Akidata Book 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Akidata_Book_1_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 1 of 8
   Asslam Alaikum warahmatullah, A madadina, ƙungiya ta da kuma 'yan uwa na da abokan arziki, ina taya Ɗaukacin Al' ummar Musulmi barka da salla, tare da fatan anyi salla lafiya, ina fatan ubangiji Allah ya karɓi ibadunmu da mukayi a watan Ramadan, sannan ina Fatan Allah yasa mu ɗore da ibadun da mukayi a watan Ramadan, Taku har Kullum
AISHA HUMAIRA (Daddy's girl) ko kuma ince Ayshercool ðŸ˜ðŸ˜ kaman yadda wasu suka fi sani.
 TALLA! TALLA!! TALLA!!!
Ina masoya wanda suka bibiye ni a littafina na ABDUL JALAL, da kuma WATA KISSAR yanzu ma na shirya tsaf domin kawo muku wani ƙasaitaccen littafin me ɗauke da sabon salo da kuma sarƙaƙiya,
ga É—anÉ—ano daga cikin littafin
     Â
            _*AƘIDA TA*_
      Â
   *PART1*     Â
         _Page 1_
*written and edited by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
What's App : 07063065680
Facebook : real Humaira
Watpad : Ayshercool7724
Gmail : Www.ayshertadam@gmail.com
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
Bismillahir rahmanirrahim, da sunan Allah me Rahama me jin ƙai, Wannan littafi ƙirƙirarren labari ne banyi shi dan cin zarafi ko cin fuska ga wani ko wata ko wata ƙabila ba, idan har wani ko wata yaga wani abu daya yi kaman ceceniya da rayuwar sa ko ƙabilar sa Amin Afuwa banyi dan cin zarafin wani ko wata ba.
  Wannan littafin mallaka tane, ban yadda a juyamin labari ta kowane fanni ba ba tare da izinina ba.
Katafaren ɗakin Bacci ne me ɗauke da kayan alatu na more Rayuwa da jin daɗi, idan ka ƙarewa ɗakin kallo zaka tabattar da ma'abocin wannan ɗakin Allah yayi masa Ni'imar Dukiya dan ya ƙawatu da dukkan wasu kayan more rayuwa, kallo ɗaya zakayiwa ɗakin kasan mamalakin ɗakin mace ce, saboda kan madubin dake ɗakin shaƙe yake da kayan kwalliya da gyaran jiki, ga wani show glass ɗauke da takalma da jakunkuna na adon mata kamar wani kantin saida kayan ado, kai da ganin takalma da jakunkunan nan kasan bana talaka bane, Makeken Gadon dake ɗakin ne ɗauke da wata kyakywar matashiyar budurwa ta baje gashin kanta tana bacci cikin nutsuwa.
Hasken ranar da ya ratso ta tagar É—akin ne yake dukan fuskarta wanda hakan yasa ta motsa a hankali, ta buÉ—e idanuwanta.
Ɗan ya mutsa fuska tayi, ta miƙe zaune ta kalli Agogon bangon dake ɗakin nata, ƙarfe tara da rabi na Safiya, a hankali ta zuro ƙafafuwanta ƙasa ta miƙe ta nufi banɗakin dake cikin ɗakin nata.
Aljannar Duniya shi kansa ba É—aya nata ya isa a tsaya a kalla.
Wanka matashiyar tayi ta fito daga ita se towel, abun mamaki har an gyara mata inda ta tashi, ta zauna a gaban mudubi, ta shafa wannan ta goga wancan, gashi komai nata a hankali cikin nutsuwa take aiwatar dashi, riga da skirt na blouse ta ɗakko ta saka da ɗan guntun mayafi, ta ɗora akanta tasaka takalmin ta me matuƙar tsini da jakarsa, seda ta kalli agogon hannun ta ƙarfe goma da rabi dai dai sannaan ta buɗe ɗakin ta fito.
Wani irin taku take na ƙasaita, takalmin ta na bada sauti ƙwas, ƙwas, ta fito wani irin ƙaton falo ta zauna, ba ta daɗe da zama ba, me aiki ta kawo fruit gabanta ta ajiye, bata kalli inda fruits ɗin suke ba, se kallon tsintsyar hannun ta da ta ɗaurawa Agogo take yi.
"wato Isa rayuwar ƙauye akwai daɗi akwai wahala"
Wanda aka kira Isa yace
"Haba ɗan uwa wani irin daɗi a ƙauye? Kai ka taɓa ganin wanda yake birni ya koma ƙauye banda zunzurutun wahala mene ne a ƙauyen?"
"to ai Rayuwar ƙauye tafi ta birni kwanciyar hankali, ba tashin hankali ba fargaba, amma kaga birni a nan rashin gaskiya ya ƙare"
"tabdijan lallai ma sani, ai tunda Allah ya kawoni birni na samu aikin gadin nan, idan naje ƙauye to ziyara na kai Amma bani babu zaman ƙauye ina daf da dawo da iyalina nan ma"
"kai gidan nan zaka dawo da iyalin naka, kaifa kace min zaman fargaba kake a kowane lokaci za'a iya sallamar ka fa"
Isa yace "rufamin Asiri in kawo iyalina gidan nan Haya zan kama"
Suka ci gaba da hirar su tare da yin taɗi akan rayuwar birni da ta ƙauye
Sake kallon Agogon ta tayi har sha biyu saura minti goma sha biyar, miƙewa tayi cikin takunta na isa ta fito harabar gidan, kai tsaye ta nufi bakin gate, inda me gadi ke zaune yana hira da abokin sa sani suna cin gyaɗa.
Isa Yana hangota ya miƙe jiki na rawa yace "Allah ya temake ki, barka da fitowa" bata amsa masa ba tace
"har yanzu Sabo driver bezo bane?"
Cikin girmamawa yace "Eh ranki ya daɗe be ƙaraso ba"
HaÉ—e rai tayi ta jinjina kai ta koma cikin gidan
Sani yace "Isa ita kuma wannan wacece naga jikin ka se rawa yake dan tazo" sani ya tambaye shi
Isa yace
"kai bari kawai, itace 'yar masu gida bata da wa, bata da ƙani shalelen Alhaji kenan, watan ta uku da dawowa daga ƙasashen Turai, yarinyar nan sam bata taɓuwa, gaba ɗaya halin turawa shi take yi, yau kam kashin sabo ya bushe wallahi "
Sani yace "kamar ya kashin Sabo ya bushe meze faru?"
Be ƙarasa maganar ba aka fara bubbuga gate ɗin gidan, da sauri Isa yaje ya buɗe, wani mutum ne a ƙalla ze shekara Arba'in ya shigo kaman an koro shi.
Isa ya kalle shi yace "Taɓɗijan sabo yau kashin ka ya bushe, yanzu ta fito gurin nan neman ka"
Wanda aka kira da Sabo ya shiga rafka salati "na shiga uku yanzu ya zanyi, wallahi yarona ne babu lafiya na kaishi chemist"
Isa yace "ai bani za kayi wa bayani ba, seka je ka same ta"
Suna cikin maganar ta kuma fitowa, Fuskarta a haÉ—e babu annuri ta kalli sabo tace
"ƙarfe nawa nace maka zan fita?"
Jiki na rawa yace "ƙarfe sha ɗaya ranki ya daɗe"
"yanzu ƙarfe nawa ne?"
"shabiyu da minti goma"
"good, bani mukullayen motocina"
Sabo yace
"dan girman Allah kiyi hakuri ranki ya daÉ—e, wallahi yarona ne ba lafiya na kaishi chemist"
Cikin tsawa tace "shut up, did I ask you? Kabani keys É—ina"
Durƙusawa yake ƙoƙarin yi amma ta dakatar dashi "kai motocin na ubanka ne ko nawa?"
"naki ne Hajiya"
"idan har nawa ne, ka kawomin makullayena, na sallameka za'a bawa me gadi kuɗinka ya baka, daga yau se ya zama izina a gare ka, Alƙawari yana da mahimmanci cika shi alamace ta amana, lokacin aiki dana ɗauke ka mallakina ne ba mallakin ka ba tunda biyan ka nake, dan haka seda izinina za kayi duk wani abu komai girmansa in ba ibada ba tunda biyan ka nake"
tana gama maganar ta juya ta koma cikin gidan.
guri sabo ya nema ya zauna ya dafe kansa yana salati.
Isa yace "Sabo se dai haƙuri, Allah ya baka aikin da yafi wannan"
Cike da damuwa Sabo yace "Ameen Isa, Nagode sosai Allah yasaka da alkhairi, idan ta bada sauran haƙƙin nawa nazo in karɓa"
Sukayi sallama Sabo ya fice daga cikin gidan zuciyar sa a cunkushe babu daÉ—i.
Bayan tafiyar Sabo,
Sani cikin damuwa yace "wai Bala in tambaye ka mana, ita bata da mafaÉ—i bata san dai dai ba, bata san Afuwa da uzuri ba?"
Bala yace "Taɓɗijan kai kasan su amma ita kam bata sansu ba, wannan da kake gani tana da wata irin muguwar AƘIDA da ta tashi akai saboda rayuwa da turawa, zuciyar ta kaman Arniya gaba ɗaya Aƙidun turawa ne da ita bana musulunci ba, babu wanda ze iya raɓarta su zauna lafiya, Akwai matar mahaifin ta dake gidan nan ita da 'ya'yan ta, seta yi sati biyu seta ga dama za su ganta balle maganar fatar baki ta haɗa su, ta maida su tamkar bayin ta, idan kaga dariyar ta to da Mahaifin ta ne, da wani babban Aminin sa, ko wasu ƙalilan daga ƙawayen ta, bata da yadda sam, gani take duk wanda ya fiye raɓarta ba shi da gaskiya, Sabo shine driver na huɗu da tayi bayan dawowar ta Nigeria, ga Albashi me kyau ga mahaifinta da kyauta, amma kowanne ma'aikaci da ƙafarsa yake guduwa saboda izza da bala'in ta, 'yan aiki kuwa koni na kawo shida daga garin mu amma da ƙafarsu suke guduwa, yanzu kalli duk haƙuri da ƙoƙari irin na Sabo kaga yau yadda ta wulaƙanta shi ta kore shi"
Sani ya sauke nannauyar Ajiyar zuciya yace "to ina mahaifiyar ta? Ya aka yi aka bari ta tashi da wannan AƘIDA wadda tayi hannun riga da Akidunmu na musulunci da kuma na Al'adar mu?"
Isa yace "Mahaifiyar ta ta rasu, shi kuwa mahaifin ta duk abunda tayi dai dai ne a gurin sa, yace ɓata mata rai tamkar zuba wuta ne a zuciyarsa"
Sani ya dinga juya maganganun Isa a ransa yana tunani, Sallama yayi wa Isa ya fito ya tura wheelbarrow É—in mangwaronsa ya bar arear.
************************************
Wani matashine da baze gaza shekaru talatin ba zaune akan kujera ya tattara dukkan hankalin sa da tunanin sa akan allon na'ura me ƙwaƙwalwa dake kan teburin gaban sa ko ƙyafta ido ba yayi da alama wani abu ne me mahimmanci yake wa wannan kallon ƙurrilar.
Ƙwanƙwasa ƙofar ofishin da'aka yi ne yasa shi dawo wa hankalin sa a hankali yace "yes bismillah"
Turo ƙofar ofishin akayi aka shigo, wata matashiyar budurwa ce ta shigo jikin ta sanye da suit baƙaƙe da ɗan ƙaramin veil shima baƙi hatta takalmin ƙafarta baƙine, cikin taku na ɗaukar hankali ta ƙaraso gaban teburin sa tace
"barka da hutawa ranka ya daÉ—e"
Fuskarsa babu yabo ba fallasa yace "yawwa sannunki ya aka yi?"
Cikin iyayi da yauƙi tace
"dama Yallaɓai ne yace yana son ganinka a office dinsa"
ÆŠan jinjina kai yayi yace
"Alright zanje Insha Allah"
Cikin sigar shagwaba tace
"can i offer you something to eat, naga yau kaman ba kaci komai ba?"
Girgiza kai yayi tare da faÉ—in
"No thank you"
"Amma Yallabai dan Allah Yusuf fa?"
Ba tare da ya É—ago ba yace mata "be shigo ba"
Haka ta fita ta bar office ɗin gwiwa a saɓule tana tunani "komai za'ayi ba'a taɓa birge gayen nan daga shi har Yusuf, gara ma wannan akan waccan me kama da saƙagon da magana ma se ya ga dama yake yi" tai maganar a fili da sigar mita
Ya tattara system din ya kashe, ya É—auki wayarsa da mukullin motar sa, ya É—ora top É—in kayansa a kafaÉ—a da jakar sa ya fito ya nufi wani ofishin.
Yana shiga dayan ofishin ya ƙame cikin girmamawa ya sarawa wanda ke office ɗin da alama shugaban sa ne, be zauna ba seda aka yi masa izini sannan ya zauna suka sake gaisawa.
Mutumin ya É—ago ya kalle shi yace
"Abbas kana ganin babu matsala a wannan aikin da'aka baka kasan hatsarin dake cikin aikin zaku iya kuwa? Kana ganin akwai wani cigaba akan case É—in?"
Wanda aka kira da Abbas yai murmushi cikin girmamawa yace "karka ji komai ranka ya daÉ—e Insha Allah zan iya, zamu yi nasara, kuma ina fatan nasara Insha Allah yanzu idan na bar nan zanje in samu Yusuf
ne kasan shine jigon aikin"
"hakane to shikenan Allah ya tabbatar da Alkhairi ya baku sa'a na yadda da ƙwazon ku, Allah ya bada sa'a"
"Ameen yallabai muna godiya".
**********************************
Zaune yake Ya barbaza takaddu da na'urori masu ƙwaƙwalwa har biyu akan gadon sa ya tattaɓa wannan ya taɓa waccan, kafin daga baya yayi zugum yana kallon hotunan wata tsaleliyar yarinya, yarinyar wadda zata yi kimanin shekaru goma sha takwas sanye take da farin gajeren wando, se wata 'yar riga a jikin ta itama fara, ta saka farar hula hat ta baza gashin da ya kasa tantance nata ne ko na sawa ne, ga ƙaton baƙin tabarau a idonta ta buɗe fararen haƙoran ta tana dariya, bayan ta wani irin makeken ruwa ne shuɗi sosai, hannun ta na hagu riƙe da igiya da aka saƙalo wuyan wani jibgegen kare, jikinsa fal farin gashi ƙal, ba ƙaramin kyau yarinyar tayi a hoton ba. ko ƙwakwaran motsi ba yayi hotunan kawai yake dubawa kaman yana ƙoƙarin gano wani abu a jikin hotunan.
Wayarsa ce ta fara ruri, wanda ya sashi dawowa daga dongon nazarin da yake yi, ya duba wanda yake kiran wayar tasa yaga sunan Abbas akan Allon wayar tasa, yasa hannu ya kai wayar kunnen sa yace "Assalamu Alaikum warahmatullah"
Daga ɗaya bangaren aka amsa sallamar sannan wanda ya amsa din ya ɗora da cewa " ina ƙofar ɗakin ka kana cikine in shigo? akwai labari da nazo maka dashi"
"eh ina ciki shigo kawai"
Kafin ya kashe wayar aka turo ƙofar akayi sallama a ɗakin nasa, tashi yayi zaune ya aje wayar yana faɗin
"kai tun shekaran jiya daka turomin hotunan wata yarinya bamu kuma haɗuwa ba, kuma ka kashe wayarka, gashi saboda aikin nan ko Office bana zuwa ina ta ƙara bincike, ina ka shiga haka?"
Abbas yace "ka bari in zauna se in maka bayani sarkin ƙorafi"
"to zauna maza ka koramin bayani, wani labari kake tafe dashi?"
Abbas Ya samu guri ya zauna ya ajiye jakarsa ya tattara hankalinsa kan Yusuf sannan yace
" Yusuf kaga hotunan yarinyar dana turo maka dasu ta email É—inka?"
"Eh nagani, su nake ta nazari ban san dalilin da yasa ka turo su ba"
Abbas ya gyara zama yace "
hotunan 'yar gidan Alhaji Nasir Daula ce, kusan aikin mu gaba ɗaya akan ta yake, sati biyu kenan ina zuwa ina gidan su a matsayin me saida mangwaro da yankan farce, na samu karɓuwa a gurin megadin gidan su, hakan yasa idan naje se in zauna muyi ta hira da megadin su sannaan in tafi"
Yusuf ya gyara zama yace "to aini banga Alƙar binkicen mu da ita ba"
"Injiwa ai ta hanyar ta zamu samu duk abunda muke so, ita kaɗaice 'yar Alhaji Nasiru, kuma itace target ɗin maƙiyan sa, aikin mu ba' a akan iya bincike bane hadda bata Kariya"
Yusuf yace
"Abbas sanin kanka ne binciken nan na sirri ne, shi kansa Alhaji Nasir be san ana yin shi ba ta yaya zamu bawa 'yarsa kariya"
Abbas yace "Yawwa ɗan gari bazata taɓa sanin Aikin da muke ba, yadda mahaifinta be sani ba itama baza ta sani ba, a hirar da muke dame gadin su yau watan ta uku da dawo wa daga America a can take Rayuwar ta, maman ta ta rasu a hannun step mum ɗin ta take, a tsawon lokacin nan mahaifinta ya sangar tata da kuɗi a taƙaice dai muguwar taɓararriya ce me wata irin AƘIDA ta kafiya da taurin kai ga mugun tsatstauran ra'ayi kamar baturiya, yarinya ce da bata da yadda tafi bawa mage da kare mahimmanci fiye da mutanen dake kusa da ita, bata san zafin talauci ba balle tayi wa wani talaka uzuri ko ɗaga ƙafa hasali ma gani take kaman talakawa bayin sune masu kuɗi bata ɗaga ƙafa ko sassauta wa na ƙasan ta san.....
"kaga dakata wannan dogon labari haka, kamin bayani a taƙaice" Yusuf ya katse shi
Abbas yace "Dadina da kai ƙosawa, hotunan dana turo maka hotunan tane"
Yusuf yace "to me zanyi dasu?"
Abbas yace "Yawwa anzo gurin, da dawowar ta a wata ukun nan direbobi biyar aka sallama saboda baza su iya jure halin ta ba, tana da gadara da wulaƙanci, a gabana tayi wa direban ta korara wulakanci jiya, Yanzu haka megadin ya bani labarin mahaifinta yasa shi ya samo mata wani direban daze dinga kaita unguwa, yake gayamin ya gaji da samo mutane tana wulaƙanta su, akwai Albashi me kyau amma halin ta da AƘIDAR TA kesa mutum ya gudu da kansa, dan haka nace ni ya barni zan samo mata direba, kuma kai nake so ka zama direban nata!!"
Wani mugun kallo Yusuf yayi wa Abbas
"Ashe baka da hankali, kaime ya hana kaje ka zama direban nata?, ni zanje in dinga tuƙa ƙaramar yarinya tana wulaƙanta ni akan me? Bazan yi ba gaskiya, ai kaine gaba dani a gurin Aikin kai kaje mana"
Cikin sigar rarrashi Abbas yace
"Calm down brother, nasan zaka iyane kai ƙarshe ne gurin haƙuri, kaga ni bani da haƙuri zan iya lakaɗa mata duka idan tayi min ba daɗi ƙarshe in ƙare a prison in shiga uku, kaikuma kowa ya san ka akan haƙuri da hikima, dan haka zaka iya, ɗazu mukayi magana da Yallaɓai na tabattar masa zamu iya aikin nan, ita kanta yarinyar a cikin gagarumin hatsari take, akwai bukatar a bata kariya da kulawa "
Ɗan tsaki Yusuf yayi yace" gaskiya ni bana son wulakanci ne, yarinya ƙarama ta wulaƙanta ni dan ni talaka ne, gaskiya ni ka gama dani daka haɗani da wannan aikin, daka barni da kayan computers ɗina da damuwar da nake ciki da se yafi min"
Abbas ya kuma gyara zama yace "cigaban mu ne idan mukayi nasara dan Allah ka daure, Sannan Yusuf lokaci yayi da zaka cire damuwa ka fuskanci Rayuwa ka manta da ƙalubale ka gina Rayuwar ka"
Cikin takaici Yusuf yace
"Abbas kenan kana yiwa matsala ta kallon ƙaramar matsala, amma Allah shi ka ɗai yasan zugi da Raɗaɗin da nake ji a raina idan na tuna ni wane ne, wace Rayuwa zan gina bayan bani da dirakun da zasu riƙe min ginin Rayuwar tawa? Abunda ya faru dani yasa naji komai yafi ta daga raina, yanzu na barwa Allah al'amura na, in riƙe mahallici na, in rungumi ummana da Aikina nasan bani da kamarsu"
Abbas ya dafa kafaɗar Yusuf yace "Yusuf nasara bata samuwa ba tare da an jarabci ɗan adam ba, kayi haƙuri da taka ƙaddarar, Allah yana sane da kai"
Yusuf yace "Hakane Allah yabani ikon cin jarrabawa"
Abbas ya amsa da Ameen, sannan ya É—ora da cewa
"Aiki na gaba se bayan ka zama direban ta sannan zan sanar da kai shiri na gaba, zan gaya maka aikin da'a ke so kayi"
Yusuf yace "to Allah ya bani iko ya tabattar da alkhairi ya bamu nasara"
"Ameen ya Allah, É—azu fa mutuniyar ka tazo office É—ina tana ta kwarkwasa, take tambaya ta kana ina?"
Yusuf yace "wa kenan?"
"kafini sani ai, wacece in ba Sakina ba"
Tsaki Yusuf yayi yace "dan Allah Abbas ka dena sa kamin wannan yarinyar cikin lamurana, ni tun abunda ya faru dani duk wata harka da mata gudun ta nake yi, wannan aikin ma da kuka bani kaida yallaɓai dan ba yadda zanyi ne harka ce ta aiki, balle wata Sakina, ni ina tsoron mata nafi ƙaunar tsira da mutunci na da kuma tsayawa matsayin da Allah ya ajiye ni, nayi darasi akan abunda ya faru dani"
Abbas yace "hakane kana da gaskiya Yusuf, Amma ka sani idan har mukayi nasara a Aikin nan cigabanka ne, sekafi kowa benefitting gaba kaɗan in aikin ya kankama zan ƙara sanar da kai wasu abubuwan"
Abbas ya ci gaba da kwantarwa da yusuf hankali tare da lallaɓa shi har ya ƙara gamsuwa ya Amince Amince akan zasu je gidan Alhaji Nasiru Daula da weekends domin a tantance shi in ze iya zama direban Wannan yarinya me muguwar AƘIDA sannan a gabatar da Yusuf a matsayin Sabon direban wannan 'yar Hamshaƙin Attajiri Me murɗaɗiyar AƘIDA!!!.
Tun bayan da Abbas ya tafi, Yusuf yake ta tunani akan wannan gagarumin Aiki, yana ƙara duba kyawawan hotunan wannan yarinyar da ko sunan ta be sani ba, she has an innocent face a hoto, gata very young and beautiful amma ya akayi take da halaye marasa kyau haka?
Idan har ya kasance da gaske tana da duk wannan halaye da'aka faÉ—a masa anya ze iya aikin kuwa?
Amma meyasa Abbas be warware masa yadda aikin yake ba gaba É—aya yace se ya fara yi wa yarinyar aiki ze gaya masa?
"Allah yasa ba cikin wata cakwakiyar zasu jefa ni ba" yai maganar a fili tare da miƙewa ya tattare kayan da ya baza a kan Katifar sa ya fito daga ɗakin nasa.
Kasancewar Yamma ce bashi da gurin zuwa da yake shi bame yawan shiga sabgar mutane bane, ya shiga É—akin Umman sa ya É—akko kayan wankin ta ya wanke tsaf, ya share ko ina, ya É—ora girki se kace mace, cikin nutsuwa yake Al'amuran sa ya kammala dafa shinkafa da miya ya zuba a flask, lokacin ana ta kiraye kirayen sallar magariba yayi Alwala ya fice Masallaci.
Ayshercool
07063065680
             _*AƘIDA TA*_
      Â
   *PART1*     Â
         _Page 2_
*written and edited by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
Bismillahir rahmanirrahim, da sunan Allah me Rahama me jin ƙai, Wannan littafi ƙirƙirarren labari ne banyi shi dan cin zarafi ko cin fuska ga wani ko wata ko wata ƙabila ba, idan har wani ko wata yaga wani abu daya yi kaman ceceniya da rayuwar sa ko ƙabilar sa Amin Afuwa banyi dan cin zarafin wani ko wata ba.
  Wannan littafin mallaka tane, ban yadda a juyamin labari ta kowane fanni ba ba tare da izinina ba.
What's App : 07063065680
Watpad : Ayshercool7724
Gmail : Www.ayshertadam@gmail.com
************************************
Wata Babbar Mace ce Zaune a cikin wani katafaren falo me girma sosai, cike yake da kayan more Rayuwa, Aƙalla zata kai shakaru hamsin, Amma kaman 'yar shekara talatin da biyar saboda hutu idonta sanye da glashi ta nutsu sosai tana danna Computer tana shan tea.
Wata matsashiya ce ta shigo falon a ƙalla za ta kai shekaru Ashirin da bakwai, tazo ta zauna a kusa da Matar.
Ba tare da Matar ta ɗago ba tace "Ya a kayi ne? Nasan akwai damuwa tunda na ganki yanzu meya faru?" ta ƙarasa maganar tana kallon matashiyar.
Ta É—an yatsuna fuska tace " Mummy kin san wani abu?"
"A'a sekin faÉ—a" matar ta bata Amsa
Cikin shagwaba tace "Mummy ki duba girman gidan nan da cikar sa, kalli dukiyar dake cikin gidan nan, Amma mota ɗaya tak na mallaka, ko ɗan direba ma ba'a sama min ba, Amma kalli 'yar masu gida motocin ta nawa? Direbobi nawa ta wulaƙanta ta sallama a dawowar nan tata? Har motocin me gidan nan take hawa in ta ga dama gaskiya ana nuna mana wariyar launin fata, banda cin fuska da wulakanci da muke fuskanta seka ce wasu Bayi"
Matar ta cire glashin fuskarta tace
"Ramlah me kike so inyi? Alhaji Baya jin magana ko ganin girman kowa sena 'yar sa, abunda take so shi yake yi, Sannan duk abubuwan nan da suke faruwa na É—an lokaci ne, Amma me kike so ayi? "
"Mum Mota nake so a canzamin sannan nima a ɗaukar min direba, bama mota ba motoci nima in dinga kece raini yadda yakamata, kalli daular da muke ciki, Amma a ce se abunda yarinya ƙarama take so akeyi, Mummy ina son inyi birthday ina buƙatar kuɗaɗe masu yawa fa wanda zan burge ƙawaye na dasu, Sannan naji labarin Akwai filayen da gwamnati za ta yi gwanjonsu a GRA ya kamata ace kin mallaka"
"Hmm Ramlah kenan samun wannan abubuwane masu Sauƙin samu a hannun me gidan nan, Amma kin san seda izini kokuma ince yaddar 'yarsa ko?"
Ramlah tace "Amma Mummy ba yadda za' ayi in samu kuÉ—in a hannun ki? Kina matarsa amma ace se Abunda 'yarsa take so haba dan Allah, yakamata ace Akwai wata Dama da zaki dinga mallakar kuÉ—aÉ—e bayan wanda yake baki"
"babu wannan damar, dan duk kuɗin dazan fitar seda sanin Lawyern sa, dan haka ba yadda zanyi, Karki manta muna da kyakkyawan shiri a ƙasa shiyasa sam bana damuwa, ni yanzu so nake in lallaɓa shi Amal me ta tafi turkey ta ci gaba da karatu a can"
Ramlah tace
"shikenan Amma yakamata kiyi wani abu akai kar wannan damar ta wuce mu, Amma kafin wannan ya batun canza motarfa?"
Mummy tace "Wannan kuma sekin yi tsani da 'yar masu gida, tana magana ko mota goma kike so kamar kin samu, batun kuÉ—i kuma zan tura miki kuÉ—i Account É—inki base munjira ba, Amma ki same ta in ta yadda za tayi masa magana a baki wata motar"
Ramlah ta yamutsa fuska tace
"A' a Mummy ke zaki mata magana, kin san ba shiga sabgarta nake ba, bana son wulaƙanci da rainin hankali, kin san bama shiri da ita"
Mummy tace "ke kina tunanin idan nayi mata magana zata saurare nine? Yau kwana biyar rabon da in sata a idona fa yarinyar nan barta kawai"
Ramlah tace "bari in kira miki ita dan Allah ki mata magana ko zata sa baki, ni kin san bama jituwa da ita"
Mummy ta É—an jinjina kai tace "shikenan Allah yabada sa'a"
Tana zaune akan stool a gaban dressing mirror ɗin ta wanda yake shaƙe da kayan shafe shafe na mata, towel ne a jikin ta tana ta ƙoƙarin tsane gashin kanta.
Ƙofar É—akin aka turo aka shigo, wata matashiyar budurwar ce ta shigo É—akin ba tare da tayi sallama ba ko wata doguwar maganaba taceÂ
"Mum nasan ganin ki a cikin gida, zakuyi magana"
Wadda akewa maganar se kace da gini ake, ko gezau ba tayi ba ta ci gaba da abunda take yi, bata kalli me mata maganar ba ta cigaba da abunda take yi .
Cikin ƙosawa da fushi matashiyar wadda aƙalla ta girmi wadda take wa maganar nesa ba kusa ba tace
"wai ba kyaji ina miki magana ne? Kin min banza kaman baki san na shigo ba?"
Cikin isa yarinyar ta Ajiye Ƙaramin Towel ɗin hannun ta, ta miƙe ta nufi wardrobe ɗin ta, Subhanallah koda ta buɗe wardrobe ɗin sutura ce a ciki kaman shara, kamar inji ne ya shirya kayan ba hannu ba, kai in akace suturar mutum ɗaya ce seka riƙe baki tareda tunanin ina mamallakin suturar ze kai ta?
Ta saka hannu ta janyo wata 'yar riga ja mara hannu, tana ƙoƙarin sakawa ba tare da ta waigo ba cikin ƙasaita tace
"Ramla ki koma ki gayawa wadda ta aiko ki banyi budget da lokacin da zan bata ba a yanzu, ko menene idan ta damu tazo da kanta ta sameni in gani ko zan iya saurarta, idan kuma bame mahimmanci bane zata iya haƙura har se lokacin da Allah yasa na shigo cikin gidan, you can go out i need privacy"
Cikin ɓacin rai Ramla tace "Waike wace irin mara ɗa'a ce haka? Mahaifiyar tawa ce zata zo ta same ki? Kika san me yasa ta kira ki? Se kace sa'ar ki?"
"koma me zesa ta kira ni nasan baze wuce biyan wata buƙata tata ba kokuma ta 'ya' yan ta, ni kuma da ku da ita bani da lokacin ku a yanzu, ɗan fitar min daga ɗaki, zan kaɗaice inyi tunani"
Ramla tace "Amma baki da kirki, a gabana kike faɗan maganganu akan uwata, ke har Abada girma da shekarun mutum baya sa ki bashi girma, Ko ance miki rayuwar Turai hauka ce? Rayuwar turai fa ta saɓa da Al'adunmu, Ko kuma akanki aka fara Arziki?"
"Enough Ramlah" Yarinyar ta katse ta ta nuna Ramlah da yatsa ta ɗora da cewa
"Amma kamar kin san ba'amin shouting ko? You know the consequences of doing that. Mahaifiyar ku, ku ta haifa, ni kuma Babana take Aure bata haifeni ba, what's the meaning of respect according to you ne Ramla? Your mother is just a human being like everyone, she don't deserve any special respect, i will treat her the same way i treat every human being, and mark you This is my father's house, if you are tired of what am doing, go back to your father's house, nan gidan mahaifina ne ina da right inyi abunda nake so, and no one should stop me from doing what I want, if you are tired of what am doing park your things and go, madam get out from my room, kaina ya fara ciwo ki fitar min daga ɗaki "
Cikin faɗa take maganar, hannun ta ɗaya riƙe da kanta, tana nunawa Ramlah ƙofar fita
Ramla ta ƙulu matuka ta fice a fusace tare da buga ƙofar ɗakin da ƙarfi.
Falo ta koma inda tabar mahaifiyar ta, kallo É—aya Mummy tayi mata ta É—anyi murmushi tace "yana ganki a fusace?"
"Mummy wallahi yarinyar nan bata da mutunci, kinga rashin mutuncin da tamin kuwa, wallahi badan ina gudun abunda ze biyo baya ba sena shaƙeta kowa ya huta"
"hmm Ramla kenan, baki ga komai akan halin ta ba, ni da nake tare da ita ni nake ƙunsar takaici da baƙin ciki, Amma ina jiran lokaci ne wanda...
Bata ƙarasa ba tai shiru tareda yin murmushi ta dafa kafaɗar Ramla tace "karki damu daughter, saura ƙiris komai ya canza, na sama ya koma ƙasa, na tudu ya koma ruwa, a wannan lokaci da dariya zata gagari kare, hmm kiyi hakuri ni da kaina zan canza miki mota, in ɗaukar miki driver kinji?"
Shiru Ramla tayi ba tace komai ba se faman huci da take yi. kaman an mintsine ta tace
"wallahi na tsani yarinyar nan Mummy, bana ƙaunar ganin ta ji yadda aka maida ke da mu kaman wasu bayi ko 'yan Alfarma a gidan nan, ai ko Albarkacin kina Auren mahaifinta ya kamata ace muna da matsayi na musamman"
Mummy tace
"nifa nace kiyi hakuri ko? Komai ya kusa zama tarihi"
********
Yusuf Yana zaune har Bayan sallar isha'i yana kallon labarai, yaji anyi Sallama amsa sallamar yayi tareda ɗan ɓata rai.
Me sallamar ta shigo falon ta ajiye jakarta da mayafi ta É—an kalli inda Yusuf yake tace
"fushi kuma ake dani, ko a kalli inda nake? Ai gani na dawo"
Yusuf yace "haba Umma tun azahar kika fita se yanzu bayan isha'i duk kaÉ—aici ya dameni"
Umma tace "kai tafi can, sekace wanda nake shayarwa ba damar in É—an fita, ka dinga damuwa kenan"
Cikin shagwaba yace "wana keda shi inba Ummana ba? Dole in shiga damuwa duk lokacin da kikayi nisa dani ummana, daga Allah seke se kuma Aikina ku kenan nake da su, niba Abokai ba ko wasu mutane na musamman ke ɗin ce dai, Allah ya jiƙan Abba na, tun abunda ya faru Umma ke kaɗai nake da yaƙinin ƙaunar ki a gare ni baza ta gushe ba, shiyasa bana son kiyi nisa dani"
Tausayin Yusuf ne ya mamaye ta, har zuciyar ta ta karaya hawaye na ƙoƙarin fita daga idon ta, da sauri ta fice ta bar ɗakin da nufin yin Alwala.
Bayan Umman Yusuf ta idar da sallar isha'i suka ci Abincin dare tare suna hira, Yusuf yana ta so ya sanar da Umman sa batun Aikin da'aka bashi a Office amma ya kasa, dan yasan idan har ya gaya mata ranta zata ji babu daÉ—i, ace É—anta Yazama direban yarinya, Yarinyar ma mara tarbiyya wadda bata san darajar É—an Adam ba, dan haka ya bar abun a ransa be gaya mata ba.
Haka ya kwana yana tunanin wace karɓa ze samu a gurin yarinyar nan? Ya aikin ze kasance? Haka yaita tunani har bacci ya ɗauke shi.
Washegari ma Yusuf yayi ƙoƙarin yiwa Umman sa zanncen amma ya kasa, haka yai breakfast ya tafi gurin Aiki.
A office ma kasa wani aikin kirki yayi, wayar sa ya É—akko yana kuma duba hotunan wannan tsaleliyar yarinyar, ya kuma tuna irin halayen ta da Abbas ya bashi labari. ÆŠan tsaki yayi ya ajiye wayar ya jingina da kujera ya dafe kansa yana tunani.
Sallamar Abbas ce tasa ya É—ago kansa, Abbas yace "Yusuf dama ka shigo yau baka nemeni ba?"
"na shigo tun É—azu ina aiki ne shiyasa ban neme ka ba"
"OK tashi muje, Yallaɓai Suleiman na son ganin mu yanzu"
Yusuf ya miƙe yabi Abbas suka fice, suna zuwa suka gaisa cikin girmamawa, yai musu umarni suka zauna.
Yallaɓai Sulaiman yace "Yusuf nace kuzo tare da Abbas ne dan tabattar da cewar aikin da muka ɗora muku zaku iya, mussman kai Yusuf nasan kana da kula da aiki kuma kana da haƙuri matuƙa"
Cikin girmamawa Yusuf yace "Insha Allah Yallaɓai baza'a samu matsala ba"
"Good kayi taka tsan2 kabi a hankali, karka kuskura wani yasan bincike ne ya kaika gidan, kasan aikin ka base na gaya maka ba, samun matsala a wannan aikin gagarumin hatsari ne da kuma Asara ina fatan kun san hakan"
Yusuf ya risinar da kai yace "Insha Allah ba zamu baka kunya ba sir"
"kai kuma Abbas ku kula yadda ya kamata"
Abbas yace "Insha Allah sir za muyi iya ƙoƙarin mu"
Haka suka ci gaba da tattauna wa akan harkar aiki, sannan Yallabai Suleiman ya sallame su.
Bayan fitowar su Abbas yaita bawa Yusuf ƙwarin gwiwa tareda bashi shawarwari, suka tsara yadda tafiyar tasu zata kasance ranar Asabar zuwa gidan Alhaji Nasir Daula.
Tunda gari ya waye Asabar gaban Yusuf yake faÉ—uwa, ya rasa dalilin da yasa tun da'aka gaya masa Aikin daze yi yaji gaban sa na faÉ—uwa a duk sa'ar daya tuna, har seda Umman sa ta fuskanci ya rage walwala, ta tambayeshi yace mata "bakomai" haka Yusuf yaci gaba da Adduo'i.
Yana nan zaune a ɗakin sa ya rasa abunda yake masa daɗi, misalin ƙarfe sha ɗaya na safe Abbas yazo, ya tsaya a tsakar gida suka gaisa da Umman Yusuf sannan ya shiga ɗakin ya same shi.
Abbas ya kalleshi daga sama har ƙasa yace
"gaskiya Yusuf wannan kayan naka ba suyi kama da wanda zeyi aikin direba ba, gaskiya ka canza kaya, ni baka ga kayan da na saka ba"
Se lokacin Yusuf ya lura da koɗaɗɗen Yadin dake jikin Abbas, Yusuf ya ɗanyi murmushi yace "Taɓɗijan, wannan wane irin kaya ne?, ni ban san wani kaya zan saka ba"
Abbas ya buɗe wardrobe ɗin Yusuf, duk kayan Yusuf masu kyaune, da ƙyar ya ɗakko masa wasu ƙananan kaya ya bashi ya saka suma dai basu ji jiki ba, Yusuf ya karɓa ya saka, yace "Allah yasa kar Umma tayi min magana akan kayan nan"
har zasu fita Abbas yace "É—an tsaya idan muka je gidan Sunana Sani me mangwaro ba Abbas ba "
Yusuf ya jinjina masa kai sannan suka fito, Yusuf ya kalli Ummansa dake kwashe kayan wanke2 yace "Umma zamu fita"
Umma tace "to Yusuf, Abbas ka gaida gida sekun dawo"
Har zasu fita Umma ta kira yusuf tace "Yusuf zo nan"
Dawowa yayi tace "Wannan wace irin shiga kukayi, kalli kayan jikinka be kamata ace ka fita da su ba, Allah ya rufa maka Asiri amma kasa wannan kayan kana yawo a gari"
"Umma shima hakan cikin harkar Aiki ne, idan na dawo zan miki bayani Insha Allah"
Umma tace "Amma harkar aiki shine zaka fita da wannan suturar kamar mara galihu"
"haba Umma wallahi kayan nan da kyansu, kiyi min Addu'a sena dawo"
ÆŠan girgiza kai tayi yayin da Yusuf yayi waje da sauri.
Napep suka tara suka hau zuwa gidan Alhaji Nasir, yayin da gaban Yusuf keta faÉ—uwa.
Tun daga bakin layin shiga rukunin gidan jam'ian tsaro ne ke kaiwa suna komo wa, seda aka musu tambayoyi kafin su wuce da yake sun gane Abbas yana zuwa, aka barsu suka wuce.
Koda suka je gidan Abbas ne ya sallami me Napep ɗin, tun daga waje Yusuf ya fara ƙarewa gidan kallo tirƙash lallai mamallakin gidan yaci ai masa inkiya da Daula.
Suka ƙarasa ƙofara katafaren gate ɗin suka tsaya, Abbas ya ɗakko wayarsa ya kira Isa me gadi, yace masa suna waje.
Befi mintuna uku ba aka buɗe ƙaramar ƙofar dake jikin gate ɗin ya leƙo yana ganin su Abbas ya washe baki yace
"bismillah ku shigo Ashe kaine"
Suka shiga suka tsaya suka gaisa da Isa.
Isa yace "Sani wannan ne É—an uwan naka daze aikin?"
Abbas yace "Eh shine"
Isa yace "Ya sunan shi?"
"Sunana Yusuf" Yusuf ya bashi amsa
Isa yace "masha Allah to Allah yaba ka iko, dan seka yi haƙuri aikin akwai samu amma babu sauƙi, bari inje in sanar wa da Alhaji zuwanku"
Abbas yace "shikenan babu laifi"
Bayan tafiyar Isa, Yusuf ya kalli harabar gidan, wasu irin motoci ne masu rai da lafiya a tsaye a gefe ɗaya, yayin da ainihin ƙofar shiga katafaren gidan se kayi wani gajeren tattaki daga gate ɗin kafin ka kai ga ƙofar.
Yusuf ya numfasa yace
"wai ni Abbas ya aka yi rukunin gidajen nan jam'ian tsaro ke gadi, Amma kuma nan gidan naga wannan ma shiriricin ke gadi"
Abbas yace "Sani dai ba Abbas ba"
Yusuf yace "Am sorry, Sani"
Abbas yace "duk yana cikin binciken da za kayi, ka kula kayi taka tsan2, banda sakin jiki da kowa dama nasan kai ba me son hayaniya bane"
Isa ya dawo yace "bismillah ku taho mu shiga, Alhaji yace a shiga daku"
Tunda suka kama hanyar shiga cikin gidan Yusuf yake ƙarewa ko ina kallo, an danƙarawa gidan dukiya kaman ba'a san ciwon ta ba.
Wasu irin faluka suka dinga ratsawa, kowanne da kalar sa da irin tsaruwar da yayi, shikan sa Abbas be san haka cikin gidan yake ba.
Sunyi doguwar tafiya kafin su iso wata ƙatuwar ƙofar glashi,Isa yasa hannu ya murɗa suka shiga da sallama.
Iya girman falon nan ya ishi wani talakan gina wadataccen gidan da ze zauna, Yusuf ya fara tambayar kansa shi kuwa wannan wane irin sana'a yake yi da har ya gina wannan gidan kamar baze mutu ba?
Babban mutum ne a zaune akan wata luntsumemiyar kujera yana karanta jarida gefen sa da wata mata, se 'yan mata biyu zaune akan kujerar dake facing É—in su.
Aka amsa musu Sallamar, cikin girmamawa suka gaisa da me gidan tare da iyalan sa, yanayin gaisawar tasu ze nuna maka mutum ne me fara' a, dan kuwa fuskarsa É—auke da murmushi ya amsa musu.
Isa yace "Yallaɓai sabon driver ne da kace a samo, shine suka zo yanzu"
Ya ajiye Jaridar hannun sa yace "Masha Allah wanne ne daga cikin su?"
Cikin girmamawa Yusuf yace "Nine"
Alhaji Nasir ya ɗan ƙura masa ido yace "masha Allah, ya sunan ka?"
"Suna na Yusuf"
Alhaji Nasir ya jinjina kai yace "Hajiya Halima kinji me sunan Yaya na ko?"
"Aikam dai me sunan shi" ta amsa
Alhaji Nasir yace "Allah sarki, Allah yasa me irin halin sa ne, ni duk Yusuf É—in dana sani mutanen kirki ne, ina fatan kaima haka?"
Abbas yace "Alhaji ba ganin ido ba Shima mutumin kirki ne sosai"
Alhaji yace "ai dama na sani, ban taɓa ganin Yusuf mutumin kawai ba"
Ya kalli 'yan matan nan dake zaune yace "Amal jeki part ɗin gimbiya ta, ki gani idan idon ta biyu bata komai ki gaya mata Daddy na son ganin ta, idan kuma da abunda take yi ki ƙyaleta"
Wadda aka kira Amal ta miƙe tare da cewa "to Daddy" .
Babban abunda ya bawa Yusuf mamaki be wuce tun lokacin da' aka ce shine ze zama direban, matar da 'yan matan nan suke binsa da kallo ba, mussman wadda aka kira Amal yadda ta tsare shi da idanuwa.
Seda akayi Minti goma sha biyu da tafiyar Amal, sannan ta dawo tace "Daddy tace tana zuwa"
Alhaji Nasir yace "to babu laifi"
Wasa2 seda sukayi minti Arba'in ba suga Alamar wadda aka kira É—in zata fito ba, iyalan suka ci gaba da hirar su aka bar su Yusuf shiru kamar mayu.
Gaba ɗaya Yusuf ya gaji da zaman, ga sanyin A. C da kallon ƙurillar da'ake masa duk yabi ya takure.
Alhaji Nasir ya kuma cewa "Ramla bawa baƙin nan Abinci kafin ta zo"
Ba tare da Ramla tace komai ba ta miƙe ta fice, ruwa da fruits ta kawo ta ajiye musu.
Abbas da Isa suka dinga É—auka suna ci suna kallon tv, shikam Yusuf ya kasa cin komai, gaba É—aya a takure yake, gashi ko É—aga kai baya son yi saboda kallon da'ake masa.
Kaman ance ya ɗaga kai idonsa yayi tozali da wata irin kyakywar halitta, babu shakka itace a jikin hoton da Abbas ya tura masa, Amma a zahiri tafi haka kyau, gabansa ne ya dinga faɗuwa ƙirjinsa yana bugawa da ƙarfi, yarinya ce sharaf amma se kwarjini fara ce ƙal tana sanye da skin tied iya gwiwarta, se wata over size shirt data saka har wajen gwiwarta, kanta babu ɗan kwali gashin ta a hargitse babu ribbon, ta sake shi a kafaɗun ta.
Fuskarta a haɗe babu annuri, ta ƙaraso cikin falon ta zauna kusa da mahaifin ta. Tana zama Hajiya Halima ta miƙe ta canza wata kujerar
Alhaji Nasir yace "Lovely daughter ina fatan ba'a takura miki ba?"
Girgiza masa kai tayi alamar A'a
Alhaji Nasir yace "Sabon driver ne gashi nan, yazo ki gani in yayi miki"
Kamar baza tace komai ba ta ɗago ta kalle su ɗaya bayan ɗaya ta tsaida idon ta akan Yusuf ta ɗan ɗau lokaci tana kallon sa kaman tana ƙoƙarin gano wani abu.
ÆŠauke kai tayi ta haÉ—e rai cikin isa tace
"Ramla kawo min madara da cup, sannan kije falona ki kawomin wata folder akan kujera"
Waigawa Yusuf yayi ya Kalli wadda aka kira Ramla, ta girmi yarinyar da har yanzu be san sunan ta banesa ba kusa ba, dan shi har yanzu beji wanda ya faɗi sunan ta ba, ramla ta miƙe ta tafi cika umarnin ta.
Yarinyar da dudu bata fi shekaru sha takwas zuwa sha tara ba, a idon ta da yadda take magana zaka gano tsabar izza, da isa, Ta kalli Abbas tace "kai kaman na sanka ko?"
Abbas yace "eh ni abokin Bala ne, ina zuwa gurin sa"
"good, kai Bala meye aikin ka?"
Cikin Rawar jiki yace "gadi ranki ya daÉ—e"
"to ka tashi da kai da shi ku fita ka koma kan aikin ka"
Ba musu bala ya miƙe, Abbas ma ya miƙe, kafin su bar falon ta kalli Hajiya Halima tace
"Madam i need privacy you can leave"
Ɗan taɓe baki Hajiya Halima tayi ta miƙe ta nufi wata ƙofar daban.
Ta kalli inda Amal take ta mata wani kallo, tun kafin ta furta komai Amal ita ma ta miƙe ta nufi barin falon.
Gaba É—aya mamaki ya cika Yusuf, yadda take wannan izzar take wa manya magana babu respect kuma a gaban mahaifin ta amma bece komai ba, ya ma maida hankali akan jaridar sa kaman be san me take yi ba.
Ramlah ta dawo ɗakin ɗauke da cup da madara tazo ta ajiye, sannan ta miƙa mata folder, taje ta nemi guri akan kujerar da ta tashi zata zauna, Amma suka jiyo zazzaƙara muryar ta tace
"wait don't sit, get out from here, bana buƙatar wani a falon zan gana da shi"
Wata irin Ajiyar zuciya Ramlah tayi ta ɗan jinjina kai ba tare da ta waigo ba ta miƙe ta fita ta bar falon itama.
Madarar ta ɗauka ta zuba a cup tana sha, tana kaɗa ƙafa kaman tama manta da Yusuf a gurin.
Alhaji Nasir ya kalle ta yace "gimbiyar Daddy bari inje in É—an watsa ruwa zan fita anjima, yadda kuka yi dashi kya gayamin in na dawo, in yayi miki.
ÆŠan É—aga girar ta É—aya tayi ta lumshe ido ba tare da tace komai ba.
Bayan tafiyar mahaifinta haka suka ci gaba da zaman kurame ita da Yusuf
Can ba zato ba tsammani yaji tace
"what's the level of your Education?"
Yusuf ya ɗanyi jim sannan yace "secondary school" yai maganar ƙirjinsa na bugawa
Shiru ta kuma yi tana kallon tv seda aka kuma jan wani lokacin sannan ta kuma cewa
"Meye sana'arka?"
Gumi ne ya fara tsatstsafo masa dukda sanyin AC da yake ɗakin, Yusuf baya son kuma yin ƙarya, Amma yace
"Eh ina É—an zuwa kasuwa ne ina yaron shago"
Cikin Tsara magana da take daki daki, da muryarta me sanyi tace
"Anyway naga kaman za kayi hankali, zan iya yadda ka zama direba na amma ina da sharuÉ—ai"
Ta É—anyi shiru kaman ba zata kuma magana ba, sannan ta É—ora
"bana son ƙarya, duk ranar da na gano kayi min ƙarya zaka fuskanci hukunci me tsauri, bana son sa ido da shishigi a cikin lamurana, bana yafewa maƙaryaci ko wanda yaci amana ta, babu ruwan ka da irin mutanen da nake hulɗa dasu, bana yadda da mutum kowaye ni kaina wani lokacin bana yadda da kaina balle wani, dan haka duk lokacin da kayi motsin da ban yadda da shi bama zan iya sawa a kulle ka, ban yadda da saɓa lokaci ko Alƙawari ba, sannan lokacin dana ɗauke ka aiki mallaki na ne bana ka ba, ibada kaɗai kake da 'yancin yi, bayan wannan baka da hurumin yin wani aiki idan ba nawa ba, se dai idan ni na baka dama, in ka amince da sharuɗai na" ta ajiye wata takadda
"kayi signing anan, salary 200k and your hard work determines your salary promotions"
Shiruu Yusuf yayi yana tunani, gaba É—aya ya rasa abun yi
Yusuf yace
"ranki ya daÉ—e ko zaki iya bani dama inje inyi shawara"
"I don't gives second chance, and I don't want too much waste of time" ta bashi amsa tana maida hankalinta kan talabijin
Shiru Yusuf ya kuma yi ya É—auki takardar yana jujjuya ta ba tare da ya karanta meye a jiki ba, gumi se karyo masa yake ya ciro biro a Aljihun sa, hannun sa na rawa ze sa hannu yaji tace
"that means you accept the terms and conditions i have mentioned?"
Jinjina kai yayi alamar yana ƙoƙarin ya saka hannu tace
"if you are here to spy don't sign this paper"
(idan kazo nan ne dan leƙen Asiri kar kasa hannu a takardar nan)
Ras! Gaban Yusuf ya faɗi, Anya babu wata a ƙasa, yarinyar nan bata san komai ba? Cikin ƙwarewar Aikin sa ya dake yace
"ranki ya daÉ—e menene Spy kuma?"
Banza tayi masa ba tace komai ba.
Seda Yusuf yayi Addu'a a zuciyar sa sannaan yasa hannu akan takardar.
Ta sa hannu ta É—auki takardar ta jujjuya ta sannan tace
"signing this paper is like signing on your death contract!!! Jeka sena neme ka"
Tana gama faɗin haka ta miƙe ta bar falon
Ras! Ras!! Ras!!! Gaban Yusuf ya faÉ—i
A fili yace "My death Contract kuma?"!!!
Ayshercool
07063065680
           _*AƘIDA TA*_
        Â
         *PART1*    Â
              _Page 3_
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Special thanks to my Association Members
Perfect writers Association
Maimaita death contract Yusuf ya dinga yi, ya rasa abunda ya kamata yayi, a hankali ya miƙe ya biyo hanyar da Isa ya biyo da su ya fice.
Abbas yana tare da Isa yana jiran fitowar Yusuf, kallo ɗaya Abbas yayi masa yasan akwai matsala, da ƙyar Yusuf yake ɗaga ƙafarsa, Isa da Abbas suka dinga tambayar sa meyafaru? Amma yaƙi cewa uffan, Abbas yayi wa Isa Sallama ya ja Yusuf suka tafi, be ƙara tambayar Yusuf ba har suka je gidan su Yusuf.
Da suka je gidan ma Yusuf yai mursisi yaƙi faɗa wa Abbas yadda suka yi, daga ƙarshe dai Abbas ya ƙyale Yusuf ya ɗauka ire iren wulaƙanci ya fara fuskanta, dan haka yaita bashi haƙuri yana kuma rarrashin sa kan ya daure kar ya karaya.
Sam hankalin Yusuf baya kan Abbas, gaba ɗaya ƙwaƙwalwar sa ta shiga lissafe lissafe daban2, a karon farko da shigar sa Aiki wannan ne aiki me matuƙar wahala da sarƙaƙiya a gare shi, yana buƙatar nutsuwa da taka tsantsan akan komai.
"Yusuf naga kaman hankalin ka baya kaina fa?"
Yusuf yayi ajiyar zuciya yace "ta yaya zaka samu hankali na, tace ba'a mata ƙarya bata yafe wa wanda yayi mata ƙarya, Nikuma akan ƙaryar ma naje nake aikin, yanzu idan ta gane gaskiya fa?"
Abbas yace "karka damu kayi abunda ya kamata kawai tana ƙoƙarin yi maka ba razana ne, idan kabi a hankali ba zata gane komai ba"
"to Allah yasa?"
Abbas yace "Ameen"
Bayan tafiyar Abbas fa tunani ya auri Yusuf, kasa jurewa yayi seda ya gayawa Umman sa aikin daze jeyi a matsayin direba gidan Alhaji Nasir Daula amma ya ɓoye mata gaskiyar halin yarinyar da sharuɗai da ta saka masa.
"Yusuf wace irin lalacewa ce kana aikin ka gwanin sha'awa zaka koma wani direba?"
"Umma ba lalacewa bace, harkar aiki ce ta kawo haka"
"hakane amma ni bana son sabga da masu kuɗin nan yaran su ba tarbiyya suka cika ba, bana so a wulaƙanta min ɗa a banza, gurin aikin naku babu wanda zasu saka se kai"
Yusuf yace "Umma Addu'arki da goyon bayanki nake buƙata, idan kika soki abun zaki kashe mun gwiwa ne"
Umma ta numfasa tace "shikenan Allah ya tabattar da Alkhairi, Allah yabada sa'a, ka kula da kanka"
"insha Allah umma na nagode sosai"
'yan kwankin nan Gaba ɗaya bacci ya ƙauracewa idaniyar ta, duk motsin da zata yi surar Yusuf take gani, rashin walwalarta da yawan son kaɗai cewa ne yasa 'yar uwatta lura da akwai abunda yake damun ta kasancewar ta me surutu da san hira.
Ramla ta dubi yadda' yar uwar tata tayi shiru tana jujjuya spoon a cikin cup ko sau É—aya bata kai abunda ke kofin bakin ta ba, bayan shafe kusan mintuna goma da zaman da tayi da niyyar cin Abinci.
"Amal wai me yake damunki haka ne, na lura tun jiya kin zama wata iri"
Amal ta ajiye spoon ɗin hannun ta a ranta tace "Mhmm Yaya Ramla ina cikin damuwa tabbas, kuma na shiga damuwa ne domin ƙoƙarin samo mafita akan gagarumin lamarin dake barazanar jefani wani bigire da be kamata ba, Amma nasan bazaki taɓa bani goyon baya ba" Amma a zahiri tace
"karki damu bana jin daÉ—i ne kawai"
"Amma yakamata kije kiga likita"
Amal tace "ba abun damuwa bane, zan ware Insha Allah"
Tun Yusuf yana fama da tunani tareda sauraren kira daga uwaÉ—akkinsa har ya fidda rai, ya fara mantawa ya shiga sabgogin sa.
Kusan sati uku kenan da zuwan Yusuf gidan daga nan Amal bata ƙara saka shi a idon ta ba, wasa wasa abu ya ci gaba da damun zuciyar ta, gashi abu na ta faman damun zuciyar ta.
Alhaji Nasir Daula ne zaune a wani ƙaton falo shida wani mutum wanda zeyi sa' ansa, sukw hira tareda ƙyaƙyata dariya kai da gani kasan akwai kyakkyawan kusanci da fahimtar juna a tsakanin su.
"Alhaji Nasir nikam daughter tunda ta dawo ƙasar nan bata zo mun gaisa ba, kota manta dani ne?"
Alhaji Nasir yace "haba Bulama yaza'ayi daughter ta manta da kai, kawai dai kasan halin ta ne Nason kaÉ—aici har yanzu a haka take, Amma insha Allah zan turo maka ita har gida ku gaisa"
Alhaji Bulama yace "kana nufin har yanzu bata dena wannan É—abi'ar ba, ba ta warke ba kenan?"
"kai dai bari kawai, lamarin daughter yana damuna, ace kaf rayuwar ɗan adam be yadda da kowa ba, ba za ta sake da kowa ba, to koni wataran ina ƙasar nan idan bata ga dama ba se tace bata son inje inda take, narasa menene mafita "
Jinjina kai Alhaji bulama yayi yace" "wai shekarun ta nawa ne yanzun?"
"18 to 19, amma menene ma fitar?"
Alhaji Bulama yace "mafita É—aya ce shine kayi mata Aure, idan har aka yi mata Aure zata dena wannan halin nata"
Alhaji Nasir yace "Aure kuma? Dudu du guda nawa daughter take? Yarinya ce ƙarama kuma waze iya jure halayen ta?"
Alhaji Bulama yayi murmushi yace "kai kake ganin yarintarta idan ka aurar da ita daram zata zauna, samun wanda ze zauna da ita da halin ta abune me sauƙi, semu haɗa ta Aure da Fahad yaron guri na da yake karatu a china, dama bata sanshi ba kaga se a haɗa su, hakan ze ƙara zumunci dake tsakanin mu, kuma kaga tunda ita kaɗai Allah ya baka seka samu 'yan jikoki"
"Masha Allah gaskiya naji daÉ—in wannan shawarar taka, amma kasan semun bi a sannu idan nace zan tursa sata, za' a iya samun matsala"
"bakomai mu bi komai a sannu insha Allah babu wata matsala"
Suka cigaba da hirarrakin su.
Misalin ƙarfe goma na dare Yusuf yayi shirin sa tsaf ze kwan ta, wayar sa ta fara ringing, Sunan Abbas ne akan screen ɗin wayar, ya ɗaga suka gaisa
Abbas yace "Yusuf ɗazu Isa megadi ya kirani, yace min yarinyar nan ta bada saƙo tace zaka kaita unguwa gobe misalin ƙarfe goma na safe, ta jadadda goma na safen nan dan haka ka kiyaye"
"Shikenan zan je Insha Allah"
Tunda Yusuf ya kwanta ya gagara cikakken bacci, da yaje sallar Asuba sam be koma bacci ba, ya zauna ya ci gaba da lazumi, da sassafe ya tashi yayi wa mahaifiyarsa aikace2, kaman yadda 'ya mace za tayi haka Yusuf ya share ko' ina yai wanke2 yai girkin karin kumallo.
Koda Ummansa ta tashi tayi mamakin inda Yusuf yake gaggawar zuwa, bata son yawan takura masa dan haka ta ƙyaleshi.
Ƙarfe tara dai2 na safe Yusuf ya isa gidan Alhaji Nasir.
Isa na ganin sa yace "kai sannu da ƙoƙari Allah yasa ka ɗore, idan ka ɗore da zuwa akan lokaci saura kuma ƙalubale na gaba"
Yusuf yayi murmushi yace "Malam Isa kenan, Kowace sana'a tana da ƙalubale, sedai fatan Allah ya bamu ikon aikata dai2"
Da yake Isa akwai surutu kaman an ƙona shi aka, haka ya dinga zubawa Yusuf surutu kuma surutun nasa ba'aakan kowa bane se kan 'yar masu gida
Yusuf yace "wai ya sunan ta ne?, nifa har yanzu ko sunan ta ban sani ba"
Isa yace "Ai abune me wuya kaji sun kira sunan ta, ban san sunan ta na gaskiya ba, amma sunan ma dai da' ake kiran ta dashi akwai wuya dan ban riƙe ba"
Yusuf yace "ikon Allah wahalar sunan ta kai ka kasa riƙewa"
"haba Malam Yusuf kaman baka san iyayinku na 'yan binni ba? Wasu sunayen ma karasa sunan tumakine kona taurari"
Ba ƙaramin dariya Isa ya bawa Yusuf ba.
Suna ta ɗan taɓa taɗi, Isa yace "Aff gata can ta fito"
Yusuf ya ɗaga kai ya hango ta, ba ƙaramin kwarjini take da shi ba, taku take na ƙasaita akan wani dogon takalmi, dogon wando ne a jikin ta dark blue da riga light blue me dogon hannu, ta ɗaure kanta da ɗan kwali, amma gashin ta seda ya fito ta baya, fuskarta sanye da wani ƙaton glashi, wayar tace kawai a hannun ta babu jaka se key ɗin mota.
Guri ta samu ta tsaya, yayin da Yusuf yai sauri ya ƙarasa inda take tsaye, gaban sa na ta dukan uku2, yaje gabanta ya ɗan risina yace "barka da safiya ranki ya daɗe"
Bata amsa ba, ta miƙa masa mukullin mota, yasa hannu biyu ya karɓa a hankali ta furta masa Lambar motar da zata hau, kowace mota dake parking space tana da lamba, dan haka be sha wuya gurin gano wadda take nufi ba, abun da ya ɗaure masa kai shine kaddai a haka da wannan shigar zata fita?.
Ya fito da motar, ya fito ya buɗe mata ƙofar Bayan motar, wuce shi tayi taje ta buɗe gaba ta shige ta zauna.
Ya zagayo ya buɗe shima ya zauna yana ta Addu'a, gashi besan inda za suje ba, haka yai shahada ya kunna motar Isa ya buɗe musu gate, taiwa Isa Alama da hannun ta yazo, a guje jiki na rawa Isa ya ƙaraso gefen window ɗin da take zaune ya risina
"kwatanta masa gidan Bulama" ta furta kaman wadda aka yi wa dole, Isa yace
"kina nufin Alhaji Bulama Abokin Alhaji?"
ÆŠauke kai tayi tana kallon wani gurin daban, se Yanzu Isa ya tuna bata maimaita magana, ya gyara tsayuwa yayi wa Yusuf kwatancen gidan.
A hankali Yusuf yaja motar suka bar gidan, tunda suka fara tafiya babu wanda yayi wa wani magana, Yusuf ya dinga bin kwatancen gidan da Isa yayi masa, har zuwa ƙofar wani katafaren gida da suka zo ƙofar gate ɗin Yusuf ya kalle ta yace
"Nan ne ranki ya daÉ—e?"
Shiru tai masa ko motsawa ba tayi ba balle ta kalle shi, ɗan taɓe baki yayi, yai horn megadi ya buɗe ƙofa ya leƙo yana ganin motar ya ja da baya da sauri, ya koma ya buɗe gate ɗin gidan, gidan yayi kyau ya tsaru matuƙa sedai be kai gidan Alhaji Nasir ba.
Yusuf yaje parking space yayi parking, kafin ya sakko ya buÉ—e mata ta buÉ—e motar ta fita.
Fitowa yayi shima ko da wani abu dazata buƙata ya fito ya tsaya a bayan ta, me gadi ya ƙaraso cikin girmamawa yana gaishe ta, bata amsa ba tace "Bulama yana nan ne?"
"Eh ranki ya daÉ—e, Amma bana jin ya tashi"
"Ace masa gani na zo, ya tashi ko be tashi ba be dameni ba, bazan haura mintuna talatin a gidan nan ba"
Da sauri megadin yace "Angama ranki ya daÉ—e" nufi cikin gidan.
Ba tare da ta kalli inda Yusuf yake ba tace "biyo ni" ba musu yabi bayan ta, Wata rumfa dake harabar gidan me É—auke da fararen kujeru ta nufa taje ta zauna akan kujera, bayan ta yusuf ya tsaya ba tare da ya zauna ba.
Me gadi ne ya fito tare da wani matashi, matashin na ganin ta ya fara murmushi ya ƙara so inda take zaune
Matashin yace "Manya maganin ƙanana, Dama yaran talaka irin mu na ganin ku?"
Ɗan taɓe baki tayi tace "Gurin Alhaji Bulama nazo, yace yana son gani na, a ce masa gani nazo"
Matashin yayi murmushi yace "Yau kuma a Alhaji Bulama yake ba Daddyn ba, WIDAD kenan, to ki shiga ciki mana ku gaisa da su Hajiya da Iman mana"
Yusuf a ransa ya maimaita "Ikon Allah wani irin suna ne wannan? Widad?
Widad tace "banzo da niyyar ganin su ba a yanzu"
"Shikenan bari ayiwa Daddy magana"
Har ze wuce ya kalli Yusuf yace "am Sorry young man bamu gaisa ba"
Ya miƙawa Yusuf hannu, Yusuf yayi murmushi ya miƙo masa hannu da nufin suyi musabiha, Amma Widad ta kalli Yusuf ta haɗe rai tace
"don't try it"
A hankali Yusuf ya janye hannun sa suka fasa gaisawar, saurayin ya girgiza kai yace "Hmm bari in kira Daddy"
Yusuf a ransa yace "wai ita wannan shikenan kowa se dai yabi abunda take so? Kowa ma wulaƙanci take masa?"
Sunan a harabar gurin, aka turo 'yar aiki da kayan drinks da fruit ta kawo musu, yadda aka ajiye kayan ko kallon su ba tayi ba.
Ba tare da ta kalli inda Yusuf yake ba tace "duk wanda yazo gurin nan ban yadda ka kula shi ba, ba ruwan ka da kowa"
Yusuf yace "angama ranki ya daÉ—e"
Wani babban mutum ne ya fito sanye da jallabiya fara ƙal, aƙalla zeyi sa' an mahaifin widad.
Ya ƙaraso gurin fuskarsa ɗauke da murmushi, yaja kujera ya zauna ya kalli widad yace
"daughter yau kuma cikin gidan nawa ne baza'a shiga ba?"
"Eh bazan shiga ba banyi niyya ba, yanzu ma Daddy ne yace kana nemana nazo" ta bashi amsa kai tsaye
Alhaji Bulama yace "yanzu daughter ace kina Nigeria amma ki kasa zuwa ki ganni mu gaisa, ko na miki laifi ne?"
ÆŠan girgiza kai tayi tace "nafison zamana ni kaÉ—ai ne"
Alhaji Bulama ya kalli Yusuf yace "daughter shi kuma wannan fa?"
"driver nane, ba ruwan ka da shi"
"Shikenan naji ba ruwana da shi, amma idan bodyguards kike buƙata ai za'a iya samo miki, wannan ba abunda ze iyayi miki"
Ba kunya Widad Ta kalli tsabar idon mutumin nan a gadaran ce tace "bana buƙata, bana son kowa ya raɓeni"
Alhaji Bulama yace "A'a daughter sama miki masu tsaron ki yana da mahimmanci, musamman tunda kin san amfanin hakan a tare da ke"
"Bana buƙatar kowa a tare da ni, bana buƙatar saka rayuwar kowa a hatsari, ban yadda da kowa ba dan haka bana buƙatar su"
Alhaji Bulama ya jinjina kai yace
"Amma daughter kin san likita ya hana ki wannan ɗabi'ar kaɗaice kan naki, rayuwa ba zata taɓa yuwuwa a ce kina gudun mutane ba, ya kamata ki samu kiyi aure zaki samu nutsuwa, da kuma farinciki zaki rage kaɗaicin nan"
Karon farko da Yusuf yaga dariya a fuskar ta, ba ƙaramin kyau tayi ba da tayi Dariya ta wani jinjina kai cike da rainin hankali tace
"Alhaji Bulama kenan, an gaya maka rayuwar kaÉ—aicin da nakeyi tana damuna ne? Karnuka na da maguna suna É—ebe min kewa sosai fiye da yadda mutane zasu yi min, tunda nasan sun baza su cutar dani ba"
Ta miƙe tsaye tsam ta kalli Alhaji Bulama ta haɗe rai kaman ba ita ta gama dariya ba tace
"Ka cire wa zuciyar ka cewar ni widad zanyi Aure, ban yadda in zauna a ƙarƙashin wani ba yana juyani yadda yake so ba, in anyi Aure ana neman Aljanna ne, ni kuma idan nayi Aure sedai Rahamar Allah ta shigar dani Aljannah, ba dan zanyi wa wanda nake tare da shi biyayya ba, na faɗa bazan zauna ƙarƙashin wani ba, babu wani farinciki da'ake a tsinta a Aure, babu komai cikin rayuwar aure se takura da matsaloli, NO MARRIAGE IN MY POLICY!!! Rayuwa ta da nake nika ɗai ta fiye min bazan gayyato wa kaina matsala ba bayan wadda nake ciki"
Ba Alhaji Bulama ba hatta Yusuf maganganun Widad sun É—aure masa kai, ita kam wannan wace irin zuciya ce da ita haka?
Inda motar su take ta nufa, hakan yasa Yusuf bin ta da sauri ya riga ta ƙara sawa inda motar take ya buɗe mata.
Suna tafe yana lura da ita, ranta a ɓace yake sosai, haka yayi tuƙi a hankali koda suka je gida part ɗin ta ta nufa ba tare da ta kula kowa ba.
Yusuf kam rasa abunyi yayi, ita ba tace ta sallame shi ba ko A'a, ga mukullin mota bata karɓa ba.
Bayan ya kulle motar Isa ya nufoshi yana murmushi yana zuwa yace
"har kun dawo kenan?"
"Eh min dawo malam Isa"
"to yaya, fatan dai bata maka halin ba?"
Yusuf yayi murmushi yace "niba abunda tayi min, ni yanzu damuwa ta ban sani ba ko ta sallameni ba tace min komai ba, ina son tafiya gida ne"
Isa yace "kaje ina? ai zama zakayi setace ta sallame ka"
Harar Isa Yusuf yayi yace
"shikenan ni bani da Abunyi na kaita inda zan kaita meya rage banda in tafi tawa sabgar, mahaifiya ta Nason ganina dan haka bazan zauna ba"
Yana gama maganar ya nufi ƙofar shiga cikin gidan, yana jin Isa yana kiransa amma yai masa banza.
Yana shiga yayi karo da Amal ta taho da sauri zata fkta.
Tana ganin sa ta tsaya tana ajiyar zuciya, taji wani farinciki na ratsa zuciyar ta Yusuf yace "barka da rana"
"Yawwa barka ya kake ya aikin?"
"Alhamdilillah, ga key ɗin mota nan bata karɓa ba ta tafi, ina son zan tafi gida ne inga mahaifiya ta"
Ya miƙawa Amal, be jira me zata ce ba yai waje abun sa.
Jinjina kai Amal tayi tace "lallai wannan besan wacece Widad ba, da alama shima kansa yana É—an rawa"
Babban abunda ya bata haushi irin yadda be tsaya ko gaisawar kirki sunyi ba.
Koda Yusuf ya koma gida ya sha tambayoyi a gurin Ummansa, seda ya tabattar mata da babu wata matsala sannan hankalin ta ya kwanta.
Tunda ya shiga ɗakinsa yake saƙawa yana warwarewa, abubuwa da yawa sun bashi mamaki yana da tarin tambayoyin da besan me bashi amsar su ba, Amma kusan akwai alamar tambaya akan dukkanin iyalan gidan akwai wani ɓoyayyen abu da kowa yake ɓoyewa a ransa.
"Amma me yasa Widad ta zaɓi rayuwar kaɗaici akan rayuwa da mutane? Me yasa tayi wa Aure mummunar fahimta haka? Me yasa kowa yake biyayya ga Umarnin ta abunda take so, ko da kuwa hakan na nufin ɓacin ran mutane ne?"
Bashi da Amsar tambayoyin nan, Shi ze nemowa kansa amsoshin tambayoyin.
Widad tana kan gadon ta ta ƙurawa sama ido, Hawaye na bin gefen idon ta, Mahaifin ta yayi Sallama a ɗakinta, tana jinsa amma tayi masa shiru, ta miƙe zaune a hankali, ya ƙaraso gefen gadon ta ya zauna ya kalli idon ta yace
"daughter ya akayi ne? Meke faruwa? Abbanki ya gayamin ko gidansa baki shiga ba iyakarki harabar gidan, daughter me yasa?"
"Bana son hayaniya ne, shiyasa na tsaya kawai a harabar gidan" ta bashi Amsa
Alhaji Nasir yayi ajiyar zuciya yace
"Alhaji Bulama ya gayamin yadda kuka yi, Lovely bamu yanke shawarar batun yi miki aure ba sedan na gaji da ganin halin dake ciki, Widad zuciya ta na shiga ƙunci da irin wannan rayuwar da kike yi, kin san larura dake damunki, likita ya hana ki kaɗaicewa, idan kika cigaba a haka fa ze cigaba da taɓa ƙwaƙwalwar ki, dan Allah daughter ki amince da roƙona, kiyi Aure ina son ganin farincikin ki, ko baki yadda da kowa ba, idan dai zaki buɗe ido kiga 'ya' yanki da mijinki zakiji daɗi sosai, dan Allah Widad bani da kowa yanzu seke, se kuma Aminina Bukar Bulama, naso Inkuma samun yara bayan ke, Allah be bani ba, zanji daɗi idan naga 'ya' yanki, please Widad help your Dad, nasan bana tunanin akwai wanda kika tsayar kike so, Amma nida Bulama mun yanke shawarar zaɓa miki mijin da zakiyi Alfahari da shi, wanda ze nuna miki so ya kula dake ko bayan raina, Widad a yau idan na faɗi na mutu bayan Alhaji Bulama bana tunanin Akwai wanda ze kulamin da Rayuwar ki, sannan kinsan a haɗarin da muke daga ni har ke, please Widad ki Amincewa batun Auren nan, am sure if you got true love you will never regret been married, Akwai Soyayya da tausayi a cikin rayuwa da wanda yake son ka, na tabattar da Aure ze wanke miki dukkanin wani pain da yake ranki"
Tunda ta ƙura masa ido ko ƙyaftawa ba tayi, seda ta bari ya gama, ta miƙe tsaye ta fice ta bar masa ɗakin ba tare da tace komai ba.
Alhaji Nasir ya jinjina kai, babu alamar Nasara, Amma ya yanke wa zuciyar sa ze cigaba da lallaɓata yana bin kanta, dan babu wata mafita da ta rage masa se Amincewa da shawarar Alhaji Bulama.
A fili yace "Wannan karon ke zakiyi biyayya ga unarnina daughter, duk wannan abun inayi ne saboda ke"
Widad kam gaba ɗaya maganganun mahaifinta haushi suka bata, kaman korarriya haka ta sakko daga kan bene, ta samu corridor ta tsaya tana zancen zuci, "wai Aure, waya gaya musu akwai Aure a tsarin Rayuwar ta? Taɓɗijan inyi Aure in zauna a ƙarƙashin wani yana juya ni yadda yake so? Ko kuma a haɗa kai da shi a cutar dani, kaman yanda yake ɗabi'ar mutane ne cin amanar wanda ya yadda da su, idan har Akwai mutane masu amana da suka rage a doron ƙasa to sunyi nisa da duniyar da ni Widad nake ciki, waima waye ake cewa za'a haɗa da shi ne Aure? Idan kuma ya zamana yana ɗaya daga cikin mutanen da nake nema fa, hakan yana nufin in masa Alfarma ko in ɗaga masa ƙafa?
A fili tace
"Baze yuwu ba wallahi, ba wani Aure da zanyi, what is their in marriage apart from pains!, hurting each other!, tensions!, regrets and restriction of rights,!! No Impossible i want free life, i can't live under someone's control, i better live alone and die alone than to got married to irresponsible man of now a day's, bazanyi Aure ba, idan har Soyayya da shaƙuwa basa hana ɗan Adam ya cutar da ɗan uwan sa, to tabbas Love doesn't exist is just an imagination, love does not exist talk less of true love, So shike sa ayi Aure, kuma yadda ce ke kawo so ban yadda da kowa ba, Daddy Bulama kayi min katsalandan bisa ga kawo wannan shawarar da ɗaya take da ƙarasa gurgunta rayuwa ta" hawaye ne ya wanke mata fuska sharkaf se ajiyar zuciya take yayin da take maganar.
Ramla da tazo wucewa ta tsaya taji surutan da Widad take yi, ta jinjina kai a ranta tace "to Aure kuma? Waye ze auri wannan Jarababbiyar? Kuma mahaukaciya? Anya Mummy ta san zancen nan kuwa?
Widad kam ji tayi zuciyar ta tana wani irin raÉ—aÉ—i, ta fito harabar gidan da sauri kanta ko É—an kwali babu, dan gaba É—aya ji tayi kaman tana cikin wuta dole ta fita dan ta samu sassauci,
Tana fitowa harabar gidan ta nufi inda Isa yake tace
"ina direban nan yake, yazo ya fita dani ya bar arear nan dani"
Isa ya kalleta ya kalli kayan jikin ta, mini skirt ne a jikin ta se wata riga armless, gashin kanta a baje kaman ta zare, Isa ya ɗan ƙare mata kallo, a ransa yace "Masha Allah, Allah ya yi halitta anan" yace
"Ranki ya daÉ—e a hakan za'a fita dake?"
Kallon da yake mata ne da tambayar da ya tsareta da shi, yasa ta ƙara fusata ba zato ba tsammani Isa yaji saukar lafiyayyen mari a fuskar sa.
Gigicewa yayi ya dafe kuncin sa yace "ranki ya daÉ—e ya tafi tun É—azu, nace ya tsaya amma yace baze tsaya ba yana da uzuri"
Ƙanƙance ido tayi ta dubi Isa, a hankali tayi ƙasa sa muryar ta tace
"ɗan uban waye shi da ze saka hannu akan dukkan sharuɗai na, kuma yau da ya fara min aiki har ya fara saɓamin doka?"
Shiru Isa yayi yana sake shafa kumatunsa dan bashi da amsar da ze bata
"Wallahi sena masa wulaƙancin da babu wata halitta data taɓa yi masa, sena sauke dukkan baƙin cikin da nake ciki akansa, waye ubansa? Yana ƙasƙantacce zeyi watsi da dokokin da shi yasa hannu da kansa, Matsiyatan banza marasa Alƙawari, shiyasa wani talakan har ya mutu baze Arziki ba saboda rashin sanin mahimmancin Alƙawari da Amana, ya shirya karɓar hukuncin da ba'a taɓa masa makamancin sa ba"
(Nikam nace masu kuɗi ne kawai suka san Alƙawari da Amana? Ko kuwa Alƙawari da Amana ce tasa suka yi Arziki? Shikenan idan mutum yana aiki a ƙarƙashin wani me kuɗi se ya zama kaman Bawa? Shi besan jin daɗi ba se Bauta? Bashi da wani 'yanci na walwala da jin daɗi kenan? Tabbas da ba talaka ƙaryar me kuɗi yaji daɗin Rayuwar sa komai Arziƙin sa kuwa, Naga kowane ɗan Adam dai ajizine babu wanda baya kuskure, ke Widad ba kya kuskure ne ko kuwa? A ce mutum ya zabi Rayuwa shi kaɗai ƙwal ba mutane? Kowa be iya komai ba ciki hada mahaifinki, Gaskiya kin zafafa Aƙidojin ki, wata sabuwa kuma Widad tace "Love doesn't exist, is just an imagination talk less of getting true love" masu karatu wannan kaɗanne daga Aƙidojin Widad
TIRƘASHI!!!
Yaseen Akwai cakwakiya, Hassada, Munafunci, tsantsar Soyayya, Fuska biyu, kutsen ƙaddara me sauya rayuwar bawa ko be shirya mata ba, da sarƙaƙiyar gaske a cikin wannan littafin kar ku bari a baku labari dan ya haɗu.
Insha Allah ze cigaba da zuwar muku 1 ga watan September
Domin sharhi, gyara, ƙorafi ko makamancin haka ku tuntuɓeni akan
Wannan lambar ta what's app kawai
07063065680
Masu bina private akan in tura musu ABDUL JALAL dan Allah kumin afuwa, Abubuwa sunmin Yawa na kammala part two a document na sake shima, idan baku samu ba ku duba manhajar watpad a account É—ina
Ayshercool7724 insha Allah zaku samu dama sauran litattaafai na.
Masoya a cigaba da haƙuri dani, sakamakon harkar makaranta da wasu abubuwan da suka sani gaba Insha Allah wannan littafi ze fara zuwar muku 1 ga watan September, a what's App, da telegram groups ɗina, da kuma Facebook a shafin mu na perfect writers Association, ko kuma YouTube channel dinmu
Ina godiya da Adduoin ku.
_*AƘIDA TA*_
*PERFECT WRITERS' ASSOCIATION*🌞
( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS 💪)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P.W.Aâœï¸
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now *AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Special thanks to all members of my Association
Perfect writers Association may Allah subhanahu wata'ala bless our pens and grant us wisdom to write what will bring positive changes to our Community.
I won't forget you my fans ðŸ˜ðŸ˜ðŸ˜ you are always in my heart, my love to you is endless, especially those that shows me love support and follow me with prayers since my first Novel to date, i can't mentioned you all but am proud of you all ðŸ˜
HAUSAWA SUKACE KYAN ALƘAWARI CIKAWA, KAMAR YADDA YAKE KOYAR WAR ADDININ MU CIKA ALƘAWARI ABU NE ME MATUƘAR MAHIMMANCI, NAZO DOMIN CIKA MUKU ALƘAWARI, A BAYA NASAKA RAN KAMMALAWA DA MAKARANTA A AUGUST, KATSAM AKA ƊAGA JARRABAWA AKA MAIDA ITA 20 GA WATAN SATUMBA, AMMA TUNDA NI NAYI MUKU ALƘAWARIN CIGABA DA KAWO MUKU WANNAN LITTAFI A WANNAN WATA, NA SHIRYA TSAF DAN CIKA ALƘAWARIN KU 'YAN AMANA, WATTANI HUƊU KUNA SAURARE NA, INSHA ALLAH BAZAN BAKU KUNYA BA, KU SHIRYA DOMIN SALON NA DABAN NE, AKWAI TUFKA DA WARWARARA ME MATUƘAR SARƘAƘIYA A WANNAN LITTAFI DA KUKA DAƊE KUNA JIRA.
KARA ÆŠAYA ZAKUYI MIN, SHINE NUNAMIN JIN DAÆŠIN KU TA HANYAR YIMIN COMMENT TARE DA SHARE, LITTAFIN NAN KYAUTA NE DOMIN JIN DAÆŠIN KU MASOYA NA, AMMA A DALILIN RASHIN COMMENT ÆŠINKU KOMAI NA IYA CANZAWA, GA MASU MANHAJAR WATPAD KU GARZAYA KU NEMENI
@AYSHERCOOL7724
KU NEMI LITTAFIN A FACEBOOK A
GROUP ÆŠIN PERFECT WRITERS ASSOCIATION
ƘOFA TA A BUƊE TAKE DOMIN GYARA SHARHI KOKUMA SHAWARA
AYSHERCOOL
07063065680
YADDA NA FARA LAFIYA ALLAH YASA IN KAMMALA LAFIYA
Haƙƙin Mallaka ⚠: Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
BISMILLAHIRAHMANIRRAHIM
ELEGANT ONLINE WRITER'S
             *PART1*
           Â
                 _Page 4_
Babu alamar sassauci fuskar Widad, yanayin fuskarta ze tabattar maka da gaske har cikin zuciyar ta zata aikata abunda ta faÉ—a, ta juya ta koma cikin gidan da hanzari.
Jinjina kai Isa ya dinga yi yana kuma sake shafa kumatunsa yadda yske masa raɗaɗi, tare da tausayawa wulaƙancin da Yusuf ze fuskanta.
Ramla kam cikin sassarfa ta nufi É—akin mahaifiyar ta, tun daga waje take kiran "Mummy"
Hajiya Halima tace "Ramla wannan wane irin kira ne haka? Ke kam bakya girma"
Ramla ta ƙarasa kusa da mahaifiyar ta ta zauna tace "wai nikam nace me akayiwa 'yar gwal ne? Naga kaman ciwon nata na ƙoƙarin tashi fa? Kuma ga dukkanin alamu yau ta kwaɓe mata itada uban tane"
ÆŠan tsaki Mummy tayi tace
"sakani yake cikin sha' aninsa shida 'yar sa ne? Ai sedai inga suna lamauran su ta yaya zan san meya sameta?"
Ramla ta sake gyara zama "hmm kinsan dai halin ciwon ta, a corridor ɗin ƙasa na haɗu da ita, tana ta surutai, wai Daddy Aure zeyi mata, se safa da marwa take tana zufa"
Zaro ido Mummy tayi tace "Aure kuma? Wane irin Aure ana zaman lafiya? Waye ze Auri mahaukaciya mara tarbiyya kamar wannan Yarinyar? Shi mijin da haukan zeji ko kuma da rashin tarbiyya?"
Ramla tace "waya sani musu?, sedai ki jiyo mana kanun Labaran muma ki fesa mana, Amma ina tunanin wanda ze kwashi wannan Mahaukaciyar"
"To nidai a iya sanina bata yadda da mutane ma, to ta yaya ta samo wanda ze Aure ta?"
Ramlah tace "Ai samun miji ba wuya ze mata ba, ko dan wannan haÉ—aÉ—iyar Daular, dan haka ko'a turu take dan hauka, za'a iya samun me sonta yace ze aureta a haka"
Mummy tace "hakane, Amma ya zama dole musan waye ze Aureta, dole in gano"
Haka Suka ci gaba da tattauna wa akan lamarin.
Yusuf kam kashe wayoyin sa yayi ya shiga sabgoginsa, duk yadda Isa yaso kiran Yusuf a waya ya gaya masa Saƙon Widad abu ya gagara wayar sa taƙi shiga, ƙarshe se haƙura Isa yayi.
Widad kam baranda ta samu ta kwanta, akan tiles ga sanyin tiles na ratsa ta amma sam bata ji, tayi ruf da ciki tana jin yadda zuciyar ta take mata raɗaɗi, kamar ta tsaga ƙirjinta ta fito, Babban Abunda ya ƙara bata mamaki shine yadda mahaifin nata be biyo sahunta ba balle ya rarrashe ta kaman yadda yake yi abaya, shima kamar yayi fushi da ita karon farko ya barta cikin damuwa, lallai wannan karon mahaifin nata dagaske yake.
Washegari Yusuf ba shida Niyyar zuwa gidan su Widad Sam, da ya tashi da safe ma shirin tafiya Office yayi abun sa, ya shirya ya fito Umman sa ta kalle shi tace
"Ya haka kuma? Yau ina zakane?"
Murmushi yayi yace "Yau Office zanje Umma"
"Kacemin kuma, an turaka aiki gidan Alhaji Nasir Daula, yanzu kuma kace min zaka gurin aiki ya haka?"
Yusuf yace "hakane Umma, an turani aiki gidan Alhaji Nasir Daula, Amma dole zan dinga leƙawa Office, ina documenting findings ɗina sannan indinga presenting sakamakon bincike na"
"shikenan a sauka lafiya, Allah ya tsare ya kiyaye hanya"
"Allah yasa Umma, dan Allah yau ki mana dambu kinji Umma na"
Umma tace "banyi Alƙawari ba, ka bari ranar da kake nan se kayi"
Noƙe kafaɗa Yusuf yayi yace "dan Allah Umma, ni gaskiya idan ba dambu kika yi yau ba bana cin Abincin"
"kar kaci É—in, ai cikin ka ba nawa ba"
Haka yaita zolayar umman nasa sannan yai mata sallama ya tafi.
Da yaje Office ɗin ma Ayyuka sun ɗanyi masa Yawa, ya duƙufa sosai yana ta shigar da ayyukan sa cikin system.
Sallamar da'akayi a office É—in ne ya sashi É—agowa yaga me Sallamar, kamar yadda ya zata sakine ce ta shigo.
Kallo É—aya yayi mata, ya Amsa sallamar ya maida kansa ya cigaba da danna system É—in shi.
Yauma cikin baƙaƙen suit Sakina take, amma skirt ga ƙaramin hijjabi da ta saka, gaba ɗaya kayan sun bayyanar da surar jikin ta.
Kujera ta ja ta zauna tana facing É—in sa.
"Yusuf sannu da Aiki"
Ba tare da ya kalle ta ba yace "lafiya kalau Alhamdilillah"
"kwana biyu baka shigowa Aiki, lafiya dai ko?"
ÆŠan É—agowa yayi yace "Eh an bani wani Assignment ne"
Cikin iyayi da lumshe ido tace "to Allah yaba da sa'a"
Ya amsa da "Ameen"
"Can i offer you something to eat?"
Ba tare da yace komai ba ya girgiza mata kai, Alamar A'a.
Miƙewa tayi ta zagayo inda yake tace
"ko Akwai abunda zan taya ka ne?"
ÆŠagowa yayi ya kalleta a hankali yace "dan Allah ki fitar min daga Office inada Ayyuka da yawa kina takuramin fa"
A Shagwaɓe tace "Yusuf meyasa kake son yi mun wulaƙanci ne?"
"ba wulaƙanci bane, gaskiya ce, Aikine ya kawo ni gurin nan ki barni inyi aikina mana"
"Amma Yusuf meyasa zaka maida Soyayya ƙiyayya, tunda na nuna ina sonka kake wulaƙantani haba Yusuf"
"Sakina niba wulaƙantaki nake ba, yanzu lokacin aiki nane, dan Allah ki tashi ki tafi, bearable in shiga lokacin aiki ba"
"Yusuf" ta kira sunansa, É—aga mata Hannu yayi ya dakatar da ita tare da faÉ—in
"Sakina dan Allah ki barmin office, kalli shigar jikin ki, kuma kinzo kin sani gaba, dan Allah ki tafi"
Suna cikin Jayayyar ne Abbas ya shigo, Sakina ta miƙe ta bar office ɗin a fusace.
Abbas ya kalli Yusuf yace
"Anya Sakina bata fara kama zuciyar ka ba Yusuf?"
ÆŠan girgiza kai Yusuf yayi yace
"Abbas kenan anyi na farko, baza'ayi na biyu dani ba, bana son yi mata wulaƙanci ne amma taƙi ganewa, Soyayya kam sedai inga anayi, bazan sake ba, in Allah yayi zanyi Aure shikenan, Amma na gama Soyayya"
Abbas ya jinjina kai yace "shikenan Allah ya kyauta, na kiraka tun jiya bata shiga ya labarin mutuniyar ne?"
Shafa Aljihun sa Yusuf yayi, sannan ya jingina da jikin kujera yace
"Aini tun jiya dana dawo na kashe waya ta, bana son a dameni ne sam"
Abbas yace "kayi mata aikine jiya?"
"Eh munfi ta, na kaita wani gida, inaga gidan É—an uwan mahaifinta ne ko makamancin haka"
Abbas yace "babu dai wata matsala ko?"
"Babu wata matsala, ba tayi min dai wulaƙanci ba, Amma fa naga izza wadda ban taɓa ganin makamanciyarta ba, dan cikin isa da gadara take wa kowa magana, bata shakkar kowa bata girmama kowa, kai ko Dariya banga tayi ba Jiyan nan, magana ma aiki ce a gurin ta"
Abbas yace "taɓ, aishi yasa nace bazan iya ba, saboda na samu labarin yarinyar, shikenan ka dai kula sosai akan abunda muke son ganowa"
Jinjina kai Yusuf yayi, tare da cewa "Insha Allah, komai ze tafi dai dai"
***********
Ƙarfe goma na safe Yusuf ya bar gurin aikin, ya koma gida seda yayi wa Umman sa cefane, ya kai mata markaɗe ya kama mata Ayyukan gida sannan ya sauya kaya, ya nufi gidan Alhaji Nasir.
Yau da yaje ya tarar da Isa mai gadi dashi da wani, Suka gaisa, Isa yayi farat yace
"Yusuf ga Nura shine direban megidan nan, lokacin da kazo yaje garin su ne, amma gashi ya dawo, shike kai Alhaji unguwa"
Yusuf ya miƙa wa Nura hannu suka gaisa.
Isa ya nisa yace "Yusuf kayi gangancin tafiya jiya, nan ta fito a birkice jiya kaman mara hankali tazo nan tana neman ka wai ka fita da ita, baka ga shigar jikin ta ba, daga tambayar ta a haka zaka fita da ita ta mareni, wallahi har yanzu ko ƙuda bana so ya taɓa fuskata dan ba ƙaramin shiga marin nan yayi min ba"
Zaro ido Yusuf yayi yace "mari kuma?"
"Wallahi Yusuf mari na tayi"
Nura yace "aiba abun mamaki bane, dama wani lokacin haka take birkice wa, kun san abunka dame rangwamen Ƙwaƙwalwa, aini tunda naji zata dawo naji aikin gidan nan ya fita daga kaina, Allah ya temakeni aka samo mata nata direban"
Kallon su Yusuf yake dan be fuskanci inda zancen nasu ya dosa ba.
Isa yayi ƙasa da muryar sa yacewa Yusuf
"wani lokacin birkicewa take kaman hauka hauka, shiyasa kaga bata son mutane suje inda take, tana da larurar ƙwaƙwalwa shiyasa....
Yusuf ya katse shi ta hanyar cewa
"Shikenan shikenan, Allah ya bata lafiya be kamata a dinga yayatawa ba, Addu'a ya dace ayi mata, faÉ—ar bashi da Amfani sam"
Widad ce ta fito ƙaton falon gidan, ta tarar da matar gidan da yaran ta Suna ta ciye ciye suna hira, tana fitowa suka yi tsit suka shiga taitayin su, suka dena hirar.
Ta dube su É—aya bayan É—aya, kamar me nazari, sannan ta yatsuna fuska tace
"Amal jeki kira min wancan matsiyacin talakan direban, yau in fara gwada masa wacece ni"
Sam Amal ba taji daɗin kalaman da Widad tayi amfani da su akan Yusuf ba, Amma babu yadda ta iya ta miƙe ta tafi kiran sa.
Tunda Amal ta fito ta hangi Yusuf yana hira da su Nura, yayi kyau sosai komai nasa gwanin sha'awa, kamar ba direba ba.
Amal Ta ƙaraso inda suke bata kula su Isa dake ƙoƙarin gaishe ta ba, ta dubi Yusuf tace
"barka da rana Yusuf"
Fuskarsa ba yabo ba fallasa yace
"Yawwa barka, ina uwa É—akina?"
Bata jin daɗin yadda koda yaushe yake taƙaita magana da ita, Amma ta basar tace
"itace tace in kira ka ma"
Yusuf ya miƙe yace "shikenan muje"
Yabi bayan Amal, tsananin kwarjinin Yusuf ne yasa Amal sam ta kasa kuma ce masa komai, se ƙamshin turare yake fitarwa me daɗin ƙamshi kaman ba direba ba.
A falon suka tarar da hakimar ta harɗe da alewa me tsinke a bakin ta, tana danna waya tareda kaɗa ƙafafuwan ta.
Kamar kullum yanzu ma kanta babu ɗan kwali, ta baje gashin ta, Amma yau anyi sa'a skirt ne dogo a jikin ta da wata 'yar ƙaramar riga shara shara.
Tunda Yusuf ya shigo ɗakin ƙamshin turaren sa ya daki hancin ta taji ya saukar mata da wata muguwar kasala, a duk lokacin da Yusuf zezo gidan nan taji wannan ƙamshin turaren a jikin sa se kasala ta saukar mata.
Kallo ɗaya Yusuf yayi mata yaji ƙirjin sa ya buga da ƙarfi, da sauri ya ɗauke idon sa daga kanta, Sam fuskar ta babu alamar afuwa.
Ya kalli matar gidan yace
"barka da yamma Hajiya"
"Yawwa barka sannu ya aikin?"
"Alhamdilillah"
Ya juya ga Widad yace "sannu da hutawa ranki ya daÉ—e"
Dama be zaci zata amsa ba, dan haka be kuma cewa komai ba se sunkuyar da kansa ƙasa da yayi.
Ya shafe mintuna Arba'in a durƙushe a gaban ta ba tare da tace komai ba, shi kuma ko kansa be ɗaga ba.
Amal ji take tamkar ita ce a durƙushe a gurin, gaba ɗaya taji kaman ta cewa Yusuf ya tashi yayi tafiyar sa.
Ba zato ba tsammani ya tsinkayi maganar ta
"Waye ya baka iznin tafiya jiya?"
"ba kowa Ranki ya daÉ—e"
Seda ta kuma jan wasu mintunan sannan tace
"meyasa ka tafi?"
Ba tare da ya É—ago kansa ba yace
"na zata na gama aikina na jiyane shiyasa, Amma hakan ba zata sake faruwa ba Insha Allah, kiyi haƙu....
Cikin tsawa tace
"Shut up, what the hell are you trying to say? Do you sign my conditions based on Assumption? Don't you read what is in that paper? Why are you trying to applogise? Talaka baze canza hali ba, baku da Alƙawari baku san ƙa'idar Aiki ba, se an jima ku buɗe baki kuna zagin shugabanni da masu kuɗi, waye kai da zaka karyamin doka? Me kake taƙama dashi da zaka nemi ka raina min hankali? Ɗan uban waye kai? Ko ban gaya maka lokacin aiki nawane ba? Har da zaka fara da rainamin hankali"
Tunda Widad ta fara zazzaga rashin mutuncin ta Yusuf be ɗaga kai ba, dukda yadda zuciyar sa ke harbawa jijiyoyin kansa suka miƙe saboda ɓacin rai, Amma ya dake.
Amal kaman ta É—ora hannu akai tayi ihu, ji take tamkar ita Widad ke ciwa mutunci, ita kuwa matar gidan da Ramlah ko a jikin su dan babu wanda Widad ta bari a rashin mutunci.
"kasan tsanani baƙin cikin da na shiga zama na a gidan nan bayan an ɓata min rai, daka nan ka fita dani da ban shiga damuwar dana shiga ba, tun jiya nake fama da damuwa saboda sakacinka, nayi kwanan baƙin ciki da ɓacin rai, this is my last warning to you, idan makamancin haka ya kuma faruwa, sena nuna maka wace ce Widad"
Risinawa ya kuma yi da kai
"zan kiyaye ba zana kuma ba insha Allah"
Jefo masa key tayi fuskar sa tare da faÉ—in
"Car Number 8, to bulama's residence"
Yaji zafin yadda ta jefa masa key a fuska, da maganganu marasa daɗi da tayi masa, amma yasa hannu ya ɗauka, kaman wanda ƙwai ya fashewa a ciki ya nufi hanyar fita.
Fakar idon Widad Amal tayi ta biyo bayan Yusuf, wajen ƙofar fita ta cin masa, yana ta sauri fuskarsa babu Annuri, Amal ta kira sunan sa, dan tsayawa yayi ya waigo yana kallon ta
"Dan Allah kayi haƙuri da abunda Widad tayi maka, haka halin ta yake muma duk haƙuri muke da ita, dan Allah kayi hakuri"
Ga mamakin ta se taga murmushi akan fuskarsa yace
"aini banji haushi ba, tabbas laifi nane da banbi komai a ƙa'ida ba, bayan nasan hakan ya saɓawa Yarjejeniyar dana sakawa hannu, kuma nasan yana daga AƘIDAR uwa ɗakina girmama Alƙawari, ya kamata in nemi Afuwa ne ba jin haushi ba"
ÆŠan zare ido Amal tayi "yanzu duk abunda tayi maka kana nufin ba kaji haushin hakan ba?"
Jinjina mata kai yayi alamar eh tareda faÉ—in,
"bari in hanzarta in fito da motar karta fito ta sameni anan ranta ya kuma ɓaci" yayi gaba abun sa yayin da shi kaɗai yasan me yake ji a ransa.
Yaje ya fito da motar da ce masa, ya buÉ—e ya shiga ya zauna ya kifa kansa akan sitiyari, tabbas badan duk cikin aikin sa yake wannan abun ba to da ko Gidan su Widad gold ake sarrafawa baze kuma aiki a gidan ba.
Jin ƙamshin turaren ta yasa shi saurin ɗagowa, ta buɗe gaban motar ta zauna, tace "jeka falo inda na zauna ka ɗakko min wayata"
Ikon Allah wayar ma bazata fito da ita ba seya É—akko mata? Bece komai ba ya fita daga motar ya koma cikin gidan, yana zuwa ya tarar falon ba kowa wayar tana kan center table, ya É—akko ya fito ya kawo mata.
Tasa hannu ta karɓa ba tare da ta kalle shi ba tace "A ina kaga wayar"
"Akan center table"
Murmushin gefen baki tayi tace "let's go"
Kamar yadda tace gidan Bulama ya kai ta, ya samu guri yayi parking ya fito ya buɗe mata ƙofa ta fito, ƙafarta sanye da takalmi me tsini sosai shigar nan tata baka ce musulma ce ba, kayan sun kamata tsam a jikin ta a hankali ta furta "do not accept any gift from anyone"
GyaÉ—a mata kai yayi yace "Insha Allah"
"Follow me"
Haka yabi bayan ta, cikin hanzari take tafiyar yau.
Yau kai tsaye bata nemi iso ba cikin gidan ta nufa, Yusuf na bin bayan ta.
A babban falon dake gidan suka ga wata budurwa da wannan matashin da suka tarar jiya, da wata babbar mace da alama itace matar gidan.
Maimakon Widad tayi Sallama se tace "Hi how are you doing guys?"
Matar tace "Widad dama kina garin nan amma ko ganin ki ba'ayi"
Budurwar tace "Wallahi Mum Ramadan yace tazo jiya amma taƙi shigowa" Yusuf dai bece komai ba saboda jan kunnen da tayi masa jiya.
Ramadan ya kalli Widad yace "you look so Cute in this outfit Dear"
Ba ta amsa musu maganganun su ba tace "Is Daddy Around?"
Yusuf ya kalli kayan dake jikin Widad, da kuma abunda Ramadan yace kawai ya girgiza kai
Ramadan yace "yeah yana nan"
Ƙoƙarin hawa bene Widad take yi, budurwar tace
"hey Baby who is this gentleman with you?"
Aiko tsaya ba tayi ba balle bada amsa, ta haye saman benen da sauri, Yusuf bashi da zaɓin daya fi yabi bayan ta.
Wata ƙatuwar ƙofa ta buɗe, ta kutsa kai Yusuf yabi bayan ta, shima wani haɗaɗɗen falo ne me girman gaske, sanyi Ac ke rasa ko ina na ɗakin.
Alhaji Bulama ne ke zaune akan É—aya daga cikin kujerun falon, yana shan tea tareda dannan system, Yusuf ne yayi sallama, Alhaji Bulama ya É—ago ya kalle su.
Murmushi yayi ya amsa sallamar Yusuf, yana ƙarewa Widad kallo, guri ta nema ta zauna tana fuskantar Bulama.
Bulama yace "Daughter wai shi wannan duk inda zaki se tare da shine? Ina direba ne kawai? Kodai Allah ya karɓi Addu'armu kin fara sakin jiki da mutane?"
HaÉ—e rai tayi tace "my policies remain constant, babu abunda ya canza, babu ruwan ka da dalilin da yasa duk inda zani yake bina"
Alhaji Bulama ya murmusa yace "shikenan Allah ya baki haƙuri"
Ya kalli Yusuf yace "Sannu ɗan Samari, daughter ɗin tamu seka na haƙuri, muma lallaɓata muke"
Da ido ta kalli Yusuf, dan haka Yusuf bece komai ba se É—an murmusawa da yayi.
Alhaji Bulama ya maida kallon sa ga Widad yace "ina jinki?"
"Meyasa ka turawa Daddy na ra'ayin ayimin Aure?"
ÆŠan girgiza kai Bulama yayi tareda murmushi "yaro yaro ne, Widad Aure shine ya dace dake, domin shine ze gusar miki da wannan larurar ki zama kaman sauran mutane"
"na taɓa ce maka ina son Aure ne? Ko kuma akwai shi a cikin tsarin Rayuwa ta?"
"look daughter, Aure shi ze gusar miki da dukkanin wannan halin da kike ciki, babu yadda za'ayi lafiyayyen mutum ya rayu ba tare da mutane a cikin Rayuwar sa ba, shi yasa muka yanke shawarar Aurar dake"
"ka dai yanke shawara sannan ka cusawa Daddy na ra'ayin hakan, ace har Daddy yamin laifi sannan ya fita harka ta dan naƙi yadda da batun Auren nan, duk kai ka jamin, sannan nida ban yadda da soyayya ba balle inyi ta har in samu mijin Aure, wazaku aura min?"
Gyara Zama Bulama yayi yace
"Fuhad mana first born É—ina, kun dace sosai, ze soki tsakani da Allah ya zauna dake, tunda ke 'yar uwassa ce"
Shiru tayi ta kalli Bulama sannan tace "what the fucking shit are you talking about? meye wani ze soni tsakani da Allah? Let me tell you something, i don't believe in Love talk less of true love, Love is just an imagination full of bull shits and stupidity, so ke sa ayi aure ko? To ban yadda yayi existing ba, dan haka ka gaggauta warware wannan maganar, dan ko aure zanyi bazan auri namiji bahaushe ba, you people that are not romantic at all, babu abunda kuka iya banda iko da ɗaukar matayen ku tamkar bayinku, baku damu da halin da zasu shiga ba idan har taku buƙatar zata biya, baku iya komai ba se masifa da hantara, don't you see how women are complaining about you? How Hausa women's are suffering because of your poor marital life? Women's are always complaining about marriage issues, this is type of life you want me to do? Do you think I can live with someone that will be shouting at me?"
Shiru Bulama yayi yana kallon ta, Ta gyara zama ta kalli cikin idon Bulama tace
" idan baso kuke ku ƙara tunzura haukan nawa ba kaman yadda kuke iƙrari ba, ya kamata ku ƙyaleni da maganar nan"
Numfasawa Bulama yayi yace "Amma kin san mahaifinki ma bahaushe ne, kike wannan maganganun akan mazan hausawa"
"da nace ban dashi a ciki ne? Shima badan yayi rayuwar Turai ba he will have the same negative habits on his wife, it seems it is in your genes, Alhaji Bulama daga yarin tata sanina da kai mata nawa ka aura bakwa tare yanzu? Go back to your senses Sir, Am not ready to ruin mad, i don't have interest of getting marriage, i don't know maybe later, but I can't married a man from hausa people, they don't value their wives "
Ba Bulama ba, Yusuf kansa yaji haushin cin mutuncin da Widad tayi wa ƙabilar Hausawa, duk lalacewar Al'umma akwai mutanen kirki ai, Amma ba shida ta cewa, tunda shi ɗan karere ne.
Ta miƙe tsaye tayi gaba abun ta, Yusuf ya rufa mata Baya, yauma har suka je gida ba wanda ya kula wani, sedai da suka koma gidan, a mota ta bar jakarta da wayarta, dole Yusuf ya ɗauka ya bita da su ba dan yana so ba, dan sam baya son shiga cikin gidan, ba ƙaramin tsarguwa yake da irin kallon da mutan gidan ke masa yake ba.
Yanzu kam ba 'a hankali take tafiya ba cikin gaggawa take tafiya, kaman tana son tayi wani abune, ta falon da zata bi ta wuce ta tarar da Mahaifinta a zaune da shi da matarsa, ko kallon su batayi ba tasa kai zata wuce.
"Widad" Mahaifinta ya kira sunan ta ba tare da juyo ba ta tsaya cak, be damu ba ya É—ora da cewa
"Munyi waya da Bulama ya gayamin abunda kika je kika ce masa, ki sani wannan karon dole kibi abunda nake so, bani zan biki ba, am doing all this for your benefit, in the next two Months insha Allah Fahad zezo ƙasar nan, ina son ayi Auren ku kafin ya koma"
Cigaba tayi da tafiyar ta ba tare da cewa Mahaifinta komai ba. Yusuf dake tsaye yana jinsu ya ƙarasa ya gaida mahaifin Widad da matarsa Hajiya Halima.
Ya amsa masa cikin, yayin da Hajiya Halima ta Amsa masa a ciki.
Yusuf ya miƙa wa Mahaifin Widad jakar ta da keys ɗin motar ta, yayi musu Sallama ya fice.
"Yaya Yusuf" yaji an kira sunan sa, tsayawa yayi ya waigo, Amal ce take tahowa da sauri hada É—an haÉ—awa da gudu.
"Sannu ashe kun dawo?"
"Eh mun dawo, akwai wani abu ne?"
ÆŠan sosa kai tayi tace "dan Allah in babu damuwa so nake ka raka ni Shopping"
"Shopping kuma? NiÉ—in?"
"Eh amma idan ban takura maka ba"
"ina batun takura ni da nake muku aiki, idan kin shirya kimin magana"
Murmushi tayi tace "nagode sosai Yaya Yusuf"
Shima murmushi ya mayar mata yai gaba abun sa.
(WASA FARIN GIRKI)
Share please 🙠🙠ðŸ™
Comment nake so ba sticker ba ko kuma thanks ba, inda suka fi Comment su zasu dinga fara samun posting
Domin gyara, sharhi, kokuma ƙorafi a tuntube ni akan wannan lambar
07063065680
Watpad Ayshercool7724
_*AƘIDA TA*_
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
Haƙƙin Mallaka ⚠: Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
ELEGANT ONLINE WRITER'S
              PART1
                 Page 5
Yusuf ya fita yaje yai alwala yai salla saboda lokacin salla yayi.
Widad kam tana zuwa É—akin ta ta jefar da Jakarta da wayar ta akan gado ta fara safa da marwa a É—akin ta
"Bulama ina ganin girman ka, ina maka kallon uba amma kana ƙoƙarin ƙetare gona da iri, kana ƙoƙarin tsallake iyakokinka, a tunanin ka yin Aure ze sa in canza ra'ayina? Daddy kunyi kuskure daga kai har Bulama, kuma bazan taɓa bari wannan kuskuren naku yayi tasiri a kaina ba, dole inyi wani abu" haka ta cigaba da surutai ita kaɗai.
Hajiya Halima ta kalli maigidan ta tace "Nikam wai Alhaji dagaske Widad zakayi wa Aure ko kuma yaya? Na kasa gane kan lamarin"
ÆŠan shiru yayi sannan yace "Eh hakane, Bulama ya bani shawarar akan cewa muyi mata Aure hakan ne kawai zesa ta canza wannan halin nata, Amma yarinyar nan kin san halin ta da kafiya da taurin kai, ta tirje tace sam bata san zancen ba, Amma a wannan karon bazan canza ra'ayi ba, ina son inga ta dawo da walwalarta, wannan karon dole tayi biyayya ga umarni na"
"Amma Alhaji baka ganin yin hakan tamkar ze ƙara tunzura rashin lafiyar ta ne, zaka ƙara sawa rashin lafiyar ta ya tsanan ta, ko ka manta sharuɗan da likitoci suka gindaya ne akanta?"
Alhaji Nasir Ya numfasa sannan yace
"Shima zaman ta a hakan bakomai ze ƙara mata ba face cigaba da dawwama a cikin damuwa da rashin walwala, akwai buƙatar ko bayan raina Widad ya zama na tana da kafaɗar da zata tada kai, ya zamana tana da wanda ze kula da rayuwar ta"
"Amma Alhaji wa zaku bawa Auren ta? ina fatan wanda zaku bawa yasan yanayin larurar ta? Tunda kaga ba shiga mutane take ba balle a ce tana da wanda take so, kar a bawa wanda besan ya take ba abu yazo ya ɓaci"
Alhaji Nasir yace "Ai ba wani bane za'a aura matan, fahad ɗin Bulama ne, itace dai batayi wayon saninshi sosai ba, rabon da su haɗu tun tana yarinya ƙarama, Amma shi ya santa kuma nasan baze bamu kunya ba Insha Allah, tunda itama tamkar ƙanwa take a gurin sa"
Jinjina kai kawai tayi ba tare da ta kuma cewa komai ba.
Wajejen la'asar Amal ta shiryo cikin wata irin doguwar riga wadda ta kama jikin ta matuƙa, se zuba ƙamshin turare take wanda turaren har hawa ka yake yi saboda ƙarfin sa ta hau kan wani takalmi me uban tsini, duwatsun jikin rigarta se ƙyalli suke suna rawa.
Cikin iyayi ta ƙarasa inda Yusuf yake zaune da su Nura da sauran ma'aikatan gidan tace "Yaya Yusuf mu tafi ko na shirya"
Ba musu Yusuf ya miƙe yayi wa su Isa sallama.
Ya karɓi mukullin Motar Amal, suka shiga mota suka fice.
Yusuf na barin gurin Murtala me bawa shukoki ruwa yace
"wai kunga abunda na gani ko kuwa?"
Nura yace "mun gani, kai kaga wata irin kwarkwasa da take masa? , anya yarinyar nan Amal ba san shi take ba? Kaga wani iyayi da take yi tana fari da idi"
Murtala yace "Amma kuwa da ta faɗo, duk zuƙa zuƙan Samarin dake zuwa gurin ta? duk iya yin da wulaƙancin nata ta ƙare a direba, wallahi da tayi faɗuwar baƙar tasa"
Isa yace "to ai gara Amal ɗin akan yayar ta Ramla, kun san agola musamman in aka samu guri akwai iskanci, yadda suke hura hanci suna Wulaƙanta mutane kai kace gidan ubansu ne, Amma fa duk da haka gara nasu lafiya ne akan 'yar masu gida wai wa yaga Azaba, idan bata ga dama ba fuskarta idan ka kalla seka yi fitsari a wando, saboda sam bata da rangwame, Azababbiyar Yarinya idonta fiƙi fiƙi kamar me maye"
Nura yace "wallahi ko san haɗa hanya da yarinyar nan bana yi, nagode Allah da yasa ba ita nake tuƙawa ba baban ta nake tuƙawa, ni nayi mamaki ma yadda Yusuf ɗin nan har yanzu basu samu saɓani taci mutuncin sa ba, dan naga wani jin kan sa yake shima, musamman idan yana jan manyan motocin nan se kace na gadon ubansa, kamar har mantawa yake direba ne shi"
Isa ya gyara zama ya waiga sannan ya ƙara ƙasa da muryar sa yace
"ku nifa ban gama yadda da Yusuf ɗin nan ba, kuna ganin sa wani haɗaɗɗe da shi, kullum tsaf tsaf da shi, babu alamar wahala a tare da shi, ga jan aji duk yafi mu kyan gani sannan ace ya ƙare a direba anya babu lauje cikin naɗi a wannan harkar kuwa?"
Murtalah yace "Nima nayi wannan tunanin, amma ya zamu san gaskiyar lamarin? Dan ya fara bani haushi wallahi, yadda megidan nan ya fara wani girmama shi wai yana da sunan yayan sa, har wani Yaya na yake ce masa shi kuma yana washe baki yana sunkuyar da kai, damabidan mutum yavfiye sunkuyar da kai munafuki ne"
Isa yace "ku ƙyale shi zan bugi cikin sani inji ko zamu samu wani bayanin muji, ai duniya seda labari, Amma ina tunanin ta yadda za'ayi kamar wannan da beyi kama da wanda yake cikin wahala ba yazo yana aikin direba"
Yusuf ya ƙudurcewa ransa ze ɗan dinga sakarwa Amal, domin samun sanin wasu abubuwa da suka shige masa duhu game da yanayin tsarin Rayuwar mutanen gidan. Suna tafiya a hanya Amal tace
"Yusuf dan Allah ka dinga haƙuri da abunda Widad take maka, sam abunda tayi maka ɗazu banji daɗi ba wallahi haka take bata san darajar ɗan Adam ba mussman talaka, bata da mutunci, mu kanmu haƙuri kawai muke da ita sam bama jin daɗin zama da ita, shiyasa babu wanda yayi farinciki da dawowarta"
Yusuf da sauri yace "A'a uwa É—akina ce fa ranki ya daÉ—e, ya zaki ce bata da mutunci a gabana? ai bazan ji daÉ—i ba gaskiya banji daÉ—in yadda kika aibata ta ba"
Kallon Yusuf tayi galala cike da mamaki tace "kana nufin baka ji haushin abunda tayi maka bane? Ai ba ƙarya nayi mata ba, da tana da mutunci da bata muzanta maka ba, harta jefe ka da key a fuska ba"
Yusuf yayi murmushi yace "yana da kyau mu dinga girmama doka kafin muyi ƙorafin anci zarafin mu, ko ba'ayi mana adalci ba, da hannu na na saka hannu akan dokokin ta kafin in fara mata aiki, na saka hannu na amince da zanbi sharuɗan data gindaya min, dan haka tunda ni na saɓa abunda na sakawa hannu, komai tayi min be kamata inji haushi ba, ko kuma ince bata da kirki ba, idan nayi haka banyi wa kaina adalci ba"
Amal tayi ajiyar zuciya tace "indai wannan ce kai da kanka zaka dawo daga rakiyar ta saboda wulaƙancin ta, dan wataran seta maka abunda zesa ka tsaneta tamkar mutuwar ka, tun bamu kai haka ba mahaifiyar mu ta auri mahaifin ta muke zaune tare, Amma bamu da daraja ko ƙima a idon ta, kai bamu ba har mahaifiyar mu bata ɗagawa ƙafa, Alhaji Bulama ne ya bada shawarar a bar ƙasar nan da ita, shine ma muka samu muka huta na wasu shekaru kafin ta dawo, se a dinga fakewa da bata da lafiya, tana taka mutane tana nuna isa da Izza"
Yusuf yace "bata da lafiya kuma? Kamar ya bata da lafiya, Meke damun ta?"
Ɗan taɓe baki Amal tayi tace "wai bata da lafiyar ƙwaƙwalwa, ko da yake me lafiyar ƙwaƙwalwa baze abunda take ba, wannan dukiyar ta mahaifin ta, da ita take taƙama da ita take wulaƙanta mutane, ta yaga duk wanda yayi mata abunda yake saɓanin raa'yin ta, aikin banza, dukiyar da'ake farautar ranta akanta, Amma take da damar Wulaƙanta mutane saboda ita"
Da sauri Yusuf yace "kamar ya farautar rai? Ranwa ake farauta, saboda dukiya?"
"Ran Widad ɗin mana, yana ɗaya daga cikin dalilin da yasa ta bar ƙasar nan fa, bayan larurar Ƙwaƙwalwa da take dashi ana farautar ranta ne, tunda maman ta ta rasu take fama da larurar ƙwaƙwalwa, kuma a kazo ana nema a kashe ta, abundai gashi nan, Amma kodan wulaƙanta mutane da take dole wani yai ƙudurin kashe ta ya huce takaicinsa, bayan wulaƙancin da take wa mutane, har ɗaure mutane take sa ayi"
Jinjina kai Yusuf yayi yana kuma nazarin maganganun Amal, baya so ya cika ta da tambayoyi, karta fuskanci wani abu dan haka yayi shiru yana É—an satar kallon Amal yana tunani a ransa.
Yusuf ya kai Amal wani katafaren mall kaman yadda ta buƙata ta dinga ɗibar kaya, sannan tace Yusuf ya ɗauki abunda ya keso.
"A'a nagode amma ni bana buƙatar komai"
Amal tace "haba Yusuf dan Allah ka É—auka, karka ji komai"
Fafur Yusuf yaƙi yadda ya ɗau komai se haƙura tayi.
Bayan sun dawo gida tace dan Allah ya taya ta ɗaukar kayan da ta siyo, babu musu ya ɗau kayan yabi bayan ta kamar yadda suke da Widad, Sedai tun a babban falon ƙasa suka ci karo da hakimar ƙafar ta ɗaya kan ɗaya tana shan tea, gefen ta kuma tana bawa magenta madara, bata kula su ba su kayi gaba za su wuce, muryar ta suka jiyo tace
"Stop there" ta faÉ—a kai tsaye cikin bada umarni, gaba É—aya suka tsaya suna jiran me za tace.
Se da ta ja wasu seconds sannan tace
"Amal yaushe muka fara sharing ɗin abu nida ke ne ban sani ba? Ya akayi matsayinki har ya kai kiyi amfani da abina ba tare da kin nemi izini na ba?" tai maganar tare da miƙewa tsaye, tavtako ta zo har inda suke tsaye ta kalli Amal, ta tsaida dubanta kan Amal, Amma tace wa Yusu
"waye ya É—auke ka aiki a cikin gidan nan?"
"kece ranki ya daÉ—e" ya faÉ—a cikin girmamawa
"Wa kayi wa aiki yanzu?" tai maganar me cike da bayyanar da tsantsar Izzar ta
" 'yar uwarki ranki ya daÉ—e" ya bata amsa
Ta ɗan lumshe ido sannan ta buɗe tace "Na taɓa gaya maka ina da ɗan uwan ko' yar uwa ne?"
"A'a"
"lokacin dana É—auke ka aiki na gaya maka nida wani zakayiwa aiki?"
"A'a" ya sake bata amsa
Ta maida idon ta kan Yusuf cikin É—aga sauti tace
"Ka karyamin doka karo na biyu da wani suna ya kamata in kira kane? Bagidajen ina ne kai? Ko kuma ince daga wani jejin kake? a haka you look civilized amma kwata2 shashasha ne kai, hala ka manta akan death contract kayi signing? Inaga ka manta ne, ko kuma ka É—auka wasa ne shiyasa kake wasa da rayuwar ka"
Ya girgiza mata kai alamar A'a
Hayaniyar da Hajiya Halima take ji sama sama ne ya sa ta fito ita da ramlah suka tsaya suka yi cirko cirko a falon Widad tana ta zuba tsiyata kunta san ranta.
Widad tace "Yanzu ina maka hukunci se ka kirani azzaluma ko? Saboda haka ɗabi'ar ku ta matsiyatan mutane take, ku kullum akan daidai kuke masu kuɗi kuma Azzalumi ko?, dukda bana maimaita magana yau zaka sani na maimaita, Ni Widad ban yadda da kowa ba, duk yadda muke da mutum karyamin dokoki na daidai suke da yunƙurin cin amana ta, kuma penalty ɗin wanda yaci amana ta, bana jin tantirin talaka wanda bashi da komai kamar ka ze iya ɗauka "
Amal tace " haba Widad be kama......
Ɗaga mata hannu Widad tayi ba tare da ta kalli Amal ba tace "har yanzu 'yar alfarma ce ke a cikin gidan nan, matsayinki be kai na 'yar masu gida ba, karki ƙara gangancin ina magana ki katseni ko kisamin baki, idan ba haka ba kin san sauran, kai kuma daga yau nikaɗai kake wa aiki a cikin gidan nan, ban yadda wani ya saka aiki kayi ba, duk wanda yace kai wani abu kace Widad kake wa aiki ba wani ba, sannan kayi a rabin salary ɗinka shine hukuncin karya min doka da kayi har sau biyu dismiss from here"
Yusuf ya risina ya ɗanyi murmushi yace "godiya nake uwaɗakina, Allah ya ƙara girma Insha Allah zanyi ƙoƙari in kiyaye dokokin ki, bazan ƙara karya miki doka ba, Allah ya huci zuciyar ki"
Gaba É—aya suka bi Yusuf da kallo wato shi duk wannan cin zarafin da aka yi masa godiya yayi, lallai wani talakan Jaki ne, besan ciwon kansa ba, Ramlah ta faÉ—a a ranta.
Widad ta kallesu ɗaya bayan ɗaya tace "bana buƙatar kowa a falon nan, madam zaki iya jan zugarki ku ɓace min daga nan"
Saboda tsabar baƙinciki da takaici Amal watsi tayi da kayan shopping ɗin da tayi a falon, tai cikin part ɗinsu da gudu tana kuka, abun yayi yawa taji zafin cin mutuncin da akayiwa Yusuf ga tsabar wulaƙanci da suke fuskanta a gidan nan se kace Almajirai, kokuma wasu bayi.
Ramlah ta kalli mahaifiyar su tace
"Mummy am tired wallahi enough is enough are we slaves? see how this little baby is shouting at both of us including you, Mummy you have to do something"
Kafin Mummy tayi magana Amal ta shigo tana kuka.
Mummy tace "Amal meya saki kuka?"
"gaskiya ni Mummy zan tattara kaya na in bar gidan nan na gaji, wannan wane irin cin zarafi ne?"
Mummy tace "duk nasan da haka amma kuyi haƙuri ku ƙara wataran se labari da munsamu abunda muke so shikenan fa an wuce gurin"
Amal tace "dan Allah Mummy yaushe wataran É—in nan zata zo, shekara nawa muna zama kaman bayi? Wallahi nagaji kalli cin mutuncin da tayi wa wannan bawan Allah dan kawai ya kaini unguwa"
A fusace Ramlah tace "dallah rufewa mutane baki, dan taci masa mutunci seme ina ruwan wani? Shi ta fara yiwa cin mutunci? Dama naga yadda kike wani zaƙewa a kansa tun wuri ki nutsu dan ni natsane shi wallahi sam ban yadda da shi ba"
Amal tace "Malama ba ruwan ki da abunda nake yi seki ta tsanar tasa ai, seki kashe shi tunda kin tsane shi"
Mummy tace "kunga dan Allah ya isa haka kar kuyi min faÉ—a, ni kaina ban yadda da wannan Yusuf É—in ba, narasa yadda aka yi megidan nan ya wani É—aukake shi haka, ina son sanin daga ina yake"
Haɗe rai Amal tayi ta zumɓura baki
Mummy tace "ku kuke tada hankalinku, Ramlah zancen da kika yi min ranan na tambayi babanta ya tabbatar min da cewa Aurar da ita zeyi"
Da yake Amal bata san zancen ba da sauri ta waigo tace "Aure kuma? A hakan za ai mata Aure? Waze kwashi wannan Jarabar"
Ramlah tace "Mummy dama na gaya miki, Amma wane me tsautsayin za'a liƙawa wannan Mahaukaciyar? Nasan dai bata da saurayi to waze ma kulata taci masa zarafi"
Mummy tace "ba wani bane Fahad ɗin Alhaji Bulama ne"
Asahar Ramla ta saki tace "Wane Fahad É—in?"
Murmushi Amal tayi tace "Bulama nawa muke da shi? Fahad dai da kika sani, Fahad naki shine me tsautsayin"
Ramlah tace "Taɓɗijan wallahi da sake, baze yuwu ba akan me? Ita Hajiyar sa tana me za'a aura masa wannan tantiriyar ga hauka gashi maybe ta gama watsewa da turawa, shekararta nawa a turai, Allah kaɗai yasan me take acan baze yuwu ba"
Ta miƙe ta bar ɗakin tana masifa.
Yusuf be bar gidan ba ranar se bayan sallar isha'i.
Koda yaje gida ya tarar Umman sa ba taci Abincin dare ba shi take jira, seda sukaci Abinci suka yi hira sannan ya koma É—akin sa.
Ya É—akko laptop É—in sa ya shigar da duk abunda ya faru da date da komai, dukkanin hirar da suka yi da Amla seda ya rubuta sannan ya kwanta.
Tun daga ranar Yusuf yake taka tsantsan gurin bin dokokin Widad, Sannan yana ta ƙara lura da yanayin mutanen gidan da ɗabi'ar kowa daga cikin su.
Widad ta aika Ramla ta kira mata Yusuf.
Ramlah tana zuwa inda suke zama ta kalle shi a wulaƙance tace
"kai wa kake kazo inji waccan yarinyar"
Yauma Yusuf ya shirya tsaf ze kai Widad Store za tayi siyayya bayan fitar su, Hajiya Halima ta aika aka kira mata Isa mai gadi, yaje ya same ta a ya durƙusa ya gaishe ta, ta amsa masa a wulaƙance sannan tace
"kaine ka kawo wa Widad direba ko?"
"Eh nine Ranki ya daÉ—e"
"Good, ina son sanin daga ina yake?"
Isa ya risina sosai sannan yace "Wallahi ranki ya daÉ—e ban san daga inda yake zuwa ba, nima wani abokina ne Sani ya kawomin shi yace É—an uwan sane amma ban daga ina yake ba"
"ka buÉ—e kunnen ka da kyau ka saurareni"
Isa yace "to Hajiya"
"Ina so duk yadda za'ayi in san daga ina yake? Daga ina yake zuwa gidan nan, sannan ina so ka ƙara samun ido akan sa sosai ina tunanin akwai wani ɓoyayyen abu a tare da shi"
"An gama ranki ya daÉ—e insha Allah zanyi yadda kike so"
"sannan wannan maganar ina so ta tsaya daga ni se kaine, bana son wani ya san munyi ta"
"babu me ji ranki ya daÉ—e"
"tashi ka tafi" Isa ya tashi fita.
Yusuf kam wani katafaren shago ya kai Widad, ta siyi kayan da take buƙata, hatta ruwan roba da zata sha seda ta siya abun ta.
Banda kayan ciye2 da sauran kayan ƙyale2
Seda sukaje gurin biyan kuÉ—i ta kalli Yusuf tace "jeka mota ka É—akko jaka ta"
Ba musu yaje ya ɗakko 'yar ƙaramar jakar ta ya kawo mata"
"buÉ—e ka É—akko ATM card É—ina"
Ya ɗakko ya riƙe aka lissafa kuɗi, kuɗi ne masu yawan gaske, ko a jikin ta tace
"basu ATM ɗin" ya miƙa musu suka saka a POS suka miƙo masa yasa ka password ya sa hannu ya karɓa ya miƙo mata domin ta saka lambobin da zasu bada damar cirar kuɗin, a hankali tai ƙasa da muryar ta tace
"7724" Yusuf ya gane me take nufi haka ya danna lambobin ya miƙa musu.
Suka ciri kuÉ—in su yana mamakin me yasa ta gaya masa password É—in cirar kuÉ—in ta.
Sun fito harabar Store ɗin zasu tafi suka wuce ta gefen wani mutum dake ƙoƙarin rufe motar sa yabi Widad da kallo tare da faɗin subhanallah.
Da sauri yabi bayan su Widad, Yusuf yayi gaba yana zuba kaya a mota mutumin ya sha gaban Widad yace
"Ahh excuse me Madam you look so hot"
Zare glashin fuskarta tayi tai masa kallon sama da ƙasa ta mayar da glass ɗin ta, tai gaba abunta.
Sake binta mutumin yayi ya sha gaban ta zeyi magana Widad tace "wai me kake nema ne?"
Yusuf kam ganin ta tsaya ya sashi komawa inda take tsayen dan ganin meke faruwa.
Mutumin yace "Wow ashe bahaushiya ce? Gaskiya beb bazan ɓoye miki ba kin tafi da imanina, kin min ina sonki, ki bani contact ɗinki mana se muyi magana, you look sexy" yai maganar yana wani kashe ido irin na 'yan bariki tare da miƙowa Widad wayar sa
Karɓar rantsatsiyar wayar tayi kaman gaske, ta sake ta a ƙasa ta fashe sannan tace "waya gaya maka samun lamabr mace kamar ni a gurin ƙasƙantattun mutane marasa amfani irinka abu ne me sauƙi, dalla matsa a gabana ko in tsinka maka mari sakarai kawai"
Waro ido mutumin yayi "ni zaki tsinkawa mari? Kin san waye ni kuwa? In baki wayata ki fasa min"
"Waye kai banda banza wofi, matsiyaci mara amfani? Kauce a gaban kafin inyi maganin ka"
Kan Widad mutumin yayo yana kumfar baki "Wallahi sena nuna miki koni waye a garin nan, 'yar uban waye ke da zaki min haka? Sena ci zarafin ki na wulaƙanta ki"
Tuni Attention É—in mutane ya fara yowa kansu kaman ze daki Widad, Yusuf ya shiga tsakanin Widad da mutumin ya kalli mutumin yace
"kana ta mana kumfar bakin ba' a san waye kai ba, ita kasan wacece? Ina ruwan ka da ita da zaka biyo ta kafaɗi maganar banza akan ta, ka kiyaye harshen ka kafin a nuna maka ƙarfin ikon data ke dashi"
"Kaikuma waye kai waye ya sakoka a cikin wannan maganar?" mutumin yasa hannu a aljihu ya miƙowa Yusuf id card ɗinsa, kafin Yusuf ya karɓa Widad tasa hannu ta karɓe ta duba id card ɗin nasa sannan tace
"Ashema matsiyaci ne taƙamarka kaki ko? Zan iya sawa a keta kakin naka a gaban mutane a wulaƙanta ka, a tozarta min kai, sannan in ɗaure ka, kuɗi sunfi wannan kakin banzar da kake tin ƙaho dashi, Widad Nasir Daula inada Arzikin da zan wulaƙanta ka ka ƙare a gidan yari sakarai kawai "
tayi jifa da ID card É—in nasa ta tofa miyau akai
Ai Sunan ta data faÉ—a yasa mutumin nan wani mummunan zare ido tare da sauke numfashi yana kuma maimaita sunan nata.
Widad ta wuce mota Yusuf ya bita suka tafi, suna tafe tana ƙwafa tareda yin tsaki jefi2 kallon ta kawai Yusuf yake.
Suka isa gida ta buÉ—e murfin motar ta fice abunta, Yusuf ya É—ebo kayan ya bita dasu, matar gidan tana falo tana kallo, Yusuf ya shigo yabi bayan Widad har É—akinta ya ajiye mata kayan, ze juya ya É—ebo sauran tace "É—an tsaya" Yusuf yaja ya tsaya tazo ta duba kayan, ta É—akko wata Jaka da turaruka a ciki ta ajewa Yusuf, cike da iko da kashedi tace
"daga yau karka ƙara saka wannan banzan turaren da kake sawa in zaka zo inda nake, ga wannan turarukan kar in kuma jin kasa wannan turaren dan yana samin tashin zuciya ina fatan ka gane?" jinjina mata kai yayi alamar Eh.
Ya É—au ledar turaruka ya fita ya kwaso mata sauran kayan ya kawo mata, yana zuwa ya tarar ta shiga wanka, dan haka ya haÉ—a da ledar turarukan da ta bashi, ya ajiye mata akan gadonta yai ficewarsa.
Bayan Yusuf yayi sallar Azahar ya nemi guri ya zauna a inda suka saba zama da sauran ma'aikatan gidan, Isa mai gadi yace
"Yusuf manyan ƙasa, gaskiya ka ciri tuta a gidan nan, ina jinjina maka"
Yusuf yace "Mena yi na cancanci jinjina haka"?
"Ahh irin yadda kake jure cin mutuncin wannan yarinyar mana, naga da alama kaman kai bata yi maka wulaƙsncin, amma dukda haka kana haƙuri wallahi yarinya se kace sheɗaniya, zuciyar ta babu Imani se miyagun Aƙidun turawa to aibtama ci uwar turawa wannan"
Yusuf yace "kaga dakata Isa, kana gidan mahaifinta kana cin Arzikin su sannan kuma ka dinga zagin ta? Aiba'a haka a rayuwa, ni duk wannan abubuwan da kuke faɗa akan ta ni bana gani, danni ba ta yi min ba"
Isa yace "ni na rasa me yasa kullum kake ƙoƙarin kare ta, da anyi magana ka hau kare ta, ina tausayawa ranar da zata maka mugun halin nata, naga yadda zaka yi ai"
"kaga Isa abar wannan maganar dan Allah"
Isa yace "shikenan tunda haka kace, nikam nace ina Sani kuwa? kwana biyu baya zuwa gidan nan ko a waya bana samun sa, nasan kai kuna haÉ—uwa tunda unguwar ku É—aya"
Yusuf yace "waye ya gaya maka unguwar mu É—aya?"
"Ai gani nayi É—an uwanka ne shiya kawo ka gidan nan, dan haka nayi zaton unguwar ku É—aya"
Yusuf ya murmusa yace "A'a ba unguwar mu É—aya ba"
"to kai a wace unguwa kake? Ko ince inane ƙauyen ku? Dukda baka yi kama da 'yan karkara ba, ni mamaki ma nake yadda matashi kamar kai yake aikin direba"
Yusuf yayi murmushi yace "Isa kenan, dama su' yan ƙauyen wata kamace dadu ta daban ne? meyasa ka damu da sanin unguwar da nake?, indai Sani ne zan nemo maka shi dukda ba unguwar mu ɗaya ba, zan kawo maka shi har nan yazo"
Yusuf ya basar da zancen yaƙi gayawa Isa unguwar da yake.
Duk wasu hikimomi Isa yabi, Amma Yusuf ya nuna masa ƙwarewa irin ta jami'in sirri ya basar da zancen ya shiga wani.
Daga ƙarshe ma ya miƙe ya bar gurin, Isa yace "wannan anyi Jarababbe me taurin kan masifa, ƙiri Ƙiri yaƙi gayamin, amma zaka ga tsiya, in kasan wata baka san wata ba, zan biyo maka ta inda koka ƙi Allah seka faɗa"
Share please ðŸ™ðŸ™ðŸ™
Masoya masu Comment ina godiya, Allah ya bar Æ™auna 😠😠😠ku sani yanzu aka fara wasan, amma gaskiya idan ba'a Comment yadda nake so zan É—au matakin da ya dace, dan Allah idan kin karanta idan kin san Tanks kawai zakice koki turamin sticker ki riÆ™e abun ki please ðŸ™ðŸ™ðŸ™
Domin sharhi, gyara ko shawara Æ™ofata a buÉ—e take, feel free to contact me, sedai in ban buÉ—e saÆ™on da wuri ba ayimin afuwa, ina godiya ðŸ˜
Ayshercool
07063065680
           _*AƘIDATA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Haƙƙin Mallaka ⚠: Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
ELEGANT ONLINE WRITER'S
      Â
             PART1
                Page 6
Widad kam koda ta fito daga banɗaki, da jakar turarukan nan data bawa Yusuf ta fara yin arba akan gadon ta, ta ƙarasa a hankali ta duba, sune dai turarukan da ta bashi,
"lallai wannan É—an rainin hankali ne, ni zan bashi abu yazo ya ajiye min?"
Fita tayi falo ba kowa dan haka ta wuce part ɗinsu Amal, tana zuwa ta tarar da su a kitchen suna ta girki suna hirarsu, Wai Ramlah zata yi baƙi, se hada hada suke da kaji da sauran kayan masarufi.
Basu san da zuwan Widad ba se muryarta da suka ji cikin isa tace
"Ramlah kije gate ki kiramin driver na yanzu"
Cike da ɓacin rai, ba tare da Ramlah ta kalleta ba tace "to"
Haka Ramlah ta fita tana ƙunƙuni ta nufi bakin gate.
Tana zuwa ta tarar Yusuf ya siyo Abinci ze fara ci, Ramlah tazo kansa ta tsaya ta ƙare masa kallon up and down a wulaƙance, ta kalli gurasar gaban sa ta masu balango da nama ta kuma kallon sa ta taɓe baki ta ɗanyi tsaji taxe
"kai kazo inji waccan yarinyar"
Banza Yusuf yayi mata ya cigaba da ƙoƙarin cin Abincin sa.
"Wai baka ji ne?" ta masa magana cikin tsawa.
Nura direban Alhaji yace "Yusuf da kaifa take magana"
Yusuf ya É—ago ya kalli Nura yace "yawwa Sunana ka ambata, meze hana ta kirani da Sunana dan me zata cemin kai, kuma ni ban san wata yarinya a gidan nan ba"
Mamakine ya kama Ramlah, dama yana magana haka da wulaƙanci amma yake iya tsayawa Widad taci zarafin sa? Ba mamaki saboda kwaɗayin abun duniya kar a kore shi shiyasa yake shnaye wulaƙancin Widad, amma har ita wannan talakan ze buɗe baki ya gayawa magana a fusace tace
"kai saurara bazan kira sunan naka ba, uban waye kai da zaka dinga tambayar ban san sunan ka bane? Kai a wa? Ka kiyaye ni wallahi bana son shirme idan kace zakamin rashin mutunci zaka ga abunda ze biyo baya, sannan idan kaga dama kaje, in baka ga dama ba karka je ka san sauran"
Yusuf yayi kaman ba da shi take ba ya ci gaba da antaya gurasar sa. Ran Ramlah ne yai mugun ɓaci da ganin wannan rainin hankalin na Yusuf, ƙwafa tayi ta koma cikin gida.
Nura yace "Yusuf dan me zakayiwa Ramlah haka? So kake kaja wa kanka a kore ka?"
Yusuf yace "Nura kenan, to a korenin mana seme?" ya ci gaba da cin gurasar sa seda ya gama cin Abincin sa, Sannan ya miƙe ba tare da ya kuma cewa komai ba ya nufi cikin gidan.
Yana zuwa ya tarar da hakimar ta É—ora kafarta akan centre table tana jiran isowar sa.
Yusuf ya ƙaraso cikin girmamawa yace "gani ranki ya daɗe"
Widad tace "se yanzu ka ga damar zuwa? Na tura a kira ka kace bazaka zo ba seka gama abunda kake?"
Da confidence É—in sa yace "bance ba zanzo ba ina cin Abinci ne lokacin"
"ba tun É—azu aka kaiwa ma'aikatan gidan nan Abinci ba?"
"Aini ban sani ba munfita tare da ke, kuma ni ba'a taɓa Abinci ba"
Tsuke Fuska Sosai Widad tayi tace "Ramlah kiramin larai" Ramlah ta juya ta tafi kiran larai, Widad ta kalli Yusuf a wulaƙance tace
"me kake nufi da in baka abu ka ajiyemin kayi tafiyar ka? Me kake nufi da hakan? Harni zan baka abu saboda wulaƙanci da girman kai irin na talaka harni zaka gwadamin halin naku na talakawa na girman kan banza akan abunda baku dashi"
Yusuf ya ɗanyi murmushi yace "ba girman kai bane Madam, bakomai ne yasa na ajiye ba face abunda kika bani yafi ƙarfin talaka kaman ni in saka, duk wanda yaji ƙamshin wannan rantsatsun turarukan to tabbas zan zama abun tuhuma ga al'umma, kiyi hakuri wannan turaren seke"
Wani irin murmushi Widad tayi wanda ita kaÉ—ai tasan ma'anar sa, sannan ta tsuke fuska tace
"Amma fa ka iya rainin wayo sosai, shikenan amma idan na kuma jin tashin wannan banzan turaren a jikin ka kasan sauran"
"Insha Allah bazan sake saka turaren da shugaba ba taso ba"
Ramlah ce ta dawo tareda 'yar aiki larai na biye da ita, jikin larai se tsuma yake tazo gaban Widad ta durƙusa.
"Larai Me yasa ake hana direba na Abinci?"
Larai ta kalli Ramlah a ɗan dirirce sannan ta dawo da kallon ta kan Widad za tayi magana, Widad tace "Idan kikamin ƙarya sena hukunta ki"
"Wallahi ranki ya daÉ—e Hajiya ce tace kar a sake a bashi Abinci, ba a cikin ma'aikatan gidan nan yake ba"
Widad tace "hmmm tunda ita ta siyo ta kawo ko? Ke Ramlah kije ki gayawa mahaifiyarku, ko kare na ajiye a gidan nan ya zama dole a bashi duk abunda yake buƙata tunda lokacin da'ake tara dukiyar gidan nan bada gumin ta aka tara ba, sannan....
Yusuf katseta ta hanyar cewa "Amma uwa É—akina ina ganin idan kika yi haka baki kyau ta ba, ki bari...
"Shut up....., do you think am doing it because of you?, let me tell you something, ba nace a baka Abinci a gidan nan dan komai ba sedan kauce wa hatsarin dake tattare da hakan, karka manta YOU SIGN ON YOUR DEATH CONTRACT ya rage naka kula da rayuwar ka"
Ta miƙe ta nufi part ɗinta cikin takunta na isa.
Jiki a sanyaye Yusuf ya fice yana mamakin waime take nufi da wannan death contract ɗin ne?
**********************
Manyan Mutane maza su uku, zaune a wani ƙaton falo, da ganinsu kasan suna da kuɗi saboda yanayin suturar jikin su, zaune suke suna tattaunawa fuskarsu ɗauke da damuwa
Ɗaya yace "nifa Al'amarin nan ya fara isa ta, tsawon shekaru muna fama akan abu ɗaya, amma abu yaƙi ci yaƙi cinyewa nifa na fara karaya"
"haba Alhaji Haruna, akan me zaka karaya haka? Ai ba gudu ba ja da baya, se burinmu ya cika se mun samu abunda muke nema, abun baƙin cikin yarinyar nan muguwar gaddamammiya ce, wani irin mugun Aƙida ne da ita tamkar tasan abunda muke nema, sam bata da wani mutum data aminta da shi ya shiga jikin ta balle mu samu abunda muke so"
Alhaji Haruna yace "kai bari kawai Alhaji Musa, Yarinya kaman ba jinsin mutane ba, duk na kusa da ita ba wanda bamu bi ba amma bamu samu abunda muke buƙata ba, Kalli yadda shirin mu na jiya ya wargaje.
"Hmmm bari kawai kaga jiya yadda ta wulakanta Jamil a harabar Store ɗin nan, ina zaune a mota na ɗauka zeyi ƙoƙari ta bashi lambar wayarta amma ta fasa wayar ta ƙare masa zagi a gaban mutane"
Alhaji Haruna ya girgiza kai "yanzu meye abunyi ko mu kashe yarinyar nan mu huta mu kama Nasir daula ta ƙarfin tsiya mu samu abun nan"
Alhaji Munir yace "kul Haruna, in baka iya kama ɓarawo ba shi seya kama ka, wannan ai wauta ne, kasan yarinyar nan a gurin sa ta gaji wannan taurin kan, idan muka kashe ta tamkar mun kashe Nasiru Daula ne, kuma kasan akwai hatsari sace shahararren mutum kaman Nasiru a ƙasar nan, dan haka ita yarinyar ya kamata mu ci gaba da farauta "
Alhaji Musa yace " to sace ta zamuyi ko yaya? Duk hanyoyin da ya kamata mubi munbi amma abu ya gagara, idan muka bari ta koma ƙasar waje aikin mu ze kuma komawa baya ne"
"to sace ta zamuyi ko kuwa?"
Alhaji Munir yace "A'a a yanzu ba sace ta ya kamata mu yi ba, zamu ci gaba da bin diddigin ta, kun san sace wannan yarinyar se anyi kyakykyawan shiri"
Alhaji Musa yace "Anya Alhaji Bulama be san komai akan abun nan ba? naga amintaccen Nasiru Daula ne ko zamu gayyato shi cikin mu?"
"Taɓɗijan ashe tamkar mu fita mu
tonawa kanmu asiri ne, kome zamuyi kar mu shigo da bare cikin mu, zamu ci gaba da yin zagon ƙasa ne a sirri har mu samu abunda muke so"
Haka suka ci gaba da tattauna wa a tsakanin su.
**********************
Yusuf na bakin gate ya bada hankalin sa akan wayar sa, Amal ta fito yana ganin ta yai murmushi tace "Sannu da hutawa"
"Yawwa ranki ya daÉ—e ya gidan?"
"lafiya ƙalau, Widad na nemanka"
"to shikenan muje" ya tashi ya bita har part ɗin Widad, suna shiga Widad ta tsira musu ido, ta sauke idon ta akan Amal ta ƙura mata ido ko ƙyaftawa ba tayi, Sum sum Amal ta fita ta basu guri, zuciyar ta ɗauke da zazzafan kishin barin Yusuf daga shi se Widad a ɗaki.
Widad ta ƙare Yusuf kallo kaman bata sanshi ba kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kai, dogon wando ne a jikin ta da vest ko kunya ba taji a irin shigar data keyi Widad tace "zan fita anjima ƙarfe huɗu zanje gurin birthday, ƙarfe huɗu, in kaga dama ka tafi yawon ka"
Ya jinjina mata kai yace
"Insha Allah zan kiyaye lokacin" daga nan ya fice.
Ƙarfe huɗu saura kwata akayi sallar la'asar, Yusuf ya gabatar da sallar la'asar, sannan ya shiga cikin gidan.
Yana zuwa ya tarar da Alhaji Nasir da iyalan gidan, gefen sa ga trolley alamun tafiya zeyi.
Yusuf yace "barka da rana Yallaɓai"
Alhaji Nasir yace "Yawwa Yusuf ya aikin, ya haƙuri da Daughter"?
Murmushi Yusuf yayi yace "ai mune take haƙuri damu, Aiki kuma Alhamdilillah, mungode Allah"
Alhaji Nasir ya jinjina kai yace "tafiya ta kamani zani Paris, se shagwaba take wai bazan tafi ba, Yusuf ga amana ta nan, na bar amanar daughter na a hannun ka, har inje in dawo kar a bari tayi kuka, idan tana buƙatar wani abun akula ayi mata dan Allah"
Widad da sauri ta kalli mahaifin ta sannan ta kalli Yusuf a wulaƙance tace
"Allah ya kiyaye Ina da komai da nake buƙata, dan haka bana buƙatar taimako daga gurin kowa balle talaka kaman direba na"
Gaba É—aya suka É—auke wuta, shi kansa Alhaji beji daÉ—in abunda Widad É—in ta faÉ—a ba.
Yusuf kuwa yai murmushi yace "indai wannan Amanar ce Alhaji na yadda na karɓa, Insha Allah zaka je lafiya ka dawo ka tarar da ita, Allah ya bani ikon kula da ita"
Alhaji Nasir yace "Ai dama nasani duk me sunan Yaya na mutumin kirki ne, ban taɓa ganin Yusuf wanda ba shi da kirki ba, Allah yayi wa Rayuwar ka Albarka"
Yusuf ya amsa da Ameen
Ita kuwa Maman su Ramla tamkar ta haÉ—iye zuciya, wai direba ake bawa amanar 'yar masu gida, tunda ita cinye ta zata yi ai dole a ce direba ya kula da ita, shikenan direba ya kula da ita in yasan wata ai be san wata ba.
Ba ƙaramin haushi take ji yadda Alhaji Nasir ke nuna wa Yusuf kulawa ba.
Yusuf ya É—aukar wa Alhaji Nasir trolley É—in sa suka fito harabar gidan, Nura ya taho jiki na rawa ya buÉ—ewa Alhaji Nasir bayan mota ya shiga.
Ramlah ce ta taho da nufin itama ta shiga motar ayi rakiyar Alhaji Nasir da ita.
Widad ta kalli Ramlah tace "ba gurin ki a motar nan, dan bama buƙatar rakiyar ki" ta kalli Yusuf tace "shiga gaban motar" .
Nura ya tsaya ya kalli Widad ya kalli Yusuf, Yusuf ma saroro yayi yana kallon Widad, Waidad tace
"ba kaji ba? ko sena maimaita"
Yusuf ya buɗe gaban mota ya zauna, yayin da ita da mahaifin ta suka shiga baya suka zauna.
Nura ya ja mota suka tafi, Ramlah ta rasa me zata yi ne, Mummy tace
"yi haƙuri ƙyalesu, in sun san wata basu san wata ba"
Haka ta rarrashi Ramlah suka wuce cikin gida.
Jefi2 Alhaji Nasir da Widad suke hira, yayin da Yusuf da Nura suka yi shiru kowa da abunda yake saƙawa a ransa
Suna cikin tafiyar ne, Alhaji Nasir yace "daughter na dan Allah ina sake roƙon ki, karki watsamin ƙasa a ido, idan fahad ya dawo ku daidaita, ina son ganin ki cikin farin ciki ne daughter bana son irin wannan rayuwar takura kan da kike yi"
Banza tayi da Daddyn, seda aka ja lokaci sannan tace "Daddy na fara tunanin ka dena sona, idan har kana tunanin yi mun aure ne ze sani farinciki, to tabbas zaka sake jefani ne cikin wata damuwar, kafi kowa sanin meye buri na, Aure ze zama tamkar barrier ne a cimma buri na"
"Daughter yanzu abun nan baze wuce a gurin ki ba? Ba zamuyi haƙuri ba mu barwa Allah, ba zamu yadda komai ya faru damu muƙaddari ne daga Allah ba?"
"Daddy bazan taɓa mantawa ba, kuma bazan yafe ba sena cika buri na, kuma ka dena min batun Auren nan bana so, bazan iya zama a ƙarƙashin wani ba inyi masa biyayya ko waye shi, ku ƙyaleni da zancen Auren nan please bana so"
Ta mirror Yusuf yake ganin Widad yadda Hawaye ya wanke mata fuska, ta rintse ido tana magana cikin kuka.
Alhaji Nasir ya rungume ta a jikin, sa cikin sigar rarrashi yace
"Am sorry my dear, i don't mean to hurt you, nasan tamkar na fama miki wani ciwo ne dake cin zuciyar ki, amma kiyi haƙuri ina ƙoƙarin wanke miki wannan damuwar ne, ina son komai ya wuce kema ki fuskanci rayuwar ki"
"No Daddy i can't, ta yaya zan manta da abunda ya faru, Daddy bazan ƙara yadda da kowa ba, yin aure na tamkar ƙara kusanto da maƙiya jikin mune, ni bazan yadda da kowa ba balle a sake cutar dani a karo na biyu ba, Daddy i repeat my self bana son kowa a kusa dani, bana so" sosai kukan nata yake ƙara ƙarfi harda sheshsheƙa.
"yi haƙuri daughter na, Amma ina sa ran Insha Allah zakiyi alfahari da auren fahad, yana da kirki sosai ɗan uwanki ne, tunda jinin Alhaji Bulama ne, bana tunanin akwai wata cutarwa da Alhaji Bulama ze mana"
Haka nan Yusuf yaji ta bashi tausayi, duk abunda zesa Widad ta sauke wannan izzarta ta, ta dinga irin wannan kukan lallai ba abune ƙarami ba.
Har suka je airport Widad kuka take, har kyawawan idanuwan ta sunyi ja, haka suka yi Sallama da mahaifin ta.
Alhaji Nasir ya dubi Yusuf yace "Yaya na a kulamin da amana ta"
A fusace Widad tace "Daddy karka ƙara cewa ka bar amana ta a hannun wani , ka barni a hannun Allah zaka je ka dawo ka tarar dani lafiya Insha Allah, amma zuwa yanzu yaci ace kayi darasin da bazaka ƙara bawa mutum yadda da Amana ba, narasa me yasa Daddy ka kasa fahimta ta"
Alhaji Nasir yai murmushi ya riƙo hannayen ta yai mata raɗa a kunnen ta, sannan a fili yace "ina da surprise a gare ki idan na dawo, ku koma karku yi dare my lovely"
Haka Widad suka juya zuwa mota, yanzu ma Nura ne ke jan Motar
Widad tace "yi parking anan" Nura ya tsaida motar, tace masa
"gaya masa inda farm house yake"
Nura ya gane abunda take nufi, dan haka yaiwa Yusuf kwatancen inda tace.
Daga nan ta ɗaga idon ta wanda suka jiƙe da hawaye tacewa Nura
"fita ka bar motar nan ka hau ta haya ka koma gida, Kaikuma ka karɓi tuƙin mu tafi"
Nura yace "Amma ranki ya daÉ—e motar Alhaji ce kuma....
"motar Alhaji ta ubanka ce? Ko ta Ubana?" ta jefo masa tambayar
"A'a amma ban fito da kuÉ—i ba"
"Idan ka bari na sake magana, zan ɓata maka rai fiye da tunanin ka, fita daga motar nan nace, idan ba tare muka haɗa kuɗi muka siya ba"
Haka Nura ya fice daga motar, Yusuf ya karɓi tuƙin.
Yusuf ya dinga bin kwatancen da Nura yayi masa, har sukaje gidan gonar Widad bata dena kuka ba, Sam Yusuf yaji beji daÉ—in yadda take kukan ba, gashi ita ba'a iya mata balle ya rarrashe ta
Wani irin tangamemen gida ne har yaso yafi gidan da su Widad ke Rayuwa a ciki girma, Yusuf ya fara tunanin anya wannan gidan gona ne? Horn Yayi aka buɗe masa wani jibgegen gate me matuƙar nauyi ya shiga da Motar cikin gidan.
Ma'aikatan gidan ne suka dinga tahowa cikin matuƙar sauri inda motar su Widad take, Kallon gurin Yusuf yake yi, dabbobi kala kala a ɓangarori daban daban wanda idon sa yake iya gani, gefe kuma gida ne sosai ginanne a ciki, cikin zafin Nama ta fito daga motar tana ta Hawaye, cikin girmamawa ma'aikatan ke zubewa suna gaishe ta, babu wanda ya samu Arziƙin kallo balle ta kula shi.
Cikin matuƙar sauri ta nufi ɓangaren da yake gida ne a cikin gurin, Yusuf ya bita shima cikin sauri, binsu ma'aikatan suka yi da kallo mussman Yusuf, Wani irin murgujejen kare ne fari da baƙi a jikin sa ya nufo inda Widad take yana wani irin gurnani gami da sufa.
Durƙusawa tayi ƙasa Karen yazo yana zagaye Widad yana shanshana jikin ta, shafa gashin karen tayi tana kuka tace "I miss you Miz"
Karen ya kwantar da kansa a jikin Widad yana zaro harshe, ko tsoron sa bataji balle ƙyama.
Haka karen yai lamo a jikin ta tareda ƙurawa Yusuf ido, ita kuma tana cigaba da kuka, can kuma ta shafa kan karen tace
"Excuse me Miz, I will see you later"
Ta miƙe zata yi gaba Yusuf ya bita, Karen nan ya bishi yana masa wani irin haushi da gurnani yana zubar da yawu, Yusuf a ransa yace
"Wane irin jarababben kare ne wannan se kace zaki?"
Widad ta juyo ta kalli karen tace
"don't Worry, I trust him Miz"
Daga nan ta miƙe ta ci gaba da tafiya, Aikuwa tana faɗar hakan karen ya dena bin Yusuf.
Sunyi doguwar tafiya sosai a cikin gidan, dabbobi daban daban wasu daka gansu kasan sun sha banban da kalar namu na Nigeria.
Gida ne sosai a ciki ginanne me matukar kyau, ya tsaru sosai sedai da alama babu mutane a ciki.
Wani ɗaki Widad ta nufa ya bita, suna shiga ɗakin Widad ta ƙara sautin Kukan ta, wani katafaren gado ta nufa ta zube a gaban gadon ta ci gaba da rera kukan ta, daga jin yadda take fidda sautin kukan kasan kuka ne me taɓa zuciya.
Yusuf se binta yake da ido cikin tausayawa halin da take ciki, amma bashi da damar yayi mata magana ko ya rarrashe ta dan bata son shisshigi, yanzu zata masa rashin mutunci.
Ba tare da ta kalli Yusuf ba, a hankali tace "Excuse me please" Yusuf ya jinjina kai ya fice ya tsaya a wajen É—akin, kusan mintuna talatin yana tsaye yana jiran ta.
Fitowa tayi É—auke da wata shigar ta daban, kamar ba ita ba, shigar jikin ta ba kace musulma ce ba.
Kallon ta Yusuf ya tsaya yanayi duk wani ilahirin surar jikin ta seda ta bayyana, Farar fatar ta se É—aukar ido take.
"let's go" shine abunda ta cewa Yusuf, haka yabi bayan ta zuwa inda motar su take, nan ma ma'aikatan ne suka kuma biyo ta suna mata Fatan Alkhairi, gaban motar ta buÉ—e ta É—ebo kuÉ—i bandir bandir ta basu, ta shige motar Yusuf yaja motar.
Wani ƙaramin kati ta miƙawa Yusuf, kwatancen inda gurin partyn yake ne, shi sam ya manta tace ze kai ta gurin birthday ne, ga yamma tayi sosai, se dai bashi da ikon magana haka ya bi kwatancen.
"Hello ranka ya daÉ—e, bayan tsawon shekaru yaufa tazo gidan gona"
"Me tazo tayi?"
"Nima ban sani ba Yallaɓai"
"ta fita da wani abu daga gidan ne?"
"A'a bata fita da komai ba, kaya kawai ta canza sannan ita da wani matashi suka zo yana tuƙota"
"Direban tane kokuma waye?"
"Gaskiya ina tunanin ba direban tane ba kawai, dan a biye yake da ita, har cikin gida duk inda ta shiga yana binta"
"Good, ina so aje anemo min waye wannan matashin, me yake yi a tare da ita, Akwai yuwuwar ze mana Amfani"
"shikenan Oga an gama"
*******************
Koda sukaje gurin birthday ɗin a harabar wani katafaren gida, da ganin yaran da suke shiga suna fita a harabar gurin kasan sun jiƙu da kuɗi, fitowa Widad tayi daga motar, Yusuf ma ya fito ya kulle motar.
Wata 'yar siriryar Murya suka ji tace "hey beb you are here?"
Da sauri Widad ta juya suka rungume juna da matashiyar Yarinyar da zata yi sa' ar Widad, suna murmushi
Widad tace "Happy born day baby"
"Thank you sweetheart"
Wani matashi ne ya biyo bayan Yarinyar ya kalle ta yace
"Sweetheart who is this beb?"
"She's My best friend in UK, we take part in the same school, She's Alhaji Nasir daula's daughter"
Ta kalli Widad tace "Baby wannan cousin É—ina ne"
Matashin yai murmushi yace "wow Nice to meet you baby"
Ya miƙa mata hannu da nufin su gaisa, Amma cikin zafin nama Yusuf ya saka hannun sa a na Matashin wanda hakan ya hana Widad gaisawa da Matashin.
Kallon sa sukayi gaba É—aya da mamaki, Widad kam mazewa tayi kamar ba taga Abunda Yusuf yayi ba, suka nufi gurin da ake Shagalin birthday É—in.
Yusuf bin bayan su yayi, Nurat ta kalli Widad tace
"Beb waye wannan ne wai?"
"Why are you asking?" Widad ta tambaye ta
"Abunne ya bani mamaki, nasan baki da brother, Amma me yasa ze miki haka? Lallai kinyi sanyi ko kin fara sauka daga kan AƘIDAR taki ne?"
Widad ta girgiza kai tace "babu abunda ya canza, sedai kin san komai na Widad a lissafe yake"
Jinjina kai Nurat tayi tace
"Wannan ma cikin lissafin ne kenan?"
Widad tace "Maybe"
Nurat tayi murmushi tace "You are wonder lady"
Sukayi Murmushi suka nufi kan stage É—in, Widad na Hawa kan stage É—in tare da Nurat aka É—auki tafi ana shewa.
Cake Nurat ta yanka, aka dinga tafi ana ihu, tare da waƙoƙin birthday.
Kyautar Mota Widad tayi wa Nurat, a matsayin birthday gift, gurin ya hagirtse da shewa anawa Widad kirari, suka shiga cashewa a stage din nan kaman ba yaran musulmi ba.
Kiran Yusuf akayi a waya, ya fita waje domin amsa Wayar saboda hayaniyar da take tashi a gurin.
Yana É—aga wayar yasa a kunnen sa tare da yin Sallama
"Idan har kana son tsira da Rayuwar ka, to ka tafi ka bar gurin nan a yanzu, in ba haka ba ko kai ko UwarÉ—akin naka É—aya ze iya rasa ransa"
SHARE PLEASE ðŸ™ðŸ™ðŸ™
Ayshercool
07063065680
_*AƘIDA TA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
_Haƙƙin Mallaka ⚠: Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode
_
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
             PART1
                Page 7
Da sauri Yusuf ya koma gurin partyn ba tare da fargabar komai ba ya shiga kutsawa yana neman Widad, amma babu ita babu alamar ta a gurin, can ya hango Nurat tana ƙoƙarin fita, seda ya bari ta fito daga gurin party, sannan yabi bayan ta a guje ya sha gaban ta, seda ta tsorata da ganin sa ta ɗan tsaya ta kalle shi tace "Are you ok?"
"Ina Widad?" ya jefo mata tambayar
"ban sani ba na barta akan stage tana rawa" tai maganar cikin wata irin gurɓatacciyar hausa.
Subhanallah shine abunda Yusuf ya furta, yai gaba yana sake duba gurin.
ba zato ba tsammani ya shammaci Nur ya fizgota ya shiga cikin duhuwar flowers da ita, yasa hannu ya shaƙeta, ya kalle ta a hasale kamar wani mahaukacin zaki yace
"Ko ki gayamin gaskiya ko kuma zan fita dake daga gurin nan, zan riƙe ki a matsayin garkuwa harse Naga Widad, idan kuwa rayuwar Widad ta salwanta taki ma ta salwanta, ki gayamin ina take?"
Yai maganar cikin ɗaga murya tare da shaƙe Nurat.
"Dan Allah, please don't kill me I will tell you, please secure my life"
"Your life will be secured if you tell me the truth" ya faÉ—a yana zare mata ido
Cikin kokawa da numfashi tace "Ok zan gaya maka, Dad ne yasa aka busa mata wani abu, yanzu tana harabar gurin nan a ɓoye, wasu zasu zo su ɗauke ta, idan baka hanzarta ba komai ze iya faruwa"
"Meyasa Mahaifinki yake ƙoƙarin sace ta?"
Cikin kuka tace "I sure to the Almighty ban sani ba, trust me"
Tasa Nurat yayi a gaba ta nuna masa ƙarƙashin bishiyar da aka ajiye Widad, tana kwance helplessly a ƙasa, unconscious kaman babu rai a jikin ta, ga jakar ta a gefen ta.
Ya waiga ba kowa a gurin, Yasa hannu ya sunkuce ta ya tafi da ita motar su da sauri, ya buÉ—e bayan motar ya kwantar da ita, yaja motar da gudun tsiya ya bar gurin.
Da gudu Nurat ta koma cikin gidan su tana haki, da yake hall É—in party a cikin gidansu yake, É—akin ta ta tafi kai tsaye ta shige banÉ—aki tana sauke numfashi, ta wanke fuskarta, ta buÉ—e fridge ta sha ruwa me sanyin gaske, sannan É—akko wayarta ta kira layin mahaifinta.
Seda ta kusa tsinkewa sannan ya É—aga yace
"Yaya i hope everything is going according to how it's planned?"
Cikin rawar baki tace "No Daddy something is going wrong"
Cikin sauri yace "meya faru?"
Cikin Rawar Murya Nurat tace "Daddy basu ƙaraso da wuri ba, nayi abunda kace Amma..
" Amma me? Ki gayamin menene? "
" Daddy ita da wani tazo, nayi abunda kace, but someone intimidate me, yace in ban faÉ—i inda take ba ze kashe ni"
"Waye shi?" ya faÉ—a a fusace
"Ban sani ba Daddy, Amma tare suka zo"
"Wace irin wawuya ce ke haka? Kinsan lokacin dana É—auka ina wannan shirin? Idan wasu suka rigani mallakar Abun nan mun kaÉ—e"
"Daddy ba laifi na bane, laifin wanda ka turo su É—auke ta nefa"
"Shut up, kin ɓata min shiri kina gayamin maganar banza"
"Am Sorry Dad is not my fault, but....
" Common Keep quiet "Â ya faÉ—a a Hasale, tare da katse wayar yana tsaki, tabbas ba dan wawancin nan 'yar cikin sa ce ta aikata masa ba da ba abunda ze hana yasa a Kashe ta.
A fili Yace
"dole in toshe duk wata kafa da zesa su Alhaji Haruna su san nayi yunƙurin sace Yarinyar nan ni kaɗai, kuma dole in gano wane yaron ne suka je gurin tare"
Yusuf kam gudu yake bana wasa ba, ya dinga kauce wa dukkanin hanyoyin da zesa ya haɗu da cunkoson ababen hawa, ko kuma jam'ian tsaro, be sassauta da gudu ba seda yaga ya shigo layin su Widad, a hankali ya ƙara sa tuƙin yana zuwa ƙofar gate ɗin ya saki wani irin horn me gigitarwa, duk a ƙoƙarin sa na ganin ya kai Widad gida lafiya.
A gigice Isa ya buɗe ƙofar dake jikin tangamemen Gate ɗin ya leƙo ya fara masifa "haba Yusufa, wannan wani irin horn ne kaman me shirin sanar da tashin duniya"
Cikin harzuƙa Yusuf yace "Open the Gate"
Dukda Isa ba turanci yake ji ba amma ya gane Yusuf na magana ne akan ya buɗe masa ƙofa, Cikin Sauri Isa ya buɗe masa Gate Yusuf ya shiga da motar yayi parking, ya sakko da sauri daga cikin Motar ya buɗe inda ya Kwantar da Widad, har yanzu bata hayyacin ta, Yasa hannu ya ɗakko ta tareda Jakar ta ya nufi Cikin gidan da ita, Isa ya biyo bayan sa da Sauri yana ƙasa da murya cike da gulma yake Faɗin
"Yusufa meyasami Uwar É—akin naka kuma? Kodai Shaye2 tayi ne? Naganta kamar a buge"
Cikin tsawa Yusuf yace "Idan ka ƙara taku ɗaya daga inda kake zan ɓata maka rai"
Gaba É—aya Isa mamaki ya kama shi yadda Yusuf É—in ke wani magana cikin Izza da isa.
Babu kowa a babban Falon dan haka Kai tsaye part É—in ta ya nufa da ita, Ya kwantar da ita akan gadon ta.
Yasa hannu a aljihunsa, ya É—au wayarsa ya kira Abbas, bugu É—aya ya É—auka yace
"Kai ya haka? Zaka kirani a wannan daren?"
"Kai akwai matsala fa"
"Matsalar meke nan?"
"Widad na kai gurin birthday akayi barazanar za'a kasheni idan ban bar gurin ba, ina komawa na neme ta na rasa, da ƙyar na ganta, yanzu haka na dawo da ita gida Amma bata san inda kanta yake ba, I thinks they Use sedative substance on her, nayi niyyar in tsaya da ita a Asibiti Amma naga hakan hatsari ne babba"
Abbas ya numfasa yace "Gaskiya kam zata farfaɗo Insha Allah, gobe in Allah ya kaimu ka shigo Office kawai za muyi magana"
"Shikenan Allah ya kaimu" suka yi Sallama, ya maida Wayar Aljihunsa ya kalli Widad da take ta bacci bata san meke faruwa ba se sauke numfashi take, Yusuf ya É—auki bargon dake gefen ta ya rufe ta dashi saboda yanayin Sanyi, wayarta ce keta ringing a Jakarta ya buÉ—e Jakar ya É—akko wayar ya kashe ta gaba É—aya, Sannan ya kama hanyar fita.
Yusuf ya fito ya nufi hanyar fita, yaci karo da Ramlah a babban falo, share ta yayi ze wuce.
"Daga ina kuke a daren nan? Me kake a ɗakin Widad a wannan lokacin?" muryar Matar gidan ce, dake tsaye a ƙafar bene.
Yusuf ya juyo ya kalle ta sannan yace "Na kaita unguwa ne"
"Me kake a É—akin ta a wannan lokacin? Bata da lafiya ne, na kaita É—akin ta ne"
"Ka kaita É—akin ta kai a wa?" Ramla ta tambaye shi.
"Ni ba a kowa ba, ni a É—an uwan ta musulmi, kuma ma'aikacinta"
"Kai shashasha rufemin baki" Hajiya Halima ta katse shi cikin tsawa.
"Naga kanka yana rawa, to bari in tuna maka kai ba kowa bane face matsiyacin talaka, ka dena jin kanka kamar wani me iko dan kaga mai gidan nan yana wani baka girma na musamman kai É—in ba kowa bane ba"
Amal da take jiyo hayaniya ta fito daga É—akin ta, tana zuwa ta tarar da mahaifiyar ta ta saka Yusuf a gaba tana zagin sa
"Haba Mummy, me Yusuf yayi miki kike masa wannan cin mutunci haka?"
Ramla tace "An zage shi ɗin, meye alaƙar ki dashi? Ɗan uban waye shi da ze dinga wani jin kansa, dan yaga ya samu gindin zama, saboda tsabar cin fuska akan wannan banzan waccan mara mutuncin ta dizgani"
Yusuf ya É—an murmusa yace
"Nasani niba kowa bane, talaka ne ni gaba da baya, dan haka ku kwantar da hankalin ku,kuma ni bana sawa kaina ni wani ne" yana gama faÉ—in haka ya juya ya fice.
Amal tace "Mummy koma menene laifin Widad ne, ni banga abunda Yusuf yayi ba"
Hajiya Halima cikin tsawa tace "dalla rufemin baki banza, naga zaƙewar ki kema tana yawa akan yaron nan, ki shiga hankalin ki tunda wuri, ni sam yaron nan be minba, ya fiye kalar munafukai"
Ramla tai caraf tace "wallahi kuwa Mummy, ni kaina ban yadda dashi ba, Ina jiran sakamakon binciken da kika sa ayi a kansa ne"
Amal tace "Mummy koma menene Yusuf bare ne aiki ne ya kawo shi gidan nan, bekamata a saka shi a wannan sabgar ba"
"Amal kenan ke har yanzu yarinya ce, baki san inda rayuwa tasa gaba ba, kashedina dake shine, tun wuri ki fita daga sabgar yaron nan, dan muddin na gano wani abu saɓanin abunda nayi zato a tattare dashi ba abunda ze hana insa ayi masa abunda ya dace da shi"
"Amma mum....
"Ke rufemin baki, shashasha kawai"
Mummy tayi maganar tare da juyawa zuwa ɓangaren ta, Ramla ma tabi bayan ta suka bar Amal a falon tsaye.
Yusuf na fitowa, Nura ya biyo shi yace
"A'a kaga ɗan gatan 'yar masu gida, gaskiya Yusuf ka ciri tuta, naga' yar masu gida tana yi da kai, ƙiri Ƙiri ta koreni kuka tafi unguwa, naga duk inda zaka tare kuke tafiya"
Kafin Yusuf ya bashi amsa, Isa mai gadi ma ya nufosu yana cewa
"Nikam Malam Yusuf baka gayamin meyasami Uwar ɗakin ka ba, nifa abun ya bani mamaki, iya sanina dai bata shaye2, sedai taɓun hankali amma meyafaru da ita haka?"
Kallon su yayi É—aya bayan É—aya yana karantar tsantsar munafunci da son jin gulma a fuskokin su, sharesu yayi bece musu komai ba yai gaba abunsa ya fice ya bar gidan.
Yusuf na fita, Nura yace
"Ji shi se kace ɗan uban wani, muna masa magana amma yayi mana banza, da Alhaji ne uban sa bansan wulaƙancin da ze ba"
Isa yace "Bar mara mutunci, ji yadda muna masa magana ya share mu, Anya Nura mutumin nan ba Asiri yayi wa me gidan nan ba?"
"Ni zance maka Asiri yayi masa hadda 'yar sa ma, kana gani É—azu ta hana Ramla binsu saboda shi, da muka dawo daga filin jirgi se cewa tayi ni in sauka in hau motar haya in tafi gida, shi kuma ya kaita unguwa"
Isa ya jinjina kai yace "Kana gani duk jin kai da izzar ta, duk Aƙidar ta ta rashin yadda da mutane Amma duk inda zata tare dashi suke tafiya, dudu yaushe yazo gidan nan? Ko wata ɗaya be cika ba ya samu wannan gindin zaman, mu kuwa shekara nawa muna aiki a gidan nan? Ba abunda yake haɗamu da ita se cin mutunci da wulaƙanci "
Nura yace "to ai magana ce a buÉ—e, Allah kaÉ—ai yasan abunda suke yi"
Isa yace "kuma fa hakane zancen ka Nura, taɓ aikuwa zamu ƙara saka ido sosai, zamuyi maganin wannan gani-ganin da yake mana"
Haka suka zauna suka cigaba da gulma, suna muzanta Yusuf da miyagun kalamai.
Yusuf kam kansa ya kulle Sosai, daya koma gida ma kasa bacci yayi, yana ta nazari akan abubuwa da dama yana son gano bakin zaren amma ya rasa ta ina ze fara, gaba ɗaya Al'amuran a cukurkuɗe suke, me zesa Baban Nurat yunƙurin sace Widad? Waye mahaifin Nurat? Dole Akwai dalilin da yasa Widad take da wannan AƘIDA na ƙyamar talaka da nesanta kanta da mutane, yanayin Abubuwan da take yi wasu lokutan yasa Yusuf ya fara gazgata cewar tana da taɓin ƙwaƙwalwa, tunani ya haɗu ya cunkushe massarafar gangar jikinsa wato ƙwaƙwalwarsa, ba shiri ya tsagaita tunanin ya kwanta da ƙudurin dole yaje Office da safe, akwai buƙatar yaga Abbas.
A hankali ta motsa daga nannauyan Baccin da take, ji tayi kanta kamar an ɗora mata wani nannauyan dutse, gaba ɗaya gaɓoɓinta sun mata nauyi, a hankali ta buɗe idon ta ta ƙarewa ɗakin nata kallo, ta mayar da idanunta ta lumshe na wasu daƙiƙu sannan ta sake buɗe su, a hankali taja jikin ta ta miƙe zaune, kallon jikin ta tayi tare da ƙoƙarin son tuna abunda ya faru, sosai take takura ƙwaƙwalwarta don ta tuna mata abunda ya faru, Amma fafur ta kasa tuna komai, dafe kanta tayi wanda taji yana sara mata, ta miƙe jiri na kwasar ta ta tafi banɗaki.
Da sassafe ko karyawa Yusuf beyi ba ya fito ze fita. Umma dake kitchen tana ƙoƙarin haɗa Abinci ta leƙo tace
"Yusuf me zan gani haka? Ba zaka tsaya ka karya bane?"
Yusuf yace "Umma sauri nake ne, bana son in makara akwai aikin da nake son yi"
"Yusuf nifa gaskiya wannan aikin da kake a gidan masu kuɗin nan ba sonsa nake ba, nasan halin masu kuɗi da rashin mutunci da wulaƙanta talaka, nidai gaskiya su canza maka wannan aikin su baka wani, danni gaskiya bana son kaje inda za'a wulaƙanta min kai"
Kallon Umman sa yayi, ya ɗanyi murmushi ya tako gaban ta ya riƙe hannayen ta yace
"Kyakkyawar Uwa, Uwa da babu irin ta, ina Alfahari dake Umma na, yadda kike kula dani Allah ya kulamin dake ko bayan raina, ki kwantar da hankalin ki, basa wulaƙanta ni, kuma yanayin aiki ne yazo a haka, dana Kamm zan koma Office, idan kuma kince ba kyason aikin se in haƙura gaba ɗaya"
Badan ranta yaso ba tace "Yusuf ba aikin ne bana so ba, ni wannan aikin da suka baka ne bana so, yaushe rabon da muci Abinci tare, in ka fita tun safe se dare, Amma shikenan dai, Allah yayi maka Albarka, Allah ya sadaka da Alkhairi a duk inda kake"
"Ameen Umma na, bari in sauri sena dawo"
"Allah ya kiyaye hanya"
Ya amsa da "Ameen" ya fice.
Kai tsaye headquarters su ta jam'ian tsaro na farin kaya ya tafi.
Kasancewar Yusuf mutumin kirki yasa tun daga gate masu gadi suke gaida shi, ya tsaya suka gama gaisawa sannan ya shige ciki.
Ofishin sa ya nufa kai tsaye, yana zuwa ya tarar da shi tsaf ana shiga a gyara masa dukda baya nan, Na'ura me ƙwaƙwalwarsa ya ɗakko ya kunna, ya ɗan jira kaɗan sannan ya fara daddanawa.
Gaba ɗaya ya nutsu sosai hankalinsa kacokan yana kan Computer, da gani kasan ƙoƙarin gano wani abu yake me mahimmanci.
Sallamar da'akayi a office ɗin ne yasa shi ɗagowa, Sakina ce sanye da suit na aiki kamar yadda ta saba, fuskar ta ɗauke da murmushi ta ƙaraso tana wani fari da ido, Sam Yusuf baya ƙaunar mace mara kamun kai, shiyasa sam Sakina bata burgeshi.
Kujera taja ta zauna, ta kalle shi tace "wata sabon gani, aiki ya ɓoye mana kai gaba ɗaya haka, ba'a jin ɗuriyar ka ko a waya, na kira ka harna gaji baka ɗagawa"
Yusuf "Aikine ya É—anmin yawa shiyasa, Ya aikin?"
Cikin iyayi tace "Alhamdilillah, Fatan dai kana lafiya?"
Cike da basarwa yace "Lafiya ƙalau"
Ya cigaba da latsa computer sa.
"Kwana biyu da baka zuwa duk gurin nan ba daÉ—i, nayi farincikin zuwan ka sosai"
Bece mata komai ba ya ɗakko wayarsa ya ɗan daddana ya kanga a kunnen sa, ya ɗanyi shiru na wasu daƙiƙu sannan yace
"Ya Abbas ka shigo ne?"
Ya sake yin shiru sannan yaceÂ
"Ok nima na shigo yau akwai buƙatar in ganka, bari inzo office ɗin naka"
Yana gama wayar ya miƙe ya fice ya bar Sakina a gurin, ba tare da yace mata komai ba.
Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tokarewa Sakina zuciya, tabi bayan sa da kallo tare da yin ƙwafa.
Yana fita ya nufi Office ɗin Abbas, yaje ya tarar da shi yana karin kumallo, ya zauna suka gaisa, Abbas ya zubawa Yusuf shayi ya miƙa masa sannan yace "Mutumin ya? Yau ka samu chance ɗin ɓullowa kenan? Meye labari ne?"
Yusuf yace "labari kam akwai shi Abbas, nifa gaba ɗaya a rikice nake wallahi, gaba ɗaya na rasa bakin zaren"
"Take it easy man, bi komai a sannu, me ake ciki?"
Nan Yusuf ya warware masa irin abubuwan da suka faru har zuwa ga yunƙurin sace Widad da'akayi jiya.
Shiru Abbas yayi yace "Lallai lamarin akwai rikitarwa, Mahaifin Nurat ze shiga cikin suspects ɗinmu, yanzu abunda za'ayi ka bani Adress ɗin gidan, zamu je muyi bincike, semun fara gano waye ma mahaifin Nurat ɗin"
Shikenan zan turomaka Complete Adress É—in ta Email É—inka. Suka zauna suka cigaba da tattaunawa.
Wayar Yusuf ce ta fara ringing ya ɗakko ya duba, lambar Isa megadi ce a akan allon wayar tasa, ya ɗaga ya kara a kunnen sa, suka gaisa Isa yace masa "Ana neman ka"
"Shikenan gani nan zuwa"
Yusuf ya kalli Abbas yace "Abbas bari in canza kaya, waccan rigimammiyar tana nemana yau nasan zan sha tijara, dan titsiyeni za tayi tace sena gayamata meyafaru"
Dariya Abbas yayi yace "Ina jinjina maka Yusuf, yadda kake iya aiki da wannan Yarinyar mara alƙibla"
"to ya zanyi tunda kun takura kunce se nayi, dole in kwantar da kai inyi haƙuri da halin ta, Amma kasan wani abu Abbas?"
"A'a seka faÉ—a"
"Ni yanzu gaba ɗaya tausayi take bani, gaba ɗaya rayuwar ta ba irin yadda kowa ke gudanar da rayuwar sa take yi ba, duk yadda zan kwatanta naka ba zaka gane ba, ina kyauta ta zaton akwai wani pain a zuciyar ta, da yake ƙara assasa condition ɗin da take ciki "
"Hmm Yusuf kenan ba wani pain, kawai iskanci ne na yaran masu kuÉ—i, ta taka wanda take so tayi rashin mutunci saboda tana da masu gidan rana"
Yusuf yace "Haba Abbas, su talakawan me suka yi take musu haka? Wai waya gaya maka talakawa kawai take wa haka? Hmm ni nasan abunda nake gani kawai, ba iya Wulaƙanta mutane ba, Akwai wani ɓoyayyen abu da yake damun ta, ina jin tausayinta sosai"
Abbas ya ƙyalƙyale da dariya yace "Kai mutumina, ko dai ka koma ruwa ne?"
"Na koma ruwa kamar Yaya?"
"To naji kace kana tausayinta, na sani ko babbar magana zaka janyo mana"
Shiru Yusuf ya É—anyi jiki a sanyaye ya kalli Abbas yace
"Abbas ai na rufe wannan babin har Abada, sedai wani ikon na Allah, just recently ka manta abunda ya faru dani ne? Ina ni ina Widad, as i told you before i give up gaskiya babu yarinyar da zan ƙara cewa ina so, zanyi haƙuri da ƙaddara ta, in zauna Yadda Allah ya ajiye ni, ni yanzu bari in tafi kar in ƙarawa kaina laifi, dukda yanzu ma nasan laifi na riga nayi shi, zan sha tijara a gurin Widad" yai maganar tare da miƙewa ya fice.
Abbas yayi shiru yabi bayan Yusuf da kallo, he's very gentle and innocent, abubuwa da yawa marasa daÉ—i sun faru da Yusuf, gashi shi kullum zuciyar sa a wanke take, baya nufin cutar da kowa.
A fili Abbas yace "Anya kuwa nayi adalci idan aka haɗa kai dani, aka cutar da Yusuf, Kai Amma kuma Alherin da zan samu a wannan sabgar ya isa in ajiye wannan wahalallen aikin in more rayuwa ta"
Yusuf ya canza kaya ya tafi gidan su Widad, ya tsaya suka gaisa da ma'aikatan gidan sannan ya nufi cikin gidan, babu wanda yake da wannan damar ta shiga cikin gidan kai tsaye, ko ba Aiken sa akayi ba se Yusuf, shi Yusuf be san da wannan dokar ba ma sam, kai tsaye ya shiga Babban falon da yake shine mahaÉ—ar iyalan gidan.
Ya shiga da sallama a bakin sa, ya tarar da Amal a zaune tana kallon zee world, tana ganin sa tayi murmushi tace
"Sannu da zuwa, yau ka makara fa"
Murmushi yayi yace "Allah ya bada haƙuri, Madam ta tashi ne?"
Amal ta kwaɓe baki tace "waya san mata, ka zauna mana ka tsaya a tsaye"
"karki damu nidai ace mata nazo"
"Ni ban zanjeba seka zauna"
Yusuf ya zauna a ƙasan carfet, Amal ta ɓata fuska tace "ya zaka zauna a ƙasa kuma, haba Yusuf dan Allah ka zauna"
Haka Amal ta uzzura masa seda ya zauna akan kujera, ta miƙe tsaye tace
"bari in kawo maka ruwa, kafin ta fito bana so inje ta Wulaƙanta ni, idan ta ga dama zata fito da kanta" tana gama faɗin haka ta miƙe ta shiga wani ɓangaren.
Yusuf na nan zaune, ya É—akko wayarsa yana É—an daddanawa, sega Nura direba ya shigo da wata babbar jaka a hannun sa, da alama Aiken sa akayi yana ganin Yusuf a zaune akan kujera yayi turus yana kallon Yusuf.
Yusuf ya É—aga kai ya dube shi yace
"ya dai Nura? Naga ka tsaya kana kallo na kamar baka sanni ba"
Kafin Nura yayi magana, sega Ramla da mahaifiyar ta sun fito, idon Ramla ya sauka akan Yusuf dake zaune akan kujera, buÉ—e baki tayi tace
"iyeee samun guri, ɗan kuturu da gaɗa cikin Rama, wato isarka da ƙasaitar taka harta kai ka dinga zama akan kujera sannu fa"
Rai a É“ace Mummy taceÂ
"Kai ubanwa ya baka izinin shigowa falon nan harka zauna akan kujera, gidan ubanka ne kona uwarka da zaka shigo min falo ka zauna akan kujera, kai na fuskanci kanka na rawa fa"
Amal ce ta fito da ruwa da cup a hannun ta, ta Æ™araso falon taceÂ
"Haba Mummy dan Allah kiyi haƙuri, wallahi ni nace ya zauna"
Yusuf kam shiru yayi bece komai ba, zama akaan kujera kawai yaja masa zagi da cin mutunci.
"dalla rufe min baki, se nayi maganin yaron nan, saboda jin kansa yake kamar É—an uban wani, matsiyacin banza É—an talaka, dama haka kuke baku iya samun guri ba, kana wani sumi sumi da kai mara mutunci, dama gaba É—aya siffofifinka na munafukai ne bari Alhajin ya dawo, sena sa anyi maganin ka, bazaka tashi ba kana jina ina magana "
Gaba ɗaya ran Yusuf ya gama ɓaci, kujera kawai wannan akanta ake masa wannan cin zarafin.
A hankali ya yunƙura ze tashi rai a ɓace, cikin tsawa da rashin mutunci Ramla tace
"ba magana ake maka ba ba zaka tashi ba, banza kawai É—an talakawa, an kusa korarka kowama ya huta, dalla tashi sakarai"
"baze tashi ba, Kujerar ba wani ya kawo ta ya ajiye ba se mamallakin gidan, dan haka babu wanda yake da ikon cin zarafi ko korara wanda ni yakewa aiki a gidan nan, baku kuka É—auke shi aiki ba, Kuma duk wanda yake tunanin ze kori wanda na É—auka aiki sedai ya bar gidan nan tunda mutum ba gidan nasa uban bane"
Widad ce tsaye sanye da gajeren wando, da vest a jikin ta gashin kanta a kwance a kafaÉ—arta kamar yadda ta saba shigar ta, cike da isa da nuna tsantsar iko tayi maganar.
Ramla ta harzuƙa za tayiwa Widad rashin mutunci Amma Mummy ta hana ta.
Widad tace "ki ƙyaleta ta faɗi abunda take so mana, keda ita kun sani banbancin ku da masu gadi da direbobin nan kaɗan ne ai, dan haka ku tsaya iya matsayin ku, kar wanda ya ƙara shiga hurumi na da wanda yakemin aiki, wannan ya zama kashe dina da gargaɗi na na ƙarshe a gareku, babu ruwan ku da ma'aikata na, wallahi duk wanda ya kuma karyamin doka zanyi ba dai dai ba, na gaya muku"
Wani ƙululun baƙin cikine ya ƙule zukatan su, a gaban masu aiki tayi musu wannan cin zarafin da wulaƙanci, saboda wannan sakaran talakan.
Widad ta ɗago idanunta cike da rashin mutunci da tsantsar izza ta kalli Yusuf tace "kai kuma biyo ni"
Jiki a matuƙar sanyaye Yusuf ya miƙe yabi bayan ta, kamar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki, dan yasan tistiye shi zata yi da tambayoyi.
Share please
Ayshercool
07063065680
_*AƘIDATA*_
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Special thanks to all members of my Association
Perfect writers Association may Allah subhanahu wata'ala bless our pens and grant us wisdom to write what will bring positive changes to our Community.
              PART1
                  Page 8
Jinjina kai Mummy tayi ta juya ta nufi part ɗinta, jiki a saɓule yaranta na suka bi bayanta.
Koda taje ɗakin ta safa da marwa ta shiga yi tana sauke wata nannuyar Ajiyar zuciya me bayyanar da tsantsar baƙin ciki da takaici.
Ramla ta numfasa tace "Mummy akwai buƙatar ɗaukar matakin gaggawa akan wannan ɗan iskan mutumin, na rasa Wani asiri yayi wa wannan daƙiƙiyar da take tozarta ki akansa, kawai kisa a kawar da shi daga hanyar ki mana"
A gigice Amal tace "A'a Ramla, meye laifin sa? Laifin sa fa kawai ya hau kan kujera, shikenan Amma Widad ce tayi laifi anan bashi ba, kiyi tunani mana"
Ramla ta daka mata tsawa ta hanyar cewa "dalla rufe mana baki, dalilin wa akayi mana haka, a gaban masu aiki aka Wulaƙanta mu? saboda wanna ɗan matsiyatan ne me kama da mataccen silifas, wallahi Mummy ko baki ɗau mataki akan sa ba ni zan ɗauka, zan ɗau matakin da ya dace da shi da gaggawa"
Cikin hanzari Mummy tace "A'a Ramla da alama akwai Amfanin daze iya yi mana a nan gaba, nasa Isa mai gadi ya binciko min É—an wace unguwa ne"
Ramala tace "Mama Isa megadin me? Me ze iya tsinanawa, kawai Kisa abi bayan sa kawai a gano inda yake, kuma É—an uban waye shi"
Amal cikin sanyin jiki tace "dan Allah Mummy karkisa a masa wani abu dan Allah, abi komai a hankali"
Mummy tace "dalla rufemin baki sakarya!"
Ramla tace "Mummy ƙyaleta dan Allah, me abun haushi kawai, Amma Mummy ta yaya ze iya mana amfani a nan gaba?"
Murmushi Mummy tayi tace "zan miki bayani Ramla, ba zanyi a gaban wannan shashashar ba, dan yanzu na kasa gane inda tasa gaba"
Widad kam, suna zuwa falonta ta tsaya ta juyo ta kalli Yusuf, ta ƙure shi da ido tun daga sama har ƙasa, yayin da shi kuma ya ƙi yadda ya ɗago ido ya kalle ta, ta daɗe tana kallon sa tana nazarinsa.
"Look up" ta faɗa a taƙaice, ɗan ɗagowa yayi ya kalleta ya maida kansa ƙasa.
"Ya aka yi na dawo gidan nan jiya? Meyafaru dani a gurin party jiya?"
Dama Yusuf yasan a rina, dan haka a dake yace
"Eh kin faÉ—i ne akan stage, shine muka taho gida"
"Malam ƙarya kake, ka gayamin meyafaru? Ko kaima kazo ne dan a haɗa kai da kai a cutar dani?"
Yusuf ya girgiza kai yace "Me yasa kike tunanin za'a haɗa kai dani a cutar dake? Meye riba ta in an haɗa kai dani an cutar dake?"
"Saboda talaka ba abunda baze iyayi akan kuɗi ba, An haɗa kai da kai an turo ka ka cutar dani, in ba hakaba meyasa lokacin da nace kasa hannu a death contract ka yadda ba tare da ko ɗar ba ka cigaba da aiki dani? Wannan shi ne karo na biyu kana min ƙarya, meyasa? Ta yaya zan faɗi haka kurum bani da wani special case, se taɓin hankali, shima kuma ƙaƙabamin shi akayi, ta yaya haka zata faru? Bana tunanin na samu mental attack ne haka kurum a gurin nan, Ka gayamin gaskiya you are here to kill me, you were sent by someone to kill me " cikin ɗaga murya, tare da tsantsar rashin yadda take maganar.
Gaba ɗaya ta birkice, Yusuf yai shiru ya ƙura mata ido yaƙi cewa komai.
A fusace tace "talk to me!!"
"Am not here to kill you, na karɓi aikin nan ne saboda shine last option ɗina, idan banyi aikin nan ba babu wata hanya da zan samu abunda zan kula da kaina da mahaifiya ta, talaka ze iya komai akan kuɗi, Amma be kai yadda me kuɗi zeyi ba, me kuɗi yafi talaka son kuɗi da aikata komai dan ya mallake su, da zan cutar dake da tuni nayi tunda kika amince kije ko ina tare dani, someone attempts to kidnap you yesterday night, that's all I know"
Dafe kai Widad tayi ta shiga sintiri a gurin, gaba ɗaya idonta yayi Ja se gumi take, a hankali ta furta
"Jeka falo ka jirani, zamuje gidan Bulama yanzu"
Yusuf ya jinjina kai ya koma babban falon.
Kusan mintuna sha biyar yana jiran ta sannan ta fito, yauma dai babu batun mayafi balle hijjabi a jikin ta, haka suka fita.
Alhaji Haruna ne mahaifin Nurat É—auke da waya a kunnen sa yana waya, yana yi yana sharce gumi duk da sanyin Na'urar sanyaya É—aki dake É—akin amma gumi yake yakicewa, cikin inda inda yake cewa
"wallahi ranka ya daɗe seda aka shirya komai, dan yarinya ta Nurat ta tabbatar min da taje gurin party, taje gidana, dan an gama komai an sumar da ita, ana jiran sahu ya ɗauke azo a ɗauke ta, wani matashi yayiwa Yarinya ta barazana ya ɗauke ta ya tafi da ita, kuma ni a iya sanina ko su Alhaji Musa da muke komai tare dasu muke neman abu ɗaya basu san mun ƙulla alaƙa da kaiba balle ince haɗin baki ne"
Ɗaya ɓangaren yace "Shikenan zanyi wani shirin na mussman, Amma idan ka bari muka kuma rasa damar mu a karo na biyu zan ajiye ka a gefe in nemo wani"
"Insha Allah baza'a sake samun matsala ba Alhaji Bukar"
Alhaji Bukar yace "Allah yasa, sannan batun wannan matashin kabar komai a hannu na, nasan abunda zanyi"
"Shikenan godiya nake ranka ya daÉ—e " daga nan suka yi sallama.
************************
Bayan fitar su Widad, Mummy tasa aka kira mata Isa mai gadi.
Isa yaje ya same ta a falo, cikin rawar jiki ya gaida ita ta amsa masa a wulaƙance ta kalle shi tace
"Kai na baka aiki amma har yanzu nani shiru ko bazaka iya bane?"
"A'a ranki ya daÉ—e, yaron ne gaba É—aya baya sakin jiki damu yanzu, wani mugun jin kansa yake kamar wani basarake"
Ta jinjina kai tace "tabbas nima naga hakan, kuma da sannu zan kawo ƙarshen wannan izzar da yake ji da ita, talakan banza asararre, kaje kayi abunda na saka, bana so yasan nasa a bibiye shi ne, ka nemo min inda yake zaune, zan sa ayi maganin sa, tashi ka koma bakin aikin ka"
Ya tashi sumi sumi ya fice.
***********************
Yusuf suna zuwa gidan Bulama suka yi sa'a yana nan, a harabar gidan suka ganshi yana shan lemo, hannun sa É—auke da Jarida.
ÆŠago idon da yayi ya sauke akan Widad yasa shi sakin murmushi, itakam fuskar nan a murtuke ba annuri.
Alhaji Bulama yace "barka da zuwa lovely daughter"
A ɗan ciki tace "barka da hutawa Daddy"
"Yawwa barka lovely daughter, ya akayi ne na ganki a haka? Meke faruwane? Ko ciki zamu shiga?"
Yusuf a ransa yace "wata sabuwa, yau kuma Alhaji Bulama take kira da Daddy, idan taga dama kai tsaye take kiran sa da Bulama, wannan yarinya akwai ta da rikici, bata da Alƙibila sam"
Ta yamutsa Fuska tace
"A'a nan ma ya isa, Amma Daddy akwai matsala fa"
Ya tattaro hankalin sa kanta yace "matsalar me daughter"
"Ana farautar rayuwa ta har yanzu, daga fita jiya aka kusa saceni, nidai tunda Daddy baya nan kamin visa zan bar ƙasar nan, gara in ƙarasa Rayuwa ta a can ƙasashen wajen"
Alhaji Bulama yace "waye yayi attemptin ɗin sace ki, kuma a ina? Shiyasa tuntuni nace a samo masu tsaron lafiyar ki"
"Bashi da mahimmanci kasan inda naje, da wanda yai yunƙurin saceni, duba da tsawon shekaru kun gaza maida hankali ku gano hakan, kuna ɗaukar wasu maganganun nawa a matsayin maganganub hauka, kawai ka nema min visa zan bar ƙasar nan"
"Haba lovely, saboda me zaki bar ƙasar ki ta haihuwa? kije ki cigaba da rayuwa ke kaɗai a wata uwa duniya? Nace a ɗaukar miki masu tsaron lafiyar ki da zasu dinga miki rakiya kinƙi, kin ɗakko wannan dogarin duk inda zaki yana biye dake kamar inuwa, shiba soja ba, shiba wata tsiya ba ta ina ze iya tsare lafiyar ki?" yai maganar yana nuna Yusuf
Widad ta haɗe fuska tace "kaikam wani lokacin se in rasa meke damun ka, aini babu me tsaron lafiya ta se Allah, Akan me zan ɗau masu tsaron lafiya ta, haka kurum a haɗa kai da masu tsaron nawa a cutar dani? I don't trust anyone"
Alhaji Bulama yace "shi wannan É—in kina da tabbacin baza'a haÉ—a kai dashi a cuce ki ba?"
Ta juya ta kalli Yusuf dake tsaye, sannan ta kalli Bulama tace "Ba'a kansa muke magana ba yanzu , babu ruwanka kasancewarsa tare dani, muna magana akan Visa zakamin in bar ƙasar nan kawai"
"wai tayaya zan miki visa ki bar ƙasar nan? Keda muke saka ran Dawowar Fahad in next couple of weeks a fara zancen Auren ku, meya.......
"shut up please! " ta faÉ—a a hasale tana É—aga masa hannu sannan ta É—ora da cewar
" wai har yanzu baka janye wannan banzan ƙudurin naka ba ko? Kana tunanin abunda na gaya maka ƙarya nake, let me repeat myself, bazan yi Aure ba, babu namijin daya dace dani, ni ba zanyi Aure in zauna a ƙarƙashin wani ba, Allah ya bani dukiya wadda ta isheni rayuwa, bana buƙatar wani Aure, hankalina na kan son ganin bayan maƙiya na, koni ko su, ko kuma muyi mutuwar kasko"
"Widad, dukiya shirme ce idan babu Soyayya da kulawa, ban hanaki gano wanda suka rusa farincikin rayuwar ki ba, Amma aure yana da mahimmanci a rayuwar ki, bakya son ganin 'ya' yan ki a duniya? Aure garkuwa ne Widad"
"Soyayyar banza, is just stupidity and form of mental disorder, an imagination and bunch of problems, bana buƙatar soyayyar kowa, nikaɗai zan gudanar da rayuwa ta, na ishi kaina rayuwa bana buƙatar kowa yayi min garkuwa"
Zuwa yanzu Yusuf ya saba jin ire iren wannan maganganun na Widad, Amma yana kallon ta a wani iri idan yaji tana faÉ—in wannan kalaman, ta yaya mutum zece ze rayu shi kaÉ—ai, ba abokin rayuwa ba 'yan uwa ba Abokan Arziki? Kafin ya bawa kansa amsar tambayoyin ya tsinkayi murayarta tana cewa
"Wallahi ko kana so ko baka so, ba zan cigaba da zama a ƙasar nan ana farautar rayuwa ta ba, kuma ba zanyi Aure ba babu shi a tsarina"
Bukama yace "Aini bance dama ki zauna a ƙasar nan dole ba, da zarar an ɗaura miki Aure ƙasar nan zaku bari gaba ɗaya keda mijinki, kinga kin tsallake tarkon maƙiyanki"
Cikin izza me bayyanar da tsantsar ikon da take dashi tace
"Wani tabbaci kake da shi shi É—an naka baza'a haÉ—a kai dashi a cutar dani ba?"
"Idan har É—an dana haifa ze cutar dake, da nine mutum na farko da ze cutar dake da mahaifinki, dan a yanzu mahaifinki bashi da ka mata"
Widad ta miƙe tsaye ta dafa teburin ta kalli idon Bulama tace
"Zan bar ƙasar nan ko kana so ko baka so, kuma bazan Auri ɗanka ba, babu Aure a tsari na, ina fatan wannan ya zama karo na ƙarshe da zan gaya maka babu Aure a tsarin Rayuwa ta, Ganin bayan maƙiya na shine a gaba na"
Ta juya ta nufi inda Yusuf yayi parking ɗin mota, da sauri Yusuf ya riga ta ƙarasawa ya buɗe mata gaban mota, dan bata zama a bayan Mota.
Yusuf ya fara tuƙi ba tare da ta kalle shi ba tace "Muje Farm House" shima be ce mata komai ba, ya ɗauke kan motar zuwa hanyar gidan gona.
Suna tafe Yusuf yana tunanin wani dalili ne yasa kowa yake tsoron Widad haka? Take faÉ—awa kowa abunda ta ga dama komai tsufan sa kuwa? Indan Mahaifinta yana da kuÉ—i ne, suma ai masu kuÉ—i ne.
Bayan tafiyar su Widad Bulama na nan inda suka barshi yana zaune yayi shiru, Matarsa Hajiya Sarah ce ta fito da shirin ta tsaf, da alama fita zata yi.
Inda Alhaji Bulama ke zaune ta nufa, ta samu kujera ta zauna ta kalle shi taceÂ
"Ya dai? Wannan dogon tunanin fa? Shekaru sun fara ja, dogon tunani be kamace ka ba"
Ya sauke Ajiyar zuciya ya kalle ta yace "dole inyi dogon tunani, Yanzun nnan Widad ta bar gidan nan, lamarin yarinyar nan kullum ƙara taɓarɓarewa yake, wai ita ba zata yi Aure ba kwata2, haka zata ci gaba da zama, Rayuwa zata yuwu a haka? "
Ɗan taɓe baki tayi tace "waini Alhaji meye nasa damuwar 'yar wani a ranka? Naga dai ba kaine ubanta ba, taje tayi abunda taga dama mana"
"A' a Sara, Kin san yadda nake da Mahaifinta, damuwata tasa ce, damuwar sa ta wace, kuma har yanzu ana kainata hari, nace a samo mata masu tsaron lafiyar ta, taƙi se wannan yaron da take yawo da shi, kome ze tsare mata oho?"
"to ku ƙyaleta tayi abunda ta ga dama mana, tunda bata san abun Arziki ba, dama ba dole a cigaba da kai mata hari ba wannan Wulaƙanta mutane da take, Yarinya ƙarama se baƙar Aƙida"
"A'a be kamata a ƙyaleta ba Sarah, nifa mun yanke shawarar zamu haɗa ta Aure ne da Fahad"
Kallon sa tayi galala sannan taceÂ
"ban gane haÉ—a ta Aure da Fahad ba? Wannan Yarinyar mara tarbiyya da bata san Darajar mutane ba zaku haÉ—a da Fahad, ko manta Fahda É—in shima yadda yake da saurin Fushi da zuciya? Tabbas babu inda wannan Auden zeje, gara ma karka fara"
"Babu ruwan ki, Insha Allah zasu zauna lafiya"
Miƙewa tayi tsaye tace "Ai se ayi in gani, ni na haifi abuna ba wani ya haifar min ba, bame Aura masa Mahaukaciya mara tarbiyya"
Ta ɗau jakarta ta bar gurin tana ƙunƙuni.
Yusuf ne zaune ya zubawa sarautar Allah ido, Widad ce take zaga dabbobin gidan, wanda mafi Akasari karnuka ne da maguna se tsuntsaye, Abunda ya bashi mamaki shine yadda tasa aka fito mata da wani jibgegen ingarmar doki, aka ɗaura masa linzami, ta ajiye Wayarta ta da 'yar ƙaramar Jakarta, ba tare da an taimaka mata ba ta haye kan dokin nan.
Kasancewar harabar gidan ƙatuwa ce sosai, hakan yabawa Widad damar yin sukuwa akan dokin nan yadda take so, ba ƙaramin ɗaurewa Yusuf kai tayi ba, yadda take sukuwa akan dokin tana sarrafa akalar sa yadda take so, ze tabattar maka ta saba hawan dokin, kuma ga dukkan Alamu hakan yana bata Nishaɗi.
Seda tayi me isar ta sannan taci birki ta sauka daga kan dokin, ta shiga cikin gidan.
Yusuf yana nan zaune ɗaya daga cikin ma'aikatan gidan wanda Aƙalla ze shakara talatin da wani abun ya ƙaraso inda Yusuf yake zaune shima ya zauna kusa dashi.
Ya miƙawa Yusuf hannu suka gaisa, ya kalli Yusuf yace
"É—an Samari daga wani gari kake ne?"
Yusuf ya ɗan ƙura masa ido Sannan yace "Kano"
Mutumin Yayi Murmushi yace "Ashema ɗan garin nan ne kai, a wace unguwa kake?"
Yusuf yace "Me yasa kake tambaya ta ne?"
"Ahh karka damu kawai dai na tambaya ne, Amma idan ba zaka damu ba, dan Allah wani irin aiki kakewa Madam haka da take yawo da kai ko ina? A iya sanina da ita tun shekarun baya bata sake wa da mutane haka, Amma kai gashi tana yawo da kai ko ina"
Yusuf yayi Murmushi yace
"Ita yakamata ta baka wannan Amsar bani ba"
Suna cikin maganar ne Widad ta fito sanye da wasu kayan daban.
Ƙure Yusuf da Saleh tayi ido, tana musu kallo irin na tuhuma, ba tace komai ba ta nufi inda Motar su take, Ma'aikatan gidan suka biyo ta suna mata kirari suna Allah ya kiyaye, bata kula kowa a cikin su ba ta hau motar Yusuf ya ja suka bar gidan.
Suna cikin tafiya yaji taceÂ
"Me Sale yace maka?"
"Waye Sale?" Yusuf ya tambaye ta, shiru tayi masa tsawon wasu daÆ™iÆ™u sannan cikin maganar ta ta isa, taceÂ
"Kana jin daɗin rainamin hankali a lokuta da yawa, na kan ƙyaleka ne saboda ina jin nauyin hukunta ka a lokuta da yawa, saboda hatsarin da rayuwar ka ke ciki Kasancewar ka tare dani, Amma hakan baze hanani koya maka hankali idan ka saɓawa Yarjejeniyar mu ba, na tambaye ka ɗazu da Safe baka bani haƙiƙanin Amsar tambaya ta ba, ka rainamin hankali, yanzu ma na tambaye ka kana sake tambaya ta, wannan abubuwan da kake kana jawowa kanka zargi ne a gurina, karo na biyu Me Sale yace maka? "
Murmushi Yusuf yayi yace
"Ya tambaye ni Sunana ne, da kuma aikin danake miki, na gaya masa sunana, Amma aikin da nake miki nace ya tambaye ki"
Jinjina kai tayi tace "Amma kamar na gaya maka duk inda muka je, ba zakayi magana da kowa ba se idan ni nayi maka izinin yin hakan"
Juyowa yayi ya kalli Widad, Yarinya ƙarama se izza da jin kai.
Yusuf ya É—an rausayar da kai yace
"Allah ya baki yawan rai ya kare ki daga sharrin maƙiyanki, banyi hakan da saɓa dokarki ba, sedai idan nayi hakan mutane zasu ga tamkar wulaƙanci ne, nasan tsoron ki kar a haɗa kai dani a cutar dake, Amma ina tabbatar miki da cewa bazaki taɓa samuna da cin amanar ki ba"
Ba tare da ta kalle shi ba tace
"Zan gani ai"
Sunyi shiru na wani lokaci, can ta jinjina kai taceÂ
"Lallai Sale, kar nake kallon sa, yana son ganin bayana saboda abunda nayiwa ɗan uwan sa, duk randa na kama shi red handed wallahi se yaje inda ɗan uwansa yaje, babu Amfani zama da maƙaryaci me cin Amana"
Yusuf ya juya yana kallon ta, yana tunanin randa ta gano waye shi, wane irin mataki zata É—auka akan sa?
****************************
A kwana a tashi Yusuf yayi wata guda cif yanawa Widad aiki, kullum cikin hantarar sa take da wulaƙanci amma sam seya nuna mata ko a jikin sa, duk abunda yayi baze burgeta ba, yayin da Amal keta ƙara tura kai a gurin Yusuf, dan ita nan duniya babu wanda yayi mata kamar shi tana matuƙar ƙaunar Yusuf saboda nutsuwar sa, Yusuf yana ta ganin Abubuwa na ban mamaki a game da uwar ɗakin sa yayin da gefe guda ya kasa gane bakin zare al'amuran gidan nan, gaba ɗaya yanayin yadda mutanen gidan ke gudanar da mu'amalarsa da ban mamaki dan kowa da inda yasa gaba kuma kowa akwai wani boyayyen abu da yake ɓoyewa a ransa.
Har wata ya cika, aka shiga wani watan Widad bata biya Yusuf haƙƙin sa ba, shi kuma bece mata komai ba, sannan duk lokacin da ta buƙaci zuwa wani guri, zeje ya kaita ba tare da ɓata lokaci ba.
Isa me gadi yana ta ƙoƙarin bugun cikin Yusuf yaji wani abu game da shi amma Yusuf yaƙi gaya masa komai.
Gaba É—aya ma'aikatan gidan suka tsangwami Yusuf suna ganin ana fifita shi akan su.
Shikam ko a jikin sa, shima ya dena shiga harkar su, har gara Murtalah me kuka da shuke shuken gidan suna hira da Yusuf wasu lokutan.
Hajiya Halima na zaune a falo tana aiki a System, gefen ta kuma Amal ce ke cin Abinci, mai aiki ta fito daga sashin Widad, ta durƙusa a gaban Mummy tace
"Hajiya, Anty Widad fa tun jiya ɗakin ta a rufe, na ƙwanƙwasa taƙi buɗewa, tun jiya da safe naje in gyara mata amma ɗakin a rufe"
Tsaki Hajiya Halima tayi tace "To ina ruwana, yarinya ce ita ƙarama da zan dinga binta, in taji yunwa zata kashe ta ta fito"
Amal tace "Mummy kina tunanin Yunwa zata saka ta fito ne? In baki wasa ba sedai kiga gawar ta kin san halin ta, idan ta mutu da wani kalamai zaki ƙwaci kanki a gurin me gidan nan? Bama ke kaɗai ba dukkan mu, sannan Burinmu baze cika ba, ƙarshe ma dukkanmu sedai mu mutu a prison"
Ɗan zaro ido Mummy tayi tace "Kuma fa hakane, tashi muje mu gani"
Suka nufi part ɗin Widad, Amma suka tarar ta rufe bedroom ɗinta, suka yi bugun duniya taƙi ta buɗe.
Rasa abunyi suka yi, suka kira Alhaji Bulama suka sanar masa da abunda ke faruwa, da kiran wayar tasa beyi mintuna Arba'in ba se gashi.
Yaje ya tarar dasu sunyi cirko cirko a ƙofar ɗakin Widad, ya taka yaje gaban ƙofar ya fara ƙwanƙwasawa
"Lovely daughter, Dad ɗinki ne, ki buɗe ƙofa kinji, karkiwa kanki illa"
Still Widad ba tayi responding ba, dan ko motsin ta basaji.
Alhaji Bulama yaceÂ
"Kuma babu wani abu daya haɗaku da ita? Kowani saɓani ko ayi mata wani abun?"
Ramlah tace "waze nata wani abu kuwa? Ita wannan se an mata wani abu? Ai sedai tayi wa wanima,wataƙila haukan nata ne ya motsa"
Alhaji Bulama yace "ku bani mukullin É—akin ta, a buÉ—e É—akin karta"
Mummy tace "taɓ wake da mukullin ɗakin basarakiya, ita da bata yadda da kowa ba, wa zata bari ya mallaki mukullin ɗakin ta ba wanda yake da mukullin ta"
Alhaji Bulama yace "to ko maza za'a kirawo su ɓalla ƙofar a gani"
Ramlah tace "A'a karka jamana Jaraba, a ɓalla mata ƙofa ka samu a tashin hankali da masifarta, a kira Baban ta aji meze ce"
Alhaji Bulama yace "Keba babanki bane Ramlah"?
Cikin tsiwa Ramlah tace "Niba baba na bane, kullum bata da gori seba gidan ubanmu bane, dan haka ubanta ita ya haifa bani ba"
Yau Yusuf ya makara dan se sha ɗaya ya tashi na safe, tunda ya koma bacci ƙarfe takwas na safe, dan haka a gurguje ya kintsa ya fito, yayi sa'a Umma bata nan ta fita, dan haka ya kulle gidan ya fita, ya nufi gidan su Widad.
Yana zuwa suka gaisa dasu Nura sama sama,suna masa wani kallon banza
Yusuf ya kalli Murtalah yace "Murtalah Madam ta fito kuwa? Ko tazo nema na naga yau na makara sosai"
Murtalah yace "ina fa, tana can tun jiya taƙi buɗe ƙofa, ana can anata fama da ita, ba wanda yasan tana raye kota mutu, gashi babu wanda yake da mukullin ƙofar ta, ana tunanin ko ɓalla ƙofar za'ayi
Zaro Ido Yusuf yayi ba tare da yace komai ba, ya tashi da sauri ba tare da tunani komai ba ya tun kari cikin gidan.
Isa ya taɓe baji yace "kalli uban shisshigi, Allah yasa yana zuwa su Wulaƙanta shi su koro shi, banza me rawar kai kawai"
Murtalah yace "Haba Isa, ka sawa Yusuf ido da yawa wallahi, gashi kullum ƙara samun matsayi yake a gidan nan fiye da kai"
"dalla rabu dani, se kace baka ganin yadda aka fifita shi akanmu a gidan nan, danma mun samu mu Hajiya tana bayan mu, duk yadda muka so samun gindin zama a gurin yarinyar nan muka kasa, Amma shi daga zuwan sa ga yadda ya samu sake yake wani zaƙewa kamar gidan ubansa"
Yusuf kuwa na shiga Babban falo ya gansu a zazzaune suna tattaunawa, Ya durƙusa ya gaishe su.
Alhaji Bulama ne kawai ya amsa, se Amal da tace "Sannu da zuwa"
Hajiya Halima tace "To Munafuki me ka shigo yi uban iya"
Yusuf yace "Naji ance Madam bata fito daga É—aki ba yau kwana biyu shine nace.....
Cikin hantara Ramla tace "shine me, mezaka iya? Bama son munafunci malam jeka mungode, Anjima baban ta ze dawo, yasan yadda zeyi da ita uban shishshigi"
Yusuf yace "Amma be kamata a barta har se ya dawo ba, babu wanda yasan halin da take ciki, ta rufe kanta a cikin É—aki yakamata a duba halin da take ciki"
Hajiya Halima tace "kai bana son rawar kai irin naku na matsiyata, ka fimu sanin abunda ya dace ne? Dalla ɓacemin daga nan"
Alhaji Bulama yace "A'a Hajiya Halima, kika san Alaƙar dake tsakanin su?, ki ƙyale shi ya Jarraba mana wataƙila kiga ta buɗe ƙofar, kaga tashi kaje ko zata buɗe"
Yusuf ya miƙe ya nufi hanyar ɗakin ta.
Yana zuwa ƙofar ɗakin ba tare da ɓata lokaci ba, yasa hannu a aljihunsa ya ɗakko mukullayen motocin ta dake gurin sa, ya saka key ya buɗe ɗakin nata, da yake yasan mukullin ƙofarta ta falo da ta bedroom tunda tana aiko shi ɗakin.
"Innalillahi wa inna ialaihi raji'un!!!"
Shine abunda Yusuf ya faÉ—a
In an karanta ayi share please ðŸ™
07063065680
Ayshercool
_*AƘIDA TA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in
             PART1
                Page 9
_Asslam Alaikum warahmatullah_da _fari dai zanyi wata magana_ _tun page ɗin farko nayi bayani_, _nace ina da Jarrabawar ƙarshe_, _ina ƙoƙarin cika Alƙawari ne yasa na cigaba da kawo_ _littafin nan ɗaya ga watan October_ _nace bazan samu yin posting kullum ba_ _amma ina iya ƙoƙarina inga nayi duk dan faranta muku_ _amma wasu na ƙorafi hadda gayamin baƙar magana_ _dan bana posting kullum_ _littafin nan dai nina sa kaina_ _kuma nace free ne balle ace siya akayi nake jan rai_ _babu wanda nayiwa dole seya karanta_ kuma ban karɓi kuɗin kowa ba, _ni nake saka data in ɓata lokacina inyi typing sannan inyi posting_ _dan haka wanda baze iya haƙuri ba ze iya dena karantawa_ ba zanyi _typing kullum ba tunda ba siyarwa nayi be_
_Ni bana Wulaƙanta kowa nasan soyayya ce tasa ake karanta littafina
_
_Masoya har kullum ina sake godiya da Comments ɗinku da Addu'oinku_ _zancigaba da ƙoƙarin faranta muku Insha Allah_
Widad ya hango zaune acan ƙarshen gado kamar Mahaukaciya tuburan, rigar jikin ta iya cinyar ta, gaba ɗaya gashin kanta a hargitse, ta sunkuyar da kanta jikin ta se rawa yake tana kuka, ta rufe ko ina babu haske a ɗakin, seda ya buɗe ɗakin sannan haske ya bayyana a ɗakin.
Babban abunda ya bawa mutan gidan mamaki be wuce yadda akayi Yusuf ya mallaki mukullayen ɗakin Widad ba, alhalin su raɓar ɗakin nata ma basu isa suyi ba, balle samun mukullayen.
Da sauri ya ƙarasa gaban gadon ta yana ambaton Subhanallah,tana ɗagowa taga Yusuf ta gigice ta fara ja da baya tana girgiza kai.
Yusuf yace "Meya sameki haka? Ki kwantar da hankalin ki, Yusuf ne direban ki fa"
Girgiza masa kai tayi tana kuka tace "Ni karka kasheni"
"No ba kashe ki zanyi ba"
Ɗaga kai tayi ta kalli su Alhaji Bulama dake tsaye suna kallon su, riƙo rigar Yusuf tayi kamar zata yagata tace "Suwaye wannan? kace su fita bana son ganin su, kace su fita su bar nan" ta faɗa cikin ɗaga murya da zubda hawaye.
Yusuf ya zauna yaceÂ
"Calm down, kinga fa wancan Dad É—inki ne Alhaji Bulama, ga Mummy, ga Ramlah ga Amal, sune baki gane ba?"
Alhaji Bulama ya tako yazo inda suke, ya miƙa hannu ze riƙo Widad.
Wata irin ƙara ta saki, ta rirrƙe Yusuf tana ɓuya a bayan sa tana girgiza kai, cikin ƙaraji take cewa
"Ni su fita, su fita su bar nan gurin, kasheni za suyi, kana kallo nima zasu kasheni, bana son ganin su ba wannan ne Daddyna ba kuma bashi ne Bulama ba"
Yusuf yace "buɗe ido ki kalle su fa, ga Daddy Bulaman nan s tsaye a gaban ki"
Girgiza kai tayi tace "bashi bane ba, na gaya maka bashi bane"
Ta rungume Yusuf gam tana ci gaba da zubar da Hawaye.
Yusuf a ransa yace "ta tabbata kenan Widad tana da taɓin hankali? In ba haka ba meze sa ta koma haka?"
Alhaji Bulama yace "Karka damu dama tana yin hakan wani lokacin, ciwonta ne ya tashi"
Ihun da take yi ne iya ƙarfinta, kai kace wadda ake yankawa, ba shiri suka bar ɗakin Amal wani irin baƙin kishi ne ya cunkushe zuciyarta, yadda Widad ta rungume Yusuf yafi komai yi mata ciwo.
A hankali Yusuf yace "Kinga sun fita ba kashe ki za suyi ba, cikani ki ga wani abu"
Girgiza masa kai tayi "tace ni A'a tsoro nake ji, kasheni za'ayi nima an kashe Ammi nima kasheni za'ayi"
Yusuf ya girgiza mata kai cike da damuwa yace "Ai ina nan tare da ke, ba inda zani babu me taɓa ki idan ina nan insha Allah , ba wani abun tsoro fa"
A hankali ta cika Yusuf tana sauke Ajiyar zuciya, hawaye na cigaba da bin fuskarta.
Yusuf ya kalle ta yace "je kiyi brush se kici Abinci, ance tun jiya baki ci Abinci ba"
Girgiza masa kai tayi Alamar A'a.
"Idan baki abunda nace ba, zan tafi in barki anan suzo su tafi dake"
A firgice ta kalle shi, ya jinjina mata kai alamar eh, rigarsa ta kuma riƙewa gam ya rakata banɗaki ta wanke baki, ta fito, tana ta binsa da kallo kamar taga wata halitta daban.
Da yayi hanyar fita seta biyo shi tana sake rirriƙe shi, gaba ɗaya tausayinta ya kama shi, ya ɗauki bedsheet ɗin dake kan gadon ta ya ɗaura mata, ya ɗakko hula ya saka mata.
Alhaji Bulama ya kalli Hajiya Halima yace "Nayi mamakin abunda ya tayar da ciwon Widad, na zata tuni ta warke?"
Hajiya Halima ta taɓe baki tace "to ni ina zan sani, daga ita se ubanta se kuma kai suke sakawa a lamarin su, ta yaya zan san kota warke ko bata warke ba"
"Amma abun da mamaki, Akwai buƙatar ta cigaba da ganin likitan ƙwaƙwalwa kenan?"
"Wannan kuma ya rage shawararka kai da Mahaifinta, ni 'yar kallo ce ai tunda alamu sun nuna haukan yana nan tuburan"
Bulama yace "Hajiya Halima ai ba kyace haka ba É—a na kowane"
"A'a wannan dai bata kowa bace, ta babanta ce kawi, ka dena wannan maganar nawa' ya'yan dai nawane, itama 'yar wasu ce"
Ƙyalƙyalewa da dariya Alhaji Bulama yayi yace "Shikenan tunda haka kikace, ni dai na tafi, Munyi waya dashi Megida kafin inzo nan yace yana kan hanyar dawowa, zezo ya dubata idan jikin da sauƙi ya koma, idan kuma da yuwuwar a maida ita ga likitocin ƙwaƙwalwa shikenan, dan be gama abunda yake ba ze yanke ya dawo, kin san idan bata da lafiya baze iya komai ba, Allah ya bata lafiya"
Hajiya Halima tace "Karma Allah yasa tayi lafiyar, Ita da ubanta ya shafa bani ba"
Alhaji Bulama ya girgiza kai ya fice.
Yusuf Ya kira Amal a waya, ta É—aga tana tura baki, dan gaba É—aya kishin Yusuf take, Yusuf yaceÂ
"Amal dan Allah ki kawo Abu me É—an É—umi a bata taci, da alama tana jin yunwa sosai"
"wallahi Yusuf ba dan kai ba ko zata mutu ba zan kawo komai taci ba, kaima É—in dai kawai zan kawo ne"
"Yi haƙuri, Nagode sosai da kika min Alfarma"
Amal ta shiga kitchen ta haɗa kayan tea, Mummy tace "Me zakiyi da tea ranar nan?"
"Widad za'a bawa" ta bata amsa
"ke meye naki a ciki to?"
"Mummy wai so kike se duniya tasan halin da muke ciki ne? Kar hankali ya dawo kanmu, Ai se munayi muna ɓadda sahu"
Mummy tai murmushi tace "daɗina dake wani lokacin akwai hankali, ɗakkomin Jakata a ɗaki"
Amal taje ta É—akko mata jaka ta dawo, sannan ta É—au tray É—in ta tafi part É—in Widad.
Yusuf ya miƙe da nufin karɓo kayan tea ɗin, Amma Widad ta riƙe rigar sa tabi bayan sa tana zare ido.
Yusuf ya kalli Amal yace "dama Amal dagaske Widad nada taɓin hankali?"
Amal tace "gashi kuwa kana gani tana yinsa tuburan"
Cikin tsawa Widad tace
"niba mahaukaciya bace, ka gaya musu niba mahaukaciya bace, su suka haÉ—ani da hauka, su suke maida ni mahaukaciya, Amma niba mahaukaciya bace"
Gaba É—aya Yusuf ya rikice, yace "is Ok ai dama ke ba mahaukaciya bace, ki kwantar da hankalin ki"
Amal ta kalli Widad tace "kina wannan tamɓelen kike cewa ke ba mahaukaciya bace? Kalli fa abunda kike yi mahaukaciya ce ke tuburan, dan me hankali baze abunda kike ba"
Yusuf yace "Haba Amal, ya ana ƙoƙarin kwantar mata da hankali Amma kike tinzira ta"
Amal ta zumɓura baki tace "kaga ni karɓi kayan nan, kalli yadda take wani riƙe ka aikin banza kawai"
Widad ta shammace ta, tasa hannu ta kifar da farantin ruwan zafin, aikuwa ya zube a ƙafar Amal, Ihu Amal ta saki, wanda ya janyo hankalin Mahaifiyar ta da Ramlah suka taho da sauri.
Idan ba gizo idon Yusuf yake masa ba, tabbas kamar ragowar ƙwayar magani ya gani a ƙasan kofin da'aka zuba tea ɗin, sedai kafin yayi wani yuƙuri
Hajiya Halima taƙarsaso tana cewa "lafiya, meye haka?"
Cikin kuka da azaba Amal tace "Mummy, Widad ta ƙonani da ruwan zafi, Mummy ƙafata"
Mummy ta kalli inda Yusuf ke tsaye, Widad na riÆ™e da shi taceÂ
"To maye Jarababbe, ka lallaɓa ka Asirce ta ita da uban ta, shine ka koma da baya zaka illatamin 'ya ko? Wallahi ka kiyayeni, kuma kafin kasa kwaɓata tayi ruwa ni zanyi maganin ka, ke kuma" ta nuna Widad dake bayan Yusuf tace
"dan Ubanki ba dai hauka ba, a haka zaki ƙare, Hauka yanzu kika fara shi, daga nan har ƙarshen rayuwar ki, keda hankali sedai ki ganshi a gurin wasu, wannan haukan haka zaki mutu kina yinsa"
Widad ta Jijjiga Yusuf tace "kai ka gaya musu niba mahaukaciya bace, kuma wallahi idan ta kasheni itama sena kashe ta, gaba ɗayansu sune zasu kasheni, suna tace min mahaukaciya zasu kasheni, wallahi in baka hana su ba ni zan kashe su"
Ramla tace "kaga Malam dalla cikata kazo ka bar gidan nan, tunda babu gadon ka a ciki, ba'a haÉ—a kuÉ—i da matsiyacin uban ka an gina ba"
Wani irin kallo Widad takewa Ramla daga bayan Yusuf.
Kallon da Widad kewa Ramla ne yasa taga kamar Widad ta dawo hankalin ta.
Widad tace "idan ka tafi ka barni kasheni za suyi, kashe mutane suke yi fa"
Mummy tace "uwarwa muka kashe miki? Mu bama kisa kumako bamu kashe ki ba mutanen da kike Wulaƙantawa suna nan suna bibiyar ki zasu kashe ki, Mahaukaciyar banza da ta wofi, Allah kaɗai yasan me sukeyi da harta yarda da shi haka, dalla kuzo mu tafi suje su ƙarata, Allah ya ƙara birkita ƙwaƙwalwar ki zauna a haka koma samu mu huta, in ƙwaƙwalwar ki ta birki ce ta Ubanki ma ta birkice kowa ya huta da iskancin ki"
Ramla tace " Mummy watch your words fa, kina ta sakin layi mu tafi kema Amal Allah ya ƙara, maganinki kina ma wannan ɗan isakan direban shisshigi, gashi ai sun ƙonaki a banza nan gaba ma illataki zasuyi"
Shiru Yusuf yayi yabi bayan su da kallo, gaba É—aya tausayin Widad da Mahaifinta ya kama shi.
Ya lallaɓa Widad ya bata youghurt da ƙyar ta sha, tana sha tana masa surutai na shirme, irin na masu taɓin hankali.
"Menene dalilin samun taɓun hankalin Widad?" Yusuf ya tambayi kansa
Kwanciya tayi a jikin sa tana lumshe ido alamar bacci take ji, ƙirjin Yusuf se bugun uku uku yake, Kasancewar ya keɓance da Widad, abunda be taɓa yi ba, a duk lokacin da yayi yunƙurin rabata da jikin sa seta saka ihu kamar ƙaramar yarinya.
Yusuf yayi mamakin iri maganganun da Hajiya Halima da 'ya' yanta suka dinga faɗa akan Widad, koda yake ba abun mamaki bane, duba da Yadda Widad ɗin ke Wulaƙanta su, Amma me sukayi mata take musu haka? " Yusuf yayi Alwashin tone duk wani abubuwa da ake ɓoyewa, kuma ya ƙudurce a ransa zeyi duk me yuwuwa ya jure wulaƙancin Widad yaga ta ina ze temaki rayuwar ta.
Yusuf yai shiru yayi zurfi a cikin tunani, yaji Widad tana ajiyar zuciya alamun tayi bacci, a hankali ya zame ta daga jikin sa, ya kwantar da ita ya lulluɓeta ya fita ya kulle ta a ɗakin yaje yai salla.
Ana idar da Salla Isa yace " Yusuf ashe uwar ɗakinka ce babu lafiya? Ance taƙi buɗewa kowa ƙofa amma tana jin muryar ka ta buɗe, gaskiya kai ɗan baiwa ne, Amma naji ance haukan nata ne ya tashi ko?"
Yusuf ji yayi kamar ya kwaɗawa Isa mari, Amma ya ƙyaleshi ba tare da yace masa komai ba.
Ya koma É—akin nata ya tarar bata farka daga baccin ba.
Falon ta ya koma yana tunani, Ba zato ba tsammani yaji sallamar Mahaifin Widad a falon, Amsawa Yusuf yayi cikin girmamawa tare da risinawa.
Alhaji Nasir a É—an ruÉ—e yace "Sannu babban Mutum, ya me jikin kuma?"
"Alhamdilillah, ta samu bacci"
"Masha Allah"
Yasa kai ya shiga bedroom É—in, ya taka a hankali zuwa gaban gadon Widad ya zauna a gefen ta ya É—agota, idon ta a rufe tana bacci, ya shafa kanta yace
"Allah ya baki lafiya my daughter" ya kalli Yusuf yace "Nayi mamaki data iya yadda da kai, idan ciwon nan ya tayar mata bata yadda da kowa seni, ko Bulama wani lokacin muɗinma bata yadda damu gaba ɗaya se an mata allurai"
Yusuf yace "Wane irin ciwo ne haka?"
Alhaji Nasir ya É—an na Numfashi cike da damuwa yaceÂ
"Yusuf, nasan mutane da yawa suna mata kallon bata da kirki, wasu suna zargina da barin 'yata ta lalace, kawai ina kallon sune, ba tare da nace wa kowa komai ba, Yusuf Widad ita kaÉ—aice' yata dana mallaka, larurar nan ta same ta ne sakamakon kashe mahaifiyar ta akan idon ta"
Zaro ido Yusuf yayi yace "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un"
Alhaji Nasir ya jinjina kai yace "ƙwarai kuwa, Akwai abunda ya faru da Widad, wanda tun daga lokacin take gudun mutane, ta haɗu da larurar ƙwaƙwalwa, dukda partially ne larurar tata da farko, Amma daga depression ya zarce mata ta samu Arthropophobia,
larurar ƙwaƙwalwa me sa mutum ya dinga jin tsoron mutane, ba mutane ba wani lokacin idan tana cikin larurar ko haske bata so, muna ta magani Sedai har yanzu na gaza samun abunda zesa ta farinciki, kana gani ko fara'ar kirki ba tayi, na yanke shawarar in mata Aure amma tace bata so, dan Allah Yusuf na san kana haƙuri haka nan naji ka kwantamin, dan Allah ka tayani Addu'a, Allah ya bawa 'yata lafiya, ita kaɗai nake da ita, ba uwa ba uba"
Gaba ɗaya tausayin Alhaji Nasir da' yar sa suka cika shi, Yusuf ya numfasa yace "Insha Allah Alhaji, Amma ba kayi......
"Yallaɓai ya akayi harka shigo ban sani ba? muna can part ɗina muna fafutukar a kira likita yazo ya duba ta, gaba ɗaya yau kwana mukayi ba muyi bacci ba saboda yadda jikin Widad ya rikice, ko Abinci ba wanda ya iya ci yanzu ma mun shiga muyi salla ne ka dawo ban sani ba" Hajiya Halima ke wannan maganar cike da salon bariki da Kissa.
Alhaji Nasir yace "Allah sarki, nasan kina ƙoƙari akan Yarinyar nan, Allah ya saka miki da Alkhairi, ina su Baby Amal ɗinne ko basu san na dawo ba?"
"Amal ma bata jin daɗi, Ramla kuma salla take, ina jiran Widad ta farka ne a bata Abinci, mun samu da ƙyar tayi bacci"
Yusuf kam bin Hajiya Halima yayi da kallo, yana mamakin wannan iya salon barikanci nata, gaba É—aya ta juye kamar tana cikin damuwar gaske.
Yusuf yace "Bari inje gida Alhaji tunda ka dawo"
"Shikenan Yusuf ka gaida gida, nagode sosai Allah yasaka da alkhairi"
"A'a bakomai Yallaɓai" Yusuf yasa kai ya fice, Hajiya Halima tabi bayan sa da harara.
Kan Yusuf ya ƙara ɗaurewa da maganganun da Alhaji Nasir ya gaya masa, yana daf da fita kawai yaga Ramla ta sha gaban sa.
Tsayawa yayi yana kallon ta, ta kalle shi cikin Isa tace
"Bani mukullayen Motar Widad dana É—akin ta dake gurin ka"
Yusuf ya tsuke Fuska yace
"É—an bani hanya zan wuce mana"
"Ni kake kallo kakewa wannan gadarar haka? Zaka bani ko sena maka rashin mutunci?"
"bake kika bani ba, ba kuma ke nakewa aiki ba, dan haka babu ruwan ki dani"
"Kai kalli tsabar Idona, karka kuskura kace zakayi Jayayya dani, naga se wani shisshigi kake kana cusa kai a gurin waccan Mahaukaciyar da ita da Ubanta, to bari kaji in gaya maka, idan ma wani abu kake kwaɗayin samu wallahi ba zaka samu ba, Kuma hauka yanzu Widad ta fara shi daga nan har ƙarshen Rayuwar ta, ba zata sake moruwa ba, gara ka cire wa kanka ƙwalamar wannan daular da dukiyar, yadda kazo a talaka haka zaka koma a matsiyaci, idan kaga dama kaje ka faɗawa duk wanda zaka faɗawa, shawara ta ƙarshe da zan iya baka itace, ka gaggauta Ajiye aikin nan ka ƙara gaba ya fiye maka Alkhairi akan wasa da rayuwar ka"
Murmushi Yusuf yayi ya dubi Ramla yace "in kinga na bar aiki a gidan nan wanda nakewa aikin ne suka sallameni, kina wani iƙrarin dukiya, dukiya nawace taki a dukiyar nan? Ki kiyayi Yusuf, matsi da takura babu wanda Yusuf be gani ba a rayuwar sa, dan haka ƙaramar barazana irin taki ba zata hanani Aiki na ba, ni babu ruwana da rayuwar da kuke a cikin gidan nan ni aikina kawai nasani, ban guri in wuce ko in hankaɗeki"
Galala tabi Yusuf da kallo, da ma akwai Yadda yake mata magana cikin Izza shima, Me yasa ba yayiwa Widad da take Wulaƙanta shi, lallai maganar Mummy gaskiya ce, ya kamata ayi maganin Yusuf.
Yusuf fa kai ya sake ɗaukar wuta, abun da ya faru yau, ya ƙara tabbatarwa Yusuf akwai wani mugun nufi a zuciyar Hajiya Halima da 'ya' yanta.
Umman Yusuf ta lura da yanayin Yusuf ko iya sakewa yaci Abinci ba yayi, Umma ta kalle shi tace
"Yusuf wai meke damunka ne haka? Naga gaba É—aya kwanan nan na kasa gane kanka, Allah yasa ba wani abun aka kuma yi maka ba?"
"Umma ni a rayuwa ta wani irin ƙalubale ne ban gani ba? Aini lamarin rayuwa ta na miƙawa Allah, aikin da aka bani ne me matuƙar rikitarwa"
Nan ya kwashe komai ya gayawa Umman sa, Umms tayi shiru na wasu 'yan mintuna sannan tace
"lallai wannan lamarine me sarƙaƙiya, nidai fatana ka kula da kanka Yusuf, kayi taka tsan tsan ka cigaba da Addu'a, Amma waye yazo ya nemi da a dinga bawa ita Yarinyar kariya?"
Shiruu Yusuf yayi sannan ya girgiza kai yace "Wallahi Umma ban sani ba"
"Ta yaya za'a bawa mutum kariya ba tare da sanin sa ba? Kaima kamar baka san aikin naka ba?"
"Umma nasan aiki na, Amma nima umarnin manya na nake bi, wataƙila be kamata in sani bane"
"Hakane amma kayi taka tsan tsan, naji tausayin yarinyar nan, Amma ni jikina yana bani wani abu game da aikin nan da aka saka, Amma kasa gane ko menene, ina dai yi maka addu'a a duk inda kake Yusuf, ni dai fatana ka kula da kyau"
"Insha Allah Umma na"
Haka suka cigaba da taɓa hirarrakin su na ɗa da uwa.
Sosai tunani ya auri Yusuf, maganar Umma tana bisa hanya, waye wannan da ya nemi a bawa Widad kariya a ɓoye, dole akwai wata a ƙasa.
*******************
Washegari da safe, Yusuf ya koma gidan su Widad, bayan sun gaisa da su Nura, Yusuf yace "Nura ya jikin uwa É—akina kuwa?"
Nura yace "ta yaya zamu sani? Kaine dama aka É—auka mutum a gidan nan, da kai ake komai mu ina zamu san wani abu? Ai kaine mutum a cikin mu"
Yusuf yayi Murmushi ya samu guri ya zauna. Murtalah ya ƙaraso inda Yusuf yake yana faɗin "Malam Yusuf, ɗazu Alhaji ya leƙo yana tambayar ko kazo, dama yace in kazo a shiga da kai ɓangaren sa"
Yusuf yace "shikenan babu laifi, muje"
Murtalah yayi gaba Yusuf ya bishi a baya, Sam Yusuf be taɓa sanin da wannan ɓangaren a cikin gidan ba, gjda se kace ba'a duniya ba, Yusuf ya buɗe ido yana bawa idonsa Abinci.
Suna shiga Ƙaton falon, Murtalah yace
"to ni na tsaya daga nan, dan bani da ikon ƙarasawa ciki, seka fito"
Seda Yusuf ya gama waige2 sannan ya kalli ƙatuwar ƙofar dake cikin falon, a hankali ya taka yaje ƙofar ɗakin ya ƙwanƙwasa tare da yin sallama.
Alhaji Nasir ne ya amsa tare da cewa "Shigo"
Yusuf ya tura ƙofar ɗakin ya shiga, Alhaji Nasir ne zaune Widad ta ɗora kanta akan cinyar sa, idonta biyu tana ta jujjuya ƙwayar idon ta, gefe kuma Alhaji Bulama ne zaune a kusa da Alhaji Nasir.
Yusuf ya durƙusa yana gaishe su, Alhaji Nasir ya faɗaɗa murmushinsa yace "Me babban suna, ashe kazo?"
"Eh nazo ranka ya daÉ—e, yame jiki"
Alhaji Nasir yace
"Jiki da sauƙi, Alhamdilillah an samu ta dawo hayyacin ta, Amma taƙi magana sam"
Yusuf ya kalle ta yace "Sannu ya jikin naki?"
Haɗe rai tayi ta tura baki tace "Malam ni lafiya ta ƙalau"
Alhaji Bulama ya jinjina kai yaceÂ
"gaskiya akwai ka da sa'a, tun ɗazu muke magana taƙi kulamu amma kai gashi tayi maka magana"
Alhaji Nasir yace "My lovely, kin san wannan?" yai maganar yana nuna mata Yusuf
"Daddy nifa ba mahaukaciya bace"
Daddy yace "Ai na sani Babyna, tambayar ki kawai nayi"
Ta tura baki tace "Nasan shi"
Alhaji Bulama yace "to waye?"
"Direba ne" ta bashi amsa a taƙaice.
Daddy yace "direban wanne daga ciki?"
Maimakon ta basu amsa seta kalli Yusuf taceÂ
"kai ka gaya musu niba mahaukaciya bace, naga suna yadda da maganar ka, wallahi ni ina da hankali"
Yusuf yace "ai dama basu ce ke mahaukaciya bace, kina da hankali"
Ta kuma cewa "ka gaya musu wani na ƙoƙarin kasheni a gidan nan, ka cewa Daddy dan Allah ya ƙyaleni in koma England"
Yusuf yace "Shikenan ki kwantar da hankalin ki, zan gaya musu Insha Allah"
Alhaji Nasir yace Â
"Naga taku tazo É—aya da Yusuf Lovely, kamar shi kin yadda da shi ko?"
"Allah ya kiyaye, direba ne kawai, yana nan a matsayin sa na direba, karma ka faÉ—i wani abu da zesa yaji cewa shi na musamman ne, ko yana da wani matsayi, i don't trust anyone"
Alhaji Nasir ya girgiza kai yace "Yusuf nagode sosai, zaka iya tafiya abunka kaje ka huta, dama na kiraka ne in ƙara maka godiya nagode"
Yusuf yace "Ai babu wani abun godiya da nayi Yallaɓai, Allah ya bata lafiya"
Suka yi Sallama ze tafi, sedai yana ƙoƙarin barin ɗakin, Hajiya Halima ta shigo da tray da kayan marmari a kai, tana ganin Yusuf ta haɗe rai ta bishi da wata uwar harara ba tare da ta bari Alhaji Nasir yaga hakan ba.
Yusuf ya kama hanyar fita, yaji ance "Yusuf ashe kazo?"
Ya juyo ya kalli inda Amal ke masa magana yace "Eh nazo, tun ina ciki na duba jikin Madam ne"
Amal tace "shikenan É—an jirani ina zuwa"
"to shikenan bari in jiraki a waje" Yusuf ya koma harabar gidan yana jiran fitowar Amal, mintuna kaÉ—an sega Amal tazo, kaya ne a jikin ta wanda sukai matuÆ™ar matsarta, ta dube shi taceÂ
"dan Allah so nake muje gurin shan ice cream tare, Akwai maganar da nake so muyi"
"Kina ganin ba matsala kuwa? Kinga wancan karon, Madam bata ji daÉ—in fita da mukayi tare ba"
"Shikenan idan ba zaka iya min Alfarma ba, na fasa zuwa"
ÆŠan shiru Yusuf yayi yana nazari a ransa, tabbas Amal bata da wayo sosai, idan ya bugi cikin ta ze samu bayanai, dan haka ze iya shanye masifa da tsiwar Widad, a fili yace "shikenan kawo car keys É—in naki mu tafi"
Ta kalle shi tayi fari da ido tace "Dan Allah meye matakin karatun ka ne? Ka iya turanci Yusuf"
ÆŠan basarwa kawai yayi murmushi ya nufi inda motocin suke.
Wani Joint tasa ya kaita, tayi ordering Pizza da tea, ta tambayi Yusuf me zeci yace shi baya cin komai.
Yusuf ya kalleta yace "Wai ya naganki duk wata iri ne yau?"
Ɗan taɓe baki tayi tace "ba lafiya ba, shine ko ka tambayeni ya jikina? bayan a gabanka Widad ta ƙonani jiya ba abunda kayi, baka damu dani ba, Amma nasan saboda rashin lafiyar ta yasa kazo da wuri yau" ta ƙarasa maganar tana tura baki
Yusuf ya É—anyi Murmushi yace
"kiyi haƙuri, kinga bata da lafiya wani mataki zan ɗauka akanta? kuma kinga kaman mamanki da Yayar ki basa Son ina yawan shiga al'amuran gidan ku"
Amal tace "ba Al'amuran gidan nan ne basa son kana shiga ba, Al'amarin Widad ne da kake nuna damuwa dashi sosai ne basa so, ko baka ga Yadda take Wulaƙanta mutane ba?"
"Eh amma, ita ina maman ta ne take rayuwa ita kaÉ—ai?"
Amal ta ɗan taɓe baki tace "Kashe ta akayi fa, shine dalilin da yasa ta zama mahaukaciya bata son mutane"
Zare ido Yusuf yayi kamar besan komai ba yace "waye ya kashe ta?"
Amal ta taɓe baki tace "Oho wayasani? Kana gani dukda mahaifinta yana da kuɗi amma a binciko wanda yayi laifin abu ya gagara, shi ne ita kuma tace zata nemo wanda suka kashe mahaifiyar ta, akwai mutanen data sa aka kama aka kulle a prison ba tare data nada wata cikkakiyar hujja ba, dan haka itama ake farmakinta, sannan akwai wani abu da'ake so a karɓa a gurin ta wanda nima ban san komenene ba, Shiyasa nake gujemaka yawan Shiga lamarin ta bayan Aƙidarta ta Wulaƙanta mutane, duk randa ka bari wani kusanci me ƙarfi ya shiga tsakanin ka da ita, ba shakka za'a fara farmakin rayuwar ka domin za'ace kasan inda abunda ake nema a gurin ta yake, shine death Contract ɗin data gaya maka ai!!!"
IN AN KARANTA AYI SHARHI PLEASE
SANNAN AYI SHARE
07063065680
Ayshercool.
          Â
 Â
            _*AƘIDATA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
ELEGANT ONLINE WRITER'S
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in
           PART1
               Page 10
Shiru Yusuf yayi yana bin Amal da kallo, tare da nazarin maganganun ta.
"Waye ya kashe Mahaifiyar Widad? Me yasa aka kasheta!!? Meyasa ake bibiya da barazana ga dukkanin wanda yake da kusanci da ita!!!? Meye dalilin rushewar binciken wanda suka kashe mahaifiyar Widad? Meye Alaƙar kisan Mahaifiyar Widad da wanda Widad tasa aka ɗaure!!!? Meye alaƙar ciwon Widad da ƙwayar dake cikin tea ɗin da'aka kawo mata?
Wannan sune jerin tambayoyin da suka shiga kaiwa suna komowa a cikin ƙwaƙwalwar Yusuf.
Ta ɗago ta kalli Yusuf tace "let's keep this aside, Yusuf ka taɓayin budurwa? Ko kana da budurwa a halin yanzu?"
Jin tambayar Yusuf yayi wani banbarakwai, ta tuna masa da abu mafi ciwo a rayuwar sa da baze manta ba har ya koma ga Allah, ya kalle ta ya ɓoye damuwar sa yayi murmushi yace "Budurwa kuma? Wacece zata so talakan mutum kamata? Ni bani da wata budurwa ni kaɗai ne, ai nayi ƙarami inyi budurwa"
Murmushi tayi tace "ka fiye abun dariya, a haka kamar baka magana, Amma ka iya sa mutum dariya, yanzu babba da kai kace kayi ƙarami da budurwa?"
"Eh mana ko dan kin gani ƙato? Yarone ni ƙarami"
Ta sake yi masa wani murmushin tace "hmm Shikenan, kodai Widad kake so?"
Zare ido yayi kamar idon ze faɗo yace "Ni, rufamin Asiri, inani ina 'ya' yan manya, ai iyakacin talaka daku yayi muku aiki ku biyashi"
"Amma meyasa kake nuna damuwar ka a kanta haka? Dukda tarin wulaƙanci da rashin mutunci da take maka a wasu lokutan?"
"Saboda batamin wulaƙanci se idan na saɓawa umarnin ta, kuma mahaifinta yana matuƙar mutuntani, kuma kinga nine a ƙarƙashin
ta, dole inyi haƙuri da duk abunda zata yi min"
Amal ta numfasa tace "hakane, Amma ina shiga matuƙar baƙin ciki a duk lokacin da naga tana cin zarafin ka, shiyasa nake ganin meze hana ka ajiye mata aikin ta, in samo maka wani aikin ka huta da wulaƙanci?"
Yusuf yayi Murmushi yace "Inajin daɗin wannan aikin a hakan, bana so kiyi wani abu da ze ɓata ran mahaifiyar ki, Amma ina godiya da karamcinki a kowane lokaci, tunda kin gama, muje in sauke ki a gida nima in tafi, kafin Madam ta farga tare muka fita dake" yai maganar cike da ƙoƙarin basar da maganganun Amal
Amal ta jinjina kai ta miƙe, suka bar gurin.
***************************
"Bayanai sun sameni cewar, Akwai yuwuwar Bala ya tona mana Asiri, yayi iƙrarin cewa tunda aka kaishi prison babu wani ƙoƙari da muke dan fitar dashi, munawa kabmu ƙoƙarine kawai, dan haka na yanke shawarar in kiraka muyi wata magana, fatan zaka buɗe kunnenka ka saurereni"
"To Yallaɓai, ina saurarenka"
"Hashim, Abunda nake so da kai shine, So nake a zuba magani a Abincin daza'a bawa Bala, wanda ze sashi rashin lafiya, daga nan se a kaishi Asibitin doctor Mukhtar, a can nake so a ƙarasamin shi, a kauda shi daga duniyar gaba ɗaya dan baze ɓata mana shiri ba"
Hashim Yace "Amma Yallaɓai aikin nan fa yana da hatsari sosai, kasada ne me girma, idan aka gano da hannuna a ciki zan rasa aikina, kuma za'a kamani"
A hasle mutumin yace "Kowace irin kasada ce gara ayita matuƙar Sunana baze fito ba, bazan zuba ido suna na ya ɓaci a banza ba ba tare da na cimma burina ba, Amfanin Bala ya ƙare dan haka a kauda shi bashi da sauran amfani a gareni, kana da damar yin hakan, kana da dama a hannunka dan haka kayi yadda nace, tun kafin raina ya ɓaci"
Hashim yace "Amma Yallaɓai......
"Sadakin aikinka naira million biyu ne, idan ba zaka iya ba zan saka a gefe in saka wani yayi min, Amma kasani kaima bazan barka a doron ƙasa ba tunda kasan sirrina, tashi ka fita na gama magana da kai "
**********************
Widad ta koma normal kamar ba ita ba, dan haka Daddy ya fara shirin komawa saboda Ayyukan da yake dasu, sedai sun fafata da Widad sosai dan ya sake yi mata batun Aure, ita kuma ta ƙara tabbatar masa tana nan akan bakarta ba gudu ba ja da baya, hakan yasa suka ɗan samu saɓani, ya tafi ba tare da tayi masa rakiya ba.
Yusuf yaje ya tsananta bincike akan gano waye mahaifin Nurat, wadda suka je gurin birthday ɗinta shi da Widad, ya samu bayanin wasu abubuwan ne daga gurin Amal, wadda ta riga ta gama narkewa a ƙaunar Yusuf.
Mahaifin Nurat babban ɗan siyasa ne, sukan haɗu da mahaifin Widad a gurin kasuwanci, amma bayanai sun nuna akwai tsohuwar Alaƙa dake tsakaninsu wadda daga baya tayi rauni, 'yarsa da Widad sun haɗu a gurin karatu ne a ƙasar waje, ita kaɗaice ƙawar Widad a Nigeria, se
'ya'yan Alhaji Bulama, shima ba wata alaƙace ta kusa tsakanin su ba, dan bata yarda a raɓeta, ba kowa ke iya jure halinta ba.
Tsangwama ta yau daban ta gobe daban, haka Hajiya Halima, Ramla da ma'aikatan gidan suke nunawa Yusuf, shi kuma ko a jikin sa, aikin da yaje yi shi kawai yake.
Isa mai gadi yayi yayi yasan daga ina Yusuf yake zuwa, Amma fafur Yusuf yaƙi gayamasa, daga baya ma se ya janye jikin sa, bayan gaisawa babu abunda ke shiga tsakankanin su.
Wasa2 aka shiga wata na uku, Amma Widad bata biya Yusuf haƙƙinsa ba, shi kuma koda wasa be taɓa magana ba.
Yusuf yana zaune a harabar gidan yana danna wayar sa, daga sama yaji ance "Ssss" ɗaga kai yayi ya hango Widad ta saman bene, tayi masa alama da hannun ta yaje.
Yusuf ya miƙe ya shiga, tana zaune a falo tana cin gugguru, tana ci tana bawa magenta, Su Hajiya Halima na falon ita da su Ramla gaba ɗaya.
Yana shigowa Amal ta kalle shi tana kashe masa ido, seda yakusa faɗuwa dan gani yake gaba ɗaya sunga abunda Amal tayi, Widad dake kaɗa ƙafa tana kallon Abunda Amal tayi, bata tanka ba ta cigaba da watsa popcorn ɗinta.
Gefen kujerar da Widad ke zaune yaje ya zauna a Æ™asan carfet yaceÂ
"Gani ranki ya daÉ—e"
Ta kalle shi ta yamutse taceÂ
"Kai nifa bana son all such kind of names, Malam sunana Widad, ka dinga kirana da sunana"
Murmushi yayi mata tare da ɗan girgiza kai yace "Bazan iya ba, nafi jin daɗin ince Madam, ko ranki ya daɗe"
"to bana so, niba basarakiya bace, ka kira ni da sunana kawai"
"Aike kinfi basarakiya ma gimbiyar Daddynta"
Wani É—an guntun Murmushi tayi, wanda ita kaÉ—ai tasan ma'anar sa.
Wani uban tsaki Amal tayi wanda bata san ya fito ba, ta miƙe a fusace da nufin ta bar falon saboda haushi.
"Amal!" Widad ta kira sunan ta. cak ta tsaya ba tare da ta waigo ba.
"Me nayi miki ne?" Widad ta jefa mata tambayar
Fuska a cunkushe Amal tace "bakomai"
Murmushi Widad tayi wanda ya ƙara fito da kyawunta, tana girgiza santala santalan ƙafafuwanta, sannan tace
"Kin san Widad bata Soyayya, balle ince zan so abunda kike so, shi kansa Son ban yadda dashi ba balle inyi shi, koda zanyi so bazan so maƙasƙancin Mutum kamar direba na ba, balle inyi wani abu da zesa kiji haushi saboda shi, ki kwantar da hankalinki ba abunda zanyi da wannan abun, rainin hankalinsa da ƙwarin gwiwarsa gurin karyamin dokoki ne ke burgeni wasu lokutan, ban taɓa ma'aikacin da yake rainamin hankali da son yimin katsaladan a cikin lamaurana yadda yakeso kamarsa ba, wani abu dana fuskanta shine, ze iya jure duk wani hali da AƘIDATA, hmm ki huta beb ba wani abun damuwa a cikin abunda nake" ta ƙarasa maganar tare da wani murmushi na rainin hankali.
Yusuf ya kalli Widad, yaji haushin maganganun ta, ya ƙudurce wani abu a ransa.
Ta kalli Yusuf cike da kashedi tace "Kaikuma tara ka kawai nake, ina sane da duk abunda kake yi, ina gargaɗinka akan contract ɗin daka sawa hannu, Ni kaɗai na ɗaukeka aiki, ni kaɗai zakayiwa Aiki, idan har zakayi soyayya or what ever Rubbish you call it, kayishi bayan ka bar gidan nan, hope I made my self clear "
Yusuf ya jinjina kai, a fusace Mummy tace "Aikuwa se naci uban Amal akan yaron nan, ka kiyayi 'yata ba kai ba ita, banda tsiyar ɗan talaka ina kai ina Amal, ƙwarya tabi ƙwarya mana, wallahi duk lokacin da ka kuma shiga sabgarta sena saɓa maka"
"Cewa akayi ana sonsa bashi yace yana so ba, ko ba kya gani ne? Kina zaƙewa gurin ci masa mutunci wasu lokutan, na lura Daddy yana matuƙar ji dashi saboda biyayyarsa, yana girmama shi sosai, ko dan haka at least dole a ɗagamasa ƙafa saboda yana matsayi me girma a gurin megida, dan haka a dinga ɗaga masa ƙafa a dena son shiga hurumin dabe dace ba"
Ta kalli Yusuf tace "Aiken ka zanyi, kaje ɗakina, ka ɗauki key a drower mudubi, ka buɗe wardrobe ɗina ta ƙarshe, ka ɗakko ATM ɗina kazo"
Ba Hajiya Halima ba har Ramla da Yusuf seda suka kalle ta da sauri.
Ta basar ta maida hankali kan talabijin, kamar ba ita tayi magana ba, jiki a sanyaye Yusuf ya miƙe ya nufi ɗakin ta, gaban sa se faɗuwa yake, inda ta kwatanta masa yaje ya ɗau key ɗin ya buɗe wardrobe ɗin da tace.
Ramla ta kalli Widad tace "Amma Widad kamar be kamata kitura ƙato kamar wannan ɗakinki ba"
Widad bata kalle ta ba taceÂ
"gayamin abunda ya kamata Uwata"
Ramla taja bakin ta ta tsuke, dan tasan idan taja maganar se ranta ya ɓaci.
"Subhanallah" shine abunda Yusuf ya furta, dan bayan sutura dake cikin wardrobe ɗin Widad, hadda bandir bandir na kuɗi na Nigeria dana ƙasashen ƙetare.
A gagguce ya ɗau abunda ze ɗauka ya fita ya kai mata, maimakon ta karɓa se ce masa tayi "Kaje na baka hutu na sati ɗaya dan ba inda zanje a kwanan nan, ina so kaje da ATM card ɗin nan, ka cire kuɗi, ka siyomin latest trending phone me kyau guda biyu"
Yusuf yace "Yanzu zan siyo in kawo miki?"
Ƙura masa ido tayi ba tace komai ba, kallon gargaɗi take masa akan bata son rainin hankali, dan haja Yusuf ya girgiza kai ze fita, Widad tace "Ji mana" ya tsaya tare da waigowa ya kalle ta
"Yanzu idan na tambaye ka kasan inda rai yake, wace amsa zaka bani?"
Æoye mamakin tambayar da tayi masa yayi yace "Allah Mahalicci shikaÉ—ai yasan wannan Amsar"
Ta jinjina kai tace "Good you can go"
Hajiya Halima a gigice taceÂ
"Widad baki da hankali ne? Ya zaki bawa baƙo wanda baki san daga inda yake ba ki ɗau ATM wanda Account ɗin cike yake da kuɗi, Yallaɓai ma yana zuba dukiyar sa a ciki, kodan baki san zafin dukiyar ba sama taka aka tara aka baki, yanzu idan ya gudu yaƙi dawowa fa?"
"Kalma ta farko kin faɗi abunda ya dace a kaina, kin faɗa daidai ba kuskure, bani da hankali ni mahaukaciya ce kamar yadda kuka saba faɗa, dukiya kuma ta ubana ce, idan na salwantar da ita ba abunda zece tunda nima akwai tawa a ciki, ki dena tada jijiyar wuya akan dukiyar daba taki ba, idan tunanin ki abunda zaki samu bayan me ita ya mutu, sena tabattar da na ƙarar da komai kafin ya mutu koni na mutu, shine hanyar da zan baƙantawa masu harin dukiyar nan rai, and Mark you idan wani abu ya samu dukiya ta a yanzu to ba shakka kece, saboda babu wanda yasan da ATM ɗina a hannun sa seke da iyalanki"
Widad ta miƙe ta barmusu falon suna kallon kallo.
***********************
"Mummy, me yasa Daddy yayi yunƙurin sawa a sace Widad ne? Am so much Confused fa, tunda akayi abun nan ta bar gidan nan bata ƙara kirana a waya ba"
Mahaifiyar Nurat tayi ajiyar zuciya tace "Nurat nima ban sani ba gaskiya, ni banda yanzu da kika gayamin ma ban san abunda yake shiryawa ba, yanzu ina magana ze iya É—aukar mummunan mataki a kaina, kin san halin sa"
"Amma Mummy abun ya É—auremin kai, kinji yadda ya dingamin masifa dan na bari an É—auke ta, kuma fa wani ne yayi barazanar ze saceni nima in har ban gaya masa inda take ba"
"Mhmm Nurat, kija bakinki kiyi shiru da wannan maganar, dan muddin kika bari wani yaji maganar nan mun kaÉ—e a gurin mahaifinki"
"Insha Allah Mum ba wanda zan gayawa"
*************************
Tunda Yusuf ya tafi da ATM ɗin nan Hajiya Halima ke cikin zullumi, dan ba ƙaramar dukiya ce danƙare a account ɗin nan ba, tunani take yadda zata gano inda Yusuf yake, tasa a ƙwato mata ATM card ɗin nan.
Ramla ta aika ta kira mata Isa me gadi, ba tare da ɓata lokaci ba ya biyo Ramla jikin sa na tsuma zuwa falon Matar gidan.
"Kai wani irin sokon gara ne haka? Har yanzu ace ka kasa gano inda wannan talakan banzan yake?"
"Wallahi ranki ya daÉ—e ya dena zama a cikin mu ma, wani girman kai yake ji da shi, yanzu shi kaÉ—ai yake al'amuransa ko inda muke ya dena zuwa, iyakacinmu da shi gaisawa"
Dogon tsaki Hajiya Halima taja tace "dallacan sakarai ni rufemin baki, tashi ka bar nan sakarai kawai, ni na tsaya bi ta kanka, zan nemi wanda zasu yi min aikin".
Isa ya tashi jiki a sanyaye ya bar falon,
Mummy ta kalli Ramla tace "Ramla meye abunyi ne? Me ya kamata muyi?"
"wallahi Mummy kaina ya kulle, na rasa abunyi, yarinyar nan ta tabbata mahaukaciya, Mummy idan dukiyar nan ta salwanta ya zamuyi?"
Hajiya Halima tayi ajiyar zuciya tace "bana tunanin yaron nan ze gudu da ATM ɗin nan, Widad tana da wayo ze iya yuwuwa tarko tayi masa, Amma tunda harta yadda dashi haka, dole mu janyo shi cikin mu"
"Hakane Mummy zeyi mana Amfani, idan har ya kasance a ɓangaren mu, Ammafa kamar zeyi taurin kai gayen"
'idan yaƙi yin yadda muke so, then we should exact power over him, you know what I mean "
Ramla ta jinjina kai tare da yin murmushi tace
"Am proud of you Momma "
*****************************
Kwance yake akan makeken gado a wani tangamemen ɗaki me ɗauke da kayan alatu, ya mimmiƙe ƙafafuwan sa hannun sa riƙe da waya yana kallon hotuna. Gefen sa wani matashin ne zaune a gefen gado yana tattaɓa System.
Hotunan Widad ne akan screen ɗin wayar kala kala yana kallo yana murmushi, kowanne se ya tsaya yayi zooming ɗinsa ya ƙare mata kallo, yanayi yana shafa sajensa tare da tattausan murmushi, ga dukkan alamu yana jin daɗin kallon hotunan nata. A hankali ya furta
"Can't wait to see you darling"
Matashin da ke gefen sa ne ya waigo ya kalle shi yaceÂ
"Nifa ka isheni, se kace akanka aka fara Soyayya, kullum se kayi zancen yarinyar nan seka kalli hotunan ta, kuma ban taɓa jin ko waya kayi da ita ba"
Shafa sumar kansa yayi tare da yin murmushi yace "bazaka gane bane Fahad, yarinyar ce 'yar daru se hankali, dukda ƙanwa tace amma halinta daban yake, ina tunanin yadda zata karɓi soyayya ta idan na bayyana mata"
"saboda me kake wannan tunanin?"
"saboda tace shi kansa son bata yadda dashi ba"
Ƙyalƙyalewa da dariya Fahad yayi yace "Wallahi Anwar kana ruwa, se kace ita kaɗaice mace kaje ka nemi wata mana, dama da ganin ta zatayi izza, nifa rabona da ita tun tana yarinya ƙarama sosai"
Anwar yace "hmm tabbas da zaka ga Widad a yanzu ba zaka taɓa cewa in haƙura da ita ba, Ina matuƙar sonta, na ƙagu in koma gida, wallahi yadda na ƙagu in ganta be kai yadda nake son ganin su Amal da Ramla ba, gashi seka rigani komawa da sati biyu"
Fahad yace "lallai ka tsunduma da yawa, nima ina son in koma inga Ramla, dukda ni muna waya da chatting da ita"
"Aishi yasa nake ta Addu'a, Allah ya bani Widad a matsayin mata"
Fahad yace "Hmm Allah dai ya baka me sonka"
***********************
Gaba ɗaya hankalin Hajiya Halima yaƙi kwanciya, gashi duk wanda ze kaiwa Alhaji Nasir ƙarar Widad to lallai zasu ɓata, ranar kwana na bakwai da tafiyar Yusuf, Hajiya Halima se sintiri take tsakanin part ɗinta da babban falo, Widad kam ko a jikin ta shagalin ta kawai take.
Yusuf ne yayi Sallama a falon, Hajiya Halima na zaune a falon tun safe ta kasa sukuni seda Yusuf yazo.
Abunda ya É—aurewa Yusuf kai be wuce yadda yau ta sakar masa fuska ta amsa masa gaisuwar cikin mutunci ba.
Zeyi magana kenan yaji ƙamshin turaren Widad, wanda ya alamta masa ta fito falon, waiwayawa yayi ita ɗin ce kuwa cikin shigarta ta ƙananan kaya kamar yadda ta saba, bakin ta ɗauke da chew gum tana taunawa tare da lumshe ido, a hankali tana taku me ɗaukar hankali ta tako ta ƙarasa shigowa falon, ta samu guri ta zauna ba tare da tace komai ba.
Yusuf ya tako zuwa gaban kujerar da take zaune ya durƙusa a gabanta ze fara magana, katse shi tayi ta hanyar yi masa alama da hannun ta na ya zauna akan kujerar dake kusa da wadda take kai.
Seda ya É—aga ido ya kalli Hajiya Halima sannan ya tashi ya zauna yaceÂ
"Ranki ya daɗe ga saƙon"
Ya miƙa mata ledar wayoyin da receipt ɗinsu da kuma ATM card ɗin. Tasa hannu ta karɓa, ta buɗe ta ciro wayoyin manya masu kyau, ta jujjuya su a hannunta sannan ta kalli Yusuf tace "can i have your phone?"
Kallon ta yayi, tare da yin sororo
"are you deaf?" ta tambaye shi tana tsare shi da ido.
Ciro wayarsa yayi daga aljihu ya miƙa mata, Android phone ce, dukda ba wata me tsada bace Amma hoton sane da Ummansa akan wallpaper ɗin wayar, seda tayi nazarin hoton na wasu seconds sannan ta buɗe wayar Yusuf ta cire sim cards ɗinsa da memory ta haɗa da sabuwar waya guda ɗaya, da tsohuwar wayarsa ta bashi sannan tace
"i want see you tomorrow by 9:am Insha Allah, you will get your salary alert today, you can leave"
"amma ranki ya daÉ—e, wannan wayar ai tayi min girma, kuma..."
Ai ko kallon inda yake bata sake yiba ta miƙe ta nufi part ɗin ta.
Gaba ɗaya hankalin Hajiya Halima akan Yusuf yake, Yusuf ya fita daga falon, ganin bashi da wani aikin da zeyi ya sashi ya ƙudure tafiya gida, yana ta ƙara jinjina kyautar wayar da Widad ta bashi.
Yayiwa su Nura Sallama ya fice ba tare da ya gaya musu abunda Widad ta bashi ba, yana cikin tafiya kafin ya kai ƙarshen layin aka sha gaban sa da mota, tsayawa yayi cak yaga waye wannan.
Ramla ce ta fito daga motar tana masa wani irin kallo, ta kalle shi a yatsine tace "Nasan zakayi mamakin ganina anan, saboda bakamata mace kamarni ta tsaya tana ɓata yawunta akan talaka mutum maƙasƙanci kamar ka ba, sedai ita kasuwar buƙata idan ta taso tamkar guguwa take bata da shamaki, magana nake so muyi da kai me mahimmanci, wadda zata amfaneka, idan ba zaka damu ba ina so ka shiga mota muyi magana"
"talakan mutum maƙasƙanci a gurin ki, amma wataƙila me matsayi a gurin Allah be cancanci ya shiga motar mace me girman kai da tinƙaho ko ince tagumi da haɓar wani ba, bana buƙatar dukkan wani abun Amfani da ze taso daga gare ki komai mahimmancin sa kuwa, a gurin Allah nake nema dan haka ki bar abunki koma menene kuma komai amfaninsa"
"karkayiwa kanka gaggawa, ƙarshe kazo kana cizon yatsa, da da nasanin fatali da abunda ya tunkaro ka kayi masa shinge da riskarka saboda girman kai na banza, talakan mutum me dakakkiya zuciya irinka, zuciyarsa cike take buƙatar samun damarmaki, dama irin wadda kowa ke lalube a duhu ko a sarari, katsam se gashi ka sameta a sarari, Amma ka kasa ƙafa kai fatali da ita, me yasa kayi hakan? "
"lokaci abune me mahimmanci a gurina, ina bashi mahimmanci fiye da yadda kike tunani, zefi kyau ki taƙaita wannan dogon surutan naki marasa amfani, a cikin taƙaitattun kalmomi kimin bayani gwari gwari kamar yadda Uwargida Widad keyi, hakan zefi min sauƙi, kuma ze adana lokacin mu".
Wani kallon banza ta watsa masa sannan tace "ko Uwargida ko ubangida wannan kai ta shafa, ni daban ita daban, dama ta sameka amma ka watsar da ita a yadda kake gaka matashi har matashi, kai dai ba muni ba kuma ba nakasa ba, a wannan shekarun naka da ƙirar da Allah yayi maka kamata yayi ace kana wani ɗan ƙwalisa meji da kansa, katsam sega shi ka ƙare a direba, direban ma maƙasƙanci, kana tuƙa ƙaramar Yarinya tana cin zarafinka yadda taso, bata ganin gjrmanka da aikin da kake mata, da kasan maƙudan kuɗaɗen dake cikin Account ɗin nan da tabbas baka dawo gidan nan ba, dan da kai da talauci har gaban Abada, ba kaiba har 'ya'yan ka da jikokin ka ba zasuyi talauci ba, sedai kash garin yin gwaninta kayiwa kanka mugunta"
Yusuf yace "har yanzu jira nake ki faÉ—i abunda kike tafe dashi, na gaji da sauraren wannan salon maganar taki me tafiyar kura, kiyi gaba kiyi baya kamar kema baki yadda da kanki ba"
"Babu batun rashin yadda da kai sedai ina so muyi tarayya gurin temakon juna ne, ina son ka gayamin password ɗin Widad ne na banki, nayi maka Alƙawarin samun wani gwagwaɓan sakamako indai kayi abunda nace, hakan ze zama madadin wannan shiritar da kayi nayin wasarere da damar daka samu, kuma ze baka damar samun 'yantuwa daga wannan aikin dakake ƙarƙashin wannan Yarinyar me Baƙar Aƙida"
Wani irin kallo Yusuf yayi mata sannan yace
"dukda kasancewa ta talaka maƙasƙanci kamar yadda kuke kirana, Yusuf yafi ƙarfin karɓar abunda zaku bashi saboda wannan baƙin aikin da kuke so inyi, ku tara dukiya da guminku seku yi barazana da ita ko tinƙaho, Bana danasanin aiki na ƙarƙashin Widad, duk inda tayi faɗa ko tsiwa to tabbas an mata ba daidai bane, shiyasa komai tayi take birgeni, kasancewata meyi mata aiki be sa naji cewar ni maƙasƙanci bane, kasancewata me aiki a ƙarƙashinta na sani ƙara samun ilimin rayuwa, dan haka kece maƙasƙanciya da kika ƙallafa rai akan abunda ba naki ba, ni talaka ne me wadatar zuci, dukiyar Widad bata isa ta yanken talauci ba"
"haka kace ko, to shikenan zakaga abunda bijirewa buƙata ta ze haifar maka, ba dai shishshigewa wannan mahaukaciyar ka zaɓa ba, a haka zata ƙare a hauka, kuma death contract data gaya maka zaka ganshi dan kusancinka da ita tamkar kusancinka da mutuwar Kane, Akwai mutanen dake farautar mutane irin ka, wanda suka raɓeta, zasu cigaba da farautarka da bibiyar ka, zasu nemi wani abu a gurin ka, muddin ka gaza yi musu zaka ga abunda ze biyo ba, ka rubuta ka ajiye zaka ce na gaya maka, sakarai mara rabo kawai "
"Ke rabon ne yasa kike zaune a gidan mutane kina harin yin zamba cikin Aminci ai, dukda irin gata da sutura da akai muku"
Wani murmushi tayi me ciwo, badan Widad tana Wulaƙanta su a gaban Yusuf ba ya isa ya kalli idon ta ya gaya mata wannan maganganun, ta ɗaga ido ta kalle shi tace "ka faɗi abunda kake so a yanzu, amma ka saurari ƙalubalen dake fuskantar ka" ta shige ta kunna motarta ta bar gurin a guje.
SHARE PLEASE ðŸ™
Please pray for my Dad, he is sick
Ayshercool
07063065680
.         Â
           _*AƘIDA TA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
Special thanks to all members of my Association
Perfect writers Association may Allah subhanahu wata'ala bless our pens and grant us wisdom to write what will bring positive changes to our Community.
        Â
              PART1
                 Page 11
Bin motar Yusuf yayi da kallo harta ƙure, sannan a sannu yaja ƙafar sa ya ci gaba da tafiya abubuwa daban daban na yawo a kwanyarsa.
Maimakon ya tafi gida seya tsaya yayi sallar azahar ya wuce gurin aiki, office É—in Abbas ya tafi yaje ya tarar da shi yana tsaka da wani aiki, Abbas na ganin Yusuf yai murmushi suka gaisa sannan yaceÂ
"Yane mutmina? Akwai wani latest update ne?"
Yusuf ya ɗan ɓata rai yace "na baka abu kayi assisting ɗina kaƙi, seni nayi abuna bakomai nagode"
"wane abu kace inyi assisting ɗin naka naƙi?" Abbas ya tambaya
"Akan mahaifin yarinyar nan Nurat mana, Nace ka tayani bincike akansa amma ƙarshe ni nayi abina"
Dafe kai Abbas yayi yace "Sorry my man, wallahi aiki yayi min yawa na manta shaf"
"Shikenan amma ina tafe da Labari ne"
Abbas ya tattara hankalin sa yace "ina jinka, dama kamar kasan jiya Oga Suleiman yayi min maganarka"
Yusuf yace "Abbas ina kyautata zaton akwai sa hannun matar Mahaifin Widad a farmakin da'ake kai musu"
Abbas ya ture System ɗin gabanshi ya sake tattara hankalinsa yace "ta yaya kenan? Meka gano?"
Nan Yusuf ya gaya masa abubuwan da Su Hajiya Halima keyi, da kuma Yadda suka yi da Ramla"
Jinjina kai Abbas ya shiga yi yace "Lallai biri yayi kama da mutum, amma kaga Oga yana Abuja akan wani case, Amma idan hakane meye alaƙar iyalan Alhaji Nasir da Mahaifin Nurat?"
Yusuf yace "Abunda zan ɗora da bincike na akai kenan"
Waya ce ta fara ringing, Abbas da Yusuf suka shiga waige waigen wayar da take ringing ɗin, Abbas yace "kamar daga jikin ka ringing ɗin ke tashi fa"
Se yanzu Yusuf ya tuna an bashi sabuwar waya, hannu yasa ya É—akko wayar ya É—aga, suka gama magana Umma ce ta kira shi.
ssebayan Yusuf ya gama Abbas yaceÂ
"jar uba mutumina wannan latest phone ɗinfa? Miƙomin in ganta, yaushe ka siyi waya haka, kaida manyan wayoyi basu dame ka ba?"
Yusuf ya miƙa masa wayar yace "Widad ce ta aikeni na siyo mata wayoyi masu tsada guda biyu, ina kai mata ta bani wannan"
Abbas ya dinga jinjina kai yana jujjuya wayar yace "Lallai ka faso gari, amma kamata yayi ka siyar da ita kai sabgar gabanka da kuɗin"
"Idan kuma ta tambayeni wayar nace na siyar taji daɗin Yimin wulaƙanci ko?"
Abbas yace "A'a ba haka nake nufi ba, Ashe dai har yanzu halin nata na nan, ai kwanan nan Insha Allah zan ɓullo gurin naku"
"to nidai in kazo ka kula, karka sake ka gaya wa wani unguwar da nake, haka kurun sun matsa da son sanin daga inda nake zuwa, dan nima kaina ban yadda da mutanen gidan ba"
Abbas ya kwashe da dariya yace "ashe dai ta koya maka halin nata"
Alert ne ya shigo sabuwar wayar Yusuf dake hannun Abbas, zare ido Abbas yayi yace "Yusuf an turo maka kuɗi"
Yusuf yace "waye ze turomin kuÉ—i tsakiyar wata haka?"
"wallahi dagaske nake, dubu É—ari shida"
Miƙewa tsaye Yusuf yayi yace "ni a wa? Waze turomin kuɗi haka?tabbas anyi kuskuren lambar account"
Abbas yace "dakata, kuma ba uwaÉ—akinka bace?"
Shiru Yusuf yayi yace "to aini bata da Account number ɗina, sedai idan naje gobe in Allah ya kaimu in tambaye ta, Amma inma itace gaskiya kuskurene, Kaga Abbas se anjima akwai inda nake son zuwa"
Gaba É—aya Yusuf ya ruÉ—e, mamaki ya cika zuciyarsa yafi tunanin ko Ramla ce, dan tana son ta siye shi yayi mata aikin data keso? Amma daga rabuwarsu ta ina zata samu Account number É—insa?.
***********************
A mugun fusace Ramla ta koma gida, tana zuwa bata tsaya ko ina bs se É—akin mahaifiyar su, taje ta tarar da ita suna magana da Amal.
"Mummy akwai matsala fa"
"matsalar me?"
"Mummy this guy is very rude, we have to exact power over him, how dare will he look into my eyes and tells me that he won't do what i ask him to do?" ta ƙarasa maganar tana ta gauraya Numfashi.
"Kinga nutsu kiyi min bayani ya kukayi dashi?"
Ramla ta warware mata komai, Amal tace "da anyi shawara dani da baza'a tun kare shi ba saboda nasan ba zeyi ba, Mutum ne me kafiya da dagewa akan gaskiyar sa"
Cikin fushi Ramla tace "A beg shut up Malama, wayafi kafiya talakan banza mara amfani, ni ya tsaya ya kalli cikin idanuna ya cimin mutunci, shikenan dani yake zancen wallahi se nasa zaman garin nan ya gagare shi banza da kansa kamar lemo"
Amal tace "Wai kansa kamar lemo, kekuma naki fa"?
"dan Allah kuyi min shiru karku yi min faɗa anan, mafita ya kamata munema ba surutu ba, sannan Amal wallahi idan baki kiyayeni akan yaron nan ba sena saɓa miki fiye da tunanin ki wallahi, bazan taɓa aurawa maƙasaƙancin mutum ɗana ba, dan haka ki shiga hankalin ki, zaƙewar da kike masa tayi yawa "
Zumɓura baki Amal tayi ta bar ɗakin.
"Mummy inaga mubi Amal a hankali, tabbas son gayen nan take, Amma cikin hikima zata iya samo mana abunda muke so, ki dena yawan hantarar ta a kansa, karta zo ta bijire mana daga baya fa"
"Bazan bari alaƙar tasu tayi nisa ba, saboda yaron kalar mayaudaran mazane, yana da mu'amala me kyau, daɗin Soyayya ze iya sa Amal ta tona komai, kin san bata da hankali, Amma zan sanar dake mataki na gaba da zan ɗauka.
**************************
Safa da marwa yake yana kaiwa yana komowa a cikin wani matsakaicin Office, yana ta sake nanata maganganun da Oga ya gaya masa game da poisoning É—in Bala a prison, wani mutum ne yayi Sallama a office É—in yace
"Yallaɓai Hisham lafiya kake nemana?"
Hisham yayi ajiyar zuciya yace "Oga Bukar ne ya bada wani aiki, kuma muddin aka samu kuskure bamuyi ba ze halaka mu"
"Kamar Yaya? Wai shi meyasa be maida kisan kai komai ba saboda buƙatunsa? Wallahi nayi dana sanin sabga dashi"
"Kwantar da hankalin ka Bashir, mu lallaɓa muyi masa wannan aikin bisa Yarjejeniyar shine na ƙarshe, idan ya cigaba da takuramu, semu ma mu ɗana masa tarko"
Tsaki Bashir yayi yace "ina jinka, me kuma zamuyi masa?"
"yace so yake ayi poisoning ɗin Bala, yadda ze fara rashin lafiya, da an kai shi Asibiti kuma zesa a ƙarasa shi, saboda Balan yayi barazanar tona Musu Asiri, sun barshi a gidan yari tsawon shekaru takwas, sunƙi fitar da shi"
"wallahi Hashim mutanen nan basu da Imani, tsaf muma zasu iyayi mana abunda suka yi wa Bala, amma salin alin muyi abunda suke so, muna dafe kan madarar kawai zan ajiye aikin gidan nan in fece"
Hisham yace "shikenan but you have to focus"
Bashir ya jinjina kai ya fice daga office É—in.
*********************************
Dogayen kaya ne a jikin Yusuf, yayi kyau sosai ya shiga falon da sallama, ba'a amsa ba kasancewar ba kowa a ciki, ɓangaren Widad ya nufa kansa tsaye, yaje ƙofara falonta ya tsaya, tare da yin knocking.
Ƙasa ƙasa ya jiyo muryar ta tace "Come in" da Sallama ya shiga falon, tana zaune tana shan tea, ya kalleta yace "barka da Safiya ranki ya daɗe" jinjina masa kai tayi ba tare da ta amsa ba, ta cigaba da abunda take ba tare da tace uffan ba.
Haka ya shuÉ—e tsayin wasu lokuta yana zaune yana jiranta, ga shan tea É—in take kamar tana shan magani.
Yusuf ya gyara zama yaceÂ
"Ranki ya daÉ—e jiya naga an turomin kuÉ—i a account É—ina masu yawan gaske, ban sani ba koke ce, shine nace bari in tambaye ki"
"Kana expecting É—in kuÉ—i daga gurin wani ne?" tai maganar tana ajiye cup É—in hannunta
"A'a, bana yi" ya bata amsa
"Anyway salary É—inka ne na 3 months da ban baka ba"
Zare ido Yusuf yayi yaceÂ
"Amma sunyi yawa fa, ya zanyi da wannan maƙudan kuɗaɗen?"
"Zaka iya zubarwa, wannan kai ta shafa"
"A'a Madam, banyi aikin da zan karɓi wannan kuɗaɗen ba, sun yi yawa ban san....
"Kai É—an Yimin shiru mana, idan ban manta ba kafin in É—auke ka aiki na gaya maka salary É—inka, kasan sunyi yawa meyasa kace zaka yi aikin? A beg keep this aside follow me"
Tayi maganar tana miƙewa tsaye ta nufi bedroom ɗin ta, jiki ba ƙwari Yusuf yabi bayan ta.
Wardrobe ɗinta ta buɗe ta ɗakko wayar nan da tasa ya siyo, ta tako zuwa gaban Yusuf, sedai tana zuwa suka ji wani shock a tare, ƙamshin turaren da Yusuf yake yasha banban da wanda ta hana shi sakawa, amma muddin zata ji ƙamshi a jikin sa se wata kasala ta saukar mata.
Shikam Yusuf ƙirjin sa ne ya shiga bugawa da ƙarfi ba tare da yasan dalilin hakan ba.
Widad ta tattaro nutsuwar ta ta dube shi ta miƙa masa wayar, yasa hannu ya karɓa yana kallon ta, a hankali tace
"Yanzu misali a ce wannan wayar ranka ce, a ina zaka ɓoye ta?"
Yusuf yayi ajiyar zuciya yace "zan mata kyakkyawan ɓoyewar da babu wanda ze san inda take se Allah"
"Good haka nake son ka ɓoye wannan wayar tamkar na baka ranka, duk kusancinka da mutum karka kuskura yasan da wannan wayar a tare da kai, karka yarda da kowa, wannan wayar tamkar na baka ranka ne!!! ka kula da ita"
A diririce Yusuf yace "Amma me yasa zan kula da ita haka? Ban gane tamkar kin bani raina ba"
Ɗan taɓe baki tayi ta juya tace "bashi da mahimmanci kaji wannan a yanzu, saboda sanin hakan a yanzu tamkar sake jefa rayuwar ka cikin hatsari ne, let me tell you something, don't trust anyone, i repeat myself don't trust anyone, jeka ƙarfe biyar zan fita yau"
Yusuf ya jinjina kai yace "Amma kuɗin nan da kika bani wallahi sunyi yawa"
Widad tace "You can go, na sallame ka"
Yusuf yace "Amma ban san yadda zanyi da wannan maƙudan kuɗin ba"
Ba tare da ta kula Yusuf ba ta shiga ƙoƙarin rage kayan jikin ta zata shiga wanka, ba shiri Yusuf ya juya da sauri ya bar ɗakin, yana mamakin wauta irin ta Widad.
*********************************
Alhaji Musa ne zaune a falon sa, 'yarsa Nurat na kujerar dake facing É—insa ta sunkuyar da kai tana wasa da yatsunata.
"Wallahi Nurat na rasa me zan miki in huce, da tuni harkar nan ta kankama, amma kikayi mana wauta da hauka, idan abun da muke nema ya samu, se kinfini mora"
Murya na rawa da alama tana tsoron mahaifin nata taceÂ
"dan Allah kayi haƙuri, nima wani ne yace ze saceni idan ban nuna masa inda take ba"
"waye shi É—in?" ya tambaye ta a É—an hasale
"Wallahi ban san waye ba, nima bata gayamin waye shi ba"
"Ni zan gano ko waye inyi maganin sa, yanzu dole ki samo wata hanyar abunda zaki yi ta sake zuwa gidan nan"
Saurin girgiza kai tayi tace "Ai kasan ba zata ƙara yadda dani ba, wallahi kome zanyi ba zata zo ba"
A fusace yace "tashi ki bar nan, komai a kasa dake se kinyi wauta, ni nasan abunda zanyi"
****************************
Album guda na hotunan Widad yake dasu a System ɗinsa, ji yake kamar ya janyo kwanakin da ze koma Nigeria, kallon hotunan ta kawai yake hakan ke ƙara samasa nishaɗi.
Video call ya kira Mummy, Hajiya Halima na ganinsa tayi murmushi taceÂ
"'yan makaranta, lokaci ya kusa ko?"
Anwar yace "Eh Mummy se missing ɗinku nake, ina su Ramla ne"
"Suna nan gasu a kusa dani"
"shine ba zasuzo mu gaisa ba, dama ba nemana suke ba"
Amal tace "waze kira ka a kwashe masa kuɗi"
Haka suka dinga video call suna hira da 'yan uwan sa, can yace "Mummy wai ina Widad ne? Naji ance tana Nigeria kuma tunda nake kira bana ganin ta"
Tsaki Mummy tayi tace "Ban sani ba, ita ta haifeka koni? Idan bani kske nema ba shikenan, kullum baka da zance sena wanne banzar yarinyar?"
"yi haƙuri Mumsy, Yadda mahaifinta ya riƙemu ai senake ganin kamar babu laifi dan na tambayi inda take"
Ramla tace "Brother dan Allah karka ɓatawa mutane rai, waya ke maganar wannan mahaukaciyar"
Anwar yace "ni a ganina, Widad rashin me janta a jiki da kuma depression yasa condition É—inta ya zama complicated, amma...
Cikin tsawa Hajiya Halima tace " Rufemin baki dan uban ka, kaga ka kiyaye ni ko in ɓata maka rai, in baka son ɓacin raina karka sake Yimin zancen yarinyar nan, ko dan kai kana can baka san irin zaman da muke a gidan nan ba"
Ramla tace "ina ze sani, muna nan ta mayar damu kamar bayi, cin kashi kala kala, ana Wulaƙanta mu muda mahaifiyar mu amma kana neman ta"
Anwar yace "Amma Mummy....
A fusace tace "ke Amal katse min kiran nan, shashashan banza kawai"
Amal ta katse kiran.
Anwar ya turawa Amal message
"Amal É—an turomin lambar Widad"
Ta masa reply da "Taɓɗijan wa kake tunanin ze samu lambar wannan? Duk yadda kake tunanin abun ya wuce haka, ba ruwan ta damu fa"
Jujjuya message É—in ya dinga yi, babban abunda yake bashi takaici be wuce duk lokacin da ya kira Mummy, ya tambayi ina Widad seta balbaleshi da masifa, duk wanda ya tambaya ya bashi lambar ta kowa se yace bashi da ita, ya rasa meye dalilin hakan.
Yana wannan tunanin Fahad ya shigo ɗakin da sallama, ya kalli Anwar yace "Man what's wrong ne? Nayi sallama baka amsa ba"
Ɗan guntun tsaki Anwar yayi yace "Fahad, ni gaba ɗaya na kasa gane kan lamuran nan dake faruwa, duk lokacin da zamuyi waya da Mummy, idan har zan tambayi Widad se taita faɗa, babban abunda yake bani mamaki shine, wai ace duk gidanmu babu me lambar Widad balle ya bani"
Fahad yace
"Widad Widad Widad, kai dai baka da zance se wannan Yarinyar, please don't kill yourself mana, Nifa yadda kake bani labarin ta sam bata Yimin ba, nifa tun tana ƙarama yadda take wannan Share mutanen haushi take bani, kuma gashi da bakin ka ka gayamin tana da taɓun hankali "
Anwar yace " shut up please, tunda ba zaka bani shawara ba ka ƙyaleni, baka san yadda nake ji akan ta ba, kai kana soyayya amma kamar baka san meye son ba, Ni anya ma in baka Ramla zaka iya riƙe ta kuwa? "
Fahad yayi murmushi yace
"Anwar kenan, aini Soyayya ta da Ramla tana sona ina sonta, amma kai banda wahala babu abunda kake yi"
"Kai kaga wahala, ni bangan ta ba, Ni na ƙagu kamar in janyo lokaci in koma gida, gashi seka rigani komawa Nigeria"
"Allah ya baka lafiya Anwar, dan ga dukkanin alamu ta shafa maka haukan"
Shiru Anwar yayi ya miƙe ya bar ɗakin, dan Fahad ya fara baƙanta masa rai.
Widad tana ta shirin fita, wayarta ta fara ringing, hannu tasa ta É—au wayar tasa a kunnen ta, shiru ta É—anyi taceÂ
"Ok, thank you very much, send the address via my email" ta ajiye wayar tana ci gaba da shiryawa.
Maimakon ta fito seta tsaya ta saman bene tana duba lokaci, Yusuf ta hango ya fito da Mota yana ta gogewa dukda a wanke take, abun da ta fuskanta da Yusuf mutum ne meson tsafta sosai, baya son datti sam.
Message ne ya shigo wayar Yusuf ya É—aga ya duba.
"Ba'a wannan motar zamu fita ba, ka fita waje ka jirani"
Mamaki ne ya kama Yusuf, tabbas Wannan message É—in daga Widad ne, 'Amma yaushe ta samu lamba ta?' ya tambayi kansa, basarwa yayi ya mayar da motar, yana fita wajen gate yaga wata mota, ba dai me tsada bace dan kamar ma ta É—anji jiki.
Guri ya samu ya tsaya yana jiran fitowar ta.
Seda yayi kusan mintuna talatin kamar ance ya ɗaga kai ya kalli gate, ganin Widad ne yasa ƙirjin Yusuf bugawa da ƙarfi.
Wani arnen black leg jeans ne a jikin ta, da wata tied pitted blue body hook, tayi stocking ta saka beilt, ɗan ƙaramin baƙin veil ta ɗaure gashin kanta, dukda ƙasan gashin nata ya fito.
Google glass ne a fuskar ta baƙi, ga takalmi me matuƙar tsini, se 'yar ƙaramar jakarta, gaba ɗaya bazaka ce idan Widad ta buɗe baki zata yi hausa ba, duk wani shape da surar jikin ta ya fito.
Tabbas da Yusuf nada damar Mayar da Widad ta canza kaya da tabbas zeyi, dan haka kurum yaji takaicin fitar Widad a haka.
Ƙarasowa tayi ta miƙawa Yusuf key ba tare da tace komai ba, jiji a sanyaye ya karɓa, ya buɗe mata motar ta shiga ya rufe ya zaga mazaunin direba ya zauna, gaba ɗaya ƙamshin turaren da take ya cika motar, ya kalle ta yace
"Ina zamu je?" shiru tayi na ɗan wani lokaci sannan ta miƙa masa wayarta, yasa hannu ya karɓa ya duba.
Adress ɗin inda ze kaita ne, ya ɗago ya kalleta zeyi magana, amma yaga ta ƙara yi masa kwarjini, dan haka ya bata wayar ta ya kunna motar.
Yana cikin tuƙi wayarsa ta fara ringing, Umman Yusuf ne a jikin screen ɗin wayar, ya ɗaga wayar yasa a hansfree ya ajiye ta yace
"Umman Yusuf"
"ÆŠan gidan Umman sa, yau zaka dawo da wuri ne, an kawomin wani kifi tun daga Yobe, nayi maka farfesu ka dawo da wuri karya huce, ko kuma in cinye abuna"
Duk da ransa a dagule yake wanda ya rasa dalilin hakan, Amma seda ya maze yaceÂ
"Umman Yusuf, ai bazaki iya ci baki ajiye min ba, zan siyo gurasa yai akwai dinner me kyau"
Hirarsa yake yi da maman sa hankali kwance, se shagwaɓa yake yi kamar yaro ƙarami, Widad kuwa ƙura masa ido tayi ko ƙiftawa ba tayi, dukda ta cikin Glas ɗin idonta take kallon sa amma yadda yake wayar da Mahaifiyar sa ba ƙaramin birge ta yayi ba.
A ranta tace 'dama suma talakawa suna jin wannan shauƙin da ƙaunar na iyaye, inama Ammi na tana raye nima in kwanta a jikin ta in ji daɗi'
Ba tayi aune ba taji hawayen da bata shirya zubowarsu ba. Cire glass É—in fuskarta tayi tana goge hawayen idon ta, katse wayar Yusuf yayi ya kalleta yace
"lafiya dai?"
"Lafiya cigaba da tuƙinka, ina so muje gurin nan kafin 5"
Ya jinjina kai ya ci gaba da tuƙin, wani katafaren hotel ne, motocine suke shiga suna fita a ciki, kowa harkar gaban sa yake yi, sedai mafi akasari kallo ɗaya zakayi wa mafi yawa daga mutanen dake shiga suna fita, ka gano rashin tarbiyya da ta ido a tattare dasu, musamman matan duba da yanayin irin shigar dake jikin su.
Yusuf yayi parking yana kallon Widad, ta buɗe motar ta tsaya tana ƙarewa harabar hotel ɗin kallo.
Da sauri Yusuf ya fito daga motar yana kallon ta, ta dubeshi tace "wait for me here"
ta sa kai da nufin shiga cikin hotel ɗin, da yawa mazan dake gurin nan hankalinsu ya dawo kanta, Widad ta haɗu iya haɗuwa, wani takaici ne ya kama Yusuf, ace 'yar musulmi ce da wannan shigar a wannan gurɓataccen gurin.
Bin bayanta ya kuma yi da sauri, ta tsaya ta kalle shi taceÂ
"I said you should wait me inside the car, don't let anyone to see you here, don't tarnish your image because of me"
Ta sake juyawa, ba zato cikin zafin nama da zafin rai Yusuf ya riƙo Widad gaba ɗaya zuciyar su ta buga a tare, Yusuf ya kalli cikin idon ta yace
"Guri irin wannan be dace da mace me daraja kamar ki ba, Mahaifinki babban mutum ne be kamata aga 'yarsa a irin wannan gurin ba, ke mace ce kuma me daraja bekamata kowane gara ya dinga kallon surar jikin ki haka ba, think about it"
Nutsuwa Widad tayi seda ya gama tsaf sannan taceÂ
"Cikani tun kan in wanka maka mari a gurin nan, kai waye da zaka gayamin abunda ya dace dani? this is my life style not yours, dalla Cikani Malam kana ɓatamin lokaci ni"
A hankali Yusuf yace "I am musulm, ina kishin yadda mutane ke ƙare miki kallo a haka, kalli irin mutanen dake gurin nan, da yawan su karuwai ne fa da mutanen banza, shigarki bata da maraba da wanda matan gurin nan marasa daraja suka yi"
Cikin isa tace masa "koba maruwanci ba, Nima shi nazo yi, am prostitute karka ƙara shiga rayuwa ta, na gaya maks"
Ta juya ta shiga Hotel ɗin da sauri, wani baƙin ciki ne ya tokare zuciyar Yusuf, ya koma mota ya zauna yana tunani a ransa
'to wai kai Yusuf banda shisshigi ina ruwanka da ita ne?'
Wata zuciyar ta tambaye shi.
Yana nan zaune a mota kusan mintuna Arba'in, gajiya yayi da zaman motar ya fito ya zauna akan motar yana ƙurawa hanyar da Widad tabi ido.
Ba tsammani ya hangota tana fitowa, sedai fuskarta ɗauke da hawaye tana ta share hawayen da handkerchief, inda motar su take ta nufo idanunta jawur, wani ne ya biyo ta yana ƙoƙarin tsaida ita yayi mata Magana amma bata tsaya ba, tana zuwa ta buɗe motar ta shige.
Yusuf ya zagaya ya shiga ya kunna motar, gaba É—aya se yaji ya tsargu da yanayin daya ganta, gaba É—aya hankalinsa ya tashi "Are you ok?"
"Do you have any conscience with me being ok or not?" ta tambaye shi a hasale
"Yes i have" ya bata amsa, tsaki tayi ta É—auke kanta taceÂ
"drive very fast please" gudu sosai Yusuf yake amma azalzalarsa take wai ya ƙara gudu, kuma still bata dena kukan ba, kuka take me fallasa da tsantsar ɓacin rai da damuwa.
Guri Yusuf ya samu yayi parking ya juyo yana kallonta, ba tace komai ba tasa hannu a jakarta ta É—akko wayar ta, ta É—an daddana sannan ta saka a kunnen ta, tayi shiru na wasu 'yan mintuna sannan tace "Hello Daddy"
Yusuf baya jin me mahaifin Widad ke cewa, cikin kuka tace "please Daddy I want Flight back to U. K, i regret coming back to Nigeria, please Daddy talk to Bulama ask him to set up my visa"
Shiru ta ɗanyi sannan tace "Daddy don't take it for granted please, i can't define what happens today, dan Allah kace ayimin visa in koma"
"Daddy why? Kayi shekaru ba tare da ni ba se yanzu zaka ce baka so inyi nesa da kai? Karo na biyu ina neman abu kana ƙin Yimin, shikenan Daddy bayan ciwon Ƙwaƙwalwa am at risk of having cardiac attack" ta saki wayar ƙasa ta cigaba da kuka.
Yusuf ya cika da mamakin meyasa Widad kuka haka? Akwai buƙatar yasan me taje yi Hotel.
"malam kayi sauri ka maida ni gida, ka tsaya kana kallo na"
"Bazan iya tuƙin ba muddin zan cigaba da jin kukan ki" yai maganar fuskarsa ɗauke da damuwa
A hankali ta É—ago idanunta da suka yi jawur, ta saka ana Yusuf tana son gano gaskiyar abunda ya faÉ—a
"to meye haÉ—inka dani da kuka na ze dame ka, just drive ba ruwan ka da kukana, kayi abunda ke gabanka"
A hankali ya kunna motar, ya bata wuta ya cigaba da tuƙi, sedai gaba ɗaya hankalin sa baya jikin sa, yana can yana tunani daban daban.
Ihun Widad ne ya dawo dashi hayyacin sa, sannan ya lura da abunda ke shirin faruwa, duk yadda yayi ƙoƙarin kaucewa motar, seda me motar ya daki tasu.
Dafe kai Yusuf yayi yace "Subhanallah"
A fusace ta kalli Yusuf "Are you out of your sense, see how you ruin my life, kashe ni kake so kayi? Baka gani ne? Dama so kake ka kasheni, an haÉ—a baki da kai zaka kashe ni ko? Dama na sani"
Kafin Yusuf ya bata amsa tuni me waccan motar ya fito yana zazzaga bala'i, an lotsa masa mota se an biya shi.
Yusuf ya buÉ—e motar ya fita jiki ba Æ™wari, ya kalli mutumin ze kai shekaru Arba'in, Yusuf yaceÂ
"Dan Allah kayi haƙuri, birki ne ya ƙwacemin, kuma kaga traffic ta tsaida hannun ka amma baka tsaya ba, kuma ni na riga na taho da gudu, amma dai kayi haƙuri"
"Shut up my friend, ni zaka gayawa traffic ta tsaida hannu na? Titin naka ne kai kaÉ—ai da zaka dinga wannan gudun, banza shashasha kuma wallahi seka biya ni asarar da kayi min kokuma kaga abunda zan maka"
Tuni mutane suka fara taruwa, suka cika gurin ana ta bawa Mutumin nan haƙuri, dukda zagin da yakewa Yusuf amma haƙuri yake bashi, amma mutumin nan ya rintse ido yana zazzaga masifa yana cin zarafin Yusuf, hakimar kuwa ko fitowa ba tayi ba tana mota a zaune.
Yusuf yace "Amma naga idan laifi ne fa kaine kayi bani ba, Amma se baka haƙuri nake kana cigaba da cimin mutunci a gaban mutane, shikenan Yimin duk abunda zaka iya ka huce"
Yusuf dama gashi a cikin damuwa yake, ga shi ze zagin sa mutumin yake, aikuwa nan da nan temper É—insa ta hau zuciyar sa ta shiga tafasa, dan haka se yayi shiru ya dena cewa komai.
Mutumin ya cigaba da zazzaga masifa "Do you know who I am da zaka dingamin magana da gadara,? I will show you what am capable of doing, sena nuna maka ni waye, sena sa an sauke maka wannan rashin É—a'ar taka mara tarbiyya kawai"
"You are nobody More than stupid Malam, waye kai idan har kai wani ne bazaka tsaya kana É—aga murya akan wannan banzan gwangwanin motar taka ba, kayi abunda zaka yi an bige motar taka, ina son inga kai waye, kuma me zaka iya?"
Gaba É—aya suka juyo inda Widad ke magana da jajayen idanunta.
Mutumin ya kalli Widad yace
"Lallai ka É—akko karuwa a mota, dole ka É—agamin murya danka birgeta, zanyi maganin ku daga kai har ita"
Ya ciro wayarsa yana waya.
Yusuf a harzuƙe zeyi magana Widad ta ɗaga masa hannu alamar yayi shiru.
Ta ɗakko wayar ta tayi 'yan taɓe taɓe.
Mutane suka ja gefe suna son ganin ƙarshen dramar, mintuna kaɗan sega motar 'yan sanda, suka zo suna wuri wuri, mutumin ya nuna musu Yusuf yace "gashi nan shine, ku kama shi shida wannan koɗaɗiyar Yarinya me kama da sadakar Yalla"
Tuni É—aya daga É—an sandan yaje ya cakumo Yusuf, sedai me É—an sandan ya jiyo bindiga a jikin Yusuf!!!
SHARE PLEASE ðŸ™
__Masha Allah nagode da addu'oinku Daddy yana samun sauƙi Alhamdilillah nagode sosai Allah yasaka da alkhairi __
Ayshercool
07063065680
_*AƘIDA TA*_
PERFECT WRITERS ASSOCIATION
(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)
https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
P. W. A
*Story and written by*
_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_
The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *
I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum
https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=in
ELEGANT ONLINE WRITER'S