Complete Hausa Novels

A Rubuce Take Complete Hausa Novel

Reading file: A_Rubuce_Take_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 85 of 101

Page 84

Yadda yayi din sai ya bata tausayi,don haka ta ajjiye wayar tana cewa

"Wai tausa da dadi ne?" Dariya ta taso masa amma a yanayin da yake ciki batayi wani tasiri ba,ya maye gurbin ta da murmushi don ta bashi dariyar sosai can qasan ransa

"Sosaima" ya furta a hankali yana lumshe idanunsa sanda tattausan tafin hannunta ya sauka a tsakiyar bayansa.

Tun tana dari dari har ta sake,ta dage ita bilhaqqi da gaske tausa take masa,yayin da idanunsa suka kasance a rufe,yana jin yadda hannuwanta ke kai komo a bayansa,shi kadai yasan abinda yake ji cikin ruhi da gangar jikinsa.

Kasa daurewa yayi,cikin wani irin zafin nama yayi mata wani irin juyi ya maidata gurbin daya tashi shi kuma ya maye nata gurbin ta hanyar mamayeta gaba daya,hadi da yi mata rumfa da mayalwacin qirjinsa.

Tsoro ya gani a rubuce cikin idanunta,ta soma rarrabasu tana kallon gajiyayyar fuskarsa dake cike da shauqi da mayen so da qaunarta,da kuma burin kasancewa da ita.

A tausashe ya rungumota cikin jikinsa,fatarsu ta hade guri guda,dumin jikin junansu ya gauraye waje daya,ya sanya kansa cikin wuyanta ta soma gaya mata wasu kalamai da suka saukar mata da nutsuwa,suka kuma sakata narkewa a wajen ba tare data sake qwaqwqwaran motsi ba.

Cikin salo da kuma qwarewa ya fara aike mata da wasu saqonni da dukkan jikin da jini ke gudana a cikinsa zaiyi wuya ya tsallake musu,saqonnin da suka dinga bin dukka wata jijiya dake aike da tunani da kuma tantance abu suna tsinketa,suka dinga dilmiyar da ita zuwa wani bigire na daban,bigiren da dukka wani tsoro nata ya gushe yayi nasa waje.

Saida komai ya kankama sannan ta fara gani kuskuren data tafka,tuni aikin gama ya gama,ya sake tabbatar wa zuciyarsa da gangar jikinsa cewa ita din mallakinsa ce halak malak.

Kamar wancan karon,wannan karon ma yanayi ya shiga sosai,ya riqeta sosai cikin jikinsa yana sauraren siririn kukan da take fitarwa,wanda kusan fiye da rabinsa shagwaba tafi yawa a ciki,yasan yau dinma dole zata jigata ta kuma ji jiki,don shi kansa yasan halinsa ta wannan fannin,amma kuma bazai kai karonsu na farko ba,baiji komai ba ya biye mata ya dinga lallashin abarsa,yana kuma dauke kowanne hawaye nata da harshensa.

Jinta yake takai masa ko ina,koma meye zai iya yi mata,haka ya lalace wajen rarrashinta.

Har sukayi sallar asuba suka idar taqi duban fuskarsa,ta gaidashi kanta a qasa,ya saki murmushi,ya matso kusa da ita ya zauna sosai har gwiwoyinsu suna haduwa,yasa hannu a hankali ya janye hijabinta baya,kyakkyawar fuskarta ta bayyana,ya sanya hannu ya kamo tafin hannunta ya saka cikin nasa yana ci gaba da kallonta

"Fushi ake dani baby?" Ya tambayeta yana narkewa kamar shima zai sakar mata kukan,kamar jira takeyi ita saita rigashi,ta sakar masa nata kukan qasa qasa

"Ba kaine ba......shine ka yimin wayo,saboda kaga ka girmeni" tayi maganar tana mele baki,kaman zaiyi dariya amma sai ya danne

"Am sorry,nima fa ba'a son raina ba,bansan nayi ba sai daga baya"

"Kuma fa gidan nan kasan akwai baqi,yanzu idan mom ahmad ta gane me zance mata?" Dariya sosai ta sake kamashi kamar yayi me,amma ya tabbatar idan yayita yanzu zai jama kansa jagwal

"Waye yace miki ana ganewa?, ba'a fa ganewa kayi,kuma ma....." Sai yayi qas sosai da muryarsa,ya sake matsowa da fuskar sa dab da ita kamar zai shige cikin hijabin

".....kowa yanayi,itama nasan sunyi jiya......." Bata barshi ya qarasa ba ta cure waje daya cikin hijabinta

"....don Allah uncle" a wannan lokacin kasa boye dariyarsa yayi,ya dora fuskarsa saman qafafunta yayi dariyarsa sosai yana jin nishadi yana wanzuwa a rayuwarsa.

**********Sati guda daya rak amma dai dai yake da wasu shekaru a wajensa,sati guda daya daya canza rayuwarsa da tunaninsa,tayi wani mugun tsayawa cikin rayuwarsa,ta kuma barma zuciyarsa wani babban tambari da yakejin har duniya ta nade bazai taba goguwa ba.

Jinta yake sosai a ransa,wani irin ji da yake ratsa zuciya matuqar ratsawa,tattali qauna da soyayya yake nuna mata irin wadda idanuwa basu saba gani ba,wasu abubuwan shi da kansa baisan yana yinsu ba,ta mantar dashi dukka wata damuwa tasa da matsalar da yakejin yana ciki.

Duk da bata gama sakewa dashi gaba daya ba,amma zai iya cewa ya samu fiye da rabin abinda yakeso,ya sani cewa da zarar ta sake sanin darajarsa ta kuma sake hankali da wayo,zai shiga sahun mazan da sukayi sa'ar matana aure a duniya,wani irin qauna da kimar hajiyarsa ke sake kwaranya a zuciyarsa,uwa uwa ce......uwa daban take,ashe irin wannan take ta kwadayin samar masa shi yasa ta dage cikin qanqanin lokaci sai data shigo da widad din cikin rayuwarsa?.

Ta fannin widad din ta sake zama wata tabararriya ta gaske,shagwabarta take zubawa yadda taga dama,biye mata yakeyi,ta koma tamkar su mimi,ko tari tayi sai ya tambayi ba'asi,duk wani koke koke da take masa a duk sanda ya samu yadda yakeso sam basa damunsa,yasa hannu ya karbe ya kuma shnaye dukka rigimarta,hasalima shagwabarta na daya daga cikin abubuwan dake saurin kunnoshi da rura wutar soyayyarta a zuciyarsa,wannan ya sake haifar da shaquwa tsakaninsu shi da ita,duk da har a lokacin yana tantamar tasan kalmar so?,abu na qarshe da yakeson ya gina gini mai ingancin da bazai rushe ba cikin zuciya dama rayuwarta gaba daya.

A qarshen watan ya gama yanke shawarar meye mafi girman tukuci da zai bawa rayuwarta?,yana tsaka da wannan tunanin saiga kyautar kujerar hajji har guda biyu daga wajen tsohon governor ya bashi kyauta,yayi masifar jin dadin aiki da abbas din,kuma har yau yana yaba masa,wannan yasa time to time yake tabo abbas din,inda tason ran Excellency dinne da tuni abbas din ya koma aiki qarqashinsa,saidai shi bashi da wannan interest din,dole ya haqura ya qyaleshi,amma lokaci lokaci yana taboshi akan wasu harkokin tsaro da suka shafeshi,kamar yanzun da zaiyi tafiyar,yaji ba wanda ya dace ya tafi dashi da yafi abbas din.

A lokacin babu wanda yaga ya dace da wannan tafiyar sai widad din,don haka ya karba daya yasa sunanta a daya ba tare da tasan ma da kujerar ba,aka soma processing na tafiyar,wadda zasu yita ne in group cikin tawagar his Excellency din.

Cikin sati na gaba suka shirya zuwa bauchi,tun bayan zuwan da sukayi suraj da matarsa sukazo musu basu sake zuwa bauchi ba sai a yanzu.

*********Karon farko data zauna ta hadawa abbas din kayan tafiya bauchin,a lokacin ya fita office,baisan ma ta hada din ba,sai daya dawo daga aiki,ya buda akwatin,ya jima tsugunne yana kallon luggage din, murmushi yana kubce masa,yadda ta shirya masa komai kamar shi da kansa ya shirya kayan nasa,ya girgiza kai ya miqe yana jin qaunarta tana sake ninkuwa cikin ransa,tasan buqatarsa,tasan choices dinsa tun yanzu.

Kai tsayr toilet ya shiga ya gama wanka ya fito,yana tsaye gaban mirror yana tsane ruwan wankan dake jikinsa,wanda ke fidda qamshin daddadan turaren wankan daya cakuda dana shower gel dinsa,fuskarsa yake kalla,cikin kwanakin har wani canzawa yaga yayi,kuzarinsa ya qaru,kamar yadda yaga yadan sake cikowa,fatarsa kuma ta qara haske kamar mai amfani da wani mai na daban.

Ana taba qofar ya maida idanunsa ga bakin qofar,ya kasa ya tsare yana jiran shigowarta.

Da sallama ta shigo cikin siririyar muryartan nan,sanye take da wata fara sol don smoked gown,kanta babu dankwali sai farin ribbon data matse sassalkan gashinta,fuskarta fes yau babu digon komai saina man lebe da ya sanya siraran lips dinta suketa qyalli,ba shiri ya saki comb din ya waiwayo harde da hannayensa a qirji yana qare mata kallo.

Shigar yau ta fidda asalin tushenta wato larabawa,kamar diyoyin larabawan da suka samu kyakkyawan kulawa,rigar ta karbeta,haka gyaran data yiwa gashinta wanda gaba daya wani abune da bilkisa ta koya mata kafin su tafi

"Bakison kiga uncle din yafi ji dake akan kowa?,to haka zaki dinga yi,ma sha Allah,inda nice da wannan jikin naki da wannan gashin.....ai da tuni na kori hafsat" ta fada tana qyalqyala dariya,don dama sam babu jituwa tsakaninta da hafsat din,duk da amintakar dake tsakanin mazajensu, bilkisa bata daukar raini ko wulaqanci,hakanan dama tun usul ita bata jituwa da marowacin mutum,wadan nan siffofi kuwa dasu hafsat tafi shuhura,wannan dalilin yasa matan abokansa da suke manyan mutane masu manyan muqamai iri daban daban a gwamnati suka janye jiki daga matarsa da gidansa,don babu wadda kejin dadin mu'amala da ita,idan sunzo gidan sai dole,kamar haihuwa da sauransu.

Dukka hannayensa ya bude mata,yana mata alamar ta taho,saita tsaya daga bakin qofar ta noqe kafada tana tura baki gaba,tana tuna azabar da tasha daren jiya a hannunsa

"C'mon mana baby doll,nayi alqawari fa bazan sake ba har sai kin yarda"

"Promise?" Kai ya jinjina yana murmushi sannan yace

"Amma kada ki manta,kema kinyi alqawarin zaki barni nayi komai banda wannan abun dai....." Yadda yayi maganar a narke shi kansa zaka dauka yarone dan shekara tara ko goma,abun ya bata kunya sosai,ta sanya zara zaran fararen yatsunta ta lullube fuskarta tana dariya,sannan ta fara takowa a hankali zuwa gabansa,yayin da shi kuma ya kafeta da ido yana jiran ta qaraso,bugun zuciyarsa na daduwa,yanajin kamar tana ja masa aji ne,kamar bata sauri.

Taku biyu ya qara ya cimmata a hanya,ya durqusa gabanta ya lullubeta cikin ingarman qirjinsa dake cike da muscles da gargasa suka yiwa tufa,haka qirar jikinsa yake tun asali,wannan ya qara masa interest na shiga aikin police.

Cikin abinda baifi second goma da shiga jikinsa ba dukka jikin nasa ya dauki rawa,ya cusa kansa a wuyanta yana shaqar qamshinta da har yanzu bai sake jin wani qamshi da yake burgeshi kamarsa ba,yadda bugun zuciyarsa ya qaru haka speed na fitar numfashinsa,banda girman alqawarin daya dauka babu abinda zai hanashi karyashi.

Tayi lamo a jikinsa ita kanta,tana jin yadda numfashinsa ke kewaye fatarta yana ratsata har cikin qashi,ko qwaqwaran motsi batayi ba,wani yanayi yana sauka a jikinta,har ya haqura don kansa,ya daga kansa a hankali zuwa ga fuskarta yana riqe da fuskartata a tsakanin hannuwansa

"Ki rage tsoro don Allah baby.....i love you" murmushi ta saka a kunyace tana son sake boye kanta,sai ya miqe yana cewa

"Nooo.....wannan kwalliyar na siyeta har fuskar,zan biya.....don Allah a barni na kalla" cak ya dagata ya azata saman madubin,ya jawo dressing chair ya zauna akai ya buda lotion dinsa ya fara shafawa,yana shafawar yana duban fuskarta hadi da tsokanarta ta hanyar tuna mata da abinda ya faru daren jiya.

Kukan shagwaba ta sakar masa tana bubbuga qafafunta

"Nidai Allah uncle......Allah.....Allah" dariya ta dinga cinsa,irin abinda bata taba gani ya sake haka yana dariya ba

"Shikenan.....wasa nake miki,na daina,amma bakiji bane?,nima fa na kira hajiya har bansan adadi ba,na dauka mutuwa zanyi,yarinyar nan haka kike da......" Ba tare data shirya ba ta saka hannunta ta rufe masa baki idanunta dukka a waje,tana jin kamar qasa ta tsage ta shige,sai kawai ta nemi silmiyowa daga saman madubin,cikin zafin nama ya tareta da cinyoyinta,sai gata zaune sosai a samansu

"Yarinya kin kawo kanki" ya fada a tausashe murmushi na kubce masa.

°°°°°°°°°Karfe goma na safe suka fito shi da ita,kallo daya zakayi musu kaji sunyi mugun burgeka,kamar hadin baki,shi da itan duka shigar sky blue sukayi,shi shadda ainihin gezner ya saka,ita kuma wani lace ne cotton mara nauyi.

Yau din bai nema wani dan rakiya ba,shi da kansa yayi driving nasu daga kadunan zuwa bauchi,duk da jirgi ma yaso subi,amma sai yaji yana da muradin awannin da zasuyi a tare cikin motar waje guda kafin su isa kadunan,don yasan dole kuma ya bawa hafsan lokaci kodon fita hakki,amma for now ya fara tunanin yadda zai dinga raba musu kwana duk lokacin da suka je bauchi,musamman idan zaiyi kwanakin da yafi biyu.

*H U G U M A*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
*Arewabooks:Huguma*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.