A Wani Gida
Reading file: A_WANI_GIDA.txt
Chapter 3 of 6
Part 60 ⏩ 65
Kwance Mama take a dakinta tun bayan fitowar ta daga wajen Malan, zuciyarta se zafi take mata. Wannan wane irin bala'i ne haka? Yanzu Malan yadena kula da yarana kamar yanda yakeyi ada.
Tunda Inne tabar gidan nan soyayyar da Malan yake ma yarana ta fita daga zuciyarshi. Kenan saboda zaman Inne agidan yake son yarana? Meyasa ma nasa yasaki Inne? Gashi yanzu ita ta cigaba ni kuma ina nan kullum se kara tsotsewa nakeyi.
Gaba daya tafiyar Inne daga gidan nan haske ne akan yaranta, ni kuma duhu ne ya mamaye ni da yarana. Shi kanshi Malan yanzu arzikinshi ba kamar da ba. Amma kalli irin motar da Inne take hawa.
Kalli kayan jikinta, gashi ta rike 'ya'yan mijinta tamkar itace ta haifesu. Yaranta sun zamo abin so ga kowa, kansu ya bude yayin da kan nawa yaran ya toshe gaba daya. Duk kokari irin na Farida da Fahad be hana anyi masu repeating ba.
Nida naso ace yaran Inne ne ja baya akaratu, lokacin da zasu fara karatun jami'a yarana sunyi nisa alokacin kuma gashi Malan ya aje aiki. Se gashi kuma anyima yarana repeating, gashi Faisal gwamnati ce take daukar nauyin karatunshi.
Ita kuma Fatima zata riga Farida gamawa, nasan duk sauran kudin Malan akansu ze kashe, tunda zasu rigasu shiga jami'a. Allah na rokeka kasa Farouk shi yaci jami'a, koshi kadai nasamu yayi karatu nasan seya riga Faisal gamawa.
Idan yasamu aiki nasan ze kula da sauran. Hawaye ne suka zubo mata, tabbas maganar Malan gaskiya ce, yanayin Fahad ya dade da canzawa, narasa meke damunshi, gashi yanzu duk abinda na aje se inga andauke, wanda ada ba haka ake mani ba.
Kadde ace Fahad yafara sata? Saurin girgiza kai tayi tana fadin, ina, acikin yarana babu barawo, domin duk dangin mu babu barawo. To kode yafara shaye shaye ne? Kara girgiza kai tayi tana fadin hakan ma baze yuwu ba.
Domin Fahad tun yana karami baya son warin koda sigari ce. To meya samu Fahad? Tabbas nasan akwai sa hannu acikin rayuwarshi, kuma koma wanene senayi maganinshi, kuma daga yau duk abinda za'a kawo na kayan dadi nashi seyafi yawa.
Bazan zauna ina kollo yarona ya lalace ba, duk yayi baki yarame, tabbas kafin ya koma sena ginashi. Hannu tasa ta goge idonta ta tashi tana kwalama Farida kira.
Shigowa tayi tana fadin kai Mama, wannan kira kamar kin makance. Mama tace wato nice ma na makance ko? Dariya Farida tayi tana fadin ai naji kina ta kwala mani kira ne. Mama tace nasan Fatima tana can gidan su Amira.
Jeki dora farar shinkafa idan ta dawo setayi miya. Farida ta turo baki tana fadin lallai ma, ai kin sande itace take aiki taya zakice inje in dora abinci? Mama tace Farida kinga yanzu kin girma, inaso kifara koyon aiki domin wata rana aure zakiyi.
Farida tayi murmushi tana fadin ai kamar kin sani, muna gama makaranta aure zanyi nida kawata. Zaro ido Mama tayi tana kallonta, Farida tace kinsan yanzu samarina nawa? Su 2 ne, damma suna tsoron Malan shiyasa basu taba zuwa gidan nan ba.
Mama tace rufa mani baki, ke yanzu har kinsan maganar aure? To bari kiji in fada maki, yanda kowa zeyi karatu a gidan nan kema sekinyi karatu. Haba Farida, so kike bakin cikinku ya kashe ni? Kina ganin yanzu shima Fahad yadawo baya.
Kema kin koma baya, Farouk ne kawai acikin yarana yagama Secondary, so kuke wadan can yaran su zama wasu manya agidan nan, ga uwarsu ta zama babbar Hajiya, suma suzo suyi kudi, shikenan ni kuma na zama baya kenan.
To kima cire tunanin aure aranki, matukar ina raye se kinyi karatu kamar kowa. Kuma daga yau zan raba maku aiki keda Fatima, idan ma bazaki iya shara da wankin bandaki ba, wannan ba matsala bane.
Nide fatana ki iya girki, sauran ko baki iya ba badamuwa domin akwai masu aiki, amma shi girki kyan mace ta iyashi, idan na dare kikeso to, idan kuma na rana zakiyi duk daya seki zaba.
Farida tace Allah Mama bazanyi ko daya ba, tunda de Fatima takeyi kawai ki barta ta cigaba, Mama tace haba Farida, meyasa bakison farin cikina? Kuka Farida tasa tana fadin ai dama yanzu naga kindena son mu.
Gashi Malan kullum seyayi mana fada, se wadan can kawai yakeso. Kuka sosai Farida tasa tana dire dire. Jawota Mama tayi tana fadin yi hakuri, ni na isa ince bana sonku? Kawai inaso in koya maki girki ne, tunda bakiso shikenan.
Je ki kira mani Fatimar tazo ta dora, share hawayenki, bakida mesonki sama dani. Murmushi Farida tayi tace anjima zanje gidan 'yar makarantarmu daga can zanje ingaishe da Hajiya. Mama tace to jeki kira mani Fatima an jiman seki tafi.
Abinda Mama bata sani ba shine, inde Farida ta tafi wajen 'yar makarantarsu da gidan Hajiya to haduwa takeyi da wani saurayinta Salisu, yana da shagon provison, kuma hade yake da dakin da yake kwana.
Tun wata rana da Farida taje siyen sukari ashagon suka hadu, tun daga nan suke soyayya, kuma Farida tana bala'in son shi, saboda yace ze aureta, ita kuma babu abinda takeso kamar maganar aure.
Sanin halin Malan yasa be taba zuwa gidansu ba, sede tayi dabara taje shagonshi, wani lokacin ma dakinshi suke shigewa suyi fira, sosai Farida ta sake dashi, duk lokacin da taje haka yake gama tabeta ya kawo kudi da kayan zaki ya bata.
Haka take boye kudin tace ma Mama sauran kayan agidan kawarta aka bata. Ta saba da abubuwan da yake mata sosai, hakan yasa duk bayan kwana 2 setaje wajenshi, daga can seta wuce wajen Hajiya dan kada tace bata zuwa.
Kuma sosai Hajiya take jin dadin zuwan da Farida takeyi, har cewa take ita da Fahad sune yan gidanta, domin shima da gidanta yake fakewa yatafi yawon shaye shayenshi.
***** *****
Bayan sun koma makaranta first term, Faisal na SS 3, Fatima da Fahad kuma SS 2, yayinda Farida take SS 1, ba laifi Fahad ya ciko, yayi kiba kuma lokacin da zasu tafi seda Malan ya kara mashi fada sosai akan rashin maida hankalin da bayayi, kuma yace idan har aka kara mashi repeating to ze maidoshi Day.
Haka suka tafi Fahad kamar ze fashe, Mama duk bataji dadin abinda Malan yayi mashi ba, haka ta dauki fushi da Malan dan yanzu haushin shi takeji sosai, duk wata kissar da takeyi ada yanzu babu, abu kadan se fada.
Shi Malan ma dariya take bashi, shiyasa baya biye mata, idan kuma ta kureshi haka zeyi mata tass, dan shima Malan akwai fada, sanin halinshi ne yasa take jin tsoron yi mashi wani abun, koya bata mata rai ma sede ta dauki fushi dashi, idan ta gaji kuma ta sauko.
Yanzu gaba daya Malan ya canza, baya ma yaranshi fada, babu abinda yake fata kamar ya dedeta tsakaninshi dasu Faisal, dan ya dade da gano tsantsar tsanarshi a idanuwansu, sede har yanzu be yarda cewa ba Inne bace ta rabashi da su ba.
Haka sam yadena ma yaran Mama fada, ya kyalesu kamar yanda bataso yana masu. Kuma har yanzu yaki barin su Faisal suje wajen Inne, suma kuma sun dena mashi maganar, domin basu da damuwa tunda suna ganinta, shi kuma Malan ya dauka sun fiddata daga ransu.
Jarabawar su Farouk ta fito, ba laifi yaci, sede be samu English ba, gashi mark dinshi na JAMB be kai ya tafi jami'a ba, kuma duka subject 5 yaci, Math, Biology, Geography, Hausa se islamic.
Sosai Mama taji haushin rashin samun mark din daze tafi jami'a, samun Malan tayi tace abarshi zuwa shekara me zuwa se ya kara sake JAMB din kuma ya nemi English idan yaso seya tafi jami'ar.
Murmushi Malan yayi yace kina da tabbacin shekara mezuwa zeci duka abinda kikace? Mama tace amma de kasan ai Farouk ba jaki bane, duk da banso ya gama karatu tare da kannanshi ba, amma dole inyi hakuri ya sake jarabawa tare da Faisal.
Malan yace to kimayi addu'ar yasamu direct a makarantar dazan samar mashi, domin tunda naga beci JAMB sosai ba na siya mashi form din Isa Kaita Collage Dutsinma yaje yayi N.C.E, kinga yanzu beci English ba.
Kinga kuwa basa bama mutum direct N.C.E se yana da Maths and English, zanje inji idan zasu daukeshi, idan kuma bazasu daukeshi ba sede yayi PRE N.C.E.
Mama kamar zatayi kuka tace kasan Allah, Farouk bazeje wanan makaranta ba, makaranta kamar gidan biki, duk wanda yataso se kaji yace can zeje, gaskiya gara ya hakura yayi zaman shekara guda, zuwa wata shekarar se yasake jarabawa yatafi jami'a.
Tashi Malan yayi yana fadin, idan ke kike da iko dashi zaki iya hanashi tafiya, kuma wallahi iname tabbatar maki matukar Farouk betafi wannan makarantar ba, wallahi bazan kara nema mashi wata ba.
Fita yayi yana masifa. Kwallace ta cika idon Mama, Farouk kuwa da yake tsugunne yayi shiru yana sauraronsu. Mama tace Farouk kana jina ko? Duk yanda Malan zeyi kada ka amince da wannan makarantar.
Idan ka nuna kanajin tsoronshi shikenan an maidaka baya, kai ne babba agidan nan kai yakamata ace anfi daukakawa amma yanzu ace wai waccan banzar makarantar zaka tafi. Ai ko Fahad da kafi kokari bazanso yaje can ba.
Dago kai Farouk yayi yace gaskiya Mama nide zan tafi kawai, koma menene nine na jama kaina, Allah yabani kokari amma na tsaya biyema abokai muna shiririta. Da ace na dage nasan zanci duka jarabawata.
Babu amfanin inzauna jiran wata shekara, domin banida tabbacin zanci jarabawar dazan sake,nide kiyi hakuri kawai zantafi. Hannu tasa ta daukeshi da mari tana huci, hannu Farouk yasa ya dafe kuncinshi.
Mama tace tunda haka kace se kaje katafi, kuma naira 1 tawa bazata kara ciwo akanka ba, tunda yanzu kaima ka koma bayan Malan da wadan can banzayen yaran sekaje kayi tayi,wata rana kai ne zakayi kuka da idon ka.
A lokacin da Fahad da Farida zasu tafi jami'a kai kuma sede ka kare da alli kaga kayo gadon ubanka. Tashi kabani waje. Mikewa Farouk yayi yafita yana kuka. Duk abinda sukeyi Malan yana jiyosu.
Har Farouk yakai kofar gida Malan ya kirashi, sosai yaji tausayinshi, hannunshi yakama suka bar gidan. A cikin mota Malan yace Farouk duk naji yanda kukayi da Mamarku.
Kada kalamanta su tsorata ka, kuma tunda yanzu ka gane kuskurenka inaso kasani lokacin gyara baya kurema mutum har se mutuwa ta riskeshi, kuma kai namiji ne, kayi hakuri da duk abinda ze zo maka arayuwa.
Kada ka dauki wannan karatun da zakayi da wasa, kuma kada ka rai nashi, idan ka dage kayi karatun kana cikinyi ma zaka iya sake jarabawa ka nemi English din, kaga duk lokacin daka gama karatunka ko kana aiki ne zaka iya tafiya ka karo karatunka.
Shi karatu da kake ganinshi ba'a rai nashi komin kan kantarshi, kuma inaso kadage idan kashiga makarantar domin ka gyara kuskurenka, inaso kadawo da kokarinka na da. Farouk yace insha Allah. Malan yace Allah yayi maka albarka. Yace amin.
**** *****
Cikin sa'a Farouk yatafi makaranta inda suka bashi Pre N.C.E ze karanci Biology/Geography, haka Malan ya shiryashi babu abinda be sai mashi ba, Mama kuwa ko sisi bata bashi, da kyar ma tace Allah ya bada sa'a, haka yatafi yafara karatunshi.
Sosai yake maida hankali wajen karatu, kuma yana dinkin hularshi, idan yagama ya kaima Malamai, cikin lokaci guda Malamai suka sanshi dan Farouk ya iya dinka hula, sosai yake ciniki a cikin makaranta har ma da wajen makaranta.
Kuma acikin aji sosai yake dagewa, duk abinda akayi masu baya bacci seya karantashi, gashi yanzu yana son addini sosai, sam baya wasa da sallah.
Wata rana sunje cikin gari shida wani abokinshi Hamza da yamma, yaje siyo kayan dikin hularshi, haka suka taho akasa se sauri sukeyi dan ankusa magriba, da yake ranar asabar ne babu class.
Ta wajen makarantar su Fahad suka biyo dan babu nisa daga makarantarsu zuwa tasu. A gefen katangar makarantar sukaga wasu 'yan makaranta kusan su biyar a jikin katangar makarantar, hayaki ne kawai yake tashi daga inda suke.
Hamza ne yace dan Allah Farouk kalli wadan can kamar ba 'yan makaranta ba, ace wai yaro tun yana secondary ya bude hun hunshi da hayaki, zuwa gaba kuma me kake tunanin zasu zama.
Juyawa Farouk yayi danshi bema kallesu ba. Karaf idonshi ya sauka akan Fahad ya daga wata farar takarda daya kunna yana zuka yana fesar da hayakin sama se daruya suke mashi.
Murtsike ido Farouk yayi domin ya tabbatar da abinda idonshi ya gane mashi. Tabbas ko a amafarki yaga Fahad ze iya ganeshi, wasu hawaye ne yaji sun zubo mashi, Hamza yace Farouk lafiya de? Hannun Hamza Farouk ya kama suka nufi inda su Fahad suke.
Daga sama Fahad yaji muryar Farouk, dede lokacin ya zuki wiwi dinshi, ido yazaro lokacin da sukayi ido biyu da Farouk, zumbur ya mike tsaye, kwarewa yayi hakan yasa hayakin yarika fitowa daga bakinshi.
Saurin wurgar da sauran wiwin yayi yana kara kallon Farouk, sauran abokanshi ma duk suka mike. Kwalla ce kawai take fita daga idon Farouk, Hamza ne yace wai Farouk ka sanshi ne? Share idonshi yayi yace Fahad din gidammu ne.
Cike da mamaki Hamza yakara kallon Fahad din. Fahad cikin sanyin jiki yace Yaya? Girgiza kai kawai Farouk yayi ya juya baya yana fadin ashe halin da kasa kanka kenan Fahad? Dama na dade ina zarginka ashe zargina gaskiya ne.
Ka cuci kanka, kuma kanka zaka lalata ma rayuwa, tun kana yaronka zaka bata hun hunka da hayaki. Cikin kuka Fahad yace dan Allah Yaya kada ka fada ma Malan. Murmushi Farouk yayi yace Malan kadai kake tsoro ko? Baka tsoron Allah.
Kuma baka tsoron lafiyarka. Shikenan, bazan fadama kowa ba, duk abinda kayi dan kanka. Hamza muje anfara kiran sallah. Fahad yace Yaya dama anan kake? Farouk yace E, kuma ka tabbatar ka koma makaranta.
Juyawa sukayi suka nufi makaranta, zuciyar Farouk kamar zata fashe wai Fahad ne yake shaye shaye? Dama yasha zarginshi akan hakan, dan wani lokacin idan yadawo da dare se yarika jin warin sigari ajikinshi.
Hamza ne yace dan Allah Farouk kada kabari wannan abun ya dameka, tabbas nasan akwai ciwo,amma hakuri shine zefi, kuma kamar yanda kace ba zaka fadama Malan ba, wannan ba shawara bace.
Domin ba'ayin shiru a irin wannan yanayin, Fahad yaro ne, idan har ba a dauki matakin hanashi wannan shaye shayen ba to tabbas idan ya girma abun zefi haka. Gara kabata dashi akan kace zaka rufa mashi asiri dan yaji dadi.
Farouk yace ina tsoron yanda Malan ze dauki maganar ne, Malan yana da zafi, kawai zan fadama Mama nasan zata iya shawo kan matsalar. Hamza yace amma Malan zefi yimashi ta zafi akan Mama.
Farouk yace baka san halin Malan bane, kawai kabari zan fadama Mama. Hamza yace to Allah yasa ya gane, kuma Allah ya shiryeshi. Farouk yace amin. Haka suka nufi makaranta.
Fahad kuwa gaba daya hankalinshi yatashi, tsoro yake kada Farouk yafadama Malan, wani abokinshi ne yace haba abokina, meye na wani damuwa? Ai tunda kaga be dauki wani mataki sosai ba shima be rasa afawa.
Koda ya fada agida kawai kace masu ka dade da denawa, amma taya zasu hanaka jin dadinka, kai bakaji yanda kakeji ba idan kana sha? Nima lokacin da aka kamani agidan mu inasha kawai dan fada ne akamun.
Kuma na nuna masu nabari, shikenan kuma se aka koma ana jidani. Haka suka yita yima Fahad hudubar banza, kafin subar wajen seda wani yakara kunna mashi yabashi yasha sannan suka koma makaranta hankalinshi kwance.
****** *****
Lokacin da akayi hutu malamin su Farida ya bama Fatima takarda ta kawo ma Malan, saboda an kama Farida da wani yaro da dare acikin class suna 'yan tabe tabe, alokacin malamin shi kadai ya kamasu, haka ya zanesu kuma yace seya kaisu wajen Principal.
Kuka suka rikayi suna bashi hakuri, seda ya farfasa masu jiki sannan yace suyi mashi alkawarin bazasu kara ba, haka sukayi alkawari suna kuka. Lokacin da akayi hutu shine ya rubuta takarda ya bama dan uwan kowa yace su kaima iyayensu.
Yasan idan yaran yaba bazasu kai ba, duk da be fadama kowa ba seyai tunanin ai kama iyayensu domin sukara ja masu kunne, kuma yafada masu idan suka sake korarsu za'ayi.
Bayan Malan ya dauko su sam Fatima ta manta da takardar, haka su Fahad da Faisal suka dawo, gidan kowa se murnar ganin dan uwanshi yakeyi. Farida tace shikenan yanzu batare zamu rika dawowa da Yaya Farouk ba? Mama tace Yaya ai yana gidan biki.
Farida tace ina ne gidan biki kuma? Mama tace Isa Kaita mana. Farida tasa dariya tana fadin N.C.E zeyi shi kuma? Mama tace shida Malan sukace sun amince, base yaje yayi tayi ba.
Kude ku dage kutafi jami'a. Fahad ne yashigo yana fadin Mama ina abinci na? Mama tace Oh! Ni, yanzu ya akayi cikinka ya bude haka? Da de baka da cin abinci, ko kun dawo makaranta se kowa yaci kake cin naka.
Fahad yace yo Mama mutum ya kwaso yunwar makaranta ba dole ya nemi abinci ba. Mama tace to kaje kacire kayanka kayi wanka sekaci, dan Allah kalleka kamar ba senior ba, duk kazama kazami wallahi.
Dariya Farida tasa, kafa Fahad ya kai mata yana fadin zanci Uwarki wallahi. Dukewa Farida tayi tana kuka dan taji zafin harbin da yayi mata a cinya. Mama tace bana son sakarci fa, ya daga dawo warku zaku fara fada abinda bakuyi ada.
Tun dazu take son kadawo kuma shikenan kana dawowa zaka hauta da duka, wai meyasa yanzu kake da saurin zuciya ne Fahad? Kuma ko kunyata ba kaji zaka zagi Uwarta, to bayan ni akwai wata Uwar da kuke da ita ne? Juyawa Fahad yayi yana fadin wallahi Mama duk kece kike bata yarinyar nan.
Wallahi idan kikace zakimun wannan rashin kunyar taki Uwarki zanci, fita yayi yana zaginta. Rike baki Mam tayi tana mamakin canjin halayen Fahad, ada yafi Farouk son Farida, amma yanzu shine yake dukanta hada zagi.
Fatima ce da Faisal suka shigo tana rike da hannunshi suna ta dariya tana fadin Allah Yaya seka bani alawata, ai Yaya Saleem ni yace akawo mawa. Faisal yace ai nafada maki sekin biyani zan baki. Kwace hannunshi yayi ya ruga dakinsu itama ta bishi da gudu suna dariya.
Wani bakin ciki ne ya kama Mama, kallon Farida tayi tana fadin yi hakuri kitashi kiyi wanka kici abinci. Farida tace ni da nayi wanka ma gidan Hajiya zanje. Mama tace a'a kibari se gobe, yanzu kizauna ki huta.
Farida tace kai Mama, nide kibarni intafi. Mama tace kinsan de yanzu Malan ze dawo kuma nemanku zeyi, ki bari kawai se gobe. Farouk ne yashigo da sallama hannunshi dauke da jaka.
Farida ce tasa ihu tana fadin ga Yaya oyo oyo. Murmushi yayi yana fadin Farida yan mata, ashe har kundawo? Amsar jakar tayi tana fadin tun dazu ma. Murmushi Mama tayi tana fadin ashe kaima kana hanya? Farouk yace wallahi kuwa.
Gani nayi duk an tafi week end shine nace nima bara inzo nasan 'yan makaranta sun dawo semu gaisa. Mama tace sannu da zuwa, yace yauwa na sameku lafiya? Tace lafiya lau. Shiga ciki inzubo maka abinci.
Yana shiga Faisal yace la! Yaya yaushe kadawo? Farouk yace yanzu nashigo, ai nasan zaku dawo hutu shiyasa nace bara indawo mugaisa. Fatima tace Yaya sannu da zuwa, yace yauwa Fatima ya karatu? Tace Alhamdulillah.
Zaune Farouk yake a dakin Mama bayan yagama cin abinci tana ta tambayarshi yanda makarantar take,Farouk yace lafiya lau Mama, tace to wa yake maka girki kuma? Farouk yace ai na iya tun ina Faskari, Mama tace da kyau.
Dukar da kai kasa Farouk yayi yana wasa da hannunshi. Mama tace wai ni tun dazu nake ganinka kamar baka da lafiya, ko wani abun ne yake faruwa? Kwallace ta cika idon Farouk. Kara matsowa Mama tayi tana fadin kafada mani mana.
Fatima ce tayi sallama, amsawa Mama tayi tana fadin lafiya? Shigowa Fatima tayi tana fadin dama Malaminsu Farida ne yabani takarta yace inkawo ma Malan, shine na manta dazu a mota ban bashi ba.
Mama tace kinji gulma kai, ba anjima Malan din ze taraku gaba dayanku kowa yakawo takardunshi ba, bazaki iya ajewa anjima ki bashi ba? Fatima tace ai batawa bace ta Farida ce. Mama tace ita meyasa be bata ba? Se ke uwar rawar kai? Dukar da kai Fatima tayi kasa. Domin ta karanta abinda yake cikin takardar, kuma ta nuna ma Faisal.
Shine ma yace kada tabama Malan ta kaima Mama dan yasan Malan ze iya dukan Farida, sosai sukayi mamakin abinda Farida tayi, Faisal yake tambayar Fatima yace dama kinsan tanayin haka ne? Fatima tace nide naji ana maganar tana yawan cewa tana son maza.
Amma gaskiya bansan lokacin da tayi wannan abun ba, kuma ma kaji malamin yace be fadama kowa ba. Faisal yace Allah ya kyauta, ina fatan kede ba ruwanki? Fatima tace wallahi ni ba ruwana da kowa.
Cikin tsawa Mama tace to Uwar me kika tsaya kinayi, kitafi kibani waje, idan Malan din yadawo seki bashi. Farouk ne yadago kanshi yace kawo nan mugani, mika mashi tayi ta fita. Mama tace ai da baka amsa ba.
Bude takardar yayi Mama tana fadin karanta mani inji abinda yace, lokacin da Farouk ya fara karantawa seda hawaye suka zubo mashi, kasancewar da turanci malamin ya rubuta yasa Mama bata fahimci duk abinda ya karanta ba.
Sede ganin yana karantawa yana kuka yasa tagane akwai matsala. Mama tace bade korarta sukayi ba ko? Girgiza kai yayi yace wai meyasa komai yake zuwa mana a haka ne? Mama tace wai me yake faruwa? Farouk yace malamin su Farida ne yakawo karar ta.
Mama tace kamar ya? Nan Farouk ya fada mata abinda yace, sosai hankalin Mama yatashi, amsar takardar tayi ta yaga tana fadin baza'a fadama Malan din ba, nida kaina zan ja mata kunne.
Wannan bala'i dame yayi kama? Farouk yace shikenan kowa da tashi kaddarar, shi Fahad ga halin daya jefa kanshi, ita kuma ga abinda take aikatawa. Mama tace bangane ba? Cikin kuka Farouk ya fada mata halin da Fahad yake ciki.
Sosai hankalin Mama yakara tashi, kuka kawai takeyi, wannan wace irin jaraba ce tashigo mata gida? A fili tace Allah ya isa tsakanina dake Inne, burinki ya cika kin lalata mani yara. Farouk yace haba Mama, me kuma Inne tayi maki? Inne bata da laifi laifinsu ne.
Mama tace wallahi banyarda ba. Kuma inaso kaja bakinka kayi shiru, wallahi idan kabari naji wannan maganar a wajen wani sena bata maka rai, kasan de yanda Malan yakejin haushinsu Fahad, idan yasamu wannan labarin shikenan sun zama abun kyama awajenshi.
Ka barni nasan matakin dazan dauka, bazan bari Malan yaji wannan maganar ba bare ya maida mani yara saniyar ware. Nasan halinshi sarai, shi kullum wanda yakeyin abun kirki shine mutum awajenshi, dan haka bazan bari yasan komai ba.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[4/5, 4:22 PM] nabilalady5: 🏡🏡 A WANI GIDA🏡🏡
😭😭😭
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
www.NabilaLady5@gmail.com
Facebook...Nabeela Ladeey