A Rubuce Take Complete Hausa Novel
Reading file: A_Rubuce_Take_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 7 of 101
Page 07
Bata fahimci zancan da gasken gaske bane sai da ummu ta fara hadata da walid qaramin dan anty madina yana rakata kaiwa ma'aruf din abincinsa,ta maida wannan aikin na kullum kullum a kanta,a nan ne hankalinta ya fara tashi,duk a qoqarin ummu na kawo kusanci da fahimtar juna a tsakaninsu.
Tun ranar farko kamar tasan manufar yin hakan bata shiga dakin ba,daga bakin qofa ta tura masa ta juyo tayi tafiyarta,hakance taci gaba da kasancewa,duk sanda aka aiketan turawa take daga qofa ta wuce abinta sassan anty madina ko sassan wani daga cikin kawunnanta.
*_RABON ZA'AYI_*
Sun tafi tiryan tiryan da walid kai abincin,tana ta qunci da dacin rai,amma ba zata iya qin zuwa ba,har sun kusa da qofar dakin taji akwai alamun baqo,sai ta koma da baya tana duban walid
"Muje na aje masa akan motarsa,yazo ya dauka" yaron yana biye da ita har gaban motar ma'aruf,ta dora masa abincin sannan suka koma sassan ummu,ta fito ne suna kallon wani cartoon,dama kuma Allah Allah take ta koma ta qarasa kalla.
Da kallon mamaki ummu ta bita sanda ta shiga ganin nan da nan ta dawo
"Har kinkai?"
"eh na kai", ta amsa kai tsaye tana komawa cikin kujera ta lafe hankalinta duka yana kan cartoon din,jim ummu tayi kamar tana tantama,sai kuma ta dauke kanta taci gaba da sabgarta.
Bayan minti goma sai naadir ya shigo ya cewa ummu
"Yaaya ma'aruf yace ba'a gama abincin bane?"
"Wanne abinci kuma bayan wanda aka kai masa,ko qaro musu za'ayi?"
"Anya?,yace dai yunwa yakeji abincin yake jira" waiwayawa ummu tayi ga widad data lafe sosai gabanta na faduwa,amma sai tayi kamar bata a wajen,ta rufe idanunta kamar mai bacci,kallo daya ummu tayi mata tasan ba bacci takeyi ba,sam qarya bata mata kyau,tun dazun ta fahimci akwai lauje cikin nadi a maganarta
"Widad a ina kika aje masa abincin?" Manyan fararen idanunta ta bude kamar zata saki kuka ta bawa ummu amsa
"Yana kan motarsa" baki ummu ta kama tana kallonta
"Kai jama'a" maama batulu ta fada cikin bacin rai,yayin data tsaya tana jiran jin irin fadan da ummu zatayi mata,idan ya kama da duka ma ta doke ta,yarinyar ta tsayewa rayuwarta gaba daya,gata qauna da kulawar da ummun ke bata nata yaran basu samu wannan ba,duk da suna samu dai dai gwargwado daga wajenta,amma ita butulu ba irinta takeso ba
"Yanzu tsabaragen iskanci a aikeki widad kije ki dorawa mutum.abinci saman mota?,ta yaya to zaisan kin kai?,idan wani ya kifar kuma bai sani ba fa?" Ta qarashe maganar tana maida kallonta ga ummu wai ko ummun zata kama mata,amma sai taji tace
"Ubangiji ya shiryeki,wannan quruciyar da shirme da kike fama dasu Allah ya maganta miki" ta juya ga naadir
"Jeka dauka daga kan motarsa ka miqa masa" amsawa yaron yayi ya juya yana ficewa,ita kuwa batulu dole ta kama bakinta jin ummun bata kama mata ba,taso taci gaba da maganar tana sake zuga abin,sai abun ya tsaye mata arai,sosai.haushi ya cikata,yarinya sai nema mata mazan aure ake tana iya shege?,wa tafi goshi?,idan kyau ne yaransu gaba daya babu wanda bashi da dai dai nashi,rashin uwa kuma a kusa ai ba farau kanta ba,dukka yaran dake can gida tare dasu kowanne ba uwar gareshi ba,amma babu wanda ummun ke shagwaba haka kamar widad din,kai hasalima ba wanda ummu ta kama ta riqe sai widad din?.
Da wannan takaicin ta baro gidan,saidai kuma ta qudire a ranta ba zataji takaicin banza ba,don haka da daddare bayan dawowar alhj mahmud ta zauna tayi masa famfo sosai,ta bashi labarin qarya da gaskiya kan abinda ya farun.
Sosai kuwa ya tunxura,ransa ya baci,abun na yarinyar ya fara kaishi bango,zuciyarsa dama yaketa danna,abinda ya faranta ran batulu kenan ta gyara zama
"Diya mace dai 'yar gidan wani ce,gwara a gyara mata zama tun yanzu,sannan idan tace shima ma'aruf bata sonshi kuma bansan wa takeso ba,gashi sai dad'a girma suke,kuma ita din ba wata budurwa ba bare ace akwai irin mijin da take hari,duka duka ma yaushe tasan rayuwa ma?". Shuru kawai yayi yana jinjina kai, tabbas zai dauki mataki,bazai bari yana ji yana gani ba gata ya lalata ba,duka sauran yaran da ake riqo a nan gidan ai ba haka suke ba,idan ma ummu ke daure mata gindi lallai gobe sai ya nuna mata kuskurenta.
Har widad din ta kwanta ummu ta tasheta
"Widad,karki sake aikata abinda kika aikata dazu kinji?,baki gani ma'aruf yayanki ne?,kuma shine zai zama mijinki a nan gaba?" Baki ta sake tana kallon ummu a sakarce,hawaye na shirin fara taruwar mata a idanu
"Miji?,ni wallahi bana sonshi ummu" sai kuka ya kufce mata sosai,ta kuma birkicewa ummun gaba daya
"Samu guri ki kwanta" kawai ummun tace da ita bayan ta gaji da koke kokenta,tana jinta daga kwancen tana jan sheshsheqar kuka har bacci yayi awon gaba da ita,wannan al'amari na widad......to wa take so?,Allah shine mafi sanin gaibu shine amsar da ummu ta bawa kanta daga qarshe,ta rufe idanunta tana fata ko meye zaizo yazo da sauqi.
*W A S H E G A R I*
Tunda ta tashi da fushin zancan ma'aruf ta tashi,ummu tayi tayi ta kulata taqi,ko larifa mutuniyarta yau babu 'yar hirar da suke tsakaninsu,da take zata kwaso undies dinta da uniform ma zata wanke mata nuna mata inda ta zubasu kawai tayi,amma abinka da zuciyar yaro qarfe goma na safe sai ta fito falo ta zauna,ummu na zaune kan one sitter,sai ta koma kan two sitter ta kwanta tana kallo a MBC3,duban sashenta ummu tayi taci gaba yankan farcenta ba tare da tace komai ba,daga nan suna jiyo hayaniyar yaran gidan a farfajiyar gidan,wanda ta tabbatar da ranta fes yake da tuni ta fice,idan ba harabar gidan ba to wajen anty madina.
Sallamar abban nata ya sanyata miqewa ta zauna suna kusan hada baki ta da ummu wajen amsa masa,haka kawai taji gabanta ya fadi,kallo daya tayi masa ta shiga nutsuwarta.
Bai jira sun gama amsa sallamar tasa ba ya qarasa wajen kayan kallon dake falon ya zaro wayar USB dake jin wuta ya nufo widad da ita,baikai ga isa ba kiran sunansa da ummu tayi da qarfi ya dakatar dashi,don tuni ta fahimci abinda yakeson aikatawa,saboda ya taba aikata hakan a baya
"Kayi hauka ne mahmudu?,da raina da lafiyata?,ina zaune a falon zaka shigo ka dauki mabugi ka dakarmin ita?,to daketa nace?,wallahi wallahi kana dukanta saina rama mata,idan kuma kana shakka to bismillah" ummu ta fada ranta a mugun bace,abinda yasa ya yarda wayar hannun nasa kenan,yana qoqarin saita kansa,tare da qoqarin gano rashin dacewar abinda ya aikata din,wannan ya bawa widad damar miqewa da gudu ta isa ga ummun,ta fada jikinta gami da qanqameta tana sakin kuka,abinda ya taba zuciyar ummun,ya kuma saukar mata da tausayin widad din,saita dora hannunta saman kanta tana lallashinta.
Gaban ummun ya qaraso ya russuna yana gaisheta,harara ta jefa masa
"Bana buqatar gaisuwarka" saita zare widad daga jikinta tana umartarta data wuce daki,ta miqe tana sharbar hawaye,sannan cikin kaffa kaffa da mahaifin nata ta gewayeshi ta wuce.
"Kiyi haquri,ni banyi haka don na bata miki rai ba,abinda yarinyar nan takeyi yayi yawa,kowa sai tace bata so?,har a aiketa taje ta dora abinci akan mota?,sa'anta ne shi?,fisabilillahi haka za'a zuba mata idanu?" Duk da taji sallamar halimatu a falon amma hakan bai dakatar da ita daga bashi amsa ba,ta gano daga inda tushen zancan ya fita
"To cewa akayi lallai lallai sai ta sosu?,ko kuma fadar Allah ce?,uwayensu ba sai da kukaji kuna sonsu ba kuka auresu?,to ahir wallahi,a sakar mata mara hakanan,ita kadai kunbi kun sata a gaba?,da kai da masu zigoka din ka gaya musu,wallahi tallahi su fita a idona akan lamarin widad,ba wanda ya haifeta ko yayi wahalarta,saboda haka su kama kansu" qas yayi da kai
"Allah ya bada haquri,ya huci zuciyarki"
"Ameeen" ta amsa a fusace,sai ya miqe,yana son tambaya yaji alhaji yana kusa amma fushinta ya sanya don dole ya juya ya fice, halimatu ta bishi da kallo sannan ta dawo da dubanta ga ummun bayan ta tabe baki
"Allah ya kyauta amma dai ummu ai da kin bari ya hukuntata,icce tun yana danye fa ake tanqwarashi"ta fada tana duban ummu da kyau
"Ya kyauta abinda yafi haka,iccen qaniyarki,duk cikinku wa aka yiwa hakan iyee?" Ganin fadan zai dawo kanta saita zame itama
"Allah ya bada haquri,ni ba haka nake nufi ba".
Wunin ranar kamar an dawo mata da zancan mahfood ne,saboda yadda taga abban nata yazo afujajan kamar yadda yayi mata kan auren mahfood,uwa uba bayan sun kebe ummu ta fara tausarta a hikimance,wannan yasa gaba daya ta shiga damuwa da 'yan koke koke,har sai da alhaji ya fahimta ya kuma bi ba'asi.
To da yake shi dinma mai sauqin kai da fahimta ne sai yace
"Ba ta haka ake bi da yaro ba matuqar anason ya fahimci abu,ta lallashi da siyasa ake binsa,gaba daya al'amarin mahmudu bansan me yake damunsa kan batun yarinyar nan ba"
"Me yake damunsa kuwa banda matansa dake zugoshi?" Kai alhaji ya girgiza
"Allah ya kyauta,amma kedai karki saka haka a ranki,mubi komai a sannu da kuma addu'a,zan sake magana da shi mahmudu din"
"Allah ya rufa asiri"
"To ameen,munyi waya dazu da muhsin,yace ko gobe ko jibi zai shigo garin" dan murmushi ummu ta sake
"Ma sha Allah,ayyukan sunyi sauqi kenan?"
"Eh da alama kam tunda har ya samu sukunin zuwa"
"To Allah ya taimaka,ya ara mana rai"
"Ameen ya hayyu ya qayyumu" alhaji ya amsa mata,sai kuma suka shiga wata hirar ta daban.
*RUMBUN K'AYA*ðŸâ€Â¥
*DAUDAR GORA*ðŸâ€Â¥
*IDON NERA*ðŸâ€Â¥
*A RUBUCE TAKE*ðŸâ€Â¥
*KI KULANI*ðŸâ€Â¥
*_uhmmmm_*😊😊😊😊😊😊😊😊😊ðŸ˜Å
*Nasan zakuce ya da murmushi haka?*
*Wanda bai shigo ba bazai gane ba*
*Sai kin shigo daga ciki zaki gane me nake nufi*☺ï¸Â☺ï¸Â
*KE DAGA JIN SUNAYEN LITATTAFAN MA KADAI KASAN CEWA AKWAI WANI BABBAN ABU MAI MATUQAR JAN HAKALI TATTARE DASU*
*KINA NEMAN INDA ZAKI HUTAR DA KWANYARKI?*
*KI SAMU ZUNZURUTUN NISHADI DA ILIMI?*
Littafi daya---400
Biyu---600
Uku----800
Hudu-----1k
Biyar din duka----1200
*ZOKI BIYA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT DIN KI ANTAYA JIRGIN FITON ZAFAFA BIYAR*ðŸâ€Â¥Ã°Å¸â€Â¥Ã°Å¸â€Â¥Ã°Å¸â€Â¥Ã°Å¸â€Â¥
0022419171
Maryam sani
Access bank.
Shaidar biya tanan👇ðŸÂ»
09033181070
*MTN CARD KO VTU ZASU SAKA TA NAN*
09166221261
🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪🇳🇪
*Ina yan uwa 'yan nijer?*
*Zaku saka katin AIRTEL ta wannan number sannan ku tuntubeta*
+227 90 16 59 91
Littafi daya---450CFA
biyu---650CFA
uku----850CFA
hudu----1050 CFA
Biyar----1250CFA
*A DADE ANAYI SAI GASKIYA!*
*SIYAN NA GARI KUMA MAIDA KUDI GIDA!*
*Thanks for choosing us*ðŸâ€Â¥
*H U G U M A*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.