Best / Popular Hausa Novels

Kalbim Book 2 Complete Hausa Novel

Reading file: KALBIM BOOK2.txt

Chapter 1 of 5

*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 1

BismillahirRahmannir.
Kumar yanda hausawa ke fada qasar kabari bata kisa sedai ta binne binnannnniya,

Wahala,kunci,talauci,sauyin rayuwa da munin kaddara bai kashe Zaadens a rayuwar da suka samu kansu rana tsaka ba saima karfin imani dana zuciyar karban kowace irin kaddara datazo musu da hannu bibbiyu,

Rayuwa a kauye ta zuwar musu a tsananin da suke ganin kamar bazasu iyaba sbd rayuwa ce da babu ko a mafarki da suka taba jin labarinta bare tsintar kansu acikinta,

Rayuwa ce dataiwa tasu rayuwar nauyin da suke jin kamar bazasu kai koinaba zasu mace a cikinta,

Ammar da maheer sunfi kowa zarewa a cikinta musamman Ammar dayake jin kamar zai zare idan ya bude ido yaga a inda rayuwarsa take,

Bandaki kadai wani abu ne me girma dayake tsananin tsoro sbd ganin yakeyi kamar zai fada dashi,

Ranar farko da suka iso kauyen ya shiga Yana leqa masai/shadda da aka nuna masa anan zaiyi kashi tsutsotsi da kyankyason dayaga sunata yawo da motsi a cikin pool na kashi yanke jiki yayi ya some a jikin garba daya rakosa.

Cikeda mamaki da tsoro garba ya ciccibosa ya fito dashi waje yana kiran jamaa.

Su Dad da jannah ne suka iso da sauri tareda su modibbo hankali tashe kowa na tambayar lafiya.

Maheer bandakin ya nufa da sauri dan dubo abinda yaiwa rayuwar Ammar din barazana yana saka kai ya dawo Yana kasa shiga sbd jirin dayaji Yana dibansa na qaton ramin dayaga bakinsa a bude sbd shi baima leqa ba bare yasan meye shi ramin.

Ruwa masu sauyin gaske garba ya zubawa Ammar yana cewa

"Modibbo nifa inaga gamo yayi a bandakin,Aljanu sunga jan bature duk da ance a hakan ya dafe sosai ko?"

Katsesa modibbo yayi da cewa

"Aikuwa dai da alamar gamon yayi,
Maza ku kawo qauri yanzu a turara musu su duka sbd tsari"

Kawu isiya na jin haka ya kalli garba yace Maza debo jar wuta,
Juyawa yayi shima yaje daki ya dauko wasu manyan jakar dinki na kyallen atampa da wani yadi yazo ya zaro wasu daurin mgani kamar na hayaqin bori ya cika hannu ya zuba a cikin wutar da garba ya kawo suka tura su Ammar din da Maheer Harma da Dad dasu jannah a daki suka ringa turarasu.

Ammar sake somewa yayi sbd tsananin azabar hayaqi dayaji yana shigar masa qwaqwalwa da lungs Harma da neman makancewa.

Maheer tare yakeyi Yana neman mutuwa shima baisan lokacinda ya cara zabga ihun azaba ba Yana neman hanyar fita baya ko gani amma garba ya dafesa yana cewa

"Tsari ne da maganin kowane qwaro zaman kauye saida magani a jikin ku"

Jannah dayake sun dan fara sabo da azabar rayuwa da hayaqin sunsha wuya sosai amma ba kamar su Ammar din ba,
Dad ba shiri aka fito dashi sbd mutuwar da sukaga zaiyi shi da Ummah da jannah amma Ammar da Maheer suna sumewa suna tashi haka suka dannesu saida suka tabbatarda ya shigesu sosai maganin tukuna.

Tsoro da tashin hankali me tsananin gaske Ammar ya samu kansa a ciki bayan dawowansa daidai sbd ganin mutanen yake kamar rayuwar dabbobi ba mutaneba sukeyi.

Maheer ma zawo ya ringa yi amma a bayan Gida a daji sbd baya iya shiga bandakin shima tsoron tsugunawa akai yakeyi amma dayake a prison sun iya tsugunawa cikin grasses kashi da fitsari so sun dan saba,

Shima Ammar dole dajin yake zuwa duk abinda yakeji amma se garba ya rakasa sbd tsoro yakeji koina a kauyen.

Dad ma na acikin tsaka me wuya da rayuwar daya samu kansa a ciki me tsanani da wuya amma ganin Jannah ta jure ta rungumi kaddara ta saba ita datake mace kuma yarinya gashi tfara shiga damuwa da ganin yanayin da suke shiga na samun kansu a inda rayuwa zata qara musu tsanani dan haka ya rungumi jarumta ya karbi kaddarar sabuwar rayuwar da suka samu a kauyen Wanda zai sun dangana sun rungumi rayuwar sun karbeta zasuji dadinta da kuma samun nutsuwar da suka rasa ta shekarun da suka wuce dan haka ya nutsu ya shirya rayuwa a kauyen har lokacinda Allah zai kawo musu wata rayuwar kokuma har karshen rayuwarsa.

Maheer ma a hakan dole ya dangana ya amshi rayuwar duk da akwai abubuwan da bazasu iya adapting nasu da wuri ba se ahankali kamar bandakinsu har yanzu tsoro sukeji basa iya shiga,
Hakama cimarsu da sauran yanda suke gudanar da rayuwar ko zasu saba sai ahankali,

Ammar ma sbd kwanciyar hankalin Jannah yayi kokari sosai ya fara karban rayuwar kauyen Ammar ko fitsari baya iya zuwa se tareda garba wanda ya zama kamar bodyguard dinsa kuma abokinsa hakama abokin fadansa sbd kullum sai sunyi fada amma koina Ammar baya iya motsawa yaje seda garba sbd garba akwai karfi da jarumta kuma baida tsoro ko kadan dan haka ko sunyi fada Ammar yayita zaginsa da turanci haka zai koma ya nemesa su shirya dole tinda baida yanda zaiyi.

Maheer ya ari jarumta da gabacin da ko yaushe shine yake dauka a Zaadens ya fara bin su kawu daji gidan shanunsu masu tarin yawa garke Guda da ake harkar fidda nono dasu manshanu da madara da taki dai sauransu harma da kulawa da shanun da kuma kasuwancin abincin dabbobi da sukeyi na hada harawa.

Fara binsu yayi Yana shiga aikin kamar sauran yaran dake aiki yana dan samo yan kudin da zasu riqa ciyar da kansu sbd Jannah ce har yanzu me dan sanaar dake suke dan ci baa maganar sha sbd sunyi kwanaki biyu a kauyen cikin azabar kishirwa karfin suka fara shan ruwan kauyen sbd direct daga kogi ake debosu,

Da farko sunyi fama da yawan ciki da yanayi na rashin kyan ruwan kafin cimarsu kafin ahankali cikinsu da jikinsu suka saba,

Fara fitar Maheer aikin wahala da nema ya dan sake kawo sauki da sassauci a rayuwarsu sbd su modibbo tini suka gama hidimar kwana biyu dasu suka dena kowa tasa ta fisshesa.

Tinda Maheer ya fara fuskantar aikin karfi da wahala ya sake jajircewa gurin neman abinda zai hana rayuwarsu shiga kunci da takura a rayuwar kauyen cikin rufin asiri,

Ammar ya kasa sabawa yanda ya kamata duk yanda yaso kokartawa kawai dai shima Yana jurewa Yana bin garba da abokansa nasu ayyukan daji sedai ya bige da mangwaro yake debowa shi yake siyarwa a kofar gida duk da mangwaron ma baya iya hawa ya debo sedai su garba dinne suke debo masa kuma su tayasa siyarwar sbd suna kaunarsa da tausayinsa duk da Yana shan wuya a hannunsu sbd tsoronsa suke sake rikitar dashi shikuma dole ko yaushe Yana biye dasu yana zagi da turanci.

***Rayuwa taja musu a kauyen wanda lokaci ma yaja Wanda ya saka abubuwa da yawa faruwa ciki harda sake samun tsananin hadin kai da sabuwar kauna me karfi a tsakanin Zaadens,
Hakama a cikin manyan alamarin da suka faru shine AUREN DZAD DA UMMAH da aka daura akan kauna da shakuwa da kusancin da suka samu me tsanani a tsakaninsu duka da Umman data maye gurbi na uwa da aka rasa a Zaadens din,

Kaunar me girma da tsaftar dake tsakanin Umma da Jannah yasaka ta shafi duka ahalinta Musamman Ammar da kusan shima kaunar uwa da kulawan uwa yake tsananin so da buqata tin Yana qanqani shiyasa Mimi ta kasance ta maye ta cike masa wannan gurbin shiyasa rashinta kusan yafi tabasa akan kowa sai kumaa yanzu da Ummah take cike masa wannan gurbin ahankali sbd kaunarta da kulawanta Kansa kamar Miminsa.

Dukkaninsu ahankali suka sani suka fahimci ciwon Ummah Wanda sukai accepting dinta ahakan cikeda zuciya daya da kauna me girma tareda cike ahalin Zaaden da ita ayanzu datake uwa gaba daya a Zaadens dan haka ahalinsu a yanzu y dawo biyar a maimakon su hudu,

Sabuwar kauna me karfi da shakuwa me girma ce take sake gudana a tsakaninsu wanda Ammar yake sake dagewa gurin takurawa modibbo akan aiki dayakeso ya samo musu a birni shi dayake yawan zuwa binnin kuma ya dan San mutane,

Yanda yake tsananin son su samu aikin da Maheer da Jannah da Ummah zasu dena aikin azaba a kauyen yasa ko aikin gadi ko ban ruwa ko wanki da guga ne binni yanason su samu dan haka kullum modibbo ya dawo binni seya samesa da maganar aikinsu,

Ta bangaren modibbon shi Kansa yanason ya samo musu aiki me kyau koda bana office ba Kona gadin ne a manyan guri tinda sunada ilimi me girma d yawan gaske dan haka zaa samu kudi me tsoka dasu dan haka ya dage sosai Musamman dayaga da gaske sunason aikin kowane iri ne dan haka yakeson y samo musu aiki a guri daya.

Maheer ma dayaji ana neman aikin duqufa ya sake yi da nema sbd su samu abinda zasu dan samu gurin zama acan binnin idan ta kama.
#MAMUH
#THE STORY BEGINS
#BEST LOVE
#BEST ROMANCE
#LIMBAS
#ZAADENS
#NEW LIFE

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 2

Ammar tin Yana jira modibbo na zuwa neman musu aikin harya kasa hakura qagara ta saka ya fara bin modibbon birnin da kansa sbd a riqa sanin girma da zurfin ilimin dasuke dashi Wanda Banda mummunan kaddarar shigowan AZIZ LIMBA rayuwarsu da babu kamfanin daya isa su kallesama da irin ilimin da suke dashi bare dan haka dole yanzu tinda suna son koma wane aikin ne ya danne ya ringa biyo modibbon dan sugarwa kansu hakama a yanda yake gani ya kuma San iliminsu duk inda aka daukesu aiki ai a babban matsayi zaa daukesu sbd ansan samun masu irin iliminsu da experience dinsu akan aiki a banza irin haka ai bama abune me yiyuwaba dan haka yasani da gudu zaa ringa jin dadin samunsu a aiki.

Zuwansu na farko da zasuyi kallansa modibbo yayi kai tsaye kafin ya gangaro da idanuwansa kan kafafunsa da suke a tsaye kamar raken da aka ciro bata gama riquwa ba kafin yace

"Nifa idan naje kafuwana sune motata yawo nakeyi dasu me nisan gaske yanda kasan mashin din da babu burki haka suke,
Zaka iya?"

Kallansa Ammar yayi kafin ya dan hadiye yawun bakinsa daya bushe sbd ya dauka ma maganar kudi modibbon zai masa sbd yanda kasan mayu haka suke akan kudi,
Jin maganar tafiyar qasa kamar zararru a cikin rana ya sakasa hadiye yawun kafin ya bude baki kai tsaye cikin jarumta da qwallafa rai da yayi yace

"Eh zan iya indai yawon neman aiki ne ko abuja tas zamu zagaye zan iya amma zaka siya mana abinci da ruwa me kyau inace ko?"

Kawu isiya dayake zaune gefen modibbo Yana sauraronsu dago qananun idanuwansa da suke a matse kamar na yan Japanese yayi ya kalli Ammar din kafin ya tsayar da idanunsa akan wuyansa daya balain ramewa yayi tsayi kamar mariqar lema yace

"Kafin aje har ayi maganar abinci kanada kudin motar tafiyar ma tukuna Ammaru?"

Matse fuska yayi Yana qasa qasa da Murya a siqe da takaicin yanda kaf kauyen ake kiransa da Ammarun kamar wani sakarai yace

"God,Ths fools are killing me slowly"

Kawu isiya dayaji yayi magana besan meya fada ba sake maimaitawa yayi Yana zare hular shape din kwanon sha datake kansa ya ajiye gefe Yana cewa

"Idan bakada kudi ka wuce ka nema su Garba suna daji gurin qona gawayi ka shiga cikinsu kayi kunar ko hada saika samu na motar"

Modibbo ne ya katsesa da cewa

"Ni gobe zan wuce banda lokacin batawa na jiran har ayi kunan itace kwana biyu su zama gawayi a hada akai a siyar tukuna ayi tafiyar sedai ya jira wani jiqon idan zan sake komawa"

Qara matsowa Ammar yayi Yana dan kwantar da kai yace

"Modibbo idan ka tafi kilama saar a tafiyar yanzu take gwara dai ko yayane a tafi dani din zan nuna musu girman ilimin danake dashi da gudun gaske zasu daukesumu aiki fa,
Kuma a matsayin da muka taka na aiki da ilimi ana daukanmu aiki mu duka zakaga yanda kudi zai ringa shigowa kamar ba wani abu me girma ba so gwara dai a duba tafiyar,ko me kace kawu isiya?"

Gyara zama kawu isiya yayi Yana bawa Ammar din hankalinsa yace

"Bangane kudi zasu fara zuwa take ba,qaran hasken shi ilimin naku da atake zai ringa bada kudi"

Qaramin tsokin da basu jiba ya sake Yana bawa Kansa karfin gwiwan zaqewa yai musu bayanin da zai sakasu rudewa shidai ya samu su tayasu neman aikin duk da ba ilimin komai da suke dashi kansu a toshe yake kamar an narka kitse an rufe musu kan ya daskare amma kuma tinda sunada yan kudaden da zasu taimakesu gurin yawon neman aikin dole ya dorasu a kai tinda mayun kudi ne dan haka kamar wani tsohon fakirin malamin boko haka ya janyo dutsi ya zauna gabansu ya fara cewa

"Mun samu iliminmu ne bayan mun barar da dukiyar da zata gine kauyen nan da zagayensa gabaki daya kada kace ginin da kuka saba gani, infact mun saka kudin da zai siya qungiyar shanunku dubu a gurin neman ilimin...

Katsesa kawu isiya yayi da cewa

"Meye kuma kungiyar shanu?

Cikin takaicin da modibbo ya rasa na meye sbd kamar rena musu wayo Ammar din yakeyi da wannan karyar ya amsa tambayar kawu isiya da cewa

"Garken shanu yake nufi lusarin"

Zaro ido kawu isiya yayi Yana tashi zaune daidai ya kalli Ammar din ido waje yace

"Garken shanu dubu fa kace Ammaru"

"Yes sbd a cikin dukiyarmu kungiyar shanu dubu is nothing.....

Katsesa modibbo yayi da cewa

"Akace maka garken shanu ne ba kungiya ba ko?"

"Koma ya yake modibbo munada dukiya da abinda babu Wanda yasan iyakarsa da yawansa sai Allah sbd ko mu bamusan yawansa ba,

Dan haka yanzuma wuyarta dai mu samu aikin zamu Tara Harma fiyeda yawan na bayan kuma kunga wannan Karan daku a cikin duka alkhairin da zaa samu zamu ringa sammuku sosai..."

A tare kawu da modibbo suka kallesa kawu daya gama hawa da rikicewa akan zancen yace

"Sammuku??

Eh kawu kuma zaku lashi arziki sosai fa indai aka samu aikin nan"

Modibbo tsoki takaici ya sake yace

"Kai yanzu isiya sbd mutuwar zuciya da shegen kwadayin dayafi na Jibo zaka yadda da zancen a neman ilimi kawai an kashe dukiyar datai yawan garken shanu dubu,
Dubu fa,
Garken shanu dubu fa isiya"

Shiru kawu isiya yayi Yana jinjina maganar modibbo din kuma sbd kaf rayuwar fillo ma ganin yake akwai me garken shanu dubu kuwa to amma kuma kowa yasan su Zaadens din gadon wata irin dukiya sukai me yawan da shima modibbon Yana fada bai taba ganin irinta ba..

Miqewa kawun yayi da sauri ko takarmi babu kafarsa ya fada cikin gida ya kirawo kawu Jibo Yana cewa

"Jibo zo muje kaine me lissafi akan zumudin harkar duniya Ammaru yai bayani ka fada mana yaya zaayi dan dai nifa bazan yadda ayi arzikinnan sabo bada niba acikinsa dumu dumu"

Fitowa sukai tin kafin su qaraso bakin shimfidar tabarmar Jibo ya zare takarminsa ya qaraso yana kallan bakin Ammar daketa kokarin dora modibbo akan zancensa dayaga kamar baya shigarsa.

Zama sukai Jibo na jin yanda Ammar ke fadar dukiyar da sukai abaya wadda yawanta yafara zarar da tinanin Jibon ya kalli isiya yace

"Idan shawara zaku tsaya nidai ina ciki dumu dumu,
Ammaru Ni zan baka Aron kudin motar idan aka samu aikin mu ringa raba albashin."

Dukkaninsu tare suka kallesa cikeda mamaki da siqewa da takaicin yanda yayiwa kowa shigar sauri dga zuwansa,

Ammar da takaicinsu duka yakeji daurewa kawai yakeyi yana sake maida Kansa dan iska Yana musu bayanin dan su basa Aron kudin duk zaayi tafiyar harya samu aikin batareda sun gaji ba a siqe ya kalli kawu Jibon daidai Maheer ya kawo Yakuma ji abinda kawun ya fada Ammar ya kalli Maheer din cikin takaicin kawu Jibon yace

"Is he mad or just stupid?

Ajiyan zuciya Maheer yayi yana kasa cewa komai
Modibbo ya katse Gardamar kawu isiya da kawu Jibo da kallan Maheer Yana cewa

"Mahe kai kadai nake yadda da maganarka a ahalinku sbd kafi wannan me kama da rubabben kabejin zama mutumin arzikin daya San Kansa,
Fadamun gaskiya akan maganar neman aikinsu shin d gaske ne wannan dukiyar dayake fada kamar ta zamanin tarihin misra?"

Kallan Maheer Ammar yayi da sauri yana nuna masa ya taimaka masa ya qarasa dora masa su akan zancen sbd maganar gaskia sai sun qarasa mutuwa akan son abin duniyar dayake fada zaa samu su saki yan kudin da suke dashi a taru ayita neman aikin koda offer din aikin ta siyarwace su taru a siya din dai suga sun kama abin arziki sbd sukaci gaba da rayuwa a haka a cikin kauye da gwagwarmayar kauyen ba jimawa zasu tashi daga kamanninsu su koma kamar wainda aka haqo daga rami dan ko yanzu idan ya kalli wuyan Maheer daya koma kamar wuyan fanka hakama Dad gabaki daya rigar jikinsa kullum a kode kamar wani me tallan yalo ga Jannah da Ummah ma duk sunyi laushi kamar alayyahun daya kwana shi kuwa Kansa baama magana dan ya koma Ammarun da suke kiransa dashi tini dan haka ransa baci yake idan yana kallansu gwara kawai su nema aiki komai qanqantar albashinsa.

Numfashi Maheer ya sauke yana zaunawa gefen Ammar din yana kallan yanda su duka suka zuba masa ido da baki da hanci da komaima nasu suna jiran abinda zai fada
Gyara murya yayi shima ya fara jero bayani irin Wanda Ammar yaketa fesa musu harma da qari akan na Ammar din sbd yafi Ammar iya tsara zance take suka rude suka rikice gabaki kansu na neman zarewa da kuncewa.

Ammar ma zaro idanuwansa yayi akansu kawun Yana jiran jin amsarsu dashi dasu kamar zararru har gumin kuncewan lissafi suke fitarwa
Kawu Jibo da bayason sanya a harkan samu bude baki yayi zeyi magana modibbo ya taresa da cewa

"Ni zan dauki nauyin nemo aikin da dukiyata"

Da sauri kawu isiya yace

"Ai gwara dai a taru a hada kudin a tsakaninmu ayi neman aikin idan ta fashe kowa nada hannun jari a ciki kenan kawai"

Kawu Jibo da sauri ya share zufa Yana cewa

"Eh nima na yrda da hakan gwara kowa ya saka hannun jari a cikin neman aikin da neman kudin Ni hannu biyu zan saka ma"

Farin ciki ne ya mamaye Ammar da Maheer suka saki fuska Ammar na cewa

"Thank God sun hau zancen"

Rigima abin yaso zama saida Dad ya fito aka sake sabuwar shawara tukuna aka yadda akan kowa hannu daya zai saka na jarin da suke magana dan haka aka karshen magana.

Washe gari tinda safe modibbo da Maheer da Ammar sukai tafiyar cikeda zumudi.

Dad kuwa dole a ranar shine ya fita aikin da Maheer yakeyi sbd ya gaji da ganin Jannah da Ummah na aiki ya dakatar dasu daga komai yace su ringa zaman banza yafi masa kwanciyar hankali da nutsuwa.

Zuwansu Maheer binni kai tsaye lokoja suka fara fafutukar neman aiki bayan sun sauka a wani gidan haya me dakuna da yawa suka biya na wata daya,

Sabon tashin hankali da firgici Ammar da Maheer suka shiga a gidan sbd ganin wata sabuwar rayuwar da basusan ana yin irinta,

Idan Ammar zai shiga bandakin gidan se Maheer ya rakasa ya tsaya masa hakama shima Maheer din se Ammar ya tsaya masa sbd tsoron mutanen gidan ma sukeyi dan kowa a gidan kamar qasurguman yan dashi da makami babu ke kyan gani a fuskarsa ga fada da a take yake barkewa a gidan a ringa ciro makaman dake kusan sakasu zarewa da tsoro.

Shi Kansa modibbo daurewa kawai yakeyi yana danne tsoronsa sbd ya nunawa su Ammar jan wuya ne shima dan kada su cucesu idan an samu aikin.
#MAMUH
#JANNAH ZAD LIMBA
#AZIZ AY LIMBA
#ZAADENS
#LIMBAS
#NEW LIFE
#BEST LOVE
#BEST ROMANCE
#NEW TWIST

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 3

Ranar da suka fara fita aiki wuni sukai suna yawo se yamma sosai suka dawo da ledar bread da kosai se ruwan pure water dasu Ammar din sukejinsu kamar ruwan zam zam,

Haka suka kwana washe gari ma suka sake fita modibbo yakaisu gurare kafin ya tafi nasa wasu yan harkokin ya barsu suna sake yawon bincikawa cikin azabar rana da rashin isashen abinci ruwa kawai suke zubawa cikinsu,

A ranar ma haka suka gama yawo suka dawo gida a gajiye suka samu kosai da dankalin hausa sukaci suka hau baccin gajiya da azaba.

Rana a uku wani kamfanin gine gine suka nufa inda wani mutumin modibbo yayi musu hanya suka isa cikeda burin su samu abinda suke so.

Zaman jira suka fara zaune a bakin office din Wanda sukaxo ganin lokaci me tsayi batareda an nemesu ba.

Dago kai Maheer yayi yana kallan koina yana karantar yanayin gurin,

Tsari da yanayin gurin dama mutanen gurin ya saka Maheer da Ammar sauke ajiyan zuciya a Karo na babu adadi sbd Banda rayuwa da sauyin kaddara basuma San akwai kananun kamfani irin wainnnan ba da mutum ma zaiyi tinanin samun albashin da zai riqe kansa harma da wani.

Wani turanci director din gurin ya wuce Yana yi Wanda ya saka Maheer da Ammar kallan juna jiki a mace sbd wannan ko securities dake aiki kamfani ko gadin gidansu sunfi wannan ilimi da lafiyayyan turanci amma wannan ace shine director din da zasuyi aiki a qarqashinsa.

Ammar ne ya bude baki cikin damuwa da takaici yace

"A hakan sunyi degree da Masters zasuce ko?

Numfashi Maheer ya sake saukewa Yana cewa

"Koma basu taba shiga aji ba is their problem mudai mu samu aikin kawai musamu mu dawo field din yanda zamu fara sake gina Zaadens"

Modibbo dayake gefe sosai tsaye sbd baa bari ya shigoba shi tinda bada shine zaa bawa aikinba.

Se bayan sallar laasar suka samu akace su shiga bayan me gidan ya dawo sallah kenan.

Miqewa sukai suna dan sake nutsuwa suka shiga cikin nutsuwa.

Dagowa yayi Yana daga zaune kan kujera ya kallesu Yana amsa sallama da gaisuwansu Yana tinanin kamar yasan fuskokin nasu.

Ganin irin kallan dayake musu ya sakasu sauke kawunansu a tare cikeda jin damuwa na rufesu sbd sunsan tabbas kila ya sansu din koda a jarida da labarai ne tinda sunyi lokacinda babu ranar da a labarai baa fadar irin tarin nasarorinsu da arzikinsu hakama kusan kowa daya sansu yasan labarin kaddarar data samesu,
Wasu sun tausaya musu wasu kuma sunyi Allah wadai dasu,wasu kuma sunyi Allah ya qara musu azaba da kunci dan haka a cikin mutane yanzu basusan da wace fuska kowa ke kallansuba.

Numfashi ya sauke yana nuna musu gurin zama a hankali tareda karban folders din hannuwansu Yana cewa

"Kun dade kuna jira ko? Baqin ne da yawa hakama ayyukan"

A natse Maheer yace

"Ba damuwa ai munsan yanayin ayyukan"

Bude takardun yayi Yana dubawa ahankali
Akan sunayensu ya tsayar da idanuwansa tsawon mintina kafin ya dago ya kallesu a natse tukuna ya sake maida idanuwansa akan takardun Yana dubawa.

Abinda ya ganine a ciki game da irin girman ilimi da tsagwaron karatu da experience da suke dashi ya sakasa jin ganganci ma ne a gurinsa daukansu aiki a gurinsa sbd ba bata lokaci yake ganin zasu dokesa su zarcesa sedai ya koma kallo.

Dan haka ajiyar zuciya ya sauke yana rufe takardun ya kallesu da dukkanin nutsuwarsa yace

"Well gaskia a yanzu ba kowace irin damar dauka aiki tako ina
Mun riga mun cike slots namu Wanda ko zaa samu wata damar ba yanxu kusa kusa ba so ina me baku hakuri sbd Kunyo tafiya me tsayi"

Numfashi me dumi suka sauke ahankali idanuwan Ammar na sauyawa ahankali zuwa ja sbd baqin ciki da damuwa da wani irin sanyin jiki

Maheer ma cikin karfin hali da juriya tareda hadiye damuwarsa ya bude baki yace

"Ba damuwa,thank you so much"

Miqewa sukai suka nufi kofa Ya bisu da kallan tausayi kafin ya bude baki yace

"Kunga ku dawo na fada muku wata damar idan kunaso"

Dakatawa sukai a tare tareda juyowa a natse suka sake zauna suna jiran bayaninsa.

Ajiyan zuciya ya sake saukewa Yana fuskewa kai tsaye yace

"Akwai securities na gate da masu aikin cikin gida da masu aiki da ake nema a wani kamfani Zaa kai gidan wani baturen Alh da baa qasar nan yake ba,
Masu aiki da securities da ake nema wainda sukeda ilimi me zurfin gaske akeso sbd yanayin familynsa da turancin suka fi ji,
So a taqaice dai masu ilimi irinku ake nema idan zaku iya
Slots din na nan amma sai anyi muku interview so if zaku iya yayi muku zan iya gabatar daku a kamfanin da ake neman"

Zuba masa idanuwa Maheer da Ammar sukai idanuwan na jajir sbd wani irin baqin ciki da qunci daya cike kirjinsu da zuciyarsu da maganganunsa wai securities masu gadi fa kenan kuma har sai an musu interview a gidan wani Wanda bayama kasar gadin gidansa zasuyi abanxa kafin ya dawo din.

Ganin yanda idanuwansu sukai jajir na Ammar hadda wasu zafafan hawayen qunci da dacin zuciya ne suka cikasu
Bude baki yayi sbd ya sake fahimtar dasu yace

"Karku damu aikin ba wani aikine me wahala ko yawa ba
Zakuji dadinsa na tabbatar sbd a bayanin gidan mansion ne sabo da aka kammala a watan nan hakama kwata kwata fa basa qasar,
Matarsa da zai aura ce baturiya shiyasa dole se masu zurfin ilimin irin naku,
Hakama a cikin mansion din akwai bangaren masu aiki da da zaku zauna acikin kwanciyar hankali da wadata tareda jin dadin gaske,
And idan kunada mata ko kanne mata kuma sunada ilimi irin naku duka sauku cike slots din sbd ku samu zaunawa dukanku a cikin mansion din bangarenku na masu aiki sbd samun nutsuwa
Daga karshe kuma albishirin da zanmuku albashin nada tsananin tsoka da girman gaske Wanda duk aikin da zaku samu na kamfani bazaku samu albashi me Kyansa ba"

Ammar kasa cewa komai yayi ya miqe hawayen idanuwansa na gangarowa yafice kirjinsa na masa wani irin nauyi,

Hannuwansa yasaka Yana share hawayensa da suka gangaro Yana jin zancen na sake yankar zuciyar ta yanda bama akansu zancen ya tsaya ba ace wai idan sunada kanne ko mata suzo suyi aikatau dasu,

Tayaya zai iya kallan Jannah a matsayin maid tana aikin aikatau a karkashin wata macen?

Tayaya zasu bari Ummah tayi aikatau a qarqashin wata bayan yanayin lafiyarta ma dasuke lallabawa dan su samu su farfado su nema mata lafiya da duk abinda zasu tara.

Maheer ma dago idanuwansa da sukai jajir yayi ya kalli mutuman ya bude baki ahankali yace

"Mun gode bama buqtaan hakan zamu ci gaba da neman aikin a wani gurin"

Miqewa yayi shima ya fice yana danne radadin da zuciyarsa ke masa.

Modibbo na ganinsu hankalinsa ya tashi jikinsa yayi sanyi sedai kafin ya juya ya bisu secretary din office din yazo yace ana kiransa.

Modibbo na shiga office din ya zube qasa yana gaidasa cikeda girmamawa.

Amsawa yayi kafin ya sake korowa modibbo zancen dallah dallah da irin tarin kudin da zasu ringa samu a aikin kafin ya ciro katinsa ya bawa modibbon yace

"Ga numbern wayata nan idan kunje gida sun sake shawara akan zasuyi saiku nemeni"

Karba modibbo yayi da sauri yana rudewa akan jin kudi da alkhairin da zaa iya samu a aikin idan sunyi.

Kudi ya ciro dubu goma ya bawa modibbon yace

"Gashi ku hau mota sai naji daga gareku,idan kuma kunja lokaci zasu iya rasa damar sbd aikine da duk me wayo ya samu zaiyi gaggawan karba"

Godiya modibbo ya hau yi Yana rawan jiki kafin ya fito yana jin idan badan masu zurfin ilimi da akace ana nemaba da babu abinda zai hanasa tattaro su Garba dasu isiya suzo su karba aikin amma ko su Ammar din wlh ba barinsu zaiyiba sai sun karbi aikin nan koda asiri ne.

Yana fita tini su Maheer sun fice daga kamfanin zuciyoyinsu cikeda daci da radadi me zafi.

Acaba suka tara su uku sukai overload suka wuce masaukinsu kowa zuciyarsa cikeda tinani me nauyi Musamman modibbo daya matsu daya koma ya fayyacewa su isiya wannan samu da rashin dasu Maheer ke kokarin janyo musu dan rashin tinaninsu,
To wlh tsaf zai gama zugasu da takurasu saiya tabbatarda sun karba aikin dukansu har Jannah tinda itama tanada ilimin da akeson gwara suje suyi aikin ai yafi zaman banza.
#MAMUH
#BEST LOVE
#STEEZ
#ROMANCE
#LIMBAS
#ZAADENS

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*

Book 2
Chapter 4

Suna isa gida Maheer jin yayi gabaki daya garin ya fita ransa kauye ma kawai yake son komawa sbd zuciyarsa ta huce daga radadin datake masa,

Ammar ma jin yayi kamar ya hakura da neman aikin gwara su fara wata sanaar su fara Gino kansu daga nan sbd baa taba cin fuska da mutuncinsu kamar yau din ba da zaa kalli girman takardunsu da babu inda ko a ido zaa samu ganin irinsu ba ace wai zaa basu aikin securities a matsayin masu gadi Jannah da suke gwagwarmayar neman komai dan inganta rayuwarta data Ummah ace suma a matsayin masu aiki,wace irin cin mutunci da tozartawa ce wannan?

Modibbo ganin yanayin da suka shiga ya saka ya dakata daga musu magana ya bari sai sun koma gida tukuna amma kam wannan aikin shi a gurinsa kamar anyi an gama ne Banda rashin godiyan Allah irin nasu tayaya zaka samu aiki irin wannan ka tsaya wani duba darajar kai da duba girman iliminka,

Banda sun samesu masu zuciyar tausayi da duba zumunci uban me zai saka su karbesu su basu gurin zama Harma da abubuwa da yawa harda gurin nema da basu damar sanaa tinda su a lokacin da suke cikin daularsu basu taba tinawa ma da akwai dangin kakarsu kakarsu a kauye ba saida suka hadu da qwallon shegen da baya barwa Allah ya fisu zama dan ta'adda ya ruguxasu tukuna suka nemesu.

Har dare babu me walwala a cikinsu sunyi sanyi sosai haka suka kwana bama tareda sun nema wani abincin kirki sunciba.

Washe gari suka so komawa amma Maheer ya daure ya dangana suka sake fita neman aikin Wanda kamar hadin baki babu inda suka samu komai sai wulaqancin dayafi na farkon dan akwai inda aka daukesu amma wai shi Maheer din driver shi kuma Ammar security a kamfani.

Modibbo ganin hakan yasa suka aje maganar aiki suka bisa sabgar kasuwancinsa data kawosa suka koma yawon kasuwannin hatsi da dabbobi a haka suka cike kwanakinsu suka tattaro suka dawo.

Dan abinda ya rage musu na canjin da suka samu a kasuwa tareda modibbo suka siyowa Jannah da Ummah sabin takarmi da dogayen riguna masu dan kyau da turare da sabulun wanka me kyau da toothbrush da sabon brushes na dukkaninsu su biyar sbd iya kokarinsu basa son Jannah ta rasa kyan sigarta ko yayane bazasu iya bari ta koma abar tausayi ba tinda sun fito zasu nema komai su kuma qarar da koman akanta da Ummah.

Jannah ce ta fara samun labarin isowansu a bakin yaran gidan daketa ihun modibbo ya dawo dan haka ta wanke hannunta ahankali daga gama gyara daure dogon gashinta da fatma ta gama mata kitso me kyau.

Kofar shigowa bangarensu ta kalla daidai lokacinda Ammar ya fara sako kai da sallama ta sake murmushi me kyau da nutsuwa na farin cikin ganinsu zuciyarta na sanyi me dadi ta karbi babbar jakar hannunsa tana cewa

"Welcome Ammar Zad"

Sanyi daya mamaye zuciyarsa ne na saukan muryanta kunnensa da yanda haryanxu take kiransa yake kashesa akanta take quncinsa ya narke yabar kirjinsa murmushinsa me kyau shima ya bayyana yana qarasawa ya zauna a kujeran data tashi Yana cewa

"Thank you Jan,
Yaya kauyen nan?
Ina Ummah ne ta shiga?

Hannu ta miqawa Maheer suka gaisa Ya jata zuwa shimfida suna kokarin zama Ummah ta fito dgaa daki tareda Dad da zai fita suna ganinsu Ummah ta sake fuska sosai tana kallan Ammar da shima ita yake kalla Yana nuna mata gefensa taxo ta zauna ya fidda Apple Guda biyu daya siyo mata ya miqa mata Yana cewa

"Ci wannan kiji yafi wancan mangwaron nasu garba me shegen tsami da saka ciwon ciki"

Cikin farin ciki me tsanani Umman tace

"Da gaske kake?
Wannan yafi wancan dadi kace??

Gyada kai yayi yana dariya

Juyawa tayi ta kalli dad ddaa farin ciki sosai a fuskanta alamar hakane

Yana dariya cikeda kulawa da wani irin sanyin kaunarta dake cikeda zuciyar Dad din ya gyada mata kai yace

"Yes kici zakiji"

Maheer ta maida kallanta akansa har lokacin farin cikinta a bayyane yake

Dariya shima yayi Yana gyada mata kai alamar eh

Zata kalli Jannah
Jannah din Tai saurin karbewa tana cewa

"Bara na wanke muji ko Ummahna"

Da sauri Umman ta miqa mata dayan tana cewa

"Wanke duka mu cinye"

Maheer dake kusa da ruwa ne ya miqo musu Yana cewa

"Ba kudine ai da ansiyo da yawa tinda nasan Ummah zata so shi sosai dan nima bana son suna shan mangwaron nan kwata kwata"

Jannah cikin kulawa ta bawa Ummah tana cewa taci.

Dad ne ya kalli Maheer Wanda shima shi din ya kalla kafin suka kalli Ammar suka miqe dukkaninsu suka fice zuwa waje.

Suna fita Jannah ta bisu da kallo sbd tin shigowansu taga damuwa boye a tattare dasu.

Suna fita masallaci suka fara nufa sukayo sallar laasar kafin suka dawo a hanya Maheer yakewa Dad bayanin abinda ya faru.

Shiru Dad yayi zuciyarsa na sanyi da damuwa kafin yace

"To Allah yasa hakan shine mafi alkhairin ya kuma kawo mana wata mafitar"

Amin" suka amsa dashi suna qarasawa gida.

Abinci suka ci da daddaren kafin suka fidda siyayyr da sukayo musu,

Fira suka hau yi hankalinsu kwance cikeda kulawa da juna har dare sosai kafin kowa ya shige.

Da sassafe Garba ya shigo bangaren yayi sallama ya sanarda Dad su Modibbo na son magana dashi.

Fitowa Dad din yayi daga daki Yana saka hular sanyi a Kansa sbd akwai sanyi ya fice Maheer na bayansa Ammar be tashi ba hakama Jannah da Ummah.

Tin daga nesa Maheer ganin irin kallan dasu kawu ke jeho musu da irin yanda suka zauna babu me faraa a fuska ya san akwai inda aka samu matsala.

Dad a natse ya qaraso yai musu sallama ya nema guri ya zauna suna gaisawa.

Maheer ma gaidasu yayi cikeda girmamawa kafin ya zauna dga gefe kan dutse.

Shiru gurin yayi tsit kafin Kawu Jibo ya bude baki yace

"Dzad kasan da labarin su Mahe sun samu aiki me kyau da asirinka da nasu harma da namu zai rufu sunqi karba sbd girman kai da ganin sunfi karfin hakan?

Kai tsaye Dad yace

"Wane aikin ne wannan??

Modibbo ya karbe da cewa

"Aikin securities me kyau da albashi me tsokar gaske"

Numfashi Dad ya sauke yace

"Ni bana takura yarana akan abinda basaso ko basuyi niya ba sbd kawai ina cikin talauci,
Idan har tin acan since bazasu iyaba to shikenan din bazasu iyaba"

Wani kallo kawu isiya yayiwa Dad din cikeda mamaki da siqewa tareda takaici yace

"Kenan dai sun fada maka kuma ka goya musu baya?
Harkar samu?
Harkar ci gaba sbd kada mu lasa arziki shine kuka taru kuka yanke shawarar bazasuyiba"

Kawu Jibo daya gama cika shima da baqin ciki kai tsaye yace

"To Ni kawai aban kudina dana bayar bazan iya wannan kayan baqin cikin ba tin yanzu anfara kafin ayi nisa,
Dubu sittin cif a miqomin abuna yanxun nan inada abin yi dasu"

Kawu isiya ma cewa yayi

"Eh gaskia indai bazaa karba aikin da aka gani a kasa ba nima aban kudina bazan iya jira ba dan ba ranar samun wani aikin gwara aban na fara wata sanaar dasu kawai"

Modibbo daya rasa abin fada kallan dad yayi ya gyara zama Yana tattaro nutsuwarsa yace

"Dzad ka nutsu ka duba lamarin rayuwar dake gudana a yanzu,
Kai din baya ba kai bane a yanzu
Hakama yayan naka da sunan da mutuncin da matsayin duka basu bane a yanzu,
A baya idan akace Zaadens magana ake ta masu qasa da wajen qasar ma amma ka duba a yanzu a ina kake?
A ina rayuwa ta dawo da kai.

Maheer ya kalla yace

"Kai Mahe inace cewa kukai zaku sake farowa daga farko ku sake gino Zaadens da guminku da gwagwarmayar da duk ya kamata,
Idan da gaske hakan ne to banga dalilin qin karban aiki kowane irri bane indai bana haram bane ko sabon Allah,
Aikin nan fa bana dindindin bane ku karba ayi na dan lokaci ana samun abin Gina kai saiku ajiye ku fara duk kasuwanci ko aikin da kukeso,
Dan haka xabi dai anan biyu ne kodai ku karba aikin nan ku samu damar fara kafa kanku kokuma ku tabbata anan kauye cikin wannan rayuwar da bakwason ku mutu a cikinta,
Hakama dukanmu idan lamarin bazai yiyuba muna buqtaan kudinmu a cif cif ba bata lokaci"

Shiru Dad da Maheer sukai jikinsu a mace zuciyoyinsu a jagule da maganganun su Kawun.

Ajiyan zuciya Dad ya sauke kafin ya kalli su Kawun yace

"Ba damuwa inshallah zamuyi shawara muga abinda zai yiyu gameda biyan kudin"

"Ah ah bawai shawara ba muji shiru,
Aikin nan dai modibbo yace kada a wuce dan lokaci Idan ba hakan ba zaa rasa dan haka ayi me yiyuwa asan nayi"

Kawu Jibo ya fada hakan Yana sake matse fuska.

"Inshallah zaa kokarta kafin lokacin" Dad yace Yana miqewa yabar gurin Maheer na bin bayansa.

Suna isa ciki babu Wanda yayi magana saima shiri da sukai suka fice bayan sun karya da madara da zafi da waina

Se yamma sosai suka dawo,
Dare nayi suka ci abinci gabaki dayansu a tare kafin Dad da Maheer suka sanar da Ammar abinda yake faruwa da kuma tafiyar da zasuyi goben hadda Dad su sake bazama neman aiki koda bana office ba koda na manyan shaguna ne haka ko supermarket ganin sukeyi gwara shi akan aikin gadin.

Washe gari tinda sassafe suka sake Aron kudi a gurinsu modibbo suka wuce.

Tinda suka tafi Jannah ta maida hankalinta ta duqufa a gurin adduar Allah ya zabar musu abinda yafi zaman alkhairi koda aikin gadin ne sbd ta jima da ajiye matsayinta na princess Jannah Zad koina ne indai zata zauna ta rayu da familynta cikin kwanciyar hankali batada damuwar komai.

Kwanansu Dad goma sha shida suka dawo babu Hasken komai a tafiyar sbd duk inda suke saka ran samun wata mafitar babu,

Aiki harna tsaron shaguna da wasu guraren sun nema basu samuba gashi duk bashin da suka laftawa kansu ya qare ba aikin.

Bayan dawowansu su kawu suka sake bude wuta akan a basu kudinsu har abin yakai anfara samun matsala da damuwa sbd tini abin ya koma hadda gori da fade.

Dad ne ya samu su Kawun a Karo na ba adadi cikin nutsuwa ya sake rokonsu akan su qara musu lokaci.

Budar bakin Garba dake tsaye cewa yayi

"Baba ni idan zaka yadda inason Jannah a bani aurenta na bada dukiyar aure se abiya bashin da dukiyar Harma ayi canji"

Wani Amai ne me karfin gaske ya kubcewa Ammar dayake bayan Dad tsaya jin maganar Garba kamar saukar Mummunan qarnin kifin daya kwana cikin ruwan jini.

Maheer ma dagowa yayi yana yiwa Garban wani mummunan kallan baqin ciki me tsananin gaske.

Dad su kawun ya kalla yaga babu Wanda ya shiga mamakin zancen da alamar sun dan da maganar dan haka take yaji gabaki daya kauyen ya fita ransa fit sbd gwara mai aikin gadi daya nakasta rayuwar Hasken idaniyarsa.

Bude baki modibbo yayi yace

"Daman ta isa harta wuce aure kuma kila sbd itane basason aikin gadin sbd bazasu iya barinta ba hakama bazasu iya barin taje aikatau ba dan haka gwara AUREN nima na amince dashi"

Kawu Jibo ma kai tsaye yace ya amince shima.

Dad kuwa idanuwansa ne sukai jajir ya saukesu akan su Kawun sbd ya gama fahimtar toxartasu kawai suke son yi sbd suna rabe a gurinsu dan haka gwara ma su tattara din su qara gaban,
Bude baki yayi zaiyi magana Ammar da idanuwansa sukai jajir hannuwansa na rawa sbd wani irin azababben kishin dayaji Yana neman kashesa take ya riga Dad cewa

"Dad pls mubar nan koda a aikin gadin ne zan iya mutuwa idan naci gaba da zama anan"

Maheer ma kai tsaye ya amince da hakan Wanda shima Dad ya gwammace su tattara su tafi gurin aikin tinda zasu zauna gabaki dayansu guri daya cikin aminci.
#MAMUH
#BEST LOVE STORY
#AZIZ AY LIMBA
#ZAADENS
#JANNAH LIMBA

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 5

Da mamaki dukkaninsu kawu suka kallesu kawu isiya Yana cewa

"Au dukiyar aurence bazaku iya biyan bashi da ita ba kokuwa aurar da ita dinne baku tashi ba?"

Kawu Jibo ne ya qarasa dora masa zancen da cewa

"Kokuma Garba dinne bazasu iya bawa Yar gwal din ba kuma ba"

Da mamaki kawu isiya ya kalli Dad yace

"Aa wane su su fada hakan tinda a yanzu babu binda akafi karfin Garba dashi tinda shine yake da abinda basada shi a yanzu"

Daqyar Ammar yaji bugun zuciyarsa na dawowa daidai ya juya gefen Garba zai kallesa ya fasa sbd zuciyarsa zata iya bugawa kokuma zai iya shaqesa ya rabasa da duniya gabaki daya dan haka su kawun ya kalla yana kokarin dedeta numfashinsa yace

"Kawu kwata kwata fadar auren ne ma a tsakaninsu tamkar mugun sabo me zunubi ne sbd ko mun rasa komai a duniya Jannah tana nan a matsayinta na na sarauniyar Zaadens kuma darajarta ta wuce rayukanmu duka,

Duka wannan gwagwarmayar da aikin da muke nema sbd ita da Ummah ne kadai,
Duka abinda zamu nema mu samu harma mike son sake gina kanmu sbd mu basu rayuwar jin dadi d kwanciyar hankali ne kawai bawai munayi ne dan kanmu ba,

Hakama Jannah tamkar matar aure ce sbd ni Ammar Zad nine mijinta dan haka sunan matata ma ya fita a jerin hada sunanta da sunan wasu"

Maheer da Dad dake cewa yayi shiru baiyiba saida yakar karshe jikinsu mutuwa yayi da jin haryanxu Ammar Yana kan bakarsa ta auren Jannah wanda a yanzu kam zasu iya fuskantar komai dan aura masa ita ta yanda zasu rayu a guri daya dukkaninsu a duk inda rayuwa zata kaisu suna tare.

Afusace kawu isiya yace

"Dzad kana kallan danka Yana mana rashin kunya Yana nuna mana kunfi karfin hada zuria damu ko?
Waton Kun rayu a cikin arzikinmu idanuwanku sun bude yanzu kunada maganganun fada,

Ita Jannah din Banda farar fata da turancin banza sai sanyin jiki mara amfani kullum mace kamar amaryar Aljanu itace zaace tafi karfin auren danmu?

Maganar ta sosa zuciyar Dad da duka Zaadens din sosai sbd har abada Jannah a zuciyar Dad babu wani abu daya kaita daraja a gurinsa kaf kuwa a duniyarsa wanda yasan hakan shine babbar jarabawarsa sbd ko a yanzu da baida komai idan ya kalli Allah bai rabasa da abinda yafi so a duniyarsa fiyeda komaiba saiyaji shi baima shiga jarabawar komaiba,
Sai kuma Ummah a yanzu da haka kawai yake jinta itama a tsakiyar ransa saima yanajin kamar auren kuruciya ne yayi sbd a baya dukiya da daula tareda yawan yawon kasashe dayake bai samu time sosai ya bawa Mimi ba dukda irin son da itama yake mata me karfi Musamman da ciwon Jannah ya bayyana suka fara gwagwarmayar neman lafiyarta gabaki daya bai sake samun nutsuwan rayuwa data sukunin zama da Mimin ba yanda ya kamata har saida Jannah ta samu zuciyarsa Ummitah Limba,

dan haka a yanzu da Ummah take rayuwar aure dashi tamkar yarinya karama sbd yanayinta yasaka rana tsaka Allah ya sakata a tsakiyar zuciyarsa itama dan haka a rayuwa yanzu bayan Jannah Ummah ce mutum ta biyu da zai jure komai munin kaddara akansu sbd haka kuma bazai iya daukan kowane cin mutunci akansu ba.

Kawu Jibo bazai iya doguwar hayaniya ba sbd baqin ciki da bacon rai daya gama rufesa yace

"Kai isiya kanada karfin batawa ne akan wannan lamarin ne ai amma ga abu a bayyane kai tsaye idan bazaa bawa Garba auren Jannah ba a bamu kudinmu a yanzu a take idan yaso su aura mata sarkin larabawa mugani dan babu ubanda talauci baya sakawa ciwon hauka tinda ai suna da ma me haukar ai"

Miqewa tsaye Dad yayi batareda yace komaiba ya juya yabar gurin sbd yanda zuciyarsa tayi mugun daukan zafi hakama bayajin yanada energy din batawa gurin magana dasu kawun sbd kwata kwata yaji ya tsani cigaba da zama da iyalinsa a cikinsu.

Maheer ne ya kallesu tareda tattaro gabaki daya kudin dayake jikinsa ya ajiye gabansu ya bude baki cikin danne daci da baqin cikin dayake ransa yace

"Sauran kudinku din inshallah bazaa a kwanaki biyu zamu hada muku"

Kawu Jibo ne ya rufe ido yace

"Wlh tallahi kwandala kai ko sisi idan babu a kudina ni bazan karba ba"

Kawu isiya kuwa daukan kudin yayi ya kirga a nasa dubu Tara ne babu dan haka ya dunqule kudin ya saka aljihunsa yana cewa

"Na biyo dubu tara kuma nima wlh kwana biyu na bayar a hadomim dubuta Tara cif a ban idan ba hakan ba har birnin tarayyar zan samu mutum ba abinda ya damen"

Maheer bai iya cewa komaiba ya juya yabi bayan su Dad da suka wuce.

Koda Dad ya shiga gidan kai tsaye Jannah da Ummah dake zaune suna nade kayansu na wanki da Maheer ya wanke musu ya kalla fuskokinsu cikeda kwanciyar hankali da farin cikin kasancewa tareda ahalinsu.

Ajiyan zuciya ya sauke me zafi Yana rintse idanuwansa yana rokon Allah yayi masa arzikinda zai dawwamanar da farin ciki da kwanciyar hankali a wainnan fuskoki da zuciyar tasu.

Jannah ce tafara dagowa da fararen idanuwanta ta kalli Dad din kafin ta kalli Ammar daya shige dakinsu Yana dafe da kirjinsa dake masa wani irin nauyi sbd ambatar auren Jannah din kadai ya dawo masa da tinanin da ko a lahira yana fatar kada Allah ya hadasa da LIMBA,

LIMBA shine sunan da har abada harya bar duniy baya fatan ya sake ji bare tinawa,
Yana kullum yanda yake rokon Allah kada ya sake hadasu da ko me sunan AZIZ bare Limba baya rokon Allah yayi musu mafita kamar hakan,

Bazai iya sake rasa Jannah ba akowane hali dan hakama kawai a yanzu yake jin zuciyarsa ta bushe qamas gwara yaje aikin security din suje inda zasuyi rayuwa a natse ba barazana ko gori bare kauyanci da dabbancin da akeson kawo masa wai jannarsa da auren wani.

Tasowa Jannah tayi ta nufo Dad dinta ta kama hannunsa ahankali cikin kulawa tace

"Dad,akwai damuwa ne?

Kallanta yayi ahankali tareda sake damke hannunta ahankali cikin nasa yana jin kamar ya maidata cikinsa ta dena fuskantar kowace irin matsala,

Wai yau Princess dinsa ce a cikin wannan rayuwar bayan wani qaton banza ya mayar masa ita bazawara.

Rufe idanuwansa yayi ya bude yanajin radadin tinawa da Wanda ya maidata bazawarar kirjinsa na nauyin da haryanzu bai manta yanda azabarsa take ba sbd a rubuce a kaddarance AZIZ LIMBA shine kaddarar ZAADENS da har abadan abada komai nisa da yawan da zuriar Zaadens zasuyi bazasu manta ko goge wannan tarihin daya riga ya kafu ba.

Ahankali Dad din ya sake sauke idanuwansa da sukai sanyi akan fuskan Jannah Wanda fuskanta take bayyanarda a kowane hali zata iya rayuwa indai dasu ne duk da akwai ciwo da kunci me zurfin gaske a zuciyarta datake rufewa zata kuma cigaba da rufesa ta ringa hadiye quncin da radadin ita kamar yanda takeyi duk tsawon wannan lokacin batareda ta taba barin ansan asalin menene ciwon dayake cintaba a yanzu harya fara taba lafiyar zuciyartaba.

Cikin kunyar yarsa daya kasa bawa rayuwar data kamace ta yakega ya sake kalleta cikin sanyi ya bude baki yace

"Jannah kiyi hakuri na gaza a matsayina na uba....

Rungumesa tayi ahankali tana hanasa karasa maganar sbd itace ta kasa a matsayinta na 'ya sbd itace ta bude musu kofar duk wannan abinda yake faruwa dasu wanda kuma haryanzu take cikin mummunan kaddarar data kasa fizguwa daga zuciyarta dan haka itace take jin ta kasamtowa Yar halak ga iyaye da yan uwanta.

Dad sake mutuwa jikinsa yaci gaba da cewa

"Kome zai daidaita inshallah amma ayanzu muna buqtaan barin nan zuwa wani gurin wanda zamuyi aiki a karkashin wasu Wanda ina jin nauyi da kunyarki akan hakan Jan"

Girgiza kai tayi ahankali tana dagowa ta kallesa idanuwanta na cikowa da hawaye tace

"Dad Jannah ta dade da karban rayuwar da duk taxo gabanta matiqar bata sabon Allah bace,
Nayi aiki a karkashin wasu,
Nayi aikin gidan abinci nida Ummah,
Munyi aikin wanke wanke sbd mu tsayu da kafafunmu da tsira da mutuncinmu harmu samu haduwa daku dan qarasa rayuwa cikin amince dan haka Dad indai ina tareda ku babu aiki da wahalar da bazan iya jurewa ba,

Dad duk inda zaku tafi zamu iya jure koman wuya dan rayuwa tareda ku nida Ummah dan haka Dad har abada ka sani baka taba kasawaba a matsayin ubana ba,
Babu uba irinka a rayuwata kaine uban dayafi kowane uba a duniya,
You are my one and only hero
And you'll forever be,I love you Dad."

Rungumeta yayi Yana jin dukkanin kuncinsa na yayewa karfin gwiwa da zuciyar daya rasa suna dawo masa yanajin zai iya aikin dayafi security qanqanci sbd Jannarsa tinda tana tareda shi.

Hannu ya miqawa Ummah dake zaune tana kallansu hakanan jikinta na sanyi itama cikeda kauna yace mata

"Come"

Batasan me yace ba duk da dukansu suna kokarin mata turanci sbd yawanci idan suna tare turancin sukafi wa juna dan haka ta taso ahankali cikin farin ciki ta kama hannun daya Mika mata ya janyota ya hada da Jannah din ya rungumesu Yana sake samun nutsuwan zuciyarsa datake ciki da daci da qunci.

Ammar ne ya shiga dakinsu Jannah din ya hada musu kayansu itada Ummah guri daya Yana kokarin rufe jakar kayan idanuwansa suka sauka akan rigar data sakasa dakatawa Yana zuba idanuwansa akanta sbd rigar Maza ce hakama mazan se wanda yakeda duniya a hannunsa sbd designer ce ta asalin Balmain.

Hannunsa daya dan fara rawa kadan yakai akan rigar zuciyarsa na nauyi ya janyota ahankali daga qasan kayanta tin bai qarasa bude rigar ba qamshin daya doki hancinsa daga cikin rigar ne ya sakasa sakin rigar da sauri hannuwansa na wata irin rawa numfashinsa na sarkewa sbd sbd asalin qamshin Jannah ne na baya a jikin hade dana AY LIMBA Wanda shima bazai taba mantasa ba koda zai mutu ya dawo sbd qamshi ne daya zama gubar numfashin rayuwarsa gabaki daya.

Bugun zuciyarsa tsananta yayi tareda wani irin sarawan kai da rawar hannuwa Wanda yake nuni da ciwonsa daya kwanta fiyeda shekara Yana neman tashi tinda ba cikakkiyar lafiya ya samu ba daman.

Takarda ce idanuwansa suka hango masa a cikin rigar a boye Wanda ma envelope ne kalar milk da rubutun golden mw dubu daga can qasa Wanda kai tsaye yasan envelope din LIMBAs ne sbd kaf kamfaninsa haka rubutun yake milk envelope ko paper da golden a jiki uLIMBAS Wanda duk duniya babu wanda yasan me u din farkon take nufi bayan Sayd d mamansa sai yanzu ne duniya tasan Ummitah take nufi.

Nauyi kirjinsa yayi masa sosai yanason kai hannu ya dauki envelope din yaga abinda yake ciki sedai kuma yanda Kansa ke neman juyewa da bugawa tsabar wani irin kishin dayake jin kamar zai kashe basu bari ya iya motsawaba se rawa hannuwansa keyi har kafafunsa...

Jin qamshin LIMBA na gauraye dakin take yaji Yana suffocating da rarrafe ya isa kofa baya gani sosai ya fado tsakar gidan Yana Jan numfashinsa dayake neman daukewa.
#MAMUH
PLS AYI MUN AFUWA BAN NUTSU BANE WLH HARYANXU AMMA INSHALLAH DAGA YANXU POSTING YA KOMA DAIDAI DA YARDAR ALLAH.

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 6

Babu wanda ya lura da halin dayake ciki sbd shi Kansa ya hana a gane din kokarin boye halinda yake cikin yakeyi sbd barin ciwonsa ya tashi a wannan halinda suke ciki na rashin mafita kamar qara jefasu cikin masifane yakeyi,

Sedai kuma a dayan bangaren tsoro da tashin hankali me tsanani ne ya shigesa na ganin Jannah na tareda abinda ya shafi LIMBA Wanda Kansa da tinaninsa sun kasa tinano masa me hakan ke nufi.

Maheer ne ya shigo Yana sake kallan Jannah da Ummah dake jikin Dad cikeda kulawa ya musu bayanin zasu sauya gurin zama ne sbd rayuwa na cikeda qalubale Yana son duk abinda zasu fuskanta suyi hkr komai zai wuce hakama kome rayuwa taxo musu dashi zasu taru su fuskanceta gabaki dayansu sbd sunada junansu kamar yanda asalinsu Allah ya halicce su da kaunar junansu fiyeda komai.

Jannah gyada masa kai tayi tana janyewa daga jikin Dad ta koma jikinsa tana sake jin kaunarsa kewan Saleem Zad na saka idanuwanta cikowa da hawaye masu tsananin ciwo da zafin da har abada bazata iya yafewa LIMBA ba idan har zuciyar Saleem bata kirjinsa tana bugawa.

Dad ma hakanan yaji kewan Saleem din ta rufesa yana fatan Allah yasa yana cikin rahama da hasken kabari.

Jannah ce ta wuce ciki lokacin tini Ammar ya rarrafa ya shige dakinsu shida Maheer yana kokarin dawo da kansa daidai.

Maheer ne ya shigo shima sedai lokacin Ammar din ya dawo daidai ya miqe yana sake hada sauran kayansu.

Jannah kuwa dukda taga kayansu a yamutse batai tinanin komaiba ta qarasa hada musu kayansu kafin ta fito ganin Ummah na gurin Dad har lokacin saita wuce can kuryar gidan gurin jamaar gidan dasuke shirinsu sosai su babu damuwar komai a tsakaninsu.

Acan cikin gida Jannah ta sanar dasu tafiya zasuyi amma bawai kwata kwata ba aiki ne suka samu dukkaninsu zasu tafi.

Damuwar sabo da sukai sosai da Jannah da Ummah da kuma yanda suke qaruwa sosai da Jannah akan abubuwa da yawa datake koya musu Musamman na tsaftace jiki dama tarbiya ya sake sakasu jin ciwon rabuwa da ita.

Fatma kuwa kusan tafi kowa shiga damuwa da tashin hankalin rabuwa da jannah sbd gabaki daya rayuwarta ta sauya sbd Jannah gashi tinda ta taso haka take ba qawaye ba sakewa harta auren qananun shekarun da akai mata ta fito ta dawo gida sai xuwan Jannah ne ya kawo walwala da sanin ciwon kai da zama mace a rayuwarta Wanda a yanzu ta zama macen da kusan yanda akeson Jannah hkaa ake sonta sbd daman itama tanada hasken asalin Fulani da jiki me kyau dan haryanxu data dade gida batai wani aurenba shekarunsu daidai da Jannah gashi duk da basu taba zaunawa sukai fira ko maganar aurensu da kowanne ya fito a cikinsa ba dukansu sun karanto boyayyan qunci da rufaffiyar damuwa a auren bayan.

Dan hakanne ma takejin shakuwa da nutsuwan datake samu da rayuwa a karkashin Jannah zata iya binta koina.

Se washe gari ne tafiyarsu sbd motocin fita daga kauyen tinda sassafe suke wucewa dan haka dole sai washe gari zasu wuce.

Dad bayason rabuwar damuwa dasu kawun dan haka da dare acan cikinsu yayi sallar magrib da ishai ya nutsu ya sake fahimtar dasu komai gameda rayuwarsa da iyalinsa da yanda rayuwarsu ta sauya ya dora da godiya sosai tareda basu hakuri tin daga cikin ransa ya kuma samu sun fahimcesa sun kuma sauko sbd kusan suma haka suke tsananin kaunar junansu su ukun duk da su dukan sunada tsananin son kudi amma kuma sam basa barin kudin na hadasu sbd basa iya barin komai ya shiga kaunar da sukewa junansu dan haka sun fahimcesa yanda ya kamata tinda kusan kaunar juna duk tsanani duk wuya basa taba iya son wani fiyeda nasu Kenan abin a zuriarsu yake.

Godia Dad ya sake musu sosai akan halacci da kaunar da sukai musu Musamman akan Jannah da suka riqe cikeda Amana da kauna da kulawa tsawon shekara Guda da basa nan da gurin zaman da suka basu.

Ammar da Maheer ya kira ya saka suma suka basu hakuri tareda godia
Su kawun suka yafe musu harma Garba da Ammar yaji ya tsana take sbd ya furta Yana son Jannah saida ya danne zuciyarsa yai masa godia sbd shine ya zama wanda ya tsaya masa ya basa kariya da kulawa harya iya rayuwa me tsayi a kauyen sbd badan Garba din ba da tini ya mutu da tsoro da tashin hankalin abubuwa da dama na kauyen.

Jannah ma taxo tayi godia cikeda girmamawa da kaunar datakewa su kawun sbd ita a gurinta sune bangon daya bata majingina a lokacinda batada sauran hope
So su modibbo sune mutanen da har abada bazata ciresu a wainda suka sake kafa sunan Zaadens dasuba.

Su kansu su modibbo Jannah itace sukafi kauna fiyeda shi Kansa Dad a cikin Zaadens sbd tafi kowannensu shiga rai da sanyin hali dan haka su kawu kudi suka ciro tareda galan biyu na madarar shanu me kyau suka bata kyauta tareda saka mata albarka suna cewa har abada ita din tasu ce ko basu taho ziyara sbd kowaba zasu ringa zuwa sbd ita Musamman idan ta samu mijin aure.

Murmushi tayi zuciyarta na cika da kewansu da jin kaunar da suke mata har cikin ranta.

Dad tareda su modibbo yaci abincin Daren ranar shima Ammar fita yayi da Garba zuwa ganin sauran abokan garban da sukaita dawainiya dashi yai musu godia yanajin sabon da sukai Yana taba zuciyarsa sbd sun kula dashi da zuciya daya batareda sun damu da basu taba saninsaba sunyi hidima dashi dan har wani kauye suke zuwa dashi me nisa akan jaki ko Keke sbd yasha ruwan famfo me kyau da sukaga baya wani iya shan ruwansu sosai.

Ayau ya sake jin ciwo da radadin mummunan talaucin dayake ciki sbd yaso yayi musu kyautar da zata sauya rayuwarsu gabaki daya,

Da a baya ne agogonsa daya kadai idan ya basu suka siyar sungama tsiya da xaman kyau bare idan ya dora hannunsa akan cheque ko Dollars idan zai basu baisan iya adadin dama zai iya basu ba sbd rama alkhairinsu gareshi amma duk da hakan ya musu alkawarin duk yanda rayuwa tayi dashi bazai manta dasu ba zasu sake dawowa garesu.

A cikin Daren su modibbo basu rabu da Dad ba sai dare sosai bayan sun yanke shawarar da Garba da Fatma zaa tafi aikin sbd duk aikin wahala ko karfin da basu saba dashi ba su garban suyi Wanda Jannah yafi karfinta kuma Fatma tayi.

Girgiza kai Dad yayi yace

"Indai zaa tafi dasu to zasuyi nasu aikin ne duka mu karbi halak din mu
Muma zamuyi namu aikin da karfin da muke dashi muci halak dinmu"

Da wannan shawarar aka kwana idan Allah yasa an dauki su Fatman a cikinsu Zaadens din shikenan suma sun samu Tara dukiyar da iyayensu zasu dangwali arziki.

A cikin Daren garba ya sake komawa yayi sabon bankwana da abokansa hakama shi da Fatma suka hau shiri.

Washe gari asubar fari dukkanin jamaar gidan suka tashi bayan sallar asuba babu Wanda ya sake komawa bacci.

Sabuwar madara aka dumama musu dukansu suka sha kafin suka fito ana jimamin rabuwa da juna suka hau mashin mashin aka wuce hadda su kawu da suka rakasu har kauyen da ake shiga mota suka wuce.

Hadda modibbo aka tafi sbd shine zai rakasu yaga har inda suke kuma ya kaisu gurin Alh Siddeq da Zai gabatar dasu ga kamfanin.

Shiru kowa yayi a tafiyar sbd kowa a yanzu jikinsa yayi sanyi sbd basusan rayuwar da zasu tararba kuma Wadda basusan wace iri bace datake saka zuciyoyinsu wani irin rashin sukuni da tsoro harma da fargaba.

Wuni Guda suna tafiya kafin suka iso a gajiye.
Kai tsaye gidan da dakinsu yake inda suke sauka suka nufa.

Kayansu suka ajiye suka fice sallah aka bar su Jannah a daki suma sukai sallolin dake kansu suka zauna suna kallan dakin shiru babu me magana.

Bread da kosai da shinkafa da wake Maheer yazo ya basu da ruwan pure water tareda maganin mosquito da ashana yace su rufe dakin dakyau idan zasu kwanta sukace to.

Abincin sukaci suka koshi Jannah tasha madaran shanu suka kwanta tareda rufe dakin dakyau.

Su Dad kuwa a masallaci suka kwana su dukansu saida sassafe suka dawo dakin suka karya gabaki dayansu a tare kafin kowa ya shirya suka fice zuwa office din Alh Siddeq din Wanda tin jiya suka sanar dashi zuwansu.

Koda suka isa shima kai tsaye su yake jira dan haka a bus din office aka daukesu zuwa wani lafiyayyan kamfanin da ya saka hankalin modibbo da Garba tashi harma da Fatma,
Su kuwa su Dad ganin tsarin kamfanin tin anan sukasan duk Wanda zaa kaisu gidansa da gasken tsayayyen Kansa ne tinda a gidansa baa wani jin hausa ace masu aiki ma sai masu degree da Masters akeso.

Gurin jira aka kaisu suka zauna Alh Siddeq kawai ya wuce ciki.

Bai wani jima ba dayake ya riga ya shigar da sunayensu d matakin karatunsu ya fito aka fara shiga dasu daya bayan daya dan interview.

Dad aka fara yiwa Wanda iliminsa kadai ya kashe baqon da aka dauko daga Lagos da tantance maaikatan kamfanin na daukan masu aiki ga manyan qasa kawai da Wanda kudinsa yakai.

Baa qasar yake ba tsawon 2years shiyasa bai wani San labarin Zaadens ba da abinda yafaru dasu dan haka take Yana yiwa Dad da Maheer da Ammar da Jannah ya saka hannu ya daukesu duka familyn batareda ma yayiwa garba da Fatma da Alh Siddeq ya tayasu rufa rufa aka shigar da sunayensu tareda approving na daukansu aka ce gobe zasu tattaro su dawo inda aka tanadar musu na zaa koya musu aiki na sati biyu kafin a miqa su 4&4 MANSION.

suna dawowa gida shiri sukai washe gari tinda safe suka isa kamfani aka daukesu da mota aka kaisu wani lafiyayyan gida me tsari da jin dadi daidai gwargwado kowa aka basa dakinsa Banda Ummah da aka baro gida tareda modibbo da wata da zasu barwa dakin idan sun tashi ta ringa kulawa da Ummah kafin su fito.

Da farko tsoro fatma ta ringa ji Jannah na taimaka mata hakama Garba dole Ammar ne ya ringa wayar masa da kai.

A cikin sati biyu an sauya musu suturar sakawa sbd bazasu da tsumma ba mansion din kamar yanda akace,
An koyar dasu ayyuka da dama hakama su Dad an koyar dasu nasu suna cika sati biyu cif harsun fara canjawa sbd sauyin guri me kyau aka daukoso zuwa mansion sedai saida aka biya dasu aka dauko Ummah Wadda Dad ya riga ya shigar da sunan matarsa ankuma bSa damar shiga da ita sbd idan aka rasasu bazaa taba samun candidates kamarsuba da iliminsu yakai.

4&4 MANSION shine sunan da suka gani baro baro a rubuce jikin qaton mansion dinda yaci uban nasu a lokacinda suna Zaadens dinsu.

Wani irin tsoro ne ya rufe Garba da Fatma Musamman ganin wasu irin samudawan securities na jamian tsoro zagaye da gate din.

Jannah kuwa 4&4 din ta zubawa ido ranar daurin aurenta n dawo mata sbd 4th April wato 4 ga watan 4 shine date da bazata taba mantawa ba rayuwarta.

Dauke idanuwanta tayi daga kan sunan tana lumshe idanuwanta tareda hadiye radadin daya tasowa zuciyarta sbd radadine datai alkawarin hadiyewa tabinne abinda yake kawosa har abada.

Ammar ma kalmomin ne suka tsaya suka soki zuciyarsa sbd sune numbers da bazai taba mantawaba.

Bude musu mahaukacin gate din akwai bayan angama duba takardun da aka kawusu dasu daga kamfanin.

Gate na biyu aka isa dasu Wanda daga shi suna shiga to shikenan sun shiga ba fita saida izini ko babban dalili.

Suna gani aka rufe gate na biyu rufe sunajin jikinsu na mutuwa sbd ta tabbata daga yanzu su Yan aiki ne dake karkashin me gidan nan da iyalansa.
#MAMUH
#BEST LOVE
#HOT LOVE
#HOT ROMANCE
#AY LIMBA
#ZAADENS
#CRAXYLOVE

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899
*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 7

Wata sabuwar duniyar da suka manta yanda take ne suka samu kansu ayau cikinta Wadda koda sun farfado basu taba saka ran zasu shigo cikinta ba a shekarun kusa kusa ba sbd gabaki daya 4&4 mansion turai ce kawai zasuce me zaman kanta a Nigeria dan kuwa tinda suka shigo gate din farko suka San sun shigo wata duniyar ce kawai ana rufe second gate kuma sukasan sun bar qasarsu a yanzu duniyar Familyn 4&4 suke ciki tsundum wadda babu komai a cikinta tukuna sai daular duniya da wata irin shiru da nutsuwa tareda kwanciyar hankali me sanyi da tsafta da suka ji suna samu.

Garba da Fatma da tinda Allah ya halicce su basu taba gani ko jin labarin irin wannan gidan ba da kusan komai nasa kashe musu ido yake hankalinsu mummunan tashi yayi sedai tsoron securities dake zagaye da gidan da bindigogi ya sakasu hadiye tsoronsa a cikinsu Wanda hakan ya ringa juya musu ciki.

Jannah da jikinta har lokacin yake a mace da sunan mansion din daya tinatar da ita rana mafi girma da muni rayuwarta itama hadiye radadin zuciyarta tayi tana jin wani irin ciwo a zuciya da kirjinta.

Ammar da bayan Jannah shi kadai ne ya riqe date din aurenta da LIMBA fes a cikin Kansa sbd shima bayan ranar rasuwar mahaifiyarsa ranar itace rana mafi muni da girman da bazai taba mantawaba a rayuwarsa sbd a wannan date dinne Jannah ta auri waninsa wanda a ranar zuciyarsa ta mutu a kirjinsa mutuwar da har yau bata farfado ba har sai ranar daya auri Jannah ta zama mallakinsa sbd baisan wane irin girman so yakewa Jannah Zad ba.

Dad da Maheer kuwa ajiyan zuciya suka sauke atare cikeda samun nutsuwan zuciya da ruhi sbd sunzo inda zasuyi aiki da karfi da lafiyarsu sbd Jannah da Ummah su samu rayuwar jin dadi da kwanciyar hankali sbd anan tsaro da kariyar da Jannah da Ummah zasu samu ko a nasu mansion dinne iyakacinsa kenan sbd ko qara da hayaniyar waje ko kadan baka jiyowa duk da wata irin anguwa ce da kusan tsaro da tsari tareda rashin hayaniyarta zai tabbatar maka da sai Wanda yakai iya kaiwa yake zaune a cikinta.

Hannun Ummah dayake hannun Dad ya sake riqeta da kyau Yana kallanta cikin kulawa zaiyi magana Chief ta maaikatan gidan ta fito babbar mace da ita Amma ba sosai ba hakama da gani batada sakin fuska ko sakewa ta qaraso tana kallansu daya bayan daya ta tsayar da idanuwanta akan Jannah Wadda take tinanin kamar ta taba ganinta sedai kuma ta kasa tinano inane dan haka ta gyara tsayuwa tareda bude baki ta amsa gaisuwarsu ta ciro wayarta daga aljihun kayan jikinta ta bude sakon da tin jiya aka turo mata na ayyukan da aka riga aka rabawa kowannensu tana sake karantawa tana fadawa kowa gurin aikinsa tana rakasu gurin daya bayan daya har aka kammala kafin ta sake kallansu tace

"Familyn gidan gabaki daya basa qasar amma suna gap da dawowa dan haka kafin dawowansu kuyi iya kokarin tabbatarda Kun sabu da aikinku babu matsalar komai sbd kwata kwata a tsarin ahalin gidan basason matsala ko hayaniyar matsalar,

Akwai me gidan kwata kwata Wanda bama lallai zaku taba ganinsa ba so ba amfanin ku sansa sbd baya lokacin kowa a duniya idan Yana gida bayan na 'yarsa Guda daya tak Wadda itace kusan zuciyar gidan sai ku kiyaye,

Sai mahaifiyarsa da qaninsa sai kuma matar da zai aura inshallah itama kuna buqatan kiyayewa sosai sbd kwata kwata bata son kuskure koman qanqantarsa hakama kusan itace take juya iko a kaf maaikatan gidan sai kuma Yar uwar mahaifiyar matarsa wadda itace tamkar uwa kokuma ace yaya ga 'yarsa dan haka ina sake fada muku da murya me kauri akan ku kula sosai kusan abinda ya kawoku,

Baa fita koina 24/7 kuna cikin 4&4 hakama duk me magana ko wani abin daban ya dameni da zancen.

Tafiya tayi suka bita zuwa can bayan mansion din Wanda acan akai bangaren masu aiki anyi tazara tsakaninsu da bangaren masu gidan hakama bangaren masu aikin me girma da tsari sosai wanda shi kansa bangaren masu aikin kamar qaton gidan wani me kudin sosai sbd hatta ac dasu fridge akwai da lafiyayyun dakuna da gadaje da beddings da komai me tsari da daula.

Ajiyan zuciya Ammar ya ringa jerowa Yana hamdala a cikin ransa sbd Allah ya kaddari ya dawo cikin rayuwar jin dadin dasuka rasa hakama a yanzu zai samu nutsuwa da kwanciyar hankalin aikin wahalar ma kowane irine.

Bangaren maza daban hakama na mata amma akwai kofar baya data hadesu dan haka hankalinsu ya sake kwanciya hakama gurin cin abincinsu daya dan haka sai ya zamana kamar palo ne da dakuna tamkar dai sun kama selfcon.

Dakin Jannah da Fatma da Ummah daya da gadajen kwanciyar mutum daddaya Guda uku sai kowa nasa daban sai rug carpet me tsananin laushi da kyau da haske sai mirror da AC da wardrobe itama kowa tasa daban da toilet dinsu a cikin dakin dashima yake irin na masu hali sosai.

Suma dakin su Maheer hakanne sedai su gado uku ne dan haka aka bawa Dad daki daban shi kadai shima komai aciki dan haka dukkaninsu suka samu nutsuwar da suka dade basu samu ba daga nan Madam Sisi ta juya tabarsu zuwa nata dakin dayake daga baya babban daki ne ita kadai dayafi nasu duka tsari.

Kayansu suka ajiye kowannensu ya zauna Yana sauke numfashi kafin Jannah ta kama hannun Ummah zuwa toilet ta nuna mata yanda zatai amfani da komai kafin ta barota tayi abinda zatai tayo alwala ta fito.

Fatma ce ta shiga bayan fitowan Umman itama Jannah ta sa fahimtar da ita komai tayo alwala ta fito kafin Jannah din ta shiga karshe.

Sallah sukai dukkaninsu suna idarwa wayar dake dakin ta hau ringing Jannah ta miqe ahankali ta isa ta miqa hannu ta dauka a natse tace

"Yes ma'am?"

Madam Sisi ce kai tsaye tace su fito su tafi kitchen.

Cikin sanyi da nutsuwa Jannah din tace "ok"

Ajiye wayar tayi jikinta na mutuwa dan batasan ta yanda zasu ringa aiki a karkashin mutanen da batasan yanda zasu ringa treating nata da familynta ba.

Gurin Dad Jannah takai Ummah har dakinsa kafin ita da Fatma suka wuce zuwa lafiyayyan kitchen din da acan ne zasu ringa aiki kafin masu gidan su dawo su koma aiki acan na cikin mansion din na masu gidan.

Koda suka isa akwai wata me aikin da suka gani dazu tanata aikin abinci dan haka kai tsaye suka saka hannu tana sake musu bayanin aikin suna yi.

Duk da aikin gas ne kuma a tsararren kitchen amma sbd abincin mutane da yawa ne hakanan sukaji sun aikatu sbd ana gama na rana aka Dora na dare ba bata lokaci kuma lafiyayyan abinci akeyi Wanda yake cikeda lafiyayyun kayan abinci.

Sai bayan ishai suka baro kitchen din sbd duka kayan abincin da akai aiki dasu saida aka wanke aka maida kitchen din kamar baayi aikin komaiba.

Jannah bata iya cin abincinta na dareba sbd cikinta daya cunkushe da yanayin kamshin abincin da kuma na rana da bai gama narke mata ba datake ji.

Suna isowa daki wanka tayi da sabulun dove da shine aka raba musu kowa anbasa set na kayan wanka da sabulu isashen da zai karshen wata hakama toothbrushes da toothpaste masu kyau da tsada duka an raba musu da body oils masu kyau da body sprays da qarin kaya kala bibbiyu sbd baa bari kazo da wasu tarkacen kaya.

Tana fitowa wankan sallah tayi ko Mai bata iya Shafawaba ta zame ta kwanta.

Ummah dataga yanda gajiya take bayyane qarara a tattare da ita zaunawa tayi kusa da ita tana cewa

"Ummijan kin gaji ko?

Gyada kai Jannah tayi tana matsowa ta kwanta jikin Umman tana cewa

"Ummah koina ciwo yake mun"

Mai Umman ta miqa hannu ta dauko tana budewa tace

"Gobe zan tayaki sbd kada ki gaji irin haka,
Banason kina gajiya ke kadai kinji"

Man ta fara Shafa mata a kafafu tana Danna mata kafafun ahankali cikeda kulawa.

Lumshe idanuwa Jannah tayi tana jin dadin yanda Umman ke mata tausan tace

"Ummahna bazaki iyaba kuma nima banason kiyi aikin ki gaji irin hakan ki bari duk ranar dana gaji zance ki tayani kinji"

Shiru Umman tayi sbd bata yadda da hakan ba.

Fatma ma wanka tayi Tai sallah Amma sanin batada me bata irin wannan kulawan ya saka tana gama sallah ta hau gadonta ta kwanta take baccin samun lafiyayyar katifa da AC ya dauketa hadda wani irin gurnanin bacci kamar ba maceba.

Jannah ma a jikin Umman tayi bacci hakama itama Umman data kasa tadata a gurin bacci ya dauketa se dare sosai Jannah na farkowa ta tashi ta tada Umman suka hau gado ta rufe Umman kafin ta koma nata gadon ta kwanta take bacci me nauyi ya sake dauketa.

Washe gari Ammar da wuri ya tashi yayi sallah ya ringa yiwa Allah godia sbd rabonsa da baccin nutsuwa da kwanciyar hankali irin na yau tin ranar da AZIZ LIMBA ya bayyana rayuwarsu dan haka yau da wani irin nutsuwa da sanyin zuciya ya tashi ya kwana a cikin lafiyayyan guri da AC da bargo me kyau yayi wanka da ruwa me tsafta da dumi a cikin toilet mafi nutsuwa hakama da soap me kyau duk da kwata kwata ko kusa bai kai Wanda yake wanka dashi a baya ba sbd sabulun wankansa a baya kadai zai ciyar da wasu da yawa Amma dai a yanda rayuwa tayi dasu yanzu wannan dinma ai babban cigabansu ne wanka dashi dan haka wankan tsafta yayi yai brush da lallausan brush yana sake godewa Allah kafin ya fito aikinsa.

Kusan hakanne ya faru da kowannensu dan kuwa sunyi tashin nutsuwa yau kowa fuskansa bayyane da kwanciyar hankali suka fito ayyukansu.

Dad da Maheer ne securities din second gate dan haka uniform dinsu suka saka suka isa bakin aiki.

Garba kuma wankin bangunan gidan dana motoci da sharan harabar gidan tin daga first gate har second shakuwa Ammar duk wata flower da grass dayake gidan shine me kulawa dasu tareda harkar ruwa shima tin daga gate din farko harna biyun.

Breakfast aka kaiwa kowa wanda su Jannah ne sukai aikin Fatma ce tayi kaiwa kowa harfa securities na can babban gate.

Ummah baya yadda ba saida ta biyosu kitchen dan haka aikin yankan su albasa da bude Maggi ne kawai suke bata.

A kitchen suka wuni se yamma suka kammala komai aka kaiwa kowa nasa sukai wanka da sallah suka zauna hutawa.

Da dare gabaki dayansu sukaci abinci a tare a palon dayake nasu hankali kwance suna firarsu kowa na fadar yanda yafara ji akan aikinsa suna dariyan juna sbd sun ringa sun karbi wannan sabuwar rayuwar kuma.
#MAMUH
#LOVE
#4&4BEST LOVE
#AY LIMBA
#HOT LOVE
#BOSS GOING CRAZY FOR.......
#JANNAH ZAD
#FALAQ LIMBA
#ZAADENS

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 7

Wata sabuwar duniyar da suka manta yanda take ne suka samu kansu ayau cikinta Wadda koda sun farfado basu taba saka ran zasu shigo cikinta ba a shekarun kusa kusa ba sbd gabaki daya 4&4 mansion turai ce kawai zasuce me zaman kanta a Nigeria dan kuwa tinda suka shigo gate din farko suka San sun shigo wata duniyar ce kawai ana rufe second gate kuma sukasan sun bar qasarsu a yanzu duniyar Familyn 4&4 suke ciki tsundum wadda babu komai a cikinta tukuna sai daular duniya da wata irin shiru da nutsuwa tareda kwanciyar hankali me sanyi da tsafta da suka ji suna samu.

Garba da Fatma da tinda Allah ya halicce su basu taba gani ko jin labarin irin wannan gidan ba da kusan komai nasa kashe musu ido yake hankalinsu mummunan tashi yayi sedai tsoron securities dake zagaye da gidan da bindigogi ya sakasu hadiye tsoronsa a cikinsu Wanda hakan ya ringa juya musu ciki.

Jannah da jikinta har lokacin yake a mace da sunan mansion din daya tinatar da ita rana mafi girma da muni rayuwarta itama hadiye radadin zuciyarta tayi tana jin wani irin ciwo a zuciya da kirjinta.

Ammar da bayan Jannah shi kadai ne ya riqe date din aurenta da LIMBA fes a cikin Kansa sbd shima bayan ranar rasuwar mahaifiyarsa ranar itace rana mafi muni da girman da bazai taba mantawaba a rayuwarsa sbd a wannan date dinne Jannah ta auri waninsa wanda a ranar zuciyarsa ta mutu a kirjinsa mutuwar da har yau bata farfado ba har sai ranar daya auri Jannah ta zama mallakinsa sbd baisan wane irin girman so yakewa Jannah Zad ba.

Dad da Maheer kuwa ajiyan zuciya suka sauke atare cikeda samun nutsuwan zuciya da ruhi sbd sunzo inda zasuyi aiki da karfi da lafiyarsu sbd Jannah da Ummah su samu rayuwar jin dadi da kwanciyar hankali sbd anan tsaro da kariyar da Jannah da Ummah zasu samu ko a nasu mansion dinne iyakacinsa kenan sbd ko qara da hayaniyar waje ko kadan baka jiyowa duk da wata irin anguwa ce da kusan tsaro da tsari tareda rashin hayaniyarta zai tabbatar maka da sai Wanda yakai iya kaiwa yake zaune a cikinta.

Hannun Ummah dayake hannun Dad ya sake riqeta da kyau Yana kallanta cikin kulawa zaiyi magana Chief ta maaikatan gidan ta fito babbar mace da ita Amma ba sosai ba hakama da gani batada sakin fuska ko sakewa ta qaraso tana kallansu daya bayan daya ta tsayar da idanuwanta akan Jannah Wadda take tinanin kamar ta taba ganinta sedai kuma ta kasa tinano inane dan haka ta gyara tsayuwa tareda bude baki ta amsa gaisuwarsu ta ciro wayarta daga aljihun kayan jikinta ta bude sakon da tin jiya aka turo mata na ayyukan da aka riga aka rabawa kowannensu tana sake karantawa tana fadawa kowa gurin aikinsa tana rakasu gurin daya bayan daya har aka kammala kafin ta sake kallansu tace

"Familyn gidan gabaki daya basa qasar amma suna gap da dawowa dan haka kafin dawowansu kuyi iya kokarin tabbatarda Kun sabu da aikinku babu matsalar komai sbd kwata kwata a tsarin ahalin gidan basason matsala ko hayaniyar matsalar,

Akwai me gidan kwata kwata Wanda bama lallai zaku taba ganinsa ba so ba amfanin ku sansa sbd baya lokacin kowa a duniya idan Yana gida bayan na 'yarsa Guda daya tak Wadda itace kusan zuciyar gidan sai ku kiyaye,

Sai mahaifiyarsa da qaninsa sai kuma matar da zai aura inshallah itama kuna buqatan kiyayewa sosai sbd kwata kwata bata son kuskure koman qanqantarsa hakama kusan itace take juya iko a kaf maaikatan gidan sai kuma Yar uwar mahaifiyar matarsa wadda itace tamkar uwa kokuma ace yaya ga 'yarsa dan haka ina sake fada muku da murya me kauri akan ku kula sosai kusan abinda ya kawoku,

Baa fita koina 24/7 kuna cikin 4&4 hakama duk me magana ko wani abin daban ya dameni da zancen.

Tafiya tayi suka bita zuwa can bayan mansion din Wanda acan akai bangaren masu aiki anyi tazara tsakaninsu da bangaren masu gidan hakama bangaren masu aikin me girma da tsari sosai wanda shi kansa bangaren masu aikin kamar qaton gidan wani me kudin sosai sbd hatta ac dasu fridge akwai da lafiyayyun dakuna da gadaje da beddings da komai me tsari da daula.

Ajiyan zuciya Ammar ya ringa jerowa Yana hamdala a cikin ransa sbd Allah ya kaddari ya dawo cikin rayuwar jin dadin dasuka rasa hakama a yanzu zai samu nutsuwa da kwanciyar hankalin aikin wahalar ma kowane irine.

Bangaren maza daban hakama na mata amma akwai kofar baya data hadesu dan haka hankalinsu ya sake kwanciya hakama gurin cin abincinsu daya dan haka sai ya zamana kamar palo ne da dakuna tamkar dai sun kama selfcon.

Dakin Jannah da Fatma da Ummah daya da gadajen kwanciyar mutum daddaya Guda uku sai kowa nasa daban sai rug carpet me tsananin laushi da kyau da haske sai mirror da AC da wardrobe itama kowa tasa daban da toilet dinsu a cikin dakin dashima yake irin na masu hali sosai.

Suma dakin su Maheer hakanne sedai su gado uku ne dan haka aka bawa Dad daki daban shi kadai shima komai aciki dan haka dukkaninsu suka samu nutsuwar da suka dade basu samu ba daga nan Madam Sisi ta juya tabarsu zuwa nata dakin dayake daga baya babban daki ne ita kadai dayafi nasu duka tsari.

Kayansu suka ajiye kowannensu ya zauna Yana sauke numfashi kafin Jannah ta kama hannun Ummah zuwa toilet ta nuna mata yanda zatai amfani da komai kafin ta barota tayi abinda zatai tayo alwala ta fito.

Fatma ce ta shiga bayan fitowan Umman itama Jannah ta sa fahimtar da ita komai tayo alwala ta fito kafin Jannah din ta shiga karshe.

Sallah sukai dukkaninsu suna idarwa wayar dake dakin ta hau ringing Jannah ta miqe ahankali ta isa ta miqa hannu ta dauka a natse tace

"Yes ma'am?"

Madam Sisi ce kai tsaye tace su fito su tafi kitchen.

Cikin sanyi da nutsuwa Jannah din tace "ok"

Ajiye wayar tayi jikinta na mutuwa dan batasan ta yanda zasu ringa aiki a karkashin mutanen da batasan yanda zasu ringa treating nata da familynta ba.

Gurin Dad Jannah takai Ummah har dakinsa kafin ita da Fatma suka wuce zuwa lafiyayyan kitchen din da acan ne zasu ringa aiki kafin masu gidan su dawo su koma aiki acan na cikin mansion din na masu gidan.

Koda suka isa akwai wata me aikin da suka gani dazu tanata aikin abinci dan haka kai tsaye suka saka hannu tana sake musu bayanin aikin suna yi.

Duk da aikin gas ne kuma a tsararren kitchen amma sbd abincin mutane da yawa ne hakanan sukaji sun aikatu sbd ana gama na rana aka Dora na dare ba bata lokaci kuma lafiyayyan abinci akeyi Wanda yake cikeda lafiyayyun kayan abinci.

Sai bayan ishai suka baro kitchen din sbd duka kayan abincin da akai aiki dasu saida aka wanke aka maida kitchen din kamar baayi aikin komaiba.

Jannah bata iya cin abincinta na dareba sbd cikinta daya cunkushe da yanayin kamshin abincin da kuma na rana da bai gama narke mata ba datake ji.

Suna isowa daki wanka tayi da sabulun dove da shine aka raba musu kowa anbasa set na kayan wanka da sabulu isashen da zai karshen wata hakama toothbrushes da toothpaste masu kyau da tsada duka an raba musu da body oils masu kyau da body sprays da qarin kaya kala bibbiyu sbd baa bari kazo da wasu tarkacen kaya.

Tana fitowa wankan sallah tayi ko Mai bata iya Shafawaba ta zame ta kwanta.

Ummah dataga yanda gajiya take bayyane qarara a tattare da ita zaunawa tayi kusa da ita tana cewa

"Ummijan kin gaji ko?

Gyada kai Jannah tayi tana matsowa ta kwanta jikin Umman tana cewa

"Ummah koina ciwo yake mun"

Mai Umman ta miqa hannu ta dauko tana budewa tace

"Gobe zan tayaki sbd kada ki gaji irin haka,
Banason kina gajiya ke kadai kinji"

Man ta fara Shafa mata a kafafu tana Danna mata kafafun ahankali cikeda kulawa.

Lumshe idanuwa Jannah tayi tana jin dadin yanda Umman ke mata tausan tace

"Ummahna bazaki iyaba kuma nima banason kiyi aikin ki gaji irin hakan ki bari duk ranar dana gaji zance ki tayani kinji"

Shiru Umman tayi sbd bata yadda da hakan ba.

Fatma ma wanka tayi Tai sallah Amma sanin batada me bata irin wannan kulawan ya saka tana gama sallah ta hau gadonta ta kwanta take baccin samun lafiyayyar katifa da AC ya dauketa hadda wani irin gurnanin bacci kamar ba maceba.

Jannah ma a jikin Umman tayi bacci hakama itama Umman data kasa tadata a gurin bacci ya dauketa se dare sosai Jannah na farkowa ta tashi ta tada Umman suka hau gado ta rufe Umman kafin ta koma nata gadon ta kwanta take bacci me nauyi ya sake dauketa.

Washe gari Ammar da wuri ya tashi yayi sallah ya ringa yiwa Allah godia sbd rabonsa da baccin nutsuwa da kwanciyar hankali irin na yau tin ranar da AZIZ LIMBA ya bayyana rayuwarsu dan haka yau da wani irin nutsuwa da sanyin zuciya ya tashi ya kwana a cikin lafiyayyan guri da AC da bargo me kyau yayi wanka da ruwa me tsafta da dumi a cikin toilet mafi nutsuwa hakama da soap me kyau duk da kwata kwata ko kusa bai kai Wanda yake wanka dashi a baya ba sbd sabulun wankansa a baya kadai zai ciyar da wasu da yawa Amma dai a yanda rayuwa tayi dasu yanzu wannan dinma ai babban cigabansu ne wanka dashi dan haka wankan tsafta yayi yai brush da lallausan brush yana sake godewa Allah kafin ya fito aikinsa.

Kusan hakanne ya faru da kowannensu dan kuwa sunyi tashin nutsuwa yau kowa fuskansa bayyane da kwanciyar hankali suka fito ayyukansu.

Dad da Maheer ne securities din second gate dan haka uniform dinsu suka saka suka isa bakin aiki.

Garba kuma wankin bangunan gidan dana motoci da sharan harabar gidan tin daga first gate har second shakuwa Ammar duk wata flower da grass dayake gidan shine me kulawa dasu tareda harkar ruwa shima tin daga gate din farko harna biyun.

Breakfast aka kaiwa kowa wanda su Jannah ne sukai aikin Fatma ce tayi kaiwa kowa harfa securities na can babban gate.

Ummah baya yadda ba saida ta biyosu kitchen dan haka aikin yankan su albasa da bude Maggi ne kawai suke bata.

A kitchen suka wuni se yamma suka kammala komai aka kaiwa kowa nasa sukai wanka da sallah suka zauna hutawa.

Da dare gabaki dayansu sukaci abinci a tare a palon dayake nasu hankali kwance suna firarsu kowa na fadar yanda yafara ji akan aikinsa suna dariyan juna sbd sun ringa sun karbi wannan sabuwar rayuwar kuma.
#MAMUH
#LOVE
#4&4BEST LOVE
#AY LIMBA
#HOT LOVE
#BOSS GOING CRAZY FOR.......
#JANNAH ZAD
#FALAQ LIMBA
#ZAADENS

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899
*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 8

Washe gari ma hakance ta kasance sosai kowa ya maida hankalinsa akan aikinsa duk da dukkaninsu babu Wanda bai fara fuskantar rashin sabo da aikinba Musamman Ammar da aikinsa yake da wuya sosai shida Garba kullum sai sunyi aikinsu ko akwai datti ko babu dan haka Maheer ganin yanda Ammar ke shan wahala sosai duk da baiyi complain ba sbd ya qwallafa rai Sosai akan zaiyi aiki dansu tsayu da kansu bazasu dawwama a cikin wannan bautarba dan haka ya fara tayasa sosai sbd su nasu aikin gadi ne kawai tinda babu masu isowa second gate se masu gidan dan haka babu wani aiki su kam sai masu gidan sun dawo tukuna nasu aikin ya fara tinda a bakin gate din ma kila zasu riqa kwana sbd koyaushe masu gidan zasu fita ko dawowa.

Su Jannah ma ahankali da kwanaki suka fara tafiya suka saba da aikin Wanda a yanzu da suka fahimcesa suka ga kamar ya rage yawa sbd kusan sun rabawa kansu aikin ne sai kowannensu na dan samun lokacin hutawa dakyau.

Iya masu aiki da securities din gidan akewa abincin safe rana da dare shikenan ne kadai dan haka suka nutsu suka fahimci aikin sai ya dena wahalar dasu suka samu qarin nutsuwa.

Watan farko da aka basu albashi kowannensu kusan kasa gasgatawa sukai Amma duba irin mansion din da suke sai sukasan fiyeda hakanma koma waye me gidan zai iya dan ko yanda ake kashewa maaikatan gidan da securities kudi gurin ciyarwa da buqatu ma kadai kasan koma waye yakai kuma yanada ilimin da kusan ya wuce nasu sbd komai a waye ba cutatarwa.

Waya suka bawa Madam Sisi ta siyowa Dad dasu Maheer Jannah tace bata buqata.

Su Garba ma da fatma tin kafin su shigo aka bude musu acct dan haka suma direct kudinsu ke shigar musu su kuwa Zaadens gabaki daya a acct din Dad kudinsu ke shiga dan haka saving kawai zuka fara tinda babu abinda zasu buqata a yanzu bayan wayar dan haka ita kadai suka siya.

******Lokaci Yakuma tafiya ahankali ahankali har sun share kusan wata biyar a 4&4 mansion sun saba sun zama maaikatan da Madam Sisi da can kamfani ke alfahari dasu hakama zuwa wannan lokacin dukkaninsu wahalar ta riga tabi jikinsu sunma dena jinta aikinsu sukeyi hankali kwance da kwarewa.

A bangaren samun lafiya da sauyi na komai sun gama samu sbd gabaki dayansu babu Wanda bai sauya ba ya dawo hayyacinsa,

Sun samu sauyin fata me kyau sbd a tsawon watannin nan basu taba fita ba sai ranakun jumaa da ake barin su Maza maaikata zuwa sallar jumaa Amma bayan ita a lafiyayyan masallacin dake cikin mansion din dukkanin maaikatan gidan musulmai ke sallah dan haka basa cikin wata doguwar wahala,

AC da samun abubuwan amfani masu kyau ya sakasu farfadowa daga mutuwar tsayen d sukai,
Garba ma ya sauya sosai ya wanke ya zama dan birni,

Jannah batai jiki ba kamar yanda Fatma tayi jiki sosai gabaki daya ta cire ramar datazo da ita tayi haske abinta kamar ba Fatman kauye ba,

Jannah haskenta ne daya dan rage ya bayyana sosai sosai ta koma fresh dinta Amma sam batai wani jiki ba,

Ummah ma tayi haske ta sauya sosai itama sbd kulawan datake samu sosai yanzu a gurin Dad duk da tana aiki tareda su Jannah Amma suna tattalinta da tarairayanta sbd tsoro da gurin tayiwa kanta wani abu da wuqa da koyaushe take hannunta gurin aiki dan sam su Jannah basa barin ta kusanci inda gas yake.

Amina shine sunan dayar me aikin da ayanzu dukkaninsu akwai shakuwa ta aiki a tsakaninsu hakama ta bangaren Madam Sisi tafi jin Jannah kaf a cikinsu sbd iliminta dayake a bayyane dan komai nata a natse ba hayaniya ba gaggawa sai hakan ya saka tafi jinta takuma fin jin itace kadai wadda zata iya kai tsaye bawa ragamar kulawa da komai na Mai gidan ko yarsa sauran sedai suji da sauran ayyukan sbd nutsuwa da rashin hayaniyar Jannah din takai wani level da take ganinta kamar sarauniyar wani gidan masu kudi.

Lokacinda suka cike wata bakwai a lokacin ne jikin Ummah ya ringa rikice musu akai akai kuma da tsanani dan haka duk hankalinsu ya tashi suka shiga damuwa walwalansu ta rage kwata kwata gashi basuda yanda zasuyi haka suka ringa lallabawa sunason su sake Tara abinda suka Tara saisu fara nema mata lafiya.

Hakan ya saka Umman ta rage zuwa kitchen sosai sbd koyaushe cikin qunci take haka kawai,
Duk yanda Jannah tayi dan sakata walwala ko farin ciki bata iyawa sedai tayita binta da idanuwanta dake fidda zallan qunci dayake rufe da zuciyarta gashi bata iya furta abinda takeji bare suyi tinanin ta Tina wani abu na rayuwarta dan haka sedai suka koma lallabata,

Dad duk dubaru da rarrashi da kulawa babu Wadda baya mata sbd ta dawo Matarsa daya sani me saka zuciyarsa samun nutsuwa yayi Amma babu sauyi dan hakama ta koma gurinsa take kwana sbd acan dinne ma take samu tayi masa kuka sosai sai ta rage nauyin kirji tayi bacci wanda shi kadai magani da sassaucin datake samu.

Ana haka Chief din gidan gabaki daya shikuma yazo ya sanar da dawowan masu gidan dan haka a karon farko da aka bude musu asalin cikin mansion din suka shiga suka wuni suna aikin gyara.

Tin daga ranar kullum sune masu zuwa aikin gyara cikin gidan sbd akalla afi satika ana gyara koina kullum kafin dawowansu yanda gidan zaiyi kamar daman akwai mutane.

Sabbin masu aikin abinci aka kawo su biyu aka hadasu da aminah a kitchen ita da Fatma kuma aka dawo dasu bangaren masu gidan gabaki daya da aiki.

Babu komai na masu gidan sbd da alama yanzu ne zasu fara zama sabon gidan basu ma taba zuwansa ba se yanzu dan haka babu kowane irin abu daya shafesu bare ya nuna yanda suke sai idan sunzo tukuna.

Aikin ciki yanzu bame wahala bane kamar na kitchen dan haka hutun da suke samu yanzu ma yafi na bayan.

*************
SIDNEY

White Royce Royce ce ta sako kai a harabar gidan datake zagaye da fresh flowers masu kamshi da tsari da qamshinsu ke tashi ahankali yana gauraye harabar gidan.

Da kansa ya tuqo motar sbd daga airport yake yaje yayi sallama da wasu baqinsu da suka taho daga Cyprus sunyi sealing wani babban deal na sabbbin kamfanin daya bude na 4&4 tinda sassafe ya fita tin gari nada sauran duhu.

Sayd ne da tasa motar wata blk Lamborghini ta biyo bayan shigowanta LIMBA yayi parking can gefe daban ya fito yana kashe wayar dayake yi da baqin da shima tin safe ya fita sallama dasu ya nufo motar.

Waya LIMBAn ya tsaya amsawa a natse kafin ya kashe daidai Sayd n bude masa motar ya juyo fararen idanuwansa masu wani irin kwarjini da asalin kyau ya kalli Sayd din ya ziro kafafunsa ya fito yana zanye da sweatsets na Balmain milk da hular sanyi akansa data rufe lafiyayyan gashin gashin Kansa da kunnuwansa.

"Good morning Hamma" Sayd ya fada Yana kallan kyakkyawar fuskansa da haskensa yake qarawa kwarjininsa yawa.

Sake dagowa yayi ya kalli Sayd din sbd a duk lokacinda ya ambacesa da Hamma yanajin zolaya ne kokuma son tabasa.

Kallan da yayiwa Sayd dinne ya saka Sayd din sakin murmushi me kyau Yana kokarin sake magana LIMBAn ya a katsesa a natse da Murya me Kamala da wani irin class da cewa

"Arrangement din sun zama ready ne??

"Yes,komai anyi angama handing over dinma ya tafi smoothly,
Anjima 12 zaa qarasa bord meeting tareda chairmans din NIELS PUBLISHERS na duka branches din harda na Greece da China duka,

After that chairman na 4&4 Sidney Branch ya aiko da email na record da zaka duba daga nan sai time na haduwanka da doctors din Falaq Aziz after that kuma.....

Hannu ya dagawa Sayd din a natse Yace

"Daga nan kayi canceling sauran schedules din sbd daga asibiti zan dawo gida da Falaq Aziz da kaina"

"Yes" Sayd yace yana fiddo wayarsa dan cancelling sauran schedules din.

Palon gidan suka shigo Wanda yake tsit babu kowa sai wani qamshi me sanyi da nutsuwa ke tashi hakama masu aikin dake aiki suna ganinsa saurin sauke kai sukai cikeda girmamawa suka gaidasa sbd yanada wuya masu aiki su gansa idan ba irin hakan ba daya fita da sassafe ya fito suna aiki.

Kai tsaye hanyar bangggarensa ya nufa Yana kashe wayoyinsa ya haye sama kai tsaye.

Yana isa kai tsaye bedroom dinsa ya wuce yana zare rigar jikinsa da fresh skin dinsa fari tas ya bayyana yana daukan idon wani irin hutu dayake bayyane a koinansa.

Ya sake budewa ya zama wani irin murdadden namiji lafiyaye da geamin ya budesa sosai.

Closet ya nufa ya zare koman jikinsa ya zaro towel a cikin jerin towels din dasuke jere guri daya fiyeda dozen biyu ya daura a kugunsa ya fada toilet ya sakarwa kansa ruwa Yana rufe idanuwansa ahankali.

Yana fitowa shirin kaya marasa nauyi yayi farare tas ya kashe hasken dakin ya kwanta bacci.

Karfe goma da sha daya mutanen gidan suka fara fitowa a natse cikin shiri na kwanciyar hankali dan lokacin ne lokacin breakfast dinsu.

Mama ce tafara fitowa kafin Falaq Wanda take sanye da doguwar riga me qaramin hannu mara nauyi ta kwanta jikinta ba hayaniya idan ka kalli rigar ma zaka dauka ta shan iska ne kawai sedai tsadar rigar kadai idan kaji kudinta zakai mamakin ace da hankalin mutum a jikinsa ya siyeta hakan.

Qamshi me sanyi da dadi take fitarwa na tsadaddiyar turaren original Fendi.

Fuskanta da skin dinta fresh na asalin Yar hutu da aka haifeta ta taso a cikinsa.

Fiddausi ce ta fito daga kitchen dauke da fresh fruits data hado tareda madara da zuma ta ajiye a dining tana kallan Mama tace

"Mama ina kwana narka da fitowa"

Amsawa mama tayi tana zama kan dining din,

Falaq ma gaida maman tayi a natse ba hayaniya sbd a yanzu falaq din ta banbanta data baya.

Zaunawan Falaq yayi daidai da fitowan AYSHA NICKI daga bedroom dinta sanye da maroon doguwar riga da itama take lafe a jikinta da dogon hannu me kyau fuskanta a fresh itama kyanta a bayyane.

Mama na ganinta ta sake fuskanta sosai cikeda wata irin kauna da kulawa
Itama AyshaNicki din da farin ciki da kaunar maman ta qaraso ta dan rungumeta ta baya tana cewa

"Good morning my mum"

Ajiyan zuciya Falaq Aziz ta sauke tana dauke idanuwanta daga kansu daidai qamshinsa daya doso gurin cikin sanyi yana ratsa hancinsu alamar Yana gap da shigowa gurin cin abincin.
#MAMUH
#AY LIMBA
#ZAADENS
#JANNAH ZAD
#AMMAR ZAD
#AYSHNICKI

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070

09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 9

Nicky dince tafara juyawa ahankali ta zubawa inda zai fito idanuwanta da babu komai a cikinsu sai asalin tsananin azababben mahaukacin son datake masa Wanda ya gama rabata da duk wani tinanin komai na duniya da rayuwarta sbd akan son datake masa zata iya komai ba abinda ya dameta indai zata samesa a rayuwarta ta yadda ta rabu da komai da kowa.

Qamshinsa ne ya tsananta Yana sake gauraye sanyin gurin wanda ya tabbatarda ya iso,

Falaq ce ta dago ahankali itama ta zubawa inda zai fito din idanuwanta dake kama sak da nasa tanajin kaman ta miqe ta hanasa karasowa inda idanuwan Nicky zasu sauka akansa kada ta cinye mata shi.

Sako kai yayi a cikin wata irin nutsuwa da kamewa tareda wani irin annurin kwarjininsa fuskansa na sake bayyanarda wani irin sirrin kyau da Kamala kamar ko yaushe,

Milk Brioni's ne a jikinsa sosai agogon Cartier dake bayyanarda ba qananun kudine ke siyansaba.

Idanuwansa masu kashe Nicky ya dago ya kalli Mama Yana zama a natse ya bude baki yace

"Good morning Mama,
Mun tashi Lfy?

Kallansa Mama tayi dakyau tana sake jin wani irin ciwo a ranta ta yanda 'danta ya sauya batareda shi Kansa ya San da hakan ba Amma akwai wani irin sauyi tareda shi wanda ita kanta a tsawon lokacin nan ta kasa tantancewa.

Cikeda kulawa da sakewa ta amsa tana cewa

"Barka da fitowa"

Gyada kai yayi Yana maida idanuwansa cikeda kauna me tsananin karfin da har koyaushe take qaruwa ya kalli Falaq wadda itama shi din take kalla tana narke fuska.

Hannunsa ya miqa mata a natse Yana cewa

"Hey my baby"

Kama hannunsa tayi tana qanqamewa cikin nata ta bude baki tace

"Good morning DADDY"

A yanzu duniyarsa gabaki daya itace ke ganin murmushinsa kai tsaye sai abokan aikinsa musu mahimmaci sai kuma fira idan anayi dashi a gidajen tv wanda ba asalin murmushin daya fito daga zuciyarsa ne suke gani ba,

Ita kadai ce take samun murmushinsa dayake fitowa daga qasan zuciyarsa sai kuma personal person nasa dan Amanarsa Sayd Limba.

Sakar mata wani lafiyayyan murmushi me nutsuwa yayi Yana kissing hannunta a natse yace

"Yau zaki samu enough time da Bestynki i promise you that my lady"

Murmushin farin ciki ke son fito mata amma tana kokarin dannewa sbd Wainda ke gurin.

Sayd ne daya iso ya saka hannu akan fuskanta yaja gefen kumatunta Yana cewa

"Yi murnanki anan waye zaki jawa aji tinda munsan lokacinda yarinya take kuka tana bin Daddynta da takarmi daya a hannu akan zata bisa duk inda zasu so just chill Ms Aziz"

Saurin kallan Daddynta tayi tana toshe bakinta batason dariya tace

"Did you hear that Daddy?"

Murmushi ya sake yi yana cewa

"Kyalesa yanason ya taba Miki steeze ne kawai"

Dariya Sayd yayi ganin tana kallansa tana juya masa ido alamar yayi trying next time yanzu baiyi nasara ba tana masa dariyar dayake jinta har cikin ransa sbd kwata kwata yanzu bata cika dariya ko dogon farin ciki ba kamar baya ba dan haka koyaushe yake kokarin tsokanarta sbd tayi dariya da farin ciki.

Nicky da tinda AZIZ LIMBA ya zauna a     dining din bata sake motsin komaiba kallansa takeyi zuciyarta na wata irin narkewa,

Murmushin daya kewa Falaq ne yake sukar zuciyarta tana jin radadinsa har cikin kowane digon jinin dayake yawo a jikinta sbd irin son datake masa har yarsa Falaq jin takeyi tana tsananin kishin irin so da kaunar dayake mata har cikin ranta,

Sonsa takeyi kuma ita kadai WA kanta,
Ita kadai takeson yaso a rayuwarsa
Koda bazai sota ba ya bari to ita kadai taso sa,
Yanda take jin kishin Falaq badan 'yarsa ce ba jininsa da tini ta cireta a rayuwarsa kwata kwata duk da batasan gaba ko xata iya jure ganin irin wannan son dayakewa Falaq din ba,

Duk ranar da AZIZ LIMBA yaso wata macen irin yanda yake kaunar Falaq batasan iya mutanen da zata iya rabawa da duniya ba sbd kaf danginsu zata karar ko sunyi yawan me..

Sayd ne ya gaida Mama Yana zaunawa kafin ya dan kalli Nicky din yace

"Good morning Aysh"

Tana dan dauke idanuwanta daga kan AZIZ Wanda baima kalli inda take ba ta gaida Sayd din itama tana dawo da kallanta kan AZIZ ta bude baki tace

"Good morning Mine"

Saida ya dauki lokaci Batareda ya kalletaba ya amsa a taqaice yana daukan fork ya fara cin Italian breakfast din da fiddausi tagama jerawa a dining.

Shiru gurin yayi kowa na breakfast da masu tinani.

Bai iya gama cin abincin ba yaji ya ishesa ya rasa appetite dinsa gaba daya dan haka ya dauki tissue ya goge bakinsa ya miqe batareda ya kalli kowaba sai Falaq daya ranqwafo yayi pecking goshinta yana cewa mama

"Mu wuni lafiya" ya fice Sayd ma miqewa yayi ya bar gurin Yana manta files dinsa dayazo dining din dasu.

Mama ce ta zubawa files din idanuwanta ta tsayar da idanuwanta akan sunan sabon kamfanin 4&4 din uLIMBAS zuciyarta na tafaso mata wani irin nauyi da damuwa tareda rashin nutsuwa da sukuni ko kadan sbd komai na rayuwar AZIZ LIMBA yana tafiya akan maana da tsari dan haka koma tayaya aka bayyanarda wannan kamfanin akwai babban mahimmaci da girman dayake tattare dashi gashi kamar yanda bai taba fadawa duniya maanar uLIMBAS ba sai bayan shekaru da komai ya fito duniya tasan maanarsa Wanda ita datake uwarsa ma bata saniba sai daga baya hakama wannan din haryanxu babu Wanda yasan maanarsa bakuma Wanda zai taba sani ta Sani sai bayan shekaru kila Amma dai koma menene wannan Karan hankalinta kwata kwata bai kwanta ba Musamman da maganar komawansu Nigeria ta bullo gabaki daya zuciyarta qunci da zafi takeyi sbd har abada bata kaunar AZIZ ya sake kusantar inda ma zasu iya samun labari ko ganin Wanda ma yasan ko labarin ZAADENS dan har abada bazata taba barin Jannah dawowa rayuwar AZIZ LIMBA da Falaq ba sbd babu alkhairi a rayuwar Zaadens da duk Wanda zasu ra6a dan haka zata tsaya komai zatayi zataisa dan hana ko tarihin Zaadens dawowa rayuwarsu dan hakanne ma ta tsani komawa kwata kwata Amma Falaq ta tsaya ita kuma Nigeria takeso hakanne ya saka ya yanke komawar,

Wannan dalilin ne ya saka kusanci da karfin kaunar dake tsakanin Mama da Falaq ragewa sbd a rayuwar Falaq babu inda take so take kuma son komawa tayi rayuwa irin Nigeria Wanda ko daddynta ya tambayi dalilin hakan Amma Sam babu dalilin datake basu Nigeria din kawai takeso.

A bangaren Mama itace ta bada umarnin auren AyshNicky ga AZIZ LIMBA Wanda haryanxu bai bata cikakkiyar amsa akan hakan ba duk da bai taba tsallake umarninta ba dan haka ya bar mata komai a hannunta Amma kwata kwata ba maganar auren a kusa sbd rashin bada fuskansa ga Nicky da kuma rashin bada fuskan sake zancen.

Maganar tafiyansu Nigeria ya saka Mama qin yadda da tafiyar kwata kwata sai anyi auren sbd tanason ko zai sauka Nigeria ya sauka da aurensa akansa ta yanda har abada ba gurin shigowan kowace irin mace sbd AZIZ LIMBA mijin mace daya ne babu tsari ko kadan na auren mace biyu a rayuwarsa kuma itama ta yadda da hakan.

Sayd ne ya dawo da sauri ya miqa hannu ya dauki files din ya juya ya sake ficewa Yana daga wayarsa dake ringing.

Mama da Nicky ne suka bi bayansa da kallo sbd idan har AZIZ LIMBA zai iya yiwa kaunar Ummitah kishiya ta hanyar bude sabbin companies da abubuwa da dama da sunan 4&4 to tabbas 4&4 din nata mahimmancin dake gogayya da kauna tareda girman Ummitah a rayuwarsa tinda bai taba bude komai da sunan Falaq ba ko wani abu daya shafetaba to tanason sanin maanar 4&4 komai tsanani sbd itama zuciyarta girgiza takeyi da koma menene bai kwanta mata a zuciya ba.

Falaq ma miqewa tayi daga dining din ta fice tana kwala sunan fiddausi tanason su fita kafin lokacin zuwanta da Daddynta asibiti yayi.

Binta Nicky tayi da idanuwa tanajin inama itace Ummitah ya haifi Falaq data samu dukkanin soyayya da kaunar AZIZ LIMBA yanda bata buqtaan komai a duniya hakan ma ya isheta.

Bayan ficewan Falaq ajiyan zuciya Mama ta sauke tana jin ciwo da radadin yanda kusancin Falaq ya rage daga gareta duk da suna tsananin kaunar juna na zamtowansu kaka da jika.

Daki Falaq ta isa ta dauki wayarta da mini bag ta chanel ta janyo jacket din Dior black ta saka akan kayanta ta fito fiddausi ma a shirye ta fito sanyeda doguwar rigar Egypt ta sanar da Mama.

Cikin kulawa mama tace

"Ki kula da ita sosai kinsan yanayinta kuma ki kula da hanya"

Gyada Kai fiddausi tayi tana cewa

"Inshallah amma dai Mama ya kamata ki shirya fa da mutuniyarki"

"Kyaleta bata ji ne haryanxu ta kasa sanin ta girma koyaushe shirme ne a tinaninta Wanda nasan inda aka samu matsalar lalacewan tarbiyanta dan haka kuje kawai"

Fiddausi tasan inda maganar Maman ta dosa da abinda take nufi dan haka bata sake cewa komaiba ta juya tabi bayan Falaq wadda maganar Maman ta sosa zuciyarta sbd Jannah da aka kira da wadda ta lalata tarbiyanta.

Suna ficewa itama Nicky ta zari mota tabar gidan sbd shirye shiryen tafiya datake dan a yanda takeso zata riga su LIMBAs din isa dan ta fara shigarda report dinta na aiki da zata fara acan ta gama komai sbd ta shirya bin LIMBA duk duniyar da zashi ko da aurensa akanta ko babu zata bisa har sai lokacin auren yayi.

Karfe 2 na rana motar Ferrari ta shigo LIMBAs din wadda take motar Falaq amma fiddausi ke ja har yanzu bata kai fara ja da kanta ba,

Suna parking motarsa daya fita da ita Porsche cayenne tana shigowa Sayd ke ja Yana gefensa sukai parking,

Atare suka shiga gidan hannunta na riqe dana Sayd tana masa wata gulma Yana murmushi sbd fadanta da Mama kwata kwata ya dena qarewa.

AZIZ kuwa waya yakeyi a natse dan haka kai tsaye wucewa yayi bangarensa Yana cigaba da wayar.

Karfe 4 bayan yayi sallar laasar ya fito a natse cikin black highneck Bally wears da fcap din Calvin Klein komai nasa clean a natse Yana fidda qamshinsa me sanyi da bayyanarda luxury life kawai.

Yayi lunch already dan haka Yana fitowa Falaq ma ta fito cikin black Louis Vuitton dinta masu kyau daidai jikinta suka fice tana gefensa.

Daga shi sai itane suka fita dan haka shine da kansa yake jan motar a natse Yana jin idanuwanta akansa dan haka ya juyo a natse ya kalleta kafin ya bude baki yayi magana ta rigasa da cewa

"Daddy kamun alkawarin idan na cire damuwan komai a raina na samu cikakkiyar lafiyata zaka barni na koma Nigeria dan Allah Daddy pls inason komawa"

Shiru yayi batareda ya juyo ya kalletaba yaci gaba da driving a natse.

Idanuwa ta zuba Masa tana jiran amsarsa sbd baa taba iya gane yanayin Daddyn nata dan haka batasan a wane yanayin ya sake karban zancen nata ba sbd wannan shine Karo na uku tana masa maganar komawansu Nigeria.

"Yaushe kikeson ayi tafiyan?" Shine abinda taji a bazata dan haka cikin rudewa a farin ciki tace

"Ko next week Daddy"

Juyowa yayi ahankali ya kalleta da fararen idanuwansa yayi shiru tsawon seconds kafin ya bude baki yace

"Next week familyn LIMBA zasu koma Nigeria Falaq Aziz nayi Miki wannan alkawarin inshallah"
#MAMUH
#BEST LOVE
#BEST ROMANCE
#JANNAH ZAD
#AZIZ LIMBA
#FALAQ AZIZ
#AYSH NICKY
#AMMAR ZAD

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 10

Wasu hawayen samun abinda zuciya ke tsananin so ne suka gangaro mata tana kasa dauke idanuwanta akan Daddyn nata kawai iya bude baki tayi ta furta "thank you Daddy"

Bai juyo ya kalletaba sbd babu wata magana da zasu iya yi akan duk abinda ya shafi Nigeria da Yan cikinta bayan wannan sbd rantsuwa me karfin gaske da alkawarin dayake kansu na Maman akan babu Wanda a ahalinta zai taba sake maganar zamansu a Nigeria baya bare abinda ya faru acikinta dan hakan ne kwata kwata a LIMBAs aka shafe wannan tarihin a fili da baki.

Shiru ne kawai ya ratsa motar sbd babu me abin fada kuma har suka isa asibiti.

Dayake likitanta ne kai tsaye Wanda shine da Dr Nico tsaye a komai kanta har aikinta da akai da donor da aka ciro aka saka mata dan haka kai tsaye ciki suka wuce dan daman shi din su yake jira.

Suna shiga cikin girmamawa Yana tsaye yana waya ya kashe yana qarasowa gurin LIMBA din ya miqa masa hannu Yana masa barka da zuwa kafin ya kalli Falaq cikeda kulawa yace

"Hi Ms Falaq Aziz barka da zuwa"

Murmushi tayi tana cewa

"Thank you Doc"

Zama sukai Yana Kiran wasu nurses Guda biyu sbd Dr Nico baya nan.

Abubuwan daya kamata ayi mata na duba cikakkiyar lafiyan zuciyar dake kirjinta da bugawanta da duk sauran abubuwa kuma komai ya fito lafiya kalau babu komai a ayanzu shikenan bata buqatan sake zuwa sai taji wasu complications din.

Ajiyan zuciya cikin samun nutsuwa AZIZ ya kalli Dr Sam din yayi masa godia yana miqa masa hannu kafin suka miqe
Itama Falaq din godia Tai masa kafin suka fito ya rakosu har mota yana sake yiwa AZIZ bayanin komai akan masu ciwon.

Mota suka shiga suka bar asibitin Yana shiga tinanin ciwon da yanda yake a yanxu a zuciyarda ta shiga qunci da damuwa.

Numfashi ya sauke a boye Yana dan juyowa ya kalli Falaq dake cikin yanayi na samun nutsuwa kafin ya dauke kansa yanaci gaba da driving kirjinsa na nauyinda Yana buqtaan nasa maganin dayake kai tsawon shekara kusan biyu a yanzu.

Suna isa gida kai tsaye wucewa yayi bangarensa Yana buqtaan kebewa kawai.

Falaq tasan hakan sbd babu ranar da zasu asibiti bai shiga irin wannan halin na baya buqtaan kowa ba sbd ciwon da ake sake maimaita illolinsa ko bayan transplant indai ka shiga kunci me girma ko tashin hankali kan tashin hankali.

Ajiyan zuciya Falaq ta sauke tana bin hanyar palonsa da kallo idanuwanta na cikowa da hawaye sbd zuwa yanzu tasan Daddynta nada matsanancin ciwon depression daya kusan taba kwakwalwansa shima sedai batada yanda zata iya masa sbd a lokuta tashin ciwonsa ba hurumin shigarta bane tin ranar data ga halinda yake shiga idan ciwon ya tashi,ta shiga mafi girman shock da tashin hankali da qunci a rayuwarta sbd a iya shekaru bata taba sanin Daddynta na cikin wannan masifar ba da batada kyan gani,

Tayi kuka,tayi kuka ta kusa zarewa akan hakan har saida Papanta Sayd ya samu ya kwantar mata hankali daqyar ya kuma sanar mata komai akan shekarun rashin Ummitah a rayuwarsa da haihuwarta sune tsawon shekarun dayake cikin wannan mummunan halin batareda kowa ya Sani ba a duniya bayan shi da likitansa sai kuma JANNAH ZAD.

dago jajayen idanuwanta tayi ta kalli papan a lokacin sbd jin sunan Jannah dinta a Karo na farko a bakin wani tin bayan tsawon lokaci kuma Jannah ta San ciwon Daddynta ta zauna dashi ahakan ta tayasu rufewa batareda ko familynta ta fadawaba su da suke neman abinda zasu bata sunansa alokacin koman kankantarsa.

Kusan depression din itama ta kusa shiga sbd damuwa da baqin cikin halinda Daddynta yake rayuwa koyaushe kamar me ciwon hauka Amma ya boye musu sbd kada su shiga damuwa Amma shine Mama zata sakasa a rantsuwa da alkawarin daya qarasa lalata lafiyarsa da Sayd yayi shekaru Yana nema sbd a yanzu ciwonsa yafi baya tsananta a yanda papan ya fada shiyasa tayi alkawarin nemawa mahaifinta lafiya kota halin yaya.

Numfashi ta sauke me tsananin zafi da ciwo a alokacinda take tsaye har lokacin tana kallan kofar palonsa tana gurin tsaye P dinta yazo ya wuce ciki kai tsaye da sauri yana rufe kofar daga ciki
Wasu hawaye masu tsananin zafi suka gangaro mata ta kasa wucewa ta nufi kujeran dake saiti da kofar palonsa ta zauna ahankali tana share hawayenta ahankali ta zubawa kofan ido dukkanin jikinta na sanyi.

Tsawon lokaci me tsayin gaske kafin Sayd ya fito yabar palon batareda ya iya kallan Falaq dinba.

Ajiyan zuciya ta sauke ahankali jiki a sanyaye ta miqe tsaye ta nufi kofar palon ta miqa hannu ta bude ahankali ya shiga.

Kai tsaye bedroom dinsa zata nufa sai gashi ya bude kofar dakin a natse ya fito sanyeda jallabiya black me kyau ta kalli fuskansa ta sauke ajiyan zuciya bata ce komaiba ta kama hannunsa suka zauna a kujera ta kwantar da kanta gefen kafadansa tana bude baki ahankali ta furta

"I love you Daddy"

Lumshe idanuwansa yayi ahankali tareda bude baki daqyar yace

"Thank you for being here Falaq"

Haka ta zauna gurinsa ta tayasa zaman harya qarasa dawowa normal dinsa tukuna ta fice ta basa damar sallar magrib itama taje tayi tata.

Bai fito cin abincin dare ba dan haka babu Wanda ya gansa sai washe gari karfe goma da mintina ya fito a kame cikin navy blue Armani suit da Prada shades black a fuskansa.

A duk lokacinda Mama ta kalli AZIZ alfahari takeyi kai tsaye tareda godiyan Allah data kasance itace uwarsa sbd babu uwar da zata haifi da kamarsa bataiwa Allah godia Tai kuma alfahari da abinta ba dan haka a kowace sallarta bata dena yiwa FATIMA adduar hasken kabari ba idan kuma tana raye Allah ya bayyanar musu da ita sbd kaunarta da Fatima a jikinsu take tana fatan Allah ya hadasu a duniyar nan kafin Allah ya dauki ranta.

Falaq ma cikeda tsananin son mahaifinta tace

"Good morning Besty"

Kallanta yayi cikeda kauna yace

"Morning my precious"

Sayd hannu ya bata suka gaisa tana cewa

"Barka da fitowa our ranka ya dade"

Dariya yayi Yana matse hannunta har saida tayi Yar kara AZIZ yayi masa wani kallan daya sakasa sakinta Yana Yar dariya yace

"Dan duba maka lafiyanta nayi Sir"

Mama ce ta amsa gaisuwarsu a tare fuskanta a sake itama cikeda kaunarsu.

Fara breakfast din sukai AZIZ black lemon tea yasha da shawarma bread da akai toasting da egg.

Yana gamawa tissue ya dauka ya goge bakinsa ya dago ya kalli Mama a natse cikeda girmamawa yace

"Next week ne tafiyanku Nigeria kowa ya shirya komai zai kammala na tafiyan nan da 5days me inshallah
Idan akwai buqtaan da kowa keso Sayd zai kawo raw cash gida"

Ajiye tissue din hannunsa yayi zai miqe Mama ta ajiye spoon din hannunta fuskanta na sauyawa gabaki daya ta kira sunansa kai tsaye wanda hakan ya sakasa fasa miqewa Yana dagowa ya kalleta a natse kafin ya dauke idanuwansa cikin girmamawa.

Tsit table din yayi gashi Allah yasa Nicky bata gidan ta fita tinda safe sbd ita yaune jirginta da daddare zai daga zuwa Nigeria sbd zata rigasu isa.

Kallan Falaq Maman tayi kai tsaye tace

"Ki tashi zanyi magana da daddynki"

Dagowa Falaq tayi zata miqe tabar gurin mama ta kallesa fuskanta babu walwala ko kadan tace

"Idan harka gama yadda da amincewa akan buqatan Falaq na son komawa a duk inda tace tanaso to ka Sani ni kuma uwa a gareka wlh tallahi bazan taba binku ba zan koma kauye ne nayi zamana sbd bazai yiyu muna maida hannun agogo baya ba...

Dagowa yayi ahankali ya kalli Maman da idanuwansa da sukai ja take
ya bude baki zaiyi magana Maman ta daga masa hannu tana rage bayyanar fushinta da yanda ranta yake sake mummunan baci tace

"Har so nawa zaka biyewa duk abinda Falaq takeso?
Baka San ta girma bane tinda ta zama budurwa,
Ka yadda ka zubar da dukkanin tarin ayyuka da huldodinka tareda companies naka ka koma Nigeria sbd kawai Falaq ta fada hakan?

To idanma baka San dalilinta na son komawarba ni na sani bare kaima nasan ka Sani din dan haka tinda duka Kun gama yadda da komawar inason ka Sani daga ranar da muka sauka Nigeria wallahi tallahi duk wanda ya sake tada maganar Zaadens bare neman inda suke wlh ABDULAZIZ AYOUB LIMBA sedai ka sauya wata uwar bani ba dan har abada na cireka daga 'dana,
Ka Sani idan har zaka nema JANNAH ZAD da kanka ko saka wani nemanta ko dan kanka ko dan sbd Falaq na yafeka Ni sakina...."

Ahankali ya rufe idanuwansa da sukai wani irin jajir Yana hadiye wani irin abu daya danne kirjinsa me tsananin nauyi yana saka hannuwansa wata irin rawa me Muni Amma ya kanne ya jima shiru kafin ya bude idanuwansa Jan su na qaruwa ya bude baki ahankali cikin kamewa batareda yanayinsa ko daya ya bayyana ba anatse yace

"Allah ya huci zuciyarki Mama har abada babu Wanda zai iya taka umarninki a nan gidan"

Falaq dake tsaye bata qarasa fita ba tana jin hakan wasu zafafan hawaye masu tsananin zafi da ciwo suka gangaro mata tana dafe kirjinta sbd take wani radadi taji Yana gauraye kirjinta ta daddafa tabar gurin zuwa dakinta tana son fasa kuka Amma radadin wannan danyan hukuncin na mama data daure Daddy dashi yafi karfin kuka sbd zai yadda ya mutu da radadin rashin abinda zuciyarsa ke tsananin haukar so akan ya take umarnin Mam dan haka taji ciwon kirjinta na qaruwa ta rufe dakinta dan itama ta xabi ta mutun ma da ciwon ta huta da ganin halinda Daddynta zai shiga sbd girman wannan alkawarin.

Sayd ma wani irin zufa ne me tsananin gaske ya feso masa sbd tsananin tashin hankali da shock din maganar Maman Wadda ta gama kashe AZIZ dinne da kanta dan har abada kuma ta rasasa sbd bazai taba komawa AZIZ LIMBA dinta ba.

Miqewa AZIZ din yayi yai mata sai anjima ya fice Sayd na miqewa zufa na sake jiqasa yabi bayansa.

Kai tsaye mota ya nufa Sayd yayi saurin bude masa ya shiga ya rufe masa ya zagaya ya bude motar ya shiga ya tayar suka bar gidan.

Sanin waye AZIZ din har suka kai office baice komaiba motar tsit take.

Parking yayi ahankali ya bude ya fice yabarsa a motar ya tsaya daga waje tsawon mintina masu dan tsayi kafin AZIZ din ya bude ya fito bayan ya hadiye dukkanin emotions nasa.

Kai tsaye ciki suka nufa maaikata tako ina suna fitowa gaidasa yana amsawa da kai ko hannu kawai sbd fuskansa dake a kame ba fuska ko kadan.
#MAMUH
#BEST LOVE STORY
#HOT ROMANCE
#JANNAH ZAD LIMBA
#AZIZ LIMBA
#ZAADENS
#LIMBAS

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899

*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 11

A lokacinda Mama tariga da tasan AZIZ zai iya komai Amma bazai taba iya take umarninta ba dan haka ayau ta samu nutsuwa da kwanciyar hankalin data rasa na tsawon shekaru akan dawowan Zaadens rayuwarsu sbd tana jin shakka da tsoron girman abinda take gani a idanuwan AZIZ gameda Jannah Zad wadda babu alkhairi shigowanta rayuwarsu hakama sbd itane akaiwa tata 'yar kisan gillar da har abada bazata iya mantawa ba.

A yanzu data daure AZIZ da kalamanta, daurin da har abada tasan bazai taba kuncewaba koda Fatima zata dawo duniya kuwa bazata iya warwaresa ba sbd yanda tasan girmanta a zuciya da rayuwarsa.

Hankalinta ya kwanta zuciyarta ta samu nutsuwa da rashin fargaban sauka Nigeria ta zauna dan tasan maganar Zaadens kuma ta rufu kenan har abada tinda Allah ma ya raba duniyarsu ta tasu sbd a yanzu duk inda suke akwai nisan da babu cikewa har abada tsakaninsu.

Babu wani abu daya rage mata a rayuwar AZIZ dinta bayan aurensa da Nicky ta nunawa duniya tayi sirikar da babu gurbataccen jini a jikinta,

Zatayiwa AZIZ auren da a duk inda Zaadens suke zasu gani a labarai Susan sun jima da rufe babinsu na shafe tahirin auren yarsu a LIMBAs a yanzu 'yar da aka kashe mata tata Yar sbd gata da nuna karfin ikon dukiya ba kowa bace face bazawara a gabansu yanzu.

Gidan a ranar tsit babu wani farin ciki ko walwala damuwa ce me girman gaske a zukatansu Musamman Falaq da gabaki daya duniyarta take ganin ta juye a lokaci daya dan badan Mama itace mahaifiyar data haifi Daddynta ba data gama tsanarta ayau Amma dayake tana girmama duk abinda mahaifinta keso dan haka take hana zuciyarta tsanarta sbd daddy na kaunar mahaifiyarsa.

Mama kadai ce a gidan take farin ciki tana zuciyarta kalau sbd matsalarta da tsoronta ya kau dan haka batada sauran fargaba hankalinta kwance saima hidimarta takeyi itada Nicky da zata wuce hakama acan Nigeria tariga ta kira Sayd ta basa umarni ayau din kafin isar Nicky tini aka tanadar mata driver lafiyayye me xamanta tareda sabuwar mota fitinanniyar sabuwar mota daidai raayinta aka kuma sanar da securities da maaikatan gidan isowanta kafin su.

Saida ya sanar da AZIZ umarnin Maman Wanda ko sauraron duka zancen baya buqatan yi yace yayi duk abinda Maman tace kawai baya buqatan ji.

Karfe 7 na dare Mama da kanta ta fito ta saka Falaq binsu dole suka raka Nicky airport tareda Dr Nico Wanda yake rungume da Nicky din kwata kwata bayason rabuwa da ita sbd yasan zata saka kanta ne a motar da zata fito da dana Sani kila da damuwa sbd baisan gaba ba Amma bayajin akwai filin da kowace irin mace zata samu a zuciyar AZIZ LIMBA dan yasan komai na LIMBA ciki da waje tinda shine likitansa.

Dagewan Nicky din ya saka yabarta ta gwada koda akwai damar samun soyayyar AZIZ din tinda zai iya kaunarta ya bata dama ko dan sbd shi.

Mama ma kamar baby haka ta ringa tarairayan Nicky din tana mata fatan sauka Lfy da fadan ta kula da kanta sosai akwai isasun masu aiki da aka zuba kome takeso zasu mata.

Lafewa jikin Maman Nicky tayi tana sake nuna mata irin kewanta da zatai sbd jinta takeyi kaman mahaifiyar data haifeta sbd tsananin son datakewa 'danta ya shafeta.

Falaq Nicky din ta rungume itama tareda sakar mata kiss a tsakiyar kai tana cewa

"I will be waiting for you guys"

Numfashi Falaq ta sake tareda gyada Kai ahankali tana furta "safe landing" a taqaice.

"Thanks my LIMBAs precious" inji Nicky tana sake rungume brothernta tana jin tsananin sonsa da kaunarsa na saka idanuwanta cikowa da hawaye kafin ta sakesa it sake rungume Mama kafin ta juya ta wuce suna mata bye bye.

Suna barin airport din ba jimawa jirginsu Nicky din ya tashi suma zuwa Nigeria.

****Adaidai wannan lokacin kuma Jannah ce kwance jikin Ummanta idanuwanta rufe jikinta a sanyaye tana jin kewan Umman na ciko mata da kwalla a ido sbd ta dauki lokaci me tsayi bata kwanta jikin Ummanta b sbd yanayin jikinta sai yau din Umman da kanta taxo ta janyota ta kwantar da ita jikinta tana Shafa mata kai cikeda wata irin kauna da babu sirki itama tayi tsananin kewan Jannah din dan haka yau ta janyota da kanta.

Hawaye ne masu dumi suka gangaro idanuwan Jannah ahankali sbd kewan mutum da har abada bazata taba denawa ba bakuma zata taba dena jin radadi da ciwon rashinsu ba wato Miminta da Wanda bai mutu ba Amma a gurinta a zuciya da rayuwarta ya mutu.

Ganin hawayen dake gangarowa idanuwan Jannah ya saka Ummah ma idanuwanta cikowa da hawaye kawai suna gangarowa batareda tasan daliliba Amma dai tasan a rayuwarta idan har zataga hawaye idanuwan Jannah to itama nata idanuwan basu kasa zubo da hawayen ba hakama duk duniya batasan tsana ba amma da zataga abinda yake saka Jannah dinta kuka to zata tsanesa da dukkanin zuciya da ruhinta.

Saukan hawayen Umman akan gefen fuskanta ya sakata bude idanuwanta ahankali ta zubawa Ummah idanuwanta tanajin kaunar da batasan ta inda take fitowa ba ga Umman,

Ta rasa wace irin kauna me tsananin tsafta da girma takewa Ummah wadda bata jinin komai da itaba Amma tanajin kaunarta har jininta kamar yanda ta rasa wace irin kauna Ummah ke mata.

Sharewa Umman hawaye tayi tana komawa ta kwanta a kafafunta tareda lumshe ido wannan karon baccin me dadi da nutsuwa tayi a jikin nata.

Se dare sosai ta farka taga Umman na dakin nasu har lokacin wato bata tafi gurin Dad ba Wanda gabaki daya yake cikin damuwar ko ta samu tayi baccin.

Rufa tai mata tareda addua kafin ita kuma ta miqe ta fada toilet tayo fitsari tayi alwala ta fito tafara nafilolin dare ta jima tana adduoi kafin ta miqe taje ta kwanta take bacci me nutsuwa ya dauketa.

Washe gari tinda asuba aka tada Ammar akai masa sauyin aiki aka basa key din lafiyayyar sabuwar motar BMW iX tareda suna da hoton Nicky Managern kamfanin 4&4 ya kawo masa yace yaje airport ya dauko matar gidan.

Baiji komaiba ya amshi sauyin aikin cikeda girmamawa ya fice daga gidan ya kama hanyar airport Yana kallan gari cikin sanyi da nutsuwa.

Yana isa babu bata lokaci ko wahala ya samu damar ganinta ya zuba mata ido kafin ta iso gurinsa Yana kallan halfcast din macen da kana ganinta bazakai mata tinanin musulma kai tsaye ba duk da doguwar Arabian gown ce jikinta dark brown Amma yanayin yanda ta Dora gyaralen ne fiyeda rabin gashinta a fili.

Dauke idanuwansa yayi daga kanta Yana qarasowa gurinta cikin nutsuwa yace

"Welcome"

Kallansa tayi kafin tace komai ganin sunan 4&4 baro baro dake jikin shirt dinsa me kyau da jeans ya sakata kai tsaye sanin drivernta ne ya iso.

Fasa amsa gaisuwarsa tayi ta miqa masa kayanta wanda ya karba ya tura har mota ya saka bayan ya bude mata motar ta shiga ya zagaya ya shiga ya tayar batareda ya sake furta komaiba har suka isa gida.

Kallo daya tayiwa gaban 4&4 mansion din ta tsayar da idanuwanta akan sunan sbd bata dauka har gidan da AZIZ LIMBA zai zauna ba a qasarsa bazai saka masa sunansa ba sedai numbers da haryanzu basuda maanar komai.

Cikeda girmamawa dukkanin securities din gidan suka taso suka mata barka sauka aka bude gate din suka shige da motar.

Maheer ne da Dad suka bude gate din na biyu a tare Wanda ya saka zuciyar Ammar dake kallansu wani irin ciwo da radadin ganinsu suna bude kofar gidan wani.

Shigowa yayi yai parking ya fito ya zagayo ya bude mata kofar suma su Dad din cikeda sosuwan zuciya suka sauke idanuwansu daga kallansa.

Fitowa tayi su madam Sisi na fitowa tarbanta cikeda girmamawa aka fara mata barka da zuwa duka cikin turanci sbd ba hausarta bata irin karfin nan ba dik da tanaji sbd tsawon shekara biyun datai dasu mama ta koya sosai.

Ciki akai da kayanta tana tafe bayansu kafin ta dakata ta kalli Ammar ta ciro 100 dollar ta miqa masa tace ya nemo mata layin Nigeria me kyau.

Karba yayi Yana cewa ok.

Lafiyayyan sitting room din farko data fara sako kafarta ta sake sauke ajiyan zuciya akusan Karo na biyar sbd ta tabbatarda taxo inda zatai rayuwa irin Wadda takeso sbd duka luxuries na rayuwar duniya babu Wanda babu a 4&4 mansion dan haka AZIZ LIMBA kawai ya rage mata ta mallaka Wanda a cikin gidan nan takeson tafara Haifa masa yayan da zasu sauya rayuwarsa gabaki daya su bata lasisin zamowa rayuwarsa har abada.

Lafiyayyan bedroom din dayake hade da wani nutsatsen palo aka kai kayanta Wanda tini aka gyaresa aka kunna ac da qamshi da komai hatta su towels da toiletries an siyo an jeresu tas.

Wanka kai tsaye ta fara shiga tana fitowa ta saka riga da wandon bacci sallarma da kyar tayi ta haye gado tareda kashe hasken dakin t shige duvet bacci me nauyi ya dauketa.

Fatma ce taxo ta duba tana bacci dan haka baa sake zuwa ba sbd kada a dameta saida ta tashi dan kanta karfe biyun rana kafin ta sake wanka ta fito sanyeda doguwar riga mara hannu da qaramar scarf na Versace akanta tana fidda qamshi ahankali.

Madam Sisi ce da kanta tayi serving dinta abinci lafiyayye varieties taci tana gamawa ta koma palo daidai nan Jannah ta sako kai a natse cikin rashin hayaniya sanye da Doguwar riga boubou daidai jikinta da hula hannunta riqe da jakar MTN da Ammar ya bata ta kawo mata.

Muryan Jannah dince data gaidata cikin fluent English dinta dayake bayyanarda kai tsaye su din a turai aka haifesu kuma suka taso...

Hakanne ya saka Nicky dago idanuwanta da sauri ta sauke akan Jannah din tareda zubawa fuskanta ido tana kallanta batareda ta iya dauke idanuwanta akantaba.

Jannah dinma dago idanuwanta tayi jin shiru ta sake magana a natse tana miqo jakar tareda tarin canjin kudin dake cikin jakar da layin yake ciki.

Hannu Nicky ta miqa ta karba Jannah din ta juya zata fice ta bude baki tace ta dawo ta saka mata layin sbd bazata iyaba.

Dawowa Jannah tayi ta karba tareda karban wayar ta saka mata ta juya t fice zuwa aikinta.

Da daddare Jannah ce tayi serving dinta abinci tanaci tana waya da mama hankali kwance batareda jin kadaici ko wani abin ba.

Washe gari kai tsaye tace aikin Jannah takeso a komai sbd tafi iliminda zata ringa fahimtar abinda takeso dan haka Jannah ce ta koma me aikinta komai bata iyayi sai anyi mata.

Nicky haka kawai ilimi da kyan Jannah tareda wani irin class datake dashi Wanda a jininta yake sai take ganin kamar girman kai Jannah din ke nunawa ita kuma ta tsani Wanda yake qasanta yafita kowane irin abu dan haka tanason raba Jannah da wannan nutsuwar datake dashi dan haka duka ayyukanta n wahala ne Jannah keyi gashi Jannah din bata wani cika magana ba komai tace tayi zatace ok shikenan.

Ammar ma ta nasa bangaren aikin yawon wahala ne sukeyi sosai dan kullum sai anfuta da ita gashi batasan koina b shine me kaita harta gama shigarda report na zuwanta zatai hutun satika kafin ta fara zuwa aikin.

A hakan sati ya zagayo gabaki daya Nicky ta rikita gidan da murnan zuwan sauran familyn gidan da zasu iso a Daren ranar amma banda mai gidan a yanda suka ji.

Sabbin motoci aka kawo da wasu drivers din daga kamfani na mahaifiyarsa da 'yarsa dan haka karfe 1 jirginsu zai suka na dare dan haka duka motocin suna airport tin 11 na dare dan daukansu zuwa gida.
#MAMUH
#JANNAH ZAD
#AYSHNICKY
#ZAADENS
#LIMBAS

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 12

Sai dare sosai motocin da suka dauko su Mama daga airport suka iso bakin main gate na 4&4 mansion aka bude musu cikeda girmamawa da farin cikin zuwansu motocin suka shige tin kafin su iso second gate Maheer da Dad suka wangale gate din suna rabewa gefensa suna musu hannu alaman barka da isowa Wanda babu Wanda ma ya lura dasu a cikin motocin harsuka wuce kurya sukai parking.

Madam Sisi da Nicky ne suka fito suka tarbesu suna musu barka da zuwa kafin sukai ciki dasu kowannensu a tsananin gajiye dan haka babu abinda suka tsaya sukai ciki.

Suna wucewa ciki su Maheer na gama rufe gate din suka nufo motar ganin Jannah itama sai alokacin take isowa sbd tsayawa yiwa Ummah addua datai sbd haka kawai taketa hawaye ba kakkautawa.

Uban akwatina ne nasu masu shegiyar tsada designers na LV dasu Versace dasu Fendi set set,

Jan kayan suka fara Jannah da Fatma da Amina suna kaiwa cikin gida a first sitting room da babu kowa sai madam Sisi datake kokarin fara hada dining kafin su sugama shigowa da kayan sbd masu gidan sun riga sunyi ciki.

Sun dade suna shigowa da kayan kafin suka gama shigowa dasu tas

Kafin daga palo suka sake daukansu daya bayan daya suna kaiwa bedrooms nasu Wanda kowannensu Yana toilet babu wanda suka tarar a daki,

Suna gama kaiwa suka sauko suna barin palon zuwa kitchen dake palon suka cigaba da hada dining da warming wasu abubuwan da duk aka dafa musu.

Suna gama shirya dining din suka wuce sbd madam Sisi ce keda hurumin serving nasu.

Dakunansu suka koma sukai abinda zasuyi suka kwanta.

Washe gari tinda safe suka tashi tinda yanzu masu gidan sun dawo aikin daban yake dana baya dan haka kai tsaye wanke Jannah tafara yi ta kafin Fatma suka shirya tsaf a natse suka nufi cikin gida.

Jannah ce me aikin sitting rooms dan haka ta fara wucewa sama tafara aikinta a natse.

Fes ta gyare koina ta kunna AC da qamshi ta sauko tafara na palon kasa shima ba jimawa ta gama koina ya sake daukan kyau da qamshi me nutsuwa da dadi tareda tsit sbd babu wanda ya tashi bacci.

Kitchen ta nufa Wanda Fatma da Amina sunyi nisa a aiki dan haka ta saka hannu suna dan fira sama sama Banda ita bata wani cika saka baki ba hakama firar bame hayaniya ba sbd kada a tada masu gidan.

Sbd abincin kusan kowa da Wanda yakeci a menu da aka basu dan haka basu gama aikinba sai kusan 10 dan haka suka jere dining tsaf ita kuma ta fara gyara kitchen din da wanke kayan da akai amfani dashi.

10:30 masu gidan suka fara fitowa ciki hadda fiddausi Wanda ta dade da zama limba itama kawai dai sbd sabo ne wani abin idan ba ita tayiba sai su Falaq din basa jin dadinsa.

Zaunawa sukai dukkaninsu a dining suka fara cin abinci madam Sisi da Fatma ne sukai serving nasu Jannah da Amina na kitchen na fama da sauran aikin.

Sosai suka samu nutsuwa da komai na breakfast din dan haka duk complain din Mama da Falaq basu ce komaiba har aka gama saima Nicky dake kokarin nunawa Mama maids din gidan ba laifi.

Suna gamawa suka bar dining din suka haye sama dukkaninsu babu Wanda ya sake jins dan haka masu aiki suka hau aikinsu a natse.

Jannah ce ta gyare dining din ta sake gyare koina,
Fatma kuma sai lokacin taje sama ta gyaro bedrooms dinsu duka ta sauko.

Lokacin sallah nayi sukaje sukayo sallah bangarensu suka taho suka Dora abincin rana Wanda shima bame hayaniya sukeso ba dan haka Jannah ce yawanci datasan kan abincin mutan turai suke barwa gurkin suna ji da sauran ayyukan walahar.

Hidima suka wuni sunayi sai magrib suka baro bangaren,
Jannah ce ma tafara wucewa tana gama girkin ta zuba a warmers da sauran abubuwan
Su kuwa sai bayan sun gama shirya dining tsaf da tsaftace kitchen din kamar baayi aiki a cikinsa ba suna kokarin ficewa fiddausi ta shigo tana sakewa dasu harda Jan su dan surutu ta dafawa Mama Arabian shayi ta kai dining suka sake gyare gurin suka fice zuwa bangarensu sbd fiddausi ce zatai serving nasu tace.

Jannah na isa dakinsu wanka tayi Tai sallah ta nufi gurin shan iskansu itada familynta ko data isa suna kan qatuwar dadduma Ammar na sallah da bai samu a jam'i ba sbd shegen yawon da Nicky ta fita dashi wai siyan facesheet dinta daya qare.

Maheer da Dad na zaune suna magana Ummah na gefen Dad din Yana bare mata lemun bawo da qaramar wuqa Garba kuwa ruwa ne yaje kitchen din girkin masu aiki ya dauko musu.

Tana isowa zaunawa tayi gefen Maheer tana miqa masa hannu a gajiye tace

"Nima zansha oranges din,am just so tired"

Kallanta Sukai dukkaninsu suna ce mata sannu.

Miqawa Ummah nata Dad yayi cikin kulawa Yana cewa

"Gashi kisha Amma karki sha da 'yayan ki zubar shima idan yayi Miki tsami karki sha a yanka Miki wani kinji"

Gyara masa kai tayi tana rabawa biyu ta basa tace

"Kasha kaima"

Karba yayi yakai bakinsa yasha Yana jin baida tsami yace

"To nasha Kisha kema zan yanda Miki wani"

Fara Sha tayi shikuma ya fara yankawa Jannah Maheer kuwa kafafunta data miqe yafara dan Danna mata sbd jikinta ya rage gajiya yanajin kaman ya cire gajiyar da duk takeji ya dawo da ita jikinsa.

Ammar na gama sallah juyowa yayi yana yanka mata lemun harda cire mata yayan yana bata Yana basu labarin tsinannan yawon da matar gidan ta jasa shikuma Dad yaci gaba da yankawa Ummah suna firarsu hankali kwance.

Fatma na isowa bayan taje itama tayi wanka da sallah suka fara cin abinci duk da baa kwano daya bane sun saba tare suke ci suna firarsu wadda take cikeda kulawan da sukewa juna da yanda suke tsananin kaunar juna.

Ummah da Dad a plate daya sukeci Wanda duk rabi ita yake bawa saita koshi kafin yaci,

Maheer da Jannah da Ammar kuwa suma a plate daya suke ci wata ran kuma Ammar da Jannah din zasu tare Maheer yaci shi kadai.

Fatma da Garba da suke uwa daya uba daya kwata kwata babu sabo ko shakuwa ko tsananin kaunar juna a tsakaninsu a baya Amma zama cikinsu Zaadens din a yanzu kauna da shakuwa ce me girma a tsakaninsu sbd suma a ko yaushe yanzu tare suke ci dan haka suke samun nutsuwa da kwanciyar hankali sbd duk wunin da kowa zaiyi Yana aiki da anyi magrib suna tare har dare sosai sungama shan iska da fira kafin kowa ya shige.

Gari na sake wayewa hkaa kowa ya sake kama aikinsa kamar koyaushe Jannah na gamo gyran sama tana kitchen tana aikinta Wanda tana gamawa zata koma bangarensu kawai dai abu dayane take fuskanta yanda Nicky haryanxu bata son aikin kowa sai nata din Wanda zatai so goma tace bai mata ba ahaka zatai rabin wuni tana wahala a dakin Nicky din.

Tana gano quntata mata da cin zarafinta Nicky din takeson yi sai bata taba nuna damuwa ko gazawa ba akan duka wahalar datake bata ba sbd kada ta nuna gazawa familynta tsaf zasu aje aikin sbd ita su tafiyarsu su hakura da duk abinda zasu samu ita kuma tinda basuda wani xabi gashi ko gurin zama basu dashi batason ta zamo sanadiyar sake jefasu wani hali sai kawai tana shanye duk wata quntatawa da wahalar datake fuskanta.

Tinda masu gidan suka dawo koyaushe suna sama basa saukowa idan ba abinci zasu ci ba dan haka kaf masu aikin gidan bayan Madam Sisi da Fatma data taba ganinsu kokuma ace datake ganinsu sbd lokacin datake zuwa gyaran dakunansu sun tashi suna gurin cin abinci ztaje ta gyaro ta sauko.

Babu wani me aiki dayake da ikon ganinsu sai da babban dalilin dan hakanne ma da sun gama ayyukansu suke ficewa zuwa bangarensu fiddausi ce me aikin serving nasu da sauran ayyukansu dan haka basu damu da masu aiki ba kaman yanda masu aiki basu taba samun dama ko hurumin tinanin ganinsu ba.

Basa yawo koina sai Nicky datake yawon fita aiki da kuma yawonta na banza koyaushe a cikin kashe kudi a banza a wofi take dan haka ne ma koyaushe tana gurin yawo tana dawowa zataita saka aikin rashin dalili sbd Mama ta tsaya mata kaf masu aikin gidan babu Wanda yasan cewa bawai asalin matar me gidan bace da babu aure a tsakaninsu shiyasa ake tsakanin girmamata da bin dukkanin umarninta.
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 13

Kusan watansu fiyeda daya da dawowa babu Wanda ta taba fita a tsakanin Mama ko su Falaq koyaushe suna sama hutu da rayuwar hutu kawai.

Suna cika wata biyu da dawowa Mama ta shirya tayi tafiya zuwa kauye dan haka aiki ya dan rage musu sbd an rage yawa sbd tareda fiddausi ta tafi daga Falaq sai Nicky ne.

Ahankali ahankali kawai Nicky taji batama kaunar Jannah kawai sbd har yau ta kasa ganin gazawarta hakama a yanda tai mata tambayoyi taji makarantikan da qasashen datai yawo take taji ta qyamaceta sbd har abada batason Wanda ya fita sbd idan aka fita jin takeyi zata iya hallaka ka ko illataka sbd ka koma nakasu akanta,

Akan marks na school tasha tura yara da yawa a staircase na school tin tana yarinya har zuwa gama karantunta Tasha taka mutane da mota ta ayi case din a gama sbd bata yadda da zuwa bayan wani ba a komai na rayuwarta dan hakanne ma takejin batada nutsuwa har abada koda ta samu AZIZ LIMBA saita San inda matarsa ta farko take idan tana raye ta kawar da ita daga duniyar gabaki daya hankalinta zai kwanta shiyasa ta dagewa zuwa Nigeria sbd tasan tabbas a Nigeria take Amma babbar matsalar datake tokare da zuciyarta shine kaf familyn har Mama babu Wanda ya taba fada mata komai na rayuwarsu na baya bata Sani ba waye matar?
meya rabasa da ita?
Tana raye ko mace?
Rabuwa sukai ko rasuwa tai?
Matarsa ce ta haifi Falaq kokuwa Ummitah?

Duka wannan abubuwan babu Wanda ya taba fada mata su ta kuma rasa tayaya zata Sani sbd AZIZ LIMBA sai Abinda yaso a Sani akansa ko familynsa ake Sani dan rayuwarsa a tsari da wani irin tsaro da privacy yake yinta.

Yayanta Dr Nico har haukarta tashi tayi akan ya fada mata Amma yaqi fada sbd sirrin dake tsakaninsa da LIMBA da yawa sedai idan sun mutu Amma akwai Amana me karfin gaske a tsakaninsu dan haka bangarenta daban bangaren LIMBA daban a rayuwarsa.

Wannan dalilin ne ya saka batada cikakken bayani komai akan tsohuwar matar LIMBA Amma tayi alkawarin bazata taba samun nutsuwa da kwanciyar hankali ba idan bata nemo ta ba.

Sosai taji ta tsani Jannah a gidan dan haka kai tsaye tace a nemo replacement dinta batasonta a mansion din kwata kwata.

Hakan ya saka Madam Sisi ba tareda tinanin komaiba ta dauki tsana itama ta dorawa Jannah din sbd sake samun gindin zama a gurin Nicky wadda manyan kudi ta direwa Madam Sisi tace tanason kota halin yaya ta nemo mata komai gameda matar LIMBA tshohuwa.

Indai ga kudi babu abinda Madam Sisi bazata iya yiwa Nicky ba dan haka itama goal dinta ya zama daya shine koda zata bata saita nemo labarin tsohuwar matarsa duk da tini Mama ta saki kudi masu yawan gaske aka goge labarai da komai daya shafi auren AZIZ LIMBA da JANNAH ZAD.

***Satin Mama biyu ta dawo d yamma motarsu ta shigo harabar gidan wanda Maheer dake gefe taya Ammar goge mota jin horn da sauri ya nufi gate din
Dad ma dayake baya da sauri ya fito jin horn ya nufo gate din shikuwa Ammar juyowa yayi Yana kallan motar dake shigowan su Dad da Maheer suka bude gate din a tare suna fitowa a tare daga bayan gate din wanda yayi daidai da dagowan Mama dake waya da AZIZ LIMBA ta kalli gabanta bakinta na rawa ahankali cikin wani irin sauti bugawan zuciya na shirin kamata tace "ZAADENS"

Shiru AZIZ yayi sbd yanda sunan ya sauka cikin kunnuwansa ahankali ya isa kirjinsa Yana yanka wani budadden ciwon dake dabaibaiye da kowane irin lungu na zuciyarsa,

Ahankali ya kashe wayarsa batareda ya iya furta kowace kalma ba sbd sanin koma menene Maman bata hayyacinta tinda bakinta ya furta kalman da itace tace bata yafe kowa a ahalinta ya fada ba.

Ajiye wayarsa yayi gefensa Yana dago idanuwansa da suka sauya take ya kalli baqin da Sayd ya shigo dasu Yana miqewa dan basu hannu su gaisa a natse cikin steeze dinsa dayake boye kowane irin yanayinsa.

Kallo daya Sayd yayiwa idanuwansa ya sauke kai Yana juyawa ya fice dan dauko takardun daya baro office dinsa Wainda dasu zasu zaman da baqin.

***Mama da bugun zuciyarta ke tsananta numfashinta na neman sarkewa ko tsayawa motar bata gama yi ba ta Dora hannuwanta dake wata irin rawa akan murfin motar zata bude sai kuma ta fasa da sauri ta janye hannunta tana zubawa fuskar Dad idanuwanta dake qanqancewa tsabar shock da masifaffen tashin hankali.

Fiddausi ma dake gaban motar zaune akan fuskar Ammar Zad idanuwanta suka fara sauka take numfashinta ya tsaya cak a rikice ta juyo da sauri ta kalli Mama dake baya taga numfashinta na neman daukewa idanuwanta kafe akan fuskar Dad.

Da sauri fiddausi ta juya inda Maman ke kalla itama nata idanuwan suka sauka fes akan fuskar Dzad kafin ta riqe numfashinta dake futa da karfin gaske Maheer ma ya bayyana a bayan Dzad din dukkaninsu sanye da shirts masu dauke da sunan 4&4 mansion Wanda babu tantama hakan na nuni da a cikin maaikatan gidan suke,

Shin sun San a inda suke kuma suka zauna suna aiki kokuwa basu Sani ba??
Shin wace sabuwar masifar ce zata afko ayanzu da katsam Allah ya bayyanardasu a cikin gidan bayan rantsuwa da alkawarin da duka ahalin gidan suke daure a cikinsa na Mama.

Kokarin dawo da kanta daidai Mama tayi cikin karfin hali da hadiye duk wata tafasan zuciya da baqin cikin daya taso tayi ta sauke ajiyan zuciya kafin ta dawo da idanuwanta ahankali akan fiddausi da har jikinta rawa yake dan yi.

Numfashi me zafi Maman ta sake sakewa kafin ta iya bude bakinta tana kame fuskanta sosai ba sakewa ko kadan tace

"Ko a cikin mayen hauka karki yadda ki fadi abinda kika gani,
Baki ga kowa ba,
Bakima San kowa ba idan wannan maganar ta shiga kunnen Falaq ko Sayd da zai iya kai zancen kunnen 'dana ki Sani zamanki da Falaq a limbas ba ma ya qare kwata kwata har abada,
Ina fatan kin fahimta kin kuma San abinda kikeyi?

Jajir idanuwan fiddausi sukai take sbd girman magana da abinda Maman take shirin aikatawa na hana kowa sanin Zaadens na mansion din duk da tasan zaiyi wuya gobe a wayi gari dasu a mansion din batareda ta tabbatarda sun bata ba.

Tayaya zata boyewa Falaq Zaadens na tareda su a mansion daya Wanda ta tabbatarda Jannah bata nesa tana kusa idanma bata cikin mansion din sbd zaiyi wuya Zaadens su iya tafiya koina batareda jannarsu ba?

Tayaya tana kallo Falaq na kuncin rashin Jannah suna guri daya Amma ta kasa gaya mata har sai Mama ta korasu inda bazata taba samunsu a kusa ba kila?

Amma kuma hukuncin Mama yayi mata tsaurin da batada xabi saina binsa dan haka ta sauke idanuwanta ahankali jikinta a tsananin mace tace

"Inshallah Mama"

Ajiyan zuciya Maman ta sauke kafin ta dauke kai daga kallan fiddausin ta cewa driver yakaisu ta gurin hanyar shigar Mai gidan idan yana gari.

Daman bai kashe motan ba ya jata zuwa gaba sosai har bakin inda motan me gidan take ta kofa ta Musamman yayi parking.

Su Dad bayan motar suka bi da kallo da mamakin kodai Mai gidan ne a ciki y dawo tinda akai can ciki sosai da ita.

Basu wani damu ba suka koma bakin aikinsu a natse hankali kwance.

Ita kuwa mama bude mata motar driver yayi ta fito ta shige ciki har lokacin zafin zuciyarta bai sauka ba.

Fiddausi jiki a sanyaye ta fito ta shige ciki da kayansu itama zuciyarta gabaki daya a sanyaye da kuma fargaba.

Suna shiga suka haye sama fiddausi takai kayan Mama har bedroom dinta tukuna ta fito ta nufi nata dakin tkaia kayanta ta kasa fitowa taje dakin Falaq sbd yanda takejin kaman bazata iya fuskantarta ba.

Da daddare a waya Mama ta kira Madam Sisi har bedroom dinta abinda bai taba faruwa ba.

Zaune Maman take kan sofa bayan gama sallar ishai dinta sanye da damuwar riga me laushi da qaton mayafi a jikinta ta fito dattijuwan datake cikin hutu da daula.

A natse Maman ta kalli Madam Sisi ta bude baki batareda ta amsa gaisuwanta ba ta jefa mata tambayar data sakata mamaki kai tsaye

"Su waye securities na second gate Dana gani?
Meye sunayensu?
Tsawon yaushe suke aiki a mansion din nan?
Su kadai ne ko akwai budurwa a tareda su???

Shiru Madam Sisi tayi kafin ta dago ta bude baki ta fara da amsa tambaya ta karshe da cewa

"Mata biyu ne a tareda su da budurwa da kuma mahaifiyarta me tabin hankali"
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS
#HOT LOVE
#HOT ROMANCE
#TWIST

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 14

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi  1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection  1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Dago idanuwa Mama tayi ahankali cikin tsananin mamaki da son sake jin abinda Madam Sisi din ta fada zuciyarta na wani irin zafi da quna me tsanani jin Jannah Zad na cikin mansion din itama,
Jannah Zad na cikin inda LIMBAs suke?
Jannah na guri daya da inda Falaq da AZIZ LIMBA zai kasance?
Jannah na guri daya dasu suna kwana a gida daya?

Wace irin juyayyar kaddara ce wannan?
Jannar datake kwana tana wuni adduar Allah ya nesanta ahalinta da ita,
Jannar datake hana kanta bacci gurin adduar Allah ya hanasu ya kore musu kaddarar ko sake zama qasa daya ko gari daya har abada itace suke kwana guri daya duk lokacin nan batareda saninta ba,
Da Falaq ce ta fara ganin daya daga cikinsu Zaadens dame zai faru kenan?

Inda AZIZ Yana qasar da shima me zai faru daga lokacinda yaga Zaadens ko Jannah din da kanta???

Wani zufan tashin hankali ne taji Yana gangara a cikin rigarta ta sake dago idanuwanta ta kalli Madam Sisi tana ma rasa tambayar jefa mata sbd tafasar da kirjinta ke yi

Madam Sisi data dauka jin akwai me hauka a gidan ne yake buga zuciyar Maman bude baki tayi dan dan gyara zancen tace

"Tabin hankalin uwar bame duka bane ko tashin hankali kawai dai kamar y maidata qaramar yarinya ne..."

A Karo na uku Mama ta dago jajayen idanuwanta ta sake saukarwa akan Sisin sbd a iya saninta da tabbacinta Mimi ta rasu hakama Anny tana gidan yari ita baa sakota ba sbd nata hukuncin daban da nasu tinda ita matar Mahmoud Zad ce ta tsaya akan saita karbi hukuncin kisan mijinta yanda ya kamata,

To ta ina Zaadens suka samu mace kokuma tayaya suka samu uwar data maye Mimi?
Aure Dzad yayi?
Shin daman yanada nutsuwar aure bayan duka masifun da suka saka mutane da Wanda su suka shiga?
Kokuwa karya sukai Mimi bata rasu ba???????

Qarasa tinanin tayi kirjinta na saiya dokawa sbd idan kuwa hakanne tabbas ma Zaadens sun wuce duk iya shedanun da ake tinanin sun kai sedai kuma baa gidanta ba kuma baa cikin ahalinta zaa qarasa wannan mummunan rayuwar ba

Hakama a nata bangaren daga lokacinda Falaq ko AZIZ suka San Zaadens na gidan komai nata zai lalace,rayuwar ahalinta zai sake shiga mummunan halinda baa San wa kuma zaa rasa ba,

Bayyanar Jannah a ahalinta zai warware mata duk wani alkawarin data daure kowa dashi warwaren da har abada bazai sake qulluwab dan haka kota halin yaya bazata taba barin hakan ta faru ba.

Hakama a dayen bangaren Nicky na sanin Jannah da matsayinta na baya a gidan bazata taba hutawaba saita aikata abinda zai iya kai sunansu inda na Zaadens yake wato mummunan suna.

Madam Sisi da duk ta nutsu tana karance tsaf halinda Maman take ciki mamaki da nazari ta shiga akan Mama tasan Zaadens kuma alamu sun nuna batason zamansu anan.

Batareda Mama ta dago ba ta bude baki fuskanta a kame kai tsaye tace

"Ki Sallamesu ayau dinnan su bar 4&4 zuwa Jibi zansa a kawo sabbin masu aikin da suka fisu sbd banda nutsuwa da zama da masu aikin da akwai masu hauka acikinsu"

Dagowa Madam Sisi tayi cikin tabbatarda tinaninta akan hakan ta bude baki cikeda girmamawa tace

"Mama zasu iya kaiwa gobe da safe sbd yanzu haka suna kan aiki kuma idan suka ajiye ba kowa a qasa,
Hakama Ammar Zad din Mss Nicky ta fita dashi yanzu nan,
Amma ayau din zan sanar dasu zasu hada komai nasu a Daren Nan da safe su wuce,sedai kuma akwai sauran balance dinsu tinda nanda sati daya zaayi salary dan haka suna bin na wannan watan"

"Zan baki balance din ko nawa ne ki basu Amma ki tabbatarda gobe koda kowa zai tashi sun bar 4&4 idan ba hakan ba kece zaki fara wucewa kafin su biyo bayanki"

Dago kai Madam Sisi tayi tana girgiza kai tace

"Kafin 9 na safe nayi Miki alkawarin sun bar gidan nan"

Kofa Maman ta nunawa Sisi da hannu sbd tsananin sarawan da kanta yakeyi batason cigaba da magana.

Madam Sisi na fitowa daga palon Mama kitchen ta wuce kai tsaye inda Jannah ke aikinta a natse,

Mandi Rice takeyi sai meatballs da chicken soup da Nicky takesha koyaushe,

Itada Fatma da Amina suke aikin Amma ta fisu nutsuwa a aikinta duk da suma babu me rashin nutsuwan kawai dai tata tafi bayyana ne sbd rayuwar data taso a cikinta da ilimin tareda wayewanta.

Daya bayan daya Sisi ta ringa binsu da kallo tan karantarsu kafin ta sake tsayar da idanuwanta akan Jannah tana shiga tinanika kala kala kafin ta bude baki kamar daga sama dukkaninsu sukaji tambayarta data saka kowannensu juyowa cikin tsananin mamaki a bayyane Banda Jannah data tsaya cak batareda ta juyoba gurin yayi tsit har sai data sake maimaita tambayarta tana kallan Fatma da cewa

"Jannah kin taba aure ne??

Numfashi me dumi Jannah ta sauke ahankali tareda lumshe idanuwanta ta budesu sun dan sauya kafin ta juyo ahankali ta kalli Madam Sisi din da girmamawa ta bude baki a natse tace

"Aa,namiji daya ne a rayuwata AMMAR ZAD kuma bamu riga munyi aurenba"

Fiddausi dake labe ta kofar palo tana kallan Jannah din cikeda wata irin kewa da kauna jin abinda ta fada ya saka idanuwanta cikowa da hawayen qaqanikayi sbd babban kuskuren da zatai Wanda hukuncinsa zaifi na mama shine tanaji tana gani ta kuma Sani tayi shiru har Zaadens subar gidan harma Jannah ta auri Ammar batareda ta nuna ko sanar da Falaq ba ko Sayd.

Sake tsayar da idanuwanta tayi akan Jannah tanajin kamar ta fito ta isa ta rungumeta ta karban mata duk aikin duniyar nan batareda gazawa ba Amma tasan ba halin fiddo kanta a gaban Jannah din sbd gargadin mama.

Madam Sisi kuwa kallan Jannah din takeyi tana juya maganar akwai aure tsakanin Ammar da Jannah bayan kallan uwa daya uba daya take musu dukkaninsu,
Kenan dai akwai abubuwan dake boye da rayuwar Zaadens din sedai kuma koman zamanka munafuki baka iya sanin komai nasu dan tin ba yanxu ba takeson sanin sun din su waye ina suka samu ilimin da suke dashi dan rayuwarsu duk da suna cikin talauci batai kama da asalin talakawan ba amma kwata kwata ko su garba da Fatma dake yan uwansu basa sanin komai game dasu daga su sai su suke sanin iya abinda ya shafesu.

Maida idanuwanta kan Fatma tayi Wadda tayi saurin juyawa tana saka hannuwanta a cikin Naman kazar data ciro a freezer zata saka mata ruwa gabanta na faduwa sbd batasan me zatace ba idan itama akai mata tambayar kokuma batason ta bada amsar da zata saka asan eh Jannah din ta taba auren.

Numfashi me dumi Madam Sisi ta sauke ahankali tana barin kitchen din tareda jiran dawowan Nicky ta sanar da ita komai.

Tana ficewa Jannah bata ko waiwayo ba taci gaba da aikinta zuciyarta na wani irin ciwo sbd a duk lokacinda aka tinatar da ita auren kaddara ya taba hawa kanta tsanar kanta da zuciyarta take ji wani lokacin Yana rufeta.

Kammala aikinta tayi ta tattara tabaro ta dawo dakinsu
Ummah bata dakin tana gurin Dad dan hkaa wanka ta shiga direct ta zare kayanta ta sakarwa kanta ruwa ta rintse idanuwanta se alokacin wani irin sabon radadin zuciya ke taso ta saka hannunta ahankali tana dafe kirjinta seti da zuciyar Ummitah dake bugawa da ciwo a kirjinta,

Wasu hawaye ne masu dumi suka gangaro mata tana sake rintse idanuwa tana jin inama zuciyar Ummitah bata dace da tata ba,

Inama tanada halin sauya zuciyar dake kirjinta sbd ta dena bugawa kowace daqiqa da digon sonsa a kirjinta,
Inama zata iya wanke jinin dayake dabaibaiye da zuciyar Ummitah dake bugawa a kirjinta sbd wankesa gabaki daya daga kirjinta.

Tsananta gudu hawayenta keyi a kan fuskanta suna gangarowa tareda ruwan dake saukan mata tana sake dafe kirjinta da karfi sbd ciwon dayake mata sosai.

Ta jima a toilet kafin ta fito idanuwanta sun sauya sosai ta shirya tayi sallar laasar da akai tana toilet ta zame ta dan kwanta sbd ciwon datake ji ya daidaita.

Fatma se yamma sosai suka gamo sauran aikin ta dawo dakin a dan gajiye tana bata labarin saida sukai sabon abinci wancan Maman gidan kai tsaye tace a bai mata.

Kallan Fatma din Jannah tayi ahankali tareda mata sannu tana cewa meyasa basuzo sun kirata ba anyi aikin tare.

Toilet Fatma ta nufa bayan ta cire kayanta tana gyara daurin zaninta a kirjin tace

"Kawai barin nayi ki huta naga kaman yanayinki ba dadi sai kawai nayi nawa da naki aikin kuma kinga gashinan mun gama ba bata lokaci"

"Nagode Fatma" ta fada tana daga kwancen.

Sai bayan magrib ta samu dawowa daidai dan ta tirsasa kanta dan bata iya barin su Dad su San halinda take ciki hankalinsu zai iya tashi ko su shiga damuwa Musamman duk abinda zai tinatar dasu LIMBA a rayuwarsu tayiwa kanta alkawarin bazata taba barin su sake shiga wannan damuwarba.

Abincin suke zaune dukkaninsu suna ci suna fira hankali kwance Musamman da a ranar Ummah ta sake samun cigaban lafiyarta sosai harda murmushi takeyi tana cin abinci a plate daya itada Dad da Jannah.

Ammar na gefe Yana yanka mata lemu da apple daya siyo mata sbd tana tsananin sonsu shiyasa yanzu dayake fita babu ranar da baya siyo mata su dan hakanne yanzu tana samun fruits sosai sai suke sake qara mata lafiyar jiki harda nutsuwa ma.

Madam Sisi ce ta qaraso fuska a sake ta nemi guri cikinsu ta zauna tana cewa

"To tinda Kun hadu dukkaninku bara na zauna anan din kawai muyi magana dan sako ne daga sama ya taho gareku"

Maheer ne ya kalleta Yana maida hankalinsa akanta.

Garba baya gurin Yana toilet gurin wanka yana futiwa nan yayo,
Ammar kallanta yayi rabin hnkalinsa na kan Ummah dake fada masa zaqin lemun daya yake bata.

Jannah ma hankalinta na kan Ummah da Ammar din Dad ne y ajiye spoon din hannunsa shi da Fatma sun bata dukkanin hankalinsu sbd jin tace sakon daga sama ne dan haka ko yayane kila yanada mahimmaci dan haka y sake bata hankalinsa shida Maheer sosai.
#MAMUH
#LOVE
#FAMILYS LOVE
#2 MOTHERS 1 SON
#AZIZ LIMBA
#JANNAH ZAD
#FALAQ LIMBA
#SZAD

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09032345899
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 15

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi  1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection  1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Gyara zama tayi ta fuskanci Dad shi dayake babba kuma jagoran Familyn ta bude baki tace

"Dzad kaman yanda kasan lissafin albashin 4&4 na watan nan ya kusa baifi sati daya ba kuma a lissafi kunada hakki cikakke na wannan watan,
Inshort dai zaa baku albashinku na wannan watan a gobe Wanda shine na karshe sbd an sallameku daga aiki zaa sauya wasu maaikatan wannan sako ne daga sama umarnin mahaifiyar Mai gidan ce,
Dan haka duk abinda kukeyi kuyisa a Daren yau gobe karfe 7 zuwa 8 zaku bar 4&4"

Gabaki dayansu a tare suka saukar da idanuwansu akanta cikeda tsananin mamaki harma da tashin hankalinda babu shiri,

Dad Su Maheer gabaki dayansu suka kalla shi kuma ya dan sauke kallansa daga kan Sisi Yana kasa kallan yayan nasa kafin suka dawo da kallansu kan Sisi din wadda fes take kallansu babu jin ko tausayin sabo na zama da akai.

Dad ne ya sauke numfashi ahankali cikin sanyi da kasa fahimtar komai yace

"Sisi akwai abinda ya faru ne?
Akwai laifi da muka aikata ne a rashin Sani da aka yanke mana hukuncin hakan?

Kallan Ammar yayi ya maida kallansa kam Sisin yaci gaba da cewa

"Ko Ammar yayiwa Matar me gidan laifi ne a rashin Sani?

Girgiza kai Ammar yayi jikinsa na tsananin sanyi zuciyarsa na nauyi da quncin dayake rufesa na tozarcin da suke haduwa dashi kashi kashi rana tsaka a Koresu dan koina anga basuda inda zasu.

Maheer ma da idanuwansa sukai jajir jikinsa a tsananin sanyaye ya bude baki yace

"Ko acan cikin gida ne aka samu su Jannah sukai kuskure?

Jannah da fatma da jikinsu suma yayi tsananin sanyi da fargaba zubawa madam Sisi idanuwa sukai suji ko laifi daga gurinsu ne.

Duka girgiza kai Sisi tayi tana miqewa tace

"Ko daya umarni ne kawai sbd angaji daku daman basa son masu aiki suna dadewa sbd kada rayuwar gidan daula da hutu ta shigeku zuciyoyinku su mutu gaba ku kasa neman na kanku shiyasa ake muku irin hakan tinda gashinan Kun shiga tashin hankalin komawa kauye anfara sabawa da hutu da ci me kyau da AC,
Gashinan masu rabin hankali ma apple da oranges akesha duk da dare dan.....

Jannah ce ta miqe tsaye ahankali idanuwanta na cikowa da hawayen baqin ciki da radadi me zafin gaske dake tafasa zuciyarta da maganganun da ake fadawa ahalinta kowannensu babu me iya cewa komai sbd yanda zuciyarsu ke quna da radadin ayau sune ake cewa kada su saba da daula..

Kallan Sisi tayi ta bude baki tace

"Zamu wuce sbd muma bamason zuciyarmu ta mutu anan kaman yanda ta wasu ta riga ta mutu suda basu saba ganin wannan qaramar daular da a gurin ahalina ba komai bace,
Har gobe mu talakawane na fili da kika gani amma a zuci da idanuwan Wainda suka San Zaadens sun San har abada zaaci gaba da ambatarsu a sahun wainda sukai arziki"

Gangarowa hawayen idanuwanta sukai daidai lokacinda ta kalli Ummah da aka ambata d rabin hankali zatai magana Dad dinta ya miqe tsaye tareda riqo hannunta ya janyota jikinsa ya rungume yana jin radadin saukan hawayenta fiyeda maganganun da aka fada musu Wanda shima har cikin zuciyarsa yaji ciwon maganar da aka yabawa matarsa.

Maheer ne ya kalli Sisi din wadda take  a zafafe da maganar da Jannah ta fada mata yace

"Inshallah goben zamu tafi Allah ya hada kowa da rabonsa na arziki"

Garba daya iso lokacin ya tadda wannan mummunan labarin jikinsa tsananin sanyi yayi ya kalli Fatma wadda take hawaye masu dumi ahankali batareda ta motsa ba.

Ummah ahankali itama ta ajiye apple din dayake hannunta tana kallan kowa daya bayan daya ganin yanda kowa ya shiga mummunan yanayi Ammar ma dayake namiji idanuwansa cikowa sukai da hawayen dake cikeda tsananin baqin cikin rayuwa da qunci.

Hawayen fuskan jannah ne ke sake gudu Wanda ya saka Umman miqewa tsaye tana bin bayan Sisi da wuqar da Ammar ya aje tana cewa

"Waye yace Miki ana saka Jannah kuka a gaban Ummanta,
Hadda Ammar ma kuka zeyi
Bazan yadda ba"

Da gudu cikin matsanancin sabon tashin hankali Garba ya fara yi kanta ya riqeta kafin su Dad din Wanda tafara fizgewa tana sake damqe wuqar a hannunta da karfi tana cewa

"Bazan yadda ba ta saka Jannah da kowama kuka saina sakata kuka na jini zatayi a idanuwanta su zan cire mata"

Madam Sisi da hankalinta yayi tsananin tashi tayi gaba da gudu tana neman hanyar gudu Amma babu sbd takai bango da rawar muryan tsananin tsoro da tashin hankali tace

"Ku fa riqeta da kyau karku saketa kunfi kowa sanin mahaukciya ce zata aikata abinda take fada kuma dukanku gidan yari zaku tana aikata hakan....
Kai kai ku riqeta da kyau,wayyo Allah na shiga uku da wannan masifar,
Wlh dole kubar gidan nan tinda dai haukar tafara yawa babu abinda zaisa mu zauna da mahaukciya irin wannan a cikin gida"

Maganar Sisin yanka zuciyar kowannensu takeyi Amma duk da hakan kokarin riqe Umman sukeyi sedai kuma wani irin karfin gaske ne na fita hayyacinta tana son kwacewa takeyi,

Da qarfi Maheer da Ammar suka riqe hannuwanta suka qwace wuqar kowa zuciyarsa da idanuwansa b dadi Musamman Ammar da baiyi karfin zuciyar Maheer ba hawayensa sauka sukeyi ahankali Yana soka Kansa qasa.

Jannah ma kuka takeyi mara sauti tana kallan yanda Umman tajiwa kanta raunika da wuqar sosai harma da Dad duk taji masa ciwo.

Da qarfi Dad din ya riqeta a jikinsa qamqam yaqi sakinta duk duka da yakushin datai masa yanajin azaba yaqi sakinta hartai sanyi dan Kanta kafin Dad din ya dauketa yayi dakinsa da ita.

Dukkaninsu kowa kasa cewa komai yayi suna ji Sisi nata aibata lafiyar Umman babu Wanda ya iya cewa komai suka shige dakunansu jikin kowa a mace zuciya na daci.

Zamewa Jannah tayi ahankali jikin bangon dakinsu ta zube qasa tana rufe fuskanta da tufukan hannuwanta biyu tana kasa sabon kuka sbd tasan wata sabuwar gararin ce take jiransu a waje sbd inda zasu raba suyi rayuwa Ya gagaresu tana fatar dai wainnan jarabawar sun zo karshe Allah ya musu mafitar da bazasu sake zaunawa a karkashin wani ko wata ba.

Fatma ma datasan komawa kauye shikenan zai sake durqushe mata rayuwarta data samu ta fara miqawa acikin ci gaba da nutsuwa jin takeyi bazata iya komawaba dadi da wuya zata bi su Jannah tayi rayuwa a cikinsu koda a kango zasu su zauna ta zaba rayuwa a cikinsu.

Ammar da Maheer Harma da Garba dukkaninsu a zaune suka kwana babu Wanda zuciyarsa bata cikin tinani me zurfi da radadi,

Ammar baqin cikin rayuwarsa kaf baifi ganin hawaye da damuwa akan fuskan Yan uwansa Musamman Jannah wadda yake ganin dukkaninsu sun gaza bata rayuwar data cancanta,

Ayau da baa Koresu ba yayi niya baida baqin cikin dawwama a cikin bautawa 4&4 mansion indai zai wadata rayuwar Jannah da Tara abinda zai mallaketa ta zamo tasa yayi rayuwa da ita,

Ita kadai idan ya samu baida baqin cikin kasancewa driver har karshen rayuwarsa sbd a yau Yana rayuwa ne sbd Jannah datake tare dashi dan badan hakan ba da tini zuciyarsa ta kasa daukan komai na wannan gwagwarmayar ya mutu,

Amma Yana komai ne sbd ya auri jannarsa ya wanke dukkanin baqin ciki da quncin da LIMBA da aurensa ya bata,
Ya bata rayuwar kwanciyar hankalina aure ya zamar mata bangon da zata jingina dashi a lokacin gazawarta,

Hakama babban nutsuwa da kwanciyar hankalin dayake samu a cikin 4&4 mansion shine Jannarsa n killace a inda har abada idan ba sun bar nan ba LIMBA ko ahalinsa bazasu taba samun ko labarinta ba bare ganinta dan haka yasan tana inda su da jannarsa kamar nisan sama da qasa ne.

Maheer kuwa yasan wani sabon babin gwagwarmayarsa ne ya tsaya na nemawa ahalinsa gurin da zasu rabe suyi rayuwa koda daki daya ne hakama yayiwa kansa alkawarin tsayawa tsayin daka ya nema halak din dazai sake gina Zaadens da ita kodan hana hawaye sauka a idanuwan ahalinsa.

Dad ma kwana yayi rungume da Ummah a jikinsa cikeda kulawa yana mata addua zuciyarsa cikeda damuwar da baisan ina rayuwa zatai dasu ba kuma a yanzu.

****Washe gari kaman yanda babu Wanda ya rintsa a tsakaninsu hakama Mama bata rintsa ba tana cikin tsananin mutsuwar gari ya waye subar mansion din,

Fiddausi ma bata rintsa ba sbd da kunnuwanta taji hukuncin Mama na korarsu,

Madam Sisi ma bata rintsa ba sbd tsananin fargaba da tsoron kada Ummah ta biyo dare ta yankata.

Dan haka dukkaninsu suna sallar asuba kowa Yana zaune gari ya fara haske suka shirya kayansu tsaf sukai wanka suka shirya,

Karfe 7 na safe suka fito dukkaninsu,

A lokacin fiddausi na tsaye windown dakinta tana hangosu zuciyarta na wani irin tsananin bugawa da tinanin me zatayi a tsakanin Mama da Falaq dashi Kansa AZIZ LIMBA.

Madam Sisi ce taxo kofar dakin Mama tai knockin Maman ta bude ta miqa mata kudinsu ta rufe dakinta tareda takawa ahankali zuciyarta na wani irin nauyi ta isa bakin window din dakinta ta tsaya sbd tanason a kan idanuwanta Zaadens subar rayuwarta data ahalinta har abada.

Madam Sisi na isa kasa qarasawa tayi har inda suke sbd Ummah da hannunta yake cikin na Dad sarke ya riqeta cikeda tsananin so da kaunar dayake mata a duk yanda take.

Ambatar sunansu tayi da

"ZAADENS"

Tsayawa sukai daga tafiyar da suka fara Maheer da Dad ne suka fara juyowa a natse suna kallan Sisin kafin Ammar wanda idanuwansa suke jajir har lokacin tukuna Jannah da Ummah Wadda ta juyo gabaki dayanta daidai nan Mama ta yaye curtains na windownta gabaki daya idanuwanta na sauka akan wadda ko mutuwa tayi ta dawo duniya bazata rasa ganeta ba ko daga nisan kilometer nawa ne kuwa...
#MAMUH
#AZIZ LIMBA
#UMMITAH LIMBA
#MAMA LIMBA
#FALAQ LIMBA
#SAYD LIMBA
#DZAD
#FATIMA UMMAH ZAD
#AMMAR ZAD
#MAHEER ZAD
#JANNAH ZAD

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
Mamuhgee

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo

ADUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

09032345899
07019691719

*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 16

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi 1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection 1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Hannuwanta da suka dauki wata irin mummunan rawa zuciyarta na bugawan da kirjinta ya kasa dauka ta saka hannuwan ta bude glass din windon tana bude idanuwanta sosai akan fuskan dake gefen Dzad tana son sake tabbatarda abinda idanuwanta ke gani amma take ganinta yafara daukewa sbd sbd tsananin tashin hankalin da ba saka masa rana ba,

Baya tayi da sauri tana fadawa cikin jerin kwalaban tsadaddun perfumes din dake jere a makeken mirror din dakinta alokacinda Ummah ta dago idanuwanta dasuke sak na AZIZ ta kalli Madam Sisi dake yin baya kadan..

Daukewa numfashi yafara kokarin yi tana fizgosa ta nufi kofa da bin bango ta bude ta fito tana bin bango numfashinta na yankewa harta sauko qasa gaba daya bata gani sosai ta fito kofa tana dafe kirjinta taci gaba da biyo bango tabi ta kofar kitchen abinda bata taba yiba tabi ta baya ta nufi inda suke tana jefa kafarta duk inda ta samu batareda tana gani ba.

Ummah dake kallan Madam Sisi zuciyarta na wani irin tafarfasa da tsallen zafi kasa riqe kanta tayi ba zato ta fizge daga hannun Dad tayi kan Sisi tana karbe jakar hannun Fatma ta daga zata buga mata daidai isowan Mama da kuma janyewan Madam Sisi da karfi jakar ta sauka a tsakiyar kan Mama wadda ko motsi daya bata qara ba ta yanke jiki a gurin ta zube qasa bakinta na furta kada Wanda ya kira kowa...bata qarasa ba ta some.

Fiddausi dake tsaye tana kallo ganin hakan ta qwalla wata irin qara me karfin gaske wadda tasan zata saka duk Wanda yaji fitowa tana ambatar sunan Mama.

Madam Sisi ma ihun ta sake tana cewa

"Shikenan Mahaukaciyrku ta kashe mahaifiyar Mai gidan mun shiga uku"

Tashi hankalin sauran masu aikin yayi da kuma Nicky da ihunsu ya tadota sbd tsoro ta dauka gobara gidan yakeyi tana ganin Mama a some itama ihun ta saki tana cewa ayi sauri a dauki Maman zuwa ciki.

Ana wucewa da Maman securities na babban gate ta kira tace kar abari Zaadens subar 4&4 din sbd sun kashe Mama kila.

Dukkanin wannan tashin hankalin da ihun da akeyi gabaki daya Zaadens babu Wanda bai riga yayi mutuwar tsaye a inda yake ba da abinda idanuwansu suka gani....

Dad baya yayi ahankali Yana neman xubewa Garba yayi saurin tarbosa cikin tsananin tashin hankali yana kallan Maheer da idanuwansa sukai jajir a Karo na farko dayaga hawaye na gangarowa daga idanuwan Maheer dayake jaruminsu gabaki daya...

Ammar kuwa wata irin rawa hannuwansa suka fara idanuwansa na juyewa zuwa jajir ba Kyan gani hakama rawar jikinsa na tsanananta kafafunsa suka kasa riqesa sbd hardasu rawa sukeyi sosai ya zube qasa a durqushe Yana qanqame jikinsa idanuwansa a kafe a qasa.

Jannah kuwa har aka bace da Mama idanuwanta basu kyafta daga kan Maman da fiddausi dake waiwayowa tana kallanta da hawaye cike a idanuwanta ba....har sai da suka bacewa ganinta ta daga hannunta daya ahankali ta dora akan kirjinta seti da zuciyarta dake mata wani irin radadi da ciwo me tsananin gaske Wanda ta kasa riqewa ta rintse idanuwanta tana durqushewa qasa itama tana furta "innalillahi wainna ilayhi rajiun"

Ummah data itama tai mutuwar tsaye tin lokacinda idanuwanta suka sauka akan Mama kanta ya fara juyawa Yana mata wani irin nauyi zubewa qasa tayi tana dafe kanta da karfi tana bubbugasa da karfi Wanda ganin zata jiwa kanta ciwo ya saka Fatma isa gareta ta riqeta tana kokarin hanata buga kanta a bango.

Tsit gurin yayi babu Wanda ya iya motsi sbd mummunan halin da zuciyoyinsu suke ciki tsawon lokaci babu wanda ya iya cewa komai sai Dad ne ya iya bude baki ahankali zuciyarsa na tsananin ciwo yace

"Hajiya sakina ce idanuwa suka ganemin a matsayin mahaifiyar me gidan nan da muke ciki?

Tanada wani dan ne bayan Wanda muka Sani?

Shin Mahaifiyar me gidan akace da 'yarsa ne suka dawo?

Shin a gidan waye muke zaune ciki muna rayuwa da bauta qarqashinsa???

Waye yasan sunan Mai gidan nan ya sanar dani dan Allah""

Babu Wanda ya iya cewa komai sai tsananin daci da nauyin da zuciyoyinsu ke qarawa Musamman Jannah wadda dole Maheer ya isa gurinta ya riqota jikinsa Yana kallan inda ta Dora hannunta gabansa na sake sabuwar faduwa ya bude baki zaiyi magana ta dago jajayen idanuwanta ta sauke akansa ta girgiza masa kai ahankali ta iya furta

"Am fine" sbd batason shigar dasu sabon tashin hankalin dayafi wannan masifar data bayyanar musu a yanzu yanzun nan.

Kenan koda akace me gidan na wata qasar se yanzu ne zai dawo da mahaifiyarsa da yarsa da matarsa kenan AZIZ AY LIMBA ake nufi,

AZIZ LIMBA shine ya koma 4&4,
AZIZ LIMBA ne yayi aure kenan ya auri wata macen.....

Ahankali ta lumshe idanuwanta tana budesu akan fuskan Dad dinta da shima ita yake kalla cikeda wani irin ciwo a zuciyarsa na yanda duka wannan ciwon da suke ji yasan nata yafi hakan Amma tana kokarin dannewa da hadiyewa....

Wace irin nannauyar kaddarace suke fuskanta a rayuwarsu da haryanzu ta kasa daidaita?
A yau Wanda suke addua koyaushe da fatan har abada kada Allah ya sake hadasu da ko wanda ya sansa shine suke rayuwa a cikin gidansa karkashin ikonsa a rashin Sani...

Ammar daya fita hayyacinsa Jannah ya zubawa idanuwansa yana girgiza kai alaman bazai taba rasataba sbd kalman 4&4 dake yawo a cikin kwanyar kansa tana shirin zautar dashi...

Jannah dake hana kowane irin yanayinta bayyana Ammar din ta zubawa idanuwa cikeda tsananin tausayinsa da kaunarsa a matsayinsa na dan uwan dayafi sonta fiyeda komai har Kansa,

Ganin yanayin daya shiga tasowa tayi ta dawo gurinsa ahankali ta miqa hannunta ta dora akan nasa dake wata irin rawa baida me rungumesa kaman yanda Mimi ke masa da tana raye ita kadai ce me kulawa dashi a irin wannan yanayin dan haka tana Dora hannunta akan nasa ahankali ya dago jajayen idanuwansa dake cike da taf da hawaye ya kalleta bakinsa na wata irin rawa me tsananin ban tausayi yace

"Jannah kece rayuwar da kadai nake nema a duniyata,
Jannah kece tawa kaddarar kece zaki zama lafiyata sbd kece maganin ciwona,
Jannah kada ki sake zabar kowa akaina zan mutu idan babu ke a rayuwata,
Zan jure komai hadda aiki a karkashin AZIZ LIMBA har karshen rayuwata idan har zaki zabeni akan kowa,
Jannah karki xabi kowa ki barni dan Allah Jannah kece kadai abinda nakeso a wannan rayuwar"

Gurin Dad ya rarrafa komai nasa na rawa sosai ya bude baki zaiyi magana Dad yayi saurin rungumesa Yana basa kyakkyawar rungumar da Mimi ke basa a duk lokacinda yafara loosing control Yana jin tsananin tausayi da kaunar Ammar din na sake cikesa koina sbd shine Zeynab dinsa kuma shine Mahmoud dinsa da duk suka tafi suka barsa shi kadai a wannan duniyar ya bude baki ahankali yace

"Ammar Jannah taka ce,
Babu Wanda zai sake rabaka da ita,
Babban saa da arzikin da muka samu a duk lokacin nan masifun nan shine samun rabuwar aurenta da AZIZ LIMBA,
Sakin daman shine abinda mukafi so Wanda shine yasha gabanmu akan komai Amma tinda mun samu mezai saka Jannah ta sake shiga hannun kowa bayan kai Ammar?

Jannah dagowa tayi ta zubawa Dad idanuwanta tana kokarin karban zancensa ta cusa a zuciyarta karfi da yaji,

Gabaki dayansu jin sukai kaman suna suffocating a mansion din dan ko fuskan Mama basa kaunar sake gani hakama su kansu su Dad basa kaunar bayan mama su sake arba da wani a familyn Musamman Jannah da basa kaunar idanuwanta su sake sauka akan Falaq Aziz bare AZIZ LIMBA din da kansa dan haka ko daqiqa daya basa buqatan sakewa a gidan dan haka suka miqe babu me karfi sosai a jiki amma kuma idan ba ganin sukai sunbar gidan ba zasu iya rasa numfashinsu sbd toshewan kirji gwara suje bola ko Tasha suyi rayuwa dasu ci gaba da zama anan din kenan Mama ta gansu shine akai musu korar rana tsaka wanda ita abinda bata saniba shine da sunsan a ina suke da wlh ko mintina bazasu qara ba a ranar da suzo zasu koma subar gidan.

Garba da Fatma da kwata kwata basusan inda kowane lamarin ya dosa ba basu iya tambayaba sbd sunsan dai koma menene ba lafiya bane kuma barin 4&4 din shine mafi alkhairi dan haka kai tsaye suka nufi gate din barin gidan batareda kowannensu ya waiwayoba dukkanin kayan da suka samu anan dinma Banda kudin albashinsu barinsa sukai anan suka fasa tafiya dashi sbd zai Tina musu daga inda suka fito dan haka komai basu dauko ba hakanan suka nufo babban gate inda suka tarar da an hanasu tafiya sai Mama ta farfado anga lafiyarta tukuna.

Garba na jin hakan tsoro da fargaba suka shigesa idan ba dauresu zaayi akan hakan ba,
Su kuwa su Dad basu wani damu akan hakan ba suka koma suka zauna zaman jira sbd saninsu ne daga su har LIMBAs din babu me kaunar wani dan haka sun San sallamarsu zatai tana farfafowa kawai mummunan baqin cikinsu daya shine lamarin yayi girman da AZIZ LIMBA zai taho qasar sbd mahaifiyarsa.

Idan akwai mafi cutatuwar da zasuyi shine haduwarsu gabaki daya da LIMBA Wanda gwara komawa gidan yari akan hakan indai zaa hadasu gidan yarin dukansu ahali daya su rayu a guri daya.

Ummah da gabaki daya ta rikice musu suka maidawa hankali sunata kokarin dawo da ita daidai Wanda duk saida tajiwa Dad din rauni Amma baiji komaiba saima rungumeta yayi a jikinsa da kyau harta samu ta dawo daidai tukuna suka dena mata addua suka zazzauna jiran tsammani.

Ammar adduarsa gabaki daya komawa tayi akan Mama ta farfado su samu su tafi kawai sbd sosai yakejin baida nutsuwa ko kadan a zaman gidan.
#MAMUH
#BEST LOVE
#HOT ROMANCE
#AZIZ AY LIMBA
#JANNAH ZAD
#AMMAR ZAD
#AYSH NICKY
#ZAADENS
#LIMBAS

07019691719
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 17

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi  1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection  1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Mama kuwa likita aka kira da gaggawa ya iso ya dubata sbd dukkanin Wanda yake gidan hankalinsa yayi mummunan tashi sun shiga tsoro da shakku Musamman Nicky da idan Mama ta mutu batada me tsyaa mata akan auren AZIZ LIMBA dan haka tafi kowa rikicewa sai kuma fiddausi da itama ta shiga tsoron kada wani abu ya samu Maman wata fitinar ta sake bullowa a tsakanin Zaadens da limbas dan haka duk ta shiga tsoro da tashin hankali tama kasa zuwa ta dubo Falaq da har lokacin bata fitoba duk ihun da akeyi tanaji ta kuma zabi koma menene ba ruwanta sbd a gidan bayan fiddausi a yanzu babu Wanda take ji a ranta sbd Mama ta zama kamar kurji ne a ranta sbd ta shiga tsakanin Daddynta da abinda yakeso a rayuwa fiyeda komai a yanzu duk da bai fada ba tasan hakan kuma a yanda Maman tayi zai zabi rayuwa da ciwon rashin macen da itace rayuwarsa a yanzu dan haka duk abinda yake faruwa a gidan yanzu babu ruwanta dashi koma menene.

Babu daukan lokaci sosai Mama ta farfado sedai numfashinta da bugun zuciyarta ya kasa dawowa daidai lokaci daya sbd har alokacin wani irin shock take cikinsa na ganin shin fatima ce ta gani tareda ZAADENS,

Shin ko sun San itace asalin mahaifiyar AZIZ LIMBA ne suka nemota dan daukan tasu fansar?

Kokuwa dukiyaraa sukeson karbewa su basa mahaifiyarsa tinda AZIZ LIMBA zai iya bada komai daya mallaka a duniya Harma da ransa indai akan Fatima ne,

Fatima itace abu na karshe da AZIZ zai gani ya sunkuyarwa da Zaadens kai ya basu komai nasa,

Fatima itace makami na karshe da zaa iya kai AZIZ LIMBA qasa akanta,

Ta ina suka hadu da Fatima?
Meye manufarsu akan hakan?
Shin da gaske sun san wacece ita kokuwa?

Innalillahi wainna ilayhi rajiun"

Ya Allah wace sabuwar masifar datafi ko wace da suka shiga wannan,
Tayaya bayyanar Fatima bata fito ta ko inaba sai ta hannun maqiyan data Fi son balain duniya akansu,

Tayaya zata iya barin AZIZ yasan Fatima ta bayyana a hannun Zaadens?

Girgiza kai tayi a quntace wasu ruwan tsananin baqin cikin da bata taba jinsaba irin wannan lokacin,

Kanta tsananin nauyi yake qarawa tana sake jin inama bata ga wannan ranar ba,

Idan haka ne tin a yanzu tafara ganin cewa dawowansu Nigeria babu alkhairi kwata kwata acikinsa komaima kila lalacewa zaiyi Wanda wannan Karan indai tana tsaye da kafafunta bazata bari duk Wanda bataga alaman alkhairi a tattaredashi ba shigowa rayuwar AZIZ,
Wannan Karan ta zabi zama villain din indai akan a rabata dashi ne.

Dago idanuwanta da sukai jajir tayi ta kalli fiddausi da Nicky bayan fitar Dr din daya dubata ta bude baki a hankali tana kokarin boye yanayinta duk da dukkaninsu sun gama sanin tana cikin rashin nutsuwa me girman gaske dan haka akwai abinda take boyewa.

"Ban yadda kowa ya fadawa AZIZ abinda ya faru ba,
Idan nace AZIZ ina nufin Sayd sbd shine kunnuwa da idanuwansa,
Ko a bisa tsautsayi karya taba sanin abinda ya faru,
Ko sunan masu aikin Nan da komai ya faru sanadinsu ban amince ya isa kunnuwan AZIZ ba har abada"

Dago idanuwanta tayi ta saukar akan fiddausi da nata idanuwan sukai jajir itama ta sauke kanta qasa a sanyaye cikeda mamakin menene ya fito da Maman bayan ko kaunar ganin Zaadens batayi hakama batason ko kadan su San a inda suke.

Da kakkauran kalami Maman tace

"Kin Sani isar wannan maganar a kunnuwan AZIZ ko Falaq daidai yake da abinda na fada Miki a baya sbd naga alamar kina son zabar zama a wajen LIMBAs Wanda babu nasara ko kadan a bangaren da kikeson zaba"

Nicky idanuwanta ta juya ta kalli fiddausi kafin ta dawo da idanuwanta akan Mama tana kokarin fahimtar abinda yake faruwa amma dai koma menene tasan yanada alaqa da abinda baa son ta Sani sbd babu abinda Mama ke boye mata bayan duk abinda ya shafi Matar LIMBA ta baya.

Fiddausi kuwa hadiye hawayenta tayi zuciyarta na daci da baqin samun kanta a tsaka me wuya irin wannan ta gyada Kai tana bude baki muryanta a shaqe tace

"Insha Allah Mama"

Kallansu tayi ahankali tace su tafi taji sauki tana buqatan kasancewa ita kadai.

Wani kallo tayiwa fiddausi wanda fiddausi ta fahimci abinda take nufi dan haka ta fara wucewa ta nufi kitchen ta fara jingina da bango tana sauke numfashi me tsananin zafi kanta na toshewa gabaki daya.

Tea me zafi sosai ta hadawa Maman ta fito kitchen ta nufi dakin sbd ta tabbatarda Nicky ta fice.

Tana shiga tura kofar tayi ta rufe ahankali ta iso gaban Maman ta ajiye tray din hannunta tana durkusawa ta dauka ta miqawa Maman a natse.

Kofa Maman ta kalla ta tabbatarda fiddausin ta rufe ta bude baki tace

"Na tabbatarda bayan abinda ya faru baa barsu sun fice daga mansion din ba suna nan haryanxu??

"Eh suna nan Mss Nicky tace kar abari su tafi sai kin tashi"

Ajiyan zuciya boyayya Maman ta sake tana ajiye cup din hannunta batareda ta iya shan tea din ba dan gabaki daya a cunkushe cikinta yake tace

"Shikenan kije zan saka a sallamesu da kaina ki sanar da securities nace idan baniba Kar Wanda ya bada umarnin zamansu ko tafiyarsu a gidan nan"

"To" tace tana juyawa ta fice daga dakin.

Nicky yau bata fita koina dan haka bata sake sauka ba hakama su Maman babu Wanda ya sake fitowa abinci ma a sama fiddausi ta kawo musu.

Mama wuni tayi a tsaye da zaune sbd gabaki daya nutsuwarta bata tattare da ita,
Duka AC dayake buga koina na cikin inda suke rayuwa zufa take yi bata iya cin komaiba sai tea da ruwa kadai datake Sha,

Bugawa zuciyarta takeyi wadda take hana numfashinta tafiya daidai sbd kasa zuwa ta tabbatarda fatimace a gaban idanuwanta hakama akan wane bagiren zata dauki lamarin.

Daga Mama har Zaadens wunin tsaye sukai babu Wanda baya cikin tsananin tinani me zurfi da baqin cikin kasancewa guri daya da juna har lokacin.

Duk yanda sukaso tafia sun kasa samun dama gashi basuda labarin halinda ake ciki Maman ta tashi kokuwa haryanxu tana can a sume.

Ga yunwa a cikinsu Amma damuwa da qunci sun hana suji yunwar yanda ya kamata dole a cikin kayansu suka hada tea kowa yasha suka ci gaba da zaman radadin zuciya.

Da daddare sawu ya dauke tsaf kowa a mansion din yayi bacci Banda su Dad da suke zaune daram har lokacin baqin cikin rayuwa ya gama rufesu sbd ayau sun sake tabbatarda su din ba kowa bane a yanzu sbd yanda aka tsaresu a inda sukejin gwara zaman cikin inda ake gasa bread dashi...

Karfe daya da mintina kamar yanda Dad yayi tinanin akwai dalilin hanasu tafiya hakan ce ta tabbata sbd sak a mutum hajiya sakina ta bayyana a palon da suke zaune su dukansu har Fatma da Ummah harma da Garba sunyi nisa sosai a bacci.

Ita kadai ce ta taho babu kowa a tareda ita hakama ta tabbatarda babu wanda baiyi bacci ba a mansion din dan haka kai tsaye ta qaraso har tsakiyar palon idanuwanta kafe akan fuskan Ummah dake bacci a jikin Dad hankalinta kwance hannuwanta duka biyun ta sarke hannuwan Dad din dasu wanda hakan ya saka Mama rikicewa ganinta na neman daukewa ta fada cikin kayansu dake gefen ajiye batareda ta saniba tsabar rikicewa.

Babu Wanda yayi yunqurin taimaka mata sai Jannah data tashi tareda miqa hannu zata kama ta Maheer ya riqo hannunta a natse tareda dawowa da ita gefensa Yana girgiza mata kai ahankali cikin sanyi yace

"Karki taba ta ace mun sake mata wani abin Jannah"

Sauke kanta tayi ahankali tana jin batajin zafin Maman sbd ba itace ta lalata rayuwarsu ba 'danta ne Amma kuma dole indai tana Zaadens kuma jininsu ne a jikinta zata tsaya dasu ako wane hali kuma ta tsaya su fuskanci duk wani wnada suke ganin abokin gabarsu ne.

Miqewa Maman tayi tana kasa dauke idanuwanta akan hannuwan Fatima da Dzad...

Bakinta na rawa idanuwanta na cikowa da hawayen da batasan ma na menene ba ta kalli Dad a rikice tace

"FATIMA"

Dukkaninsu kallanta sukai suna miqewa tsaye daya bayan daya ahankali kafin Jannah ta isa kusada Ummah tana kokarin riqota Mama ta riqe hannun Jannah din cikin tsananin tashin hankali tace

"Ina kuka hadu da Fatima?

Dad sake riqe hannun Ummah yayi wadda ta bude idanuwanta ahankali tana miqewa tsaye ta sake riqesa da kyau batareda ta kalli Mama ba.

Ganin hakan Mama ta sake ambatar sunanta da dan karfi tana kokarin isa gurinta ta fizgota daga jikin Dad Amma a lokaci daya Umman taja da baya tana riqe Dad da Jannah da kyau kuma a daidai lokacin Ammar da Maheer suka sha gaban Maman suna kallanta cikeda dukkanin tsanar duniya da baqin cikin sake ganin wani daga cikin LIMBAs a rayuwarsu.

Da tsananin mamaki Maman ta kallesu kafin ta tsayar da idanuwanta akan Fatiman dake kallanta fes Amma ta kasa sakin Dad bare Jannah da dawo da idanuwanta akan Dad cikin tsananin tsanarsu datake jin tana qaruwar mata tace

"Kunsan waye ita??

Sai alokacin Dad ya bude baki a natse yace

"Nine nafi kowa sanin ita waye sbd ita din matatace,
Idan kuma kinada wani bayanin akanta ki zaki iya sanarwa kafin mu wuce tinda gashi naga harkin tashi akan kafafunki bamuda sauran abinda ya rage mana anan"

Wani qaton qullutun baqin cikin dayafi kowane a rayuwarta ta hadiye tana kallansa da tsananin mamaki tace

"Matarka?
Fatiman ce ta zama Zad itama?
Tayaya ta ina?

Babu wanda ya tanka ta ta nufi Fatiman da sauri ta riqota tana janyota da karfin gaske tana cewa

"Wlh bazai taba yiyuwa ba"

Fizge hannuwanta Ummah tayi daga na Maman tana komawa bayan Dad

A lokacin ne Dad bacin ransa ya bayyana cikin fushi ya kalli Maman yace

"Ko zan iya sanin alaqarki da ita idanma har kin Santa"

Kallansa Mama tayi bayan ta dauke idanuwanta daga kan Ummah tanajin wani irin zafi da radadi sedai kuma idan har basusan wacece ita din ba kenan da gaske basusan wacece itaba kuma a yanda take gani Fatiman haryanxu duk tsawon shekarun nan bata warke ba dan haka bazata taba barin su San wacece itaba barema AZIZ ya San Fatima tana cikin Zaadens kuma ma a matsayin Matar dzad.

Duk yanda take tsananin so da kaunar Fatima bazata taba iya barin AZIZ yasan tana hannun Zaadens ba bare kuma wai ace ta zama Zaaden din itama,
Tayaya ma zata iya barin hakan?
Hakama suma Zaadens bazata taba barin su San wacece fatima ba bare suyi yunqurin wani abin sbd zasu samu kaman power ne a hannunsu ta yaqarsu.

Dago jajayen idanuwanta tayi da sukai jajir hatta fuskanta tayi ja ta kalli Dzad ta bude baki kai tsaye tace

"Na taba saninta ne baya kuma nasan yan uwanta dan haka inason ka bani ita zan baku dukiyar da zaku Gina sabuwar rayuwar da kuka rasa a baya ta dukkanin daula wadda zamuyi nesa da juna babu haduwa har abada."

Wani irin kallo Mai cikeda tsananin mamaki da tsana me karfi dukkaninsu suke mata Wadda saka zuciyarta sake bushewa itama tana gyada Kai alaman tabbas abinda sukaji take nufi.

Ita kanta Jannah da tsananin mamaki da takaici take kallan Maman sbd kaman da akwai jahilci a cikin zancen.
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS

07019691719
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 18

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi 1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection 1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Dad cikin tsananin mamakin dayafi kowane mamakin daya shiga a dan wannan lokacin na rayuwarsu ya dago ya kalli Maman Wadda ta sauya lokaci daya dukkanin annurin fuskanta ya kawar ya zuba mata ido yana nazarin ko dai bata hayyacinta ne,
Kodai dukan da Ummah tai mata ya taba kanta ne a lokaci daya?

Maheer ma kallan ba lafiyar tinani yake mata sabanin Ammar da hannuwansa suke dan rawa Yana jin kaman ya shaqe Maman harsai ranta ya fice jikinta koma zasu samu sassaucin abinda sukeji gameda LIMBAs din.

Jannah ma kallan mamakin takewa Maman ta bude baki ahankali zatai magana cikeda kasa gasgata Maman ce kokuwa Dad ya tareta ta hanyar takowa ahankali ya fito fili daga kariyar da Maheer da Ammar suka bawa Umman.

Tsayawa yayi a gaban Maman tareda waiwayowa kadan ya kalli Ummah Wadda itama shi ta kalla ganin ya kalleta tana sake qanqame hannunsa da dukkanin zuciyarta batada niyar sakinsa ko Jannah.

Wata sabuwar soyayyarta ce ta sake cike dukkanin zuciyarsa sbd yanayin rashin lafiyanta ya saka da gasken gaske take tsananin sonsa da yayansa wnada ya Sani babu abinda zai taba sauya hakan daga zuciyarta to bare su,

Idan har ita mara lafiya tana musu tsananin wannan son to su masu cikakkiyar lafiya nasu ya wuce hakan bare daga lokacinda ta riga ta amsa sunan Zad to sun hadu kenan dan mutuwa ce kadai take cire Zad daga Zaadens.

Mama ya juyo ya saukewa wani irin kallan tsanar da yake ganin batama cancanta samu daga garesu ba sbd sunfi son masifa da duk Wanda yake cikin familyn LIMBAs dan haka dan dauke idanuwansa ma yayi daga kanta yace

"Sakina kina mantuwa Amma ki tambayi shi 'dan naki bazai taba mantawa da babu abinda duk duniya yake raba Zaadens bayan mutuwa,

Allah dayayo mu ahali daya shine kadai yakeda wannan ikon na rabamu ta hanyar daukan rayukan daddaya daga cikinmu Amma babu mutum ko wata dukiya bare daular duniya da zata rabamu,

Fatima da kika magana ta riga ta zama Zaaden,
Sunan Zaadens take amfani dashi,
Shine a bakinta kuma shine a zuciyarta,

A ganin ido Bata isa haihuwanki ba kaman yanda baki isa haihuwanta ba Amma duk da hakan ko a matsayin uwa da ya kuke koma uwa daya uba daya kuke wlh ni bazan baki matata ba har abada idan kuma kina son tabbatarda zancen saninta ko alaqardama duk take tsakaninku ina buqatan cikakkiyar sheda da bayyanarwa duniya da zancen bawai iya mu Nan a daki ba a cikin tsakiyar dare sbd magana ake akan Matar dzad uwa ga Zaadens a yanzu,

Bayan wannan duka idan bakida wani abin bama buqtaan son kai safe a cikin gidan nan bcz we are suffocating "

Dago jajayen idanuwanta da suka qara jajir Mama tayi tana kallan Fatima datake jin tsananin ciwon yanda take zabar makasan Yarta a gaban idonta sbd kawai ciwon hauka Wanda ko hauka tasan nata yakamata ace a jikinta taji tsanar Zaadens koda bata hayyacinta.

Akan Jannah Mama ta maida idanuwanta tana tsayar da dasu akan kirjin Jannah din tana kallan yanda kirjinta ke harbawa tanajin sabuwar tsanar Jannah din na rufeta sbd tanada tabbacin zuciyar dake kirjinta ce ta samu kauna daga Umman wanda ta take feelings na tsanar daya kamata taji tai musu sai kaunar tayi nasara akan tsanar,

Har xuwa yaushe ne Zaadens zasu ringa samu da mallake komai na Fatima data ita kanta Fatiman,

Sun mallake zuciyar Ummitah sun qwace,
Sun qwace mata AZIZ dinta Wanda bai taba fada ba Amma ta gani da idonta ta Sani ta qara Sanin Soyayyar Jannah tayi nasara akansa da fansarsa,
Soyayyar Jannah Zad ta sauyasa daga AZIZ LIMBA dinta na baya,
Soyayyar Jannah Zad tayi nasara akan Soyayyar Ummitah tinda har ya zabi Jannah akan fansar ran Ummitah,

Ayanxu data riqesa ta dauresa daga dukkanin Soyayyar da babu amfani a cikinta tayi nasarar shiga tsakanin Soyayyarsa da Jannah har abada kawai rana tsaka sai Fatiman da zai iya komai akanta,
Fatiman da tin yana qaraminsa haryanxu bai taba dena nema da quncin rashintaba,
Fatimar da itace rayuwar data rage masa yanzu dazai iya sadaukar da komai akanta,
Fatiman da batasan tsakanin ita da Ummitah waye yafi tsananin so ba
Shine kwatsam ace ta bayyana a cikin Zaadens kuma a matsayin macen Dzad??

Wannan shine abinda har abada bazata iya yadda dashi ba sbd AZIZ zai zabi Fatima ya kuma zabi wanda ya kawo masa Fatima,

Tasan har abada AZIZ bazai taba barinta ba amma kuma bazai taba barin wanda suka kawo fatima garesa ba amma kuma shi kansa zai shiga mummunan baqin cikin samun mahaifiyarsa a hannun Zaadens.

Zata karbi Fatima bazata taba barin su tafi da ita ba sbd koman Daren dadewa zata bayyana tinda tana hannunsu ta Sani zasu sake daga kansu sbd bazasu taba zama ahakan ba a wannan lokacin ne duniya zatasan Fatima a matsayin uwa a Zaadens kuma AZIZ zai gani kuma zai san ta sani dan haka bazata taba barin hakan ba.

Kallan dzad tayi ta sake bude baki a Karo na biyu tace

"Zan ninka muku abinda nace a farko so biyar ka bani Fatima ku tafi duk Inda zaku tafi dan Gina sabuwar rayuwa"

Tsoki Ammar ya sake Mai cikeda tsananin baqin cikin dayake cinsa ba damar duka,

Maheer ma cikeda mamakin yace mata

"Babu rayuwar dtaake ta siyarwa a Zaadens
Idan da gaske kinsan Yan uwanta ki bamu bayanai da address din komai zamu nemesu da kanmu Amma ki Sani da Sanin danki zamuyi hakan sbd komai ya zama a bude"

Jannah kasa cewa komai tayi sbd lamarin ta kasa yadda kwata kwata da Mama ce ke tsaye a gabansu.

Dad bai iya cewa komaiba ya kalleta yace

"Wallahi tallahi Fatima bazata shiga hannun kowaba sai ranar data samu lafiyanta da kanta ta furta ita din wacece da bakinta dan haka ki Sani ko Banda komai kika sake kwatanta darajar matata da dukiya zanyi sharia dake a kotu koda banda komai kuwa"

Wani irin sarawa kan Mama ya sake yi idanuwanta na sake rinewa sbd ganin komai na neman kubuce mata dan idan yace kotu Fatima zata bayyana kenan sbd ba abu bane da zaa boyewa AZIZ idan aka sakata qara kotun duk da tanada power da kudin da zata hana shariar amma Zaadens bazasu bari ba sai sun tabbatarda sunyi abinda zai janyo hankalin mutane akan case din Wanda hakan ne zai saka AZIZ ji ko gani dan haka bazatai wannan gangancin ba,

Idan har bazasu bata Fatima ba to tabbas bazasu taba barin 4&4 ba kuma bazata taba barin AZIZ yasan Fatima na 4&4 din ba har sai lokacinda ta samu karbeta ta Koresu tukuna ta bayyanar masa da ita.

Juyawa sukai dukkaninsu zasu fice dan barin mansion din gabaki daya ta qurawa hannun Ummah dake cikin na Dzad idanuwanta ki tsaye kaman saukan tsawa sukaji saukan maganarta....

"SALEEM ZAADEN!

cak dukkaninsu suka tsaya babu wanda gabansa baiyi mummunan bugawa ba

Jannah da Ammar ne suka fara juyowa da sauri suna kallan bayanta zuciyoyinsu na wata irin rawar firgici da wani irin yanayi na tsananin kewa.

Dad kasa juyowa yayi sbd yanda zuciyarsa ta cike da wani irin yanayi na tsananin ciwon rashin 'dansa da bai San dalilinta n ambatarsa yanzu ba,

Maheer kuwa ita ya juyo ya zubawa ido sbd kai tsaye yasan tasan ina Saleem yake tinda ta ambaci sunansa.

Numfashi ta sauke a boye sbd ganin ta sara akan gaba dan haka ta sauke ajiyan zuciya a fili tana bude baki cikeda tabbacin abinda zata fada tace

"Saleem Zad Yana raye kuma yana tare da AZIZ LIMBA,
Yana hannunsa,
Ni kadai nasan inda yake,
Ni kadai nasan wane hali yake,
Ni kadai zan iya kubuto muku dashi ya dawo gareku ku taru kuyi rayuwa gabaki dayanku,

Idan har kace dukiya bata siyan daya daga cikin Zads to ai Rai zai iya siyan Rai ko???

Hawayene masu tsananin zafi da tsananin kewa da kaunar Saleem suka gangaro mata ta rintse idanuwanta tana jin farin ciki me tsanani bayan tsawon lokaci jin Saleem Yana raye,

AZIZ LIMBA bai taba mata Saleem dinta ba,
Saleem Yana raye,
Saleem Yana cikin koshin Lfy kenan.

Hawayen farin ciki ne suka cigaba da gangaro mata tana kasa sharewa.

Dukkaninsu farin ciki ne ta wani bangaren me tsananin gaske ya cike zukatansu sedai basu nuna mata hakan ba.

Dad ya sake kallanta jikinsa na mutuwa da jin nutsuwar 'dansa na raye a natse a sanyaye yace

"Saleem idan har Yana raye har xuwa wannan lokacin na tabbatarda ya tsayu ya jajirce ne ga duk azabar rayuwar dayake fuskanta a hannun AZIZ LIMBA dan hkaa nasan zaici gaba da jajircewa har ranar da wahalarsa ta qare dan haka haryanxu babu abinda a duniya zaki iya samun Fatima dashi daga hannuna sai lafiyarta idan ta samu"

Da fushi Mama da hakurinta ya gama qarewa tace

"Indai bazaka ban Fatima ba to bazaku bar 4&4 da itaba idan kuma ka tirsasa tafiyanku da ita wlh nayi maka alkawarin bazaku isa inda zaku ba saika samu labarin Saleem Zad yabar duniya..."

Wani irin jiri ne ya dibi Dad wanda ya sakasa dafa bango da sauri Yana rintse idanuwansa.

Kowama irin shock din Dad ya shiga Banda Ammar dayayo kanta Kansa na neman juyewa Jannah ta riqesa da sauri tana qanqamesa.

Kallan baqin cikin ganinsu da takaici Mama ta sake musu tana cewa

"Zaku zauna a 4&4 a matsayin ku na masu aiki zaku ci gaba da zama matsayin Yan aiki sbd harsai lokacinda kuka yanke shawarar bani Fatima,
Idan AZIZ kuke baqin cikin gani to yafi ku baqin cikin hadewa daku
Idan kuma 'yarka kake baqin cikin ta dawo LIMBAs to har abada nima bazan bar hakan ba sbd bata cikin rayuwar AZIZ kwata kwata a yanzu yanada wata Matar dan haka zamuyi rayuwa daku a gida daya akan dole bakwaso bama so duk lokacinda kuka gaji zaku iya bani ita ku tafi,

Karku manta Saleem Zad rayuwarsa ce take a tsakiya,
Ban hanaku tafiya ban kuma hanaku qara ba Amma dai kafin kuyi nisa a duk abinda zakuyi Saleem ya karbi hukuncin.
Ina fatan zamu zauna lafiya akan hakan."

Tana gama fadar hakan ta juya ta fice sbd tana buqatan ajesu a mansion din kafin dawowan AZIZ ta samu hanyar dauke Ummah daga garesu kafin ta koresu sbd taga alamar bazasu taba bata itaba dan haka a yanzu datai amfani da sunan Saleem tasani bazasu taba tafiya ba zasu zauna sbd shegen son junansu.
#MAMUH
#LIMBAS
#ZAADENS

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 19

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi  1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection  1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Tana isa dakinta zubewa tayi a gefen gado tana dafe kirjinta sbd ciwon dayake mata a lokaci daya ciwon zuciya na neman kamata sbd Zaadens da ciwon Fatima.

Magani ta ballo tasha ta sauke numfashi da ajiyan zuciya ahankali tana tinanin lokaci yayi da dole zatasan inda Saleem Zad yake sbd bayan Sayd babu Wanda yasan inda AZIZ yakai Saleem a tsawon shekarun nan,

Idan har zata ci gaba da juya Zaadens akan Saleem to yakamata tasan inda yake,

Hakama ta bangare daya a yanzu batada baqin cikin zamansu a guri daya matiqar zata samu nasarar dauke Fatima daga garesu a lokacin ne zatai musu korar kare ta kai fatima ta ajiye inda itace da kanta zata bayyanarwa AZIZ da ita Amma idan ba hakan ba komai nata lalacewa zaiyi sbd Zaadens hatta AZIZ dinta zasu iya shiga tsakaninta dashi gwara ta hadasa da mahaifiyarsa da kanta sbd ya sake Sanin itace dai uwarsa da babu me kaunarsa kamarta ko Fatiman data haifesa kaunarsu sedai taxo daya.

Ta bangare daya kuma tana buqatan hana AZIZ dawowa kasar Nan a yanzu.

Da wannan tinanin ta kwanta baccin me Yar nutsuwar samun biyan buqata na daukanta.

Acan Zaadens kuwa dif kowannensu yayi mutuwar zaunen da babu sauran tinanin daya rage akansu saina baqin ciki da rashin mafita,

Basa kaunar LIMBAs,
Basa kaunarsu,
Ayau sun sake tsanarsu tsana me girma sbd duk duniya baa taba sakasu a tight spot ba irin wannan.

Idan tayi hakan dan karbe Ummah daga hannunsu to tayi babban kuskure sbd hakan bame yiyuwa bane,
Hakama idan riqesu a 4&4 shine take ganin zata iya komai akansu to tabbas tayi kuskurenda batasan ina wannan rikicin zai kaisu ba.

Ta bangare daya kuma dukkaninsu idan har Mama ta dage haka sosai akan Ummah to tabbas tasan wani abin akanta Wanda suma a yanzu sunason Sanin wacece Umman dan haka suma saisun tabbatarda wacece Umman sbd daman rashin karfi da ikon ne ya hanasu neman asalinta Amma yanzu lokaci yayi daya kamata Susan hakan tinda har Mama ta riga ta nuna Sani akanta.

*****Washe gari da safe dukkanin Wanda ke 4&4 da mamakin Mama suka fara tarban safiyar sbd fes ta tashi hankali kwance kaman bata taba ciwon komaiba,

Mamakin jamaar gidan bai qaru ba saida sukaga Zaadens sun fito bakin aikinsu kowa hankali kwance batareda bayyanarda tsananin baqin cikin rayuwa a 4&4 din dake cikin ransu ba,

Fatma da garba sunsha mamaki sosai sbd duk wainar da aka toya da tsakiyar Daren basuda labari sundai wayi gari da komawa bakin aikinsu dan haka sukai farin ciki da hakan,

Madam Sisi da kwata kwta bataso hakan ba gurin Maman taje kai bayani kai tsaye Mama tara kowa har securities din main gate ta sanar dasu Zaadens zasu ci gaba da zama da aiki a 4&4 ba buqatan tambayar komai.

Da mamaki kowa ya watse sedai ba damar tambaya.

Fiddausi data riga tasan akwai dalilin hakan itama a nata bangaren yanke shawarwari ta fara yi akan zabar LIMBAs ko Zaadens wanda zatai hakan ne sbd Falaq dinta Amma zata Kara jira tagani.

Nicky ma alaman tambaya me girman gaske ta Dora kan Zaadens Musamman ganin Mama sosai take hana barinsu hutu aikine sukeyi yanzu ba kadan ba Wanda duk takun Maman Zaadens na sane kuma sun shanye sunqi nuna damuwa ko gazawansu.

Itama Nicky qara takura Jannah tayi da ayyukan fiyeda na baya Wanda itama Jannah din Sam bata damuba.

Mama umarni me girman da tsaurin gaske ta bawa madam Sisi akan duk rintse kada a ringa barin Umman Jannah fitowa fili kada a taba barinta fitowa bangaren masu aiki koda hakan na nufin ringa sakawa bangaren tsaro ne.

Fiddausi duk yanda taso ta ringa taimkawa Jannah Sam Jannah din bata bari sbd batason ayita fada ko hayaniya idan Mama ko Nicky sun Sani,

Mama ta saka fiddausi duk rintsi kada ta bari Jannah da Falaq su hadu kaman yanda itama Jannah din batason harta bar gidan ta hadu da Falaq sbd zuciyarta zata iya samun raunin da zata iya bawa ahalinta matsala dan haka duk abinda zai kaita sama aiki tana tsananin kiyaye haduwa da Falaq wadda haryanxu Allah bai hadasu ba.

********Ahankali tafiya ta sake fara tafiya lokaci na qara tafiya duk lokacin Mama taji tahowar AZIZ saita tabbatarda ta hanasa ta hnyar datasan zai fasa da kansa,

A duk lokacinda yayi maganar tahowa kai tsaye take nuna masa ta matsu da dawowan tasa sbd Yana dawowa alkawari ne sai anyi aurensa da Nicky zai koma,

Tana fadar hakan yake fasa tahowar sbd bazai taba iya musa mata din ba idan haryazo tabbas zai aikata abinda tace din.

Bayan hakan akwai babban Al'amarin dayake riqesa acan din Wanda koyaushe baya cire tsammanin zuwan Wadda yayiwa alkawarin jira na har tsawon rayuwarsa a cikin sakonsa dan hakanne kwata kwata barin qasar baya cikin tsarinsa saida Falaq ta sakasa cika nata alkawarin na dawowa Nigeria Amma duk da hakan shi bayada tabbacin dawowansa gaba daya sbd alkawarin dayake Kansa.

Wata irin tsana ce wadda take a bayyaane Mama da Nicky kewa Jannah a gidan wadda take sake saka Jannah din zama jaruma sbd komai da suke mata ta hadiye tana shanyewa,

Duk abinda ake mata Su Dad sun Sani Amma a haka suke hadiye baqin cikin da ciwon duk abinda suke ji sbd ta nuna musu zata iya kada Wanda ya damu da komai.

Abu daya ne yake girgiza zukatansu fiyeda zafin qin da sukewa LIMBAs shine dawowan AZIZ LIMBA da kansa da basa fata suna nan sbd basusan yaya Jannah zata iya karban hakan dan haka a fili a boye addua da fatansu daya kada Allah ya kaddari haduwarsu dashi sbd Jannah dinsu kawai.

Ammar yafi kowa shiga tashin hankali na boye da tsananin rashin nutsuwa akan dawowan LIMBA wanda a yanzu adduarsa ta koma akan Allah ya hanasa dawowa harsai ranar da Allah yayi suka bar 4&4.

******
Karfe 7 na safiyar da Jannah ta raba dare tana yiwa Mama aiki a dakinta ya saka Fiddausi kasa riqe zuciyarta daga abinda takeson aikatawa Wanda shine zai kawo AZIZ LIMBA gabaki daya a qasar koda Sanin kowa ko bada sanin kowa ba sbd Mama bazata taba barin ya dawo ba matiqar Zaadens na gidan.

Tsaye take a kitchen tana kallan tray din da cup data dafawa Falaq madara yake tanajin bugun zuciyarta na qaruwa hakama idanuwanta na cikowa da ruwa...

Mama ta sakata alkawarin bazata taba fadawa Falaq ko Sayd Zaadens na gidan ba hakama ta sakata alkawarin bazata taba barin falaq taga Jannah ba to batada zabin daya wuce ta saka Jannah zuwa ga Falaq din da kanta hakama AZIZ LIMBA yazo ya kawo Kansa  ga 'yarsa da duk abinda yake koma menene zai aje yazo.

Tsoro ne yake cike kirjinta da fargaba sosai,
Shakka takeji matiqar gaske amma kuma duk motsinta Mama da madam Sisi harma da Nicky suna sane dashi dan haka batada zabin daya wuce hakan.

Kwalban chemical based sweetener dake hannunta ta daga tana kalla Wadda ana ajiyesa ne sbd Nicky dake amfanin dashi sbd komai nata kamar bana mutane ba.

Budewa tayi ahankali idanuwanta na cikowa da hawaye ta zuba sosai a cikin tea din tareda maidawa ta rufe ta dauki spoon din ta juya tea din a hankali ta maida kwalban inda take ta goge hannuwanta zuciyarta na wani irin nauyi ta bude baki ahankali ta tace

"Falaq ki yafemun,
Daddyn Falaq and Jannah duka ku yafemun Banda zabin daya wuce hakan ne kuma bazan taba illata falaq ba ciwonta kawai zan tayar"

Daukan tray din tayi ahankali tana ficewa daga kitchen daidai lokacin su Fatma suka shigo dan fara nasu aikin Jannah na bayansu sosai sbd da dan zazzabi ta tashi yau din.

Ahankali fiddausin ke takawa zuwa saman tanajin kaman ta fasa abinda take niyar yi din sbd zuciyarta dake hanata hakan dan tamkar jinin daya fito daga jikinta take jin Falaq...

Duk da abinda zatai tana kokarin yi dinne sbd hada Falaq da abinda take tsananin kauna amma kuma tana jin kaman bazata iya sakata a mummunan hali ba sbd ta hadata da Jannah da kuma zuciyar asalin mahaifiyarta.

Kofar bedroom din Falaq ta tsaya cak tana jin bazata iyaba.

Ajiyan zuciya da numfashi me zafi da daci ta ringa saukewa tana hana zuciyarta.

Ta share tsawon mintina biyar a tsaye bakin kofar dakin kafin ta juya ahankali jikinta a tsananin sanyaye ta fara takawa Falaq ta bude dakin ahankali da wayarta a hannunta charger dinta taqi yi tin jiyan dan haka ta fito dole dan neman fiddausi din.

Ganin fiddausin na kokarin sauka da tray din tea din datasan ita ta hadowa ya sakata fitowa gabaki daya tana nufo fiddausin tana cewa

"Ina zaki kuma tinda nariga na tashi zansha kawai daman da yunwa na tashi da haushin wayana ya kasa caji and I really need to talk with my daddy"

Sauri fiddausi ta qara tana kokarin basarwa tace

"Yayi sanyi bara na sake dafa Miki wani"

"Inji waye bayan I can still see its hot"

Yanda fiddausi take sake sauri yasa Falaq sake dariya tana binta da gudu tinda sun saba irin wannan wasan.

Hayaniyarsu ya saka Mama fitowa da sauri jin falaq na sauka a daidai lokacinda bata saba sauka ba kuma Jannah na nan.

Fitowan Mama ya saka Nicky fitowa a tare suka nufo qasan.

Daidai isar fiddausi palon qasa tana tsananin addua da fatan Jannah tana palon tana aiki..

Falaq kuwa biyota tayi ta riqeta a tsakiyar palon tareda dauke cup din da sauri tana juyawa da gudu tana kai cup din bakinta tafara Sha tana kokarin komawa sama Mama na saukowa fiddausi kuwa sakin tray din hannunta tayi cikin tsananin tashin hankalin tea din da Falaq din ke Sha tana dariya sbd sun dade basuyi wasa irin haka ba.

Qarar faduwan tray din hannun fiddausi ya saka Falaq juyowa tana qarasa shanye tea din da yayi wani irin taste zatai magana Jannah da Fatma suka shigo lokaci daya a palon sbd qarar faduwan tray din,

Fatma ce ta fara sako kai kafin Jannah din a natse tana dago fararen idanuwanta tana saukesu akan fiddausi...

Cup din hannun Falaq ne ya subuce daga hannun nata yana faduwa qasa ya tarwatse tana kasa motsawa daga abinda idanuwanta suka gano mata Wanda kaman bazai taba yiyuwa ganin Jannah a 4&4 ta bayyana....

Mama wani irin baqin cikin dayake rufe idanuwanta ne yake saukowa daga samanta zuwa qasanta idanuwanta akan Jannah Wadda itama qarar watsewan teacup din ya sakata dagowa idanuwanta na sauka akan Falaq wadda tai mutuwar tsaye..

Kafafunta da suke mutuwa Falaq ta daga har lokacin idanuwanta basu dauke daga kan Jannah ba ta fara saukowa bugun zuciyarta na tsananta yana sauyawa da karfin gaske sbd shock da kuma abinda tasha..

Taku biyu tayi Mama ta riqe hannunta tana hanata qara taku ko daya sedai kafin kowa yayi kowane irin motsi Falaq din ta yanke jiki ta fadi a stairs din tana gangarowa wnda ya saka fiddausi fasa ihun kuka tana yi kanta.

Ita kanta Maman kan Falaq din tayo hankali tshe.

Jannah taku daya tayi idanuwanta na sauyawa zata isa ga Falaq din sai kuma ta dakata tana komawa gefe ta tsaya zuciyarta na wani irin radadi.

Hankali tashe Mama da fiddausi suka dauketa zuwa sama Mama na cewa Nicky tayi gaggawan Kiran likita.

Da sauri Nicky ta dauko wayarta amma kuma batada niyar fara Kiran doctor saita fara Kiran AZIZ ta fada masa mummunan halinda Falaq din ta shiga sbd tasan yau bazai kwana ba saiya biyo jirgin zuwa Nigeria Wanda zuwansa shine aurensa da ita daman tana neman hanyar kawosa Nigeria yau Allah ya kawo mta dan haka bata damu da gargadin mama datace kada Wanda ya sanar masa ba.

Kiran farko datai bai daga ba dan haka kai tsaye ta kira Sayd Yana dauka ta fasa wani irin kuka tana cewa

"Falaq ta ynke jiki a stairs ta fado tana bleeding tako ina"

Dayake a handsfree take AZIZ na zaune Yana jin abinda ta fada dukansa dan haka dif kawai taji wayar ta mutu sbd Sayd bai dauka abinda zata fada ba ya saka handsfree din.
#MAMUH
#AY LIMBA
#AZIZ LIMBA
#ABDULAZIZ LIMBA
#4&4 LIMBA

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 20

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Breast
Magungunan gyran Breast
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi 1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection 1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Su Mama nakai Falaq daki suka kwantar wayarta dake hannunta tafara ringing Wanda bata damu da dubawab sbd kokarin Shafawa Falaq din ruwa dasuke sedai ba alaman zata farfado Wanda hakan yake basu tabbacin ba suman shock bane akwai abinda ya sakata collapsing wanda suke fatan ba ciwonta bane Musamman fiddausi da hankalinta yayi mummunan tashin da har take jin tana fita hayyacinta sbd tsoro da fargaba tareda mummunan baqin cikin abinda ta aikata din.

Sake shigowan Kiran ya saka Mama dago wayar cikin tsananin fushi tana dubawa gabanta ya yanke y fadi sbd Kiran AZIZ ne.

Kasa dagawa tayi kirjinta na harbawa harta yanke wayar,

Kokarin sauke numfashin tsinkewan Kiran takeyi sbd tasan baya wuce kira daya tsananinsa biyu dan haka tinda na biyu ne yayi bazai sake kira ba...

Sake shigowan kiransa ne ya saka zufa tsatsafo mata tana dagowa ta kalli fiddausi da batama hayyacinta daidai tasan ba lallai ta fada masa to Amma wannan kirn nasan dole da dalili.

Shigowan Nicky ne tana cewa

"The doc will be here in no ti..."

Kallan da Mama ke mata ya sakata kasa qarasa zancen tana shiga mamakin ko dai Falaq din ta mutu ne.

Kiran AZIZ ne ya sake shigowa ba kakkautawa a wayan na Mama data kasa dagawa har lokacin,

Wayar fiddausi ma dake dakinta Sayd na can na mata Kiran da babu adadinsa Amma baa dauka.

Fatma dake gyaran dakin fiddausin ne dataji Kiran yayi yawa ta fito da wayar ta iso dakin tai sallama kanta a qasa tace

"Anata Kiran wayar ne"

Tasowa fiddausi tayi ko ganin gabanta batayi ta riga Maman karban wayar tareda dagawa a take bama tareda ta duba waye ba Amma tasan bazai wuce Kiran Daddyn Falaq din ba ko Sayd..

Muryan AZIZ ce kai tsaye ta bayyana babu rahama ko kadan a cikinta cikeda kamewan da hatta Mama saida cikinta ya juya yace

"Meya samu Falaq din?

Kuka fiddausi ta fasa mara sauti sosai sedai cike yake da tsananin tashin hankali tace

"Ta yanke jiki tana tsaye stairs sai ta fado amma ankir....dif taji ya kashe wayar yana dago idanuwansa da suka sauya take yace

"Siyamun ticket na tafiya yau dinnan idan akwai"

Sayd da tin dazun yafara kokarin siyan tickets din yace

"Already on it"

Miqewa yayi daga zaunen dayake yana barin office din cikin gidansa da suke suna wani aikin ya wuce ciki Yana kallan agogon hannunsa sbd ya kwatanta time din isarsa idan ansamu ticket din yanzu.

Acan kuwa wayar na mutuwa fiddausi dagowa tayi ta kalli Mama wadda tariga ta shiga mummunan yanayi me girman gaske sbd tasan mutuwa kawai zata hana AZIZ LIMBA isowa Nigeria zuwa dare ko asuban yau,

Fiddausi take kalla da wata irin mummunan yanayi zatai magana fiddausi ta girgiza kai tana cewa

"Bani bace kawai Kiran na samu a yanzu gabanki aka kawon wayar Mama"

Juyawa Mama tayi kan Nicky dake kokarin isa gurin Falaq ta riqota ta dawo da ita gabanta idanuwanta jajir tace

"Waye ya kira AZIZ ya fada masa?
Kece kikai hakan?

Damuwa Nicky din ta bayyanar sosai a fuskanta dan nuna kulawanta akan Falaq tace

"Na shiga tsoro da tashin hankali ne shiyasa na sanar masa sbd kada yaji daga baya yaga laifinmu da muka boye masa amma ai bai daga wayanba Sayd na kira....."

Zamewa Mama tayi ta zauna kan sofa dake dakin tana rintse idanuwanta cikeda wani irin tsananin baqin ciki da takaicin Nicky din ta kalleta kaman zatai mata duka tace

"Kin kirawa kanki balai da masifar da bazaki iya ba garin neman sunanki,
Kin kira mana ruwan da baya taruwa,
Meya kaiki?
Wa ya aikeki.
Innalillahi wainna ilayhi rajiun"
Tinda kikai hakan saiki shirya ganin abinda baki tsammata ba kala kala sbd.........

Kasa qarasawa tayi tana dafe goshinta sbd yanda kanta ma yake sarawa,

Babu daqiqiya irin Nicky sbd ta wargaza mata komai da wannan Kiran dataiwa AZIZ,

Itadai haduwansa da Jannah tasan bazata taba iya hanawa ba indai ya iso din sedai tasan bazai taba komawa Jannah dinba tinda tai rantsuwa dan haka wannan Nicky ce a ruwa tsundum ita tata matsalar shine cigaba da hana Ummah fitowa duk rintsi bazata fito inda AZIZ zai ganta ba ko Sayd sbd Sayd na ganinta a take zaiga kamannin Ummitah a tattare da ita kuma ma tana shakkar idan kila bai taba ganinta koda a photo bane dan akwai sketches dinta da a baya AZIZ ya ringa sakawa anayi masa na nemanta suna nan daki guda a yanzu batasan inda AZIZ yakaisu ya boye ba da ko ita ta dena ganinsu tinda Falaq t fara wayo y boye su sbd kada ya raba mata hankali tinda haryau bata san cewa ba Mama bace ta haifesa ba.

Nicky shiru tayi tana nazarin maganganun Mama Amma bata wani damu dasu ba sbd ita dai a saninta kaf duniya Falaq zata nunawa kulawa da so ta samu AZIZ sbd Falaq ce abinda zakaso ka Samu isa zuciyarsa kuma indai hakan zaisa y dawo Nigeria batada baqin ciki tinda dawowan nasa shine aurenta dashi dan haka koma me zai biyo bayan ya biyo bai dameta ba indai zai diro qasar buqatanta ta biya.

Isowan Dr ne ya saka dukkaninsu fitowa sai fiddausi aka bari suka dawo palo suka zauna ran Mama babu dadi kwata kwata.

Nicky kuwa breakfast dinta ta saka Jannah ta kawo mata har saman ta ajiye mata ta fara ci a natse hankalinta kwance.

Kallan takaici da baqin ciki kawai Mama ke binta dashi tana rasa abin fada mta amma dai tasan idanuwanta da zuciyarta zasu fada mata nan ba da jimawaba indai AZIZ LIMBA da JANNAH ZAD suka hadu.

Jannah da wani irin nauyi ne yake danne da zuciyarta a natse ta gama ayyukanta tana kokarin saukowa fiddausi ta bude dakin Falaq ta fito tareda Dr da zai wuce ta sauke idanuwanta da sukai jajir akan Jannah dake kokarin sauka ta bude baki kai tsaye tace

"JAN"

cak Jannah ta tsaya idanuwanta tana lumshe idanuwanta ahankali sbd Falaq dinta ce kadai me kiranta da sunan fiyeda kowa.

Kasa juyowa tayi saida fiddausin ta tako a natse ta tsaya bayanta tace

"Tana buqatan black tea zata Sha magani dashi"

Ajiyan zuciya ahankali Jannah din ta sauke sbd tasan fiddausin na kokarin fada mata Falaq din taji sauki.

Gyada Kai tayi batareda ta juyoba ta fara sauka tana sauke ajiyan zuciya a jere sbd ayau bayan shekaru zata hadu da Falaq ta kalleta da kyau taga lafiyan data samu zata hadu da Falaq ayau a matsayin 'yar da zuciyan dake kirjinta ta Haifa.

Tana isa kitchen din kai tsaye tea da pancake ta fara kokarin hada mata da lafiyayyan zuma da chocolate mix.

Acan saman kuwa Jannah din na sauka miqewa mama tayi ta isa dakin Falaq ta sameta zaune tana kokarin saukowa gadon ta fito jikinta har wata irin rawa yakeyi idanuwanta suna tara ruwan hawayen farin cikin datake jin kaman uwar data haifeta ce ta dawo duniya,

Kuka takeson fasawa tana son furta JAN Amma bakinta sbd rawan dayake ya kasa furtawa ta nufi kofa da sauri zata fita Mama ta shigo dakin.

Rufe kofar dakin Mama tayi tareda juyowa ta kalli Falaq da idanuwanta fes tace

"Jannah ce da gaske kaman yanda kika gani amma a matsayin me aikin 4&4,
Bazaki taba komawa yanda kike da ita a baya ba zaki mu'amalanceta ne only as Yar aikin gidan nan idan kikai abinda ya wuce hakan nayi Miki alkawarin korarsu aiki su tafi inda har abada bazaki taba sake ganinta ba,
Dan haka indai kinason ganinta zaki kulata ne kadai a matsayin me aikin gidan nan,

Duk kaunar da mahaifinki ke Miki karki manta baya taba saba umarnina dan haka korarsu ba wani big deal bane a gurinsa idan nace hakan,
If kinason Jannah ta zauna lafiya a 4&4 ba azabar aiki ba wulaqantawa kibi yanda nace,
Zabi ya rage naki"

Juyawa tayi ta bude kofar dakin zata fice Jannah ta buga kofar dakin ta fiddausi n gefenta.

Bude dakin Mama ta qarasa yi ta kallesu kafin ta juyo ta kalli Falaq wadda idanuwanta sukai jajir tanajin kaman zuciyarta zata buga sbd tsananin baqin ciki da radadi me zafi...

Mama tasha gabanta anan sbd bazata taba yadda a rabata d Jannah ba ayanzu,
Bazata taba yadda a wulaqanta Jannah ba hakama bazata taba iya kallo a wahalar da ita ba.,

To amma indai Mama tace hakan zata yadda ba komai bane indai Jannah na mansion din Daddy dinta ma yananan hakan ya isheta zata nunawa Mama umarninta daban abinda zai faru daban sbd indai hakanne ma Jannah a matsayin me aiki shine abu mafi kyau a yanzu gareta dan hakan na nufin zata bawa Jannah umarni tabi kowane irin ne kuma zata sakata aiki kowane irin ne tayi ba gardama.

Ajiyan zuciya ta sauke tareda dagowa ta kalli Mama tana share hawayenta da suka gangaro ta juya batareda ta kalli Jannah dinba ta zauna bakin gadon data tashi.

Shigowa Jannah tayi a natse ta ajiye tray din hannunta tareda dagowa ta saukar da idanuwanta akan Falaq tanajin duk wani tsananin kaunar Falaq din data danne tana tasowa cikeda kewa.

Qin kallo Jannah Falaq tayi ta dago a hankali ta kalli fiddausi ta bude baki tace

"Bani maganin"

Fiddausi data gama cika da mamaki sanyin jiki na shigarta ta kalli Falaq din ta juya ta kalli Jannah da jikinta ya fara sanyi sbd da alama Falaq ma ta tsaneta kenan kaman duka LIMBAs.

Numfashi ta sauke a boye tana juyawa ahankali ta nufi kofa ta fice tana hadiye duk abinda ya taso mata a kirji sedai hawaye ne ke kokarin saukowa daga idanuwanta tana kasa riqesu sbd Falaq idan ta qita zuciyarta zata iya kasa dauka.

Tana isa kitchen bata iya riqe kanta ba durkusawa tayi tsakiyar kitchen din tana rufe fuskanta da tufukan hannuwanta hawaye na gangaro mata.

Falaq ma Jannah na ficewa daga dakin hawayen ta gangaro tana dagowa ta kalli Mama data fice hankalinta kwance.

Fiddausi data fahimci abinda ya faru zamewa tayi ta zauna tana kasa cewa komai.

Shiru gidan yayi a wunin babu motsi me yawa bayan na Nicky daketa kai da kawo cikin farin cikin dawowan rabin ranta dan haka karshe ma fita tayi taje spa sai dare ta dawo a lokacin suna dinner gabaki dayansu a dining,

Zaunawa tayi aka qarasa da ita ana gamawa kowa ya haye sama da tinanin ko yaya maigidan sbd kowa ya kasa samunsa bare Sayd a waya dan haka basuda Sani ko tabbacin zuwansa da haka har dare yayi sosai suka kwanta.
#MAMUH
#LIMBAS
#ZAADENS
#BEST LOVE
#HOT ROMANCE

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 21

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi  1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection  1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Karfe 7 na safe Jannah ta iso bangaren ta hau sama kai tsaye tafara aikinta a natse itada Fatma da itace me gyaran dakin Falaq.

Jannah na gamawa ta sauka ta koma kitchen suka fara aikin breakfast da Amina wadda keta bata labarin Madam Sisi tinda safe tana dakin Mss Nicky haryanxu bata fito.

Shiru kawai tayi batareda tace komaiba sbd batasan me zatace din ba,

Karfe 9 suka gama jere komai a dining suka dawo kitchen,

Jannah kai tsaye bangarensu ta koma dan Ummah ta tashi yau bata jin dadi jikin nata ya dan motsa..

Ko data isa su Dad ta tarar zaune dukkaninsu a guri daya da alama magana suke suna ganinta suka zuba mata idanuwa dukansu kowa yanayinsa ba dadi.

Dauke kallanta tayi daga kansu tana zaunawa gefen Ummah dake shan ruwa ahankali tace

"Dad,wani abin ya faru ne na ganku hakan?

Shiru sukai Banda Ammar da idanuwansa sukai jajir kaman zai kashe Kansa yakeji ya kalleta ya bude baki ba zato yace

"Dad dan Allah a daura mun aure na Jan kafin na mutu,
Dan Allah a cikamun wannan burin kafin Allah ya dauki Raina"

Kallansa dukansu sukai batareda mamaki ba sbd a yanzu da AZIZ LIMBA ya sauka a qasar Yana kuma cikin gidan Ammar bazai taba samun nutsuwa ba,
Suma bazasu taba samun nutsuwanba matiqar ba daurawa Jannah aure sukai ba da Ammar din.

Jannah kuwa kallansu ta sake yi tana cewa

"Ammar wani abin ya faru ne??

Girgiza kai yayi idanuwansa na cikowa da hawayen da baisan ya zaiyi da abinda yakeji a zuciyarsa gameda Jannah din ba yace

"Jannah aurenki shine burin Dana jima dashi tin kina ciki dan Allah ki cikamun wannan burin na aurenki sbd zuciyata takasa samun nutsuwa,
Wlh akanki ban daddara ba zan iya sake zama makashin duk wanda zai rabani dake sbd rasa tinani na nakeyi lokuta da dam.....

Dad ne ya hanasa qarasawa Yana kama hannunsa yace

"Ammar na maka alkawarin muna barin 4&4 dinnan a ranar zan daura maka aure da Jannah Ni nayi maka wannan alkawarin insha Allah."

Da sauri Ammar ya rungume dad din hawaye na gangaro masa.

Jannah ma ajiyan zuciya ta sauke batareda tace komaiba sbd batajin zata iya cewa komai sbd indai aurenta da Ammar zai qarasa wanke abinda yake zuciyarta ta shirya hakan sbd ta samu ta wanke idan hakan zai yiyu.

Shiru sukai babu wanda ya fada mata AZIZ LIMBA ya iso da asubar yau din Wanda Garba ne ya bude second gate din dukkaninsu tinda suka ga shine suka kasa bayyanar da kansu sbd abubuwan baya da suka ringa dawo musu na baqin ciki me girma.

Wanka tayi sbd yau tayi lattin tashi batai wanka ba ta tafi tayi aikin safen,

Tana fitowa cikin sauri ta sake shiryawa ta koma kitchen din suka hau aikin lunch ta tadda hadda madam Sisi ake aikin.

Kallan renin hankali madam din tai mata tana cewa

"Kada ki sake barin kitchen batareda angama aikin masu gidan ba daga yau sbd naga kina wasa da aikinki sbd ganin Mama ta daure muku gindin zama a gidan bayan muguwar taasar da me hankalinku tayi"

Shiru jannah tayi batareda tace komaiba tana ci gaba da aikin yanka carrot data tarar.

Maganganu Sisi tahau yi wanda babu Wanda yace komai sukai shiru suna jinta banda Jannah data hana kanta jinta ta hanyar dauke hankalinta akan maganganun.

Karfe goma da mintina mutan gidan suka fito suka halarta a dining dan breakfast dinsu suna zaune banda fiddausi dake tsaye dan serving nasu.

Kokarin fara cin abincin sukeyi Sayd ya bayyana a dining room din cikin sallama da kwanciyar hankali idanuwansa akan Falaq da itama mamaki ya gama kasheta sbd ga dukkanin alama ba yanzu yanzu ne suka iso ba hakama bata taba saka ran ganinsu a yanzu ba dan ta dauka bazasu dawo din ba...

Mama take taji yunwar cikinta ta bace bat ta zubawa Sayd ido tana jiran bullowanu uban gidan nasa.

Fiddausi kuwa tinda take a cikin LIMBAs tsawon shekaru bata taba farin cikin dawowansu irin yau ba hamdala tayi tana sauke ajiyan zuciya daidai nan qamshin Grand soir ya fara bayyana a gurin Wanda ya saka Falaq ajiye cup din hannunta tana miqewa tsaye daidai nan ya sako kai a natse sanyeda fararen kayan Brioni na zaman gidan fuskansa fresh da wani irin kwarjini da nutsuwa,

Idanuwansa akan 'yarsa suka fara sauka Wadda tin a Daren jiyan yaje dakinta tana bacci dan haka bai tashetaba y fice ya kyaleta...

Da wani irin gudun tsananin kaunarsa da kewansa datai ta nufesa dole ya zaro hannuwansa daga aljihunsa yana budewa dan tarbanta ta fada masa ya rungumeta gabaki dayanta yana sauke ajiyan zuciyan da saida ya bayyana a fili na ganinta fit and fine sbd kafin isowansa bugawane kawai zuciyarsa bataiba da tinani kala kala.

Sake qanqamesa tayi a natse tana cewa

"I love you Daddy,i love you"

Dagota yayi ahankali Yana kallan fuskanta cikin sake samun nutsuwa yace

"Ok ok karki gajiyar d kanki da yawa kin riga kinsan kene zuciyan Bestynki"

Murmushi ta sake farin cikinta yana qara tsananta sbd ganinsa a gabanta a gida daya da Jannah batareda ya Sani ba.

Mama ya kalla Wadda ciwon zuciya ma taji kaman Yana neman kamata cikeda girmamawa yace

"Barka da safiya Mama,
Mun sameku Lfy?

Ajiyan zuciya ta sauke tana sake fuskanta tareda bayyanarda farin cikin ganinsa tana amsawa tareda kallan Sayd dayake gaidata ta amsa shima tana cewa

"Ashe gida daya muka kwana daku shine baku sanar mana da isowanku ba tin cikin Daren"

Zama AZIZ yayi har lokacin Falaq na riqe da hannunsa cikin nata ya dago yayiwa Nicky dake gaidasa kallo daya da idanuwansa da suka kusan sumar da ita daga zaune ya amsa mata kai tsaye ba damuwan komai kafin ya amsa gaisuwan fiddausi itama.

Zaunawa kowa yayi fiddausi zatai serving nasu Mama ta kalli Nicky take ta miqe ta karbi aikin tafara zubawa AZIZ din komai daidai yanda zai ishesa tukuna ta bawa fiddausi tayi serving kowa.

Da mamaki Sayd yake kallan hakan hakama fiddausi ganin sabon salon batai wani dogon mamaki ba.

Mama kuwa sai yabawa Nickyn takeyi shikuwa Wanda akeyi akansa baice komaiba abincin yafara ci a natse Falaq ma murmushi tayi tana saka spoon cikin nasa tana diba tana hadawa na nata tanaci.

Dagowa Falaq tayi ta kalli fiddausi tace

"Fi pls wani daga kitchen ya kawo mun honey banason Nutella mix dinnan"

"Ok" fiddausi tace da sauri tana juyawa zuwa kitchen din sbd saka Jannah kawowa.

"Fiddausi ki kawo mata da kanki bama buqatan Yan aiki anan yanzu Musamman ga AZIZ Yana zaune koba yau ba kada a gwada hakan"

Shiru kowa yayi banda AZIZ da hakan bai damesa ba sbd bai taba damuwa da harkan masu aiki ba bare tin can iya fiddausi ce ke iya xuwa gurin cin abincinsu idan yana gari ita kadai ce me wannan matsayin sbd ta zama Yar gida.

"Barshi kawai" Falaq tace tana kallan Dad dinta kafin ta kalli Mama Wanda itama AZIZ din ta kalla.

Fiddausi ficewa tayi batareda ta dawoba har suka gama tukuna ta dawo ta tattara gurin.

Daga dining kai tsaye samansa ya wuce tareda Falaq da Sayd zuwa palonsa suka zauna Nan aka sake Kiran Dr yazo yayi masa bayanin ba matsalar komai.

Fira suka hau yi har yana mamakin irin farin cikin dayake gani tareda ita ya bude baki a natse ya dan kallanta ya maida hankali kan wayarsa dayake dubawa yace

"Ya dai?
Akwai wani abin da kika samu ne??

Murmushi tayi tana kallansa tace

"Ina tsananin murna da farin cikin ganin Daddyna ne kawai"

Sayd dayake tura sakon da basu samu nutsuwar turawaba suka taho yace

"Anya?
Bara dai na gama mu saka labule"

"Da waye ne zan saka labule?
Da kai?
Ina gama fada maka Daddy zai maka kallo daya ka fada masa komai
Ai Ni na dena sirrin komai da kai"

Dagowa Daddyn yayi ya kalleta da duka hankalinsa yace

"Akwai wani abin kenan"

Dariya tayi tana cewa

"Daddy nace fa ba komai tukuna"

Fira suka wuni yi sbd babu inda daga AZIZ din har Sayd zasu dan haka ko gate babu Wanda ya fita a cikinsu bayan sallah da suke fita zuwa masallaci Wanda Zaadens suka kasa yadda su tafi dan babu me kaunar ganinsa Garba ne a gate ya karbe aikin dole.

Basu sauko lunch ba sbd babu me wani jin yunwa sai abincin dare suka sauko shima Yana gamawa ya koma yayi wnka ya fice sallan ishai Yana dawowa yayi wayoyi ya sauya zuwa pjamas ya kwanta.
#MAMUH
#LIMBAS
#ZAADENS
#LOVE
#LOVE
#LOVE*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 22

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi 1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection 1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Washe gari haka Mama ta toshe duk wata hanyar bayyanar Jannah a cikin bangarensu sosai iyakacinta kitchen,
Karhema sauya mata aiki akai cikin kwana biyu aka barta iya kitchen aka hanata shigowa kowane aiki kwata kwata bayan kitchen batareda tasan abinda yake faruwa hakama su Dad babu Wanda ya fada mata sbd tinanin ta Sani kawai bata son zancen ne.

Nicky tafara damun Mama da maganar aurenta dan haka Mama ta fara yiwa AZIZ maganar duk da hankalinta Yana neman tashi daga auren sbd hankalinta daya gama rabuwa ya rikice a gidan sbd tabbatarda Ummah bata taba fitowa fili ba.

****Yau saida yamma tayi harsun gama aikin abincinsu Jannah na kokarin barin kitchen din Falaq ta shigo da kanta dukkaninsu suka dakata tareda tsayawa jiran jin umarninta.

Madam Sisi ce ta qarasa gabanta cikeda neman faranta mata tace

"Akwai abinda kikeso Ms Falaq Aziz"

Idanuwanta ta sauke akan Jannah Wadda bata dago ba daga hannuwanta datake wankewa daga fanfon kitchen din hakama bata waiwayoba duk da tanajin idanuwan Falaq din akanta.

Wani irin kallo Falaq din ta zuba idanuwa tanaiwa Jannah din tsawon lokaci kafin ta sauke numfashi tana dauke idanuwanta ta dawo dasu kan Madam Sisi tace

"Tuwo"

Dukkanin kallanta suka dago sukai suna boye mamakinsu
Madam Sisi tace

"Tuwo kuma?
Tuwo da Miya?

"Yes,inason ayimun tuwo na rice da Miya koma wane iri ne"

Washe baki madam Sisi tayi tana cewa

"Angama Ms Falaq"

Juyawa tayi batareda ta kalli Jannah ba itama Jannah har lokacin bata juyoba ta fice.

Aikin tuwon suka fara Wanda zai jima tinda magrib ma tayi.

Karfe 8 na dare aka gama cin abinci fiddausi ta tattare komai masu gidan kafin 9 kowa ya haye sama sai kuma gobe bame sake saukowa dan haka har an kashe komai sai haske kadan.

Mama kai tsaye tana dakinta da Nicky suna kulla maganganun auren da zaa fara bikinsa.

Karfe 9 ta wuce suka gama abincin tuwon suka jere a dining
Madam Sisi ta hau har sama taje dakin Falaq ta sanar da ita angama.

Numfashi ta sauke ahankali kafin ta kalli time tace

"Zuwa 10 idan sun gama gyara kitchen din wace a cikinsu ta iya aiki yanda ya kamata?

Da sauri madam Sisi sbd mugunta da son wahalar da Jannah tace

"Jannah ce, zata iya kwana ta aiki ma"

Batareda ta kalli Sisin ba cikin rashin kulawa tace

"suna gama komai ki aikata gyaran palo da bedroom din Bangaren Daddyna"

Da sauri Sisi ta kalli Falaq din tace

"Ms Falaq ai ya shige tin dazu kaman yana ciki"

Dagowa tayi ta kalleta a gazarce da kosawa da kallan fuskanta tace

"Yana office dinsa na palon baya Yana aiki sai tsakar dare zai koma,
Kuma ba buqatan me aikin tasan bangaren waye zata sbd kada tayi tinanin daukan wani abin"

"Zata iya kuma indai Jannah ce akwai son rayuwar karya bayan Allah bai basuba"

Hannu Falaq ta daga mata tana cewa ya isa.

Ficewa Sisi tayi zuwa qasa.

Tana zuwa ta samu har Jannah ta wuce tin dazu dan haka bin bayanta tayi.

Ko data isa Jannah din harta shiga wanka.

Tana fitowa madam Sisin ta sakata gaba ko shiryawa sosai bataiba tace suje.

Rigar bacci doguwa ce kawai ta saka saita sako dogon hijab akai.

Suna isowa koina an kashe komai dan haka kayan shara da mopping ta dauka ta wuce saman.

Dayake palonsa daban nasu Mama da Falaq daban tini fiddausi ta rufe nasu palon tareda kashe komai suka shige.

Itama madam Sisi komawa tayi bangarenta tana zubewa sbd gajiya tana kallan agogon karfe goma sha daya har tayi.

Kai tsaye palon ta isa ta bude a natse ahankali ta shiga.

Ga mamakinta AC a kunne hakama wani irin qamshin da bata saniba bane me wani irin sanyi bayyanarda class dinsa suka doki hancinta.

Gurin bai mata kama da inda ba kowaba sbd komai na palon kana gani kasan gurin asalin wayayye me abin duniya ke rayuwa ne sbd komai na palon luxuries ne kawai tako ina.

Ajiye kayan hannunta tayi tafara yi tana kashe AC dan bata buqtaan abinda zai dauketa mintina a bangaren duk da Mai bangaren baya Nan bama ya qasar Amma jin takeyi numfashinta na shaqewa.

Babu Kurar komai a palon barena datti da baiga guri ba dan hkaa kai tsaye bedroom din ta nufa dan farowa daga can..

Tana gap da isa kofar bedroom din ta dakata ahankali tana jin kafafunta na tsananin sanyi bugun zuciyarta ma na tsananta sbd Sanin dole zata iya ganin wani abin da zai tinatar da waye me dakin,

Ko baya Nan bata kaunar haduwa da duk abinda zai Tina mata shi da rayuwar datai dashi a baya...

Rintse idanuwanta tayi tana sauke numfashi da ajiyan zuciya sbd tana buqatan yin abinda aka sakatan ta bar gurin ma da gaggawa.

Bude idanuwanta tayi tareda takawa ahankali ta isa kofar bedroom din ta Dora hannunta a natse ta bude kai tsaye anan ma wani irin sanyi da qamshi ne ya sauka a fuskanta ahankali Wanda ya sakata shigowa dakin tana kallan wutar dakin dake da duhu baa gani sosai ta isa makunnin wutar ta dora hannunta akai tareda kunnawa tana juyowa Yana fitowa daga bathroom daure da brown towel na Albiosos a qugunsa ruwa na bin farar fatar jikinsa suna gangara ahankali sbd tsantsi da hutu dayake cikin fatar.

Towel dayake rufe da fuskansa ya yaye ganin haske a dakin idanuwansa suka fara sauka akanta itama sai alokacin nata idanuwan suka juyo inda taji an bude kofar toilet din.
#MAMUH
#AZIZ LIMBA
#THE GREAT LIMBA
#JANNAH ZAADEN
#JAN ZAD LIMBA

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 23

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci  cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi  1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA  NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection  1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Idanuwansa kasa kyaftawa ko motsawa sukai ya kafar dasu akan fuskan daya gasgata abinda yake gani sbd ya saba gizon hakan sedai kuma bugawan zuciyarsa Yana kokarin banbance masa mafarki da gaskiar dake gabansa ayau...

Daga ina?
Ta yaya?
How?
How?

Sune kalmomin dake juya Kansa da karfin gaske suna aika wani irin yanayin dayai shekaru Yana dannewa a kirjinsa.

Ita kanta a cikin tsananin mamaki da shock din daya hanata motsawa take kallansa sbd ta kasa ydda da gaskia ce a gabanta take kalla sbd a saninta baya qasar kuma babu ynda zaayi ya dawo su Dad dinta bsu saniba da sun sanar mata tinda shine bakin gate bazai taba shigowa batareda sun San ya dawoba.

Kasa yadda tai da shi dinne sbd tasan daman tana shigowa inda yayi rayuwa zata iya samun wannan gizon dan haka take kallansa da idanuwanta da suke ja ahankali suna tara wani irin hawayen 'dacin zuciya da sabon kuncin dayake cike kirjinta batareda ta motsa ba.

Cikin wani irin slow da sautin dayake tone dukkanin sirrin zuciyarsa akan abinda yake gani gabansa ya bude baki ya furta

"4&4" Wanda sauti ne daya sauka cikin kunnuwanta Yana tada dukkanin gashin jikinta daya dawo da ita hayyacinta cewan ba mafarki ko gizon ne take ba shi dinne a gabanta,

AZIZ LIMBA dinne a mutum da kansa yake gabanta...

Dauke idanuwanta da suka qarasa komawa jajir tayi daga Kansa tareda juyawa take ta nufi kofa tana kokarin bude baki ta furta sorry sbd ganinsa yanda bai kamata ba Amma wani irin dacin daya danne kirjinta me tsananin nauyi ya hana muryanta fitowa dan haka kai tsaye ta fice daga dakin tana hadiye dukkanin abinda takeji na tsananin daci da baqin cikin wannan seconds din na rayuwarta ta tareda controlling kanta sbd bata buqatan manta ita ba kowa bace face me aikin gidan da babu wata sanayya bayan hakan.

Gurin kayan aikinta ta isa da dan sauri ta tattara ta dauka tareda miqewa ta nufi kofar ficewa dgaa palon tana Dora hannunta zata bude hannunsa ya riga nata sauka ahankali Yana dafe kofar tareda riqo hannunta daya da dayan hannunsa ta bayanta.

Cikin sauri ta qwace hannunta tana janyewa daga jikin kofar tareda juyowa kanta bai dago ya kallesa ba ta bude baki kai tsaye tace

"Am Sorry Sir na shiga ne aiki bansan akwai kowa a ciki ba"

Tana gama fadar hakan ta rabesa ta bude kofar ta fice har lokacin kayan aikinta n hannunta.

Mutuwan tsaye ya sake yi a gurin sedai batai nisa ba ya sake binta batareda damuwa da babu komai a jikinsa ba bayan towel.

Bata ganin gabanta take taka stairs din saukowan sbd yanda idanuwanta suke rufewa da tsanar ranar ta yau gabaki daya.

Jinsa a bayanta tafe shima ko ganin gaban nasa bayayi ita kawai yake son riqowa ya tsayar a gabansa ya gama samun gamsuwan ita dince a gabansa amma tana kasa basa damar hakan.

Tana jefa kafarta a stairs din kusa da karshe ta dora ba daidai ba sbd rashin ganin gabanta.

Da sauri ya miqa hannu zai tareta ta hana hakan ta hanyar kaucewa ta fada gabaki dayanta hadda kayan dake hannunta.

Rintse idanuwanta tayi cikeda tsananin azabar kanta daya bugu da hannunta.

Neman dena bugawa zuciyarsa ke yi sbd gabaki daya shi yama kasa gane meyake faruwa ko gamo yayi s cikin gidan.

Da hannuwansa biyu ya saka ya dagota lokacinda take kokarin tashi ta sake tafiya ya girgizata da karfi tareda furta "4&4" da karfin gaske sbd yanda take fizgewa daga riqon nasa tanajin kaman a wutar lantarki ne aka jonata.

Ihunsa dabai yisa a hayyacinsaba y sakata tsayawa cak tana qin dagowa ta kallesa har lokacin sbd wani irin riqon da yayi mata me tsananin karfi da ciwo.

Rawa hannuwansa suka fara a jikinta ya zuba mata ido jajir Yana tabbatarda ita din ce tabbas a gabansa,
4&4 ce zahirinta a gabansa ba hallucinating yake ba...

Tsananta rawar jikinsa ta fara ya saketa numfashinsa na sarkewa sbd ayau Karo na farko ya sakata a idanuwansa bayan shekaru,

Ayau Karan farko ya tabata da hannuwansa bayan shekarun nema da jira,

Ayau ta bayyana a gabansa bayan rantsuwar datake Kansa ta mahaifiyarsa na rashin nemanta sai gashi Allah ya kawo masa ita gabansa,

Meyake faruwa?
Tayaya hakan ta faru?

Sarawan gaske kansa yafara sbd tinnainsa dayake rikicewa hakama jikinsa gabaki daya rawa yakeyi sosai...

Ganin ciwonsa dayake nemen tashi ya sata janyewa ta sake zamewa ta bar gurin tareda bi ta kitchen ta bace bat daga bangaren.

Ragewa ganinsa keyi harta bacewa ganinsa bai iya motsawa ba sbd baya gani sosai hakama jikinsa tsananta rawa yakeyi.

Cikin taurin zuciyar da bayajin koda aljana ce zai iya barinta tinda har tayi kama da 4&4 ya tinkari inda tabi gadan gadan daidai nan Sayd ya fito daga palonsa sbd kusan babu Wanda baiji qarar muryansa ba data amabaci 4&,

Sayd daya San waye 4&4 shiyasa ya fara fitowa cikin mamaki da shakka.

Ganin yanayin AZIZ din da kayan da babu ajikinsa ya saka hankalin Sayd mummunan tashi ya qaraso da sauri yan taresa fita a hakan Wanda yayi daidai da fitowan Mama da Nicky sbd dukkaninsu sunji sautin muryansa sosai duk da basu tantance me ya ambata ba.

Mama na ganin yanayin da yake ta saki salati me karfi hankalinta na mummunan tashi jikinta na rawa d muryanta tace

"Innalillahi wainna ilayhi rajiun
Na shiga uku me zan gani haka?
Tabin hankali ne ya samesa?
Na lalace Ni Sakinatu da wannan mugun gani AZIZ baya hankalinsa wlh "

Sayd da shima hankalinsa ya gama qarasa tashi jnsa yayi suka bar palon qasan da sauri suka koma sama.

Kuka Mama ta fasa Wanda ya saka su Falaq fitowa daman a tsaye suke sbd tsoron da suma yafara kama su.

Nicky kuwa mutuwar tsaye tayi sbd tinda ta saukar da idanuwanta akan fitinanniyar kirar jikin AZIZ LIMBA gabaki daya shaawarta ta tsananin buqatan Namiji ta taso mata sbd karfin dayake bayyane a kirar jikinsa kadai ta isa ta tabbatarda duk macen data shiga hannunsa zatasan ta shiga hannun cikakken Namijin da zai saka kowace gaba ta jikinta samun gamsuwa.

Bata iya dauke idanuwanta akansa ba ta gangaro da idanuwanta kan qugunsa datake jin inama zata samu damar Dora hannunta akai ta zagayosa ta rungumesa.

Kukan Mama da adduoin tashin hankali data kasa dainawa ne suka saka Nicky din juyowa ta kalleta bayan Sayd yabar palon dashi ta nufeta tana cewa

"Mama ki kwantar d hankalinki ba abinda kike tinani bane inshallah kawai dai inga mummunan shock ko wani abin ne daban ya samu amma Mine bazai taba samun abinda kike tinani ba."

Mama da zufa yafara jiqata kasa bawa Nicky amsa tayi sbd tasan wlh tallahi ba lafiya ba sbd duk abinda yasaka AZIZ saukowa a haka to wlh ma yafi gamo da aljani dan ko aljani bazai sakasa fitowa hakan ba.

Tsaye suke dukkaninsu babu wnda ya iya cewa komai kuma sai kaida kawo sukeyi suna jiran saukowan Sayd suga lafiyar AZIZ tukuna.

Falaq da fiddausi ma gabaki daya hankalinsu na kan kofar saman Falaq na jin kaman tahau t dubo idan Jannah n ciki kokuwa sbd ta kasa gane komai,
Tsoronta koda maganar Maman ta tabbata Daddynta ya samu matsalar kwakwalwa sbd har abada haukacewan ce kawai zata sakasa fitowa a yanayin da Maman tace.

Hawaye ne suka cika idanuwanta ta miqe tsaye tana jin sabon tsoron kodai ciwonsa ne y tashi?

Shin baiga Jannah din bane?
Basu hadu bane?
Meya faru?

Sayd ne ya fito yazo gurin su Maman kafin ya bude baki yace komai aka sake bude kofar saman gabaki dayansu suka juya suna kallan saman da dukkanin hankalinsu da ido bude..

Saukowa yafara yi Yana qarasa saka bottoms na gaban transparent rigar daya sako fara da farin quarter sweatpnt Yana cewa Sayd

"A sanar da securities ko mage Kar abari ta fita mansion dinnan ina buqatan ganin duk wani me Rai da numfashi dayake mansion dinnan koda dabba ne kuwa yanzun nan a fadawa duka securities suyi raiding koina"

Take Sayd ya nufi kofa da sauri Yana cewa

"Yanzu kuwa" sbd Sayd baya taba tsayawa tambaya ko bata lokaci akan umarnin AZIZ ko wane iri ne dan haka kai tsaye da sauri ya fice yana fidda wayarsa tin bai isa gate ba ya bugawa securities din ya sanar musu take dukkaninsu suka fito.

AZIZ dinma yana saukowa ficewa yayi batareda yaji Kiran da Mama take masa sbd gabaki daya baya cikin hayyacinsa 4&4 din daya gani kawai yake sake son gani koda aljanarta ce kuwa.

Falaq na jin hakan tasan yaga Jannah ne dan haka da sauri tabi bayansa hakama fiddausi,

Nicky ma bin bayansa tayi dukkaninsu suka fita sbd take gidan yake neman maida kowa tsaye cikin Daren.

Mama har wani sarkewa kafafunta keyi tabi bayansu sbd jin AZIZ yace duk Wanda yake da Rai a mansion din ko mage ce a fito da ita
Fatima kenan itama fitowa zaayi da ita ko me??
Inaaa.

Fitowa tayi a rikice bata ko gani sosai ta nufesa,

Tashin hankalin datake ciki da rikicewa ya hanata ganin mummunan yanayin dayake ciki sbd koina jikinsa wata irin rawa yakeyi Yana kokarin controlling kansa sbd yanason ganin komai da kowa idanuwanta indai 4&4 ce yagani yasan zaa fito da ita dan haka bazai bari ciwonsa yafi karfinsa ba a daidai wannan lokacin yanason ko fuskanta ne yafara gani kafin yayi loosing control.
#MAMUH
#AZIZ AY LIMBA
#JANNAH ZAD

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 24

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi 1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection 1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.

******************
Koda Maman ta isa garesa gabaki daya ya fara loosing control gashi take duk Wanda yake aka maida kowa tsaye cikin qanqanin lokaci securities suka dagawa kowa hankali sai ga masu aiki da duka maaikatan gidan ana fitowa dasu kaman anzo patrol..

Jannah datake qanqame da Ummah a dakinsu data taddata taxo tana kokarin daidaita bugun zuciyarta dayake fita da karfi Yana mata ciwo a kirji me tsananin gaske idanuwanta sunyi jajir sake qanqame Umman tayi Wadda itama take sake rungumeta da kyau tana son tambayarta lafiyanta kuwa Amma kuma ganin yanayin nata sai ta fasa ta rungumeta tanajin kaman ta kurma ihun ganin Jannan ahaka.

Jin ana busa wani irin security whistle na tashin hankali ya saka Fatma dake kokarin tambayar Jannah lafiya ta fito.

Su madam Sisi da sauran kowa duka anfito hankali tashe cikeda tsoro da fargaba jiki na rawa,

Duk wanda ya fito yaga maigidan da kansa a tsaye shiga tashin hankali da sabon tsoro yakeyi.

Mama dake neman mutuwa sbd bugawan zuciya gabansa ta tsaya zatai magana Dzad ya bayyana gaban AZIZ din idanuwansa akan AZIZ din wanda shima nasa idanuwan suka tsaya cak akansa cikin wani irin tsananin mamakin dayake sake tsananta yanayinsa,

Maheer ne ya fito bayan Dad shima idonsa akan AZIZ din kafin Ammar wanda idanuwansa sukai jajir yana kallan AZIZ din cikeda wata irin tsana da baqin wannan lokacin fiyeda kowane lokaci na rayuwarsa..

AZIZ LIMBA duk yanda yaso boye yanayinsa kasa boyuwa yayi Wanda ya saka Sayd dayake cikin mummunan shock shima saurin jansa yana barin gurin dashi sbd kowane lokaci kowa zai iya gane waye AZIZ LIMBA a boye sbd yanayin yafara fin karfinsa.

Falaq ma datake hawaye tinda taga yanayin Daddynta tasan ciwonsa ya motsa gabaki dayane da sauri ta bi bayansu tana kokarin riqe hannunsa daya sedai ba damar hakan sbd gabaki daya ya rikice.

Mama data gama jiqewa da wani irin mummunan gumin tashin hankali da firgici itama kasa tsayuwa tayi sbd tana gab da yanke jiki ne ta fadi gaban AZIZ din Wanda tasan hakanne kawai zaisa a dakatar da wannan tashin hankalin na tsakiyar Daren da a gareta ba alkhairi bane.

Ya riga yaga Zaadens Amma hakan a yanzu bai dameta ba akan yaga abinda yake tattareda Zaadens din.

Toshewa numfashinta yake sake yi sbd bata fita tashin hankalin data shigo b dan haka Nicky ce ta kamata har zuwa dakinta daga Nan kowa ya watse aka koma ciki Banda securities da suka kwana a tsaye kan aiki sbd bazasu iya barin ko mage fita ba indai sun ganta har sai maigidan ya bada umarnin.

Mama na komawa daki ta samu nutsuwanta tafara dawo mata ta sallami Nicky.

Dare har ya raba sosai bata iya rintsawa ba tana zaune Daram cikin rashin nutsuwan xuciya da damuwa..

Sai data tabbatarda har securities sun koma waje ta miqe ta fito daga dakinta cikin rashin hayaniya ko dogon motsi ta nufi bangaren masu aiki ko karfin jiki batada sbd bata gama dawowa daidaiba har lokacin dan ba qaramin tashin hankali da shock ta shiga ba.

Ko data isa cikin kaman yanda tayi tinanin suma suna zaune zasuyi kwanan baqin ciki sbd ganin su da AZIZ sun hadu,

Hakan ta samesu a zaune dan haka kai tsaye ta tsaya gabansu babu bata lokaci ta fidda daurin sabbin Dollars dake hannunta ta ajiye gabansu batareda kwana kwana ba ko batawa kai lokaci ba tace

"Na baku damar tafiya batareda kunban Fatima dinba ku tattara a cikin Daren Nan ko asubar farin kubar nan,

Amma da sharadin zaku sanar Dani duk inda kukaje sbd Fatima zan Aiko masu dubata sbd zan nema mata lafiya"

Ammar da zuciyarsa ke gap da bugawa hakama kansa juyewa yakeyi yana sake juyawa miqewa yayi jikinsa na kakkarwa me tsoro ya shaqo wuyanta da karfin gaske Yana hadata da bango da karfin gaske.

Ihun azabar da bata taba ji ba a rayuwa taso fasawa Amma tinawa da halinda suke ciki ya sakata hadiye ihun tana wuni gurnanin azaba ido a waje,
Baki takeson budewa ta nema ceton su Dad Amma ba damar hakan sbd shaqar rabata da duniya Ammar yayi mata dan haka hannu ta ringa dagawa dakyau tana kokarin cetan kanta.

Dad da Maheer ne suka miqe suna banbare Ammar din daga gareta Amma gabaki daya baya hayyacinsa ya koma kaman wata halittar daban ma.

Da karfin gaske suka ringa kokawa dashi suka cirosa da kyar Maheer na qanqamesa da karfin gaske Yana rufe masa baki da karfi sbd wani irin numfashi Mai hade da ihu dayake kokarin sakewa.

Kallan Maman dake neman hanyar fita a rikice dad yayi yace

"Ki dauki kudinki ki tafi zamu tafi a cikin Daren Nan bazaa tashi damu ba
Nema kuma idan kin matsu kinsan Yan uwan Fatiman ki sanar musu su nememu kokuma ke ki kawosu gurinmu"

Yana fadar hakan ya juya itama bata tsaya daukan kudin ba ta fice tana cewa

"Ku tabbatarda Kun bar nan kafin safe"

Hanyar komawa ta kama tana hada hanya da numfashi koina jikinta na rawa.

Ko data Isa dakinta qasa ta zube tana son fasa kuka amma yaqi xuwa sbd wannan ne Karo nabiyu tana shan dukan mahaukata a cikin gidan nan.

Bata iya bacci ba sbd fargaba da yanayin datake ciki na tsoron daya kasa sakinta na shaqar Ammar da kuma gadin window taga ficewansu.

Akan idonta karfe biyu saura suka fito dukkaninsu ba Sanin kowa suka fito suka fice gate na biyu.

Ajiyan zuciya ta sauke tana zubewa bakin gadonta cikin samun wani abu me nauyi da tsoro da suka danne kirjinta.

Sai alokacin taji wani irin zazzabi ma Yana sauko Mata daqyar ta kwanta wuyanta na tsananin ciwo.

Suna isa babban gate kai tsaye aka dawo dasu tareda sanar dasu taku daya wlh idan dayansu yayi zuwa qarasowa gate zasu fasa qashin kafar mutum da bullet.

Babu annuri ko sauki ko kadan a duka fuskokin securities na gidan Wanda kuma har wani dogon Imani basu dashi dan haka zasu aikata abinda sukace dole suka dawo suka koma dakunansu suka kwanta.

******Washe gari sai qarfe 9 na safe AZIZ ya farka daga alluran da Sayd yayi masa a cikin Daren.

Kansa yayi nauyi dan haka kan yake a toshe baya iya tinanin komai saiya dawo daidai.

Toilet ya nufa ya sakarwa Kansa ruwa.

Ya jima sosai Yana duk abinda y saba kafin ya fito sanyeda bathrobe fara.

Sallah yayi wadda ta zame ta latti sosai haka sbd lalura shiyasa baya son yayi loosing control sosai ta yanda sai anmasa wannan allurar dake kaman sumar dashi kaman sakasa bacci na awanni.

Yana gamawa ya dade Yana istighfar da adhzkar kafin ya miqe.

Mama ma tayi Lattin tashi sbd zazzbin data kwana dashi Amma kuma tinawa da matsalarta ta kau sai ta tashi zuciyarta fes ba damuwan komai dan haka karfe 9 da rabi dukkaninsu suka fara fitowa breakfast daya bayan daya.

Suna zaunawa Shima ya iso a natse a kame Yana fidda kwarjinsa da haibarsa Yana daukan idanuwan duk Wanda yake kallansa.

Nicky da yanayinsa na jiyan yake dawo mata wasu mayun yawu ta hadiye tana masa kallan maita.

Gaida Mama yayi a kame hakama a Kamen ya amsa gaisuwan kowa Yana zaunawa.

Fara breakfast din sukai wanda Yana daukan cup din gabansa yakai bakinsa Fiddausi da Jannah suka sako kai a palon...

Jannah ce baya cikin nutsuwarta da a kame fuskanta bata kowace halitta a cikinsu ba ta qaraso gurin Nicky dauke da qaton plate din chicken potato.

Sayd daya dago a lokacin tea din dayake bakinsa ne ya dawo masa da karfin gaske haryana biyo ta hancinsa sbd mummunan firgicin da ba zato.

Mama m kusan abincin bakinta dinne ya dawo mata ta sarke da karfin gaske tana neman agajin ruwa da gaggawa sbd qwai da yayi mata cikin kai.

AZIZ LIMBA cup din hannunsa ya dire da karfi a kan dining din wanda ya saka gaban kowa faduwa tareda dagowa ya sauke idanuwansa da tin jiya basu koma daidai ba akanta.

Nicky ganin hakan da sauri tareda son nuna kokarin datai tace

"Mine na saka ayi maka wani abinda zakaci bayan tea sbd nasan bazaka ci breakfast me nauyiba"

Kallan Jannah tayi tace

"Ki ajiye a gabansa ki tafi"

Mama datake tari har lokacin cikin tsananin baqin ciki tace

"Waye ya bawa me aiki izinin shigowa muna breakfast"

Da sauri Nicky tace

"Nice na sakata ta kawowa Mine abu ne"

Zuciya Mama kejin kaman zata hadiya sbd baqin ciki ta bude baki zatai magana Nicky ta katseta da cewa

"Mama shatin meye a wuyanki?
Rataye kanki kina tashi yi ne sbd abinda ya faru jiya ko me?
Kodai mahaukciya Maman Jannah ne ta sake Miki wani abin kaman wancan Karan?
Mama kin hana a koresu last time gashinan tana neman sake illaki
Mama ki......

Wani irin baqin cikin daya taso ya rufe mama akan Nicky da babu alkhairi ko daya a duk lokacinda zata aikata abu dan haka bazata kashe ita kadai da ciwon zuciya ba sedai su mutu tare dan haka batasan lokacinda tace

"sbd JANNAH ZAD ce matar AZIZ shiyasa"

Daidai lokacin da maganar Maman ta fita daidai AZIZ din na kama hannun Jannah data juya zata bar dining din ya juyo da ita gaba dayanta.

Ita kuwa Nicky dip ta dauke wuta zaune a gurin maganar Mama tayiwa qwaqwalwanta saukar bomb din soji.

Shi kuwa budan bakinsa kalman daya furta itace

"Mimi na raye????

Sayd kuwa bakinsa a rikice yace "4&4"
#MAMUH
#ZAADENS

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 25

*SHOP WITH ME BY RANO*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

************
Qarasa sarkewa mama tayi da jin abinda AZIZ yace ruwan datasha suna qarasa biyowa ta hanci da yi cikin kanta,

Ita kuwa Nicky maganar Maman da 4&4 din da Sayd ya ambata Yana kallan Jannah suka saka jini fara fitowa kawai ta hancinta habo me karfi na balle mata.

Fiddausi a rikice take bawa Mama ruwa tana kuma daukan tissue da sauri tana dorawa Nicky a hanci da hannunta daya..

Jannah da maganganun Nicky itama suka gama tinzira zuciyarta akan Ummanta Fizge hannunta tayi daga cikin nasa tana juyawa zata fice Nicky tayi wani irin yunquri tana daukan ruwan tea masu tsananin zafi ta watsa mata setin fuskanta Wanda kafin saukansu AZIZ din ya miqe tsaye da sauri Yana rufe fuskan jannah da tafin hannuwansa biyu yana bada bayansa ga ruwan zafin.

Falaq da sauri cikin tsananin tsoro ta miqe tana daukan tissue tafara goge bayansa hnkali tashe tana cewa

"Daddy ruwan zafi ne f sosai?
Daddy ka cire rigan da sauri"

Ko abinda Falaq din ke fada baya ji hannun Jannah din ya sake komawa ya jata kai tsaye suka bar dining din yana janta zuwa palonsa sedai ko taku hudu basuyiba ta qwace hannunta da karfi tana dakatawa tareda dagowa ta kallesa da idanuwanta da sukai ja suna bayyanarda tsanar datakewa duk Wanda yake gidan tace

"Idan umarni ne dakai ka fadamun ba buqtaan zuwa koina,
And Ni me aiki ce inada haqqina na Yar Adam kuma musulma dan haka tabani keta haddin Allah da kuma na addini na ne"

Wani irin zafi da radadin gaske zuciyarsa ke yi ya kalleta da idanuwansa da sukai jajir ya bude baki yace

"Meya samu tinani da hankalinki?
Aiki kike magana?
Ke me aiki a cikin gidana?
Are you mad or just stupid?
Wane son of a bitch dinne ya baki matsayin me aiki a gidan nan?,
Duka Zaadens suna aiki a gidana a matsayin me aiki waye da waye suka San da hakan a gidan nan?

Cikin izgilin maganar da yayi mata ba tsoro ko shakkar kowa ta juya ta kalli Mama da idanuwanta tana bude baki tace

"Wannan maganar ahali ce Ni dai a matsayina na me aiki idan har aka sake wucen iyakata ta hanyar tabani ko sake ambatar Ummana da wani sunan da ba itace ta dace dashiba masu gidan ne to tabbas zamu tafi kaman yanda ake bin dare ana biyanmu dan hakan"

Juyowa yayi ya kalli Maman Wadda gabaki daya ta qarasa rikicewa tana debewa Jannah da Nicky albarka cikin ranta...

Baki ya bude zaiyi magana Nicky ta kalli Mama cikin wani irin tsananin baqin cikin da zarewan kai har lokacin hancinta na jini tace

"Meyasa tin farko kika boyeta kina kallo bayan alkawarin da kikai har abada bazata dawo rayuwarmu ba,
Amma shine Mama kina kallo kika hana a koresu bayan dukan da mahaukaciyar mahaifiyarta tai Miki?
Menene yasa kika hana su tafiya Mama?

Cikin wata irin tsawan data saka kowannensu sake shiga mummunan tashin ya katse Nicky da cewa

"Kina shan weed ne?
Mahaifiyan Jan kike ambatarwa hauka ko me?
Daga lokacinda bakinki ya qara furta mata irin wannan kalman zakisan matsayinki bai gama cikaba a gidan nan......

"AZIZ" Mama ta kirasa da idanuwanta jajir na azabar da bata gama futa ba ta sarkewa zuciyarta na wani irin tiririn fara kare mahaifiyar Jannah da yayi maimakon ita tace

"AZIZ jin nayi kaman Kana daga matsayin Zaadens akan taka Uwar??
Menene matsalanka da duk sunan da zaa kirasu?
Inace Jannah din tsohuwar matarka ce da babu aure a tsakaninku idanma akwai wlh ban yafe yau auren ya kwana ba batareda ka saketa ba"

Dago jajayen idanuwansa yayi y sauke akan Maman yana hadiye maganar da yayi niyar fada sbd idan akwai wnda yake girmamawa da jin nauyi a duniyarsa yanzu d baida mahaifiyar data haifesa to Mama ce,

Fada mata magana a cikin ido ba dabia ko halinsa bane Amma kuma akwai abinda ko bai fadaba mutuwa ce kadai takai can.

Nicky da hawaye ke bin fuskanta jikinta koina na wata irin rawa fita tayi da gudu bta ko ganin gabanta tayi kitchen wanda ba shiri dukkaninsu suka bi bayanta Banda AZIZ din daya qi motsawa ko taku daya sbd yasan dai haukarta ko rabin tasa bataiba ita qananun likitoci take gani shikuwa manyan likitan kwakwalwa yake gani.

Mama datasan bangaren masu aiki Nickyn tayi kuma kowama zuwa zeyi dan haka ganin Fatima ayau din kila ya tabbata dan haka da gudu take bin bayan Nicky din tana kiranta tareda yimata tsinuwar da duk taxo bakinta sbd tana taba Jannah Allah ne kadai me hana AZIZ zuwa bangaren.

Cikin daga sauti Mama ke cewa

"Sisi ki tareta duk tsanani kada ki bari ta qasa bangaren Nan"

Sisi na jin hakan suka fito itada Yan aikin gidan gabaki daya.

Nicky a haukace take bata ji bata gani abu daya takeso ta kashe Jannah idan yaso ko bata auri AZIZ ba tasan dai bazai taba auren kowa ba.

Ammar ne a tsaye Yana goge motar Nicky din y hango Nicky tafe a haukace da kwalban glass cup a hannu.

Jannah dake kokarin fitowa daga bangarensu ta tinkara gadan gadan dan haka da gudun gaske ya tinkari Jannah din

Kafin ya isa Nicky ta daga kwalban da karfi zata bugawa Jannah a kirji Jannah ta kauce sedai cikin tsautsayi kwalban ya yankata sedai ba sosai ba sbd ta kauce.

Cikin mummunan tashin hankali Ammar da idanuwansa suka rufe ya zabgawa Nicky wani mahaukacin marin daya saka Mama tsallakewa da wani irin tsallen gudun gaske sbd tasan shima haukar ta motsa kenan bige bige zaayi.

Madam Sisi da daman a tsorace take itama wani mugun tsallen ta daka tana neman hanyar guduwa kafin uwar Yan haukar itama ta fito jin ihun 'yarta Wanda tasan duka gidan haukacewa zeyi tinda mahaukatan ciki sunfi masu lafiya.

Sayd da gabaki daya hankalinsa ya tashi da wannan tashin hankalin da rikicewa da gidan yayi da sauri ya nufi Ammar shi da Maheer sbd ganin yanata kifaw Nicky Mari ba kakkautawa.

Mama gabaki daya hankalinta ya rabu kashi biyu ga tsoron haukar gaske tuburan datke gani ga tashin hankalin kada Ummah ta fito.

Riqe Ammar akai har lokacin itama Nicky bataji bata gani Jannah take son illatawa..

Ammar hannuwansa na wata irin rawa ya dawo gurin Jannah dake tsaye idanuwanta jajir tana kallansa cikeda tsananin kauna da tausayin halinda yake shiga akanta ya zubawa kirjinta dake jini ta cikin doguwar rigar jikinta.

Qara ja idanuwansa ke yi ya miqa hannunsa kai tsaye zai bude rigarta ta wuya ya duba gurin
Hannunsa na isa kafin ya sauka jikinta aka riqe hannunsa cak.

Wata irin rawa hannunsa keyi Wadda ba tasa rawar hannun ce ba ta hannun daya riqe nasa hannun ne...

Gabaki dayansu tsit sukai tareda tsayawa cak sbd yanayin AZIZ din yayi munin da tsoronsu ya qaru.

Falaq kuka takeyi tin dazu tana jikin fiddausi a qanqame.

Mama kuwa rawa kafafunta suka dauka ganin AZIZ din da bata taba ganiba tin yana yaronsa kuwa.

Alluran dake hannunsa ya jefawa Sayd Yana bude baki da mummunan sautin daya saka haukar Nicky tsayawa cak yace

"A rufeta a daki bayan wannan masu daukanta na zuwa"

Dawo da kallansa yayi kan Ammar zaiyi magana sai kuma ya fasa ya miqa hannunsa ya kama hannun Jannah a gaban kowa ya jata ze bar gurin Ammar ya riqesa kai tsaye jikinsa na rawa yace

"And where d hell do you think are you going wit my wife?"

Wani irin mummunan sarawa kan AZIZ yayi ya juyo da idanuwansa jikinsa na tsananta rawa ya kalli Ammar din yana hadiye wani irin masifaffen ciwo da wutar data kama kirjinsa take wanda ya sake saka dukkanin masu aikin sake ja da baya
Mama ma da bata hayyacinta idonta na kan kofar fitowan Fatima sake samun kanta tayi da tsananin shakkar AZIZ wanda a yanzu take zargin ba daidai ba.

Kasa cewa komai yayi ya juya ya kalli Sayd
Nicky da sauri cikin tsananin baqin cikin da wutar dake ci kirjinta ta kwace daga madam Sisi tana cewa

"Eh matarsa ce aurenta...... Bata qarasa ba Sayd ya someta da allurar hannunsa ya nufi Ammar yana qwala Kiran securities dan shima Ammar din dole a rufesa kafin zuwan likitocin mahaukatan.

AZIZ na juyawa Mama tayi wuf ta fada dakinsu Jannah dan dubo Fatima sbd daidai lokacin saceta ne yanzu batasan tana dakin Dad ba tareda Dad din.

Jannah kuwa cikin tsananin fushi da ciwon da kirjinta ke mata ta fizge hannunta sedai kafin tayi wani motsin ya dauketa cak dinta yabi ta kofar da shi kadai ne me bi da ita.

Daqyar ya isa Sama da ita sbd yanayinsa dayake tsananta ya sakawa dakin key tareda zarewa yayi jifa dashi da karfin gaske Yana buga bango da hannunsa cikin wani irin tsananin fushi da wutar zuciya.

Baya taja sosai tana kallansa cikin wani irin yanayin tashin hankali sbd gabaki daya ciwonsa ya wuce yanda ta Sani,
Ciwon ya qarasa nisan da abin yayi Muni.

So take ta hanasa jiwa kansa raunin sbd yanda jini ke futa a hannunsa din Amma kuma ta kasa motsawa bare isa garesa sbd zuciyarta dake cikeda tsana har lokacin.

Ganin abin yayi tsananin gaske ya sakata isa gurinsa cikin daga sauti da nata fushin tace

"Ya isa,idan kashe kanka zakayi ka me yasa zakayi hakan a gabana?
Idan ka......

Wata irin tsawa me karfin gaske ya sakar mata Yana juyowa ya kamata da hannuwansa biyu ya girgiza da karfi yace

"Da auren nawa akanki wani yake kiranki matarsa?
Ina raye igiyoyin aurena uku suna raye kika bari wani ya kiraki matarsa?
Kin shirya zarar Dani ne bayan Wanda nake fama da ita?
Kinason maidani makashi ne??

Da wani irin mahaukacin sauti da kararsa ta fice ta me hankali da gabaki daya gidan saida ya amsa jikinsa na wata irin jijjiga yace

"Wayace ya kiraki da sunan matarsa"

Wani irin mummunan firgita tayi sbd tsananin tsoron yanayinsa da kaman ita zai fara kashewan.

Tsit gidan yayi kowa na sake shiga tausayinsa sbd alamu sun fara bayyana me gidan kansa ba lafiyayye bane a tsakanin jiya zuwa yau.

Juyawa yayi sbd wani irin tafasa da wutar dake ci jikinsa da zuciyarsa dake ingizasa ga maidata macensa a yanzu da tsakiyar ranar kowama ya huta Amma kuma a yanda yake zai iya mata illar da zatai Muni dan haka ya nufi toilet baya ko gani ya sakarwa Kansa ruwa yana zubewa qasa suna sauka a jikinsa.

Daqyar ta iya daukan key din dakin ta fice da sauri itama bata ganin gabanta sbd tsananin tashin hankali da firgicin maganganunsa ta nufi daki kai tsaye dan dauko takardar sakinta ta duba.

A daidai wannan lokacin Mama ta isa dakin su Jannah din da kwalban da Nicky ta yadda bayan ta sume dan neman Ummah.
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS

07019691719

*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 26

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

******************
Mama da hannuwanta ke tsananin rawa idanuwanta na rufewa ga kuka tsananin tsoro da fargaban dayake cike da kirjinta sbd Sanin bame hankali ce zata dosa da makami ba hakama kusan duka ahalin ita ganin takeyi kowama a gidan mahaukaci ne,

Shakkar haukar Umman takeyi sbd taga dukan gaske takeyi gata bata gama wartsakewa daga muguwar azaban datasha a hannun Ammar ba a Daren jiyan Amma bazata bari wannan damar ta wuce taba ta dauke Fatima tabar gidan da itaba sbd matiqar tana gidan batada zaman lafiyar zuciya data kwakwalwa dan itama kila zarewan zatai kaman Su Nicky ta ari hauka ba shiri dan haka gwara ta fiddata gidan tasan yanda zatai da ita bayan barin gidan da ita.

Hannuwanta har qara rawa sukeyi ta bude dakin su Jannah din tana shigowa kai tsaye sbd Sanin babu kowa a bangaren duk suna can.

Duba dakin tahau yi da idanuwanta a zare tana qarasa shigowa da tsoronta na ficewa.

Ummah bata dakin dan haka sake riqe makamin hannunta tayi dakyau tana nufar toilet din dakin.

Da karfi ta budesa tana soko kwalban ciki da karfi tin kafin ma taga waye a ciki sedai babu kowa a ciki.

Zufa ne ya fara gangaro mata ta juyo tana sake riqe makamin da kyau ta nufi dakin Dzad tana ayyanawa a zuciyarta tana dakinsa tareda tsinewa wannan masifaffen auren da a yanzu batama fatan ya mutu so takeyi suyita son junan ta samu suqi rabuwa su dauketa suyita tafiya ko zaa barta taji da 'danta ta dawo Kansa da zuciyarsa dake neman sauka daga inda ta dorasa.

Kokarin fitowa dakin takeyi kaman daga sama Umman ta bayyana gabanta ta fito daga dakin Dzad idanuwanta jajir kuka ne da tsananin tashin da ciwonta yayi suka saka kamanninta gabaki daya sauyawa.

Mummunan faduwa gaban Mama yayi zuciyarta na neman tsinkewa da ganin mummunan yanayin Fatiman dan haka taja da baya kadan tana dago fasashiyar kwalban hannunta tana nuna Maman da ita ta bude baki zuciyarta na bushewa tace

"Fatima kece kika zabi mu zama hakan tinda tin farko kinqi yadda ki bini kika zabi makasan 'yarki,

Kika zabi Wanda suka kashe Ummitah da karfi d yaji suka cire zuciyarta suka bawa tasu Yar Wadda kike yiwa tsananin son asara,

Kin zabi maqiyiyar ABDULAZIZ dina tinda kika zabi maqiyansa akansa,

Kin zabi Wanda suka wargaza rayuwar 'dana suka illata rayuwarsa illar da bazata barsa ba har abada,

Hakanne yasa bakida wani amfanin bayyana a rayuwarsa Fatima,
Ya dade da manta ki,
Ya rufe babinki
Nice uwa kuma mahaifiyarsa da bazai taba sauyani ba har abada,

Kinsan abubuwan dana fuskanta akansa tin yarinyartarsu shida Ummitah har zuwa yanzu?

Tayaya zaki dawo a lokacinda bazan iya baki shi ba,
Bazan taba iya rasa AZIZ LIMBA a matsayin Dana ni kadai ba,

JANNAH itace masifar gabaki daya rayuwar AZIZ Dina dan haka saina tabbatarda dga ke har ita babu Wanda har abada zai iya shiga tsakanina da.....

Kaman a mafarki taji anyi sama da ita an rafkawa tiles din gurin wnada ya daka idanuwanta da kanta juyewa tana kasa gane a mace take ko raye sbd azabar da tinda Allah ya halicceta tin haihuwa bata taba jinta ba irin yau.

Sake shaqurota Ummah tayi ta daga jikin bango ta sake bugata da qasa wanda ya saka wani rikitaccen ihun neman agaji fitowa bakinta jikinta na tsananin rawa sbd dukan rabata da duniya Ummah takeyi idanuwanta a rufe cikin rashin hankali da haukarta daya tashi tuburan sbd sunan ABDULAZIZ da Ummitah dayaketa juya kanta Yana sake haukatar da kwakwalwanta sbd tabbas sunayen sunzo mata a daidai sune sunayen dake mata yawo akai koyaushe ciwonta ya tashi.

Mama balain dataji Yana neman rabata da duniya ya sakata bude baki tana ihu ba shiri sbd hadiye azabar takeyi da farko tana hana kanta ihu sbd kada azo a samesu zancen yaje gaban AZIZ.

Jin Ummah zata rabata da sassan jikinta da duniyar ma gabaki daya ba shiri ta fara ihun neman ceto.

Koda Dzad dake toilet ya juyo ihun da sauri y fito
Ya duba dakin bega Ummah daya bari tana bacci ba da sauri ya saka kayansa ya nufi kofa cikin tsananin tashin hankali.

Maheer ma da tsananin gudu ya baro Ammar dayake kokarin taimkawa ya dawo daidai a dakinsu ya fito.

Mama suka gani a hannun Ummah tayi mata wani irin jina jina dan haka da tsananin gudu sukai kansu Dad ya janye Ummah Yana qanqameta jikinsa da karfi Yana rungume kanta zuciyarsa na bugawa da karfi idanuwansa na jajir sbd ganin gabaki daya ciwonta ya qarasa rikicewa.... tsananin tausayinta ne ya saka idanuwansa tsananta ja ya kalli Maheer yace

"Ka miqata inda zasu bata taimakon gaggawa"

Daki Dad yayi da Umman ita kuma Mama cikin tsananin azaba Maheer ya fito da ita sedai ko nisa basuyiba Madam Sisi tagansu ta qaraso jikinta na wata irin rawa tana neman buga ihun jawo hankalin maigidan yaga abinda ya samu mahaifiyarsa.

Cikin tsananin azaba mama ta hanata ihu tana cewa karta sanar da kowa idanma tayi nauyi tace a stairs ta fado.

Da sauri da mamaki Madam Sisi ta bude baki zatai magana Maman ta yanke jiki ta fadi daidai suna isa palon qasa dan haka dole Madam Sisin ta fito da gudu tana neman Sayd Wanda tini yakai Nicky dakinta aka rufe.

Falaq da fiddausi ne suka fito jin hayaniyar madam Sisi suka tarar da Maman a zube qasa harda jini a fuska da jikinta.

Madam Sisi data dawo jiki na rawa tace stairs Mama ta fado.

Fiddausi na jin hakan ta qarasa gurinta da sauri hakama Falaq.

Daki akai da Maman tareda Kiran likita Falaq ta hana a sanar da daddynta sbd Yana tareda Jannah Wadda a daidai lokacin ne gidan ya dauki ihun tsawarsa data saka kowa sake yin tsit Yana magana da Jannah.

Ko da Jannah ta baro palonsa bata ganin gabanta maganganunsa ne ke neman juyar mata da kai sbd tasan har abada ta gama zama Matar AZIZ LIMBA dan haka bama zai yiyiba abinda kwakwalwansa take basa yana fada.

Zaadens da Garba da suka San abinda ya faru na dukan da Ummah taiwa Mama da kuma yanda jikinta ya rikicen fuskewa sukai kaman ba abinda ya faru basu fadaba kuma basu nuna ba,
Ummah na daki tareda Dad Yana sake kokarin ganin ta dawo daidai ko yaya ne,
Hakama Ammar Maheer sun samu ya koma daidai sedai a cikin kwakwalwansa da zuciyarsa babu sauki ko sassauci ko kadan dan kuwa a wannan Karan idan ya rasa Jannah baisan abinda zai zamaba dan gwara ya mutu yabar duniya da hakan ya faru dashi.

Ko da Jannah ta iso babu kowa duka kowa Yana dakinsa dan haka kai tsaye dakinsu ta shiga ta nufi wardrobe dinta hannuwanta na wata irin rawa idanuwanta na qafewa da rikitaccen tashin hankali sbd bata fatan ko kadan taga komai bayan rubutaccen saki na mutuwar aurenta da AZIZ LIMBA.

Kayan cikin wardrobe din tafara janyowa tana wurgi dasu tsakiyar dakin idanuwanta na sake qafewa jajir...

Bataji bata gani kayan ciki kawai take fitarwa tana jefarwa,

Acan qasan kayanta rigarda ta bayyana wadda envelope din yake nade a cikinta.

Hannuwanta dake tsananta rawa takai da sauri ta fizgo rigar tana budewa bugun zuciyarta na tsananta.

Bayyanar envelope din ya sakata jefar da rigar tana budewa da wani irin rawa da dukkanin jikinta keyi.

Kasa budewa tayi dan haka ta saka karfi ta yagasa gabaki daya..

Takardu uku ne suka zube qasa daga ciki Wanda ta zubawa idanuwa tana kafesu da wani irin kallon da takardan saman itace ta bayyanar mata da ticket ce...

Sarewa qafafunta sukai ta zube qasa da karfi tana jin dukkanin jikinta na daukan wani irin zafi da zazzabi me karfin gaske.

Kasa saka hannuwanta tayi akan takardun sbd yanda zuciyarta ke wani irin juyawa tana kamuwa da ciwo me tsananin gaske.

Daqyar ta iya miqa hannuwanta suna rawa ta dauki takardun duka ukun tana fara bude ta farko Wadda ta sakata damqe takardun da karfi tana qasara zubewa zaune qasa gabaki daya.

Sabon ticket ne aka siya da sunansa da komai na tafiya a wancan ranar da limbas suka bar qasar.

Kafe ticket din tayi da idanuwanta tana kasa kyaftawa zuciyarta na tsananta ciwo da wani irin yanayin dake saka idanuwanta fara cikowa da hawaye masu tsananin ciwo.

Ta biyun ta dago ta bude ahankali Wadda rubutunsa ne a tsare cikinta na kalmomin da basu wuce biyar ba.

"KINYI NASARA AKAN AZIZ LIMBA DA DUK ABINDA YAKE ZUCIYA DA RAYUWARSA,

FATIMA DA FATIMA SUNE RAYUWAR AZIZ LIMBA IDAN ZAN MUTU DA KAUNARSU TO ZAN MUTU NE DA SON WADDA ITACE ASALIN ZUCIYAR,

AUREN AZIZ LIMBA AKANKI MUTUWARSA CE KADAI ZATA RABA WANNAN AUREN"

Rintse idanuwanta tayi hawayen dake cikinsu masu tsananin zafi suka gangaro tana fasa wani irin kukan da babu sauti tana kasa bude takardar karshen hannuwanta na damqe takardun hannunta da karfi suna nadewa.

Kuka takeyi sosai wanda daqyar ta iya dago takardar karshen ta bude...

Address ne na gidansa da qasar dayake na ticket da aka siya mata sai a qasa da aka rubuta.

Zan jira zuwanki a duk lokacinda zuciyarki ta aminta Dani na Miki alkawarin wannan"

Rintse idanuwanta tayi tana cusa kanta cikin kafafunta kukanta na sake tsananta sbd wannan envelope Yana kokarin maidata inda rayuwa take tsawon shekaru biyu da suka wuce,

Tayaya a lokaci daya komai yake neman juyewa ya komar da ita kaddarar da bata fatan komawa?

Tayaya auren data jima da wankesa ta kakkabe a zuciya da rayuwarta zai dawo mata,

Ta gama cirewa da yafe AZIZ LIMBA a rayuwarta,
Da Ammar Zad ta shirya ta yadda fara rayiwa sbd gyara kuskurenta ta baya Amma tayaya ma zata iya kallan ahalinta data cewa aurenta da AZIZ ya rabu kuma a yanzu da suka gama karban sabuwar rayuwa da wanke komai na baya tace musu auren da dukkaninsu sukafi kaunar mutuwa dashi tace Yana Nan?

Dago jajayen idanuwanta tayi tana kallan takardun hannunta wasu hawaye suka sake gangaro mata na wani yanayin me karfi dake fitowa can qasan zuciyarta tana dannewa ta bude baki tace

"Nima ban karbi auren Nan ba bazan karbi duk wannan zancen ba har abada anrufe babin AZIZ LIMBA rayuwata dan haka babu wani sauran abinda ya rage musu bayan rabuwa da juna batareda ma kowa a ahalinsu yasan da akwai aurenba har yanzu.
#MAMUH
#ZADENS
#LIMBAS
#LOVE PSYCHOs
#CRZY LOVERS
#MAMA
#NEW LIMB*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 27

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
https://chat.whatsapp.com/IexiuY21PP75lt4yoJtNsK
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

************
Miqewa tayi ta sake share fuskanta ta tattara takardun tareda daukan envelope din ta hada dashi ta juya ta nufi kofa ta fice idanuwanta a rufe bataji bata ganin komai bayan sabuwar takardar karshen auren AZIZ LIMBA.

Ko data iso palon qasa babu kowa sai Sayd da zai wuce da likita zuwa zamansu Mama ko kallansa bataiba shima hanya ya bata sbd ganin yanayinta Musamman da idanuwansa suka sauka akan takardun dake hannunta take ya fahimci abinda zai faru dan haka cikin sauri ya wuce da likitan sama dan ya duba mama ya gama ya fice.

Yanda take hawa stairs din idanuwanta a rife ya saka har faduwa takeyi amma bata tsaya ba sai data Isa kai tsyae kuma ta bude kofar palon ta shiga.

Baya palon dan haka bacin rai da tsananin baqin ciki bai barta jiran komaiba ta isa kofar bedroom dinsa ta bude kai tsaye.

Zaune yake a couch har lokacin fama yake da kansa jin yake kaman ya fasa ihun dazai rusa gidan gabaki daya,

Jin yakeyi wata irin wuta na balbala a zuciya da jinin jikinsa,

Idan har wani zai iya sake ambatar 4&4 da sunan matarsa a gabansa babu abinda zai iya hanasa zama makashi...

Dago jajayen idanuwansa da suka sakata dauke idanuwanta akansa tana qarasowa gurinsa...

Rintse idanuwansa yayi sbd indai a daidai wannan lokacin aka cigaba da wannan hayaniyar zai iya rasa control na Kansa dan haka qin dagowa yayi ya kalleta yana sake rufe idanuwansa ya bude.

Takardun hannunta ta zubar masa a gabansa tana bude baki da sautin dayake bayyanarda fushi da kuka ciwon abinda zata fada dake zuciyarta tace

"Ni Jannah Zad bazan taba iya zama matarka ba,
Ayau a Karo na biyu na sake zabar rabuwa dakai,
Wancan Karan I choose my family wannan Karan kuma I will choose Amm......

Qarar glass din table din gabansa da yayiwa wani mahaukacin duka ne ya sakata rintse idanuwanta idanuwanta da karfi ya hanata karasa zancenta.

Qarfin karar har palon da dukkaninsu Falaq da Sayd suke said sukaji kowannensu yayi qasa da kansa babu me iya cewa komai bare motsawa Musamman Falaq da idanuwanta suka ciko da hawaye sbd komai na rayuwar gidan d daddynta sun rikice a qanqanin lokaci amma dai idan har zai shirya da Jannah komai da zai faru me sauki.

Miqewa tsaye yayi tareda fizgota da hannuwansa biyu da karfi zuwa jikinsa wanda ya saka rauninta fiddo jini tana rintse idanuwanta cikin karfin halin hana kanta sanyi ta bude idanuwan ta sauke akan fuskansa datai jajir idanuwansa da babu abinda yake cikinsu bayan wata irin fitinar wutar kishin dake neman kashesa ya bayyanarda haukansa gabaki daya zuwa level din karshe.

Ita ya saukawar idanuwan Ya zubawa Yana rasa abinda zai mata,

Wata irin azababbiyar Soyayyar da yakejin zatai ajalinsa ke ci da wuta a kirji da zuciyarsa,

A cikin kwakwalwansa wani irin jijjiga da yamutsi yakeji duk akan Jannah Zad Wadda duka wannan masifar da balain dayake ji bai taba jinsu akan rashin Fatima da Fatima ba Amma a yanzu Yama rasa wace masifar da baya iya controlling ne yake ji...

Ruwa ne take gani suna cika idanuwansa Yana kasa cewa komai jin yake kawai Yana zarewa dan haka ya janyota jikinsa ba zato ya qanqameta ahankali Yana rintse idanuwansa ko zai samu sassaucin abinda yake ji sbd azaba ma yake ji yanzu wanda Tai masa yawan da bazai iya riqewa ba..

Qwacewa ta fara yi tana fizgewa sbd itama azabar take ji a kirjinta da azabarta take mata yawa.

Duk yanda taso qwacewa kasawa tayi dan haka ta fasa masa kuka me karfi tsawon lokaci har takai karfinta ya qare ta bude baki cikin sautin gajiyawa da komai na rayuwa tace

"I hate you AZIZ LIMBA,
I hate you,I hate you"

Saukan kalamanta a kunnuwansa sakasa rintse idanuwansa yayi Yana sake qanqameta jikinsa wasu hawaye masu dumi a Karo na farko suna gangarowa daga idanuwansa dake rufe jikinsa na wata irin rawa alaman Yana cikin yanayin ciwo har lokacin.

Hawaye takeyi sosai itama tana sake furta masa ta tsanesa.

Yanda jikinsa ke tsananta da kalamanta ya sakasa kasa sakinta ya nufi toilet da ita a hakan Yana isa ya sakar musu ruwan daya saka karfinta dawowa tafara turesa tana tsananta kukanta da fada masa irin girman tsanar datai masa tareda tsanar dataiwa kanta na taba sonsa a rayuwarta.

Rintse idanuwansa yakeyi Yana sake qanqameta kalamanta naci gaba da hargitsa qwaqwalwa da rayuwarsa ma gabaki daya Yana sake zarewa.

Binsa ruwan sukeyi suna basa nutsuwa da sassauci ahankali tsawon lokaci shiru sai kukanta dayake tashi ahankali ahankali Yana ratsa kunnuwansa.

Dagowa yayi ahankali ya saukar da jemamun idanuwansa da sukai tsananin laushi ya saukesu akan fuskanta daya dago ahankali ya kafeta da kallon da bai taba yiwa kowace halitta irinsa ba.

Baya taja ahankali jikinta na dan rawar sanyin ruwan da suke dade suna rasata na sanyi batareda ta kallesa ba ta juya har lokacin zuciyarta zafi take mata.

Riqo hannunta yayi ahankali batareda yace komaiba ya dawo da ita jikinsa ta baya bayanta ya sauka kirjinsa cikin rashin karfi sbd kukan datai sosai yaci karfinta sosai.

Hannuwansa ya saka ahankali ya zagayo cikinta Ya rungumeta Yana rufe idanuwansa ahankali sbd nutsuwarsa data samu.

Sake bude idanuwansa yayi tareda daga hannunsa daya yakai wuyan rigarta ba tsammani taji yaja rigar kai tsaye ya sauke daga kafadanta yana birkitota.

Da sauri taja baya tana dafe rigar sedai jikin bango ne take dan haka taku daya yayi me sanyi ya rifeta a bangon Yana sake Dora hannunsa gurin yana kallan fuskanta datake a tsananin hade.

Hannunta ya cire kai tsaye tareda sake janye rigar Wanda take saman kirjinta ya bayyana ta sake saka hannu zata tare ya hada hannuwanta biyu da nasa daya ya riqe ta bayanta ya kalli idanuwanta da nasa idanuwan da suke mata nuni da a ayanzu Yana hayyacinsa ya dawo daidai karfinsa a cike yake 100%

Itama kallansa tayi da rashin shakkarsa zata bude baki tayi magana ya sako Kansa cikin wuyanta ya ruwan da suka gangaro daga fuskanta suka sauka kan dogon hancinsa ya saki wata ajiyan zuciya ahankali Wadda ta sakata sarqewa tana son qwacewa Amma ba daman hakan.

Ciwonta dayake buqatan gani ya zubawa ido Yana hadiye radadin ganin raunin kafin ya saka hannu ahankali ya kashe musu ruwan ya saketa ahankali tareda juyawa ya nufi towel Yana zare rigar jikinsa kai tsaye wadda ta bayyanarda kakkarfan jikinsa daya sakata juyawa tana kallan jikinta da kayan jikinta da batasan yanda zata fita dasu ba a hakan Wanda zai iya saka familynta tambayar inda ta fito.

Towel ya daura a jikinta tareda juyowa baice mata komaiba ya kamo hannunta tareda janta suka fito jikinta duka sanyi dan batada niyar sauya kaya ko zare na jikinta,

Bai iya tilastata ba sbd bayason su sake fara hayaniya dan haka kai tsaye janta yayi har gaban dresser dinsa ya kaunar a kujera yana dauki cotton me laushi da tsafta ya sake sauke rigarta zai Dora hannunsa ta riqesa da hannunta daya tana qin kallansa har lokacin ciwon rayuwarta dashi takeji.

Hannunsa ya saka ya zare hannunta tareda kai hannunsa kan qaramin yankan yayi mata wata irin gogewa ahankali cikin nutsuwa tareda kai bakinsa gurin ahankali ya bude bakinsa ya hura wani irin iska me sanyin daya saka numfashinta tsayawa cak tana qanqame hannuwanta sbd saukan iskan bakin nasa akan fatarta dake jiqe sanyin yayiwa lafiyarta yawa taji.

Rintse idanuwa tayi sbd zafin dataji a gurin tana kuma gujewa kallansa..

Ganin sanyin dake ratsata zai mata yawa ya sakashi miqar da ita yanzu zauna tareda janyota ta fado Kansa ya mata wani kyakkyawan riqo Yana zagayeta da hannuwansa da kirjinsa sbd rage mata shigar sanyin AC na dakin Yana qara goge kirjinta dayake ganin yanda zuciyarta da numfashinta ke bugawa da karfi suna sama da qasa.

Akan tabon dinkinta na zuciya yankan ya sauka dan haka ya sake zubawa gurin idanuwansa Yana jin zuciyarsa na kasa daukan girman abinda yake ji akanta sbd ita da Ummitansa ne kaman a guri daya,inama Ummansa na raye ya ajiyeta guri daya da Jannah su kansace mata uku a rayuwarsa dayafi so fiyeda rayuwarsa sun hade guri daya.

Yanda ya kafeta da idanuwansa dake sake zama wasu sexy Yana kallanta kaman zai iya hana komai da kowa sake ganinta ne ya sakata miqewa da sauri tana nufar kofa ta durqusa ta dauki takardun datazo dasu tana kokarin ficewa tana isa kofa ta dakata batareda ta juyoba ta bude bakinta da nayi nauyi tace

"Ina Nan a matsayata na aurenka akaina ko ka yankesa ko kada kayi hakan bazan taba sake zama da auren kowa ba bayan na wanda nake s......"

Juyota kawai taji anyi da karfi tareda hade bayanta da jikin kofar datake tsaye yana Dora bakinsa ahankali akan lips dinta tareda zira harshensa cikin tsakiyar bakinta Yana saka dukkanin karfinsa ya yaga rigarta da daman ba wani karfi ne da itaba tinda material din ba tsada.
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 28

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
https://chat.whatsapp.com/IexiuY21PP75lt4yoJtNsK
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

**************
Janyewa tayi da karfi kirjinta na harbawa da karfi sbd yanda yazo mata a bazata kuma kaman hankalinsa na gushewa sedai ko gama janyewa bataiba ya dawo da ita jikinsa da karfi Yana qarasa raba rigarta ya jefar cikin glass din dayake fashe na table din daya fasa dazu...

Black bra ce a jikinta da skintight Wanda suke a jiqe suma tayi saurin sake turesa kafin ma ya sake dawowa gareta ta baya da sauri idanuwanta na cikowa da hawayen 'dacin zuciya ta daga hannu zata nunasa tayi magana ya kama hannunta da hannunsa daya Yana sarke yatsun cikin nasa ya dago idanuwansa da sukai ja ya kalleta babu abinda yake ji a zuciya da jininsa bayan tsananin azabar maganar data sokesa da ita ya rufeta jikin bango yana kasa hadiye wutar datake cinsa ya bude baki Yana saka idanuwansa cikin nata da wani irin azababbiyar sautin ciwon dake cin kirjinsa yace

"Zan mutu,
Zan mutu ne sbd abinda nakeji zuciyana bazata iya dauka ba,
Bansan yaya zan iya controlling abinda nakeji ba,
Kin Sani Ni mara cikakkiyar lafiyan kwakwalwan da zata iya daukan jin sunan wani a bakinki ko jin sunaki a bakin wani,
Zan qarasa zarewa zan qarasa zama wanda zaki tsana ne bayan kuma komai girman tsanan da zakimun bazan taba barinki ba koda hakan na nufin bayyanarwa duniya haukana ne.....

Kansa ya cusa a cikin wuyanta Yana rintse idanuwansa dake masa radadi suma Yana jin kaman ya kurma ihu ya qanqameta jikinsa saita shige cikinsa kowa ya dena ganinta bare jinta sai shi..

Kansa ya daka ya sake dakawa Yana dagowa ya zubawa fuskanta datai straight tana jiran ya fara dawowa daidai ta fice sbd a yanzu gap yake da juyewan dayake magana...

Ganin taqi kallansa idanuwanta na qasa tana jiran motsin dazai bata damar raba jikinta da nasa ya sakasa karantar yanayinta da babu abinda yake cikinsa sai tsanarsa dayake hangowa take ya kasa riqe Kansa....

Saukan bakinsa taji akan bra dinta da hoqoransa ya fizgeta Yana wurgi da ita Yana bude jajayen idanuwansa cikin slow zuwa ga fuskanta data kallesa cikin tsananin tsoro da faduwan gaba ba shiri tayi saurin mannuwa da kirjinsa tana rintse idanuwanta da suka ciko da hawaye masu tsananin zafi tana hanasa ganin kirjinta daya bayyana...

Saukan tsinin kirjinta a nasa kirjin da babu kaya a ba zato take ya dakatar da duk wata hanyar wucewan ruwan jiki da jini dake yawo a jikinsa ya dafe bango da hannunsa daya cikin wani irin yanayi sbd loosing balance dinsa da yayi na jin abinda bai taba ji ba gabaki daya gashin jikinsa na miqewa ya rintse idanuwansa ya budesu jajir akanta.....

Wani irin numfashin daya maqale masa ya fizgo da karfi tareda daukanta gabaki dayanta ya nufi gaban mirror da ita ya zaunar kafin tayi wani yunquri ya saka bakinsa ahankali ya laso fatar kunnenta Yana sauke mata wani irin fitinannen numfashi me tsananin dumin daya sakata fasa kuka tana rufe kirjinta da hannuwanta biyu,

Hannuwan ya janye tareda shigar da kirjinsa ya rufe mata su da kirjinsa Yana mannesu da dan karfin daya sakasa sauke numfashi me karfin gaske Yana buga miron da karfin daya watse take a gurin.

Fuskanta ya dago jajayen idanuwansa Na rufewa ya sake saka harshensa ahankali ya lashi wuyanta Yana jin zuciyarsa na samun nutsuwan dayake rasasawa akanta,

Gangaro da karshensa yayi ya lashi gefen fuskanta kafin ya lasa lips dinta ya hadiye wani numfashi me shegen karfi kafin ya zira harshensa ahankali cikin bakinta da take ta gartsawa harshensa cizon da saida ya fasa.

Lumshe idanuwansa yayi Yana shanye radadin kafin ya bude idonsa akanta Yana sake jin tsananin sonta na neman illata rayuwarsa gabaki daya,

Raba kirjinsa yayi da nata tareda yin baya da wuyanta ya saka harshensa tareda saukar da bakinsa kai tsaye kan kirjinta Yana qanqameta kaman zai rabata biyu Kansa na juyewa.

Azabar riqon da yayi mata da zazzafan yanayin datake ji na irin yanda yake lasanta ya sakata qanqame Kansa tana son dagosa Amma Sam yama tashi daga AZIZ LIMBA dinsa dan haka jikinta ya fara rawa tafara kokarin Kiran sunansa Wanda bakinta ne dayake setin kunnensa sautin muryanta dake shigarsa kai tsaye da kukanta ya sakasa jin gabaki daya gashin jikinsa na sake miqewa ya dago kansa tareda kama kanta ya hade bakinsa da nata cikin wani irin tsananin mahaukacin so da shaukinta Yana kamo harshenta cikin wani irin fitinannen yanayi yake tsotsanta Yana zuqo duk wani albarkatun bakinta Yana jin kansa na kuncewa.

Kissing dinta yakeyi Yana sake qanqameta jikinsa kaman zai ballata yana sake jin kirjinta dake manne da nasa suna neman dakatar d bugawan zuciyarsa....

Daukanta yayi cak zai nufi lafiyayyen gadon dake dakin da ita ta fasa kuka me karfin gaske tareda bude baki cikin tsananin kukan daya taho mata tace

"AZIZ LIMBA na roqeka kada ka keta mun haddina,
Na rokoka kada kamun dole,
Karka manta kayi alkawarin bazaka taba mun dole ba dan haka ka Sani komai da kakemun dole ne kakemun kada ka karbi haqqin da ba naka........"

Cak ya dakata tareda tsayawa yana bude idanuwansa da take suka qara sauyawa...

Ajiyeta yayi a gadon tareda juyawa kai tsaye batareda ya sake kallantaba ya wuce bathroom ya shige...

Yana shiga da towel din a jikinsa ya sakarwa kansa ruwa Yana riqe kansa dan hannuwansa biyu yana hana kansa shiga mummunan yanayinsa sedai idanuwansa sun nasa riqe tsananin dacin zuciyarsa wasu irin hawayen da baisansu bama suka cika jajayen idanuwansa suna biyo ruwa suna gangarowa.

Itama cikin hawayen ta dafe kanta tana rufe idanuwanta kuka na zuwar mata ta rufe bakinta tana fasa kukan mara sauti tana zamewa qasa tana dafe jirjinta dake mata radadin halinda take jin zuciyarta.

Ta jima a hakan kafin ta miqe tana share hawayenta batada zabin daya wuce daukan doguwar jallabiyansa datai mata yawa sosai ta zira tareda daukan hularta ta saka ta dauki takardunta ta fito daga dakin gabanta na faduwan kada Allah ya hadata da kowa Musamman daya daga cikin familynta Musamman Ammar.

Harta sauko ta fice zuwa kitchen babu kowa dan haka tana shigowa kitchen din Fatma ce ta fara ganinta ta kalleta cikeda mamaki me tsananin da fargaba tana kallan kayan jikinta da fuskanta datai ja.

Amina ma cikin mamaki ta juyo ta kalleta kafin ta saukan da idanuwanta akan rigar tin daga sama har qasa zatai magana Jannah din ta juya musu baya tana dan kare kirjinta da hannuwanta biyu sbd ganin suna kallan kirjinta dake nuni da babu bra a jikinta.

Kokarin basarwa tayi ta hnyar cewa

"Fatma ina hijab dinki"

Fatma da itama take son subar kitchen din sbd kallan da Amina keyi wa jannah din da kuma yanda fuskanta ta nuna tayi kuka da sauri taje ta dauko hijab din ta kawo mata tana tayata sakawa.

Tana gama saka hijab din Madam Sisi na shigowa kitchen din ta kalli kowannensu taga sunyi tsuru tsuru banda Jannah din data qi barin ma Sisin taga fuskanta ta juya tana kokarin ficewa.

Binta da kallo Madam Sisi tayi tana qureta da kallo kafin idonta suka sauka akan rigar jikinta da sosai tayi maya yawa hakama idan idanuwanta sun fada mata daidai kaman yau da safe rigar ce a jikin me gidan.

Zaro idanuwa tayi da sauri cikin karfi tana bin bayan Jannah din tana sake qafewa rigar ido gabanta na faduwa tinani kala kala na shigarta dan haka ta juya tana tinanin yanda zataiwa Nicky bayani idan ta farfado.

Jannah na isa dakinsa Allah ya taimaketa harta isa bata hadu da kowaba,
Tana shiga dakin Fatma na shigowa dan haka Fatma ta sakawa kofar key tana isowa gurin Jannah din wadda ta dago idanuwanta da suka sake ja suna cikowa da hawayen data kasa barin su sauko tana kokarin danne abinda takeji amma kuma zuciyarta ta kasa tana neman wanda zata fadawa dan ta samu sassauci Amma bazata iya fadawa familynta ba sbd zata wargaza dukkanin karfin gwiwansu da suka samu da power da suke tinanin sunada ita akan yarsu,
Zata sakasu dawowa a cikin quncin da matsin da suke tinanin sun fito na AZIZ LIMBA,
Ammar kuma zarewa zeyi zaima iya rasa kansa kwata kwata idan yaji hakan dan haka bazata taba iya fada musu ba zata yaqesa da kanta har sai sakin da suke fatan itada familynta ya tabbata,to Amma ta yaya???
Tayaya zata iya hakan???

Fatma ta dago ta kalla ta sunkuyar da kanta tana sake sabbin hawaye masu zafi ta bude baki cikin kuka tace

"Fatma bai sakeni ba,
Ba takardan saki bace nake dako duk tsawon shekarun nan,
Da aurensa akaina nake yawo duk lokacin nan,
Me yasa Yamun hakan?
Me yasa ya dawo dan ya sake wargaza mana rayuwa?
Tayaya zan iya cewa su Dad babu sakin da muka zuba shekara biyu muna farin cikin samu?
Tayaya Ammar zaiji da auren AZIZ LIMBA haryanzu akaina a daidai lokacinda yake sakaran aurena dashi?
Tayaya zan saka AZIZ LIMBA din ya datse mun wannan auren nasa dayake kaina?
Fatma bansan ya zanyi ba zuciyata ciwo takeyi."

Fatma da duk itama ta rikice cikin tsananin tsoro da fargaba tace

"AZIZ LIMBA me wannan gidan da naji Garba yace?
Shine mijinki?
Innalillahi ya zamiyu yanzu to?

Kasa cewa komai Jannah tayi sbd bata ko iya magana sarawa kanta yake tsananin yi,

Fatma kuwa tsoro ma taji ita duk ya kamata Amma kuma dole ta Sani Jannah ta shiga mummunan tashin hankali sbd bataga alaman sakin zai yiyuba anan gidan sbd me gidan kansa abin shakka ne dan ita ko iya dagowa batai ta kallesa sosai ba sbd tsoro da shakka.

Rarrashin Jannah din Tai duk da batasan me zatace mata akan lamarin ba dan haka dai ta rarrasheta akan ta cire damuwan komai tukuna dan sai ancire damuwa zaa samu nutsuwa da tinanin fuskantar matsala.

Wanka dole jannah din ta sake yi sbd jikinta da duk yake mata nauyi ta saka wasu kayan tayi sallah kafin ta fita ta tafi gurinsu Dad inda Ammar an samu ya dawo daidai dan haka Sayd ya saka aka barsa baa tafi dashi din ba.

Babu me wani abin fada a tsakaninsu sbd tinanin da yayiwa kowa yawa dan haka abincin rana ma sama sama sukaci kafin suka gama kowa ya koma bakin aikinsa.
#MAMUH
#JANNAH ZAD
#AZIZ LIMBA
#NW LIMB

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 29

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
https://chat.whatsapp.com/IexiuY21PP75lt4yoJtNsK
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

*******************
Sai datai laasar ta isa kitchen aikin abincin dare,

Ko data isa a natsenta ta isa kaman babu abinda ya faru sbd ta sakawa ranta kaman yanda ta yafe AZIZ LIMBA a bayan ko a yanzu tana kan bakanta da aurensa da babu aurensa ya riga ya fita a ranta dan haka batajin a yanzun ma zata sauya hakan,

A masu aikinsu zasu ci gama da zama bata buqtaan kowane irin matsayin daya wuce hakan har sai Allah yasa sun samu damar sanin inda Saleem yake sun tattara sun bar mansion din.

Su Fatma ma sunyi nisa a aikin dan haka ta saka hannu suna qarasawa.

Mama kuwa sai yamma lis Allah ya saka ta farfado da zazzabi me dan karfi a jikinta,

Su Falaq ma ganin ta farfado sai suka samu nutsuwa sbd har yamman babu Wanda yaga saukowa ko fitowan Daddynta.

Sai dare karfe 8 na tukuna ya fito sanyeda doguwar jallabiya navy blue fuskansa tayi laushi sosai hakama fuskan a kame babu sakewa ko kadan.

Abinci dukkaninsu suka zauna dinning ci bayan kowa ya zauna ya dago a natse ya kalli fiddausi dake kokarin fara serving nasu ya bude baki a kame yace

"Ina Mama"

Shiru sukai dukkaninsu kafin fiddausin ta bude baki cikin girmamawa da jin nauyin fada zatai magana Sayd ya karbe zancen da cewa

"Mama ta samu tsautsayi dazu a stairs Amma likita ya dubata kuma tama dawo daidai tana hutawa ne sbd dan sauran zazzabi ma ciwon jiki sai zuwa gobe ko zata iya saukowa.

Ajiye spoon din hannunsa yayi ahankali Yana kallan Sayd din yace

"Mama ta hadu tsautsayi haka me yasa baa fadamun ba?
Akwai wani dalilin qin fadamun ne?

Shiru dukkaninsu sukai sbd ganin yanda ransa ya baci da yanda kuma bacin ran da fushi yake a bayyane.

Sake maimaita tambayarsa yayi cikin fada wadda ta saka Sayd cewa

"Baka kusa ne shiy.....

"Unbelievable" ya fada yana katse Sayd din tareda miqewa Yabar dining din falaq ta bisa da kallo cikeda mamakin ganin fushin daddynta da duk abinda zakai masa baka iya ganin fushinsa a bayyane.

Sayd kuwa daya San ba qaramin abu ke fidda fsuhin AZIZ dinba dan haka maganar Mama bata kai sakasa wannan mummunan bacin ran d fushin ba.

Mama data fito daga dakinta cikin dauriya da dannewa sbd batason ciwon yayi nauyin da AZIZ zai nema bin dalilin yawan rauninta a kwanakin dan haka ta lallabo ta fito sbd cin abinci a cikinsu ko yayane sai gashi tana kawowa kunnuwanta suka jiyar mata fadansa da tashin muryansa data sake tabbatarda matsayinta a gurinsa Yama wuce yanda take tinanin yayi sanyi sbd Soyayyar Jannah dan haka kai tsaye ta juya tana jin sanyi na mamaye ranta,

Idan har ransa zai mummunan baci hakan to tabbas ita babu ma abinda take buqata a yanzu bayan ganin ta rabasa da Jannah sbd idan ta rabasa da itane zai nesanta da Zaadens su qara tsanar junan da zasu zabi nesa nesa da juna su bace a rayuwarsu da Fatima gbaki daya,

Abinda ta tabbatar a yanzu shine idan bata nesanta kanta da Fatima ba Fatima zata iya ajalinta sbd idan ta sake mata irin wannan dukan zata iya rasa ranta ko wani sashen na jikinta dan haka idan har bazata iya korar zaadens su tafi su fita rayuwarsu da Fatiman ba sbd AZIZ ya saka dokar babu me barin 4&4 sedai izininsa to tabbas shi datake da cikakken iko dashi zata sake tabbatar masa da bata yafe ya sake ko kallan Jannah ba bare Zaadens,

A baya ta fada masa baya yadda ko yafe ya sake ambatar ko sunan Jannah da bakinsa ba Wanda kuma ta tabbatarda hakan dan kuwa har yau bakinsa bai taba sake furta sunan Jannah ba.

Idan duk yanda taso ta kasa yiyuwa zata juya danta da shine takeda cikakken ikonsa.

Ko daya iso saman kai tsaye dakinta ya nufa tareda miqa hannu yayi knockin a natse kafin ya bada seconds tukuna ya bude dakin bakinsa dauke da sallama.

Zaune take Maman a bakin gado ta dago tana kallansa da yanayi na sanyi da rashin cikakkiyar lafiya.

Qarasowa yayi ya zauna a sofa Yana dagowa cikin nutsuwa shima ba wata sakewa har lokacin a fuskansa yanayinsa na fushin da zuciyarsa take ciki a dan bayyane dan itama maman kai tsaye tana kallansa ta gano hakan zuciyarta ta sake cikewa da jin dadin ganin damuwa da bacin ransa akan ciwonta.

Gaidata yayi cikin kulawa ya Dora da cewa

"Yaya jikin?
Ko zaa sake Kiran likita ya dubaki ne?
Kokuma Mama zaa gyara Miki sabon daki ne a qasa ki koma sbd stairs dinnan kaman sun fara damunki"

Girgiza kai tayi tana bude baki tace

"Aa ba buqatan hakan tsautsayi ne kawai da zuwan lamari"

"Allah ya tsare gaba Mama"

"Amin" tace tana gyara zama ta kallesa kai tsaye tace

"AZIZ a yanzu da Zaadens suke gida daya a tareda mu duk da a karkashinmu suke kuma suna matsayin masu aikinmu ne inason sake tinatar dakai alkawarin dayake Kanka akansu,
AZIZ Ni mahaifiyarka ina Nan kan bakana ban yadda ba ban aminta ba idan har da gaske nice uwa a gareka ka kulasu ko basu wata kulawa ko sabuwar fuskar data wuce matsayinsu na masu aiki da suke dashi,

Ban Aminta da kowace irin muamala a tsakaninka dasu ba hakama ban Aminta ko inda Jannah take ka sake kalla ba idan ba hakan ba kuwa sedai ka zaba ko su ko ni nabar gidan nakoma kauye,

Zabi Yana gurinka a tsakanin mahaifiyarka da kuma Wanda suka kashe kanwarka suka raya tasu Yar"

Tinda ta fara magana bai dagoba ya kalleta sai datakai karshe ya dago idanuwansa ya kalleta,

Magana yaso yi akan cikakken aurensa dayake kan Jannah din da tin daga ranar data sakasa alkawarin rashin sake ambatar sunanta bai sake ambatar sunan ba Sedai 4&4 daya saka mata wanda bayan Sayd babu Wanda yasan maanarsa,

Wani abu me nauyi da zafi ya hadiye a moqoshinsa zuwa kirjinsa kafin ya hadiye maganar ya fasa fada sbd auren dai ba mutuwa zeyiba koda hakan na nufin rasa rayuwarsa ne bazai iya bawa kowa 4&4 ba koda mahaifinta daya haifeta ne kuwa hakama shi kansa idan har kowa na tinanin aurensa da ita ya qare tintini baya buqtaan fadawa kowa da bakinsa lokaci duka zai bayyanarwa da kowa kaman yanda ya zabi ya bata lokaci ta sauko daga fushinta ita kanta Jannah din sbd a yanzu iya tsanarsa ce kawai yake gani a tattare da ita wadda hakan ze iya kashesa daga tsaye.

Miqewa yayi ya fice daga dakin Maman tabisa da kallo tana sauke ajiyan zuciya sbd ta hakan dai tasan zai bawa Zaadens baya koma kila ya bari a basu damar tafiyarsu ta yanda komai zai tafi mata a daidai,

Koda basu tafi a kusa ba tasan dai yanzu zai dauke idanuwansa kwata kwata daga Zaadens ita kuma zata saka Sisi tsananta tsoron hana Fatima fitowa koina duk rintsi kafin ta samu hanyar fiddasu daga gidan.

Yana saukowa kai tsaye fita yayi bayan ya bada umarnin a gyara samansa.

Mota ya dauka ya fice daga gidan gabaki daya.

Fiddausi ce tahau saman da kanta taga aikin sosai ne sbd glasses koina dan haka ta kira Fatma sbd Jannah a gurinsu har abada ta wuce zama Yar aiki.

A gurin gyaran Fatma ce idanuwanta suka fara sauka akan bra din Jannah dake yashe a tsakiyar dakin ta dago a sace zata kalli fiddausi wadda itama ta gani tin dazu ta kasa cewa komai.

Cikin sanyi Fatma ta dauke bra din ta dauke hadda rigar suka qarasa gyra koina suka fito.

Fatma na wucewa itama fiddausi sama ta nufa tana Kiran Sayd ta sanar dashi ba mirror na dresser da Ctable na dakin AZIZ din sbd a kawo wasu gobe.

Fatma na zuwa da kayan hannunta dakinsu takai batareda ta bari su Dad da kowa dake zaune ana dan fira b sun gani tukuna ta dawo ta zauna cikinsu ana yi da ita.

*******Washe gari a gidan kowa fes ya tashi da sabon kudirin daya daukanwa Kansa,

ZAADENs dai suna Nan akan bakansu babu har abada abinda zai sake hadasu da LIMBA,

Hakama maganar auren Jannah da Ammar ba fashi Dad ya fada ya tabbatar hakama Maheer dan haka Ammar ya samu karfin gwiwan gaske Musamman ganin Jannah din kanta shi take so shi ta zaba,

Ita kanta Jannah batajin akwai sauyi a kudirinta na rabuwa da aurensa batareda ma kowa yasan akwai auren ba hakama babu sauran muamala a tsakaninta dashi bayan ta matsayinsa na Boss a gareta da familynta.

A bangaren fatma ma tayi shiru babu alaman tasan komai ma sbd kada su Dad su gano kaman yanda Jannah tace batason kowa ya Sani dan haka zata tayata boye dukkanin sirrin dayake tsakaninta da AZIZ.

****AZIZ LIMBA da kansa ma ya daukewa kowa dayake gidan sbd gabaki daya Yama dena zama ya saka kansa zama busy sosai,

Kwata kwata ya dena saukowa dining sbd da safe yake fita da dare yake dawowa.

Hakan yayiwa Mama daidai yanda takeso dan haka ta warke ta saki jikinta tana komawa huldodinta da Nicky wadda itama sai datai kwana biyu kafin ta dawo cikakken hayyacinta.

Ticket da komai na komawa AZIZ yayi mata ta tashi zarewa saida Mama ta dakatar da tafiyar tareda sake tada maganar aurensa da Nicky din.

Duk lokacinda ya bawa Jannah na rage fushinta bai alaman hakan zai yiyuwa bayan a nasa bangaren a cikin azaba yake rayuwa a yanzu,

Rashin ganinta kadai ya saka lafiyansa na neman gagaransa hakama a tsakaninsa dasu Dzad kwata kwata babu wata fuska ko alaman akwai sassaucin gaba da tsanar da suke ciki sbd ko kallansa basa kaunar yi kaman yanda shima haryanxu ya kasa jinsu ko kadan a zuciyarsa,

Jannah kawai yake son,ita kadai yake buqata,itace lafiya da warakar da kawai yake nema a wannan rayuwar tasa da rashin Ummansa da Ummitah suka birkitata.

Nicky wadda yau ta fita tareda Ammar wanda ta sakar masa fuska Amma shi bai sauya daga yanda yake ba ba sakewa a tsakaninsu..

Sai yamma sosai suka dawo gida har ta fice motar ta dawo ta bude jakar hannunta ta miqa masa robar Soft drink na pineapple tace

"Ina fatan abinda duk ya faru ya wuce"

Gyada kai kawai yayi batareda ya kalleta ba ya karba ya wucewansa.

Yana gap da isa dakinsu ya hadu da fatma ya jefa mata Yana cewa

"Ki bawa wani Ni bana Sha"

Cikin dariya fatma tace

"Nagode ya Ammar"

Kitchen zata dan haka ta shiga daki ta ajiye ta fice zuwa kitchen.

Jannah dake toilet tana fitowa daga wanka ummah na shigowa dakin ta zauna tana cewa

"Ruwa zansha"

Cikin kulawa Jannah tace

"Ummah ba ruwa a dakin Nan amma bara na shirya naje na dauko Miki kinji Umman Jan"

Girgiza kai Umman tayi idanuwanta n sauka kan soft drink din ta miqa hannu ta dauka tareda bawa Jannah tace ta bude mata.

Turaren hannunta Jannah ta ajiye tana karba ta bude mata tana cewa

"Fatma ta ajiyesa kisha idan naje kitchen na dauko mata wani"

Budewa tayi ta bawa Umman ta karba ahankali takai bakinta Tasha ta sake Sha taji bai mata dadiba dan haka ta miqawa Jannah din tana cewa

"Na koshi bana Sha"

Karba Jannah tayi cikin sauri ta qasara shanyewa ta ajiye robar tana saka hijab kan kayanta ta fice sbd aikin data bari kitchen.

Nicky wani irin farin ciki da nutsuwa ta samu tana jin ayau matsalarta data Mama zata kau sbd matiqar Ammar yasha abinda ta basa ayau bazai kwana ba saiya haiqewa Jannah wanda ko bai haiqewa Jannah ba to zata yanda zatai ta tura Falaq can ya haiqe mata ta yanda AZIZ zai tsani Zaadens tsana mafi muni idanma bai illatasu gabaki dayansu ba.

Kallan mama tayi bayan ta gama jero mata bayanin komai ta miqe tana fatan Ya haiqewa Falaq sbd itace AZIZ LIMBA zaifi haukacewa akanta,

Ita kuwa Mama ajiyan zuciya ta sauke tana jin kome zaiwa Jannah tinda daman aurenta zaiyi da saukobatareda tasan menene a zuciyar Nicky akan Falaq ba,
Hakama kodai baiwa kowa komaiba yayi attempting ta yanda AZIZ zai Koresu dan itadai fatarta kawai a koresun koma menene laifin.

Wannan ne kadai zai faru a gidan AZIZ ya tsani Jannah ya Koresu su huta duka da wannan masifar da basusan ranar qarewanta ba.

*****Karfe 7 suka gama ayyukansu suka bar kitchen din,

Zazzbi Jannah taji tanaji me karfi sbd koin jikinta dake zafi dan haka bata iya zama cikin su Maheer ba daki ta wuce ta sakarwa jikinta ruwa sbd jin abin na neman fin karfinta.

Ummah ma wani irin zafi jikinta yayi Wanda ya saka Dad tinanin batada lafiya ga zufa tanata yi sai fita yake mata.
#MAMUH
#LIMZAD
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 30

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
https://chat.whatsapp.com/IexiuY21PP75lt4yoJtNsK
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

*****************
Yanayin Ummah da kaman zazzabita ke qara qarfi da Jannah daman da bata samu fitowa ba ya saka kowa ya watse suka shige da wuri daman kowa a gajiye yake.

Fatma ko data shigo daki karfe 9 ta dan wuce Amma har lokacin Jannah bata saka kaya ba duk sanyin dakin na ac zufa takeyi tana zaune ta qanqame jikinta.

Qarasowa Fatma tayi tana kallanta cikin mamaki tace

"Jannah kina lafiya kuwa?

Kasa dago jajayen idanuwanta da suka shige ciki sosai tayi ta kalli Fatman ta dauke kafafunta daga qasa tana hawowa gadonta dasu ta girgiza kai ahankali alaman batada lafiya batareda ta iya bude baki ba.

Sake kallanta Fatma tayi da kyau taga kwata kwata bata cikin yanayi me kyau hakama zufanta sai qaruwa yakeyi.

Abin fita Fatma ta juya ta dauko tareda dawowa ta zauna kusa da ita tafara mata fita tana saka abu me kyau tana share mata zufan dayake ya sake jiqata.

Bude ido Jannah tayi tareda kallan Fatma idanuwanta na cikowa da hawaye da sanyin murya tace

"Fatma kaman jinina Yana konewa nakeji,
Kaman zan mutu nakeji?
Bansan meya sameni ba hadda marana Yana ciwo...." Hawayen idonta ne suka gangaro tana rintse idanuwan tana kwantawa jikin na dan fara rawa.

Damuwa da tsoro Fatma ta dan shiga ta kalleta tace

"Jannah ko naje na fadawa Su Dad ko Maheer ne ko zaa kaiki asibiti ne?

Girgiza kai tayi tana tashi zaune ta ziro kafafunta qasa tana saukowa daga gadon ta nufi toilet ta sake saukarwa kanta ruwa sbd anan ne take samun dan sassauci.

Bakin toilet din Fatma ta tsaya har Jannah din ta fito suka sake komawa bakin gado zuwa lokacin Jannah ta fara maye ta jiqo har dogon gashinta dayake a kunce Wanda a ranar Fatma ta wanke mata shi zasuyi kitso bata samu anyi ba sai gobe Fatman tai mata.

Gabaki daya jikinta ta jiqasa ta fito tana tafiya ahankali idanuwanta sunyi wani laushi sosai cikin mayen data fara tace

"Fatma ruwa"

Ruwa Fatma ta tashi da sauri ta dauko mata ta bude mata ta bata a baki tana goge mata ruwan dake gangarowa daga gashinta suna sauka jikinta.

Tin lamarin na kadan kadan har dare ya qara tafiya Fatma na fama da ita zuwa lokacin gabaki daya hankalinta ya gama tashi ta shiga tsoro sosai kada wani abin ya faru kafin safe ta rasa me zata fadawa su Dad.

A daidai wannan lokacin Dad na can na yana fama da Ummah itama a cikin irin wannan halin sbd nata daya hada da rashin lafiyan kwakwalwa sai itama lamarin yayi nauyi sosai.

Yanayin yanda take zufa da dafe mararta tana cewa "Dad ciwo sosai anan" ya saka yafara tinanin mara take nufi,

To meya hadata da ciwon mara shine ya fara tinani kafin ya sake kaita toilet ya zare mata doguwar rigarta yabarta daga ita sai farar vest qal dake jikinta me dan tsayi ya kunna mata shower Yana goge mata ruwan dake sauka kan fuskanta sbd kada ta shaqa ruwa.

Daga shi har ita duka sun jiqe sbd ta kasa tsayawa murkusus takeyi sosai tana cukuikuyesa karshe ma kuka ta saka masa wanda ya rasa ya zaiyi sbd damuwa da tsananin tausayinta ya rungumeta Yana dawo da ita daki aka cire jikakkun kayanta ya saka mata wasu kayan marasa nauyi na bacci sedai gabaki daya ta qarasa rikice masa dan haka ya kwantar da ita jikinsa Yana mata addua yanajin tana cakudasa cikin wani irin mayen dayake rufeta koinanta.

Rintse idanuwansa yayi ahankali yanajin wani irin yanayin datake kokarin tayar masa wanda ya dade da dannewa riqewa sbd tinda ya aureta bai taba mata komaiba sbd Yana fatan ta samu cikakkiyar lafiya ta amshesa a matsayin mijinta a hankalinta Amma ayau kaman hakan bazai yiyuwaba sbd ita kanta kaman ciwon dayake neman illata kenan a cikin Daren.

****Fatma ganin masifar dake neman fin karfinta cikin karfin hali ta kama Jannah din ta saka mata qaramar rigar shan iska da hijab suka fito tana dan riqe da ita sbd su samu iskan waje ya daketa ko zata dena wannan zufan datake tayi.

Fitowa sukai lokacin karfe goma sha daya saura dan haka sunsan kowa ya shige.

Suna fitowa iska me dan karfi ya fara buga Jannah din wadda tafara jero ajiyan zuciya tana rufe idanuwanta.

Fili suka fita sosai inda iskan yafi kadawa Fatma na riqe da Jannah din har lokacin tana mata sannu.

Hasken mota ne ya sako kai harabar gate na biyun gidan wanda garba ne da bai shigeba sbd Sanin me gidan be dawoba yaje ya bude musu gate motar black Royce Royce ta sako kai cikeda wani irin rashin kukan dayake bayyanarda ba kudin qananun masu kudi ke siyanta ba.

Garba na rufe gate din ya juya ya nufi hanyar dakinsu ya shige batareda ya hango su Jannah din ba.

Fatma dake cikin tsananin damuwa ita kanta bata wani damu da waye ya dawo ba bare Jannah da batama ji ko ganin komai sbd ita kadai tasan masifa da balain take ciki.

Kashe motar Sayd yayi tareda dan juyowa ya kalli AZIZ Wanda ayau baida niyar kwana baiga Jannah dinba dan haka m wayar Falaq yake kokarin kira dan aikata neman Jannah din
Cikin sanyi da mamaki sayd Yana maida kallansa kansu Fatma yace

"Kaman 4&4 ce acan tareda dayan me aikin"

Dakatawa AZIZ din yayi daga Kiran dayake kokarin sakawa tareda dagowa ahankali ya sauke idanuwansa akan inda Sayd din ya fada.

Ba haske sosai a gurin Amma kallo daya yayiwa gurin ya ganta tsaye a jikin Fatman.

Kashe wayarsa yayi gabaki daya tareda ziro kafafunsa waje daga kofar da sayd harya fito ya bude masa.

Kai tsaye inda take ya nufa Yana dago hannunsa ya kalli time ya maida kallansa akanta Yana qarasowa.

Fatma da bata lura dashi ba sai dataji wani fitinanniyar qamshi na dosota ta juya tagansa yana qarasowa bata fa fuskansa ba saida ya iso gap dasu fuskansa ya bayyanar mata,

Mugun firgita tayi da ganinsa gabanta na mugun faduwa dan haka a rikice tayi baya tana sauke kanta qasa tana dabarcewa tareda manta halinda Jannah ke ciki a jikinta.

Janyewanta ya saka Jannah da bata iya tsayuwa se a jikinta din zamewa zata zube qasa.

Hannu daya ya saka ya tarota batareda ya bari ta kai qasa ba Yana kallan fuskanta da idanuwanta suke rufe tana sauke numfashi me tsananin rashin karfi.

A jikinsa ta zube Yana sake riqeta jikin nasa da kyau ya dauke idanuwansa akan fuskanta dake bayyanarda ba lafiya take ba kwata kwata ya kalli fatma wadda ta sake qasa da kanta sosai cikeda girmamawa.

Bude baki yayi a natse da kamewa yace

"Me yake faruwa?

Cikin kama kai Fatman ta bude baki tace

"Batada lafiya tin dazu kuma ta hana na fadawa su Dad"

Sayd daya iso lokacin kallo daya yayiwa Jannah din daga jikin AZIZ din ya dauke idanuwansa Yana dawo dasu kan fatma yace

"Tsawon awa nawa ne?

Shiru tayi sbd bazata iya Tina ko awa nawa bane.

Magana AZIZ ya bude baki zeyi Jannah ta dago kanta tareda sama da kanta zuwa cikin wuyansa ta shago qamshinsa taja cikin hancinta tareda bude idanuwanta da sukai jajir tana kallan bakinsa daya bude zeyi magana take taji wani irin maitarsu na cikata ta dago hannunta ahankali ta Dora akansu tai musu wata irin shafar data sakasa mutuwar tsaye yana kallanta da tsananin mamaki.

Sayd saurin sauke kansa yayi Yana dan ja da baya batareda ya dago ba.

Fatma ma rikicewa ta qarasa yi ta juya batareda ta Sani ba ta ringa jefa kafarta duk inda ta samu tabar gurin zuwa dakinsu.

Riqeta yayi da kyau ganin tana kokarin zubewa qasa ya kalleta da kyau yaga tana sake jiqewa da zufa.

Fuskanta ya Shafa ahankali Yana goge mata zufan fuskanta da handkerchief dinsa daya ciro daga aljihu ya bude baki cikin sauti mara hayaniya da tsananin kulawa yace

"Menene kikeji Yana damunki?

Girgiza kai tayi batareda tasan tayi ba kafin ta bude idanuwanta ta saukesu akan lips dinsa dake motsawa suna maganar da batajin komai jinta ya dauke..

Gangaro da idanuwanta tayi wuyansa dayake motsi ahankali Shima ta sake dago hannu ahankali ta shafi wuyansa tana yi sama ta sake shafan lips dinsa tareda hadiye wasu yawun da suka wuce maqoshinta ahankali tanajin taste din bakinsa a nata bakin...

Ganin tsayuwar ta gagara ya dauketa gabaki dayanta ya juya ya bar gurin da ita.

Sayd na ganin hakan ya wuce gaba da sauri ya bude masa kofar da zai wuce kai tsaye Yana isowa ya shige da ita tana sake cusa kanta cikin wuyansa tana janyo qamshinsa dake qara tsananta halin datake ciki.

Babu kowa a palon qasan sai fiddausi data sauko daukan ruwan daya qare a palon sama zata kai tana fitowa kitchen Yana sako kai palon da Jannah din dan haka itama da sauri ta dakata tareda komawa baya kitchen din tana sauke kai qasa.

Samansa ya wuce shikuma Sayd ya tsaya ya rufe koina kafin ya wuce nasa dakin.

Fiddausi data tabbatarda sun shige ta fito itama ta haye nasu saman tana isa a palo data bar Mama da Nicky suna fira cikin tsananin nishadi ta kalla cikeda mamakin Mama da bata kai wannan lokacin batai nisa a bacci ba.

Cikin mamaki tace

"Mama haryanxu biki bacci ba lokacin baccinki yanzu ya sauya lafiya ta qara samuwa yanda mukeso"

Duk da Maman na fushi da fiddausin har lokacin Amma tinda sun sama sakewansu kuma tana cikin farin ciki dan haka Murmushi tayi tana cewa

"Eh yau dai kam baccin ya tafi sai zuwa anjima kila kokuma dan nay baccin rana ne"

Itama fiddausin cikin murmushi da nata farin cikin tace

"Nima dai yau banajin baccin Nan bara na kai ruwan fridge Nazo na taya Mama da 'yarta fira mu raya Daren kila alkhairi ne a cikinsa"

Nicky da takejin kaman tayita ihun farin ciki cewa tayi

"Kwarai wannan Daren na alkhairi ne"

Mama dai murmushi kawai takeyi tana hadiye dadinta ita kadai.

Fiddausi na ajiye ruwan ta dawo ta zauna a cikinsu suka hau fira duk da hankalinsu na kan madam Sisi da suke jiran ihunta sbd Nicky ta tabbatar mata kada tayi bacci tayi gadin bangaren su Jannah tana ganin Ammar ko alaman namiji tayita kurma ihun da kowa seya fito.
#MAMUH
#BEST LOVE
#TOO HOT
#ROMANCE
#JANNAH ZAD LIMBA

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 31

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
https://chat.whatsapp.com/IexiuY21PP75lt4yoJtNsK
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

************
Dukkaninsu bacci ne yake zuwar musu me karfi Amma zuciyoyinsu sun kasa yadda da baccin dan haka suka qara nacewa Daren,

Fiddausi data gaji bazata iya ba ta miqe ta shige daki tabarsu Anan wanda ba jimawa dukkaninsu suma baccin ya daukesu a palon.

AZIZ kuwa Yana isa sama ajiyeta yayi a tsakiyar palonsa Yana kokarin zare mata hijab dinta sbd ya qara mata AC kafin ya samu daman Kiran Sayd ya kira mata likita Amma Sam ta kasa tsayawa,

Bayason ciro mata hijab din ta qasa yazo wuyanta ya bata matsalar nade mata fuska Tasha wuya bayan wadda yaga tana Sha zuciyarsa bazata dauka ba dan haka daga wuyanta ya yaga hijab din yana zame mata shi qasa yana sake kamo fuskanta ya amabaci sunanta cikin kulawa Amma bata amsaba sai binsa takeyi da wani mayen kallo da idanuwanta dake kashesa...

Gashinta dayake a jiqe ya kalla kafin ya gangaro da idanuwansa wuyanta yaga ruwa kaman na gashin kaman zufa ya dago idanuwan ya kalli fuskanta itama shi take kalla har lokacin tana sake shiga yanayinsa..

Daukanta ya sake yi ahankali ya isa kujera da ita zaunar yaje ya dauko qaramin towel me kyau ya dawo,

Rankwafowa yayi gabanta ahankali cikin nutsuwa Yana sake ambatar sunanta da wani natsatsen sauti yana kai towel din wuyanta ya shafo tareda kai hannunsa daya Yana janye mata gashin fuskanta...

Numfashinsa me dumin gaske ne ya sauka a fuskanta da wuyanta daya matso yana goge mata wuyan ta rufe ido ahankali tana jin gashin jikinta gabaki daya suna miqewa taja wani kasalallen numfashi...

Saukan lallausan tafin hannunsa akan fatar wuyanta yana gogawa ya sakata bude ido akansa tareda Jan wani sabon numfashin daya sakasa kallanta Yana karantar yanayinta Wanda kusan idan yana karanta daidai tana cikin tsananin desire ne Wanda yasan bata hankalinta dan idan tana ciki bazata taba nemansa ba sbd fushinta akansa,

Ina ta hadu da koma menene?
Waye ya bata? Sbd yasan har abada bazata taba shan koma menene a Karan kanta ba?

Kukan data fasa ahankali ne ya sakasa kallanta Yana bude baki zeyi magana ta rigasa cikin kuka da cewa

"I hate you AZIZ LIMBA" da qarasa maganar ta kamo gaban rigarsa tareda fizgosa da karfi ta kalli lips dinsa da suke kaman fresh ta kai bakinta akansu tana hadesu da nata tareda bude bakinta tana jefa harshenta a bakinsa tana masa wani irin lafiyayyan shan daya saka towel din hannunsa faduwa Yana jin duniyarsa data wargaje tana haduwa guri daya.

Kissing din data kewa bakinsa tana jin dukkanin zafin jikinta na ragewa Yana sauka ya saka kanta sake juyewa ta saka hannuwanta biyu ta zagayo wuyansa tana lumshe idanuwanta qamshinsa kawai yana sake kashe wutar dake ci a jikinta.

"Sorry 4&4" ya furta a hankali bakinsu na hade kafin ya saka hannuwansa biyu ya kamo qaramin qugunta yayo sama da ita Yana fara tsotsan bakinta cikin wata irin nutsuwa da tsananin sonta dayake cin jini da zuciyarsa kowace daqiqa.

Kan ctable ya zauna tareda bude kafufunta ya zaunar da ita akan kafafunsa suna fuskantar juna ya bude jajayen idanuwansa Yana bin fuskanta zuwa wuyanta da kallo Yana jin kaman ya hadiyeta da dukkaninta sbd abinda yake ji akanta.

Itama shi takewa wani irin kallo a cikin mayen dayake sake juyata....

Rigar dake jikinta mara nauyi ya tattaro ahankali Yana Shafa lafiyayyun cinyoyinta bakinsa yakai gefen kunnenta ya sakar mata numfashi me tareda zira harshensa ahankali ya laso fatar hannunsa na isa kan mararta da yayiwa wata irin shafa da tafin hannunsa taja numfashi me karfin gaske tana zagayo wuyansa da hannunta daya dayan kuma tana bin hannunsa cikin rigar ta dora akan nasa hannun tana jin kaman zata zare.

Cibiyarta ya Shafa ahankali Yana sake cusa kansa cikin wuyanta Yana sakar mata kiss masu sanyi da numfashin dayake sake saka jikinta daukan zafi.

Sama yafara yi da hannun Yana Dora bakinsa akan bakinta Yana tsotsa lips dinta da sukai jajir....

Saukan hannunsa a samanta ya saka su biyun numfashinsu daukewa a lokaci daya Yana sake matseta da karfi jikinsa..

Gashinta ya kama yayi baya dashi kanta na baya ya saka kansa cikin rigarta gabaki daya yana hadesu guri daya..

Bude idanuwanta ta basa ganin komai da komai bayan shi kadai da zuciyarta takewa so daya babu wani bayansa ta zagayosa da hannuwata tana son bude baki tayi magana Amma bata iyawa sbd abinda yake faruwa a cikin rigarta da kansa yake ciki...

Numfashin dayake fitowa daqyar take saki tana neman rasa kanta gabaki daya tana sake rungume Kansa cikin tsananin shauki da son daya taso mata gabaki daya a cikin yanayin.

Kansa na ciki ya saka hannu ya zare musu rigar wadda ta barta babu komai a jikinta sai black panties...

Hannuwanta ta saka ahankali gaban tsadaddiyar rigar dake jikinsa ta budeta gabaki daya lokaci daya botiran rigar suka zube qasa ya dago Yana mata wani mayen kallon dake bayyanarda wannan moments sune best moments na rayuwarsa sbd idanuwansa dake nuni da hakan tareda mamakin 4&4 dinsa dayake sake jinjina karfin abinda yake aiki akanta.

Wurgi tayi da rigar jikinsa shi kuma ya saka hannu ya mannota kirjinsa da nasa suka hadu ya lumshe ido Yana Jan wani fitinanniyar numfashi me karfin gaske ya budesu akanta ya bude baki daqyar yace

"4&4 banason da safe ki tsani kanki akan abinda yake faru.....

Bai qarasa ba ta saka bakinsa cikin nata tana sake mannuwa dashi.....

Miqewa yayi da ita a jikinsa qafafunta na zagaye dashi ya nufi bedroom dinsa da ita Yana zuqo yawun bakinta da ko iya su darajarsu tafi masa duk abinda ya mallaka yana.

A lafiyayyan gadonsa ya jefata ahankali Yana zare doguwar Sweatpnt din dake jikinsa Yana binta da wani mayen kallon dake sake juyar da kansa.

Bakinsa ya dora akan Mararta ya sakar mata wani irin zazzafan kiss tareda saka harshensa ya lashi cibiyarta ta qanqame pillow da karfi tana rasa numfashinta na Yan daqiqu...

Asalin lafiyayyar fatarta me laushi da tsafta ya saka harshensa Yana lasa Mararta zuwa cibiyarta ya qarasowa tsakiyar kirjinta inda da harshensa da numfashinsa a tare suka sauka ta bude baki zatai wani irin numfashin cetan Rai ya dago kanta Yana rufe bakinta da nasa yana hannunsa na bin kirjinta zuwa bayanta da wata irin shafar datake sake rabata da numfashinta Amma ya hana hakan sbd bakinsa dayake bata wata irin tsotsan da taste din bakinsu ya zama daya...

Yanayinsa fara fin karfinsa yayi yafara loosing control na kansa sbd yanda yake yake tsotsanta Yana bata zafafan romance Musamman kirjinta da sukai jajir dan haka zai iya kasa riqe kansa yayi abinda zata tsanesa idan ta dawo hankalinta shi kuma zuciyarsa da rayuwarsa bazasu iya daukan tsanar da zatai masa ba...

Juyar da ita ya ta kifu a gadon ya kwanta bayanta hannunsa daya na zagaye da kirjinta daya dake tafin hannunsa hannunsa daya kuma Yafara Shafa bayanta ahankali Yana sakar mata kiss me sanyi a bayan wuya da gefen fuskan Yana sakar mata numfashi me sanyi a cikin kunnenta idanuwansa a lumshe yana jin dumin jikinta na shiga jikinsa ahankali Yana sauka.

Numfashi suke saukewa ahankali dukkaninsu itama idanuwanta a lumshe tana samun relief da saukar abinda take ji yana quna a jininta,

Jikinsa dayake rawa na yanayinsa dayake cinsa ya sakasa sake rintse idanuwansa Yana jin wani irin yanayi a zuciyarsa da bazai iya rayuwa ba duk yanda zai samu gwarin gwiwa idan ya rasa 4&4,

Rashin Ummansa Ummitah ce ta zama qwarin gwiwa da fitilan data haska rayuwarsa harya cigaba da rayuwa,

Bayan rasa Ummitah Falaq ce ta zama jagorar data kawo rayuwarsa a yanzu,

Bazai iya rasa Jannah Zad ba sbd a duniya babu abinda zai iya hanasa fading idan babuta a rayuwarsa,

Lumshe idanuwansa yayi da sukai jajir ruwa masu tsananin dumin dake cikinsu suka gangaro suka sauka akan bayan wuyanta tareda gangarowa ahankali suka diga gaban idonta data bude jin saukan dumin ruwan..

Ahankali itama idanuwanta suka ciko da hawayen abinda take ji a zuciyarta akansa,

Gangarowa sukai gefen idonta suka sauka tanajin rawan da jikinsa keyi tana qaruwa sosai ahankali ahankali na tinanin dayake cin kwakwalwansa da zuciyarsa....

Tsananta yanayinsa keyi har Yana jijjigata ita da jikinsu yake hade.

Zamewa yayi Yana qanqame jikinsa ya sauka gadon Yana sake jijjiga ya nufi toilet idanuwansa na rufewa.

Yana shiga tin bai qarasa ba ya zube qasa yana riqe kirjinsa Yana kokarin miqewa ya isa ga shower...

Gudu hawayenta suka tsananta yi tana jin zuciyarta na bude dukkanin wani tsohon ciwo da raunin zuciyarta...

Bata gama dawowa daidai ba sbd abinda yake jikinta bai gama sakintaba
Kasawa tayi dan haka ta sauko gadon itama da qyar ta nufi toilet din tana shiga Yana durqushe cikin mummunan halinda ya kasata qarasawa da sauri ta zube gabansa tareda rungumesa gabaki dayansa a jikinta tana ambatar sunansa ahankali wanda sautinsa ma ya banbanta da yanda a yanzu take kiransa sbd wani irin tsananin so da kewan datake cikin wannan.

Hannu ta miqa ahankali ta kunna musu ruwan Yana sauka akansu ta kamo fuskansa da tafukan hannuwanta biyu ta kallesa cikeda yanayin da batasan yaya zatai da zuciyartaba ta bude baki tace

"AZIZ LIMBA I hate....."

"But I love you JANNAH ZAD." Ya fada daqyar cikin wani irin mummunan yanayi Yana katseta batareda takai karshen maganarta ba da zuciyarsa bazata iya dauka ba.

Rintse idanuwanta tayi tana kokarin zamewa ya riqeta tareda hanata zamewa ya kalli cikin tsakiyar idanuwanta yana saka bakinsa akan nata yana shigar harshensa ciki.

Qanqamesa tayi tana karbansa ahakan....

Fatarta dake bawa tasa nutsuwa ya sake janyowa cikin ruwan Yana cigaba da kissing ruwa na sauka akan fatarta dake saks santsi a tasa fatar Musamman yanda suke cakuda babu me riga a jikinsa.

A jikinta ya samu nutsuwarsa ta dawo zuwa lokacin zazzabi me karfi ya rufeta sbd maganin dayake kokarin sakinta da kuma ruwan data shiga sosai tsakanin fara ciwon.

Da kansa ya dauro mata towel suka fito ya rage ac din dakin tareda dauko rigarsa me dan kauri ya saka mata tareda bata ruwa mara sanyi Tasha ya kwantar da ita jikinta na rawa sosai sbd take jikin yayi karfi.

Kwantawa yayi gefenta ya rufesu tareda shigar da ita jikinsa sbd ta sake samun dumin datake buqata.

Shi kansa Kansa a nauyaye yake dan haka ba bata lokaci baccin ya daukesa.

Itace tafara farkawa da asuba taji sauki ba laifi dan haka ta miqe.

Tashi yayi shima Yana taba jikinta yaji da sauki ya kalleta zaiyi magana ta katsesa cikin rashin sakewa da rashin walwala tace

"Pls don't"

Fasa maganar yayi ya kalli toilet da ido ya nuna mata.

Saukowa tayi da dan sauri ma tayo alwala ta fito
Shima alwalan yayo sukai sallah.

Suna gamawa ta miqe ta nufi kofa da sauri gabanta na faduwan kada tsautsayi yasa wani yasan a inda ta kwana.

Hijabinta ta dauka a yagensa ta saka ta fito AZIZ din na biyeda ita tareda riqo hannunta a natse yace

"Ki nutsu baki gama warware ba and I need to talk to you akan abinda ya sameki"

Bata amsa ba take tafiya tana son qwace hannunta Amma Sam yaqi saki har suka isa kofar bangarensu bai damu da komai ba ya shigo daidai lokacinda Madam Sisi ta gama baccinta ta Tina da aikinta aka sakata Wanda bacci ya saceta sai yanzu.

Inuwar namiji da mace ta gani a daidai kofarsu Jannah din wanda ya sakata bude ido da karfi tana sake tabbatar da mace da namiji ne take gani kuma hannuwansu a riqe....

Fili ta fito yanda kowa zeji ta bude baki duk iya karfinta ta fasa ihun a kawo musu dauki kwarto.

Wata mummunan faduwa gaban Jannah yayi ta juya a rikice ta kalli kofar dakin Dad datasu Maheer da ake kokarin budewa cikin saurin jin ihun.

Kafin AZIZ din yayi kowane irin motsi ta kama hannunsa da karfi ta bude dakinsu ta turasa tareda shigewa tana rufewa daga ciki.

Tana rufewa Ammar da Maheer na fitowa cikin tsananin tashin hankali da makamansu a hannu.

Ammar dakin su Jannah din ya nufa Yana tare kofa,

Dad ma a rikicen ya fito yana saka jallabiya,

Su Mama ma cikin bacci suka firgita tareda miqewa tsaye suna rige rigen fitowa itada Nicky suna taya Sisin ihu.

Sayd ma dauke da pistol dinsa ya fito yana busawa securities whistle take gidan kowa ya miqe tsaye cikin tashin hankali da tsananin duhun asubar.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 32

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

*************
Ihun Nicky da Mama ne ya sake karade gidan suna nufo scene din,

Fiddausi ma da duk basu kai ga tashi sallar asuban ba cikin bacci taji ihun kwarton da neman agaji ta bude ido tana dirowa gado bata tsaya saka komai akan kayan baccin jikinta ba ta fito da gudu a firgice gabanta na tsananin faduwa da tsoro.

Dakin Falaq take kokarin nufa ta dubota hankalinta tashe saiga Falaq din itama ta fito a tsananin tsoroce jikinta na rawa idanuwanta na qanqancewa tana ganin fiddausin ta iso gurinta da gudu tana cewa

"Fi waye kwarto?
Meye hakan??

Fiddausi data samu ganin Falaq din a gabanta kalau numfashi ta ajiye ta fada maye ake nufi da hakan,

Da sauri falaq ta juya jikinta na tsananta rawa ta nufi stairs da tsananin gudu kaman zuciyarta zata fado sbd jin bangaren masu aiki ihun ke tsananta Wanda tasan Jannah dinta na can zuciyarta bama zata kwatanta wani abu ya taba Jannah ba,

Biyota fiddausi tayi da tsananin gudun kada taje ta hadu da kwarton tinda kila neman gudu yake daga gidan..

Su Mama na isa idanuwansu sun rufe basa gani sosai hakama bacci bai gama sakinsu ba gaba daya dan a cikin bacci kawai sukaji ihun take suka karba suna rige rigen fitowan dayake da abin suka kwana a Rai,

Duhun asubar da rashin hasken gurin sosai y saka basu gane waye da waye a tsaye a gurin ba dan haka Nicky ta fara ihun cewa

"Ku balla dakin ku fito da Ammar din,
A kira AZIZ,
Ina securities? Wayyo kwarto"

Madam Sisi kuwa har gurin hanyar bangaren AZIZ ta isa ta ringa ihun kwarton tana neman agaji.

Securities da Sayd dayake Daga pistol din hannunsa baya cikin flowers din gidan suka nufa d manyan haske Sayd na cewa

"Kuna ganinsa ko waye ku harbe kafarsa duka biyun a take Umarni ne"

Maheer da Garba dake dauke da manyan sandunan gora suma bayan dakunansu suka zagaya Dad na zagayawa bayan dakin su Jan da wuqar daya fiddo.

Ammar kuwa dakinsu Jannah ya tsare dan bada kariya dan yafison Yana ganin duk abinda zai shiga dakin ya sare wuyansa da karfen hannunsa,

Mama ganin gida ya rikice har lokacin Nicky da madam Sisi ihu sukeyi ba AZIZ bai fitoba ta nufi bangarensa da gudu tana sake goge idanuwanta da basu qarasa washewa ta riga kwala masa kira.

Daga waje ma sauran securities din sun zagaye gidan an basu umarnin duk wanda suke gani su harbesa a spot din.

Gabaki daya hankalin maqotansu sauran mansions da gidajen manya dake gurin tashi hankalinsu yayi sbd ihun d tashin hankalin yayi yawa hakama sai harba bindiga akeyi sama wadda ta saka securities na anguwa gabaki daya suma miqewa tsaye aka hau zagaye unguwa da shirin harbe duk Wanda aka gani shine kwarton.

Fatma da balain da masifar ya sakata tashi a firgice cikin baccin da bai dauketaba sbd gadin jiran dawowan Jannah sai asubar me nauyi ya dauketa.

Tana bude idanuwanta a rikice taga mutane tsaye tsakiyar dakin Jannah na qanqamesa da karfi idanuwanta cikeda hawaye tana rokonsa kada ya fita a lokacin shikuwa Kansa Yama kasa daukan uban waye yake ihun kwarto a cikin gidansa sannan ita ta sakasa daki ta boye?

Fatma datake a rikice da ihun su Madam Sisi kurma sabon ihun tayi sbd da duhu a dakin ba haske tana miqewa da tsananin gudun gaske itama ba Kayan arziki a jikinta ta banka kofa da gudun gaske ta fito tana taya su Nicky ihun.

Rintse idanuwansa d sukai ja sbd tsananin bacin rai yayi zai yi magana jannah tayi saurin saka hannunta dake rawa bakinsa tana rungumesa cikeda tsoro da kunyar da zata iya kasheta idan ya fita.

Nicky na ganin tsananin tashin hankali da firgicin da Fatma ke ciki bata tsaya wata wata ba ta nufi dakin ta fada tana tsananta ihunta sbd ta tabbata Ammar da Jannah suna ciki.

Tana sako kai cikin duhun dakin tana ihun AZIZ da yagama kai maqura a bacin ransa hannu ya daga ya zabga mata wani mahaukacin marin daya sakata zubewa baya tana fadowa Madam Sisi data biyota suka zube qasa take jikin madam Sisi ya dauki muguwar rawa cikin tsananin mugun tsoro ta ture Nicky da karfin gaske tana miqewa ta bar gurin da gudu tana cewa

"Wlh yana dakin,
Gashinan a ciki"

Mama n jiyo hakan ta dawo da gudu duk a rikice,
Su Maheer ma dasu Sayd zagayowa da gudu dukansu sukai gabaki daya gidan suka taru a kofar dakin,

Zaadens da sukasan zinariyarsu n ciki take suka qarasa haukacewa suna tinkarar dakin da karfin gaske.

Falaq dataji Jannah na ciki hakama kwarton kasa riqe kanta tayi da gudun da babu wanda ya ankara ta wuce kowa ta isa kofar dakin jikinta n Tsananin rawa ta tura kofar dakin daidai Jannah zata rufe dakin d key.

Da karfin gaske Falaq ta fada jikin Jannah din tana qanqameta jikinta na rawa har lokacin ta fasa kuka tana sake kankameta kaman zata shige jikinta.

Gari ya fara haske dan haka Sayd yayi saurin cewa kowa ya dakata da makaminsa sbd Falaq data tare kofar..

Kuka takeyi sosai tana sake qanqame Jannah,

Jannah dake rikice cikin tsananin tashin hankali kasa motsawa tayi tana kokarin janye Falaq din Falaq ta bude idanuwanta ahankali kaman a mafarki idonta ya sauka akan Daddynta dayake tsaye dukkanin bacin rai da fushinsa a fili amma ya kasa take rokon Jannah din ya fito yaci uban duk wani mahaukacin dayake gidansa.

Da tsananin mamaki me karfi ta saki Jannah ahankali tana kallansa kafin ta dawo da kallanta kan Jannah Wadda kunya ta sakata qasa da kai.

Juyowa Falaq tayi da sauri taga yanda kowa yayi cirko cirko tsuru tsuru suna jiran ta fadi abinda ta gani sbd sun tabbatarda duk abinda yake bayan Jannah cikin dakin ta gani.

Cikin ihu Fatma tace wlh naga mutum a cikin dakinmu,

Madam Sisi da tin dazu take zuba rantsuwar taga kwartaye da idonta karbe zancen tayi tana maimaitawa.

Nicky da tini jinta ya dauke sbd Marin datasha hakama ganinta rawa yake a hakan ta saka aka kawo mata wayarta ta kunna recording dn kofar dakin sbd tanason nunawa AZIZ lokacinda aka kamasu suna fitowa dakin.

Juyowa Falaq tayi ta sake tare kofar ita kuma Jannah ta sake kama hannunsa ta jasa bayan kofa tana sake riqe hannunsa cikin nata idanuwanta duk sunyi ja kuka takeson yi sbd abinda take ji na wannan mugun yanayin da suka samu kansu.

Falaq bude hannuwanta tayi ta sake tare kofar ta bude baki tana kallan Sayd tace

"Ba kowa a ciki Jan ce kadai"

Mama da duk ta haukace tace

"To ta fito mana me takeyi a dakin kowa ya fito dan wanke Kansa"

Sayd Falaq ta kafawa ido Wanda yake kokarin fahimtar me take son fda masa tace

"Papa ina Daddyna? Sai yazo zan matsa jikin kofar Nan"

Sayd na jin hakan ya kalli kofar dakin da sauri Ya juya ya kalli fiddausi wadda itama take ta shiga shock ta kallesa tana soke kai.

A rikice Sayd din ya fito yana cewa securities su koma bakin aikinsu,

Kallan kowa yayi zaiyi magana Ammar cikin tsananin zafi ya katsesa da cewa

"Karma hauka ta debeka kace mubar gurin Nan sbd wlh duk abinda yake dakin Matata saina shiga na dubosa idanma mutum ne ya Sani yau kwanansa ya qare,
Waye ya isa ya shigarmun gon...

Kaman saukan tsawar aradu suka ji wani mahaukacin ihun tsawarsa yana bayyana gabansu idanuwansa jajir kaman zasu kama da wuta ya bude baki gabaki daya gidan Yana daukan sautinsa yace

"Securities,ku bude motarku duk Wanda yayi ihun kwarto da duk Wanda ya dauki makami a cikin gidana ko waye da waye ku kwashesu gabaki daya ku kai office ku rufemun"

Jannah dake bayan kofa silalewa qasa tayi tana cusa kanta cikin kafafunta kuka me karfin gaske na zuwar mata.

Mama kuwa jiri ne ya debeta taji kaman rabin jikinta na neman shenyewa idanuwanta na kasa gasgata AZIZ da kansa a dakin masu aiki.

Nicky wayar hannunta ce ta kubuce daga hannunta ta fadi qasa hannuwanta na kakkarwa sbd kasa gasgata abinda idanuwanta suka ganar mata AZIZ LIMBA dinta bangaren masu aiki kuma a cikin daki.

Su Dad kuwa tsananin tashin hankali da shock din da suka shiga ya saka su kasa motsawa Banda Maheer daya Yar da makamin hannunsa Yana isa dakin da sauri ya shiga dan dubo Jannah.

Yana shiga ya isa gurinta da sauri Yana dagota ta rungumesa tana fasa kuka me karfi tana cewa

"Maheer babu abinda yazo yi ba girina yazo ba babu ruwana dashi ba abinda yake tsakanina dashi"

Ynada take maganar tana kuka sosai ya saka jikinsa sanyi hakama Dad da Ammar Wanda yayi mutuwar tsaye sanyi sukaji jikinsu yayi sbd sun tabbatarda Jannah bazata taba komawa AZIZ ba tagama dashi har abada hakama bazata taba musu karya akansaba.

Securities da sukafi kowa hauka akan umarnin uban gidansu da ayau suka tabbatarda a zafafe yake tini suka taho da mota doguwa a rife koina aka bude bayanta aka fara gargada kowa idonsu a rife basaji basa gani dan bama asalin securities na gidan bane bare kaga sauki ko damar nuna matsayinka.

Kowa makaminsa aka sakasa sake dauka aka dinga turasu mota hadda Sayd sbd kowa da kowa akace dan haka babu ruwansu ko Mama rufe ido sukai suka bude mata motar.

Madam Sisi da Fiddausi tace ita ta fara ihun talla mata mari daya daga cikinsu yay Yana cewa

"Zakaci uban bakinka"

Fiddausi da Falaq da Jannah se Amina kadai aka bari sai me gidan kansa da tinda ya bada umarnin yabar gurin Yana samansa kishin Jannah zai kashesa sbd zuciyarsa dake jin zai iya illata Ammar har abada akan kalmarsa ga matarsa.

Falaq ce ta dakatar dasu daga tafiyar sbd tasan kwata kwata daddynta baya hayyacinsa ya bada umarnin dan haka idan ya dawo hayyacinsa zai tsani kansa har abada akan hakan ace shine ya bada umarnin aka rufe hadda mahaifiyarsa da mahaifin jannarsa dan haka bazata bari ya dandani wannan dacin ba.

Samansa taje tayi tayi tagansa Amma shiru bama ya palon yana bedroom dinsa Wanda ta tabbatarda ba lafiya ba.

Tsoro ne ya kamata dan haka ta sauko da sauri taje gurin Jannah da batama San an tafi da kowama ta sanar mata.
#MAMUH
#LIMBAS
#ZAADENS
#4&4
#PSCHS

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 33

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

**************
Daqyar ta iya zuwa inda yake din sbd ita kanta tasan zai tsani kansa sosai daga baya idan ya gane abinda yayi sbd tsananin son dayake wa mahaifiyarsa da kuma yanda itama yasan tana tsananin son mahaifinta.

Numfashi ta ajiye tareda ajiyan zuciya ta miqa hannu akan kofar bedroom dinsa ta bude Falaq na komawa palon qasa dan jira.

Duhu ne a dakin dan haka ta isa gurin haske ta kunna ahankali tana juyo da idanuwanta ga dakin.

Kwance yake a tiles can bayan sofa ya qanqame jikinsa jikinsa na rawa sosai Yana yaqi da zuciyarsa dake illata tinaninsa,

Qarasawa tayi ahankali tareda durkusawa gefensa ahankali ta miqa hannuwanta duka biyun ta rugumosa tana kwantawa jikinsa ta lumshe idanuwanta hawayen cikinsu na sauka akan fatar wuyanta.

Qanqameta yayi kaman zai ballata ta rinse ido tana shanye azabar hakan sbd ta saba tin ba yanxu din ba sbd tasan lafiyansa sai ta koyi hadiyewa.

Qanqameta yake sakeyi da karfin da azabar take mata yawa Amma bata iya kwacewaba ko magana sbd tasan relief din dayake samu da hakan.

Shiru sukai a jikin juna tsawon minta ya samu sassaucin zuciya da jiki.

Ahankali ta bude baki tace

"Zasu tafi dasu Dad da Mama ka dakatar dasu pls"

Shiru yayi idanuwansa a rufe har lokacin,

Wayarsa ta tashi ta dauko masa tareda zaunawa ta kamo hannunsa ta saka masa a ciki tana kallansa cikeda tsananin abinda takeji a zuciya bakinta yana kasa furtawa.

Shiru tsawon lokaci kafin ya daga wayar Yana miqewa tsaye yabar gurin Yana nufar balcony dinsa ya tsaya.

Jannah ma miqewa tayi ta fice daga dakin ta sauko a sanyaye,

Falaq na ganinta ta taso tareda riqe hannunta tana kallanta kaman zata cinyeta sbd kauna tace

"Is my daddy ok?

Numfashi Jannah ta sauke ahankali tana dagowa ta zubawa Falaq din idanuwanta tsananin kaunar Falaq din na taso mata.

Falaq ma ganin hakan sake riqe hannun Jannah din tayi tana cewa

"My Jan,
My Dad's Jan"

Rungumeta Jannah tayi tana cewa

"I love you my baby"

Shigowan Sayd palon ce Kansa a qasa ya saka Jannah sakin Falaq tana kallan kofar alaman an sake kowa.

Qarasa sakin Falaq tayi tana barin palon ta kofar AZIZ tana isa harabar gidan inda bata tarar da kowa ba.

Bangarensu ta nufa da sauri tana jin jikinta na sake sanyi.

Da garba ta fara cin Karo Yana ganinta ya tsareta da ido Yana ransa inda komai ma na rayuwarsu data mutan gidan ta dosa.

Maheer da Dad ta sama suna kokarin shigewa da sauri ta iso gurinsu tana Kiran sunan Dad bata tsaya komaiba ta fada jikinsa tana fasa kukan kunyar dake neman kasheta ta hau bayanin babu abinda ya hadata da AZIZ din kawai ganinsa tayi ita kuma tsoron ihun da ake ya sakata jansa ta boye ciki sbd ta dauka Ammar ne kada ayi masa sharri.

Ammar dake tsaye zuciya na son kashesa jin Ashe shi taje karewa take zuciyarsa tayi sanyi Yana sake jin sonta na cike koinansa.

Dad ma da Maheer da dukkaninsu koyaushe kaunarta ke rufe idonsu akan komai na rayuwa ydda sukai da zancenta suna tsake tsanar AZIZ din akan basusan niyarsa ta zuwa kofar dakin su Jannah din da dareba dan haka gabaki daya jin sukai sun sake tsanarsa da tsanar zama a 4&4 din akan a taba mutuncin Jannah sun zabi yafe Sanin inda Saleem yake zasu bar mansion din kota halin yaya ne.

Jannah data samu sassaucin nauyin kirjinta ganin sun amince da zancenta numfashi da ajiyan zuciya ta sauke ta dago ahankali tace

"Ina Ummah??

Gabaki dayansu daki suka kalla
Dad ya sauke numfashi me sanyi cikin nutsuwa da Yar damuwa yace

"Batajin dadi sosai sai asubar ma ta samu yin bacci bayan Tasha magani shiyasa inaga bata farka ba haryanxu abarta ta samu hutu yanda ya kamata.

Ammar ne ya bude baki yace

"Ko zaa kaita asibiti ne Dad sbd Ummah fa bata baccin safe har haka"

Girgiza kai Dad yayi yana qin kallan ko wannensu ya juya Yana cewa

"Zata farka Lfy kalau inshallah"

Jannah ma kaman munafuka ta juya dakinsu ta shige tana shiga ta zube qasa tana jero ajiyan zuciya da numfashi tana dafe kirjinta da bugawarsa ayau ta kusa tada ciwon data jima bataiba.

Fatma datai sallah take tsaye tsuru tsuru tana jiran Jannan sbd tasan ta kwafsa Amma kuma batai tinanin su bane tinda ko a mafarki bata taba tinanin AZIZ LIMBA a bangaren masu aiki ba bare dakinsu.

Jannah bta iya cewa fatma din komaiba toilet ta wuce ta sakarwa kanta ruwa tayo wanka ta fito zauna tareda kallan Fatma da zatai magana ta katseta da cewa

"Fatma pls kada kice komai nima haryanxu ban gama dawowa daidaiba abar abinda ya wuce kawai banason Tina wannan masifar ta yau"

Shiru fatma tayi tana sake jin kunya na rufeta itama na yau din.

*********Da taimakon fiddausi Mama ta isa dakinta ta zube qasa tana son fasa ihun kuka amma girmanta ya wuce hakan hakama radadi da wutar dake cin zuciyarta ya hanata komai bare iya cewa komai,

AZIZ dinta ne ayau a bangaren masu aiki a cikin dakin Jannah?
AZIZ dinta ne idonsa ya rufe akan mace ya hadata da Zaadens ya zuba a motar karfe?
Idan AZIZ zai mata haka akan wata macen mezai faru idan yaga Fatima?
Menene kuma bazai iyayiba akan fatima?
Wlh tallahi wannan ba AZIZUN ta bane dan har abada AZIZ bazai taba take doka da umarninta ba bare tattarasu a zuba a mota kamar wainda aka kamo gidan gala,

Wlh da sake dan kuwa tana buqtaan tashi da tsayen gaske dan kwato danta daga hannun kowa da kuma hanasa shiga hannun kowa koda zata zama zarrriya ne.

Miqewa tayi daqyar takai kanta bathroom tayo alwalar asubar da basuyiba suka ari hauka suka tada anguwa.

Nicky kuwa tana shiga dakinta wani mahaukacin ihun ta fasa tana fasa kayan dakin da karfi cikin tsananin hauka da wata masifar wuta dake ci a kirjinta tana tafarfasa jininta.

Hannuwanta da wasu sassan jikinta jini sukeyi sbd yanda take fasa komai da hannuwanta ga glasses tana kukan baqin ciki batareda ya damu da jinin ba.

Dayake kowa yasan yanayin nata babu Wanda yayi yunqurin zuwa dakin shiru sukai Banda Falaq datake jin zuciyarta fes batajin sauran baqin ciki ko damuwar komai sbd Jan dinta data samu.

Duk sautin haukarta Bata isa bangarensa dan haka baisan mema Yan gidan suke ciki ba.

Dan kanta ta gama tayi laushi ta zube qasa tana kuka kaman ranta zai fita tanajin babu Wanda takeson rabawa da duniya irin Jannah da duka ahalinta ma.

Fatma da Amina ne sukai aikin abincin gidan wunin ranar sbd Jannah kasa fitowa tayi dakinta hakama madam Sisi da take a tsorace,

Su kuwa masu gidan kowa baqin cikin duniya ya hanasa fitowa cin abinci.

Fiddausi ce kadai ta sauko ta dauki abincinsu takai musu sama sukaci itada falaq hankali kwance.

Sayd ma ya fito dining yaci ya koshi ya koma dakinsa Yana ayyukansa.

Me gidan babu Wanda ya gansa har washe gari tukuna kowa ya samu danne abinda yake ransa suka hadu gabaki dayansu a dining hadda shi daya sauko a kame kyakkyawar fuskansa ba sakewa cikinta ko kadan.

Gaida Mama yayi a taqaice yana zaunawa,

Gaidasa kowa yyai ya amsa a taqaice daga Nan babu Wanda ya sake magana har aka gama ya miqe daga dining din ya fice Sayd na miqewa yabi bayansa.

Bayansa dukansu sukabi da kallo Banda Falaq data miqe tabi bayansa tana riqe hannunsa tana masa magana.

Mama da dankalin datake ci ya tsaya mata cak a maqoshi ya tokare jin tayi kaman ta Dora hannu akai tayita zunduma ihu tana tsinewa asalin Wanda ya haifo zuriar Zaadens a duniya.

Nicky kuwa jin tayi idan bata cika kudiranta akan Jannah da Ammar ba bazata iya rayuwa a duniya ba hakama idan bata mallaki AZIZ ba tafi son ta bankawa 4&4 wuta kowama ya mutu har ita har AZIZ din shikenan a rufe tarihin kowama ya huta dan haka bawai faduwa a karon farko zai sakata hakura ba idan na farko beyiba na biyu zeyi ta tabbatarda wannan.

Tashi sukai kowa yakoma dakinsa dan kulla sabon shiri.

Wuni guda babu Wanda ya fito hakama gidan tsit har dare,

Washe gari ma haka dan haka Jannah ta fito ta koma bakin aikinta sbd ganin komai ya lafa.

Madam Sisi ma ta fito ta koma bakin aiki sbd jin shiru maigidan yaqi cewa kowa komai.

Kwana biyu kowa ya nutsu babu tashin hankalin komai hakama ita kanta Jannah din kwata kwata bai sake nemanta ba sbd kaman hadda ita a laifin.

Ummah tayi jinyar kwana biyu kafin ta warke ta koma daidai ta dena kwnaa dakinsu Jannah kwata kwata kuma.

Ranar da akai sati da lamarin Nicky ita kadai ta fita batareda Ammar ba tana dawowa Garba ne ya bude mata gate ta shigo tayi parking ta fito motar.

Garba ta kira ya taso ya iso gurinta a natse Yana sake mata barka da dawowa.

Kallansa tayi tareda bude Jakarta ta ciro apple a leda Guda biyu ta miqa masa batareda ta masa kallan arziki ba ta miqa masa tace

"Give it to Ammar kace abokinsa drivern Office Dina yace a basa"

Gyada Kai Garba yayi Yana cewa "ok ma'am"

Juyawa yayi da sauri ya nufi Ammar dake wankin kayan Jannah a baya nufesa.

Da Sauri tabi bayan garban dan ganewa idonta.

Tana isa ta leqa sai kuwa taga Ammar na cin abu a bakinsa kuma a hannun garban ma tana dubawa daya ta Gani a hannun.

Wani irin tsananin sanyi da nutsuwa taji tana samu ta juya tabar gurin tana jin dukkanin ciwon ransu ayau inshallah zai wanke.

Garba juyawa yayi zai tafi Ammar dayake cin carrots kallan garban yayi yace

"Ka dauki dayan ka hada duka banaci daman ummah da zan bawa dayan Amma kuma zan siyo mata da kaina dan ban yadda da Nicky dinnan kwata kwta ba.

Garba bai tsaya musu ba ya dauka dayan ya hada biyu ya wuce yana fasa daya Yana fara ci.

Yana fitowa daga baya Fatma na ganinsa ta karbe dayan tana cewa lallai ya Garba hr apple kakeci da yamman Nan,

Dariya sukai a tare cikeda jin dadin apple din yace

"Ke duniya fa ta samu gwara muji dadi"
Dariya tayi tana wucewa kitchen sauri takeyi itama.

Tana isa aiki ta saka hannu a ciki tana ajiye apple din saita gama ta koma daki.

Jannah dake tattara gurin bata wani San na waye ba ta dauka ta saka a Fridge cikin Sauran apples din tana rufewa.

Har dare suna aiki suna gamawa Fatma ta bude Fridge ta dauki apple dinta daya suka fice bayan sun kashe komai.

Da daddare fiddausi ce ta kawo ruwa da juice a dining a lokacinda zasu abinci tareda fruits hadda su apple ta jere a dining din.

AZIZ da Sayd har lokacin basu dawo ba dan haka daga Nicky se Mama da Falaq da fiddausi suka ci abincin Daren suka gama suka koma sama zuciyar kowa fal farin ciki.

Karfe 10 na dare ta wuce motar AZIZ din Tai parking Sayd ya bude masa kofar ya fito kai tsaye.

Garba ne ya bude musu gate a cikin mummunan halin da bayason kowa ya gansa sbd a tsaye yake qyam.

Wanka AZIZ yayi tareda sako jallabiyansa ya fito sbd gobe tafiya zeyi karfe 9 na safe jirjinsa zai tashi dan haka Yana buqatan magana da ita.

Nicky data biyo bayansa sbd tana isa palonsa Yana fitowa bai lura da ita ba take ta biyosa bata iya magana ko tsayuwa bata iya yi daidai.

Tsayuwa yayi a bakin kofar dakin tareda saka hannu kai tsaye yayi knocking.

Jannah wadda idonta yake biyu tana ji kai tsaye zuciyarta ta sanar da ita shine dan haka ta taso a natse tana bude dakin,

Ummah wadda itama batai bacci ba jin an buga dakin Jannah ta taso ta bude kofar dakinsu kai tsaye daidai Jannah na bude baki tace

"AZIZ LIMBA yasan meye time kuwa a yanzu??

Baice komaiba hannunta ya kama ahankali tareda janyota suka wuce Batareda ya juya bayansa inda Ummah ta kafesa da idonta da kankancewa tana furta "ABDULAZIZ LIMBA"

Motsawa tai zata bisu wani mahaukacin jiri ya dibeta ta yanke jiki a gurin ta zube.

Bangarensa ya nufa da ita bayan ya dauketa a jikinsa gabaki daya.

Nicky dasuka wuceta batareda sun ganta ba yanke jiki tayi zata fadi Garba dake sauri yana sintiri a harabar gurin tareta yayi Yana taimaka mata jikinsa na tsananta rawa kmaan yanda nata keyi.
#MAMUH
#4&4 MANSION
#ZAADENS
#LIMBAS

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 34

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

**********
Miqar da Nicky tsaye daidai garban keyi Yana sake shiga mummunan hali jin mace a jikinsa Wadda ke qara miqar dashi tsaye Amma ita kuma ta kasa tsayuwar da kafafunta sbd mummunan halin datake cikin itama.

Bude idanuwanta tayi daqyar akansa tana kallansa idanuwanta ciki ciki kuma dishi dishi
Yana kokarin sakinta tayi saurin riqe hannunsa da karfi tana maqalewa jikinsa dake fidda kamshin Sabulun wankansa dayaketa yi tin dazu ko zai samu sassaucin balain dayake jinsa a ciki Wanda bai taba faruwa dashi ba a kaf rayuwarsa dan shi idan ba Jannah dayaso a bayan ba baitaba kula kowace mace ba koda da sunan Soyayya bare harkar banza.

Jinta jikinsa tana mannuwa dashi tana son magana amma masifa ta hanata idonta sun rufe babu abinda take buqata bayan ta samu ruwan kashe gobararta dan haka cakumosa ta sake yi da karfi tana mannuwa dashi,

Da farko tsoro da shakka sun so dakatar dashi amma a hannu yake kuma komai yafi karfinsa ne a lokacinda take sake mannuwar dashi dan haka hannuwansa dake rawa yasa shima ya matsota jikinsa Yana saka hannuwansa duka biyun cikin rigarta ya caf kirjinta da karfin daya sakata sakin wahalallen nishin daya kara kashe garban yaji ya qarasa rasa kansa gabaki daya ya dauketa sukutum.

Dayan dakin masu aikin da babu kowa a cikinsa suka fada ya jefata akan gadon yana zare kayan jikinsa.

Gurin zare nata kusan yaga rabi sukai suka iya cire rabin..

Dukkaninsu a mugun yanayin mutsuwar fitan hankali suke dan haka babu wata doguwar shafe shafe ya wareta yafara bata karfinsa daya sakata buga ihun da bata san tayiba tana neman turesa.

Rufe bakinta yayi d hannunsa daya yana jin abinda bai taba jiba a duniyarsa sbd har cikin tsakiyar Kansa da bayansa yakejin wata irin yanayin datafi mallakar garken shanu dadi.

Karfinsa ya ringa nuna mata ba sauki Yana sake matseta cikin gadon Yana wani irin gurnanin dake bayyanarda duniyar dayake ciki.

Ita kanta wani irin kuka takeyi bakinta rife da hannunsa sbd samun yanda takeso d kuma jin abinda yafi karfinta dan haka kukan yake na duka biyun.

Wani irin uban zufa suka hada dukansu su biyun sbd basu samu damar kunna AC din dakinba sbd rashin nutsuwa gashi abu daya suketa yi daga shi har itan babu Wanda yaji yanada alaman koshi duk da duk sun gaji amma kuma sun kasa denawa bata kawai yakeyi tana karba.

**********
LIMBA kuwa kai tsaye palon qasa ya ratso da Jannah din Wadda tayi saurin kallansa tana bude baki da sauri sautinta a qasa tace

"AZIZ"

Yanda ta kira sunan nasa da wani qaramin sautin mamaki ya sakasa kallan idanuwanta kafin ya kalli bakin nata da yayi maganar tana kallansa ba zata ya dora lips dinsa akansu yayi kissing nasu ta sake juyawa da sauri tana kallan palon cikin tsananin tsoro da mamaki ta sake bude baki tace

"AZIZ are you ok???

Sake dora bakinsa yayi a lips din ya basu kiss.

Dukan kirjinsa tayi sa sauri zata leqa bayansa idan Sayd baya bayansu.

Bude baki tayi zatai magana ya buse baki cikin tsananin sonta da kewanta yace

"Kinsan bazan gaji ba right?

Hannu daya ta saka ta rufe bakinta tana riqe da wuyansa da hannun daya sbd daukan da yayi mata.

Kallan fuskansa takeyi tana son magana Amma tasan bazai gajin da abinda yace ba.

Sama ya haye da ita kai tsaye har tsakiyar palonsa tukuna ya ajiyeta tareda juyowa ya kalleta yace

"You can talk now"

Sauke hannunta tayi daga bakinta fararen idanuwanta na kan kyakkyawar fuskansa dake kasheta tace

"Why did you bri..... Saukan bakinsa kawai taji a hankali kan nata Yana zagayo qugunta da hannuwansa ya janyota tareda hadesu Yana zira harshensa cikin bakinta Yana bata wata lafiyayyar tsotsa cikin nutsuwa da bayyanarda tsananin son dayake mata me sanyi.

Ahankali yaji hannuwanta sun zagayo bayansa ta rungumesa wanda yaji hakan kaman a cikin mafarkin da bai taba tsammani ba dan haka ahankali ya dago idanuwansa ya kalli cikin idanuwanta datai kasa dasu ta kalla kallan cikin nasa idanuwan.

Ahankali ya bude baki cikin sanyi da nutsuwan dayaji tana shigarsa yace

"Jan Zad ki....

Sakinsa tayi tana kokarin juyawa ya dawo da ita ya rungumeta ta baya ya saka kansa cikin wuyanta ya goga fuskansa a fatan wuyanta ahankali suna lumshe idanuwansu a tare yakai bakinsa kunnenta ahankali cikin nutsuwar yanayin dayake ciki da ita da muryan data kashe dukkanin jikinta ta sake lafewa a jikinsa yace

"Kin manta bakice AZIZ LIMBA I hate you ba....

Rintse idanuwanta tayi da sauri tana dukan cikinsa ba yanta zata kwace ya hanata Yana sake zagayeta da hannuwansa ya sarke yatsun hannunsa daya da nata ya sake cewa

"JANNAH ZAD na kasa fushi dake,
Na kasa bayyanar Miki da fushin laifinki na ranar
Why Jan?
Kinsan kene kadai kike iya maidani AZIZ zallah da baya iya komai akanki ba AZIZ LIMBA ba da babu Wanda ya isa a gabansa da idonsa."

Shiru tayi batareda ta motsaba tana saurarensa zuciyarta na sanyi da irin son datake masa Wanda ta tabbatarda kila be kai nasa ba.

Meyasa take tsananin sonsa haka ne itama?
Meyasa AZIZ LIMBA a Karo na biyu Yana kokarin cin nasara akan zuciyarta?
Shin zata taba iya son kowane namiji a duniya bayan AZIZ LIMBA?
AZIZ LIMBA shi kadai ne a zuciyarta da bazata taba iya sauya hakan ba wannan itace jarabawar rayuwarta ta Sani.

Gefen fuskanta ya saukar da lips dinsa ahankali ya saukar mata da kiss me sanyi yana sake sarke hannuwansa da nata yace

"I love you 4&4"

"I hate you AZIZ LIMBA" ta furta ahankali itama tana lumshe idanuwanta.

Wani irin murmushin da ya jima rayuwarsa baiyiba ya sake Wanda taji sautinsa cikin kunnenta dake kusa da bakinsa.

Jin murmushinsa datasan ya manta rabon ya samesa ya saka zuciyarta cikewa da wani sanyayyan farin ciki da nutsuwan data saka murmushin sauka a tata fuskan tana kokarin hanasa gani sedai yaji dan haka ya juyo da ita yana kallanta yace

"Don't pretend na riga naji"

Rufe fuskanta zatai da hannuwanta ya riqe hannuwan Yana kallanta kaman zai hadiyeta ya sauke ajiyan zuciya ya kama hannunta suka isa bedroom dinsa ya zaunar da ita a sofa yace ta jira ya gama shiri zaiyi magana da ita.

Sanin zata iya tafiyanta ya sakasa rufe dakin kafin ya isa bathroom ya shige.

Wanka yayi da duk sauran shirin baccinsa ya fito daure da towel.

Kallo daya tayiwa inda yake ta dauke kai tana saukewa.

Closet ya nufa bayan ya gama goge jiki da Shafa su body mist da sauransu ya saka fararen silk pyjmas.

Jinsa tayi gefenta ahankali ya zauna tareda kama hannuwanta duka biyun ya kalli fuskanta ya bude baki yace

"Zanyi tafiya gobe"

Dagowa tayi ta zuba masa idanuwanta ahankali kafin ta bude baki tace

"Allah ya tsare"

Lips dinta da sukai maganar yai kissing ahankali kafin ya janyota jikinsa ya kwantar tareda rungumeta da hannu daya Yana hade hannuwansu da dayan.

Shiru sukai dukkaninsu babu Wanda yace komai bare motsawa tsawon mintina suna samun nutsuwan da suka rasa ta shekaru tana dawo musu ahankali.

Bude baki yayi cikin wani irin sanyi da nutsuwa yace

"Forgive me JAN"

Lumshe idanuwanta tayi ahankali sbd jin saukar kalmomin bazata da yanda suka ratsata.

Bugawa zuciyarta tafara yi ahankali da karfi,

Hannunsa ya zare daga nata ya Dora akan kirjinta seti kan zuciyar Ummitah yaji bugunta ya sauka akan tafin hannunsa ya rufe idanuwansa ahankali wasu hawayen tsananin kewa da rashin Ummitan suka ciko idanuwansa ya bude baki cikin tsananin rauninsa daya bayyana akan duk abinda ya shafi Ummitah sautinsa na karaya yace

"Ummitan Hammah Az......kasa qarasawa yayi sbd wani irin kukan dayazo masa Karo na farko daya yadda ya karbi kaddarar rasuwarta ya kuma yafe sake tada maganar har abada sbd zuciyarta n kirjinta bazai taba hurting ba har karshen rayuwarsa.

Tashi gashin jikin Jannah gabaki daya yayi sbd kukansa daya zo a wani irin yanayi na karyewan zuciyar Wanda yake tsananin son abinda yariga ya rasa har abada,

AZIZ na yiwa Ummah son da har abada babu wanda zai cike masa gurbinta ita kadai,

Yayi rashin da har abada an riga anyiwa rayuwarsa gibin da koda zai cike sai lokacinda Allah ya nufa....

Mutuwa jikinta yayi ta Dora hannunta akan nasa dake kirjinta tana rungumesa gabaki dayansa tana kasa riqe hawayenta akan kukan dayake Wanda ayau ne yake asalin kukan rashinta na gaskia da dangana ta har abada.

A Karan farko daya budewa wani dan Adam Guda daya tal rayuwarsa cikinsa yasan damuwarsa sbd a cikin yanayin quncin zuciyar ya bayyanarda damuwar dake cinsa tin ta yarinya ta rashin asalin mahaifiyarsa.

Babu Wanda yasan meye a zuciyarsa a kaf rayuwarsa sai ita kadai ayau tasan kuncin dayake ciki na rashin asalin mahaifiyarsa dayake yiwa son daya zarce komai da kowa.

Ayau Jannah tasan asalin waye AZIZ LIMBA,
Waye shi a boyensa da babu Wanda ya Sani,
Ayau tasan mahaifiyarsa Ashe itace asalin weakness dinsa da haryanxu babu Wanda ya Sani sbd bata tareda shi,
Rashin Mahaifiyarsa itace kuncin da bazai taba warkesa ba har abada.

Kuka tayi sosai wanda ta jima ita kanta batai irinsa ba sbd tsananin tausayinsa da sonsa daya riga yagama breaking loose a zuciyarta sedai kuma gyra daga Allah.

Sun jima sosai a wannan yanayin har wani lokaci na tsakar dare kafin bacci me nutsuwa ya daukesa a jikinta ya cukaikuyeta kaman qaramin yaro.

Zubawa fuskansa ido tayi tana kallansa babu ko kyaftawa tana jin kaman ta hadiyesa sbd tsananin so da tausayin inama zata iya nemo mahaifiyarsa da zata iya bada fansar ranta akan ta bawa AZIZ LIMBA mahaifiyarsa da itace warakarsa.

Hannunta ta daga ahankali ya Shafa fuskansa tareda kai bakinta ahankali tayi kissing goshinsa tana sake rungumesa jikinta tareda lumshe ido.

Baccin ne ahankali ya dauketa a hakan itama cikin nutsuwa.

Tsakar dare sosai ya bude idanuwansa yaga yanayin da suke ciki ya zame ahankali tareda miqewa tsaye ya dauketa ahankali yakai kan tsakiyar gadonsa dayake gyare da tsadaddun beddings masu tsadan gaske da laushi.

Rufeta yayi ahankali bayan ya dan rage musu AC din kafin ya kwanta gefenta Yana shigewa cikin jikinta Yana jin rayuwarsa na daidaita sbd samun Jannah a cikinta.

Da asuba tare sukai sallah da addua tana gamawa ta miqe tsaye tana neman guduwa tsoronta na dawowa sbd kada kowa yasan bata Nan.
#MAMUH
#4&4
#LIMZADs

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 35

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

************
Dawo da ita yayi kan kafafunsa batareda ya tashi daga kan inda yayi sallah ba.

Zare mata rufanta yayi ahankali Yana kallanta ba zato ya bude baki taji yace

"Zan tafi dake"

Cikin faduwan gaba da rikicewa tace

"AZIZ"

Qarasa rungumota yayi tana fadawa jikinsa gabaki daya yace

"Yes"

"No" tace da dan karfi tana kallansa da mamaki dan ita tsoro ma taji duk ya rufeta.

Ganin yanda ta rikice ta shiga tsoro ya sakasa sakin wani sanyayyan murmushi Yana tinanin yanda zatai a gaba idan har batason kowa ya Sani ya Sani akwai lokacin zaa Sani din.

Shafa fuskanta yayi yana cewa

"Ok then its okay"

Ajiyan zuciya ta sauke jikinta na saki ta kallesa tana sake sauke ajiyan zuciya.

Miqewa take sake kokarin yi ya sake riqeta Yana zagaye cikinta da hannuwansa ya hade fuskansu guri daya ya shaqi numfashinta ahankali Yana lumshe ido ya budesu akanta itama shi take kallan jikinta a mace da iskan daya sakar mata me dumi da qamshinsa.

Kunneta yakai bakinsa yayi kissing ahankali kafin da wani sautin daya sake kashe jikinta yace

"Good morning JANNAH ZAD"

wani irin tsananin sanyi taji Yana shigarta ta bude ido ta kallesa fuskanta a cikeda haske ta bude baki zata amsa ya sakar mata kiss me sanyi a lips din Yana kallan bakinta.

Qasa zatai da kanta ya dago fuskanta Yana ci gaba da kalla Wanda hakan ya sakata bude baki tana kasa kallansa tace

"AZIZ" cikin sautin data saba ambata me dadi

A duk lokacinda ta amabaci sunansa wani kakkarfan feelings yake samu akanta dan haka hannuwansa ya zira cikin rigarta Ya yiwa cikinta wata irin shafa me sanyin data saka numfashinta daukewa tana qanqamesa.

Mararta ya maida hannun Yana sake matseta jikinsa suka mannu ahankali Ya fara shara Mararta zuwa bayanta Yana tfiya tareda rigar jikinta zuwa sama sedai taji rigar ta fita ta wuyanta ahankali tabar jikinta zuwa qugunta.

Baya yayi da wunyata Yana fara jero kisses tin daga hancinta zuwa bakinta zuwa wuyanta ahankali ahankali har zuwa kirjinta daya sauke wani numfashi me karfi Yana Dora bakinsa da hannuwansa a lokaci daya.

Rawa jikinta ya dauka ta riqe kansa da tana neman rasa numfashinta.

Cibiyarta ya sake Shafawa kafin ya dago kansa Yana kallan idonta da suka ciko da hawaye ya kama bakinta da nasa ahankali yana shiga cikinsa da wani irin sanyi yafara tsotsa Yana sake gyara Mata zama akan jikinsa.

Wasu zafafan romance yake bata da kwakwalwanta ta kasa daukansu dan haka ta fasa masa kukan da batasan yaya zatai ba sbd babu inda bakinsa be sauka ba a jikinta dan haka jikinta har rawa ya fara sosai ganin abin na neman fin karfinta.

Jin kukanta yake har cikin ransa dan haka ya sassauta harya qyaleta ya rungumeta jikinsa sbd bazai iya mata dole ba zai jira ya dawo.

Bayanta da babu komai yake Shafawa Yana rungume da ita akansa Yana hura mata iskan dayake tada gashin jikinta ahankali Amma tsoro ya hanata motsin komai.

Bacci yaso daukansu a hakan Amma ganin garin yanata qara gaske ya sakata miqewa ta sake shiryawa.

Shiryawan yayi Shima ya kama hannunta zasu fito ta zame hannunta tana girgiza masa kai tace dan Allah kada ya biyota a sake samun matsala.

Bai kula zancenta ba ya kama hannunta ya bude kofar palon daidai nan Sayd ya iso zai buga kofar.

Ganin Sayd tayi saurin qwace hannunta tana yin gaba d sauri tana cewa dan Allah kada ya biyota da hannu.

Binta yayi da ido harta bacewa ganinsa ya sauke ajiyan zuciya a boye mara sauti kafin juyo ya maida kallansa kan Sayd Wanda Kansa yake qasa ya bude baki Yana kamewa yace

"Yes?? Yana juyawa palo Sayd yabi bayansa dan bada bayanin daya kawosa.

Ita kuma tana sauka ta dayan palon tabi ta isa kitchen dinsa ta tadda Fatma da Amina.

Da kallo Fatma ta bita tana son magana ganin Amina a gurin yayi shiru tana jefawa Jannah maganar data dauke kallo da mamakin da Amina ke binta dashi.

Cikin karfin hali suka fuske Jannah dole batama koma dakiba ta saka hannu a aikin.

Madam Sisi ce ta iso kitchen ta buqaci milk tea me kauri sosai da zafi.

Babu bata lokaci Amina ta hada ta bata ta karba a tray ta fice duk a rude.

Sama ta nufa dakin Nicky wadda take kwance Rai hannun Allah.

Tada ita tayi ta ringa bata tea din da sauri tana mata sannu cikin tsananin tashin hankalin ganin halinda take ciki.

Ko gama shan tea din bataiba ta fara Amai a gurin.

A rikice madam Sisi ta sake kamata xuwa toilet acan ta sake shiga ruwan zafi sosai Wanda azabar ruwan kadai ta ringa sakata ihu tana fasa kukan azaba da tsananin baqin cikin rayuwar datake ciki na mummunan kaddarar data hau kanta.

Fatma Sisi ta kira ita ta gyare dakin ta tsaftace suka fice bayan Nicky din ta shirya da kyar ta fito Sisi riqe da ita suka fito Ammar ya dauketa zuwa asibiti batareda Sanin kowaba.

Suna Isa kai tsaye aka shige da ita,

Ba qaramar gurzuwa tayi ba da shan azaba dan haka suka kwantar da ita aka daura mata ruwa da sauran duk abinda ya kamata.

Dayake ta hana Sisi fadawa kowa kaman yanda itama Sisin batasan meya samu Nickyn ba Amma dai tasan dole namiji ne yayi mata wannan abin sbd a dakinta ta sameta da duhun asuba ta yanke mata jiki tana cewa kada ta fadawa kowa ta kaita dakinta.

Tin a duhun asubar suketa fama har yanzu din.

Karfe 7 ya sauko breakfast tareda kowa sbd Sanin zaiyi tafiya shiyasa kowa fitowan da wuri dan suyi bankwana.

Duk yanda yaso ganinta Sam taqi fitowa daga kitchen din bare zuwa dining kawo wani abin duk da tasan Yana sakaran fitowan tata.

Karfe 8 saura ya wuce tareda Sayd zuwa airport.

Mama ce kawai ta damu da fitar Nicky batareda Sanin kowa ba dan haka ta ringa kiranta amma wayar baya zuwa sbd ita a yanzu da AZIZ yayi tafiya duk rintsi duk balai bazata bari ya dawo ya tadda Zaadens a gidan ba bare Fatima.

Nicky a asibiti sai yamma lis ta samu kanta ta wartsake sosai sedai ba karfin jiki dan haka suna baro asibiti gurin cin abinci me tsada suka tafi sukaci suka koshi ta sake samun karfi kadan sbd batason duk rintsi kowa ya fahimci akwai halinda take ciki.

Sai kusan dare suka dawo gidan a gajiye dukkaninsu.

Wanka tayi ta sake gasa jikinta ta sake samun yanda takeso Tasha magani take baccin wahala ya sake dauketa.

Garba ma wuni akai dashi babu lafiya sosai dashi dan Ummah Wadda tinda ta farfado bata iya cewa komaiba ido kawai take binsu dashi.

Ansamu Garba yaji sauki bayan kwana daya ana fama amma kwata kwata Ummah ta dena magana bata taba cewa komaiba tinda aka sameta a sume har yanzu,

Hakan shine abu mafi tashin hankali daya samesu me girma hakama ta dena son zama da kowannensu Kebe kanta takeyi tana tinani me tsananin tsayin gaske.

Dad gabaki daya neman rasa nutsuwansa yakeyi dan haka suka fara tinanin guduwa kawai subar 4&4 dan tafiya neman lafiyarta da abinda suka Tara me kauri a yanzu.

Wannan shawarar itace kowa ya yadda da ita hadda Jannah da hankalinta ya rabu gida biyu sbd a yanzu ta tabbatarda bazata iya rayuwa ba AZIZ LIMBA ba,

Batajin zuciyarta zata sake moruwa idan ta rabu da AZIZ a daidai lokacinda suke tsananin so da buqtaan junansu,

Tayaya zata tafi tabarsa ya shiga mummunan halinda zai rasa kansa gabaki daya?

Gabaki daya sanyi tayi itama kunci da damuwa na dawowa rayuwarta sbd a yanda ahalinta ke tsananta so da shiri AZIZ LIMBA bazai taba dawowa ya tadda su ba duk tsanani.

Ta bangaren su Dad ma damuwar tayi nauyin da kowa yake cikin kunci da nauyin zuciya dan haka kowa rayuwar tayi masa duhu da daci,

Garba ma a cikin tsananin damuwa da qunci yake ta yanda babu abinda yakeso shima kaman son barin 4&4 sbd zuciyarsa dake cikin Dana Sani da baqin cikin halinda ya samu Kansa a ciki na aikata zina da matar da zata kasance Matar me gidan.

Fatma gabaki daya itama kuncin dayake cikeda rayuwar kowa Musamman Jannah da Garba ya sakata sanyi da damuwa rayuwar kawai sukeyi.
#MAMUH

07019691719

*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 36

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

********
****Nicky ta warware sosai ta dawo daidai cikakkiyar lafiyanta ta dawo bayan jinyar kwanaki datai fama da ita wadda ta hana kowa kira mata likita bare zuwa asibiti,

Mama tayi jinyarta da kulawa da ita sosai tareda fiddausi harta warke ta dawo kan kafafunta.

Abu daya ne ya kasa warkewa a zuciyarta kuma bazai taba warkewaba har abada idan ba ganin bayan Jannah da Zaadens tayi ba tareda shi garban kansa dan Sai ta tabbatarda garba baya duniya kwata kwata ta yanda bazai taba qarar da labarin abinda ya faru tsakaninsuba.

Da wani irin sabon baqin cikin zuciya me karfi da kudirin daukan fansar abinda ya sameta ta warke dan haka kai tsaye bayan warkewanta ta kalli Mama tace

"Mama Zaadens sun yiwa rayuwata illan da bazan taba iya yafe musu ba,
Mama wallahi wannan Karan sai Zaadens sun biya abinda sukayi?
Sai na tabbatarda Zaadens ko da kafafunsu koda gawarsu sai sun bar rayuwar gidan nan kafin dawowan AZIZ sbd zan rasa kaina idan na sake ganin Zaadens da AZIZ,
Mama ki....

Cikin gajiya da nata baqin cikin dayake cin ranta da rayuwar da gabaki daya ta juye ta koma batada nutsuwa duk ta haukace akan Zaadens da AZIZ dan haka itama ta gaji amma kuma tafi gajiya da masifun da koyaushe tsarin Nicky yake janyo musu dan ta kusa rasa sashen jikinta akan Nicky tace

"Aisha na gaji da tsarinki da haryanzu babu abinda yake bani sai ciwon zuciya da neman rasa kaina a gaban AZIZ,
Tin yaushe zamu zauna ace mutanen Nan sun gagaremu?
Ni na gaji,abu daya na sani ko a rayen ko a macen nidai su bar gidan nan kafin dawowan AZIZ,

Idan zaki iya mun hakan ta kowace hanya na Miki alkawarin wlh Yana dawowa bazai kwana ba sai an daura aurenki dashi koda a cikin dare ne.

Da sauri Nicky ta juyo idanuwanta jajir sbd kanta dake wata irin rawa tanajin wuta na ci a cikinsa tace

"Mama wlh tallahi sai sun bar duniyama gabaki daya ba 4&4 ba"

Mama da idonta ya rufe tace

"Indai zasu bar AZIZ koma lahirar ne su tafi."

Nicky da maganar aurenta da AZIZ ta birkitata gabaki daya ficewa tayi tana buga kanta da juyasa sbd yanda yake wani Kara Yana mata motsi.

Numfashi me zafi Mama ta sauke tana bin bayan Nicky din da jajayen idanuwanta sbd Nicky zata kawar mata da matsalar rayuwarta a yanzu datafi komai zamar mata babbar masifar rayuwa wato Haduwan AZIZ da Fatima.

*****Falaq ako yaushe yanzu tana gurin Jannah bacci ne kadai se wani abin ke maidata ita da fiddausi sun tare acan duk da basa samun fuska ko kadan a gurin Zaadens sbd tsanar da kiyyyar a bayyane take sosai.

Itama Falaq bata damu dasu din ba Jannah kawai takeso a cikinsu dan haka ita kadai tadamu da ita.

Ammar neman zarewa yakeyi sbd dawowan Falaq rayuwar Jannah zai iya lalata masa komai kamar a baya dan haka ya tsananta fidda tsanar LIMBAs a fili wadda ta qar bayyanarda tsanar da kowa kewa juna a tsakaninsu.

Ayau tin safe kowannensu ke parking a bisa umarnin Dad dan haka zaune take a dakinsu ta kasa hada kayanta data fidda gabaki daya daga wardrobe.

Fatma bata dakin ita kadaice shiru zuciyarta tayi wani irin nauyi da sanyi.

Ummah ce ta shigo dakin ahankali cikin tsananin sanyi itama ta qaraso gurin Jannah din ta zaune gefenta a sanyaye idanuwanta jajir.

Qurawa Jannah idanuwa tayi tsawon mintina kafin ta ciro hannuwanta dake tsananin rawa zata dafa Jannah din sai kuma ta fasa ta rintse idanuwanta ta bude ahankali ta bude baki da wani sautin daya saka Jannah kallanta da nata jajayen idanuwan.

"ABDULAZIZ AYOUBA LIMBA?

Rintse idanuwa Jannah tayi ta budesu akan Umman cikin tsananin mamaki da shock din cikakken sunansa a bakinta sedai tinanin komai baizo kanta sbd mutuwar da jikinta yayi da tsananin ciwon abinda ake shirin aikatawa na rabasa da abinda yakeso idan aka tafi da ita.

Hawayene suka ciko idanuwan Umman ya sake maimaita sunan Wanda ya saka Jannah rungumeta tana gangaro da hawaye masu tsananin zafi da wani irin raunin zuciya tace

"Ummah AZIZ LIMBA shine rayuwata,
Bazan iya rayuwa babu sa ba,
Bazan iya dena sonsa ba har abada,
Zan dena numfashi idan na rasasa,
Zuciyar Ummitah zata mutu kaman yanda ta Jannah ta mutu da dadewa idan aka rabata da AZIZ,

AZIZ yana tsananin buqata,
Baida kowa,
Ya rasa mahaifiyarsa Fatima tin yana qaraminsa shi da Ummitah,

AZIZ yana cikin quncin rayuwar da warakarsa mahaifiyarsa ce,

Babu mahaifiyarsa babu Ummitah tayaya zan barsa nima?

Zamewa tayi ta kwanta jikin Umman ciwon kirjinta na tsananta da quncin dayake ciketa ta rintse idanuwanta hawaye masu dumi suna sake gangarowa muryanta tayi sanyi tace

"Ummah kaddara ta saka ahalina da AZIZ LIMBA zama maqiyan juna tin kafin mu hadu sbd kaddarar zuciyar Ummitah dake cikin nawa kirjin,

Rasuwar Ummitah ta sauya duniyar AZIZ LIMBA da Zaadens gabaki dayanmu sbd haryanxu muna cikin tsananin Dana Sani da baqin cikin abinda ya faru,

Bantaba Sanin an daukan ran wani dan rayani ba dana dade da karban kaddarata na zabi mutuwata da AZIZ bai shiga qunci da ciwon rasa Ummitansa ba,

Da ayau bamu shiga quncin daukan ran da ahalina sukai ba,

Sun tuba sun nema yafiyar,sunata qara tubarwa Allah,
Ran mahaifiyata ya tafi a gurin girban abinda ya faru,
Ran daddy Mahmoud ma ya tafi,
Mun rasa Saleem,
Mun rasa Anny,
Mun rasa mummy duka akan wannan mummunan kaddarar data hadamu Amma haryanxu gabar tana qin qarewa,

Ummah inason AZIZ LIMBA inason Ahalina dan haka bansan yaya zanyiba..

Kuka takeson fasawa yaqi zuwa sbd ciwon komai dayake dawo mata ta ringa fayyace komai da irin rayuwar datai a hannun AZIZ da rayuwar da suka fada da ahalinta tareda halinda suka shiga na tozarci da rasa komai hatta suna da mutuncinsu ayau sun qare a zero Amma quncin ya kasa qarewa.

Ummah da jikinta ke wata irin jijjiga idanuwanta jajir wani irin gunjin kukan daya girgiza Jannah ta fasa me karfin gaske tana dafe kirjinta dayake mata wani ciwon data ke jin kaman ranta zai fita sbd azabar radadi.

Tashi Jannah tayi jikinta da sauri tareda kallanta Amma ganin yanda jikinta ke tsananin rawa tana kukan Wanda yake daga ja na ciwon rashi ne da baqin cikin.

Rungumeta Jannah tayi da sauri tana fasa kukan tausayinta da kaunarta tana cewa

"Ummah ki dena kuka irin wannan bazamu iya ganinki a wannan halin ba shiyasa zamu tafi dan neman lafiyarki,
Nima Ummah na zabi tafiya nabar AZIZ din sbd neman lafiyarki indai zaki dena jin quncin dayake tokare da kirjinki...

Kuka takeyi sosai wanda Umman ma kukan takeyi.

Fatma ce data shigo taga mugun halinda suke ciki taje ta sanar dasu Dad.

Su Dad na zuwa kowannensu idanuwansa sukai jajir Dad ya kamo Umman tareda rungumeta a jikinsa Yana kasa cewa komai sedai tsananin damuwarsa da dacin dayake ransa a bayyane yake.

Shiru sukai dukkaninsu cikin dacin zuciya suna sauraron kukan Umman wanda ta jima tana yinsa kafin ta dena ta kasa dagowa ta kalli kowannensu.

Jannah ce takaita toilet tayo wanka Maheer ya bata magani Ammar ya bata ruwa tasha ta kwanta Dad ya rufeta kafin dukkaninsu suka fice.

Wunin sukuku sukai cikeda damuwa da dacin zuciya sbd yanayin Umman wadda duk ta kasa cewa komai sedai binsu da ido a duk hidimar da sukeyi da ita.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 37

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

**********
Washe gari Dad ya samu Mama yayi magana da ita akan koma yayane suna son tafiya subar gidan.

Da farin cikin zancen ta kallesa tace su shirya tayi alkawarin komai tsurin tsaron AZIZ zasu tafi a gobe sa sassafe kafin kowa ya tashi.

Koda ya taho kai tsaye ya sanar da kowa dan haka suka qarasa shiryawa.

Mama shugaban securities na gidan gabaki daya ta kira da daddare har palon qasa ta sauko tareda kallansa bata son batawa kanta lokaci ta kallesa ta sanar dashi Zaadens kawai takeso ya bari su tafiyarsu kafin dawowan AZIZ,idan ya dawo ztsan abinda zata fada masa Wanda bazaiga laifinsa ba.

Kudi ta ciro bundle goma na Yan 1k ta ajiye masa tana kallansa.

numfashi ya sauke me nauyi shima bai tsaya bata lokaci ba yace gate zai zama a bude goben idan suka tashi tafiya.

Murmushi da ajiyan zuciya me karfi Mama ta sake tana cewa ya tafi zataji da sauran.

Yana fita Nicky dake labe tanajinsu ta sauke numfashi zuciyarta na tafarfasa sbd bata dauka Mama zata bata Mata shiri ba,
Ita Sam batason Zaadens su tafi dan su rayu sbd Jannah zata iya dawowa rayuwar AZIZ hakama Garba har abada zaici gaba da Tina yanda ya sameta dan haka ita sam batada niyar subar gidan a raye dan haka bama kowa ze kai gobenba bare kai labari.

Da daddare karfe 9 na dare Mama ta iso bangaren Zaadens din gabaki dayansu suna zaune.

Abinci Dad ke kokarin ganin ummah taci ko kadan ne Amma kwata kwata ta kasa zazzabi ne sosai a tattare da ita kuma har lokacin taqi cewa komai.

Ammar dake gefen Umman daya Yana mata fita ahankali ko dagowa beyiba ya kalli Maman sabanin kowa daya dago ya kalleta hadda ummah data dago jajayen idanuwanta ahankali ta kafeta dasu.

Mama bata batawa kanta lokaci ba ta jefa musu kudin dayake hannunta a gabansu ta kalli Fatima cikin idanuwa kafin tace

"Gobe karfe 7 na safe kubar 4&4 zaa bude muku gate wannan kudin kuma ku tabbatarda kunyi nisan da AZIZ bazai taba ganinku ba har abada"

Tana fadar hakan ta juya tabar gurin babu Wanda ya kalli kudinta bare tankawa

Harta bace ummah bata iya dauke idanuwanta akanta ba kafin ta rufe tana sunkuyar da kanta.

Har karfe 10 suna waje kafin suka tattara kowa ya shige.

Ummah Dad ne ya kama hannunta har dakinsa suka shige.

Itama Jannah suna shigewa wanka ta fada tayi da brush tana fitowa ta zauna ta shafa turare kadan kafin ya saka doguwar rigar bacci me tsantsi ta nufi gadonta ta hau.

Cikin bacci taji fatma na tada ita batareda tayi nisa sosai a baccin ba.

Bude idanuwanta tayi ahankali ta kalli Fatman.

Janyewa Fatma tayi tana kasa cewa komai dan Jannah taga waye a bakin kofar shigowa dakin daga waje.

Kaman a mafarki ta gansa tsaye sanye da ash Armanis da waya da jacket a hannunsa da alamar daga mota nan ya wuto direct.

Farin cikin daya cike zuciyarta ne ya sakata saukowa gadon da sauri ta nufesa da wani irin gudu tana isa ya dauketa sama Yana rungumeta itama tana qanqamesa farin ciki fal zuciyarta.

Fatma ma farin cikine ya ciketa ta sunkuyar da kai.

Kallan fatma yayi batareda ya sauke Jannan ba ya furta "thank you" ahankali cikin kasala yana juyawa da ita ko takarmi ko wani abin rufe jikin babu a tareda ita.

Suna barin gurin baifi da minta biyar ba Ummah ta dawo dakin ta kwanta a gadon Jannah tana duqunqunewa.

Suna isa bai ajiyeta ba sai tsakiyar bedroom dinsa Yana kallan fuskanta ya kama bakinta ya sakar mata wani zafafan kiss kafin ya rungumeta yana cewa

"Alhmdlh ya Allah"

Murmushi takeyi tana sake qanqamesa itama kafin ta dago ta kallesa tace

"Daman yau zaka dawo?
Amma kowa besan yau zaka dawo ba?

Fuskansa ya saka a wuyanta ya shaqi qamshinta yana gangarowa har kirjinta Yana shakarta kafin ya bude baki yace

"Yes sedai sa safe su ganni bayan kin gama Dani"

Murmushi tayi tana kokarin janyewa sbd yanda shinshinarsa ke kashe mata jiki hannuwansa na yawo jikinta kaman cakulkuli ta bude baki cikin son kwacewa da dariya tace

"AZIZ"

Tana rufe baki ya sake maida bakinsa cikin nata ya tsotseta da kyau kafin ya saketa Yana binta da kallo idanuwansa a kasalance.

Daqyar ya saketa ya wuce toilet ita kuma ta sauka kaman barauniya taje kitchen ta hado masa tea me karfi da short bread biscuits na shan tea tareda fruits ta dawo.

Taba barin kitchen karfe daya tana bugawa daidai lokacin Nicky ita kuma ta fito dauke da abinda yake hannunta tabi ta kitchen din ta fice zuwa bangarensu.

Motarta ta nufa ta bude ta dauko qaton galon na diesel da ashana ta rufe motar ta nufi bangaren Zaadens.

Ita kuma Jannah tana dawowan ya fito wanka kenan.

Ajiye tray din hannunta tayi kafin ta motsa yayi Sama da ita tace

"AZI....bata qarasa ba suka fada gadon taba jikinsa ya zagayeta da hannuwansa sbd shine a qasa itace a samansa.

Zubawa juna ido sukai Yana zagaye bayanta da hannuwansa Yana Shafa lafiyayyun cinyoyinta da suka bayyana dan rigarta data janye.

Ahankali ta bude baki zata kira sunansa cikin kasala yace

"Pls don't,youre killing me slowly da yanda kika fadan"

Murmushi tayi tana yin qasa da kanta ya dago fuskanta da hannunsa daya yai kissing hancinta Yana sake shakar qamshinta kafin ya saka kansa wuyanta yai kissing fatar wuyan.

Saukan lips dinsa a fatar wuyan nata ya sakata sake numfashi me dumi ya sauka akan fuskansa ya lumshe idanuwansa tsigar jikinsa na tashi gabaki daya.

Ayau sosai yake jinta ta yanda bazai iya tsallake yau bai mallekta gabaki dayanta ta zama cikakkiyar macen AZIZ LIMBA dan haka juyar da ita yayi ta dawo qasan ya koma samanta Yana zare rigar jikinta gabaki daya daga jikinta Yana zubawa farar lafiyayyan fatar cikinta ido zuwa kirjinta.

A daidai wannan lokacin ne karfe daya da hamshi da biyar ta buga,

Sama sama kunnuwan Jannah suka fara jiyo mata ihun Madam Sisi da hayaniyar iska kaman na hadari.

Dakatar dashi tayi tana ambatar sunansa ahankali cikin mutuwar jikin halin da suke ciki.

Idanuwansa ne suka sauka akan hasken dayake tashi saka ta balcony dinsa kaman na wuta.

Da mamaki ya miqe Yana saukowa gadon kafin ya isa window wutar tayi wani irin karfin gaske.

Hayaniyar mutanen dake gidan da securities ne yake tashi ahankali wanda sakasa qarasawa balcony din idanuwansa suka sauka akan wuta dake cin Bangaren masu aiki sosai.

Jannah wani irin mummunan mutuwar tsaye tayi idanuwanta na neman makancewa

Shikuwa da sauri ya saka kaya jikinsa ya dauko kayansa ya saka mata suka fito bata ko ganin gabanta wani irin gudun tashin hankali takeyi tana ambatar sunan Dad dinta da Ummah.

Ko da suka isa Dad dasu Maheer na fitowa cikin wutar a tsananin hali suna tarin azaba.

Kowa ya fito hankali tashe da tsoro,

Mama Nicky ta kalla wadda kai tsaye ta gane itace tayi aikin

Bata damuba kawai dai fatarta aikin kada ya zama na banza a garesu,

Falaq da fiddausi ma saurin taresu Sayd yayi duka masu aiki kowa ya fito hankali tashe.

Cikin tsananin hali Dad ya kalli Jannah dake tsananin rawar jiki yace

"Ina ummanku?

Shi ta kalla da sauri tana girgiza kai a rikice,

Maheer daya shiga firgici cikin daga mury yace

"Ina Umman take?

Ammar ne yahau ture kowa da sauri Yana dubata bai ganta a wajen ba baisan lokacinda yayi cikin wutar ba da karfi Yana kwala Kiran sunan Umman.

Securities ne sukai saurin riqesa

Jannah ta miqe da gudu tana dosar dakinsu tana kwala sunan Umman cikin tsananin kukan gaske da tashin hankali.

Riqeta AZIZ yayi yana cewa a riqe Maheer da Dad da sukai cikin wutar suma.

Damben gaske aka ringa yi dasu suna kwacewa amma anki sakinsu

Mama kuwa jin takeyi kaman ta qarawa wutar karfi da gudu takeji kowama ya huta.

Ammar ne ya sakarwa security daya mugun noshi ya kwace ya fada cikin wutar Dad na bin bayansa.

Nan Jannah ta sake haukacewa tana Kiran sunan Dad dinta da Umman kaman ranta zai fita.

Buga kofar su Dad suka hau yi da karfi Wadda ta bude da qyar bayan duk sun kona hannuwansu.

Suna shiga ummah da idanuwanta suka kusa rufewa akan idonta Dad ya sako kai yana nufota da sauri Ammar kuwa daukanta yayi gabaki dayanta suna kokarin fitowa garba ya fado ya dauki fatma Shima.

Suna fitowa Maheer ya kwace da karfe Yana nufosu ya karbi Umman sbd Ammar da dad din dake neman xubewa a qasa.

Yana karbanta Jannah dake ihun Kiran sunanta ya nufa ta fizgo da gudu itama tana zubewa gaban Ummar da Maheer ya kwantar a qasa gaban ABDULAZIZ AY LIMBA Wanda yayi mutuwar tsaye idanuwansa kafe akan fuskar dake gabansa kwance.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 38

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

*************
Wani irin haske idanuwansa suka cike dashi jinsa na daukewa daga sautin komai saina ihun Kiran sunan da Jannah da ahalinta ke yi,

Dumm kansa yayi Yana kasa motsa ko yatsa daya daga jikinsa ya bude bakinsa ahankali cikin wani irin sauti da slow yace

"UMMAH"

Falaq ce datake isowa gurinsa da gudu tana kokarin riqesa cikeda tsoron wutar ya tureta da karfi Yana ficewa hayyacinsa gabaki daya komai na jikinsa na tsananin daukan rawa ya isa gabanta da karfin gaske yana ture Maheer tareda kowannensu ya cakumota da karfi yana kallan fuskanta cikin karfin gaske yace

"UMMAH, UMMAH FATIMA.....

Mama da gabaki daya imaninta yake akan wutar batareda tasan nafito da Umman ba jin saukar muryansa a kunnuwanta ya amabaci Fatiman ya sakata juyowa da karfin gaske a rikice gabanta na mummunan faduwan data saka jikinta daukan rawa idanuwanta na sauyawa gabaki daya.

Ture Nicky da Madam Sisi tayi da karfi daga gabanta tana nufar inda AZIZ din yake kafafunta na hardewa ta kife qasa da karfi,

Da rarrafe jikinta na rawa ta iso gurin tana zubawa fuskanta Fatima idanuwanta dake cikowa da tsananin hawaye zuciyarta na cewa

"Fatima sai da kikai nasara akaina,
Fatima saida kika bayyana gaban AZIZ,
Fatima kin kasa tafiya ki barni da AZIZ sbd nice na cancanci zama uwarsa Ni danake da cikakken hankali,
Fatima bazaki iya rabani da AZIZ ba sbd na riga na zama uwar da bazai taba iya sauyawaba...
Fatima kin lalata komai."

Nicky ce ta iso da sauri gurin Maman ta kamota Zata tayar Maman da babu karfin komai a jikinta tanajin kaman taje da gudu ta fada wutar ta kone ta huta akan yanda zata iya fuskantar AZIZ akan bayyanar Fatima gidan.

AZIZ kuwa sake dago Umman yayi gabaki dayanta da karfi yana sake ture duk Wanda ya kusantota ya sake ambatar sunanta da karfin gasken daya saka idanuwanta budewa a wahalce suka koma suka rufe tana qarasa somewa gabaki daya.

Dad ne da babu karfi sosai a jikinsa sbd zafi da hayaqin wutar daya dakesu,

Ganin irin girgiza da riqon da AZIZ yayi mata Yana tare kowa da isa gareta ya sakasa tahowa ya ture AZIZ din da karfi dan ya saketa sedai ko gezau sbd ba qaramin riqo yayi mata ba gabaki daya ya fice hayyacinsa.

Ammar ma turesa ya hau yi jin Yana kiranta da Umman da suke kiranta Wanda duk a tininsu sbd Jannah ne yake kiranta hakan,

Maheer ma banbareta daga hannunsa suka hau kokarin yi suna kasawa,

Su uku suka tarar masa suna kokarin cireta Amma hakan ya gagara,

Wasu hawaye masu tsananin zafi da gudu ne suka fara gangarowa daga idanuwansa ya dagota da karfi ya rungumeta a kirjinsa qamqam Yana fasa kuka a gaban kowa me karfi da tsananin tsima zuciya sbd kukane da duk duniya babu Wanda ya taba ji yayi,

Cikin kukan ya sake ambatar sunanta da "FATIMAN ABDULAZIZ DA UMMITAH......
UMMAH FATIMA...

Cak Jannah da duka Zaadens suka tsaya daga kokuwar da sukeyi dashi dan basu hakura ba sai ya saketa,

Fatiman daya ambata ne ta AZIZ da Ummitah ya sakasu kallan Umman da wani irin sauri da tashin hankali me tsananin gaske wadda sukasan sunanta Fatima a bakin Mama,

Dad ne da Ammar a lokaci daya suka juya gurin Mama suka kalleta wadda ta rintse idanuwanta da sukai jajir hawaye na cikowa a cikinsu.

Maheer kuwa kai tsaye fuskan Umman tasu ya zubawa idanuwa jikinsa na daukan tsananin rawa sai kawai a take kamannin AZIZ LIMBA suka ringa bayyanar masa akan fuskan Umman da basu taba tsayawa suka lura da hakan ba sbd abune da ko a mafarkin sun haukace basu taba kawosa ba.

Jannah kuwa qanqancewa idanuwanta sukai cikeda yanayin da batasan ma ya zata fassaraba ta rarrafa gurinsa da sauri ta kamo fuskansa dake cikin wuyan Umman Yana kuka sosai..

Qwace fuskansa yayi da karfi yana sake maidawa wuyan mahaifiyarsa yana jin kaman yana motsi ba daidaiba zata bace daga gabansa.

Sake riqo fuskansa Jannah tayi da sauri hawaye na bin fuskanta muryanta na rawar tashin hankali tace

"Ummanah ce....

Girgiza kai yayi da karfin gaske kaman qaramin yaro jikinsa na sake daukan rawa yanayinsa na tsananta ya sake qanqame Umman yace

"Umman AZIZ ce,
Umman data haifi ABDULAZIZ ce,
Umman data haifawa AZIZ Ummitah ce,
Ummanah ce,
Rayuwata ce ita ba Umman kowa bace bazata....

Rungume Kansa Jannah tayi tana fasa kukan ganin yanda haukansa gabaki daya ta bayyana a gaban kowa hakama Umman na tsananin buqtaan taimakon gaggawa tace

"Umman AZIZ ce,Fatiman AZIZ ce,
Ummanka ce babu Wanda zai sauya hakan amma tana buqatan taimakon gaggawa ka bari a tafi da ita AZIZ"

Yana jin hakan ya dago da sauri Yana sakin Umman daga jikinsa ya miqe jikinsa na rawa ya dauketa sukutum gabaki dayanta yana barin gurin da ita da gudun gaske Yana qwala Kiran Sayd Wanda tini ya kira likitoci kusan uku duk suna hanya gashi basuda nisa.

Gabaki daya duk Wanda yake gurin mutuwar tsaye ce ta kamasu Musamman Nicky datake jijjiga sbd a gban idonta ko yanzu aikinta ya lalace lalacewan da kila dama irin wannan zatai wuyan samu,

Bata yadda da AZIZ nada wata uwar ba bayan Mama sbd tasan dai koma wacece wannan din Mama dai itace ta haifesa dan haka kallan Maman tayi jikinta na sake rawa da jijjiga ta bude baki zatai magana Mama datake jin jininta na qonewa batasan lokacinda ta daga hannu ta sauke mata wani lafiyayyan mari ba tana mata kallan tsananin baqin cikin shigowanta rayuwarta ma gabaki daya.

A rikice Nicky da rabin hayyacinta yabar jikinta sbd kanta daya motsa ta kalli Maman zatai magana Maman ta katseta cikin mugun yanayin na tafarfasa da cewa

"D farko bansan wace kaddarar takaini karbanki ba Sedai a yanzu na San mummunan kaddara ce sbd babu alkhairi ko daya a tattare dake,
Duk abinda kika sakawa hannu saiya lalace ya zama mugun Abu,

Kinsan ayau me kikayi?
Kinsan me kika janyo da wannan aikin da kika lalata mana?
A tinaninki zaki kashe matsalolinki ne a cikin wutar da kika Cinna?
To ki Sani dukkanin manyan matsalolin da suke kwance ne kika tayar mana Wanda wutar zata cinyemu,
Babbar matsalar dataci uwar tasu Zaadens ce kika tado mana wadda a yanzu sedai kowa yayi ta Kansa dan kuwa a yanzu babu sauki ko kalilan a lamarinmu sai kuka da baqin ciki."

Nicky data kasa yadda da faduwa cikin tafasar zuciya tace

"Mama bazan taba yadda da faduwa ba akan Zaadens,
Bazan taba barin.....

A tsananin fusace da tashin hankali Mama tace

"Kin San waye Fatima?
Kinsan waye mahaukaciyar Zaadens da kike fada koyaushe?
Kina ganin yanda suke tsananin sonta take sonsu??
To itace Asalin mahaifiyar data dauki cikin AZIZ LIMBA ta kawosa duniya,
Itace macen datafi kowace mace a duniyarsa da babu kamarta kuka babu Wanda zai iya cika gurinta a ransa har abada,
Akan Fatima AZIZ zai iya fito na fito da kowa,
Akanta ne idan ba mafita muka samo ba AZIZ LIMBA ya gama zama bawan Zaadens har abada sbd Fatiman da kanta ta zama Zaadens sbd auren Dzad ne a kanta....

Baya Nicky tayi tana faduwa qasa jikinta na tsananin rawa da shiga mummunan tashin hankalin da bata saka masa rana ba.

Mama ma datake jin tana neman haukacewa juyawa tayi ko gabanta bata gani tabi bayan AZIZ da Zaadens da sukai ciki tin dazu acikin tashin hankali.

Palo AZIZ ya nufa da Umman ko gabansa baya gani kaman zai kife suna biye dashi dukkansu suma kaman zasu kife din sbd basuda wata niya ko qarama ta daga masa kafa akan Fatiman dan haka wutarsu a riqe take.

Jannah ce take kwashe pillows din kujera Ammar da baida hakuri ya fizgosu gabaki daya ya watsar dasu qasa AZIZ ya kwantar da ita Yana kasa dauke idanuwansa akanta har lokacin jikinsa rawa yakeyi sosai kansa kaman zai buga hakama ya hana kowa tabata a cikin rashin hayyacinsa dayake ciki sbd gabaki daya duk Wanda yake gurin yasan ba AZIZ LIMBA bane a gurin wani AZIZ LIMBA dinne da basu sani ba dan haka Sayd daya san meyake faruwa yace subi komai a sannu idan ba hakan ba komai zai lalace dan AZIZ din yanzu baya Kansa.

Falaq da gabaki daya hankalinta yayi mummunan tashin da tsoro ya ciketa sbd ayau Daddynta ya tureta sa karfi har sai dataji rauni,
Kuka takeyi sosai a jikin fiddausi da itama ta dade da Sanin Mama ba itace asalin mahaifiyar AZIZ LIMBA ba to Amma shock dinta shine babu Wanda ya santa daga AZIZ din sai Mama kuma Mama ta dade da Sanin Umman na gidan duka lokacin nan tayi shiru Harma suke kiranta mahaukciya
To kadai Maman bata gane Umman bane??

Jannah ma daya hanata motsowa kusa dashi Sam jikin Dad dinta ta lafe tana tsiyayar hawaye zuciyarta cike fal da tsoron sabuwar kaddarar data bullo musu a yanzu na kasancewan Ummansu mahaifiyar AZIZ LIMBA Wanda tasan wlh komai AZIZ zai iya basu Amma bazai taba barinsu da mahaifiyarsa ba,

Zai durkusawa Zaadens qasa ya basu damar takasa Amma bazai taba basu Ummansa ba kaman yanda tasan Dad dinta zai rasa ransa da shi kadai ne ya rage masa Amma bazai rabu da Umman ba.

Hawaye masu tsananin zafi ne suka gangaro mata tanajin tsananin tausayin AZIZ din ganin yanda yake cikin rashin nutsuwansa da hankalinsa kwata kwata sbd ganin macen daya rasa tin Yana qanqaninsa,

Ya rasa kaunarta,ya rasa duminta,ya rasa kulawanta,ya rasa nutsuwar mahaifiyar,ya rasa walwala duk sbd rashin uwa mahaifiya,

Mama sunan uwa kawai take amsawa a garesa Amma babu shaquwa da kauna me zurfi da kusancin dayake tsananin buqata daga uwa shiyasa rayuwarsa take gabaki daya a baibai.

Maida idanuwanta tayi akan fuskan Umman ta kafeta da ido kaman bata taba ganinta ba kamanninta na bayyanar mata tanajin zuciyarta na narkewa sbd kaunar datake jin tanawa ummah me tsananin da babu sirki ta zuciyar Ummitah ce dake kirjinta da kuma kasancewarta uwar data haifi love of her life,
Uwar data haifi AZIZ LIMBA mutumin da bazata taba iya dena so ha har qarshen numfashinta.

Isowan likitoci ne ya saka AZIZ din miqewa tsaye Yana basu guri yana cewa kada su bari komai ya sameta zai basu komai na rayuwarsa.

Lafiyayyan bedroom din a cikin na palon aka maidata doctors din suka shiga.

Ana rufe dakin ya juyo idanuwansa jajir hannuwansa na rawa ya dago idanuwansa ya fara kallan Zaadens din daya bayan daya hawaye na ciko idanuwansa kafin ya tsayar da idanuwansa akan Jannah wadda take kallansa cikeda tsananin kauna tanajin kaman ta rage masa abinda yake ji a zuciyarsa na tsananin halinda baimasan yaya yakeji ba.

Shima kallanta yakeyi da dukkanin tsananin sonta da buqatanta hawayen idanuwansa na saukowa kan fuskansa...

Kasa riqe Kansa yayi ya iso inda take idanuwansa na rufewa ya janyota jikinsa ya rungume yana fasa kuka mara sauti Yana cewa

"Ummanah ta dawo gareni"

Hawayenta ne suka gangaro tana Manta kowa da komai ta rungumesa tana kokarin basa sassauci.

Dad da Maheer mutuwar tsaye sukai suna kallansu zuciyoyinsu na rawa da jijjiga,

Ammar da daman baya cikakken hayyacinsa bin bango yayi Yana fita waje sbd numfashinsa dayake sarkewa Yana neman rasa ransa yana fita waje y zube qasa wani irin kuka na zuwar masa Amma kirjinsa ya kasa dauka dan haka ya zube qasa yana dafe kirjinsa.

Mama dake tsaye itama mutuwar tsayen tayi sbd ganin sabon tashin hankali a gabanta AZIZ a jikin Jannah Yana kuka.
#MAMUH
#JAZIZ 2025
#LIMZAD 2025

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 39

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

***********
Qanqameta yakeyi kaman zai shige jikinta tamkar yaro qanqanin da baisan abinda zeyiba da neman sassauci a jikin wanda yake samun nutsuwa,

Sassaucin take kokarin basa ta hanyar sake basa daman rungumeta da kyau tana shafa bayansa duk da yafita tsayi sosai tana kokarin hana nata tashin hankalin kere nasa sbd duk yanda suke cikin tsananin shock da tashin hankalin me yake shirin tabbatar musu na cewan Ummansu itace Umman AZIZ LIMBA amma tasan nasa tashin hankalin da mummunan shock din ganin Matar daya shafe shekaru tin Yana yaro yana nema dole ya kere nasu.

Dad da tashin hankalin dayake ciki da kuma abinda idanuwansa ke gane masa zuciyarsa ta kasa dauka yana kokarin isa gurin Jannah ya fizgota Maheer da tasa zuciyan take radadi da bacin rai ya rigasa isa tareda kamo hannun Jannah ya janyota daga jikin AZIZ din da karfi Yana jefata gaban Dad dinsu daya dago ya kalleta da idanuwansa jajir zuciyarsa na sake shiga wani halin tsananin tsoro akan tashin hankalin d suke ciki.

Me AZIZ yake kokarin yi masa akan 'ya?
Shin bai gaji da wasa da zuciya da rayuwarta bane bayan duk abinda yayi mata ya kuma dankara mata saki?
Menene kuma sukai masa yanzu da zai sake lalata rayuwar Jannah ta hanyar kokarin dawo mata da sonsa,

Numfashi ya sauke me zafin gaske Yana kallan Jannah da fuskanta ke kallan qasa cikin tsananin tsoro da baqin cikin kasa riqe zuciyarta datai ta bari ta sakawa ahalinta shakku akan zuciyarta da zata iya sake jefasu wani masifar kaman farko data jefasu masifa akan son datake wa AZIZ LIMBA Wanda shine ya lalata komai.

Cikin sanyin jiki sbd damuwar dataci karfinsa Dad yace

"Kinsan me kikeyi Jannah?
Kinsan haramcin abinda kikeyi kuwa?
Karki manta ba aure tsakaninku a yanzu kuma babushi har abada sbd ba abu ne me yiyuwaba ba dan tamkar ma ya haramta ne dan mun haramta so yafi Miki kiyi gaggawar dawowa hayyacinki kafin ki saka raina mummunan baci"

Shiru tayi tana qasa da kanta tareda hadiye hawayenta da suka ciko idanuwanta tana janyewa gefe inda Maheer ke mata kallan mamaki dan kuwa kaman yanda Dad ya fada menene zai sake sakasu barin tabi raayinta akan duk Wanda takeso bayanma maganar aurenta da Ammar ta riga ta gama tsayuwa ba fashi har abada.

AZIZ da baya hayyacinsa cikakke baisan me suke yi ba bare fada sbd ya zube zaune a kujera dafe da kansa.

Tsit palon ya sake dauka kowa a tsaye da fargaba da tashin hankalin dake tsananta sbd farfadowan Ummah dake tattare da tabbatarda abubuwa da dama wanda zasu kawo sabon rikicewa a rayuwar kowa,

Shin da gaske mahaifiyar AZIZ LIMBA ce Ummansu shine tashin hankalin da Zaadens suke ciki Wanda idan hakan ta tabbata basajin zasu sake nasu matsayin a kanta tinda ta riga ta zama  mata kuma a uwa a Zaadens tsawon lokaci dan haka ba abu ne me yiyiwa ba kai tsaye su sake barin AZIZ LIMBA ya rabasu da abu me mahimmaci dan haka suke tsaye cikin rikici da tinani suna fatar ba hakan bane ya zamto sabanin tinani kawai aka samu da kamanni.

AZIZ LIMBA kuwa babban buri da tsananin buqatansa daya a yanzu kada wani abin ya samu Umman tukuna ta farfado ta kallesa ya samu kallan rahama daga idanuwan da sukafi kowane daraja a rayuwarsa,

Ummansa ko ya girma zata ganesa sbd kamanninsa da basu sauya ba,
Zata gane 'danta,jininta kuma hamma AbdulAziz dinta itada Ummitah koda kuwa tana cikin yanayi na gushewan hankali haryanxu.

Falaq ce data kasa isowa garesa tin dazu sbd tsoro ta daure ta iso ta zaune gefensa ahankali tareda kama hannunsa daya da duka hannuwanta biyu ta qanqame tana kwantawa jikinsa tace

"Daddy Ummansu Jan zata ji sauki ka kwantar da hankalinka dan Allah kaji"

Lumshe idanuwansa yayi ahankali Yana zagaye Falaq din da hannunsa daya ya rungumeta Yana sauke ajiyan zuciya ahankali batareda ya iya cewa komaiba.

Mama da kiris zuciyarta ke jira ta buga hakama jikinta gabaki daya kaman zai kama da wuta sbd zafin tashin hankalin daya gama kameta,

Tsoro da tashin hankalinta daya ne tak wato AZIZ,
AZIZ ne iya tashin hankalin datake tsoron rasawa ko shakkar fita a ransa datake fiyeda kowa,

Zaadens takejin sabuwar tsanarsu na cike koinanta sbd abinda tai gudun shine suka hadasa mata tareda qarin zasu iya fadawa AZIZ komai akan Fatima data kasa fda musu gaskiar wace ita,

Idan har suka bude baki suka fadawa AZIZ ko kalma daya akan yanda komai yake tsakaninta dasu sun gama lalata mata rayuwa sbd AZIZ zai cireta ne daga ransa Wanda tafi kaunar kowa ya mutu kafin a samu maganar fahimta a tsakaninsu harma a fada abinda tayi,

Bare bazata taba iya gani ko barin AZIZ ya samu shiri da Zaadens ba kaman yanda tasan zafin tsana da fushinsu na Nan fil a ransu saita dawowa da AZIZ tasa akansu ta yanda bama aure tsakaninsa da Jannah zai dawo ba dan kuwa irin son da Fatima kewa Jannah AZIZ zai qare ne gabaki daya akan Jannah da Fatima,

Duka batama fatan hakan ta faru adduarta da fatanta Fatiman ma kada ta tashi kwata kwata idanma ta tashi bata fatar ta dawo hankalinta shine lamarin zaiyi saukin sauki.

Nicky kuwa tana dayan palon t kasa qarasa shigowa sbd yanda kanta ke rawan rashin lafiyanta tana jin kaman ta Dora hannu akai ta kurma ihu kokuma ta sakawa 4&4 din wuta kowama ya mutu ta huta da wutar datake jin tana cin kirjinta tana tafasa jininta sbd batajin zata iya daukan ace mahaifiyar data AZIZ LIMBA itace a hannun Jannah tana riqo tamkar uwar data haifeta,

Kenan ko anan Jannah ta sake shan gabanta sbd zata sake samun AZIZ ko akan hakan ne,
Ita kuma fa?
Wa ta kama? Uwar da bata haifesaba Ashe ta kama wadda ta gama lalata mata komaiba itama a yanzu ta kanta takeyi.

Fitowan doctors ce ta saka kowa miqewa tsaye suna kallansu da dukkanin hankalinsu da nutsuwarsu,

"Bata cikin kowane irin mummunan hali yanzu zata farfado kowane lokaci inshallah so sai ta farfado zamu iya qarasa dubata da wasu aune aunen"

Shiru dukkaninsu sukai kafin Dad cikin damuwa yace

"Hope dai ba konuwa a jikinta koina"

Numfashi Dr ya sauke Yana kallan Dad din yace

"Eh babu a iya dai inda muka duba so banajin akwai konuwa koina inshallah"

Ajiyan zuciya suka sauke dukkaninsu palon Banda Mama data bar palon idanuwanta na cikowa da hawayen tsananin baqin ciki.

Dad ne da Jannah kai tsaye suka nufi dakin da Umman take sedai kafin su isa AZIZ ne yafara isa cikin dakin Yana zubawa fuskanta idanuwansa da har lokacin suke kasa gasgata itace a gabansa har cikin gidansa.

Zaunawa yayi gefenta tareda Dora hannunsa ahankali kan nata zaiyi magana su Ammar da Maheer suka shigo Dad kuma ahankali ya janye hannunta daga na AZIZ din Yana riqewa cikeda kulawa ya riqe cikin nasa Yana qin dagowa ya kalli AZIZ din sbd ko fuskansa baya son kalla kaman yanda su Maheer ma babu wanda ya kallesa.

Jannah ce ta saci kallansa cikeda fargaba taga ya dago jajayen idanuwansa ya zubawa Dad cikeda mamaki da wani irin dacin daya taso masa ya maida kallansa kan su Ammar yaga sun dauke kai suna sake tsananta hade fuska cikeda baqin cikin kasancewansu guri daya dashi suna shaqar iskan daki daya.

Hadiye radadi da bacin ransa yayi Yana kokarin kallansu da fuskan rahama ya miqe tsaye kai tsaye y zare hannun mahaifiyarsa daga cikin na dad din ya kallesa cikin ajiye komai yace

"Bansan tayaya mahaifiyar AZIZ LIMBA ta zama Ummah a zuriar Zaadens ba,
Bansan meyake faruwa ba anan Amma dai nasan duk duniya mahaifiyar data haifeni daya ce kuma itace Nan a gabana Wanda babu Wanda zai iya sauya hakan kaman yanda duk duniya babu Wanda ya isa ya sake rabani da ita idan ba Allah ba dan haka inaga abinda kaima kakeyi din haramun ne ga mahaifiyata sbd.......

Ammar ne cikin tsananin quncin dake cin zuciyarsa y katsesa da cewa

"Kana tinanin kai tsaye zamu yadda da ka Santa ne kafin ma a yadda da ita din mahaifiya ce a gareka??

Ba kaine ka fara ikirarin ka santa ba mahaifiyarka ce ta fara yi mana barazana da dukiya harma da rayuwar dan uwanmu akan mu bata ita tasan Yan uwant, ohh nama manta kudi tace mu fada zata siye mana Umman ta rabamu da qaya hkaa ta fada,
Kai kuma yanzu sai ka fada mana nawa ne naka farashin da zaka bayar akan siyanta kokuma kaima rayuwar Saleem din zaka dauka sbd ka qarasa gamawa damu??

AZIZ da idanuwansa sukai mummunan ja yana sanqarewa a tsaye da jin mummunan abinda Kansa yake kasa dauka bare fahimta.

Maheer ne ya karbe zancen da cewa

"Koma menene abu daya ne da zaka fara Sani anan shine Ummah tamu ce halak malak sbd matar mahaifinmu ce kuma uwa a Zaadens dan haka kasan abinda zai fito bakinka....

Cikin wata irin mahaukaciyar Muryan da baitaba Sanin Yana da ita ba ya daga hannu dukkanin jikinsa na rawa zai saukewa Maheer wani lafiyayyan Mari Dad ya riqe hannunsa tareda tsayawa gabansa ya kallesa yace

"AZIZ LIMBA ka koyi riqe fushinka sbd kada mu bayyana maka namu fushin abin zeyi muni dan haka gwara mu tsya a iya qiyayyar datake cikin kowannenmu a yanzu.....

Da wani irin tsananin fushin maganganun Ammar na farko dake kashesa yake jin saukan maganganunsu da bama yanda ko daya zai yiyu sbd Mama bazata taba gani ko sanin fatima na kusa dashi ba ta kasa fada dan abune da har abada bazai yiyuba,

Sai kuma maganar aure da akeyi na cewan Ummansa Matar wani ce ba waninma Dzad Wanda a tasa zuciyan be San matsayinsu ba a nasu Bangaren kuma ya San tsana ce zallah mara sirki,

Wayene ma ya isa yace masa ya auri mahaifiyarsa a cikin yanayi na ciwon rashin hankali?

Me suke nufi da wai Ummansa Matar Zaadens ce?
Tayaya ma hakan zata faru?
Bama abu ne me yiyuwaba dan kuwa yasan ba saukowa zasuyiba kaman yanda shima a yanzu baima karba aurenba bare se yaji Wanda ya bada ikon yin hakan.
#MAMUH
#LIMZADS

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 40

*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.

************
Jajayen idanuwansa ya dago ya saukesu akan Dzad Yana masa wani irin kallan fushi Yana kasa riqe dukkanin abinda yake ransa dayake riqewa sbd Jannah akansu Amma sun wuce limit na yanda zai iya riqe kansa sbd Ummah Fatima ta kere kowace irin darajar rayuwarsa ya bude baki Yana kallansu daya bayan daya da tsananin fushi kafin ya tsaida idonsa akan Dzad da yake ganin shine ma kadai yakai ya iya magana dashi yace

"Anan,a gabana, a cikin gidana a cikin kunnuwana da gaban idanuwana Mahaifiyar LIMBA ce ko Fatima sbd maganar Aure da tarkacen da yake cikinsa babu Wanda ya isa duk duniya ya tsaya gaban idanuwana yace mun kai tsaye shi mijin mahaifiyata ne Wadda batada lafiya hankali batareda na masa mummunan daurin da seya rasa nasa hankalin ba sbd girman laifin hakan,

Kallan Maheer yayi yace

"Kuna tinanin kunada mahaukata ne?
Mahaukacin ku yanada license na zama cikakken mahaukacin gasken?
Idan akwai cikakken daya isa ya rabani da mahaifiyata zan gansa ko shi waye"

Shan gabansa Maheer yayi Shima cikin tsananin fushin da bacin rai a bayyane yace

"Wannan kuma ba kaine zakai deciding ba Umman ce da kanta idan ta farka zata tabbatarda ita waye a gurin kowa daga Nan ne zakasan kai din ba kowa bane face AZIZ LIMBA dan kuwa ba Umman kadai ba ko Jannah ka saka kalla wlh nayi maka alkawarin ganin cikakkiyar haukar da kake ambatar Zaadens din nada sbd har abada Jannah ta gama dakai babu abinda zata sake yi da Wanda yayi sanadin rasuwar mahaifiyarta da baqin cikin ahalinta tareda salwantar da dan uwanta.."

Lumshe idanuwa AZIZ yayi ahankali Yana controlling da hadiye tsananin fushi da masifar dake quna cikin jininsa ya bude idanuwansa akan Jannah ahankali Wadda idanuwanta sukai jajir wani irin daci da ciwo ke cin kirjinta akan tashin hankalin AZIZ LIMBA da familynta da batasan yaya zataiwa kowannensu ba.

Magana yaso fada musu wadda har abada bazasu dena jin zafinta ba sbd idan ana maganar wani yayi sanadin rasuwar wani sunkai karshen marasa kunya da har bakinsu yake iya furta hakan sbd abu daya dashi kansa daya Sani shine bai dauki fansar daya kamata akansu ba sbd Mummunan son 'yarsu daya shiga gabansa ya dakatar da komai ya hanasa ganin sun karbi hukuncin daya kamata Wanda shine hukuncin kisa dan koda kowa bai karba hukuncin kisa ba Wanda shine asalin hukuncinsu to Ammar da Dzad zasu karba Amma ya hana barin hakan ta hanyar zabar musu hukuncin dayafi kowane sauki dan kawai kada ya dawwamar mata da baqin cikin rashinsu a rayuwarta,

A yanda sukaiwa Ummitah kisan gilla ko me gadin gidansu akaiwa wannan kisan ya tabbatarda wani labarin ne daban bare ace daya daga cikinsu ne Amma sunada bakin fada masa magana.

Numfashi ya sauke me zafin gaske kafin ya juya ya fice daga dakin dan zai iya kasa riqe zafi da tsanarsu shima daya danne yana kokarin gogewa tsawon shekarun nan da kuma bayyanar mahaifiyarsa a hannunsu Wadda zai iya musu komai akan hakan sbd sun basa sabuwar rayuwar da bai taba tsammani ba Amma kuma yaga alamar bama zasu taba samun fuskantar juna bada wannan fushin da qiyayyar ba sbd Shima a nasa bangaren abinda suke kokarin zuwa dashi bazai taba yadda ba dan Yama fisu jin duk abinda suke ji dannewa yakeyi Amma akan mahaifiyarsa gwara suyi fito na fiton.

Yana ficewa daga dakin Dzad ma ya fito haka dukkaninsu aka bar Jannah kawai Wadda ta rasa tinanin yi sbd kanta dayake toshewa.

Yana fitowa kai tsaye palon su Mama ya nufa Falaq da fiddausi na bayansa koda ya isa Nicky na tsaye tana bubbuga kanta dake neman bugawa,

Mama dake zaune idanuwanta jajir tana ganinsa ta miqe tsaye ahankali zuciyarta na neman fadowa sbd bugawa ta zubawa fuskansa da babu rahama ko kadan tana kallansa lokacin Sayd y shigo palon shima fuskansa jajir sbd tashin hankalin dayake qin qarewa a gidan.

Wani mugun 'daci da zafi tamkar na wuta AZIZ ya hadiye a maqoshinsa daya bushe ahankali kafin ya bude idanuwansa yaqi kallan Mama sbd maganganun Ammar Zad akan Maman dake yawo cikin Kansa suna neman haukatasa da bakinta yakeson ji ta fada.

Rawa hannuwansa ke yi ya bude baki a Karan farko daya hadesu gabaki daya gidan har Mama dayake banbanta girmanta akan kowa,

"Waye da waye ya San da Ummah Fatima na gidan nan?
Waye da waye ya taba ganinta?
Waye kuma ya taba magana da ita?

Shiru dukkaninsu sukai tsit kowa jikinsa na daukar rawan fargaba sbd yanda yake din d yanda yayi tambayar kai tsaye kowannensu yasan ba AZIZ LIMBA din bane wannan tsananin fushi da bacin ransa a bayyane yake da zai iya aikata komai akan duk wani me laifi lokacin.

Falaq ce da duk take cikin tsananin rudanin kasa gane gaskiar waye Mama waye Fatima a gurin Daddynta da Ummitah ta matso gaba ahankali tana kallansa tace

"Daddy ina ganinta duk naje gurin Jan Amma kafin na fara zuwa gurin Jan ban taba ganinta ba kuma haryanxu bantaba jin maganarta ba ni"

Fiddausi ma cikin sanyi daga inda take tsaye bayan Sayd ta bude baki tace

"Ina ganinta idan naje gurin Jan Amma na fara ganinta ne a lokacinda ta fara bugawa Mama kai.....

Qafewa yawu da numfashin Mama yayi ta rintse idanuwanta tana jin jikinta na mutuwa gefe daya tana kallan AZIZ da sauri wanda rufe idanuwansa ahankali ya budesu akan Nicky.

Nicky da gabaki daya ta rude da tashin hankali sbd bata taba ganin AZIZ a cikin wannan yanayin nasa ba a rikice tace

"Mama ce tafara zuwa gurinta acan nasan Ummansu Jannah ce"

Bai juyo ya kalli Maman ba saida ya tattare duka fushinsa ya saka a maqoshi kafin ya ambaceta Yana qin kallanta har lokacin sbd gudun yanda zuciyarsa zata karbi zancen da zai fito bakinta akan idanuwansa sbd zuciyarsa ta kasa yadda da har abada Mama zata ga fatimanta ta kasa bayyana masa bayan yasan yanda suke kaunar junansu.

Shiru Mama tayi tana kasa magana idanuwanta sunyi jajir sun kafe da tashin hankalin da bata taba saka ran zai risketa ba sbd tin a yanzu tana hango wata irin zazzafar tsanar da AZIZ zai mata Wanda bazata taba iya daukan hakan ba sbd ta San bazai taba iya cigaba da zama da ita ba zai raba kansa da ita ne a lokacinda take ganin babu wanda ya isa yaci amfaninsa idan ba ita ba sbd itace tai dawainiya dashi ta shanye baqin cikin da duk ya shiga da qunci.

Shirun mama ya saka jikinsa tsananta rawar daya saka kowa ja da baya suna sauke kai ya juyo ya kalli Maman da idanuwansa da babu kyan gani ya bude baki yana kokarin riqe girmanta dake idonsa har lokacin da da'a yace

"Mama kinsan da Fatima na Nan gidan tareda Zaadens?

Kinsan da Ummanah na 4&4 tin lokacinda kika dawo tsawon watannnin Nan?

Kinje gurinta?
Kinyi magana da ita?
Kinyi magana da Zaadens akanta?

Mama ban yadda da maganarsu data kowa ba taki kawai nakeson ji sbd kece kika San girma da mahimmacin Umma Fatima a rayuwata,
Kece kadai kikasan waye Fatima a duka fadin duniyar AZIZ LIMBA"

Bakinta na wata irin rawa hakama hannuwanta da kafafunta ta bude baki tana kallansa idanuwanta jajir tana kasa musawa sbd tsanarta da zata wuce misali da gyara a zuciyarsa tace

"Eh AZIZ nasan tana Nan Amma wallahi inason......

Wata dafar data saka console mirror din dake gefensa yayi Wanda ta sakasa fashewa da karfin gaske Yana yanka hannunsa sosai yayiwa mirron jikinsa na wata irin jijjigar data saka Sayd da Falaq matsowa da sauri zasu riqesa ya daga musu hannu jikinsa na tsananta rawa koina.

Mama na ganin hakan ta matsosa kafafunta na sake rawa idanuwanta n sake rinewa da rikicewa tace

"AZIZ walh da farko bangane ba inason tabbatarwa ne kafin na sanar maka sai ga....

Sarewa kafafunsa sukai Yana zubewa cikin glass din gurin da gwiwansu idanuwansa na rintsewa hawaye masu tsananin zafi na cikowa idanuwansa sbd bayan mahaifiyarsa data haifesa Mama itace uwarsa daya san haihuwansa ne kadai bataiba Amma zata iya bda ranta dan nemo masa duk abinda tasan shine rayuwarsa wato mahaifiyarsa,

Amma a Karan farko Mama ta basa shock din dayafi na Zaadens sbd su daman yasan zasu iya komai akan son kai da zuciya... itace ta farko data fara boye masa ganin Fatima....

Dafe kirjinsa yayi sbd wani irin azabar dayake jin Yana kasa dauka ya rintse idanuwansa Yana kasa magana sbd bazai iya yanke hukuncin Mama cikin fushi ba.

Falaq da sauri ta qarasa gurinsa tana fadawa jikinsa tana fasa kuka tana kokarin tadasa sbd hannunsa dake jini sosai tana Kiran sunansa da karfi.

Nicky ma gabaki daya tsoro ya rufeta jikinta wani irin rawa yakeyi tayi baya ta kasa matsowa sbd tsoron AZIZ din.

Maman ma hawayen baqin ciki da dacin zuciya ne suka fara gangaro mata tana son matsawa Amma fushin dake tattaredashi ya hanata hakan sbd kada ta tinzirasa aikata abinda baiyi niya ba akanta.

Sayd ne ya isa garesa Shima zai kamasa AZIZ din ya miqe Yana sake dafe kirjinsa yabar gurin baya ganin gabansa ya nufi stairs yana dakatar da kowa daga binsa.

Kallansa sukeyi cikeda kulawa da faduwan gaban kada ya fado sbd yanda baya gani harya haye saman ya shige palonsa ya rufe kofar.

Yana shiga suka fara jin qarar fashewan kaya da karfin gaske tareda glasses.

Da sauri Falaq ta yunqura zata bisa saman Sayd ya riqeta yana rungumeta ta fasa kuka tana cewa

"Daddy na zai sake illata Kansa,
Yana cikin qunci da damuwa,
Banason inga Daddyna a cikin irin wannan yanayin Ya Allah ka basa lafiya ka kawo nutsuwa da kwanciyar hankali a rayuwarsa"

Mama zubewa tayi qasa tana dafe kanta cikin hawaye da baqin ciki halin data saka AZIZ din da kuma tsananin tsanar Zaadens da Nicky dama duk Wanda yake rayuwar AZIZ din bayan ita.

Zaadens da duk abinda yake faruwa suna ji shiru sukai suma zuciyoyinsu a tafashe sbd tana sake tabbata dai Umma Fatima mahaifiyar AZIZ LIMBA ce,

Babu Wanda yayi farin ciki ko misqala zarratin da hakan,
Basa kaunar abinda duk zai sake hadasu da LIMBA,
Basa kaunarsa basa kaunar zuriarsa basa kaunar duk wani ma me kaunarsa tayaya yanzu kwatsam zaa ce Ummah itace uwar data haifesa?

Babu ruwansu da hakan tinda dai watsi yayi da ita suka samu suka tattala suka kaunata suka bata sunansu dan haka ba gudu ba ja da baya bazasu taba basa ita ba karshenta ma tana tashi tattarawa zasuyi su tafiyarsu da ita idan ma Yana ikirarin mahaifiyarsa ce to ai mijinta a yanzu yafisa iko da ita zasu nuna masa power da igiyoyin aure yake dashi ya gani ganin idonsa.
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 41

Jannah da sautin komai itama yake sauka a kunnenta rufe idanuwanta tayi tana jin zuciyarta kaman zata dena bugawa sbd tausayin AZIZ da jin ciwonsa cikin ranta,

Yana tsananin buqatanta ayanzu dayake cikin mummunan halin ciwonsa da duk saiya raunana Kansa rauni me Muni ma kila batareda kowa ya rungumesa ba ya basa sassauci.

Kofa ta kalla da idanuwanta da sukai ja itama tana Sanin acikin familynta kowannensu a yanzu qiyayyar AZIZ ta kere sonta a zukatansu ta yanda zasu iya illatata idan ta zabi zuwa garesa dan basa kulawa da sassaucin dayake nema.

Har karfe 10 na safe gidan babu motsin kowa bare ayi maganar breakfast sbd kowa na cikin damuwa ga Umma har lokacin bata tashi ba.

Me gidan kuwa kwata kwata duk zaman jiran da kowa keyi na saukowansa babu Wanda ya sake jin ko motsinsa.

Fatma da Amina ne a kitchen da Sisi sukai aikin abincin rana ga na safen ma baa ci ba,

Karfe 2 na rana duka Zaadens suka fice sallah tareda Sayd Wanda yake tareda su jiran tashin Umman wadda daga qarshe bayan sun kira doctor ya sanar musu tashinta suna sakaran ba kusa ba sbd hayaqin ya shiga lungs nata sosai ga kuma shock da suke tinanin ta shiga dan hakanne ma kowa ya samu damar matsawa zuwa fita.

Sayd ne cikin mutuntawa ya gabatar musu da lafiyayyun bedrooms dake palon qasa na bangaren kofar gaba bana qasan su Mama ba,

4 bedrooms ne a qasan Wanda Dad daya Jannah da fatma daya sai Maheer daya Ammar da Garba daya sbd Ammar din ya saba da yanda Garba ke kulawa dashi.

Basuda niya ko raayin cigaba da zama a 4&4 kwata kwata a yanzu ko me zai faru tafiya zasuyi Amma zasu jira tashi Umma dole Wanda hakan ne kadai ya sakasu karban dakunan.

Shigewa sukai dan wanka daga qaurin wutar da suke ta yi.

Lafiyayyun bedrooms ne masu komai da komai da hutu yake buqata ko beddings din da decos din are all classy dan haka ba bata lokaci sukai wanka suka fita sallah.

Suna dawowa anan palon Fatma da Amina suka kawo abincinsu suka jera musu a dining da duk abin buqata.

Jannah kuwa anan dakin Fatma ta kawo mata abinci ta tirsasa taci daqyar ta Sha maganin kanta dake tsananin ciwo tai sallah.

A inda tayi wanka anan wahalallen bacci ya dauketa se yamma ta farka da sauri ta nufi toilet tayo wanka ta fito daure da sabbin towels da Amina ta kawo daga store ta jere a dakin Umman Harma da dakinsu sbd Umarni da sabuwar doka da odar da Sayd ya bawa duka maaikatan gidan akan Zaadens Musamman Ummah da Jannah Wadda a yanzu babu abinda ya hada suna bare matsayinta da kowa a gidan.

Hijab ta saka dogo har qasa ta tayarda sallah a natse jikinta a sanyaye.

Tana idarwa ta miqe tana zare hijab din jikinta tana tinanin inda zata Samu kayan sakawa sbd kayansu gabaki daya sun kone.

Kofar dakin aka bude kai tsaye cikin nutsuwa da kamewa.

Juyowa tayi da sauri tana nufar hijabinta taji an rufe dakin ahankali cikin nutsuwa da sanyi.

Qamshinsa ne ya shiga hancinta me sanyi ta juyo da sauri tana rufe jikinta da hijabin data dauka tana kallansa da idanuwanta a sanyaye.

Fuskansa datai fresh ta kalla idanuwansa sunyi fada sosai a wuni guda kana kallansa kasan Yana cikin samun nutsuwar shekaru daya rasa tin yarinta ta ganin mahaifiyarsa da kuma qunci da ciwon abinda Uwarsa tai masa tareda damuwar dake neman sake bullo masa tsakaninsa da Zaadens daya yankewa Kansa fuskantarsu da duk abinda sukeji zai nuna musu uwa dai tasa ce.

Zuba mata idanuwansa yayi bayan ya kalli mahaifiyarsa yaga har lokacin bata farka ba,

Kallanta yakeyi cikeda so da kauna Harma da tsananin buqata sbd a yanzu da mahaifiyarsa take a hannunsa ko da auren Dzad akanta ko babu shidai burinsa da nutsuwarsa cikakkiyace zai iya fuskantar komai a yanzu hankali kwance.

Jannah ganin irin kallan dayake mata ya sakata jin jikinta yayi sanyi sbd tausayinsa da tinanin kamar baya cikin walwala..

Magana ta bude baki zatai ya rungumeta kai tsaye Yana sauke numfashi da ajiyan zuciya lokaci daya tareda jin dukkanin damuwa da kuncinsa na yayewa samun mata biyu da sune rayuwarsa a guri daya.

Duk duniya a yanzu kam yanajin babu abinda zai bata ransa ya quntata masa sbd baqin cikinsa ya qare sedai gwagwarmayar dawo dasu a hannunsa.

Ajiyan zuciya ta sauke tana jin farin ciki na mamaye zuciyarta jin Yana jero ajiyan zuciya a jikinta yana sake qanqameta ya bude baki ahankali cikin nutsuwa da sanyin murya yace

"A zuciyanki nine nayi sanadin mim....

Saurin dago fuskansa daga jikinta tayi tana Dora hannunta bakinsa ta hanasa qarasawa tana kallan cikin idanuwansa ta girgiza masa kai ahankali batareda tace masa komaiba.

Zuba mata ido yayi kafin ya bude baki ahankali yace

"Thank you Jan,Bansan yaya rayuwata zatayi ba a tsakanina da familynki Amma ki San abu daya da bazai taba sauyawaba shine ina sonki fiyeda rayuwana Jannah Zad,
Bazan taba iya rabuwa dake ba kome familynki zasu yi,.I can't live without you Jannah Zad"

Sama da dago ahankali tareda kai fuskanta gap da tasa tai kiss din gefen fuskansa ahankali tareda bude baki tace

"I hate you AZIZ LIMBA"

Wani kyakkyawan murmushin da ita kadai ke ganinsa fuskansa ne ya subuce masa ya sake Yana kallan fuskanta da dukkanin idanuwansa ya kama fuskanta ya hade da tasa Yace

"Thank you baby"

Murmushi tayi tana kokarin janyewa ya sake dawo da ita jikinsa Yana saka hannuwansa cikin hijabinta Yana shigar da ita jikinsa yakai bakinsa ya ya zaro harshensa ahankali ya lashi lips dinta Yana sake Shafa wuyanta zuwa kirjinta da towel yake daure.

Jin Yana kokarin kunce towel dinta tayi saurin saka hannunta akan nasa tana dafesa tareda girgiza masa kai ahankali tana nuna masa kofa.

Hakan datai ya sakasa sake sakin wani kyakkyawan murmushin Yana matseta jikinsa yace

"U are mine kinsan da hakan?

Girgiza kai tayi cikin tsokana tana boye murmushinta..

Sake matseta yayi cikin jikinsa Yana kunce towel din jikinta ba tareda ta ankara ba ya shige cikin hijabin Yana hade bakinsa da nata cikin hijabin tareda yin baya ahankali ya jingina da kofa ya saka hannunsa daya ta baya ya sakawa kofar key Yana dauketa daga qasa ya zageye qugunsa da qafafunta ya samu cikakkiyar daman samun bakinta da kirjinta yanda yakeso.

A cikin hijab din tafara kokarin dakatar dashi sbd jin yanda numfashinsa ke fita cikin nutsuwan samun yanda yakeso da kuma shiga duniyar jin dadinsa.

Ita kanta jin takeyi tana neman rasa kanta sbd yanda yake shafarta Yana lasar fatarta tareda kirjinta da harshensa me dumi dayake tada tsikar jikinta.

Fuskansa ta kamo ta dakatar dashi tana kallansa ahankali cikin sanyi da mutuwar jiki ta bude baki tace

"AZIZ....

Bakinta ya tsurawa idanuwansa da suka sauya da laushi ya sake kai bakinsa ya bata light kiss Yana cewa

"Jannah zad bazaki taba zama ta kowaba har abada sai AZIZ LIMBA shi kadai...

Ratsata kalmarsa tayi ta kama fuskansa da hannuwanta biyu ta kai bakinta zatai kissing hancinsa ya kama lips dinta ya tsotsesu ahankali Yana sauketa qasa tareda daukan towel dinta ya tayata daurawa ta cikin hijabin daidai Nan akai knocking kofar dakin.

Fitowa tayi hijabin tana kallan kofar da sauri gabanta na faduwa.

Bai kalli kofarba Hankalinsa kwance ya nufi mahaifiyarsa zuciyarsa na sake samun nutsuwa da ganinta ya zauna gefen gadon Yana gyara Mata rufa ahankali ya sake jin zuciyarsa fes.

Jannah ce ta isa kofar tana daidaita kanta gabanta na tsananin faduwa da bugawa ta bude kofar.

Dad ne da Ammar dan haka ta janye gefe ahankali tana basu hanyar shigowa.

Kallan AZIZ Ammar yayi cikeda mamakin ganinsa a dakin kafin ya maida kallansa ga Jannah Wadda gabaki daya ta kasa dagowa.

Dad ma Jannah din ya kalla baice komaiba ganin AZIZ din yaga Umman ma bata farfado ba ya juya ya fice.

Bin bayansu tayi kamar munafuka ta wuce dakinsu gurin Fatma sbd shirun da suka mata tasan zafi da magana ne a cikinsu.

Dad damuwarsa ninkuwa tayi sosai sbd yaga alamar AZIZ zai iya samun nasarar Jannah a Karo na biyu dan haka gwara suyi gaggawar daukan matakin hakan.

Da daddare ma baby wanda yaje main dining room na gidan cin abinci daga Falaq sai fiddausi sai Nicky kuma wadda takejin ma gabaki daya batada lafiya a dan jin take kaman jininta yayi qasa dan haka ta sauko cikeda tsoro taci abinci sosai jikinta har rawa yakeyi su Falaq na binta da kallon mamaki.

Dad kuwa bayan sun gama cin abincin da babu wanda yaci da dadin Rai kallan Jannah yayi kai tsaye babu walwala ko sauki a fuskansa yace

Bazaki kwana a gurin Fatima ba ki kwana a daki tareda fatma kuma zuwa gobe idan Umman bata farfado ba keda fatma zaku wuce kauye kafin muzo daga baya.

Dagowa tayi da sauri sedai ta kasa kallansa tayi shiru tareda gyada Kai ahankali.

Maheer da Ammar da sukafi matsuwa goben tayi ta bar gidan kallanta sukai Maheer yace ku kwanta da wuri sbd tafiyar safe zakuyi.

Miqewa tayi ta wuce daki jikinta na tsananta sanyi dakuma fargaban yanda AZIZ zaiji zancen da yanda zai iya reacting.

Har karfe 11 batai bacci ba tana zaune shiru ga Fatma tayi bacci.

Miqewa tayi ta shiga wankan data kasa jiki a sanyaye tana fitowa ta batada kayan sakawa dan haka ta fito sanyeda hijab zataje dakin Maheer ta aro ko shirt dinsa ta saka sbd bazata iya kwana da towel ba.

Tana fitowa kuwa Maheer din zai wuce dakinsa zai bar palon cikin sanyi ta kirasa.

Juyowa yayi ya kalleta Yana cewa

"Jan keda zakuyi tafiyan safe shine bakiyi bacci ba"

Sunkuyar da kai tayi idanuwanta na cikowa da hawaye son fada masa abinda yake zuciyarta amma ta kasa sbd tasan sabuwar fitina ce zata kullu.

Cikin zafi da fushi yace

"Idanma akwai wani abu a ranki Jannah akan AZIZ LIMBA kiyi gaggawar ciresa sbd har abada bazamu sake hada zuria da shi ba,
Babu kalman JANNAH ZAD da AZIZ LIMBA har abada gwara kiyi gaggawar sakawa ranki hakan sbd wannan Karan munfi son mu danne wuyanki da kanmu damu bari hakan ta sake faruwa shashasha kawai"

Wucewa yayi cikin fushi yabar gurin batareda Yama tsaya jin bayanintaba yabarta tana hawaye masu tsananin zafi.

Juyawa tayi tana kokarin barin palon taji an kama hannunta ahankali cikin sanyi tareda juyowa da ita.

AZIZ ne da kansa kuma duka abinda Maheer din ya fada a kunnensa dan haka baice komaiba ya saka hannunsa Yana share mata hawaye a natse ba damuwan komai a fuska ko ransa sbd abinda ya Sani ayau shine Jannah Zad saita hada jini da AZIZ LIMBA idan akwai wanda hakan zai kashe saiya shirya mutuwa.

Daukanta yayi a natse yabar palon da ita yana girgiza mata Kai alaman ta dena kuka.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 42
07019691719

Gidan tsit yake babu kowa sbd kowa y riga ya shige da masu ciwon Rai da masu damuwa da masu kuka da masu baqin ciki duka kowa ya shige idanma basuyi bacci ba to kowa na can na jinyar abinda yake zuciyarsa.

Samansa ya wuce da ita suna Isa bai direta koina sai bedroom dinsa Yana kallanta har lokacin hawayenta sun kasa tsayuwa sbd harda faduwan gaba kawai takeji.

Numfashi ya sauke ahankali tareda zaunar da ita a sofa zauna kusa da ita Yana kama hannunta cikeda nutsuwa da kulawa ya bude baki hankalinsa kwance yace

"Kinci dinner?

Dagowa tayi ta kallesa tana sake zama abar tausayi ta bude baki tace

"Banajin yunwa shiyasa banci ba"

Hannunsa daya ya saka ya shafi fuskanta Yana kasa dauke hannunsa daga fuskan Yana jin kaman sonta zai illatasa sbd yawansa a zuciyarsa yayi yawan da zuciyar kaman bazata iya dauka ba,

Baisan wane irin so ne yakewa yarinyarba Wanda yake jin kaman son yaqi isarsa ya kasa kwatantasa..

Wayarsa ya juya gefensa ya dauka a natse ya saka Kiran Sayd.

Dauka Sayd din yayi cikin girmamawa sbd baiyi bacci ba dan yanzu ne ya dawo daga dauko nurse din da zata kwana da Ummah ya kuma kaita har dakin Umman dan haka Yana dauka kai tsaye AZIZ din cikin kamewa yace

"4&4 na buqatan something light to eat da fruits may b"

Kashe wayar yayi tareda juyowa ya kalleta itama shi ta juyo ahankali ta kalla jin koyaushe Yana ambatarta da 4&4 Wanda a yanzu take tabbatarda da gaske date din da aka daura aurensa da ita ne.

Miqewa yayi sbd baiyi shafai da wutri ba ya nufi gurin sallansa daman jallabiya ce a jikinsa fita yayi sake dubo Ummansa ya samu Maheer na qayyadewa matarsa raayinsu na iska da zasu mamakin rayuwa indai suna alfahari da raba Jannah da AZIZ LIMBA.

Tayar da sallar yayi a natse ya fara.

Zuba masa idanuwa tayi tareda tallafe fuskanta tana jin itama tata zuciyan na kasa daukan tsananin son datake masa sbd ita nata son tana jinsa ne daga ranar farkon data fara Dora idanuwanta akansa,

Tana son AZIZ LIMBA da dukkanin jini da ruwan dayake yawo a jikinta,
Batasan irin son dayake mata ba Amma dai ita tasan bazata iya rayuwar da babu sa a cikinta ba,
Tana sonsa a baya,tana sonsa a yanzu kuma tana sake cigaba da sonsa koda zai dena sonsa bazata iya qinsa a zuciyarta ba sbd a cikin tsokar dake bugawa a kirjinta asalin sonsa yake da sonsa tsokar kirjinta ta rayu dashi aka halicceta.

Cikowa idanuwanta sukai da hawaye datake kasa tarewa na sonsa harma batasan ya sallame sallan ba sai jin hannunsa tayi cikin nata ya kamata ya miqar tareda janta har inda yake sallan ya kalli cikin idanuwanta Yana ganin yanda sonsa ke dawainiya da ita ya saka hannu ahankali ya Shafa fuskanta Yace

"Nayi Miki alkawarin AZIZ LIMBA na Jannah Zad ne har abada,
AZIZ LIMBA baida amfanin komai a gurin kowace macen da ba Jannah Zad ba"

Hannunta ya Dora akan kirjinsa Yana kallanta yace

"Abinda nake ji Jannah bana fatar kiji irinsa sbd nawa yayi yawan da zai Miki illa idan kika jisa"

Sunkuyar da kai tayi tana kasa kallansa,

Tambayarta yayi tayi shafai and wutr dinta?

Girgiza kai tayi har lokacin bata dago ba ta kallesa.

"Zakiyi?? Ya tambayeta

Gyada Kai tayi tana cewa tanada alwala.

Gyada Kai yayi tareda juyawa ya dauko mata wata farar shirt dinsa ya kawo mata ta saka ta cikin dogon hijabinta batareda ta cire ba.

Rigar ta sauka har cinyoyinta kadan dan haka towel din jikinta ta ajiye ta fada sallar sbd hijabinta ya kai har qasa sosai harya zuba.

Sallar tayi a natse cikin koyarwan addini kafin tana gamawa ta miqe kenan wayarsa tayi haske alaman kira.

Wayar ta dauka a natse tareda nufar makeken balcony dinsa dayake da girman gaske harda lafiyayyan swimming pool.

Tsaye yake Yana shakar fresh air dayake ratsasa ta Kai masa wayar.

Sayd ne dan hk ya dauka a natse batareda yayi magana ba.

Shima Sayd kai tsaye ana dauka yace

"Ga abincin 4&4 a kofa"

Kashe wayar AZIZ din yayi Yana jefa wayar kan couch ya kama hannunta suka fito.

Kai tsaye palon suka nufa yana isa ya bude kofar kai tsaye.

Fiddausi ce dauke da tray babba a natse ta gaidasa tana shigowa.

Kai tsaye table ta nufa ta ajiye ta juya ta fice zuciyarta fal farin cikin ganin Jannah a dakin.

Tana fita ya rufe kofar Yana kama hannun Jannah din suka zauna,

Meat balls ne da salad warm milk da zuma a cikinta sai kuma fruits din da aka yanko mata masu sanyi da tsafta.

Akan qafafunsa ya zaunar da ita bayan ya zare mata hijab yana daukan plate din meat balls din da fork ya fara bata a baki tana karba a natse tana ci tana kallansa ta bude baki tace

"Thank you"

Murmushi me kyau daya qarawa fuskansa wani irin kyau da kwarjini ya sake yana cigaba da bata a natse da tsananin kulawa.

Glass cup din warm milk din ta dauka da hannunta ahankali takai bakinta Tasha ahankali sosai kafin ta ajiye tana ce masa ta koshi.

Ajiye plate din hannunsa yayi Yana zero tissue ya goge mata bakinta.

Fruits din ta dauko da hannunta tana nuna masa da ido idanuwanta akansa.

Girgiza mata Kai yayi alaman no baya ci,

Girgiza kai tayi itama alaman no bata yadda ba sai yaci.

Sake girgiza kai yayi yana murmushi me tsananin kyau Yana kallanta.

Bude baki tayi tana dariya ahankali tace

"You sure??

Gyada Kai yayi Yana cigaba da murmushi..

Pineapple ta dauka ahankali takai bakinta ta saka tana kallansa tai mata wani irin taunawa ahankali Wadda gabaki daya ruwan pineapple din suka gangaro daga bakinta suna kokarin sauka jikinta...

Wani mayen kallo ya yi mata Yana kai bakinsa kai tsaye yana karbe ruwan suna sauka cikin bakinsa ya lumshe idanuwansa Yana budesa akan nata idanuwan datake kallansa tana dariya me kyau.

Tin daga qasan bakinta ya fidda harshensa me dumi da qamshin fresh lemonMint ya bugo mata daga cikinsa ya fara lashewa Yana matsota jikinsa ya manne kirjinsa da Nata Yana lumshe idanuwa ahankali.

A bakinta ya isa ya bude idanuwansa ya kalli bakin kafin ya zira harshensa a cikin bakin cikin sanyi da nutsuwa Yana karban pineapple din daga bakinta Yana dawowa da ita nasa bakin ya hadiyeta batareda ya tauna ba sbd ta riga ta fara tauna masa ita.

Kokarin zame bakinta takeyi tana dariya ya hanata ta hanyar girgiza mata Kai Yana lumshe ido ya zagayeta dakyau da hannuwansa Yana juyota dakyau suna facing juna bayan ya zagaye bayansa da kafafunta.

Idanuwansa ya gangara dasu ahankali kan rigar jikinta data kwanta a kirjinta sbd sanyin daya saukar mata ya tsayar da idanuwansa akan tsinin kirjinta da babu bra a jikinta kuma rigar is transparent batama Sanin ba.

Ganin inda yake kalla ya sakata jin wata matsananciyar kunya da faduwan gaba ta daga hannuwanta ahankali zata rufe kirjinta ya riqe hannuwan Yana kallan fuskanta da kunyarta ta bayyana sosai tana kasa kallansa.

Bakinsa yakai cikin wuyanta yayi kissing ahankali Yana saka hannuwansa masu sanyi a cikin rigarta ya shafi shafaffen cikinta taja wani irin wahalallen numfashi mara sauti tana qanqame hannunsa daya.

Cibiyarta ya Shafa Yana sake saka kansa cikin wuyanta gashin jikinsa na tashi ahankali.

Sama yayi da hannunsa cikin wani irin yanayi me sanyi da nutsuwa ya shafi kirjinta Yana sauke numfashi me karfi a wuyanta daya saka jikinta daukan dumi take tana neman yin baya ya tarota Yana baya da wuyanta ya sako Kansa cikin rigarta daga qasa Yana rikitata da wasu mahaukatan kisses da tsotsa a ciki yana sauke mata numfashi masu zafi akan duk inda harshensa ko bakinsa ya sauka.

Rawa jikinta ya fara tana qanqame hannuwansa daga zagaye da ita tana neman rasa numfashinta sbd yanda yake sarke mata tana jin wasu irin shock tako ina.

Ta wuyan rigar ya fito da kansa Yana sake kama gashinta yayi baya da wuyanta cikin yanayi na nisa dayake sake samun Kansa ya saka kansa wuyanta zuwa kirjinta Yana abinda yake zare notikan Kansa daya bayan daya.

Rawan da jikinta yakeyi jikinta na sake daukan dumi zuwa zafi ya sakasa dago kansa Yana bude jajayen idanuwansa fes akanta baya ko ita gani sosai sbd nauyin da idanuwansa sukai..

Fuskanta ya kamo da hannuwansa biyu ya kama bakinta da nasa ahankali Yana hade bakinsu harshensa na isa cikin bakinta ya zuqo bakinta da dukkanin imaninsa ya hadiye yawun da sukabi maqoshinsa suna Isa cikinsa suka qarasa balle duk wata hakuri da nutsuwarsa yaji kawai yana loosing control na komai bayan na yamutsa jikinta ya cakuda ta..

Hannuwansa biyu ya saka bayanta batareda ya saki bakinsa da nata ba ya yaga rigar da suke cikinta Yana wurgi da ita gefe ya dauketa sama a jikinsa yana sake tsotsan bakinta da wani irin zafi Yana nufar bedroom da ita.

A gaban Ctable ya fara sauketa Yana Fizge rigar jikinsa yayi wurgi da ita Yana rankwafowa ya saka bakinsa s cikinta ya sauke lips dinsa akan Mararta Wanda bata dan lokacin Da tai baya ba tana rasa gabaki daya kanta ya tarota Yana Shafa cinyoyinta da hannuwansu masu sanyi Yana Dora bakinsa a zallan fatar kirjinta Yana mata abinda ya sakata fasa kuka me sauti tana riqe kansa dan karfi jikinta na tsananta rawa.

Yanda yake shafa cibiyarta zuwa samanta ya sakata bude baki da wani irin kuka zata amabaci sunansa Amma sautin ya kasa fita sbd numfashinta daya dauke cak jin Yana rabata da iya qaramin abinda ya rage a jikinta ya dagosa a hannunsa yakai hancinsa yayi masa wata irin fitinanniyar shaqa Yana lumshe ido gabaki daya notikan da suka rage masa suna fizgewa ya jefar dashi Yana daukanta gabaki daya ya isa lafiyayyan gadonsa da ita ya kwantar Yana bin cinyoyinta da wani mayen kallo kafin ya miqa hannunsa yayi wurgi da bedside lamb da haskenta ne ya haske dakin ya rage saura daya wadda haskenta baida wani yawa ko kadan.

Dagota yayi jikinta na tsananta rawa tana kasa motsawa bare kwatar kanta ya sake sake bakinsa a nata cikin zafi Yana mata tsotsan datake tabbatarda ayau babu sauran abinda ya rage mata....

Irin yanda yake bata wani fitinannen kissing Yana sake baya da wuyanta da kafafunsa ya bude kafafunta gabaki dayansu Yana samun damar Kansa a tsakiyar kafafunta.

Abinda bata taba sanin masifa da balai bane taji Yana ratsata cikin wani karfin da tasan ba AZIZ LIMBA dinta bane.
#MAMUH
#JAZIZ LOVE
#ZAADENS
#LIMBAS
#2 BBS
#NICKY
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 43
07019691719

Bata iya tsayawa jin inda azabar zata tsayaba sbd gabaki daya ta fice hayyacinta tama zare gabaki daya jikinta wata irin fizga ya fara tana fasa kuka me karfin gasken da dakin ta dauka gabaki daya sbd tinda Mimi ta haifeta bata taba jin azaba me ratsata irin wannan ba Musamman daya fara bata karfinsa na namiji lafiyayyen da bai taba sanin mace ba a rayuwarsa shima ga wani irin abinda yakeji Wanda bai taba jinsa ba ko a yanayi na haukansa bai taba jin motsin gaske a cikin kwakwalwa da barqonsa ba sai ayau,

Zarewa kansa yayi gabaki daya hakama tinani da hankalinsa gabaki daya gushewa sukeyi Yana rasa kansa tsananin sonta da abinda yake samu da ji a tattare da ita a matsayinta na macen data fara saninsa ya Santa suka kunto juyewan kansa gabaki daya ya ringa nuna mata karfin gaske da Yana buga Kansa da wani irin karfin gaske da hannu daya sbd jin kaman ana bikin mahaukatan Aljanu a cikinsa...

Kuka takeyi sosai na fitan rai da neman sauki da sassauci Amma babu sauki ko sassauci tako ina sbd tako ina tamkar ba AZIZ LIMBA bane.

A daidai lokacinda yake sake rasa kansa wani hayaqi yaji tamkar Yana fita kunnuwansa da suka dauke jin komai na duniya dip sai wani mahaukacin numfashinsa dayake sauka a kunnenta hawaye na bin gefen idanuwanta bata iya motsawa...Wani irin abin da yake kokarin rabasa da ransa yaji ya taso masa tin daga tsakiyar bayansa zuwa mararsa daya sakasa daga hannu ya sakarwa glass door din balcony dinsa dayake har gurin jikin gadonsa a daidai kuma inda suke wani mahaukacin dukan daya saka glass din wata irin qara me karfin gaske da gabaki daya gidan ya dauka Yana watsewa waje.

Ya saki wani irin kuka me hade da ihu Yana mata wata irin qanqamar data kusan rabata biyu ta qarasa macewa a jikinsa numfashinta na sarkewa.

Dukkanin Wanda yake gidan sautin qarar fashewan kofar ya samesa wasu a cikin bacci wainda basu iya bacci ba kuma a kunnuwansu Amma babu wnda ya fito sbd a yanzu kowa ya fara koyan saurarawa da kyau tukuna.

Ammar ne daya kasa bacci a cikin Daren zaune yake Daram kirjinsa na masa wani irin matsanancin ciwon da yakejin ayau tsananin kewan mahaifiyarsa da Mimi,

Ciwon dayake ji a kirjinsa ciwo ne dayake jin numfashinsa na toshewa idanuwansa sukai jajir ya kasa rintsawa ko kadan.

Garba daya kasa bacci sbd halinda Ammar din yake a ciki a bayyane yake sbd yanda idanuwansa sukai jajir.

Tashi yayi jin qarar ya nufi kofa ya fito Ammar din na bin bayansa da kallo idanuwansa na cikowa da wasu zafafan hawaye masu dacin gaske suka gangaro daga idanuwansa yanajin a Karo na farko kewan tasa mahaifiyar yasa Yana jin inama ya bita a yanzu ya huta da radadin dayake ji yana nauyaya kirjinsa...

Kuka ne Mai karfin gaske da wani irin sauti me ban tsoro suka taho masa ya cusa kansa cikin kafafunsa jikinsa na wata irin sanyi Yana yi Yana qanqame jikinsa dumin jikin Uwarsa data barsa a duniyar da baida asalin ubansa daya yafesa bai taba nemansa ko buqtaan son ganinsa ba tana cike kirjinsa da ciwo me tsananin gaske.

Jin Yana neman rasa numfashinsa ya miqe yana hada hanya ya fito Shima yana fita harabar gidan gabaki daya batareda duba da Daren daya tsala ba.

Garba ne ya isa da sauri gurinsa yana tarosa jikinsa sbd yanda Ammar din ya zube akan gwiwansa yana dafe kirjinsa.

******Tsawon mintina ya dauka a jikinta qanqame da ita kafin ya fara kakkarwan sanyin dayaji Yana ratsa har cikin qashinsa.

Bude idanuwansa da suka bude dakyar yayi ya zubawa fuskanta datai jajir har lokacin hawaye ne ke gangarowa gefen idanuwanta dake rufe sun kumbura sosai.

Numfashinta dake fita ahankali ya Shaqa cikin hancinsa Yana lumshe ido karfin jikinsa na dan dawowa ahankali.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.