Kalbim Book 2 Complete Hausa Novel
Reading file: KALBIM BOOK2.txt
Chapter 3 of 5
Cigaba Daci tayi tana Jin dadi abarta ta dauki mango juice din dake cup Tasha sosai ta juyo ta kallesa ita ya zubawa kyawawan idanuwansa masu kashe jikin Mai kallansu yana kallanta cikeda kulawa da kauna me sanyi.
Murmushi tayi ta miqe ta dawo kan kafafunsa ta zauna suna facing juna ta debo Indomie din me tsayi da baa karyaba gurin dafawa ta nufo bakinsa da ita tace ya bude baki.
Cikin idanuwanta ya kalla bai musa na ya bude mata bakin ta saka Masa Indomie din tana murmushin mugunta sbd yajin dayake cikinta.
Hadiyewa yayi da sauri yana kallanta da idanuwansa da suka sauya tsabar masifar dayaji ta masifaffen yaji ya bude baki zai yi magana ta dauki mango juice takai bakinta ta cika ta ajiye tana Dora bakinta akan nasa tana basa ahankali yana sha yana lumshe idanuwansa da har sun Dan sauya sbd bayason yaji gaskia ko kadan yana sakasa zafin ciki.
Sassauci ya samu na abinda yaji bayan data basa juice din ta tsotse Masa yajin tas ya lumshe ido yana sauke ajiyan xuciya cikin sanyi.
Zufa ne ya da tsatsafo a goshinsa ta dauki tissue ta goge Masa ahankali tana sake debowa takai bakinsa tana dariya.
Cikin sanyi ya bude baki yace
"Is this a punishment or......
Katsesa tayi da cewa
"Yes Mr Husband,
Kwana nawa no calls,no massages bare zuwa....
Wani murmushin wahala ya sake yana marairaice Mata fuska kaman ba Shiba zaiyi magana tace
"No,no just take your punishment in peace AZIZ LIMBA"
Bude bakin yayi ta saka Masa ya cinye yana daurewa idanuwansa da goshinsa na nunawa sbd idonsa da yakeyi Dan ja goshinsa Kuma yana Dan fidda qananun zufa kadan.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee
Book 2
Chapter 56
Dariya takeyi tana basa yana cinyewa ahankali yana kallanta da idanuwansa cikeda kauna da shauqin yanda take dariyarta ransa na sanyi da ganin dariyan da farin ciki a fuskanta.
Tausayi ya Bata cikin yar dariya da tsananin kaunarsa ta dauki ruwa me sanyi takai bakinsa ya girgiza mata kai yana kallan bakinta data basa juice dashi ta sake murmushi tana cewa
"Zaka Sha anan?? Ta fada tana nuna bakinta da yatsanta kaman wata qaraman yarinya mara wayo.
Gyada kai yayi Shima yana kallanta idanuwansa gwanin tausayi.
Fruits ta janyo ta dauki watermelon me sanyi sosai jajir da ita takai bakinta ta tsotsa ahankali kafin ta kamo fuskansa da hannuwanta biyu ta Dora bakinta akan nasa ta saka Masa ciki direct tana kallan idanuwansa daya lumshe yana karba cikin sanyi da samun nutsuwa.
Sauko daukowa tayi tana sakawa bakinta ta sake basa ya karba yana zagayo qugunta dake zaune kan kafafunsa.