A Rubuce Take Complete Hausa Novel
Reading file: A_Rubuce_Take_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 1 of 101
_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM_
*_A RUBUCE TAKE !!!_*
(K'addarata)
*Huguma*
Arewabooks: huguma
Free page 01
Babban falo ne,wanda yake malale da marron din carfet mai taushi da kuma saitin kujeru kalar labulen wadanda suka yiwa falon qawanya,a tsare falon yake,ta yadda duban farko kuma kai tsaye ba zaka dauka falon tsohuwa bane,saboda ya wadata da kayan alatu na rayuwa bakin gwargwado.
Daga tsakiyar falon,mamallakiyar falon ce zaune saman carfet din,babbar macace wadda gashinta mai tsaho da kuma santsi ya fara bayyanar da furfura saman sumarta,kana iya hangen hakan sakamakon gocewar daurin dankwalin dake kanta,fara ce sol har yellow takeyi,tsufanta bai boye kyan siffa da take dashi ba,wanda da alamu ta sameshi ne tun daga zamanin quruciya kawo yau,kana kallonta kasan ba cikakkiyar bahaushiya bace,hakanan kammanninta bana fulani bane.
Daga gabanta kuma wata matar ce da suke diban kamanni da ita,saidai nata shekarun gaba daya ba zasu rufa talatin ba,ita dinma fara ce sol kamar matar dake zaune kusa da ita,wanda kana dubansu zakasan cewa 'ya da uwa ne,yaro ne saman cinyarta tana shayar dashi,dattijuwar mahaifiyar tata kuma tana daga kayan dake gaban nasu
"Duk da kayan sunyi kyau humaira,amma gaskiya nafison wadanda sukafi wadan nan tsada,Banason siyawa widad kaya masu sauqin kudi,gwara masu dan tsada da inganci" mai da dubanta halimatu tayi ga kayan tana sake qare musu kallo duk kuwa da cewa itace ta siyosu da hannunta,kayan irinsu ta siyawa yaranta,ta siyama widad din irinsu ne a nata zaton shine qarshen abinda zatayi ta burge ummu,saita maida dubanta ga dattijuwar
"Ummu,yanzu duk kyan wadan nan kayan basuyi miki ba?" Kai ta girgiza
"Basuyimin ba,kuma tunda nace basuyimin ba ai sai a canzo ko?,tunda dai kudina na saka zan siya,ba kudin wani bane" baki halima ta tabe tana sanya hannunta guda daya tana tattara kayan gefe,zuciyarta cike fal da bacin rai,akwai maganganu da yawa a ranta,amma tasan bata isa ta fadesu ba,yanzu yanzu rai zai iya baci indai akan widad ne
"Kin karba min kudin a wajen yaayan?"
"Yace sai ya dawo zai bayar na ajiye miki" sake baci ranta yayi,wannan karon ta gaza boyewa
"Uhmmm,Allah sarki,to Allah yasa suna da rabon saka ankon" kallonta ummu tayi ba tare da tace mata komai ba,idan da sabo ta saba da irin wadan nan dabi'un,ta rasa me yasa suka gaza fahimtarta,tana ganin son rai ne kawai da son kai irin na dan adam.
"Latifa!" Ummu ta waiwaya bayanta inda qofar kitchen dinta yake ta qwala kira,daga ciki aka amsa sannan mamallakiyar sunan ta fito,wankan tarwada ce,mai matsakaicin jiki,a nutse ta qaraso
"Gani ummu"
"Shiga dakina saman pillow akwai purse dita ki daukomin" amsawa tayi da to sannan ta juya.
Saidai bata ko kai ga isa dakin ba,ihu ya karade gidan cikin wata siririyar murya,ihu ne sosai hade da kuka.
Da sauri Latifa ta dakata da tafiyar,sannan ta waiwayo tana duban ummu,itama ummun ita take kallo,fuskarta cike da tsoro
"Ummu kamar muryar widad fa" kai ta jinjina da sauri
"Haka nake shirin fada nima"
"Yo wace idan ba ita ba?,kaf gidan nan waye yake wannan tabarar idan ba ita ba?" Dauke dubanta ummu tayi daga kan.haliman zuwa ga ladifa,wadda tuni ta fara nufar qofa
"Yawwa,dubamin ita don Allah latifa"
"Yanzu kuwa" ta amsata tana ficewa daga falon.
Yaronta halima ta kwantar a gefe sannan ta miqe itama tabi bayan latifan tana qunquni cikin ranta.
Babbar harabar gida ne wadda ke dauke da interlock shimfide a ko ina,duk da irin girman harabar gidan,jikin kowacce katanga data zagaye gidan dake dauke da sassa sassa guda biyar shukoki ne da.flowers da sukabi bangon gidan suka zame masa ado.
Daga bakin daya daga cikin sassan gidan wasu daga cikin ma'aikatan gidan ke tsaye,daga inda kake kana iya hangota,yarinya ce da duka duka ba zata wuce shekara goma zuwa sha daya a duniya ba,farace sol,irin farin nan me cakude da surkin jaa,ma'abociyar yalwatacciyar suma me santsi data sauko har zuwa bayanta ta kuma bazu har saman kafadunta saboda tsallen da take faman yi tana kuma dage maroon din doguwar rigar dake jikinta,manyan idanunta cike da hawaye da suke saukowa saman kumatunta wasu na zirara har gefan dogon hancinta da ya gauraye da majina da hawayen
"Babu komai fa widad,na gaya miki na cire shi tun dazu" wata mace dake tsaye a gafe sanye da riga da zani na atamfa ta fada tana qoqarin riqe yarinyar.
Dai dai lokacin latifa ta qaraso halima na biye da ita
"Meye haka?,me ya faru?" Yayi tambayar tana nufar widad da keta zabga tsalle da kururuwar kuka
"Tana tsaka da barci a falona bayan sun gama guje gujensu,kawai ina kitchen ni da marka na jiyo ihunta,da nazo sai tace wai kyankyaso ne ya shige mata riga,dana duba sai naga ashe qwaro ne dan qarami,na daukeshi aka fitar dashi,amma tace kyankyaso ne,nayi duban duniya ban ganshi ba" tsaki halima taja
"Iskancin banza da wofi ne da zallar tabara data yi mata yawa,wuce mu tafi kafin na tsitstsinka miki mari" ta fada cikin tsawa
"A'ah dakata a duba matan halima" latifa ta fada tana tsugunna wa gaban widad din,ta dage rigar tata da kyau sannan tace
"Kalli ki gani,babu komai a jikinki" cikin tsoro dubi fararen qafafuwanta,ganin ba komai din kamar yadda latifa ta fada,saita gyada kanta,saidai kuma har yanzu batabar kukan da take ba.
A gaba halima ta sanyata tana ta faman sababi m,wannan ya sake tunzura kukan widad din,har suka isa qofar falon ummu.
"lafiya ko?,me akayi mata?" Ummu ta fada idanuwanta da hankalinta gaba daya yana kan widad,tambayar data yi mata sai ya zamana kamar an tunzura ta,cikin sassarfa ta shige falon,tana kuma isa ta fada jikin ummun tana sake sakin kukan.
"Me kuwa akayi mata banda tsoron banza da wofi da take dashi,wallahi ummu sakalcin yarinyar nan ya fara yawa,haba" halimatu ta fada cikin huci tana neman saman kujera ta zauna kamar zata fashe
"Kin taba gani haka kawai mutum yana kuka ne?,ke me yasa kike haka?"ummu ta fada tana jifanta da harara
"Kyankyaso ne ummu yabi ta jikinta,an cireshi amma ta dauka bai fita ba" latifa data shigo ta sake yima ummu bayani tana dosar kitchen.
Waiwayawa ummun tayi tana jifar halimatu da harara
"To kinji,amma shine zakice kukan banza takeyi?,bayan kinsan widad da tsoro,kinsan kuma halittarta ce a haka?"
"Da sakalci wallahi ummu,haba don Allah,ko nabiha da take qanwarta bata wannan abun sai ita shafaffa da mai"
"To anji,saiki rufawa mutane baki hakanan" ummun ta fada tana maida hankalinta ga widad dake kwance saman cinyarta tana share hawaye
"Sannu kinci abinci?" Kai ta girgiza alamun a'ah
"Anty madina ta zuba mana,sai nayi bacci"
"Shikenan,tashi maza kije latifa ta zuba miki,idan miyar tayi miki yaji ta zuba miki wadda takeyi yanzu tunda naji kamar ta soyu,ki biya bandaki ki wanke fuskarki,bazan sake bari kije ko ina cikin gidan nan ki kwanta bama bare irin haka ta sake faruwa" miqewa widad tayi a hankali ta soma barin wajen,sai data shiga dakin ummun ta wanke fuskarta kamar yadda tace matan,ta cire rigar jikinta saboda jiqewa da tayi ta saka wata,riga da zani ne,da qyar ta iya daura zanin saboda rashin iyawa da rashin sabo sannan ta wuce kitchen wajen latifa.
"Halimatu,banason irin wannan dabi'ar nasha gaya miki,idan baku tausayawa widad ba bai kamata ku sata a gaba ba"
"Nifa ba a gaba na sakata ba ummu,sakalcinta yayi yawa ne,fisabilillahi duk cikin gidan nan wace ake nunawa gatan da kike nuna mata?,ai ba ita kadai bace jika a gidan,sannan ma girma takeyi fa,nan da shekara uku tsaf xa'a iya tayar da batun aurenta,niba tsangwamarta nake ba,so nake naga ta gyara" ido ummu tadan zuba mata na wani lokaci kafin ta janye dubanta daga gareta,ta fuskanci ba zata gane ba
"Allah ya kyauta" kawai ta sake cewa,tasa hannu ta janyo purse din da latifa ta ajjiye mata,ta bude ta fidda 'yan dubu dubu ta lissafa ta miqa mata
"Gashi,ki lissafa ki cire kudin da zaa qara na kayan da zaki canzo din,ragowar ki siya ma yaran sauran abinda ya rage" hannu biyu tasa ta karba tayi mata godiya,duk daba haka taso ba,ta rasa me yasa ummun take kasa dai daita widad da sauran jikokinta.
Sanda ta shiga kitchen zamanta tayi wajen latifa bayan ta zuba mata abinci,tana ci suna hira,sai ka rantse da Allah ba ita ta gama sambada ihun ganin kyankyaso ba,tana ta zubawa latifa surutu ita kuma tana biye da ita,wannan yasa akwai shaquwa sosai tsakaninsu,kusan tana daya daga cikin wadanda basuson kukanta cikin gidan.
Sai data cinye tas sannan ta ajema latifa kwanon ta sauka daga kujerar data hau kai ta zauna
"Kizo ki wanke hannunki mana kafin ki fita" latifa ta waiwaya tana ma widad magana,wadda tuni ta kusa qofa tana sude hannu
"Ina zuwa,zan wanke a wajen anty madina,na manta na baro alawar madarata dazu a can,Allah yasa su faruqu basu shanyemin ba" bata ko sake tsaiwa sauraron latifa ba tayi qofa abunta.
Su uku ne yanzun zaune a falon sabanin dazu,anty halimatu,ummu da kuma wani baqon daban.
Matashin saurayine fari ne shima kamar yadda na lura da kusan mafi yawa na launin fatar jama'ar gidan farare ne,yana da sassalkan gashi mai santsi gami da duhu,kamar yadda sumar qabilar larabawa ko buzaye suke da ita,sanye yake da shadda dinkin zamani da ya zauna masa sosai a jikinsa,kanshi babu hula,hannunsa riqe da wayarsa yana dannawa,gefe daya kuma suna hira da ummu da anty halimatu.
Turus widad tayi tana kallonsa,ta tsareshi da idanu duk da babu wanda ya ankara da fitowarta a cikinsu,dubansa take tana jin wani haushi yana cikata,tsaki taja a hankali don kada su jiyota,sai kuma ta tura baki gaba kamar zata saki kuka.
,juyawa tayi kamar zata koma cikin kitchen din,amma kuma saita sauya shawara,saboda tasan indai ta koma din ummu tasan tana can kuma zata kirata ta fito,abinda bata so din kenan,sai ta dawo tana duban bayan kujerar falon,akwai hanya da zata sadata har qofar falon,don haka ta duqa ta fara tafiya a durqushe ta bayan kujerun,gabanta yanata faduwa,fatanta Allah yasa kada ummu ta ganta.
A hankali ummu ta waiwaya zuwa sashen kujerun,motsi take jiyowa,saita sauke idanunta zuwa qasan kujerun,fararen qafafuwan widad ta hanga,dariya taso subuce mata amma saita danne,ba tare da kowa dake wajen ya ankara da abinda ke faruwa ba tace
"Widad!" Idanunta na kan qofar falon,ba zaka zaci ta ganta ba,cak widad ta tsaya tana zare manyan idanuwanta waje,gabanta yana faduwa,tana jin kamar ta juya ta koma,amma kuma idan tace zata koma din asirinta zai tonu
"Widad,ko bakya jina ne?" Ummu ta sake kiranta tana kallon sashen da alamu suka nuna a nan take a tsaye,saddaqarwa tayi,ta tabbatar ummu ta ganta,don haka sai kawai ta miqe tsaye,fuskarta a daure,ta tattare dan qaramin bakinta ta turoshi gaba,sannan ta fara takowa zuwa inda suke.
Dukkansu suka bita da kallo,halimatu ta tabe baki tana dauke kanta,haushin widad din yana sake kamata,ummu kuwa girgiza kai kawai tayi,cikun zuciyarta tana cewa
"Allah ya kyauta aikin quruciya".
Ta bangarenshi kuwa da kallo ya bita,ya kafeta sosai da idanuwansa,irin kallon da sautari abokansa kan masa dariya,su kuma ce sukam basuga abun kallo ga qwaila kamar widad ba,tun tana tsumman goyonta Allah ya jarabceshi da soyayyarta,har yau kwanan gobe kuma babu abinda ya canza a zuciyarsa game da ita,saidai ita din da baiga alamun koda sakewa dashi tattare da ita ba bare akai ga zancan soyayya,soyayyar da yake da yaqinin bata santa bama,batasan kuma mece ce ita ba,shi yake saka ran ta koya daga gareshi,saidai bata sakewa dashi bare ta bashi wannan damar,tako ina bashi da matsala,yasan zaya sameta za'a bashi ita kamar yadda yake muradi,amma kuma babbar matsalar daga gareta ne.
"Bakiga mutane ba ba zaki gaishesu ba?" Ummu ya fada tana hade fuskarta tsam waje daya,duk yadda takai ga gantanta widad da nuna soyayyarta a gareta,amma bata da sassauci wajen tarbiyya.
Kamar wadda aka sheqawa mari haka ta waiwaya gareshi
"Yaya mahfood ina yini?" Tattausan murmushi ya saki yana kallonta,kanta babu dankwali kamar yadda ya santa,bata qaunar daura dankwali sam
"Lafiya lau widadun ummu,ya makaranta?" Bata amsa masa ba,saita juya ga ummu tana bata rai
"Gani ummu" ummun na shirin miqewa tsaye tace
"Bani nake nemanki ba" saita miqe a abunta tana riqe da hijabinta a hannu
"Muje ki gyaramin wardrobe dita kafin ki wuce gida" ummu ta fada tana yin gaba.
Miqewa halimatu tayi ta saba yaronta a kafada tabi bayan ummun tana cewa
"Har yau ita widad din dana koyawa yadda akeyi bata koya din ba kenan?"
"Nidai ba wannan na tambayeki ba,in zakimin kimin,idan kuma fashin baqin naki zakiyi ki barmin kayana,ko intisar tazo sai tayimin" jin ummun ta fara mita saita tsuke bakinta,tabi bayanta kawai din kawai,sai falon ya rage saura su biyu.
*_DOGUWAR TAFIYA CE,WADDA KE QUNSHE DA TARIN DARUSSA,TAFIYA CE MAI DAUKE DA WANI IRIN SALON KISHI,GOGAYYA CE DA FAFATAWA TSAKANIN MABANBANTAN MATSAYI BIGIRE GAMI DA MATAKI NA RAYUWA_*
*_Ta fita zurfin karatu_*
*_Ta fita yawan shekaru_*
*_Ta fita wayo dabara da siyasa_*
*_GOYON KAKA CE_*
*_SAKALTACCIYA_*
*_ME QANANUN SHEKARU K'WARAI_*
*AKWAI TAZARA MAI TARIN YAWA A TSAKANINSU,KWATANKWACIN SAMA DA QASA*
*AMMA DUK DA HAKA TA CITA DA YAQI*
*GARIN YAYA?*
*_Kin karanta HANGEN DALA?,to ba shakka wannan tafiyar ta fishi zafi darussa da kuma ilimi a cikinta(in sha Allah)_*
*_ku taho kawai muje,kuyi jumurin bibiyata,kamar yadda aka saba har kullum,babu gaggawa cikin tafiyata_*😄✋ðŸÂ½
*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*
*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*ðŸâ€Â¥Ã°Å¸â€Â¥Ã°Å¸â€Â¥Ã°Å¸â€Â¥Ã°Å¸â€Â¥
0022419171
Maryam sani
Access bank
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*ðŸâ€Â¥
*_A RUBUCE TAKE!!!_*
(Kaddarata)
*HUGUMA*
Free page 02
*MAAB LUXURY HOME*
*_idan kaji gangami akwai labari_*
*_SABUWAR DUNIYA CE_*
*ALFAHARIN UWAR GIDA*
*FARINCIKIN AMARYA*
*MAIDA TSOHON GIDA SABO*
*DUNIYAR QYALE QYALE*
*KAYA NA ALFAHARI DA TAQAMA*
*_Ba iya kyawun idanu suka tsaya ba,harma da ingancinsu da kuma qwarkonsu,ka dade kana mora kana kece tsara a tsakanin tsararraku da sauran mutane_*
*nasan zaku tambaya ina ne nan?*
*MAAB LUXURY HOME*
😊*Kai daga jin sunan ma babu tambaya*
*_duniyar qawata muku gidajenku ku ganku kamar a wata nahiya ko wata duniyar_*
*Suna kawo kayan kitchen rankatakaf manya da qananu*
*Kayan gado dana parlor*
*Kai...suna kawo kowanne nau'in kayan ado na cikin gida*
*Karkiyi qasa a gwiwa kuma kada kiyi sake ma dafe,maza garzaya ki nemesu a*
_adress dinsu dake No 22 Ahmadu bello way,kano state_
*Ko kuma kuyi order din kayanku kuna daga gida ta shafinsu na instagram*
@maabluxuryhome
*Facebook*
@maabluxuryhome
*Ko ku nemesu ta lambar wayarsu kamar haka*
08034631010
*Kyau inganci da rahusa shine takenmu*😊😊ðŸ¤ÂðŸ¤ÂðŸ¤ÂðŸ¤Â
____________________________
waiwayowa yayi yana dubanta bayan ficewarsu gaba daya,maficin da ummu ta tashi ta bari ne riqe a hannunta tana tsige adon jiki,fuskarta a dinke tsaf,yakanyi.mamakin yadda take masa,kamar wata qatuwar budurwa,ya rasa dalilin da sam bata son su zauna waje guda ko su hadu,saidai har yanzu zuciyarsa na bashi nutsuwar cewa quruciya ce kawai da rashin sanin ciwon kanta,da zarar ta sake hada hankalinta zata fuskanceshi?
"Amma sai yaushe?,lokaci qara quracewa fa yake" zuciyarsa ta gaya masa,sai ya dan gyada kai
"Soon in sha Allah" ya fada yana bawa kansa qwarin gwiwa,qwarin gwiwar da kusan kullum itace madogararsa
"Widad" ya kira sunanta
"Na'am" ta amsa a cunkushe ba tare data kalleshi ba,murmushi yayi
"To kidan kalleni mana?,ummm,ke da zaki zama matata?,so nake ki saki jiki da yayan naki" manyan fararen idanuwanta ta daga tana kallonsa,wani haushi da kuma tsanarsa suka saukar mata,lallai yaaya mahfood ta tabbata dan iska ne,ita yakewa zancen ta zama matarsa?.
Yadda ta zuba masa fararen idanuwan nata sai yaji dadi cikin ransa,don takan jima bata tsaya ta kalleshi ba,wannan ya bashi qwarin gwiwar janyo ledar daya shigo da ita wadda ke shaqe da kayan kwalliya,kasancewar ya santa da son kayan ado da gayu ya tura gabanta
"Ga kayan kwalliya nan 'yammatan ummu,sai ayita shafawa ko?" Dauke idanunta tayi daga kansa ta mayar kan kayan,saita dalla wa kayan harara,ita zaiwa wayo?,ya dauka bata da hankali kenan,haka kawai,bayan ummu tasha gaya mata ko zama tayi kusa namiji ciki zatayi,shine zai wami bata kayan kwalliya?,to bai isa ba,tana gama wannan tunanin ta miqe abinta ta nufi qofa da saurinta.
"Zo mana widad.....widad"ya fara qwala mata kira,gudun kada latifa ko ummu dake daki su jiyo shi,su kuma sanyata dawowa dole saita fella da gudu ta qarasa ficewa,don ta lura shi kadai ne zaifi mata saurin barin sassan.
Bata tsaya ko ina ba sai sassan anty madina,taja birki tana zabga haki,dai dai lokacin da dukka yara yaran gidan da suke da shekaru irin nata ke zaune a falon anty madina,kaf cikin matan gidan ta fisu qarancin shekaru,tana da faran faran da son mutane,tana yawan jansu a jiki gami da biyewa shirmensu,wannan yasa kafatanin yaran gidan kowa ke sonta,yake kuma son zama a sassanta.
Dago kai tayi tana duban widad,muhassana ce kwance a cinyarta diya ga qanwar mahaifin widad tana mata tsifa
"Lafiyarki widad?,irin wannan cin burki haka?" Guri ta samu kusa da khalisa ta zauna tana maida numfashi,sai kuma ta bata rai, idanuwanta sukayi rau rau suka ciko da qwalla
"Yaya mahfood ne"
"Mahfood kuma?,biyoki yayi?" Kai ta girgiza tana turo baki gaba,ita sam sam ma batason maganarsa,yanzu su mahassana zasu fara tsokanarta
"Wai cemin yayi matarsa" tana fadin maganar qwalla na gangaro mata,qaramin murmushi anty madina ta saki,ta rasa wanne irin rashin haduwar jini ne haka tsakaninsu,duk wanda ya kwana ya tashi yasan yadda mahfood din ke qaunar widad,hakanan kowa yasan yadda take gudunsa,bata qaunar hada inuwa dashi
"To banda abinki mene ne don yace miki matarsa iyi widad?,bakiga su zahira ba aure za'ayi musu?,kuma daga su sai ku?" Kafin anty madina ta kammala bayaninta widad din ta saki kuka harda turje qafafu,baki anty madina ta sake tana kallonta gami da jan salati,yayin da su muhassana suma ke kallonta suna dariya
"Tsaya,bakya sonshi ne shi yayan naku?" Kai ta gyada
"Wallahi ni bana sonsa Allah"
"To ya isa,ki share hawayenki,an gama maganar,ba wanda zai baki shi" dif kukan ya tsaya,ta tashi ta zauna dai dai tana goge qwallarta tana kuma hararar su khalisa kan dariyar da suke mata
"In sha Allahu sai su abba sun baku dauda" dariya sosai anty madina ta tuntsire da ita,duk da quruciyarta wani lokaci idan tayi wani abun kamar babba,dauda shike wankin gidan,na kowanne sashe,daga qauye yazo a gidan aka riqeshi
"Bakinki ya sari danyen kashi" khalisa ta fada tana dariya
"Saidai naki bakin" widad ta fada tana sake harararta,dole anty madina ta shiga fadan ta raba,ta kuma janye musu hankalinsu da wani abu na daban.
Qememe taqi komawa sassan ummun,duk da ummun ta aiko latifa har kusan sau uku amma taqi komawa,zatonta mahfood yana nan bai tafi ba,wayo ummun keso tayi mata don ta dawo,har abbanta yazo ya tafi bata koma din ba,son samunta ma tayi kwananta nan wajen anty madina cikinsu farisa,amma kuma tana tsoron kyankyaso,kada yayi mata irin yadda yayi mata daxun,har sai data fara barci sannan latifa tazo ta tafi da ita bayan ta tasheta ta sakata a gaba.
Tana shiga dakin ummu ta haye gadonta taja bargo ta duqunqune sosai harda cusa kanta cikin pillow,tun tana kasa kunne taji shigowar ummu har bacci yayi awon gaba da ita.
Washegari ummun bata ce komai da ita ba,saidai ta bata ledar kayan kwalliyar tace ta dauketa taje ta adanata,aifa kamar jira take,saita dire cup din da take shan tea dashi ta saki kuka
"Allah ni bana so,banaso ummu" tana turje qafarta a qasa
"Hukumullahu" ummun ta fada a ranta tana zuba mata idanu,wannan abun na widad din kuwa na qare ne?,kullum abu kamar ma sake ci gaba yakeyi?,kafin takai ga sake cewa komai akayi sallama falon,ta dauke kanta daga widad ta maida gareshi taba amsa sallamar.
Babban mutum ne ko ace magidanci,wanda kallo daya zaka masa kasan danta ne daga tsatsonta ya fito,a nutse ya qaraso falon yana kallon widad da fuskarta tayi sharkaf da hawaye
"Ke kuma da baki rabo da rigima me akayi miki?" Ya fadi yana neman wajen zama,baki ummu ta tabe tana girgiza kai
"Don anyi maganar mahfood ne" saita zarce da gaya masa abinda ya faru jiya.
Maida dubansa yayi gareta yana nazartarta na wasu daqiqu,shima kallon quruciyarta yakeyi,yasan ita ke dawainiya da ita,don idan a wani gidanne ko zancan aurar da yayunta da za'a aurar yanzu ba'a fara ba bare ita,to amma haka tsarin yake,a haka kuma dukka suke tafiya
"K'aniyarki" abba ya fada yana tsuke fuska
"Don gidanku mahfood ba babanki bane kike masa irin wannan?,maza tashi ki dauki kayan ki adana su" fuskarta jiqe da hawayen ta miqe ta dauki ledar,sai tayi hanyar fita da ita
"Ina zaki?,nan ne dakinki?" Cikin muryar kuka ta waiwayo
"Anty madina zan kaiwa...."
"Eh itace ke iya jurewa shirmensu ai" ummu ta karba zancan tana qarashewa abba bayani,sai baice komai ba,wannan ya bawa widad damar ficewa.
Tana tafe ita daya tana sharar qwalla,maimakon sassan anty madina,sai tabi siririyar hanyar da zata sadata da parking lot na gidan,tasan can ne babu kowa,don duka samarin gidan masu fita kasuwa kawo yanzu sun fita din,sai su 'yan makarantar da suke shirin komawa ranar litinin,sune daliban da aka yaye daga primary school zasu wuce zuwa qaramar secondry jss one.
Dan bencin da ake ajewa a wajen lokaci lokaci ta haye ta zauna a kai,sai a sannan ta buda ledar tana duba abinda yake ciki,kayan makeup ne sosai irin wadanda takeso,batayi mamaki ba,don uncle mahfood din ya jima da sanin zabinta da kuma duk wani abu da takeso.
Sai data fiddosu tsaf ta qare musu kallo,sai kuma ta tabe baki,motsin da taji daga parking space din ya sanyata fara tattara kayan cikin hanzari,tana gudun ko abba ne ya fito zaya tafi,ta tabbatar idan ya ganta a wajen fada zata sha.
Wanda ta gani a wajen yana niyyar fitowa daga motar tasa ya sanyata sauke ajiyar zuciya,tasan cewa kome zatayi ba kulata zaiyi ba bare ya hanata,don kuwa tsahon tasowarta ta sanshi amma ba zata iya tuna rana daya da magana ta taba shiga tsakaninsu ba.
Kamar yadda ta zata din kuwa,ko a yanzun ma dauke kansa yayi ya soma rufe motarsa sanna ya jefa key din a aljihu ya kuma soma takawa yabar wajen.
Da kallo ta bishi tana tabe baki gami da jifansa da harara,har sai da ya bacewa ganinta sannan ta dauke dubanta daga wajen,a hankali take tattare kayan tana maidawa cikin ledar,qasa qasa take magana ita daya
"Wallahi banaso,bayarwa zanyi,ni ba wani aurensa da zanyi,dan iska kawai" dif maganar tata ta yanke,sai kuma tahau zaro idanu cikin tsoron kada wani ya jita,sai data tabbatar babu motsin kowa sannan ta qarasa kwashe kayanta ta kuma fito.
Isowarta farfajiyar gidan yayi dai dai da budewar gate din gidan,qaramar motar qirar 406 ta danno kai ciki,sai ta dakata daga yunqurin isa sassan anty madinan tabi motar da kallo,sai kuma ta saki murmushi har dimple din dake kwance saman kumatunta hagu da dama ya lotsa,saita cilla da gudu gudu sauri sauri zuw wajen motar,cike da zumudi da kuma murna.
Sanda ta isa daura da motar tuni mamallakiyar motar ta kasheta tana yunqurin fitowa
"Anty dina sannu da zuwa" waiwayawa tayi sashen da widad din take tana niyyar dauko jakarta daga back seat na motar
"Widad rigimammiyar ummu,ya na ganki a gida kuma?" Murmushi tayi tana leqen cikin motar da alama akwai abinda take nema
"Anty secondry zamu tafi fa,muma mun zama manya kin manta?"
"Au anyi haka fa,kice zamu sake samun qarin 'yammata cikin gidan namu....."
"Anty wai ina aysar ne?" Ta tambayeta cikin katsar numfashinta
"Gashi nan a daure" ta fada tana nuna mata shi a kujerar dake kusa da tata cikin baby car seat,zagayawa tayi da hanzari
"Don Allah anty kwantomin shi"
"A'ah widad......ke kanki yaushe ummu ta daina goyaki?, barshi yanzu zan fito na kunceshi" bata rai tayi,wai me yasa kullum suke maidata baya,bayan ita kanta tasan girma take?,to idan ma har yanzu yarinyace ita a wajensu me yasa suke mata zancan uncle mahfood?,dole daga bisani anty dina ta ciro yaron ta miqawa widad shi,sannan suka nufi sassan mahaifiyarta tana ankare da widad din.
"Ke kuma wanne tsautsayin ne ya sanyaki daukar yaronki ki bawa wannan yarinyar?" Cewa momma mahaifiyar anty dina bayan shigarsu babban falon sassan nasu.
Kafin anty dina tace komai widad din ta rigata magana
"Momma Allah na iya fa,gash.i nan ma ni na daukoshi tuyn daga parking space" ta fadatana turo baki,wanda ke sake nuni da zallar quruciyarta,abinda ya sake batawa momma rai,taja tsaki tana miqa hannu gami da yunqurin karbar yaron
"Miqomin shi nan,me kika iya?,yarinyar da ko pant dinta har yanzu batasan ta wanke ba" momma din ta fada tana jifanta da harara,zallar quruciya ya hana widad fahimtar kuma,bugu da qari kuma,akwai wata irin wankakkiyar zuciya da take da ita,ba kasafai ta fiya damuwa da abubuwan da suke faruwa cikin gidan ba,duk da ta soma girma,hankalinta ya fara fahimtar wasu abubuwan
"Allah na fara koya momma"
"Naji,jeki da Allah" ta fada tana sake harararta kamar idanunta zasu fado,sai dauke dubanta daga fuskar momma din tana nufar hanyar kitchen dinta.
Wata tsawa ta kwatsa mata,wadda sai data sanyata ta kusa tuntube da kujerar dake gefanta
"Ina kuma zaki?" Ta fada tana fidda idanu
"Wajen Aafiya zani"
"Kiyi mata me?" Ledar hannunta ta daga tana nuna mata
"Kayan kwalliya na kawo mata ta zaba"
"Uhnnnn,salon kije kisa ta bata aikin dana sakata,to zauna nan har sai ta fito,kada ki shiga ku hadu ayimin shirme" narkewa tayi tana duban momma din,da alama tanason ta roqeta ne ta barta ta shiga,tana kuma tsoron tsawarta,don ba abinda ta tsana sama da tsawa da kuma fada.
"Ki barta mana momma,idan yaso tana shiga saita fito kada ta zauna" dina ke fada qasa qasa,saboda tausayi da widad ta bata,waiwayowa momma tayi ta kalleta tana dan juya aysar a hannu kamar zata masa rawa
"Wannan yarinyar?,tsab zasu iya barnatar min da guri,kuma baka da damar yi maya fada balle duka,tunda tana da uwa a bakin murhu"
"Kiyi haquri momma,yanzu zata fito"
"Naji,amma indai ta shiga din duk barnar da tayimin ke zaki biya"
"Na yarda" sai.anty dina din ta daga kai ta dubeta
"Shiga kikai mata kizo na aikeki sassan anty madina"
"Tohm" ta amsa da zumudinta tana shigewa,deena ta bita da kallo,bata fiya yin fushi ba don mutum ya bata mata ko ya tsangwameta,bata sani ba ko tsabar quruciya ce?,ko sai nan gaba zata fahimta komai idan hankali ya gameta?.
*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*
*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*ðŸâ€Â¥Ã°Å¸â€Â¥Ã°Å¸â€Â¥Ã°Å¸â€Â¥Ã°Å¸â€Â¥
0022419171
Maryam sani
Access bank
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*ðŸâ€Â¥
*_A RUBUCE TAKE!!!_*
(k'addara ta)
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.