Complete Hausa Novels

Fin Karfi Part 2 Complete Hausa Novel

Reading file: Fin Karfi Part 2 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 3 of 6

Page 3

Dady yana dariya ya miƙe ya buɗe fridge ya ɗauko Hollandia ya ce "Ina Baba Saude?"

Ta ce "ta je É—auko mana markaÉ—en waina."

Ya ce "To wai Hajja shima tsohon mijin naki haka aka ce miki ga miji?".

Ta ce "ƙwarai kuwa to mu ko kinada ƴan samarin ki na dandali ba lallai bane ki auri ɗayan su dan ni kakan ka ko ganinshi ban taɓa yi ba sai da aka kaini gidan su."

Ya ce "Shi fa ya taɓa ganin ki?"

Ta ce a ina zai ganni? Mahaifinshi aminin tsohon mu ne ba ma a Katsina ya ke ba yana gurin yar mahaifinsu a Huntuwa sai da aka yi auranmu sannan ya dawo nan gidan su."

Dady ya ce "Da kenan ni yanzun ya ma za'a yi na yarda."

Ta ce "To bama kai ba mahaifinka ma soyayya yayi da uwar ka kan ayi auren shi ka biyo ai da yake ance magaji ma fiyi taka take murika tashi."

Dady yayi shiru ya ce "Zan kam bar tarihi dan ni nasan tawa ta ƙare."

Hajja ta ce"kai dai baka da fatan arziƙi mu can za labari."

Ya ce "wa ne canza labari Hajja aini banida labari mafi soyuwa a raina kamar na Pretty na."

Ta ce "Kai ni ja can ga sunan yarinya Ruƙayya mai daɗi amma kaƙi kiranta dashi sai wani kiristine ko pristine ma Oho."

Yayi dariya ya ce "Hajja tawa ni na Ruƙayya gashi kina son sunan ta amma baki iya faɗa ba wai Rukayya."

Ta ce "Aifa ku Æ´an bokon nan komai aka ce ba'a iya ba sai ku."Haka sukayi ta hira har zuwa sallar magriba.

Dady yana zaune gaban Affa bayan sun gaisa sai ya ce "Yusufa sai kuma ka ji yanda Ubangiji ya yi ikon sa ko?"

Dady kanshi a ƙasa ya ce "na ji Affa sai dai har ya zuwa yanzu kaina yana duhu Affa ban san laifi na ba kai min irin wannan horon duk da nasan kai uba ne na gari mai hangen ƙwarai nasan bisa ga babban dalili ka aikata wannan abu zan so nasan dalili inda hali.

Jikin Affa ya yi sanyi ƙwarai da jin lafazin Yusuf kuma har ma yaji kunya, ya gyara zama sannan ya ce "Yusufa da farko dai kai min afuwa har ga Allah da nasan cewa Alhaji Mansur Yusuf Katsina shine mahaifin ka da babu dalilin da zan baka ƴata da sauri Dady ya dubi Affa bakin shi yana rawa ya ce "Affa saboda me?"

Affa ya ce "kafin haka ina son kayi haƙuri ka bar Ruƙayya,ga kayan ku nan da kuɗin ku kai hatta ƙyautar farko da kayi mata duk da na kashe,na samo na harhaɗa na maida na fasa baka Ruƙayya mahaifinka shi ne yakamata ya baka labarin dalilin da yasa na fasa aura maka ƴata, kuma nima dole ne na hana aurenta koda hakan yana nufin zaku rasa rankune kai da ita zan so ka gane, yanzu bari na shiga in sa a haɗo maka kayan ku. Zan cigaba da yi maka fatan alheri dan kaifa ɗa ne Yusuf."

Ɓari jikin Dady ya soma yi ya kasa magana har sanda Affa ya shigo ya zube mishi kuɗi a gabansa,ko takan kuɗin Dady bai bi ba, ya ce "Ka ce na tambayi Dad ɗina ko?"

Affa ya ce "Ƙwarai ka ce masa wanene koda yake ai kasan Jega ko?

Ya ce "Alhaji Aminu Jega?"

Affa ya ce "Shi"

Dady ya ce "nasan shi, shi ne mai kula da harkokin gine ginen Dad É—ina."

Affa ya ce "yauwa ka ko san shi, to ka je kace da mahaifin naka na ce ya sanar da kai me ke tsakanina dashi da Jega?"

Ikon Allah ne ya kai Dady gida ya fito a mota hankalin nan nashi a tashe yana shiga cikin falon su ya hangi Momy ita da Dad wajen daning Dad yana tsaye da alama ma faɗa yake yi, ya isa gurinsu Dad ya dube shi da sauri ina ka shigane Son tunda na dawo nike neman ka a phone ka kashe ka shiga gari kaji dai abin da Doctor ya ce kana buƙatar hutu shi ne amma zaka tashi kalar neman damuwa ai gashi nan kana yaronka jininka ya soma hawa nida girmana nawa be hau ba sai naka dan kaine kasa kanka, Momy ta miƙe ta ce "Haba Alhaji yaya zaka sanar dashi halin da yake ciki in kuma yaji ya ƙara tada hankalinsa fa."

Dad ya ce "ai gara yaji in zayayi mentain É—in lafiyar sa yayi in bazai yi ba shi ya sani."

Tunda Dad yake ta faɗa Dady ko ajikinsa sai da ya gama ya zauna sannan Dady ya dube shi ,kayi haƙuri Dad nima dole ce tasa na fita ya cigaba. Ya ce "Dad wai dan Allah meke tsakanin ka da Affan Ruƙayya da kuma Alhaji Aminu Jega?" Ido Dad ya tsura mishi na ɗan lokaci sannan ya ce me kake son sani ne? Wannan ba damuwar ka bane,kana ji na ko Son?"

Dady ya ce "Damuwa ta ce domin akan ta zan rasa Ruƙayya wanda hakan zaya iya haifar da komai mahaifin Ruƙayya shi ne ya turo ni gurinka dan naji daga gareka,dan ya ce kaine kafi cancanta ka sanar dani dalili kuma ya ce na yarda duk abin da ka gaya min."

(Dad ya katse shi) "Son ka kiyaye ni fa zanyi fushi da kai banason kana zuwa gurin wannan ɓarawon mutumin ka koma shi ya gaya maka da kansa tunda kai ya zama dole sai ka auri ƴarsa." Da faɗar haka yayi saman shi cikin ɓacin rai.

Kai Dady ya kifa akan daning table zufa ce ƙwarai ke zubo masa ya yin da kansa ya soma sarawa ya sa hannu ya riƙe kan.

Momy ta tashi ta kamoshi ta ce "Dady zo muje É—aki zo ka sanar da ni yanda kukayi."

Ko gani sosai bayayi suka shiga ɗaki bakin gado suka zauna ta dafashi "Yaya kuka yi da Affan Ruƙayya? A hankali ya sanar da ita komai."

Ta ce"ka ƙwantar da hankalinka gobe zamuje ni da kai dan ya sanar damu komai kenan daga nan sai naga abin zanyi akai."

Duban Momy Dady ya yi ya ce "Nagode Uwata mai maganin damuwata Allah ya bar min ke" ta ce to kayi bacci bana son hirar dare ka ji." Ya ce "insha Allah " ya miƙe cikin ƙarfin gwiwa.

Talatainin dare tunda ya ƙoƙarta ya yi wanka sai ya zama ya kasa bacci sai faman sintiri yake a tsakar ɗaki,ƙarfe biyu da minti ashirin sannan ne ya samu ya faɗa kan gado, hannu yasa ya janyo filo ya rungume shi tsam,ban da muryar Pretty dinshi babu abin da yake muradi hannun shi yasa ya ɗauko wayar sa ya soma neman ta nan take ya tuna cewa ta ce suna ƙwana tare da Yayyanta. Amma duk da haka sai yaji zuciyarsa tana matsa masa, don haka sai ya ci gaba da neman layin ta, ringing ɗin farko Ruƙayya ta miƙe ta ɗauko wayar da sauri ta koma can bayan jakunkunan kayan su,a hankali take magana "Dady ya ya ne?" Ya yi ajiyar zuciya gami da juyi rigingine ya kuma ƙara rungume filon tsam ji yake tamkar ita ce a ƙirjinsa ya ce "Oh my sweet heart,ina cikin damuwa na kasa bacci."

Ta ce, nima haka ya ce "Allah sarki, yanzun dama ɗaya ta rage mana don haka gobe zamu zo da Momy ƙila ya yarda."

Ta ce "Allah yasa haka."

Ya ce "Amin,ki dinga zama koda yaushe da wannan wayar zan dinga kira."

Ta ce "To, amma kada ka kirani kuma lokacin da mutane.

Ya ce "Zan gaya miki yanda zaki maida ta a silent in na kira sai dai tayi vibrating ba mai ji sai ke kinga sai ki kauce daga gurin mutane."

Ta ce "To."

Ya ce "Yanzu gaya min kina zaune ne ko kina ƙwance?"

Ta ce "A'a ina ma raɓe ne bayan kayan sawar mu,kai fa?"

Ya ce "Allah Sarki,Ni kam yanzu ina ƙwance a ɗaki na kan gado rungume da filo a ƙirjina,sai ina ji tamkar Pretty ɗina ce na mannata." Ta yi ƴar dariya ta ce

"Kai ko."

Shima ya ce "Ke ko." Suka yi dariya tare.

Ya ce "I love You."

Ta ce "me too"

Sai kawai taji ya yi kiss ɗin ta a wayar a kunnanta taji ya ratsata har tafin ƙafarta,da sauri ta kashe wayar tayi ajiyar zuciya gami da ɗan murmushi cikin jakar kayan ta ta tura wayar ta koma tayi ƙwanciyar ta.

Shima dariya ya yi har da wuntsilawa zuciyarshi ta yi fes ya miƙe ya shiga toilet ya ɗauro alwala ya shiga miƙama Ubangiji matsalar sa.

Ruƙayya tana sharan tsakar gida Umma ta na ɗaki lokacin dai dai ƙarfe biyar sun gama abincin dare sun sa a kula Fati da Murja suna ɗaki suna labari Momy ta yi sallama da sauri Ruƙayya ta miƙe suka dubi juna murmushi Momy ta saki ta ce "Ruƙayya ƴata kina shara ne."

Ruƙayya ta sunkuyar da kai sannan ta ce "Momy sannu da zuwa."

Momy ta ce "yauwa ƴata ina Umman taki?"Ruƙayya ta shiga ɗakin Umma ta ce "kinyi baƙuwa." Ta fito ta shiga ɗakin su,Yaya Fati anyi baƙuwa fa.

Suka dube ta "Wacece."

Ta ce "Momyn Dady ce." Da sauri suka tashi suka fita sun samu Umma ta fito mata da tabarma ta shinfiɗa mata a tsakar gidan dake share ƙal. Dan Umma ta ce mata ta shiga ɗaki amma sai ta ce nan yayi ma, Yaya Fati ta kawo mata ruwa mai sanyi na randa sai ƙamshin saiwar da ake sawa cikin ruwa ta zuba shi ne cikin sabon jug irin na kayan auran Ruƙayya Yaya Murja kam tuwon Affa ta kawo mata cikin sabuwar kula da yake ance baƙon ka annabin ka.

Momy ta ce "Agaishe ku Æ´aÆ´ana." Suka russuna suka gaishe ta.

Ta ce "ina Æ´ata shi ne ta shige É—aki."

Suka yi dariya sun yabawa Momy mace mai sauƙin kai da rashin ƙyamar talaka, ita ma sun burge ta sosai.

Ta yaba da tarbiyyar su ta girmama na gaba,sun gaisa da Umma, Umma ta ce to baki ci tuwon ba.

Momy ta ce Alhamdulillahi na sha ruwan,dan dama nazo gurin Affan nasu Ruƙayya dan Dady ya ce min ƙarfe biyar zamu sameshi."

Umma ta ce "ƙwarai ya kan dawo biyar ɗin, to yau dai gashi har shida saura nasan dai yana hanya."

Momy ta ce "Allah ya kawo shi lafiya."

Umma ta ce "Amin." Phone É—in ta ta soma kuka ta É—auka.

Ta ce "Yaya ne Dady?"

Yayi muryar tausayi "Please Momy ki turo min Pretty mana."

Momy ta ce "A'a ka shigo mana kaima ai gidanku ne."

Ya ce "Ina jin kunyar Umma,dama dai Affa ne zan iya shigowa."

Ta ce "to sai ka jirashi don be ƙaraso ba." Ta kashe wayar.

Affa tare suka shigo da Dady,yana riƙe da ledar da Affa ya ruƙo daga kasuwa mai ɗauke da lemu da yalo da kuma gautan ɗaci, Umma ta tashi tana sannu da dawowa Malam, ta buɗe mishi ɗakinsa Momy ma ta mai sannu ya amsa sannan ya shiga ɗakin Dady ya ɗan russuna ya miƙa ma Umma ledar bayan ta fito daga ɗakin Affa inda ta kai masa ruwan sha, ya ce "Yusuf shigo mana."

Shi kam yana ta waiwayen inda zai hango Pretty É—in sa.

Momy ta ce "kaifa yake kira." Sannan ya bar leƙen windon ɗakin su Ruƙayya inda ya hango ta,tai mishi gwalo ta tsugunne shi ne yake ta faman leƙen windon.

Ya shiga suka gaisa sannan ya ce "Na kawo Momyna tana son ganin ka."

Affa ya ce "to ai babu damuwa,sai ku shigo."

Momy ta nemi guri ta zauna a cikin É—akin, Affa ya dubi Momy "sannu da zuwa Hajiya."

Momy ta amsa sosai suka gaisa, sannan ta ce "Dama dalilin zuwa na shi ne, ina neman alfarma da kayi haƙuri ka yarjewa yaran nan da su auri juna, musamman ma ita Ruƙayya dake fama da matsala,ni na rasa menene ainihin matsalar.

Affa ya gyara zama ya ce "shi maigidan naki bai sanar dake komai a kai ba?"

Ta ce "Wallahi bai gaya min komai ba."

Ya ce "Ni dai nafi son kuji daga gareshi."

Momy ta ce "Babu komai,in kaima ka sanar damu."

Ya ɗan ɗaga murya ya ce "Ke Fati." Ta amsa, ya ce "Kira min Ruƙayya ku zo harda Murja.."

Suka shigo da sallama ciki suka wuce suka zauna, Dady kam ko kunya ya tsurawa Ruƙayya ido, ita kam sunkuyar da kai tayi tana tunanin Allah yasa Affa ya amince su auri juna.

Ya dube su duka, sannan ya ce "Hajiya ina son ki bani aron hankalinki har da naku ku ma,ki min adalci shin ya dace na bada Æ´ata ga É—an wanda ya yi min wannan aikin.?

Wata sansayar yamma ce ta ranar Laraba ina aiki cikin gonar gadon mu da mahaifina ya rasu ya bar mana ni da ƙannena mu goma sha ɗaya mu biyar mazane shida kuma mata,mu huɗu da ƙannena uku muna aikin noman rani da damina sai ga wani mai gadi nan kusa damu mai suna Isa ina aiki ya shigo muna gaisawar zumunci da Isa shi yana gadin filin former I.G Alhaji Mansur Yusuf ƙaton fili ne kuma an zagaye shi da katanga, shi wannan filin rabin shi na mahaifinmu ne, former I.G ya karɓa ya bashi dubu sha biyar amma can lokacin,ya nemi gwamnati ta mallaka mishi filin wanda a yanzu zai kai miliyan hamsin.

Malam Isa ya ce dani "Malam Sani an aikoni gurinka." bayan mun zauna sai yake min bayanin Alhaji Mansur mai gidan shi yana son gani na,na ce to ko lafiya? Ya ce lafiya lau ina ga dai alheri ne dan mai gidan namu mutumin kirki ne,na je na kira ƙanina Sulaiman na ce yazo mu je.

Affa ya dubi Momy ya ce "Kina ji na?"
Ta ce "ina jin ka."

Ya ce "wannan abun fa da nike sanar dake duk a can gida Katsina ya faru.

Momy ta ce "Tunda na ji ka kira ƙaton fili na gane can gida abin ya faru."

Ya ci gaba "Koda muka je gaban Alhaji Mansur shi da Alhaji Aminu Jega muka sameshi wani dallali kuma mai Kula da gine-ginen Alhaji Mansur da filayenshi muka zauna ƙasa muka gaisa dasu cikin girmamawa Alhaji Mansur ya dubeni "Kaine Sani."

Na ce "Eh,ni ne ranka yaÉ—aÉ—e."

Ya ce "muna tare da ku amma ban san ku ba?" Muka yi shiru.

Ya ci gaba "Ni nasan mahaifinku sosai dattijon arziƙi mai son jama'a sam shi abin shi be rufe mai ido ba,kun san fili na na kusa da ku gurinshi na amsa,naima filin kuɗin gwamnati, kuma na bada ma wasu kuɗin daga baya akai mishi ashe saƙon bai same shi ba." Mu kace ya wuce ba komai." Ya ce "yanzu ya labarin wannan gurin naku? Ni ina son gurin zan siya.

Na ce "To bari muje muyi shawara da sauran Æ´an'uwanmu, mahaifiyarmu tana nan da rai dan haka sai mun shawarta.

Ya ce "To hakan ya yi."

Jega dake gefe ya ce "Kuna da takardar gurin ta gwamnati?"

Na ce "Muna da ita."

Alhaji ya ce "Ku nawa ne gurin mahaifinku."

Na ce "mu sha É—aya ne sai mahaifiyarmu."

Ya ce "amma ai kuna da gidan kan ku ko?"

Na ce "ƙwarai gidan mu muke ciki."

Ya ce "Ni ku ɗauke ni tamkar ɗan'uwa don bazan cuceku ba, kuyi shawara nawa zaka saida min da gurin dan ba zan ci haƙƙin marayu ba."

Muka ce "To." Muka tashi muna godiya.

Bayan munyi shawara mu saida mishi sai muka sake dawowa da ƙanina. Miliyan uku da rabi muka ce su bamu.

Jega har yana cewa wai shima tunda shi ne yazo ya yi ma Alhaji tallar gurin sai mun bashi wani abu,sai muka ce babu komai.

Dubu É—ari biyar muka ce zamu bashi in an biya mu, duk da ba tallah muka yi ba.

Bayan wasu ƙwanaki suka bamu miliyan biyu saura ɗaya da rabi,da shike muna cikin buƙatar kuɗin ne sai muka ce mu raba.

Malamai ne ma dai suka raba mana kowa aka bashi nashi,muna jiran sauran kuɗin, rannan sai ga saƙo daga Jega,wai fili gwamnati ta riga ta ba wani, kuma wanda aka ba yaron Alhaji Mansur ne, don haka takardun mu na ƙarya ne mu dawo da kuɗi,ki na ji?

Momy ta ce "Ina sauraron ka." Ya ci gaba "Koda na ji sai naje na ce to muje land and sobe ɗin ai fayil ɗinmu na can a taƙaice dai Hajiya haka wannan Jega ɗin suka yo takardun bogi suka ce na gurin ne sai mu dawo da kuɗi. Bayan duk unguwarmu kowa yasan tsohonmu da gurin ga takardu ga komai, haka suka sa ƴan sanda suka kamamu suka tafi damu (State C.I.D) aka tsare mu da har ma ance gidan yari za'a kaimu tunda mu rasa wanda zamu cuta sai (former I.G).

Munsha wuya,don ma ƴan'uwanmu da Abokaina sun yi ta ƙoƙarin ganin haɗa kuɗin an basu, tunda sun ce sai mun basu kuɗin su sannan zasu sake mu, wasu suka ce duk sharrin Jega ne aje a samu (Former I.G) shi zai sa a fito damu dan mutumin kirki ne, ana zuwa ya ce magana tana gurin Jega, anyi-anyi amma yaƙi ya ce a sake mu, tunda shi ne mai kuɗin, Hajiya lokacin ƴan'uwana da mahaifiyarmu sun shiga tashin hankali, mata ta......

🖊️🖊️🖊️
[7/28, 08:27] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 2*

*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.