kasala, gajiya, had’i kuma da bayyana yanayi irin na marassa lafiya.
Inda ya saukesu acikin nata idanun.

Da sauri tayi kasa da kanta, saboda har abada bazata tab’a iya jurewa Kallon cikin idanunsa, a irin wannan yanayin ba.

Shikuwa Rayyern Jajayen labbansa masu sheki ya motsa.

“Da sauki.�
Ya amsa mata cikin muryarsa da bata fita sosai.
Kasan cewar ta kasa kunne kuma hankalinta na gareshi yasa taji,
Jin yanda sautin muryar tasa ke fita ne kuma yasa, Jannart d’ago Kanta ta kalleshi.

Gaba d’aya ya rame sosai, labbansa sun sakeyin ja, Yayinda idanunsa duk suka bayyana ramar fuskarsa, tabbas kallo daya zakayi masa kafahimci cewa ya matukar jin jiki sosai, saboda yanda komai nasa ya sanja, amai makon yayi muni kuma sai ramar ta k’ara masa kyau.

Wato atakaice dai Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara irin mutanen nanne, da a kowani irin yanayi suka samu kansu suna kyau, badon komai ba kuwa, sai dan kyau din a jininsu yake.

Idanunta ta d’an kawar daga kallonsa.

Akaron farko kuma kenan da ta tausasa muryarta sosai, cikin nuna kulawa tace.

“Allah Ya baka lafiya.�

“Ameen Idan da gaske kike.�
Ya fad’a akasalance, cikin kuma kauda Kai daga Kallon ta.

Jin abunda ya fad’a d’inne kuma yasa Jannart din, girgiza kanta batare da tace masa k’alaba ta maida hankalinta wajen had’a masa tea.
Acikin zuciyarta kuwa cewa tayi.

“Mai Hali dai baya sanja halinsa, ko bashi da lafiya sai yayi.�

Ta k’are zancen zucin nata, tana me sauke Idanunta akan fararen legs d’insa, wanda gargasa suka yi musu k’awanya, ba kuma irin normal gargasa da kowa ya sani ba, gargasane dogaye kuma masu taushin gaske, wanda suka kwanta lub-lub ajikin fatar nasa.

Kauda kanta daga Kallon k’afan nasa tayi, adai-dai lokacin kuma ta kammala juya masa tea d’in.

Tea spoon ta sanya acikin cup din tare kuma da d’ago kanta ta kalleshi.

“Ga Tea din.� Ta fad’a tana me mik’a masa cup din.

Ahankali ya d’an jujjuya mata kai, tare da karyar da wuyansa gefe.
Alamun bazai shaba.

Idanunta tad’an zuba masa, saboda wani irin tausayinsa da taji, sanin kuma halin marassa lafiya da kin son cin abinci ne yasa, cikin tausasawa da kuma kwantar da murya tace.

“Bazaka sha ba?�

Kansa ya kuma jinjina mata, alaman “Eh.�

“To Meyasa?� Ta tambayeshi da wata irin murya, kana kuma cikin yanayin da ita kanta batasan tayi ba.

Fararen hakwaransa yasa ya dan danne lipsl d’insa, cikin wata iriyar fitinenneyar murya yace.

“Banaso!! Bsnaso! banassso!!!�.
Idanu ta zuba mishi tana mai jin yadda tsikar jikinta ke zubawa sabida yadda yayi mata mgnar like É—an yaye mai shogoba.

Kai ta É—an kwantar kana cikin murya da bata san ta yaya ya ziyarci harcentaba tace.
“Bakason me?�.
Kwaɓe fuskarsa tayi tamkar zaiyi kuka yace.
“Banason tea me madara empty zaki baneeee.�
Yayi maganar cikin sake yin kasa da murya, saboda gaba daya baya wani jin dadin jikinsa, ga kuma rashin karfi dake damunsa, wanda hakan yasa maganan ma wahala yake basa.

Jannart kuwa jin abunda ya fad’ane yasa, ta d’an kwantar da kanta gefe, tare kuma da Kallon kayan tea din da ta shigo dashi.

Ajiyar zuciya ta d’an sauk’e, kana cikin sanyi tace.

“To bari naje na d’auko wani cup, saina had’a maka empty din.�

Ta k’are maganan tana me mik’ewa tsaye,batare kuma da ta jira wani abuba kaitsaye ta fice daga Cikin d’akin.

Direct falon nasa ta dawo, harta kawo bakin kofar fita daga falonne kuma sai ta hango, kofar dake gefe da dining area d’insa, da dukkan alama kuma nanne kofar kitchine din dake Cikin falon nasa.

Ahankali ta k’arasa jikin kofar tare da turawa ta kutsa kanta ciki.

Idanunta tad’an ware saboda ganin yanda kitchine din nasan ya tsaru, da komai na zamani, domin wani irin kitchine carbinet akayi na musamman acikinsa, ga kuma plates da cups hadi da sauran kayan aiki masu kyau kana Kitchen din nada girma ga kuma kofar store ta ciki.

Jinjina kanta tayi saboda yanda ta yaba da kyawun kitchine din.

Wani cup ta d’auka tare da k’arasawa gaban sink ta wankesa.

Juyowa tayi Anutse ta dawo cikin d’akin.

Yana nan zaune a inda ta barsa dan ko motsawa baiyi ba, saidai idanunsa daya sake lumshewa.

A ranta tace.
“Ga kafiya faɗa ga kuma raki da sakalci�.

D’an durk’usawa tayi, agaban stull din tare da d’aukan lipton ta saka acikin cup din, sai kuma k’wayan shugar guda hud’u da ta d’auka acikin k’wali, bayan ta saka shugar’n ne kuma ta saka ganyen lemongrass leaves wanda already dama tazo dashi akan tray din, murfin flask ta bud’e tare da zuba ruwan zafi acikin cup din, kana tasa cokali tadan jujjuya.

Ganin sugar din ya narke ne kuma yasa ta, d’ago cup din tare da mik’a masa cikin kulawa tace.

“Gashi.�

“Ki ajiye.�
Yafad’a agajarce tare kuma da gyara zamansa, wanda kuma daga yanayin maganarsa kad’ai zaka fahimci cewar bayajin dadin komai.

Ajiye cup din tayi agefensa kamar yanda ya fad’a. Cikin nutsuwa kuma ta mik’e tsaye, tare da d’aukan tray din.

Ahankali batare kuma da ta sake ce masa komai ba, ta juya ta fice daga cikin dakin, tare da mayar masa da kofar ta rufe.

Kaitsaye k’asa ta nufa.

Shikuwa Rayyern jin alamun fitanta ne yasa shi sake lumshe idanunsa.

Ahankali ta gama sauk’owa daga kan steps din.
Ganin babu kowa acikin main falon ne kuma yasa kaitsaye ta wuce kitchine.
Dan aciki ne takejin motsin Mamy.

Tana shiga kuwa ta samu Mamyn nata aikace aikace.

“Sannu da aiki Mamy.�
Ta fad’a tana me ajiye tray din dake hannunta.

Mamy kuwa jin muryar Jannart abayanta ne yasakata sakin murmushi, cike kuma dajin dadin d’an jimawan da taga Jannart din tayi a sashin Rayyern din tace.

“Yauwa sannu dai Jannart.�

K’asa Jannart din ta d’anyi da kanta, kana anutse tazo kusa da Mamyn tare da k’arb’an aikin da Mamyn keyi ta soma Taya ta.

Hakan yasa cikin yan mintuna suka kammala had’a komai na breakfast.
Bayan sun zuba komai acikin food flask ne kuma, Jannart takai kulolin kan dining Table.

Mamy kuwa na Abba ta d’auka takai masa zuwa part d’insa.

Dai-dai lokacinne kuma Ramadan da Riyyam nsra suka shigo.

Jannart dince ta bawa Riyyam nsra food flask din su Baba Maud’o ya Kai musu.

Koda ya dawo kuwa anan falon suka zauna su dukansu, atare sukayi breakfast, inda suna cin abincin Riyyam-nsra nata zuba musu surutu, wanda kuma bashi da wani labari saina y’an tiktok.

Suna ahaka ne kuma Dr. Sulaiman da kuma Baba Maud’o suka shigo cikin falon.

Fuska d’auke da fara’a suka gaisa, dasu Mamy dai-dai lokacin kuwa Abba ma ya fito daga nan part d’insa.

Bayan Abban sun gaisa da Dr. Sulaiman ne kuma yayi musu jagora zuwa sama.

Ahankali Abba ya tura kofar dakin Rayyern din ya shiga bakinsa dauke da sallama, Yayinda su Baba Maud’o ke biye dashi abaya.

Rayyern dake dan kishingid’e kuwa jin muryar Abban nasa ne, yasa shi dan yunkurawa ya tashi zaune.

Akusa dashi Abba da Baba Maud’o suka zauna, cikin kulawa Baba Maud’o yace.

“Rayyern ya jikin naka?�

Murmushin karfin hali ya d’anyi, tare da gyara zamansa, kana cikin tausasawa yace.

“Alhamdulillah jiki da sauki Baba Maud’o.�

Kai Abba da Baba Maud’o suka jinjina, cikin kuma danjin dadi suka had’a baki wajen cewa.
“Allah ya baka lafiya.�

Da “Ameen.� ya amsa.

Inda Dr. Sulaiman kuwa ya zauna akan bedside drawer, cikin nuna kulawa ga abokin nasa yace.

“Sannu Dr Rayyern ya jikin naka? da Fatan ka d’anji k’arfin jiki.�

Idanunsa ya d’an lumshe kana Ahankali yace.

“Alhamdulillah, nasan komai zai dawo dai-dai soon.�

“Insha Allah, amma fa kasan dole saika dage, musamman wajen cin abinci, domin yanzu ma haka akwai magungunan dana kawo ma, amma dole sai kaci abinci kafun kasha su.�

Cewar Dr. Sulaiman yana me fito da wasu magunguna daga aljihunsa.

Rayyern kuwa Ganin magungunan ne yasa shi d’an yamutse fuska, tare da komar da kansa ya kwanta.

Sanin da sukayi cewa Koda lafiyarsa, bayason yawan surutu, bare kuma yanzu da bashi da cikakken lafiya ne, yasa su mik’ewa tare dayi masa Allah ya sauwake, kana duk suka fice daga cikin dakin, Dan ayanayin da suka gansa kamar ma bacci yakeson yi.

Atare suka sauk’o k’asa dukansu.

Anan cikin falon suka zauna, inda Dr Sulaiman ya d’ago kansa ya kalli Mamy.

Cikin girmamawa yace.

“Mamy akwai wasu magunguna dana kawowa Rayyern, To amma kuma dole akwai buk’atar sai yaci abinci kafun yasha su, saidai kuma na lura kwata kwata Rayyern bayason cin abinci.�

Ajiyar zuciya Mamy ta sauk’e, cikin kuma yanayin sanyi tace.

“To ya zamuyi Sulaiman, kafasan halin Rayyern komai nasa dabanne dana kowa, amma Insha Allah Zamuna kokari akan cin abincinsa.�

Kai Dr Sulaiman din ya jinjina, domin kuwa yasan halin Rayyern din Sarai.

Jannart kuwa dake zaune anan dining table din, ahankali ta ajiye spoon din dake hannunta, tare kuma da d’aukan tissue ta goge bakinta.

Ganin alaman ta kammala cin abincin ne kuma yasa Mamy, kallonta cikin kulawa tace.

“Yauwa Jannart tunda kin kammala cin abincin naki, ga food flask nan d’auka ki kaiwa Rayyern nasa abincin, ki kula dan Allah ki sashi ya d’anci ko kad’anne, sai ki bashi magungunan kinji.�

Mamyn ta k’are maganan cikin sigar kulawan, da tasaka Jannart yin kasa da Kanta.

Ahankali kuma Cikin nutsuwa tace.

“To Mamy.�

Mik’ewa tsaye tayi, tare da gyara mayafin dake jikinta, kana ta d’auki d’an tray ta saka food flask da kuma cups, din da aka gama had’a masa duk breakfast din nasa aciki.

Cikin nutsuwa da kuma d’abi’arta na hankali kaitsaye ta nufi saman.

Ganin tafiyan Jannart dinne kuma, yasa Ramadan d’an gyara zamansa, tare da fuskantar su Abban nasa, cikin tausasawa da kuma yanda yasan zasu fahimcesa yace.

“Alhamdulillah wannan karon ba ayiwa Hamma Rayyern allura ba, saboda likitotin China sun sanja masa magani, wanda iya maganin ya wadatar basai an had’a masa da wannan, alluran mai matukar kashe jikin ba, sun kuma ce typhoid ne ke causing stomach pain din nasa, wanda kuma dama tuntuni munsan cewa akwai cronic typhoid ajikinsa, wanda ayanzu harya fara tab’a masa hanjinsa, shiyasa ma yake yawan sa masa ciwon ciki, amma yanzu likitotin can din sun bamu magunguna wanda, zasu na taimakawa wajen wanke masa hanjin nasa, dama kashe duk wata cuta dake cikinsa,
shiyasa ma suka sallamemu, amma hakan fa bawai yana nufin shikenan bane, sunce akwai yiwuwar dole za’ayi masa aiki, amma Idan anyi dace, magungunan zasu iya wanke duk wani cuta dake damunsa, Insha Allah zai samu sauki, akwai watarana na zuwa da Hamma Rayyern zaiyi bankwana, da wannan ciwon bazai sakeyi ba da Yardar Allah.�

Ajiyar zuciya duk su Abba da Baba Maud’on suka sauk’e, saboda bayanin da Ramadan din yayi musu, yasa sun samu gamsuwa sosai.

Cikin samun nutsuwar zuciya Abba yace.

“Allah yasa Ramadan, Allah Ubangiji ya yayewa Rayyern wannan ciwon, Insha Allah ma basai anyi masa aikin ba nasan zai warke, ai waraka ta Allah ce.�

“Sosai kuwa, da yardar mai duka watarana komai zai wuce, Allah dai ya yaye masa.�
Cewar Baba Maud’o.

Da “Ameen.� Duk suka amsa.

Inda Ramadan kuwa ya gyara zamansa, tare da sake Kallon su Abban nasa murya araunace yace.

“Amma Abba fa Doctors din sun tabbatar mana cewar, harda yawan shan zak’in da yake ma, domin shi zaki kana shansa yana taruwa maka aciki ne, bazai tashi yi maka illa ba kuwa, sai ya samu wani ciwon dazai tashi maka, zai iya had’ewa da wannan ciwon ya cutar dakai, batare da kasan da hakan ba, kuma shi kansa Hamma Rayyern ya sani, amma bansan yaushe ne Hamma Rayyern zai sanja ba, bansan yaushe ne zai daina maida abun zaki abun sonsa ba.�

Shiru duk su Abban sukayi saboda acikinsu babu wanda baisan halin Rayyern dason zaki ba sai dai sun sani laifinsune sune suka rainesa da zaƙin dan yawan soyyaya.

Saidai Abba ya kud’urtawa ransa cewar.

“Insha Allah zai dage tukuru wajen ganin ya raba Rayyern din, da yawan shan zakin da yakeyi.�

Haka dai suka d’an tattauna, kafun daga bisani Abba da Baba Maud’o suka fice, haka shima Dr Sulaiman.

Acan b’angaren Jannart kuwa ahankali, ta murd’a handle din kofar ta shiga bakinta d’auke da sallama.

Kwance yake akan lallausan gadonsa, Yayinda yayi kwanciyarnan irin ta rub da ciki.

Jin sautin muryarta ne kuma yasa shi, lumshe idanunsa dake bud’e.

Ita kuwa Jannart k’arasa shigowa cikin d’akin tayi, tare da ajiye tray din dake hannunta.

D’an Kallon yanda ya bawa kofar shigowa dakin baya tayi, cikin sanyi da kuma tausasa murya tace.

“Ga abincinka nan.�

“Nak’oshi.�
Ya fad’a atakaice saboda ayanzun Sam bayason takura.

“Katashi kaci abinci inji likita.�

Jannart din ta fad’a tana me bud’e food flask din, tare da d’aukan spoon ta zuba Coastarian breakfast dish din, gyara zaman plate din akan table tayi, tare da d’ago da Kanta ta kalleshi.

“Please ka tashi, Mamy ne tace kaci abinci sai kasha magani kaji ko.�

Tayi maganan cikin sanyin murya, da kuma zallan yanayin shagwab’an da ita kanta batasan tayi sa ba.

Idanunsa ya d’an rumtse ahankali, tare kuma da sa hannayensa duka biyu, ya sake matse pillow’n dake kirjinsa.

Kwata-kwata bayason yawan damuwa, bawai kuma dan bayajin yunwa ba, no kawai dai bayason yaga Jannart din akusa dashi har haka ne, musamman ayanzu daya fahimci wani abu, adangane da ita, shine tana da wani special Mood wanda yafahimci ita kanta batasan tana dashi ba tana kuwa yiwa zuciyarsa raraka.

Sake gyara kwanciyarsa yayi, cikin kuma nuna halin ko inkula yace.

“Kije zanci.�

Idanunta ta d’an zubawa faffadan bayansa, tare da kama waist dinta ta rik’e, dama tasan halinsa, ta kuma san cewar bazai tab’a daina wa ba.

“Nifa bawai na wani damu dakai bane, Dan kawai kaga Ina baka attention dina, saboda baka da lafiya ne kawai Malam, baya ga haka me mazaisa nazo wajenka.�

Ta fad’i hakan acikin zuciyarta, tare kuma da murgud’a bakinta gefe.

“Da kika tsuramin ido haka wani abu ne zaki bani? Ko cinyeni danye zakiyi!?�

Rayyern din ya fad’a, batare daya juyo ba.

Saurin kawar da kanta gefe tayi, tare da turo dan karamin bakinta gaba, cikin yanayin Mood din shagwab’a tace.

“Ni ai ba kallonka nake ba kuma ba kai nake kalloba�.

A hankali yace.
“Toh wa kike kallo�.

Baki ta É—an turo.
“Ni babu�.

Dan gajeren tsaki yaja tare da cewa.
“Mayya�.
Yayi mgnar a hankali so batajiba.
Sai ta d’an kwab’e fuska tare da cewa.
“Kuma ni Mamy ce ta aikoni, Dan Allah katashi mana katashi ka tashhhhhi....�

Ta kare maganar tana slowdown da muryarta.

Hakan kuwa shiya sanya, Rayyern din d’an juyowa akaron farko ya kalleta.

Karab kuwa kyawawan idanunsu suka had’e acikin na juna, da sauri Jannart din ta kawar da kanta gefe.

Shidinma kuma janye kallonsa daga gareta yayi, inda ya sauke ganinsa akan Coastarian breakfast dish din.

Idanunsa ya d’an lumshe akasalance, kuma cikin muryarsa da tayi sanyi yace.

“Give me the water.�

Kallon d’an madaidacin bakinsa dake motsawa tayi, sai kuma Ta kau da kanta, tare da rusunawa ta zuba masa ruwan swan acikin cup.

Mik’a masa ruwan tayi.

Ganin hakanne kuma yasa shi d’an yunk’urowa ya zauna.

Karb’an cup din ruwan yayi, tare dayi masa kurb’i d’aya ya ajiye.

Kyawawan yatsun k’afarta ya zubawa ido, cikin sauk’e numfashi yace.

“Naji zanci amma ki tafi, nima zan iyaci da kaina, banason abunda za’amin wanda baikai zuci ba, dan ni bana son abun zuciya biyu da manufa.�

Ya k’are maganar still yana me Kallon yatsun k’afar nata.

Idanu Jannart din ta d’an tsura masa, saboda har yanzu tana mamakin wasu kalamai da yake yawan jifanta dasu, wanda batasan me hakan suke nufi ba ta dai fahimci tabbas bai yarda da ita bane zarginta yakeyi.

Pink lips dinta ta d’an turo, tare da soma motsasu tana mamul mamul dasu, tamkar dai Wacce takeson fad’an wani abu.

Lips din nata ya kalla, ganin yanda suke motsawa ne kuma yasa shi kauda kansa gefe.

“Da wani k’aramin bakinta kamar na tsuntsu.�

Ya fad’i hakan acikin zuciyarsa, Yayinda afili kuwa idanunsa ya lumshe tare da cewa.
“Zagina kikeyi ko?�.
Da sauri ta zaro ido tare da cewa.
“Ni dai a'a�.
Kana ta juya, tana me wasa da y’an yatsun hannunta ta nufi hanyar fita daga cikin dakin.

Har takai bakin k’ofar d’akin nasa kuma saita tsaya tare da juyowa, cikin sanyi da kuma muryar dake nuna lallashi tace.

“Kaci abincin dan Allah sai kasha magani.�

Batare kuma da ta jira abunda zaice dinba ta fice daga cikin dakin tana mgnar zuci.
“Sherri kayan kolba, wannan ai yafi Yah Junaid neman sababi da hujja wai na zageshi�.

Bayanta yabi da kallo harta fice din.
Idonsa ya lumshe tare da sauke wani irin sassayan numfashi,
Kana a hankali ya buÉ—e su,
Anutse ya jawo plate din abincin, cikin sanyi da kuma yanayi irin na marassa lafiya, ya soma dan tsakalan abincin.

Baiwani ci sosai ba kuma ya ture plate din gefe, tare da d’aukan tea yasha, bayan yasha tea dinne kuma ya b’alli magungunansa yasha.

Yanasha kuwa ya koma ya kwanta.

Jannart kuwa Koda ta sauk’a k’asa, Bata samu Mamy ba, Riyyam nsra kawai ta samu, da shidinne kuma suka sha hira, kafun daga bisani kowannensu ya tashi ya tafi.

Alhamdulillah yau kwanan su Rayyern, uku da dawowa daga China, Masha Allah kuma ciwon cikin nasa yayi sauki sosai, saidai jikin nasa ne baigama samun karfi ba, har yanzu.

Kulawa kuwa yana samunshi sosai daga wajen ahalin nasa, Abba, Baba Maud’o, Mamy, Ramadan Riyyam, da kuma Dr. Sulaeman harma da Usman P.A duk suna iyaka kokarinsu wajen bashi kulawa, saidai kuma har yanzu bai iyacin abinci sosai.
Wanda kuma hakan al’adarsa ce ta tuntuni.

Yau ne kuma Barrister Kabir da kuma Dr Sajo suka shirya musamman dan zuwa duba Rayyern din.

Koda suka Iso gidan tarba na musamman, Abba da Mamy sukayi musu, bayan sun gaisa dasu Mamy da Jannart ne, Abba yayi musu jagora zuwa part din Rayyern din.

Koda sukaje akwance suka iske shi, duk da cewar bayajin karfin jikinsa, amma daya gansu ya d’an sake sunyi hira.

Yanzun kuma saukowarsu k’asa kenan.

Dr Sajo ne ya kalli Abba, cikin kulawa yace.

“Amma Alhaji Bashir me zai hana baza’a sake maida Rayyern din, hospital ba tunda naga har yanzu jikin nasa bawani karfi sosai.�

Mamy dake zaune acikin falonne, ta d’an gyara zamanta, tare da fuskantar Dr Sajon, cikin bayyana damuwarta tace.

“Ai bawai wani abune matsalar ba, bayason cin abinci ne kwata kwata, komai aka basa sai yace a’a, Koda an matsa masa kuwa, bai wuce yayi loma biyu ko uku ba, sai yace ya koshi, bashi da wani abinci sai tea, nan ma yanzu ne yake d’an shan tea din da madara, da bayason ko madaran saidai empty, shiyasa bayi da karfin jiki.�

Kai Dr Sajo ya jinjina, cikin gamsuwa yace.

“Eh to kin san dama duk inda dan adam yayi ciwo abinci yake fara tsana.
Tabbas kuwa bazai samu wadataccen karfin jiki ba, harsai in ya dage da cin abinci, amma ana tambayansa ko yana da buk’atar wani abu, sai anayi masa.�

“To.�
Mamyn tace.

Yayinda Abba kuwa cewa yayi.

“Idan naga abun nasa yaki karewa ai, dolensa na daukesa na maidashi hospital, yasan duk wani illar rashin cin abinci, amatsayinsa na Dr amma baya kiyayewa.�

“Hakane kam sai hakuri da majinyaci, Allah dai ya bashi lafiya.�

Cewar Barrister Kabir.

Da “Ameen.� Duk suka amsa.

Basu wani jima ba kuma, Abba yayi musu rakiya suka tafi.

Bayan suntafi dinne kuma Mamy ta haura saman.

Azaune tasa meshi yasaka Laptop d’insa agaba, yana Dan lallatsata.

“Rayyern.�
Mamy takira sunansa da kulawa.

Jin sautin muryar Mamyn nasa ne kuma yasashi d’ago kansa Ahankali ya kalleta.

“Na’am Mamy.�
Ya amsa adan kasalance.

Karasa shigowa cikin dakin Mamyn tayi, tare da matsowa kusa dashi, cikin kulawa da kuma nuna tausayawa agareshi tace.

“Meyasa ne haka Babana? Meyasa kwata kwata bakason cin abinci? kasani fa bazaka samu isashshen karfi ba, har sai inkana cin abinci, yanzu fad’amin mekakeson ci, ko meye saina dafa maka.�

Fuskarsa yad’an kwabe tare da marairaicewa.

Cikin yanayin sakalci yace.

“Nifa Mamy bana sha’awan komai, kawai dai abincin yanzunne baya min, nafison abu me d’an melting da kuma tsami, like Chinese dishes dai, ko Mamy amin irin kunun ranan.�

Ya k’are maganan yana langwabar da kansa gefe.

Murmushi Mamy tayi tare da cewa.

“To za’ayi maka kunun kaji kada ka damu.�

Mamyn ta fad’a tare da juyawa ta fice daga cikin dakin.

Direct kasa Mamyn ta sauk’o, inda ta samu Jannart ta gaya mata, cewar Rayyern yana son ayi masa irin kunun ranar.

“To.� Jannart din tace, babu musu kuwa ta wuce kitchine, Anutse ta soma had’a kunun kamar yanda ya buk’ata.

Tsab ta gama had’a kunun, da yayi kyau sai tashin kamshi yake, juye kunun acikin flask tayi, tare da daura flask din akan tray ta daura cups agefe, sai kuma madara da zuma wanda suke cikin wani abu mai kaman glass.

Fitowa falo tayi rike da tray din ahannunta.

Mamy dake zaune afalon kuwa Ganin Jannart din harta kammala ne yasa, cikin jin dadi tace.

“Masha Allah Jannart har kin kammala, Allah Dai yayi miki albarka, ki kai masa nasan yana nan yana jira.�

Murmushi Jannart din tayi, tare kuma da dan sunkuyar da kanta, cikin nutsuwa ta nufi saman.

Tafiya take Ahankali, Yayinda tayi kyau cikin riga da wandon pallazon dake jikinta, wanda ta yafa mayafi. Dan babba akan shigar nata, saidai duk da hakan ga wanda yayi mata Kallon k’urulla, tsab zai iya hango tsararren cikakken hips dinta.

Ga kuma rigar shirt din da yayi mata cibcib ajikinta, cikin tan nan alafe yake, tamkar babu hanji acikinsa.

Karasowa bakin kofar falon nasa da tayi ne kuma yasa ta, tura kofar ahankali, bakinta dauke da sallama ta kutsa kanta ciki.

Babu kowa acikin falon hakane yasa ta nufi, Bedroom nashi,
a hankali ta tura ƙofar tare da sallama a bakinta.
Still nan É—in ma babu shi,
Cikin mamaki ta É—an ware idanunta tare da jujjuya kanta, tana mai kasa kunne wai ko zata jiyo mostinsa a Bathroom,
jin shirune ba motsin komai, harta nufi kofar dakin dan fitowa falon nasa ne kuma, saita hangosa zaune acikin wani balcony wanda labulayensa keta kaduwa saboda iska.

Kaitsaye wajen ta nufa tana isa wajen kuwa, idanunta suka sauka akansa.
Da sauri tayi kasa da kanta, saboda ganinsa ahaka da tayi, domin yau dinma ba wani kayan kirki bane ajikinsa, singlet ne da kuma gajeren wando.

Shikuwa Rayyern jin sallamanta ne yasashi dago kansa, ya sauke idanunsa akanta.

Tashin farko kuwa idanunsa suka sauka, akan lafaffen cikinta, wanda ta daure kasansa da adon igiyan wandon dake jikinta.

Janye idanunsa yayi daga Kallon nata, tare da maida kallonsa gefe.

Anutse ta karasa isowa inda yake, tare da Dan dukawa ta ajiye tray din dake hannunta.

Cup ta d’auka tare da zuba masa kunun, kana ta saka masa madara da zuma aciki.

D’an d’agowa da kanta tayi, hade da mik’a masa cup din.

Cikin sanyi tace.

“Gashi.�

Tayi maganan tana me sauke idanunta, akan lallausan beard d’insa. Wanda yake matukar yi mata kyau.

Ahankali ya juyo da kallonsa zuwa gareta, lokaci daya kuma ya sauke idanunsa akan kyakkyawar fuskarta, da kuma dan karamin lips dinta, dake shining din lipgloss.

Hannunsa yasa ya karb’i cup din, Ahankali kuma ya dan motsa lips d’insa, saidai kuma ita kanta bataji mai ya fad’a ba.

Kan Wani had’add’en rug dake gefensa ta zauna, tare kuma da rike flask din ahannunta.

Saurin kallonta yayi, saboda baiyi tunanin zama zatayi ba, kamar zaice wani abu kuma sai ya fasa,Ahankali kuma ya janye idanunsa da suka sauka akan waist dinta.

Cikin nutsuwa ya soma sipping kunun, yana me lumshe idanunsa saboda yanda yakejin dadin kunun.

Itakuwa Jannart gaba daya kallonta ta mayar k’asa, inda take hango Riyyam-nsra da Baba Maud’o wayanda suke zaune abakin gate.

Kallonsu takeyi sosai, musamman ayanzu da taga Riyyam din na waya, ba tare da taga ya jima yana wayan ba kuma ya mikawa Baba Maud’o.

Hannayenta duka biyu ta had’e tana kallonsu.

Yayinda acan kasan kuwa.

Mammy ce takira tana tambayan Riyyam din jikin Rayyern .

Nan Riyyam din yake shaida mata cewar jikin da sauki, Koda ta nemi ta gaisa da Rayyern dinne kuma, Riyyam yake sanar mata cewa, baya kusa da Hamma Rayyern din, ananne kuma Riyyam din yace.

“Mammy Ina tare da Baba Maud’o bari na bashi ku gaisa.�

“To.� Mammyn tace.

Yayinda Riyyam-nsra kuwa ya mikawa Baba Maud’o wayar.

Karb’an wayan Baba Maud’o yayi tare kuma da karata akan kunnensa, Cikin nutsuwa yace.

“Assalamu Alaikum.�

Acan Ethiopian kuwa Mammy dake zaune akan kujera, Jin amo da kuma sautin muryar daya daki dodon kunnenta ne, yasa taji zuciyarta tayi wani irin bugawa, take kuma tsikar jikinta suka shiga wani irin mimmikewa, cikin wani irin yanayi ta mik’e tsaye, tare da sake sauraran muryar dake kan wayar.

“Assalamu Alaikum.�

Baba Maud’o ya sake maimaita sallaman nasan, saboda Jin shiru da yayi.

Komawa Mamyn tayi ta zauna, tare kuma da sanya hannu ta dafe kirjinta, cikin rawar murya tace.

“Wa’alaikassama.�

Zumbur haka Baba Maud’o ya mik’e tsaye daga zaunen da yake, tare kuma da d’an zazzaro idanunsa waje, lokaci daya wani irin yanayi ya bayyana atattare da Baba Maud’on.

Wanda hakan yasa Riyyam dake zaune kallon Baba Maud’on, Cikin yanayin mamaki yace.

“Baba Maud’o lafiya?�

Kallonsa Baba Maud’on yayi, tare kuma da komawa Ahankali ya zauna, saidai kuma har yanzu jikinsa bai daina tsuma ba.

Daga can b’angaren kuwa cikin rawar murya Mammy tace.

“Ina wuni, ya maijiki?�

Hannu Baba Maud’on ya d’an dunkule cikin wani irin abu dake dukan zuciyarsa yace.

“Lafiya mai jiki kuma Alhamdulillah.�

“Masha Allah Allah ya kara sauki, mungode sosai Baba Maud’o nasan kuna nan kuna fama da rigiman Riyyam, Allah ya bada lada.�

Mammyn ta fad’a cikin sanyin murya.

Baba Maud’o kuwa murmushi ya aro ya sakawa muryarsa, kana shima cikin sanyi yace.

“Ameen summa Ameen, ai Riyyam kam babu wani rigiman da yake yi mana, harma mun saba dashi kwannan yana ta cewa kin matsa ya komo mu kuma bamu son rabuwa dashi.�

Murmushi Mammyn tayi, cikin kuma karfin hali da danne bugun zuciyar da takeji, tace.

“Shikenan to Baba Maud’o ahuta gajiya.�

“Yauwa.�
Baba Maud’on ya amsa, tare da zare wayar akan kunnensa, cikin sanyi da kuma wani irin tunani dake dukan, kwakwalwarsa ya mikawa Riyyam nsra wayan.

Karb’an wayan Riyyam-nsra yayi tare da Karawa akan kunnensa.

Jin muryar Riyyam dinne kuma yasa, Mammy sauke wani irin nannauyar Ajiyar zuciya.

Cikin sanyi tace.

“Riyyam ka had’ani video call da Rayyern, inason naga ya yanayin jikin nasa.�

“To Mammy zan hadaku amma maybe sai gobe, saboda nasan yanzu haka yana sama, kuma Idan magriba ta kusa bayason yawan magana.�
Riyyam din ya fada atausashe.

Daga can b’angaren kuwa Kai Mammy ta jinjina, tare da cewa.

“Shikenan to badamuwa Allah ya kaimu goben.�

“Ameen�
Riyyam din ya amsa kana sukayi sallama da Mamyn.

Duk abunnan da sukeyi kuwa Jannart na kallonsu, saboda gaba daya hankalinta ya tafi garesu ne ma, yasa har yanzun take nan bata tafi ba.

Shikuwa Rayyern tuni ya shanye kunun da ta zuba masa din tas.
Ganin bata da niyan kara masa ne kuma yasa shi, dagowa ya kalleta.

Akaron farko kenan daya tsaya ya k’are mata kallo, idanunsa ya dan tsayar akan fuskarta, saboda yanda yaga hankalinta ya tafi izuwa wani waje na daban.

Ajiye cup din dake hannun nasa yayi, Karan ajiye cup dinnasa ne kuma yasa hankalinta dawowa garesa.

Ahankali ta juyo da kanta zuwa garesa, karab kuwa idanunsu suka sarke acikin na juna.

Sunkuyar da kanta k’asa tayi, tare da sauke numfashi, cikin silent voice dinta tace.

“Nak’ara maka ne?�

Kansa ya d’an girgiza mata, tare da lumshe idanunsa, cikin wani irin yanayin daya saka zuciyarta harbawa yace.

“Um um nakoshi.� yayi mgnar yana jin dadi bakinsa yayi masa wasai yawunsa ya sinke alamar dandanon bakinsa zai dawo.

Kallonsa tayi, haka kuma shid’inma.

Kasa tayi da Idanunta tare da matsowa ta durk’usa, tray din ta ke kokarin dauka.

Dan kusancin da sukayi ne kuma yasa, daddad’an kamshin turarenta ratsa cikin hancinsa.

Idanunsa ya dan lumshe, Yayinda itakuwa tray din ta dauka Anutse ta juya ta tafi.

Kaitsaye kasa ta sauka, bayan takai kayan kitchine ne kuma ta wuce dakinta.

Shikuwa Rayyern kiran Sallan magriba ne ya tadashi awajen.

Washegari.

Yau dinma kunun da Jannart din tayi masa jiya ya kuma sha, sai kuma abu mai romo da Mamy tasa ta dafa masa, babu laifi kuma yaci sosai.

After 3days.

Mamy ce tsaye agefensa, Yayinda shikuwa ke zaune akan daya daga cikin kujerun falon.

Murmushi Mamyn tayi tare da dubansa cikin danjin dadi.

Tace.

“Masha Allah Babana Lallai jiki yayi sauki, tunda har ka iya fitowa falo.�

Murmushi ya d’anyi tare da Kallon Mamyn nasa, cikin sanyi yace.

“Mamy yunwa nakeji sosai, kuma nafison abu mai dan tsami, please Mamy roasted fish da ruwan lemon tsami nakeso, ko kuma miyan da akayi ranan nan pls Mamy.�

Murmushi Mamyn tayi tare da cewa.

“To Rayyern amma ni bansan yanda akeyin miyan ba, rannan ma bani nayi ba Jannart ce tayi, amma bari na turo maka ita saikayi mata bayani.�

Fuskarsa yadan kwabe cikin shagwaba yace.

“Eyyah Mamy kifada mata mana, dole sai ni?�

“Eh mana bakaine kakeso ba.�

Mamyn ta fad’a tana me nufar dakin Jannart.

Ramadan dake zaune agefe kuwa, Kallon Hamman nasa yayi, tare da mik’o masa magungunan daya b’are.

Cikin kulawa yace.

“Please Hamma Rayyern karb’a maganinka kasha.�

Fuskarsa yadan yamutsa, kamar zaice a’a sai kuma ya karba yasha.

Bayan yasha maganin ne kuma Ramadan ya Mike ya tafi, domin dama hospital zai tafi, ya tsaya bawa Hamman nasa maganine.

Already Abba kuma dama ya tafi company, Riyyam-nsra kuwa yana waje .

Jannart kuwa dake falon ta zaune take, inda tayi kyau cikin wani fitted gown na maroon lace dake jikinta, sosai rigar tabi jikinta ta zauna, saboda yanda dinkin ya fita sosai.

Bak’aramin kyau yau Jannart din tayi ba, musamman da ta watsa jelan gashinta haka bata kitseshiba, tare dasa dan siririn mayafi daga kanta zuwa kirjinta.

Shigowar Mamy ne kuma yasa ta d’agowa, fuskarta dauke da murmushi.

Itama Mamyn murmushi tayi, tare kuma da Kallon Jannart din Cikin kulawa tace.

“Jannart kije mijinki yana kiranki.�

Kai Jannart din ta d’an sunkuyar kasa, cikin sanyi kuma tace.

“To.�

Juyawa Mamyn tayi ta tafi, Ganin hakanne kuma yasa Jannart din mikewa, Cikin yanayin nutsuwarta ta nufi part din nasa.

Ahankali ta murd’a handle din kofar ta shiga, bakinta dauke da sallama.

Saidai kuma dan ja baya tayi, ganinsa da tayi yana waya, hakan yasa ta matsawa jikin kujera ta d’an zauna, wanda hakan yasa suka zama suna fuskantar juna.

Ahankali ta dan saci kallonsa, musamman yanda taga yayi kyau cikin shigar riga da wandon DG dake jikinsa.

Ahankali ya ajiye wayar tare da d’ago kansa ya kalleta.

K’asa tayi da Idanunta, cikin sanyi tace.

“Ina kwana.�

Idanunsa ya sauke akan labbanta zuwa kan kirjinta, wanda dinkin jikin nata ya masifar fitar da shape din samansu.

Kauda kansa yayi batare da ya iya amsa mata ba

Itakuwa Jannart jin bai amsa mata dinbane yasa ta cewa.

“Ya jiki.�

“Da sauki.�

Ya amsa mata da wani irin murya, wanda yasa ta dago ta kalleshi.

Ahankali kuma tace.

“Gani Mamy tace kana kira na.�

Idanunsa ya dan marairaice cikin sanyin murya mai hade da zallan shagwab’a yace.

“Yunwa nakeji sosai, kibani abinci, but mai dan tsami kawai kinji....�

Yaja maganar tasa cikin wani irin yanayi, tare dasa hannunsa ya shafa cikinsa.

Hakan kuwa shiya sanya Jannart ta d’ago Kai ta kalleshi, lokaci daya kuma taji wani irin tausayinsa ya cika mata zuciya.

Ahankali Cikin yanayin ta itama dake kama da shagwab’a tace.

“To meye kakeso? Miya ko kuma abinci?.�

Idanunsa dake lumshewa ya rufe, tare da bud’e labb’an sa ahankali yace.

“I don’t know kimin komai kawai, ko miyan da kika tab’ayi ranan mai ɗan sami.�

“To.� Tace asanyaye tare da juyawa ta nufi hanyar fita.

Koda ta fito daga dakin nasa, Anutse ta soma sauka daga kan steps din.

Dai-dai lokacin kuma Riyyam-nsra yake haurowa saman, hannunsa rike da waya.

Ganin Jannart dinne kuma yasa shi sakin murmushi, Cikin kulawa yace.

“Good morning My Aunty ya jikin Hamma Rayyern.�

Murmushi tayi tare da dubansa, cikin sakin fuska tace.

“Jikinsa da sauki Riyyam, yanzu ma na sameshi afalo.�

Murmushi Riyyam din yayi tare da cewa.

“Masha Allah, bari naje na sameshi.�

Riyyam din ya fada, Yayinda ita kuwa Jannart kaitsaye kasa ta wuce, inda ta nufi kitchine Dan fara had’a masa abunda zaici.

Riyyam kuwa direct falon ya wuce, yana zuwa zuwa kuwa ya zauna akusa da Hamman nasa.

Tare da dan rankwafar dakai cikin sanyi, yace.

“Hamma Rayyern Mammy tanason yin magana dakai, tace kuyi video call saboda taga ya jikin naka, na kirata please?�

Idanunsa ya dan lumshe, akasalance kuma ya d’an gyad’awa Riyyam din Kai alaman “Eh.�

Murmushi Riyyam din yayi cikin, Jin dadi kuma ya zaro wayartasa tare da dannawa numbern Mammy kira video call.

Ring kadan kuwa wayar tayi Mammy ta d’aga.

Tana d’agawa kuwa Riyyam yayi murmushi, tare da Kallon Mammyn nasa Cikin kulawa yace.

“Mammyna Barka da safiya, ga Hamma Rayyern dinnan ku gaisa.�

Ya k’are maganan yana me mik’awa Rayyern din wayar.

Kasancewar kuma kan Rayyern din yana dan jingine ne yasa, Riyyam cewa.

“Hamma Rayyern ga wayan.�

Ahankali ya d’an juyo tare da kai dubansa ga fuskar wayar, wani irin bugawa yaji zuciyarsa tayi da karfi, wanda hakan ya sashi zabura tare da yunkurawa ya gyara zamansa, inda ya sauke ganinsa akan fuskar.........!

Littafin TUBALI dai na kuÉ—ine ko kin gansa a wasu group É—in na satane

By
*GARKUWAR FULANI*
22/12/2021, 19:45 - 🥰🥰: Tare da fuskantarsu dukansu, cikin dan nisawa yace.

“Gaba d’aya matsalarmu a kullum akan Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara ne, wanda kuma ni kaina bani da iko, ko wani matsayi da zan iya dakatar dashi akan abunda ya saka agaba, saboda duk wani k’a’ida da dokokin da akebi ya bisu, Idan kuma har nace zan wargaza masa tsari.
To tabbas zai iya Kai k’arata wajen na sama dani, hakan kuma zai iya sawa na rasa aikina, yaron ya wuce duk yanda muke tunani, kowacce hanya da zamu b’ullo masa ya sani, kansa yana ja sosai, babban abunda na lura dashi kuma shine, kwata kwata baya tsoron magautansa yaron yana nan Tamkar a haifeshi ne domin daukan fansa!!!.�

Numfashi mai nauyi duk suka ja, musamman Alhaji Idi Sale Dakata wanda gaba daya abubuwa suka had’e masa.

Ga zafin b’atan Jannart ga kuma, na wannan shegen yaron Dr. Rayyern.
Barrister Kabir kuwa, kalaman Alhaji Bala Tambari na karshe yaketa nanatawa a zuciyarshi don son fahimtar wani abin.

Haka dai taron nasu ya watse gaba d’aya zuciyar Alhaji Idi, da kuma na Dr. Lukman Alhaji Abdu Tababa babu dadi, kowannensu kuma saboda Rayyern.

Dr. Lukman din, da kuma Alhaji Abdu Tababa ne suka had’a hanya wajen tafiya, haka ma Alhaji Bala Tambari shima tafiya yayi.

Hakan yasa falon ya rage daga, Daddy sai Barrister Kabir.

Juyowa Alhaji Idi Sale Dakata’n yayi? Ya fuskanci Barrister Kabir, cikin kuma nuna halin damuwa yace.

“Kabir ayanzu babu abunda yake damuna, kamar b’acewar Jannart, har yanzu babu wani labari, kwata kwata ayanzu ma ba batun companyn Rayyern Mai-nasara bane ke damuna, matsalar b’acewar Jannart itace ke damuna hukuma suna iya yinsu abin yaci tura.�

Afakaice kuma ta k’asan idanu, Barrister Kabir ya kalli Yayan nasa, tare da d’an ya mutsa fuskarsa.

Wanda kuma daga wajen Alhaji Idi Sale Dakata’n ma hakan yake, domin kuwa bayan yayi maganar shima, ta k’asan idanu, ya kalli K’anin nasa, tare da sakin wani Shu’umin murmushin, da shi kad’ai yasan ma’anar yinsa.

Barrister Kabir kuwa, mur yasha tare da saka fuskar tsare gida, irin tasu ta lawyoyi, saboda shima akwai wani abu daya gano amatsayinsa na lawyer.

Shi yanayiwa Barrister Kabir kallon biri, shi kuwa Barrister Kabir yanayiwa yayan nasa kallon Ayaba.

Koda suka fito daga d’akin taron Alhaji Idi Sale Dakata’n, main falon gidan suka dawo, inda suka samu Momy ta gama had’a abinci.

Sama sama haka Barrister Kabir yaci abincin, bayan sun kammala ne kuma yayiwa Yayan nasa sallama, kaitsaye kuma daga gidan Alhaji Idi Sale Dakata’n, gidansa ya nufa.

Koda ya isa gidan afalo ya samu Dijat.

Hira kadan suka tab’a kana kaitsaye ya wuce bedroom d’insa.
Key ya sawa kofar bedroom din, tare da komawa ya zauna, bayan ya d’auko wasu takardu.

Anutse yake wargaza takardun, tare da Ware wasu daga ciki yana duddubawa.
D’ago wata takarda da yayi ne kuma, ya sashi tsurawa rubutu, da kuma hoton passport din dake jiki idanu.

*** ***

Almost 4weeks kenan yanzu da, dawowar Rayyern daga China, Alhamdulillah kuma jikinsa ya warware.

Bisa taimakon Ramadan da kuma Jannart, way’anda suke kula da shan maganinsa.

Hakan yasa ciwon cikin nasa yayi sauki, ya kuma gama samun karfin jikinsa, duk da cewar time to time ya kanji, ciwon cikin na tashi masa, amma da yasha magani yake jin sauki.

Ahankali yake sauk’owa daga kan matattakalan falon, inda yayi kyau cikin shigar Ash colour suit dake jikinsa.

Yayinda hannunsa ke rik’e da briefcase, da alama kuma aiki zaije.
Ya dawo asalin Rayyern d’insa, big man wanda bai wani cika son wasa ba, wani Rama da yawan kasalan da yakeji ada, duk sun kama gabansu.

Mamy dake tsaye akan dining table, jin alaman takun takalmansa ne yasa, ta d’ago kanta ta kalleshi.

Ganin yanda yayi kyau ne kuma, yasa Mamyn sakin murmushi, Cikin kulawa tace.

“Babana yadai, yau na ganka cikin shiri haka fita zakayi ne?�

Kansa ya jinjina, adaidai lokacin da yake gama sauk’owa daga kan steps din yace.

“Eh Mamy yau zanje company.�

Murmushin dake kan fuskar Mamy ne ya fad’ad’a, cikin jin dadi tace.

“Ah Lallai Masha Allah Babana ya samu sauk’i, amma Ina fatan kanajin karfin jikinka sosai.�

Idanunsa ya d’an lumshe tare da jinjina mata kai alaman. “Eh.�

“To kayi breakfast tukun kafun ka tafi.�

Mamyn ta fad’a tana me nuna masa kujera, tare dayi masa alama akan ya zauna.

Fuskarsa ya d’an shagwab’e, kamar zaice a’a kuma saiya zauna.

Dai-dai lokacin kuwa Jannart ta shigo cikin falon, sanye take da riga da wando ajikinta, saidai wandon irin mai fad’in nan ne, haka ma rigar Wacce take da igiyan d’aurewa, hakan ne kuma yasa lafaffen cikinta bayyana, saboda yanda ta d’aureshi da igiyan, haka ma shape din cikin nata ya bayyana sosai.

Kasancewar kuma kayan nada kalan baki, shiyasa ta yafa siririn mayafi daga kanta zuwa wuyanta.

Sassanyan kamshi take bazawa, shigowarta cikin falonne kuma yasa shi sauk’e idanunsa akanta.

Mamy kuwa Ganin Jannart dinne yasa Cikin kulawa tace.

“Yauwa Jannart yi saving din mijinki mana, yana sauri zai tafi wajen aiki ne.�

Kai Jannart din ta d’an sunkuyar k’asa, cikin yanayin nutsuwa tace.

“To Mamy.�

Kaitsaye dining table din da yake zaune ta nufa, saidai koda wasa bata bari sun had’a idanu ba.

Koda ta k’arasa inda yake, plate ta d’auka tare da bud’e food flask, cikin sanyin muryar dake bayyana nutsuwarta tace.

“Ina kwana.�

“Lafiya.�
Ya amsa mata atak’aice, tare da zubawa kyawawan fararen yatsunta idanu.

Abincin ta zuba masa, bayan ta kammala ne kuma ta turo masa plate din gabansa.

Tare da saka masa apple juice din da ta had’a, acikin wani d’an glass cup.

Ahankali ya soma cin abincin, tare kuma da dan lullumshe idanunsa, saboda yanda yake jin kamshinta na shiga hancinsa.

Jannart kuwa Ganin ya fara cin Abincin ne, yasa ta wucewa kaitsaye ta nufi sama, Dan d’auko maganinsa.

Ahankali ta tura kofar d’akin ta shiga.
Lumshe Idanunta tayi saboda, wani irin kamshi daya bugeta.
Ga kuma sanyin ac dake busa ko ina.

Dan bud’e Idanunta tayi, tare da soma bin ko ina dake cikin dakin da kallo, komai nasa need babu alaman datti, duk da cewar ya kwana acikin dakin, amma saida ya gyara komai kafun ya fita.

Hakanan kawai ta samu kanta da sakin murmushi, kaitsaye kuma cikin nutsuwa, ta wuce ta dauko magungunan nasa.

Koda ta sauk’o k’asa harya kammala cin abincin nasa, saidai juice dinne da bai gama shaba, wanda kuma yake sipping d’insa ahankali.

K’arasowa kan dining table din tayi, Anutse ta b’are magungunan tare kuma da zuba su acikin tafin hannunta.

Kallonsa ta d’anyi, tare da mik’a masa magungunan, alaman ya karb’a.

D’ago idanunsa yayi ya kalleta, cikin yanayinsa daya saba yi mata magana yace.

“Ni yaro ne, da har sai kin b’aremin magani, ni bazan iya dakai na bane akace miki? Sai kiyi ta wani ɗuɗɗuramin magunguna babu ko tausayi�

Idanunta ta d’an janye daga kallonsa, saboda ayanzu babu wani abu nasa da bata sani ba, saikayi masa abu sau goma, amma baya tab’a gani yanzu zai gwatsaleta ta fahimci zarginta yakeyi ma shi.

K’wayoyin idanunta tad’an juya ahankali, sau d’aya kuma cikin sigar lallashi tace.

“Okay I’m sorry take it.�

Hararanta ya d’anyi ta k’asan idanunsa, sanin Mamy na cikin falonne kuma yasa shi, bud’e tafukan hannunsa, Anutse ta zuba masa maganin ahannunsa, gudun kada hannunta da nasa su had’e, tayi hakanne kuma saboda, ita kadai tasan me takeji, aduk sanda ta tuna lokacin da fatar hannunsa ya tab’a nata.

Rayyern kuwa bayan yasha Maganin ne ya mik’e tsaye, tare da d’aukan briefcase d’insa, cikin sauri yace.

“Mamy na tafi saina dawo.�

“A dawo lafiya Allah ya bada sa’a.�

Mamyn ta bashi amsa, Cikin kulawa.

Da “Ameen.�
Ya amsa kana ya sakai ya fice daga cikin falon.

Ganin hakanne kuma yasa Jannart dawowa, kusa da Mamyn ta zauna.

Shikuwa Rayyern yana fita kaitsaye company ya wuce,
Koda yaje kuwa ya samu ma’aikatan nata aiki, kowa na aikinsa kamar yanda ya dace.

Gaba d’aya ma’aikatan sun bada himmansu wajen yin aikin tsakani da Allah.

Domin har anfara har had’a cattoon's din abubuwa, wanda kowanne kwali d’auke yake da sunan tambarin.
MAI-NASARA.

Komai Yayi masa sosai, hakanne ma yasa shi jinjina kansa, kaitsaye kuma ya wuce office d’insa dake nan cikin companyn.

Wasu d’an aikace aikace yayi, bayan ya kammala ne kuma ya fito, kaitsaye hospital d’insa ya wuce.

Bashi ne ya dawo gidan ba kuwa sai k’arfe 10:00 pm dai dai.
Hakan ya faru ne kuma saboda tsayawa da yayi, yiwa wata operation, baya ga haka kuma, ya tarawa kansa aiki sosai, wannan dalilin yasa shi tsayawa, ya d’an rage ayyukan.

K’asa k’asa ya danna Horn din motar tasa, cikin abunda bai wuce mintuna 2 ba kuwa, aka wangale masa gate din gidan.

Anutse ya tura hancin motar ciki, bayan yayi parking motar ne kuma ya fito.

Tare da Kallon Baba Maud’o wanda shine ya bud’e masa gate din.

“Baba Maud’o da kanka, ai daka bari na fito na bud’e, sam banaso naga kana wahalar da kanka, saudayawa Idan naga kana wannan aikin sai naji duk babu dadi, please Baba Maud’o ka bari.�

Rayyern din ya fad’i haka ga Baba Maud’o cikin tausasa harshe.

Baba Maud’o kuwa Murmushi yayi tare da d’an gyara tsayuwarsa, kana Cikin kulawa yace.

“Haba Rayyern meye na damuwa kuma, bayan kasan hakan aikina ne, kuma gashi Ari yayi bacci shiyasa.�

Fuska Rayyern din ya d’an kwab’e, hade da karyar da wuyansa yace.

“Ni dai Baba Maud’o da gaske banason hakan, banajin dadi Idan naga kana bud’e gate inajin wani nauyi a zuciyata.�

Murmushi Baba Maud’o yayi, tare da komawa wajen zamansa ya zauna.

Ganin hakanne kuma yasa Rayyern d’in ma, matsawa ya zauna akusa da Baba Maud’on.

“D’azu Barrister Kabir yazo dubaka da jiki, amma baisame ka ba, saidai yace agaisheka.�

Baba Maud’o ya fad’a yana me Kallon Rayyern din.

Shikuwa Rayyern Ajiyar zuciya ya sauk’e, tare da d’an mammatsa hannunsa.
Cikin kuma taushin murya yace.

“Ina amsawa, bari na shiga ciki Baba Maud’o, yau duk na gaji aikin office ya gajiyar dani.�

“To Rayyern Mukwana lafiya.�

Da “Ameen.�
Rayyern din ya amsa, tare da wucewa ciki kaitsaye.

Koda ya shiga main falon nasu babu kowa, hatta su Ramadan da Riyyam nsra duk suna daki.

Kaitsaye kuma shima d’akin nasa ya nufa.
Yana shiga kuwa ya soma rage kayan jikinsa.

Bayan ya shiga toilet yayi wanka ne kuma, ya shirya kansa cikin lallausun kayan bacci.

Bayan yasha Nutri milk ne kuma ya koma kan gado ya kwanta.

Kasancewar agajiye yake ne kuma, yasa yana kwanciya bacci ya d’aukesa.

Washegari.

Arewa24 tv station.

Aunty Fauziya ce ke tafe cikin d’an sauri, saidai kallo d’aya zaka yiwa Fuskarta, ka fahimci cewa tana cikin yanayin damuwa.

Fitowarta kenan kuma daga dakin yad’a labaransu, sukayi Karo da Salman.

Kallonta Salman din yayi, Ganin damuwa afuskarta ne kuma yasa shi d’an tsayawa, Cikin kulawa yace.

“Aunty yadai naganki haka, wani abu ya faru ne?�

Kai ta d’an girgiza, cike da damuwa tace.

“Salman b’acewar Jannart ke damuna, tayaya za ‘ace mace kamar Jannart ta b’ace b’at kamar kud’i? hankalina yana tashi sosai Salman, ka duba dai irin jami’an tsoron da Babanta ya bawa cikiyar nemo ta, ga kuma mu da kullum sai munsa cikiyarta, amma har yau babu wani wanda yace ya ganta, abun yana min ciwo Salman, ga mahaifinta asanadin haka ko lafiyar kirki bashi dashi, kwanan nan naji har India aka fita dashi, duk kuma akan lamarin b’acewar Jannart, Ina cikin damuwa akan hakan.�

Ajiyar zuciya Salman ya sauk’e.

Dai-dai lokacin kuwa Asiya tazo ta wucesu, saiwani karairaya takeyi tamkar zata b’alle.

Ganin hakanne kuma yasa Aunty Fauziyan wucewa office dinta, take kuwa Salman ya rufa mata baya.

Koda suka isa cikin office din zama, duk sukayi, ananne kuma Salman ya d’ago ya kalli Aunty Fauziyar.

Cikin sanyi ya d’an gyara zamansa tare da cewa.

“Gaskiya da banyi niyan fad’awa kowa ba saboda sirrine, saidai ke naga gaba d’aya hankanlin atashe yake, akan b’atan Jannart, amma Dan Allah duk wata magana da zan fad’a miki inason ta zama sirri.�

Nisawa Aunty Fauziya’n ta d’anyi, tare kuma da fuskantar sa tace.

“Kafad’i duk abunda kakeson fad’a Salman, Insha Allah bazan gayawa kowa ba, kasanni kasan koni wacece zan rik’e duk wani sirri.�

Kai Salman din ya jinjina, tare da dan gyara zamansa kana yace.

“K’warai nasan hakan Aunty Fauziya, nasan ke ta musamman ce shiyasa ma na yanke shawarar sanar dake, danki cire wannan damuwar dake zuciyarki, agaskiya Jannart ba b’ata tayi ba.�

Idanu Aunty Fauziyan ta tsura masa cike da mamakin, Jin abunda ke fitowa daga bakinsa tace.

“Kamar yaya Salman ka warwaremin maganar ta yanda zan fahimta.�

“Jannart ba wai b’acewa tayi ba, K’anin Babanta Barrister Kabir shi yayi mata aure, batare da sanin kowa ba, yace kuma yayi hakanne saboda wani dalili nasa maik’arfi, wanda kuma acewarsa hakanne kad’ai zai tseratar da rayuwarta, daga fad’awa koman magauta masu farautar rayuwarta.�

Wani irin gauron Ajiyar zuciya Aunty Fauziyan ta sauke, duk da cewar taji mamakin maganan k’warai, amma kuma taji sanyi acikin zuciyarta.

Numfashi ta d’anja tare da Kallon Salman din, cikin sanyin yanayi tace.

“To wannan al’amarin da d’aure kai yake gaskiya, amma kuma shi yaron da aka aura mata d’in tana sonshi ne, ko kuma shi yana sonta?�

Kai Salman din ya girgiza, kana asanyaye yace.

“Agaskiya kuma wannan ne bansani ba Aunty.�

D’anjim Aunty Fauziyan tayi, na y’an wasu dak’ik’u kuma tace.

“Kayi hakuri Salman, agaskiya ada nayi tunanin duk abunda zaka fadamin zan rufeshi, amma kuma sai gashi yanzu, naji ajikina tamkar akwai wata rawa da zan iya takawa, akan wannan al’amarin, lalle dole zan san yadda zanyi naga Jannart, muje wajen MD.�

Ta k’are maganan tana me mik’ewa tsaye.

Hakan yasa Salman rufa mata baya, kaitsaye suka nufi ofishin MD.

Koda sukaje Aunty Fauziyan ce ta kawo masa maganan Jannart, tare da nuna b’uk’atar ta nason Ganin Jannart din.

Jin buk’atar tasu ce kuma yasa MD jinjina kansa, cikin kokonton hakan yace.

“Agaskiya inajin kamar hakan bazaiyiwu ba Fauziya, saboda maganan nan sirrice da ba’aso kowa ya sani, nima kaina ba’a gayamin Dan matsayina ko wani abuba, a'a kawai dai angaya minne saboda, kada Jannart din ta rasa aikinta anan gaba, haka ma Kai Salman kasan dalilin da yasa aka gaya maka, saidai ba damuwa bari mu jarraba, zan k’ira Barrister Kabir din muji.�

Ya k’are maganan yana d’aukan wayarsa.

Aunty Fauziya kuwa murmushi tayi, tare dayi masa godiya.

Shikuwa MD’n kiran numbern Barrister Kabir yayi, cikin sa’a kuwa ya samu Barrister Kabir din ya d’aga wayan.

Bayan sun gaisa ne kuma yake shigar da buk’atar Aunty Fauziyan awajen Barrister’n.

D’an Jim Barrister Kabir yayi, cikin d’an nazari kuma yace.

“To shikenan MD, amma kana ga kayarda da matar kuwa, kana ga sirrinmu bazai fita awajenta ba.�
Yayi mgnar murya a sake dan yanzu ko mgnar ta fita yana da ɗan yaƙini fito na fito da magautanta sai dai baida cikekkun hujja.

“Sosai kuwa Barrister, saboda Fauziya D Sulaiman macece mai amana, karanci, tausayi, da saukin kai, kuma akwai rawar da zata iya takawa, musamman Kodan wajen bawa, Jannart din shawarwari ma.�

MD din ya fad’a.

Jin hakanne kuma yasa Barrister Kabir cewa.

“Badamuwa bari na turo muku numbern, amma ko Salman ban yarda a bashi numbern ba, ita matar kawai za’a bawa.�

“To Insha Allah.�
MD din ya fad’a.

Nan ya katse wayar, da kaman minti d’aya kuwa sai ga, text na numbern Jannart din ya shigo cikin wayar MD.

Take kuwa MD ya tura mata numbern.

Godiya Aunty Fauziyan tayi masa, cikin jin dadi kuma ta juya ta tafi.

Haka dai Rayuwa ta ci gaba, inda yau ansamu k’arin kwanaki, akan wata d’ayan daya shud’e.

Alhamdulillah kuma abubuwa duk, suna tafiya yanda ya kamata, musamman a b’angaren Rayyern, wanda ayanzu kusan kullum Idan ya fita, baya dawowa sai dare, saboda yakanje asibiti da company, shiyasa gaba d’aya ma ko isashshen zama baya samu.

Ab’angaren Jannart kuwa rayuwarta take normal, saboda ayanzu ta gama sabo da duk y’an gidan, Masha Allah komai yana tafiya mata daidai sai dai time to time tana tuno gidansu har tayi kwalla.

Acan tashar tasu kuwa, yau din Aunty Fauziyan ce zaune, acikin office dinta, wayarta ce kuma ke rike ahannunta.

Gaba daya ta shiga cikin nazarin kiran wayan Jannart, saboda yanda take kokonto akan ta kira ne ko a’a.

Ayau dai kam ta yanke shawarar kiran wayan Jannart din.

Acan gidansu Rayyern kuwa, yau Nasir yazo, hakan yasa suka had’u shida Riyyam nsra da kuma Ramadan.

Gaba d’ayansu afalon saman suka zauna, haka duk suka cika musu gidan da sowa, saboda Kallon wasan k’wallo da sukeyi.

Wanda kuma sun samu freedom din nasu ne, saboda ganin Rayyern baya nan.

Ciye ciye kuwa ba kalan wanda ba suyi ba, bayan pizza da shawarman da sukaci, hatta sweet saida suka sha, anan kuma cikin falon suka zubar da ledodin musamman Nasir shima dan masifan son zaƙine, haka kuma duk wasu pillows dake jikin kujerun falon, saida suka watsar dasu sukayi musu d’add’aya.

Bayan sun gama abunda za suyi ne kuma suka fice, batare da sun gyara falon ba.

Rayyern kuwa yaudin ad’an gajiye ya dawo gidan.

Wanda hakanne ma yasa bainemi su Mamy ba, kaitsaye ya wuce saman.

Saidai yana shiga, abunda ya gani ya sashi d’an zaro idanunsa.

“What is this?�

Ya fad’a yana me Kallon yanda falon nasu ya haukace.

Saurin Ajiye briefcase d’insa yayi, tare da juyawa cikin sauri ya koma, domin yasan hakan ba aikin kowa bane, saina su Ramadan da Riyyam-nsra.

“Mamy Mamy!!�

Da k’arfi yake d’an k’wala k’iran sunan Mamyn, yana me saukowa daga kan steps din.

Mamy kuwa jin kiran da Rayyern din keyi mata ne, yasa ta d’an lek’owa daga kitchine tare da cewa.

“Lafiya kuwa Rayyern?�

Fuskarsa ya d’an kwab’e tare dasa hannu, ya kama waist d’insa, cike kuma da takaici yace.

“Mamy Ina su Ramadan, kinga yanda suka yi min kaca kaca da falo kuwa? sunb’ata min komai, sunyi ciye ciye sunbar duk wani datti awajen, Mamy wallahi ki kirasu suzo su share.�

Ajiyar zuciya Mamyn ta sauk’e, tare kuma da komawa ta zauna, tana me cewa.

“Nifa banmasan da yaushe suka fita ba, nasan dai d’azun sunanan harma da Nasir, amma yanzu kam da ‘alama basa ma cikin gidannan.�

Fuskarsa ya sake kwab’ewa, still cikin kame k’ugu yace.

“Gaskiya ni Mamy azo agyaramin, sun b’ata komai ko wajen da mutum zaibi mai tsabta babu.�

Murmushi Mamy tayi saboda sanin halin rigima, irin nasa da tayi ne kuma yasa, ta kalli Jannart da yanzu fitowarta, cikin dan tausasawa tace.

“Dan Allah Jannart jeki gyara masa falon, nikam aiki nakeyi a kitchine, Idan ba haka ba wannan da kike gani bazai barmu ba, ya tamana kwarnafi kenan kaman mu muka b’ata.�

“To.�
Jannart din tace tare da sunkuyar da kanta k’asa, kana anutse ta haura saman.

Shikuwa Rayyern sauka falon kasan yayi ya zauna.

Koda ta haura kuwa Anutse ta soma tattare falon, cikin mintuna kad’an kuma ta kammala, air freshener ta fesa tare da jawo kofar ta rufe.

Kana anutse ta sauk’o k’asa.

Tun fara sauk’owanta daga kan steps kuwa ya tsurawa, kyawawan k’afafunta ido, musamman yanda ta d’an tattare sket dinta, hakan yasa yake iya hango kyawawan singalalinta.

Itakuwa Jannart Anutse ta k’arasa sauk’owa k’asan.

“Yunwa nakeji.�

Ya fad’a still bai d’auke idanunsa daga kan kafarta ba dan yana tsoron kallon samanta gani yake zata tsole mishi ido da waɗannan abubuwan nata saukinta ɗaya bata rabuwa da mayafi.

Kai kawai ta jinjina masa, alaman to, kana cikin nutsuwa ta nufi kitchine.

Fried rice and coleslaw da kuma tamarin juice ta kawo masa, Anutse ta ajiye abincin agabansa, daidai lokacin kuma wayarta dake aje gefensa, ya soma tsuwa alaman shigowar kira.

Saurin d’agowa tayi tare dakai dubanta, ga screen din wayar, Ganin new number’n dake kiranta ne kuma, yasa duk ta cika da mamaki, Ahankali kuma ta dawo da kallonta garesa, wanda shidin ma kuma idanu ya zuba mata.

Sake Kallon wayartata tayi, cike da mamaki.

Shikuwa Rayyern fuska ya tab’e, cikin kuma halin ko inkula yace.

“Kima daina wani pretending ki daga, ki fada musu cewar na warke, domin basu samu yanda suke soba, ban mutu ba.�

Idanunta ta d’an zuba mishi, cike da mamakin kalaman nasa, da yakeyi wanda akullum bata fahimta, batasan me hakan yake nufi ba, shin wai baiyarda da ita bane ko kuwa, yana ga kamar cutar dashi zatayi.

Kanta kawai ta girgiza tare da d’aukan wayan nata, Ahankali ta sakala wayar akan kunnenta, saidai batayi gangancin fara magana ba.

Daga can b’angaren Aunty Fauziya kuwa, Jin an d’aga wayar ne yasa ta yin sallama.

Aikuwa take Jannart ta d’auko muryar, lokaci guda cikin mamaki da farinciki tace.

“Laa My Aunty kece?�

“Eh nice Jannart, ya kike ya kwana biyu.�
Aunty Fauziyan ta tambaya tana murmushi.

Cike dajin dadi Jannart din tace.

“Lafiya kalau my Aunty, wallahi nayi kewarki a ina kika samu number na.�

“Nima haka Jannart, numbern ki kuma Abbanki ne ya bani.�

Aunty Fauziyan ta fad’a cikin kulawa, tare kuma da cewa.

“Fatan kuna lafiya ya maigidanki?�

D’an juyowa Jannart din tayi ta kalleshi, wanda kuma shidinma kuma ita yake kallo.

Saurin juyar da kanta tayi, kana cikin sanyi yace.

“Lafiyanshi k’alau.�

“Masha Allah, Kodai yana kusa ne naji muryarki k’asa k’asa.

“Uhummm.�
Jannart din ta amsa tana dan Murmushi.

Jin hakanne kuma yasa Aunty Fauziyan cewa.

“Shikenan Jannart muyi waya anjima, yanzu bari na barki kiji dashi.�

Tana gama fadin hakan kuwa ta katse kiran.

Jannart kuwa batare da ta sake juyowa ta kalleshi ba kaitsaye ta wuce d’akinta.

Shikuwa Rayyern bayan ya gama cin abincin ne ya tashi ya haura sama.

To ahaka dai rayuwa taci gaba da tafiyar musu, bayan 5 weeks kuma abubuwa duk sun sanja, yanayin gari da kuma weather ya juya izuwa, yanayin zafi, domin zuwa yanzu har anfara iska da kuma hadari dake nuna shigar yanayin farko-forkon damuna.

Kamar yadda yayi kwanaki shida baya, yau din ma tun bayan sallan la’asar, misalin biyar saura.
Gaba ɗaya garin ya game da hadari, bak’ikk’irin daga gefen gabas kowa ya daga ido ya kalli hadarin sai ya razana, sabida yadda yayi gangami yayi duhu. saidai kuma cikin dan wani lokaci hadarin ya fara komawa ja, da dukkan alamu kuma, iskane mai k’arfi yake kokarin tashi irin na forkon damuna.

A cikin compound din gidan nasu kuwa, Abba ne da Baba MauÉ—o ke zaune, suna nan zaunen ne kuma suka hango Rayyern wanda ya fito, Cikin nutsuwa yake tafiya.
Yana mai daga kanshi yana kallon saman gidan nasu tare da zazzagaye kowani lungu da sak’o na gidan.

Baba MauÉ—o kuwa binshi da ido yake yana wani irin murmushi mai cike da jin daÉ—in.

Idanu Abban ya dan lumshe tare da jingine kanshi da jikin bango.
Cikin yanayin nazarta yace.

“Hmmm gado ba karambani ba, komai na daga cikin d’abi’ar mahaifinshi bai bari ba.�

Shikuwa Rayyern dake ta faman zazzagaye gidan, yanayin hakanne saboda sunnah ce da Manzon Allah (S.A.W) ya keyi, Idan yaga hadari Yakan zazzagaye gidansa, Dan dudduba abubuwa abinda ke bukatar gyara ya gyara na killacewa a killace.

Yana cikin zagayen ne kuma wayarsa dake cikin aljihunsa ta soma kara.

Koda ya duba, ganin sunan sunan Dr. Sulaiman ne ya sashi d’agawa.

Bayan sun gaisane kuma Dr. Sulaiman din yace.

“Dr batun tafiya Mascow fa, komai ya riga daya Kankama, Insha Allah nanda 2 to 3 weeks masu tafiya zasu tafi.�

“Okay.�
Kawai Rayyern din yace atakaice tare kuma da katse kiran.
Sabida iskar ta fara saukowa,
Ci gaba yayi da zagaye wajen, harta side din su Baba Maud’o kuwa saida yaje ya duba, Ganin komai normal ne yasashi dawowa cikin gida.

Wanda zuwa lokacin kuwa iskan ya taso gadan gadan.

Lokacinne kuma Abban shima ya shigo, tare da neman waje ya zauna.

Baba MauÉ—o Kuma ya shiga side É—insu

Rayyern din kuwa windows din dake abude ya rurrufe.

Yayinda Abba kuwa ya zuba masa ido, adai-dai lokacin kuwa shi kadai yasan me yake rayawa acikin zuciyarsa da kuma abinda yake tinawa

Rayyern kuwa Bayan ya gama rurrufe ko inane, idanunsa suka sauk’a akan k’ofar falon Jannart, da iska ke bud’eshi yana rufewa shi gib da karfi.

Juyawa yayi kamar zai haura sama kuma sai ya fasa ganin Abba nata kallon shi sai kuma ya kalli wannan kofar.
Anutse ya nufi kofar tata, Koda ya isa hannunsa yasa ya tura k’ofar, tare kuma dasa kansa acikin falon, yayi hakanne kuma saboda nan ne kadai falon daya rage da bai duba ba.

Ahankali ya sauk’e idanunsa akan Jannart Wacce ke zaune akan kujera.

Sanye take cikin wata riga Marar nauyi, wanda tayi mata kyau sosai, ga kuma gashin kanta dake watse dan ko d’ankwali bata dashi.

Idanunta da hankalinta kuwa, duk yana ga tv inda take Kallon wani cartoon mai abin dariya.

Idanunsa ya d’an janye daga kallonta, had’e dajan d’an guntun tsaki, kaitsaye kuma ya wuce dan rurrufe windunan falon.

Sautin tsakin nasa ne kuma yasa Hankalin Jannart dawowa kansa, da sauri ta juyo, ganinsa da tayi ne kuma yasa ta, saurin tashi ta gyara zamanta.

Saidai kuma gaba daya babu mayafi akusa da ita, hakan yasa ta d’an takure jikinta waje daya.

Shikuwa Rayyern ci gaba da rufe windows din yayi har ya juya ya fuskanci tsakiyar falon.
Sai kuma ya É—an juyo kansa ya kalli bayanshi ganin yadda labuyen suka a harde alamun iskane ya hardesu, ba tare daya juya ba.
Ahankali kuma ya dan Mika tsawonsa, dan son gyara labulen daya hard’e asama sabida iskar sosai ya daga hannunsa sabida windows din sunada tsawo sosai.

Hakan kuwa shi yasa rigarsa ta d’age ta ɗanyi sama.
Daga cibiyarsa zuwa kasa suka bayyana,
Dai-dai lokacin kuwa Jannart ta sauk’e Idanunta akan shatin, saman mararsa kasan cibiyarsa da kuma black boxer din dake jikinsa.

Wanda ya kara haska farar fatarsa.

Idanunta ta zubawa wajen, bata ko k’yaftawa, saboda yanda shatin marar tasa ya bayyana sosai, ga kuma hasken da wajen ke dashi kana ga wani tattausan gargasa dake kwance daga ƙasan cibiyar tasa har zuwa ƙasa sosai inda robar boxes dinsa ke manne da jikinsa har ana iya ɗan hango saman mararsa kana asalin dogon wondon kuma yayi ƙasa sosai kan mazauna sa wanda haka yasa shatin surar jikinsa bayyana.

Wani irin rawa takejin jikinta da idanunta sunayi.
Yayinda gaba ɗaya tsikar jikinta ke mimmiƙewa tsaye.
Wani irin harbawa zuciyarta keyi mai tafe da tsoron abinda idonta bai taɓa katari dashiba.

Rayyern kuwa kanshi na sama, baima san tana kallonshi ba.
Saida ya gama warware labulen.
ahankali ya d’an sauk’e hannunsa sama, tare da juyowa ya sauk’e idanunsa akanta da sauri ya sunkuyo ya kalli setin inda take kallo a jikinsa.

Fuskarsa ya tsuke tare da tab’ewa kana ya watsa mata wata Zazzafar hararanta cikin takaici yace.

“Meye? Mayya kawai cinyeni zakiyi ne?�

Da sauri ta kauda idanunta tayi daga garesa, tare da mikewa tsaye ta d’auki wayarta yayinda wata azabebbiyar kunya ta rufeta.

Ahankali ta dan Raba zata wuce zuwa daki.

Shikuwa Rayyern cikin tsautsayi, labulen da yake gyarawan ya ture wani goran ruwa dake gefe, hakan kuwa shi yasa ruwan ya malale awajen.

Juyawa shidinma yayi da niyar fita, dai-dai lokacin kuma Jannart ta iso sukayi gab da gab, batare da sun Ankara ba kuwa, saiji yayi gaba daya tsantsi ya debe sa Suuuuuu haka ya tafi idanunsa ya zaro, tare kuma da fad’awa kan Jannart, wani irin masifeffen tsorone da fargaba ya rufeta wanda yasata rumtse idanunta jin sun tafi suuuu sun f...!!!

*GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.

Dan Allah masu son kaya in dai kin san baki shiryaba baki da kudi a ƙasa ki huyar dani da kanki kasa kimin mgn.

GARKUWAR MA'AURATA

By
*GARKUWAR FULANI.*
22/12/2021, 19:45 - 🥰🥰: Matar da hoton fuskarta ya cika fuskar wayar.

Wani irin harbawa yaji zuciyarsa tayi da karfi, wanda har saida hakan yasa shi zaro idanunsa waje.

Da matukar mamaki yake Kallon fuskar matar, Wacce bata da wata maraba da fuskar Ramadan, domin kuwa tsananin kaman Ramadan daya hango akan fuskarta ne ma, ya sanyashi jin wani irin bugun zuciya.

Lokaci daya kuma yaji wani irin nauyi, da kuma dattakun matar ya cika idanunsa, Yayinda daga cikin zuciyarsa kuwa, wani irin girma, kima, karamci, martaba da kuma haibar matar ne ke hauhawa cikin duk harbawar da zuciyarsa keyi.

Ganin fuskar matar ne kuma yasa, kowanne kofar gashi dake jikinsa budewa, take yaji wani irin sanyi na ratsa shi tako Ina, Yayinda kuma nutsuwa ke kara saukar masa.

“Mammy Ina kwana!!�
Ya fad’a cikin tausasa murya daga can cikin maƙoshinsa har zuwa kan labbansa.

Daga b’angaren Mammy kuwa da ta tsura masa ido bata ko k’yaftawa, wani irin abu itama takeji acikin zuciya da gangar jikinta, lokaci daya kuma taji zuciyarta tayi rauni sosai, tabbas Kallon fuskar Rayyern din da tayi ayanzu, yana tattare da wasu abubuwa da dama, ciki kuwa harda abunda ke kwance acikin zuciyarta, a mafi rinjayen tsawon shekarun rayuwarta.

“Lafiya Maud’ona ya jikin ka?�

Mammyn ta tambaya cikin boye rauni, da kuma damuwar dake kwance akan fuskarta yace.

“Alhamdulillah jiki na yayi sauki Mammy.�

Rayyern din ya bata amsa, cikin sanyi da kuma sigar tausasawa.

Riyyam-nsra kuwa dake zaune agefe idanu ya zubawa, Hamma Rayyern din nasa.

Mammy kuwa Daga can b’angaren ta, murmushi ne ya dan bayyana akan fuskarta, cikin tsananin kulawa da kuma muryar tausayawa tace.

“Allah Ubangiji ya karamaka lafiya, ya kareka aduk inda kake, ya tsare gabanka da bayanka, ya kuma nisanta ku da duk wani sharrin mutum da aljan, Allah ya baku zaman lafiya kaida iyalinka, ya albarkaci rayuwarku ya cika haske a rayuwarku Allah yayi maka al'barka!!!.�

“Ameen thumma Ameen Mammy nagode sosai.�

Rayyern din ya fada cikin nuna tsananin jin da d’insa, domin kowacce kalma da Mammyn zata fad’a, jinsa yake yana tasiri acikin zuciyarsa, Yayinda kuma yakejin wani irin farinciki na musamman yana lullub’eshi.

Mammyn ma Ganin farinciki kwance akan fuskarsa ne yasa ta jin dadi aranta, cikin kuma sakin fuska tace.

“Ya Ramadan da Mamyn ku?�

“Lafiyansu kalau Mammy, saidai Ramadan ya tafi wajen aiki, Mamy kuma tana k’asa.�

Ya bawa Mammyn amsa asake, yana mejin Karin nutsuwa na saukar masa sabida mgnar da yakeyi da itan.

“Masha Allah Allah ya taimaka, Ina Surukata Jannart, fatan itama tana lafiya.�

Mammyn ta tambaya da kulawa.

Idanunsa ya d’an lumshe tare kuma da bud’e su alokaci guda, cikin kwarin jikin daya samu yace.

“Lafiya yanzu ta sauk’a k’asa.�

Murmushi Mammy tayi, tare da jinjina kai, cikin farincikin dake da d’a mamaye zuciyarta duk bayan minti guda tace.

“To bari na bawa Zaytoon ku gaisa, gatanan duk ta tsareni da ido.�

Murmushi Rayyern din yayi dai-dai lokacin kuma, Mammyn ta mikawa Zaytoon dake gefen ta wayar.

Karb’an wayar Zayton tayi, tare da fadada fari’ar dake kan fuskarta, cikin muryarta mai dan sanyi tace.

“Hamma Rayyern.�

Saurin d’ago idanunsa yayi, ya kalli kyakkyawar yarinyar da ke magana acikin wayar, wanda muryarta tayi masa sak da wata muryar da yaji kwanannan , idanunsa ya Dan bud’e da kyau, tare kuma da zaro su waje, badon komai ba kuwa saidan Ganin still kamanin yarinyar sak na Ramadan ga kuma kamannin muryarta da waccar tsohuwar kamar dai yadda kamannin Muryar Ramadan Riyyam-nsra da ita Zayton ɗin a can wani sashin na zuciyarshi kuwa kamarsa da Riyyam-nsra ne ya fado masa “Yah salam�.
Yace a ransa a zahiri kuwa,
Idanu ya dan zubawa yarinyar, har na tsawon minti daya, kafun daga bisani ya fadada fara’ar dake kan fuskarsa, cikin sakewa yace.

“Na’am Zayton.�

Murmushi Zayton din tayi, kana cikin jin dadi tace.

“Sannu Hamma Rayyern ya jikinka, Ina fatan dai kayi sauki sosai, kuma kana cin abinci sosai ko?.�

Wani irin Murmushi Rayyern din yayi, wanda har saida kyawawan hakoransa suka bayyana, tashin farko yaji matashiyar budurwar tashiga ransa sosai.

“Jikina da sauki sosai Zaytoon, amma banason Ina yawan cin abinci saboda kada na zama ɗan lukuti kamarki.�

Dariya sosai Zaytoon ta kwashe dashi, saboda daga jin yanda yayi maganar ma kasan akwai tsokana aciki.

“Haba Hamma Rayyern ni har wani jiki ne dani, kanaga saboda banida jiki ne ma ai, Riyyam ya rainani, Hamma Rayyern Ina Auntyna Jannart take?�

Zaytoon din ta tambaya, cike da kulawa.

Murmushi yayi tare da d’an shafa lallausan sumar kansa, cikin muryar tausasawa yace.

“Tana k’asa.�

Kai Zaytoon din ta jinjina, tare kuma da dan rausayar dakai, cikin nuna kulawarta agaresa tace.

“To ka gaishemin da ita kaji, sannan please Hamma Rayyern kana kulawa da kanka kaji, Allah Ya baka lafiya mai amfani.�

Idanunsa ya d’an lumshe tare kuma da sauke Ajiyar zuciya, saboda sosai yaji dadin addu’ar da yarinyar ta masa kana har cikin ransa yake jin sonta a ransa.

Wanda har hakan yasa shi cewa.

“Ameen nagode Zaytoon.�

Kai Zaytoon din ta jinjina, Yayinda shikuwa Rayyern ya mikawa Riyyam nsra dake zaune agefe wayan.

Da sauri Riyyam da zuciyarsa ke cike da farinciki ya karb’i wayan tare da fuskantar screen din wayar, cikin kula dajin dadi yace.

“Mammyna yau kam kinga Hamma Rayyern dinmu ko.�

Kai Mammyn ta jinjina, cike da jin dadi tace.

“Kwarai kuwa Riyyam yau kam naga Rayyern.�

Tayi maganan cikin kasa da murya, ta yanda Riyyam dinne kadai zai iya Jiyota.

Jin abunda ta fada dinne kuma yasa Riyyam nsra tashi, rike da wayan a hannunsa kaitsaye ya nufi dakin Ramadan.

Shikuwa Rayyern maida kansa jikin kujera yayi, tare da lumshe idanunsa, ahankali yake lumshe idanunsa, yana mejin wani irin nutsuwa na saukar masa.

Mammy da Riyyam kuwa basu wani jima suna magana ba, Mammy ta katse kiran.

Acan Ethiopia kuwa bayan Mammy ta ajiye wayanne, Ta zame daga zaunen da take tare da durk’usawa k’asa tayi sujjada.
Na nunawa Allah tsananin jin dadinta, da kuma godiya agaresa, domin komai da yake faruwa shine ya tsarashi, shine kuma yake bawa ahalinta dama ita kanta kariya akoda yaushe.

Acan b’angaren Jannart kuwa Anutse ta kammala gasa masa roasted fish, tare da matsa masa ruwan lemon tsami aciki, kamar yanda ya gaya mata yana buk’atar abu mai d’an tsami tsami, bayan ta kammala had’a masa roasted fish dinne kuma, ta soma kokarin yi masa miyan kase kamar yanda ya buk’ata, saidai kuma kasancewar miyar tana daukan lokaci sosai, shiyasa gama ta ba yanzu yanzu ba.

Rayyern dake zaune afalo kuwa, Ganin almost 1hour ya kare ba akowa masa abincin nasa bane, yasa shi haurawa saman sofa ya kwanta.

Ahankali yake lullumshe idanuwansa, wanda da’alama kuma bacci yakeji, duk da cewar kuma yana jin yunwa, amma hakan baisa baccin yaki daukarsa ba.

Domin yana nan akwance cikin abunda bai wuce 20mn ba, bacci ya d’aukesa, kasancewar acikin magungunan da yake sha akwai mai dan saka yawan bacci.

2hours later.

Ahankali yake bude idanunsa, wanda suka shafe sama da awa biyu a kulle.

Mik’a ya d’anyi ahankali tare da ambaton sunan Allah acikin zuciyarsa.

Ahankali ya dan tashi zaune, tare dasa hannu ya shafa kan lafaffen cikinsa, da keyi masa kukan yunwa.

Numfashi ya d’an fesar akasalance kuma, yakai dubansa izuwa babban agogon dake cikin falon.

1:25 pm dai-dai agogon ya nuna masa, wanda hakan ya sashi d’an yunk’urawa ya mike.
Musamman saboda ganin da yayi lokacin sallah yayi.

Hannayensa ya zura acikin aljihun wandon dake jikinsa, kaitsaye kuma cikin tafiyar, dake nuna ya Dan samu karfin jikinsa ya nufi bedroom d’insa.

Koda ya shiga cikin bedroom din Anutse, ya soma kokarin rage kayan dake jikinsa.

Bayan ya cire trouser’n dake jikinsa ne kuma, ya d’auko wani towel ya d’aura akan waist d’insa.

Direct toilet ya wuce, inda ya had’ewa kansa ruwan wanka mai d’an d’umi.

Anutse yayi wankan nasa tare da d’auro alwala ya fito.

Koda ya fito daga toilet din kuwa wani irin kamshin shower jel ne ke tashi ajikinsa, Yayinda kuma tausassun gashin jikinsa suka kwanta lub.

K’awataccen sajen dake kwance akan fuskarsa kuwa, shek’i take tayi saboda danshin ruwa dake jikinta.

K’arasawa gaban mirror yayi, tare da d’aukan mini towel ya shiga goge ruwan dake jikinsa.
Komai nasa da nutsuwa yakeyinsa.
Hakan yasa duk wanda zai kallesa sai yaji ya burgesa.

Had’add’en body lotion d’insa ya shafa, sai kuma turaren companyn Gucci daya shafa ajikinsa.

K’arasawa gaban drawern d’insa yayi, inda ya ciro wani riga da wandon companyn Ouchpan masu kyau da taushi.

Rigar irin long sleeve d’innan ne, sai kuma wandon daya kasance tight, Wato mai dan kama jiki, amma kuma irin jeans dinnan ne, masu yanayi da crazy.

Anutse ya zura kayan ajikinsa, tare da d’aukan wasu simple shoe ya zura akafafunsa.

Masha Allah! Ba k’aramin kyau kayan sukayi masa ba, kasancewar su black colour kuma shiyasa suka k’ara bayyana, hasken da fatarsa ta k’ara.

Ahankali ya d’an ciji jajayen labb’ansa, tare kuma dasa hannunsa ya shafa cikinsa dake kukan yunwa.

Fuskarsa ya d’an kwab’e tare da karyar da wuyansa gefe, Allah ya sani yunwa yakeji sosai.
Domin har wani jiri jiri yakeji.

Wayarsa dake kan gado ya d’auka, tare kuma da nufan falon nashi kaitsaye.

Koda ya fito idanunsa ya sauk’e akan dining table din dake cikin falon, saidai kuma rashin ganin an ajiye masa abunda zaici ne yasa shi b’ata fuska, tare da d’an rausayar da idanunsa, cike da kasala da kuma yunwa ya nufo main falon nasu kaitsaye.

Acan b’angaren Jannart kuwa bata jima da kammala had’a abincin ba, kasancewar kuma garin ana d’an yanayin zafi shiyasa, Koda ta kammala had’a abincin a tray, kaitsaye part dinta ta koma.

Wanka tayi da sabulun beauty touch, wanda yasa gaba daya jikinta ya d’au sassanyan k’amshin sabulun.

Bayan ta fito daga wankanne kuma ta shirya kanta, cikin wani had’add’en English wear gown, wanda kwata kwata bashi da nauyi, kasancewar kuma rigar tight gown ne shiyasa ya bayyana duk wani shape din jikinta.
Harta kan nipples dinta kuwa saida ya bayyana, sosai rigar tayi mata kyau, tare da k’ara bayyana tsararren surar jikinta.

Turaren oud mai kamshin gaske ta shafa ajikinta, bayan ta tubke dogon gashin kanta, wanda yasha kitson da Mamy tayi mata ne kuma, ta yafa wani mayafi mai kauri ajikinta, daya rufe duk wani shape dinta, tayi hakanne kuma saboda sanin da tayi cewa, akwai maza agidan.

Juyawa tayi Ahankali kuma Cikin nutsuwa ta fice daga cikin dakin.
Kaitsaye kitchine ta nufa, dan daukan abincin da ta dafa din.

Rayyern kuwa Ahankali yake saukowa daga matattakalan steps din.

Cikin nutsuwa da kuma d’aukar hankali yakeyin kowanne takunsa.

Ahaka yake saukowa daga kan steps din.
Hannunsa daure akan cikinsa, yana shafawa tare da d’an lumshe idanunsa.

“Mamy Mamy!!�
Sunan Mamy yake kira ahankali, cikin kuma muryarsa da tayi sanyi sosai, saboda rashin k’arfi da kuma yunwan da yake fama dashi.

Adai-dai lokacin kuwa Jannart ta k’araso tsakiyan falon, Jin kamar muryar mutum ne kuma yasa ta d’aga kanta, karab kuwa Idanunta suka sauk’a akansa.

Kyawawan Idanunta ta d’an zuba masa, tare da soma Kallon shigar dake jikinsa, Wacce tayi masa kyau sosai.

Dai-dai lokacin kuma shima ya sauk’e idanunsa akanta.

Ahankali ya zame tare da zama akan steps din karshe dake kan matattakalan, idanunsa ya d’an lumshe tare dasa hannu ya dafe cikinsa, wani irin numfashi yake sauk’ewa mai d’auke da gajiya, cikin sanyin muryar dake nuna gajiyawarsa ya k’wala kiran sunan Mamy.

“Mamy tana d’akinta.�
Jannart din ta bashi amsa, tare kuma da d’auke Idanunta daga kallonsa.

Idanunsa dake alumshe ya d’an bud’e, tare da k’ara d’aura hannunsa akan cikinsa.
Wanda yayi Dan ƙugin yunwa, har saida Jannart din ta jiyo sautin.

D’an kallonsa tayi, gaba daya duk ya marairaice, ya wani zama abun tausayi, da dukkan alama Yunwa ce ke wahalar dashi.

“Meye kike wani kallona haka kamar zaki cinyeni, ni yunwa nakeji.�
Rayyern din ya fad’a yana me sauke mayun idanunsa akanta.

Wanda kuma hakanne yasa tayi saurin dauke Idanunta daga kallonsa.

Batare kuma da tace masa komai ba ta juya, Cikin nutsuwa ta wuce kitchine.

Da idanu yabi bayanta, har saida yaga wucewarta cikin kitchine din kafun ya tashi ya dawo cikin falon.

Jannart kuwa tray da plates ta d’auko, tare da dawowa falon.

Ahankali ta sunkuya dai-dai zata ajiye tray din agabansa ne kuma, mayafin dake jikinta ya zame ya fad’i.

Saurin ajiye tray din tayi tare da juyawa da sauri dan daukar gyalen nata.

Juyawan da zatayi dinne kuma yasa, Rayyern din sauke Idanunsa akanta.

Ganin inda idanun nasa suka sauk’ane kuma, ya sashi saurin rumtse su, tare kuma da kawar da kansa gefe sabida gani yayi tamkar nimples ɗin ta zasu tsole mishi ido, kasan cewar batasa bra ba yasa breast ɗinta ke tsaye kam nimples ɗin sunyi tsaye cur motsin da take yasa duk ƙirjinta rausayawa kara rumtse idanunshi yayi sabida ganin abin da yakeyi duk da ya rufe idon.

Itakuwa Jannart cikin sauri ta d’auki mayafin nata ta yafa.
Saboda kunyan da taji ya lullub’eta ne kuma yasa ta kasa d’ago kanta ta kalleshi.

Ahankali ta bud’e food flasks din, roasted fish din ta zuba masa, sai kuma miyar kasen shima da ta zuba masa shi, awani plate na daban dasa mishi tuwo kwaya ɗaya.

“Gashi.�
Ta fad’a cikin wata irin sassanyar murya, still batare kuma da ta d’ago ta kalleshi ba.

Akasalance ya d’ago kansa, tare da mik’a hannayensa alaman ta basa plate din.

Sai Alokacinne kuma ta d’ago Kai ta kalleshi, kasancewar kuma tana d’an nesa dashi ne, yasa dole saida ta matsa gab dashi.

Ahankali ta d’an ajiye guiwowinta akan tattausan carpet din dake malale atsakiyar falon.

Hannayenta duka biyu ta sanya wajen Ganin ta mik’a masa plate din.

Ak’ok’arinta nayin hakanne kuma, batare da duk sun Ankara ba, Rayyern din yasanya hannunsa ta k’asa zai karb’i plate din, hakanne kuwa yasa shi sauk’e tafukan hannayensa, akan lallausan fatar hannayenta, masu tsananin taushi tamkar auduga.

Wani irin abu Jannart taji acikin jikinta, wanda har hakan yasa tsikar jikinta mimmik’ewa, lokaci daya kuma gyalen ta ya zame zuwa kan kafad’unta, hakan yasa lallausar sumar kanta ya bayyana.

Idanunsa ya d’an zubawa gashin kan nata, Yayinda ita kuwa ahankali ta zame hannunta daga cikin nasa tare da sanya hannu ta jawo gyalen zuwa kanta.

Dai-dai lokacin ne kuma Mamy ta fito daga d’akinta.

Ganin Rayyern da Jannart din atare ne kuma, ya sakata sakin murmushi Cikin kulawa tace.

“Babana lafiya kuwa Ina sallah naji kana ta rabka min kira.�

D’agowa yayi ya d’an kalli Mamyn, cikin yanayin sigar shagwab’a yace.

“Mamy To ba yunwa nakeji ba.�

Murmushi Mamyn tayi, tare kuma da neman waje ta zauna.
Cikin sakin fuska tace.

“To Rayyern Idan kanajin yunwa, baga matarka ba, komai ita zaka tambaya ba niba, kuma ga abincin ma, Ina naga ankawo ma, Jannart sannu da aiki.�

Mamyn ta fad’a tana Kallon Jannart, da ta janye jikinta daga kusa da Rayyern din.

D’an murmushi tayi, batare kuma da tace komai ba, ta dawo kusa da Mamyn nan k’asan sofa ta zauna.

Shikuwa Rayyern d’an k’aramin bakinsa ya taɓe, kana ashagwab’e cikin kuma yanayinsa na marar lafiya, ya soma cin abincin da Jannart din ta kawo masa.

Tun aloman farko da yayi kuwa, ya lumshe idanunsa, saboda dadi da kuma gardin kifin daya ratsa shi, bugu da kari ga kuma ruwan lemon tsamin da taste d’insa, ya hadu dana kifin sai ya bada wani dandano na daban.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.