Complete Hausa Novels

Akidata Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Akidata_Book_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 6 of 8

Kashingiɗa Yusuf yayi yace  "kin daɗe baki yi ba, rashin mutunci wanne ne bakimin ba, ba wanda ban gani ba, dan haka duk wanda kika yi zan shanye amma ba zaki shiga gurin nan ba"

A cikin matuƙar hasala tace  "ka buɗemin ƙofa Malam, nima karuwanci nazo yi gurin nan ka ƙyaleni inyi rayuwar da naga dama"

"Aikuwa da ajinki ya zube beb, duk yadda kike yanƙwana gayu kizo nan kiyi karuwanci ba class, ki canza guri mana"

Wani ƙululun baƙin ciki ne ya tokare zuciyarta, wai ita Widad yau direbanta yake yanƙwanawa yana raina mata hankali yadda yake so, hakan be taɓa faruwa ba a tarihin rayuwar ta

"Naji ajin nawa ya zube, malam ka buɗen ƙofa nace"

Ramawa Yusuf yayi kamar yadda takewa mutane, yayi kamar baya jin me take faÉ—a.

Jikinta har rawa yake saboda masifa tana zazzagawa Yusuf faɗa, a zafafe ta miƙa hannu zata yi unlocking ɗin motar Yusuf ya riƙeta, a tare suka ji wata irin faɗuwar gaba, Jikin Yusuf har rawa yake dan besan yadda akayi ya riƙeta ba, yayin da nata ƙirjin ya dinga bugawa fiye dana Yusuf.

Tattaro Jarumtarsa yayi ya maida ita seat É—inta, ya saka mata seat belt yaja motar ya bar gurin.

Widad zata iya cewa tunda take bata taɓa haɗuwa da mutumin daya raina mata hankali kamar Yusuf ba, dukda yana matuƙar yi mata biyayya tabbas yau ya tsallake iyakarsa, da yasan me tazo yi a Club ɗin da be mata haka ba, dole ta nuna masa munin kuskuren daya aikata yau, bata kuma ce masa uffan ba.

Ta naji tana ganin ya maida ita gida, zuciyarta na cigaba da tafasa kamar ta tsaga ƙirjinta.

Seda suka koma gida sannan yayi parking, ya fito ya buɗe mata ƙofar motar, ta fito ta tsaya ta saka idonta a nasa tace

"ban taɓa sanin baka da hankali ba se yau, kana tunanin na manta da contract ɗin daka sawa hannu? Harka samu damae da zaka nunamin ban isaba, saboda jahilci da rashin tunani irin na talaka, kasan me na jeyi gurin? Har zaka nunamin isa da Izza, ina ruwanka dani meyasa kake son zaƙewa cikin al'amuran rayuwa ta?, ko dan ina ɗaga maka ƙafa shiyasa kake ƙoƙarin takani, yau zan nuna maka ka saɓamin doka kuma dole ka karɓi hukuncin abunda kayi, banza mara amfani ka lalata min komai saboda Jahilci da son nuna kai wani ne, kamin hauka da wauta ka wargazamin komai saboda ƙaramin tunaninka, Amfaninka shine kamin aiki in biyaka amma ka zaƙe, dan haka zan nuna maka kai ba wata tsiyar bane a gurina kuma ka tsallake gona da iri "

Shiru Yusuf tayi seda ta gama sannan ya kakmeta yace " da bani da amfani da Allah be halicceni ba, babu wata halitta da Allah yayi wadda bata da amfani, tunda bani da Amfani zan ƙyaleki ki amfani kanki, tabbas da Allah yayi kowa me kuɗi da babu wanda zeji daɗi, kuma babu wanda ze mori wani, talaka yana da amfani, muma ba laifi mukayi wa Allah yayi mu a ƙarƙashin ku ba"

Yasa hannu a aljihunsa ya ɗakko key ɗin motar, ya kamo hannunta yace "bani da Amfani, dan haka ki nemo me Amfani ya cigaba da yi miki aiki, idan harni ɗan halak ne bazan ƙara miki aiki ba, ga mukullayenki nan talaka mutum ne kuma yana da zuciya tunda iyayene suka haifemu kamar yadda aka haifeki"
. Ya ɗanƙa mata key ɗinta a hannu, jifa tayi da mukullayen tace "baka isa ba, wallahi yadda kasa hannu a takardar yarjejeniyar ka fara aikin seka kammala shi, se anje ƙarshe da kai"

"sedai ki nemo me Amfani yayi miki amma bani ba"

cikin gida da sauri, hakan yayi daidai da shigowar motar Anwar.

Tana zuwa ɗaki tayi jifa da kayan hannunta ta shiga sintiri hawaye na bin idonta tace  "shikenan babu wanda ze fahimci halin da nake ciki? Wannan banzan ya ɓata min shirina ya wargaza komai, me yake tunani ne? Har na bashi damar daze shiga rayuwata haka ya yanke min hukunci, yanzu ina hukunta shi kuma Daddy ni ze ɗorawa laifi"

Anwar ne ya shigo da sauri ɗakin yace  "Widad lafiya kuwa? Meke faruwane?"

Girgiza masa kai tayi tace "bakomai"

"a'a ya bakomai naga kamar kuna cacar baki da direbanki, kuma gashi kina kuka meyafaru"

Shiru tayi masa ta wuce kan gadonta tayi zamanta.
Kusa da ita yaje ya zauna yace  "dawowata naga abubuwa daban daban wanda suka bani mamakiba gidan nan, wanda ban gane kansu ba, gashi Daddy yace wai Aure ze miki, meyasa zaki Auri Fahad"

Kallon Anwar tayi amma taƙi cewa komai.

"Say something please"
Lumshe ido tayi taƙi magana, duk yadda Anwar yayi taƙi magana haka ya ƙyaleta ya bar ɗakin jiki ba ƙwari.

Yusuf kam har ya koma gida zuciyarsa na tafasa, wai shine mara Amfani a tarihin rayuwarsa babu irin kalar cin zarafin da ba'ayi masa ba ya jure, Amma yau na Widad yaji zafinsu sosai.
Haka ya ƙarasa gida, Umma ta lura tunda ya dawo baya walwala sosai dan haka tace  "tilo meke faruwane? Naga kamar ranka a ɓace yake"

"bakomai Umma"

"bana son fulatanci fa, ko kana da wanda zaka gayawa damuwar ka bayan ni?"

Girgiza kai yayi yace  "Umma na rasa abunyi gaba ɗaya, Anyiwa Abbas transfer, yarinyar da nake wa aiki mun samu matsala na ajiye aikin, gashi ban sanar da shugabanni na ba kafin in yanke hukuncin, kuma ba aikin direba kawai nake mata ba kare lafiyar ta nake, ba ƙaramin hatsari take ciki ba ga mahaifinta wai Aurar da ita zeyi, Umma abubuwan dayawa nama rasa me zanyi "

"Allah sarki Jarumin ɗana, tun tasaowarka da jarumta na sanka da juriya meze sa ka karaya a wannan lokacin? Ni kaina ina jin tausayinka amma kasa Allah a lamarin ka sannan kayi haƙuri da komai, ɗaukaka bata zuwa ana kwance ba zato Aka ƙara maka matsayi a gurin aiki, jajircewarka ce tasa suka baka, dan haka ka zama Jarumi Yusufa, nan gaba iyali zaka riƙe kaga zama da mata se kayi haƙuri se Jarumin gaske, lokuta da dama bama gane Amfanin mutum se bayan ya matsa daga kusa damu"

Kallon Ummansa yayi yace  "wani irin iyali kuma?"

"kayi Aure mana kaima ka hayayyafa, nima inga jikokin tilon É—ana"

Girgiza mata kai yayi yace  "na yanke ƙauna Umma, kiyi haƙuri mu ƙarasa rayuwar mu a haka, nima na isheki"

"haba Yusuf, me rai ai baya yanke ƙauna daga rahamar ubangiji, dole kayi Aure wataran"

"Umma bana son tarihi ya maimaita kansa, bana son abunda ze sake É—aga mana hankali, dan haka mu bar wannan maganar seda safe"

Ya miƙe yana tafiya a hankali ya bar ɗakin, Umman Yusuf ta dafe kai tace  "Allah ka kawo mafita da sauyi na alkhairi ga rayuwar wannan bawa naka, Allah ka kawo masa mafita ka yaye masa damuwarsa"

Yusuf ya kashe wayoyinsa gaba É—aya, baya fita ko'ina kullum yana gida, Dama bashi da wasu abokai a unguwar, dan haka baya zuwa ko ina.
Umma bata takura masa ba ta ƙyaleshi.

Widad kam tun daga ranar ko falo ta dena fitowa, Daddy kam dama ba shiga harkarta yake ba, se bayan tafiyar Yusuf ta gane Amfaninsa ta ɓangarori daban daban, gashi taga dagaske Yusuf ya dena zuwa gidan kwata kwata.

Haka nan Alhaji Nasir yaji ya damu da son ganin 'yar tasa dan ba ƙaramin missing ɗinta yake ba, yanzun ma ya danne zuciyarsa ne kawai dan ya samu ta saduda amma abun ba sauyi.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.