Complete Hausa Novels

Akidata Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Akidata_Book_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 5 of 8

Cigaba da Ƙarasowa Widad tayi, Yusuf na bayanta da jakarta a hannunsa, tana kallon Fahad suka zo zata wuce shi
"Widad Nasir Daula" Fahad ya kira sunanta.

Ta tsaya cak bata juyoba tace  "Fahad Bulama"

"Amma kin san gurinki nazo kina kallona zaki wuce ki tafi"

A hankali ta juyo cike da izzarta ta ban mamaki, ta ƙare masa kallo sannan tace  "banyi tsammanin kaine Fahad ɗinba ai, na ambaci sunan ne dan tabattar da kai ɗinne ko ba kaiba, dan abun da mamaki ace kaine Fahad ɗin, ina jinka faɗi abunda ke tafe da kai"

Fahad ya jinjina kai yace "tun É—azu nake gidan nan ina jiranki, meze hana mu shiga daga ciki mu samu guri mu zauna se muyi magana"

"bani da wannan lokacin, yi maganar ka anan inajinka" ta faÉ—a tana kallon Idon Fahad.

Fahad be taɓa zaton haka Widad take ba, ta kai mace har mace sedai tana da girman kai da izza.

Ya kalli Yusuf yace  "Amm ko zaka iya bamu guri, zamuyi magana"

"Ko da Bulama zanyi magana agabansa ake yi, dan haka cigaba da maganar ka" ta faÉ—a cikin isa

"Amma kin san Aure zamuyi, meyasa zaki dinga gayamin magana haka ba respect, har ki dinga kiran sunan mahaifina kai tsaye"

"Anƙi ayi respecting ɗin naka, Babana ma ina faɗar sunansa balle wani Bulama, kai a tunaninka  kai namijin daze tunkareni a matsayin wadda ze aurane?, ɗan sake kallon kanka mana sannan ka kalli da wadda kake magana kasan niba ajinka bace, haka Bulaman be gaya maka yadda mukayi da shi bane? Bana soyayya ban yadda da ita ba kuna ba zanyi Aure ba, ana ƙoƙarin cusamin kaine kawai kuma bani da ra'ayin Auren namiji irinka, dama ka kai Namiji ne zan iya maleji, amma sam baka da ƙira da zatin da za'a kalleka a kiraka Namiji balle ace mijin Widad, ka sani koda ace Widad nada ra'ayin Aure bazan taɓa zaɓarka a matsayin miji ba, banga alamar nagarta da kamala a tare da kai ba, idan kana da zuciya kaje ka gayawa Babana Bulama baka son haɗin Auren nan, 'yar tasa bata sonka, in baka da ita kuma kace masa kana son Auren kaga yadda zamu ƙareta da kai "

Aiba Fahad ba hatta Yusuf jikinsa yayi sanyi da wannan mummunan cin zarafi da'akayi wa Fahad, koba komai É—an uwansa ne namiji.

Gaba ɗaya Fahad kasa magana yayi, be taɓa tunanin haka Yarinyar nan take ba, duk wadda za'ayi sedai ayi amma seya auri Widad, sedai hakan yayi sanadiyyar ɓatawarsa da Anwar, ze tabbatarwa da Widad shi Namiji ne, Namijin ma irin wanda kowace mace keda burin samu, be tsaya ba ya shige motarsa ya fice.

Yusuf yana diving ya kalli Widad data cika tayi fam yace  "Madam amma kamar abunda kikayi wa wannan bawan Allah be dace ba, bakya tunanin ya Alhaji zeji idan yaji labarin abunda kika yi, baki kyauta ba

"Yoseef!!!"  karo na farko da Widad ta kira sunansa cike da gargaɗi, koda wasa bata taɓa attempting kiran sunansa ba, danshi be zaci tasan sunan nasa bama, sannan yadda ta faɗi sunan nasa yasha banban da yadda ake kiran sunan nasa, dukda Wasu lokutan hausa bata isheta ba, idan ta faɗi wani abun yasha banban da yadda ake faɗa.

"karka kusakura in dawo kanka, meyasa kake son shiga rayuwata, ban taɓa ganin mutumin da nake ɗagawa ƙafa kamar kai ba, shiumrun da nake maka Albarkacin mahaifina kakeci, kar in ƙara yin abu kace zaka yi challenging ɗina, duk abunda kaga nayi inada dalili karka ƙara challenging ɗina if not i will teach you a lesson you never forget "

Tai maganar a matuƙar fusace cike da gargaɗi.

" Allah ya huci zuciyarki, Allah ya baki haƙuri insha Allah ba zan sake ba"

Ya kaita gurin saloon kaman yadda ta buƙata.

Ramlah tayi kuka sosai akan wannan wulaƙanci da Widad tayi mata, seda idanunta sukayi jawur saboda kuka, ƙanwar bayanta dan kawai suna zaune a gidansu ake musu wannan wulaƙancin haka.
Mummy ta tako tazo gaban gadon Ramla ta zauna ta dafata tace  "Am sorry daughter nasan....

"Mummy dan Allah ki ƙyaleni wallahi wannan karon sena ɗau mataki, haba abun ya isa haka wace irin rayuwace wannan muke a gidan nan se kace zamanin Bayi, wallahi sena ɗau matakin daya dace"

"A'a Ramla tynda kikaga na haƙura ban ɗau mataki ba kema haƙuri zakiyi, karki ja mana Asara goma da Ashirin, kin san taɓa wannan yarinyar dai dai yake da kawo ƙarshenmu a gidan nan"

"Niba ita zan taɓa ba, wannan sakaran zan nunawa kuskurensa, se yayi dana sanin zuwa gidan nan, zega abunda zan masa"

******************************

Alhaji Munir, Musa, Haruna se kuma Sale ne zaune a katafaren Falon suna tattaunawa, kana ganin fuskokinsu zaka san abunda suke tattaunawar yana da matuƙar mahimmanci a gurinsu.

Nurat ce ta shigo falon bakinta É—auke da Sallama tana É—auke da manyan kuloli a hannunta.

Gaba ɗaya suka bita da ido, kanta a ƙasa ta ƙaraso cikin falon ta durƙusa tana gaishesu, Amsawa sukayi gaba ɗaya Alhaji Munir yace  "wai yanzu Nurat ce ta girma haka, gaskiya babu zumunci yakamata ace yaran nan suna zumunci suna a tsakaninsu"

Alhaji Haruna yace  "gaskiya kam danni banda yanzu ma ban santa ba"

Nan sukayi ta surutunsu, yayin da Saleh yake gefe yaƙi cewa komai, Nurat ta gana hada hadar kawo musu Abinci ta juya bar falon.

"Wai kai Saleh bazaka saki jiki damu bane? Akwai fa riba a harƙallar nan" cewar Alhaji Musa

"Niba ribar ce a gabana ba É—an uwana ne a gabana, yana gadon Asibiti kunsa an bashi guba ku kuma kuna nan kuna cin Abinci"

Alhaji Haruna yace  "to kuka kake so muyi? Wallahi idan asirinmu ya tonu dagamu harshi sedai wasu bamu ba danme zamu bari ya fallasamu"

"shikenan a rayuwa kenan kowa kansa ya sani"

"ƙwarai kuwa ka bari harƙallar nan ta faɗa, idan ta faɗa ka samu kasanka seka fiddashi"

Alhaji Musa yace  "Wasan yana dab da zuwa ƙarshe indai abunda muka tsara ya tafi daidai"

Alhaji Haruna yace  "ƙwarai kuwa"

Suka maida kai suka cigaba da hirarsu yayin da Saleh gaba É—aya abun duniya ya dameshi.

***********************************

Gaba ɗaya a sukwane Fahad ya koma gida, se huci yake kamar wani fusataccen kumurci, a falo ya tarar da mahaifiyarsa da ƙannensa, yazo ze wuxe fuuu Hajiya Sarah ta miƙe da sauri tace  "lafiya kuwa Fahad?"

Ya daki kujera yace  "harni za'a kalla ace ban kai namiji ba? Me take taƙama dashi ne haka? Ni Fahad Bulama har akwai Yarinyar da zata kalleni taci zarafina, dan kawai tana da kuɗi, toni na ganta kuma ina sonta sannan zan nuna mata ni cikakken namiji wanda mata je rububin samu!!! Meta taka da harta ke wannan izgilin da cin zarafi ga mutane?  "

"kuɗi yaro wanda hausawa kance masu gidan rana, tabbas Widad ko ba ran Mahaifinta tana da kuɗin da zata taka wanda taso, kar ka manta da bazarsu muke rawa Fahad, ina son saka alkhairi ne da alkhairi shiyasa nake ƙoƙarin haɗaka Aure da ita, karka kusakura inji kayi mata wani abu wanda ze ɓata ranta kona mahaifinta, bazaka taɓa gujewa wannan Auren ba"
Alhaji Bulama ne tsaye a ƙafar benen dake falon, yana wannan maganar

" dan tana da kuɗi, kuɗin banza kuɗin wofi, akanta aka fara arziki? Aiko da ance a gujewa Auren bazan guje masa ba ina sonta tayi min, amma wallahi na aure ta she must pay for what she did, kai kafin in Aureta ma zan Wulaƙanta ta wulaƙanci mafi muni wallahi ni za'ayiwa cin zarafi irin wannan bata isa ba Wallahi "

Ya juya ya bar falon a matuƙar fusace

Hajiya Sarah cikin masifa tace " Alhaji seda nace maka bana son wannan haɗin, kawai ka kaimin yaro ana Wulaƙanta shi daga dawowarsa yaje gurinta zata ci zarafinsa haka, yarinya babu tarbiyya babu ta ido, na gaji da wannan abu"

"maza ki ziga shi, wallahi duk wanda yayi yunƙurin kawowa auren nan cikas zega matakin da zan ɗauka, sannan kija masa kunne, wallahi idan yayi yunƙurin yi mata wani abu ta ɗaureshi wallahi ba zan sa baki a sake shi ba, kinji na gaya miki ku bar komai a hannuna nasan matakin da zan ɗauka"

Yai maganar tare da barin falon ya koma benensa

Yusuf kam tunda aka masa warning yaja bakinsa ya tsuke har sukaje suka dawo be kuma cewa komai ba, amma yana jinsa a ƙoshe saboda garar da ya kwasa yau.

Se bayan isha'i ya baro gidansu Widad, yanata sauri ya koma gida

Ba zato kawai yaga an saka masa wuƙa a saitin Ƙirjinsa, tasayawa yayi cak ba tare da yayi yunƙurin guduwa ba.

Kamar waccan ranar mutanen da suka tareshi ne suka sake tareshi.

"munzone dan mu cigaba da jadadda maka har yanzu muna bibiyarka, muna jiran karɓar wannan abun daga hannunka muna nan muna cigaba da sa maka ido da duk wani motsinka"

"Wai wani abune wannan kuke son karɓa? Ku gayamin in karɓo in baku ku ƙyaleni"

"An gaya maka bamu da lissafi ne? Ba zamu gaya maka menene ba, amma da zarar ka samu abun zamu sani, kuma zamu biyoka mu karɓa"

Suka koma cikin motarsu suka tafi, sedai sunyi ganganci dan tuni Yusuf ya É—auke lambar motar akansa.

Yau yaci sa'a basu dake shiba suka tafi suka barshi, gida ya tafi yana tunanin meye wannan abun da'aka damu se an karɓa a gurin Widad.

A haka har ya ƙarasa gida, Seda ya zauna sukayi hira da Ummansa dukda abubuwa sun cunkushewa ƙwaƙwalwarsa.

Ya gama cin Abinci ya tafi É—akinsa, dole zeyi tracking É—in lambar motar nan ya gano motar waye.

Da ya koma gida Ummansa taita mita akan daren da yake kaiwa a waje, yaita bata haƙuri yana rarrashinta sannan ya tafi ɗakinsa, ya nutsa a duniyar tunani sosai wayarsa ta fara ringing.
Lambar Sakina ce kamar kar ya É—aga, sekuma ya É—aga yasa a kunnensa tare da sallama.

"Yusuf baka yi bacci ba?"

"Eh banyi ba" ya bata amsa a taƙaice

"dama magana nake so muyi"

"Amma kinsan dare yayi ko?"

"eh nasani, maganar tana da mahimmanci ne a gareka"

Yusuf yace  "to ina jinki"

"Yusuf akwai buƙatar ka dinga taka tsantsan da wasu abubuwan, akwai mutanen da suke nuna suna tare da kai amma a bayan idonka suna cin dunduniyarka, ba kowane mutum ne aboki na gaskiya ba"

Yusuf yace  "nifa bana son irin wannan ƙananan maganganun, ni ina zaune da kowa lafiya"

"ba ƙananan maganganu bane ba, ka dai yi a hankali sannan karka yadda wani yasan sakamakon binciken da kake komai kusancinka dashi in ba yallaɓai ba shawara ce yakamata ka kula"

"Shikenan nagode" Yusuf ya faɗa cike da ƙosawa, shi sam baya san abunda ze haɗa shi da Sakina baya son mace mara kamin kai sam.

Amma nazarin maganganun ta  ya shiga yi, wayarsa ce ta sake ɗaukar ringing har yayi tsaki ze kashe wayar yaga lambar Alhaji Nasir.

Cikin ladabi ya ɗaga wayar suka gaisa da Baban Widad, Alhaji Nasir yace  "Yusuf meyefaru ɗazu da Fahad yazo gurin Daughter"
. Cikin kame kame Yusuf yace  "Amm.. Yallaɓai yazo sun gaisa"

"Yusuf karka kareta, ka gayamin gaskiya me tayi masa? Wace irin karɓa tayi masa?"

"da alama dai beyi mata bane, ta É—an dai nuna masa bata sonsa ne"

"Yusuf karka fara ƙarya saboda ka kare uwar ɗakinka, Bulama ya tabattar min da wulaƙanci tayiwa Fahad, kuma nasani zata aikata na kiraka ne dan in tabattar, saboda zan ɗau mataki na ƙarshe daya dace da ita, duk abunda nake dan gyaran rayuwar ta nake amma ta kasa ganewa, dan haka zan ɗau matakin da bata taɓa zata ba akanta wanda ze kasance hukunci na ƙarshe da zan yanke akanta "

Domin gyara sharhi ko shawara, feel free to contact me
Ayshercool
07063065680

                       _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 19_20

Gaba ɗaya Yusuf ya dirircei yace  "Amm... Amma Yallaɓai wani mataki zaka ɗauka haka akanta, ina fatan ba wanda ze mata tsauri bane?"

"Yusuf kenan, ka damu da al'amarin Widad haka nan naji na yadda da kai, shiyasa har nake saka a cikin abunda ya shafi rayuwar mu, na yanke shawarar tsayar da ranar Aurenta a ƙarshen wannan watan zuwa farkon wata me kamawa"

"Amma yallaɓai baka ganin hakan ze sake jefa rayuwarta cikin hatsari, duba da yadda babu Aure a tsarin Rayuwar ta?"

"Yusuf, Widad fa mutum ce kuma lafiyayyiya tana ƙin Aurene saboda wasu dalilanta da suke masu rauni a gurina, bana so in mutu in barta cikin kaɗaici, nasan Bulama baze taɓa barin ɗansa ya Wulaƙanta Widad ba ko bayan raina, dan Allah ka cigaba da yimana addu'a, Amma insha Allah ko ba taso zan ɗaura mata aure karo na farko a rayuwata da zan ɓata mata rai, amma ina fatan hakan ya zama alkhairi a gareta, Insha Allah gobe zuwa jibi zan dawk"

"shikenan Yallaɓai, Allah ya tabattar da alkhairi ya dawo da kai lafiya"

"Ameen Yusufa nagode sosai"

Tunda sukayi Sallama da mahaifin Widad abun duniya ya damu Yusuf, ji yake matakin da mahaifin Widad ke shirin ɗauka tamkar ƙarasa rugurguza rayuwar uwar ɗakinsa ne gaba ɗaya, matakin yayi tsauri sosai, haka nan yaji wani irin matsanancin kishi na taso masa game da Widad ɗin.

Dafe kansa yayi tare da faÉ—in "Innalillahi wa inna ialaihi raji'un, Allah ka tsareni da sake faÉ—awa hatsarin Soyayya, Allah yasa tausayinta kawai nake ji, tabbas idan na fara son Widad zan shiga matsala fiye da wadda nasha a baya"

Bacci kam se Ɓarawo ne ya kama Yusuf.

Kwana biyu a tsakani Yusuf yana zuwa gidansu Widad amma ba wani aiki da yake yi, kuma sam baya ganinta.

Abubuwa sun ƙara cakuɗewa Yusuf, tunani kala kala a zuciyarsa amma zuciyarsa tafi fargaba akan hukuncin da Daddy ya yanke ɗauka akan Widad.

Ya ɗakko wayarsa yana ɗan duddubawa kawai yaga message ya shigo wayarsa, anyiwa ma'aikata canjin gurin aiki ciki harda Abbas, an maida Abbas aiki a kudancin Nigeria, abun ya ɗaurewa Yusuf kai sosai, mafi akasari anfi yin wa mutum wannan canjin aikin ne, kodai dan wani mahimmin bincike, ko ƙarin girma kokuma dan hukunci ga wani laifi da ya aikata, sedai shi a ganinsa babu ɗaya da Abbas yayi wanda zesa ayi masa wannan transfer.

Ba shiri Yusuf ya bar gidansu Widad ya tafi gurin aikinsu, kai tsaye ofishin Oga Suleiman ya wuce, gaje suka gaisa Suleiman yace  "Yusuf naga aikin daka turomin, kayi ƙoƙari sosai Yusuf sannan ina taya ka murna da sabon muƙaminka"

Yusuf cikin rashin fahimta yace  "Yallaɓai nida ban fahimci abun nan ba, me Abbas yayi za'a ɗauke shi daga gurin nan akaishi wata uwa duniya?"

"Nima ban san meyasa hakan ta faru ba, sedai daga sama ne akayi wannan transfer sannan ka samu ƙarin matsayi"

Yusuf ya dafe kai yace  "Yallaɓai babu yadda za'ayi a bar Abbas a gurin nan ne? Bekamata a raba shi da iyalinsa ba zuwa wata uwa duniya ba, ni dai banji daɗin hakan ba, zanyi kewar abokina kuma ɗan uwana"

Suleiman ya jinjina sauƙin kai irin na Yusuf yace  "ya za'ayi se haƙuri haka sha'anin aiki yake"

Jiki a sanyaye Yusuf ya baro office É—in Suleiman ya nufi na Abbas, se sarawa Yusuf ake ana masa murna amma shi sam hankalinsa yana kan wannan transfer da'akayiwa Abbas.

Da sallama ya shiga Office É—in ya tarar da Abbas yana ta tattara kayansa dake Office É—in.

"Abbas ya akayi haka? Me yasa akayi maka transfer haka ta gaggawa?"

Abbas yace  "nima ban sani ba Yusuf, jiya aka sanar dani kuma akace lallai gobe in Allah ya kaimu in tafi"

"yanzu babu wani abu da zamu iyayi a fasa wannan transfer É—in?"

"Yusuf nayi duk ƙoƙarin da zanyi amma abun ya gagara"

Gaba É—aya Yusuf ya rasa abunda yake masa daÉ—i, dan har cikin ransa yake jin rabuwa da Abbas É—in, dan yana jin Abbas tamkar wani É—an uwansa.

Wayar Yusuf ce ta fara ringing, ya É—akkota daga aljihunsa ya É—aga.

"Yusuf mai gida ya dawo yanzun nan, yace a kiraka"

"Shikenan gani nan zuwa"

Yusuf ya kashe wayar yace "Abbas zanzo gida insha Allah, zan ganka muyi sallama"

Abbas yace "Yusuf na ta yaka murna, an ƙara maka matsayi"

Yusuf yace  "Abbas sam bana murna da wannan ƙarin matsayin, ni tafiyarka ce damuwa ta, bari inje wannan kiran zan nemeka Insha Allah"

Sukayi musabiha, Yusuf ya juya ya fita, Abbas ya raka bayan Yusuf da harara tare da yin ƙwafa.

Tun daga harabar gidan Yusuf yaga manyan motoci da alama bayan dawowar maigidan anyi baƙi a gidan.

Kansa tsaye ya nufi cikin gidan, a falon ya tarar da Alhaji Nasir, Bulama, Fahad Hajiya Halima da iyalanta.

Yusuf ya ƙaraso yana gaishesu, Alhaji Nasir yace  "ƙaraso kusa dani Yayana, nace a kiraka aka cemin ka fita ne"

Yusuf yace  "eh naje wani uzuri ne"

Fahad se wani hararar Yusuf yake, shiko Yusuf ya basar kamar be gani ba.

Tsit falon yayi na wani lokaci, Yusuf ya rasa dalilin hakan, yana ɗaga kai yaga gimbiyar ta fito daga ƙofar part ɗinta, da alamu wannan zaman fitowarta ake jira, seda ta tsaya ta ƙare musu kallo ɗaya bayan ɗaya sannan ta ƙaraso cikin takunta na isa, ta samu kujera ɗaya ta zauna ba tare da ta kula kowa ba.

Alhaji Nasir yace "daughter"

"Na'am Daddy"

"waye wannan?" ya nuna mata Bulama

"Alhaji Bulama"

"kin san matsayinsa a gurina?"

"Just a long time business partner to you"

"he is more than that to me, kuma kin sani danme zan baki umarni kiyi fatali dashi? Duk abunda mukeyi munayi ne dan rayuwarki, danme zaki ciwa Fahad mutunci? A gaban Yusuf komai ya faru, daughter nasan duk abunda kike yi, ina ƙyale ki ne saboda nasan halinda kike ciki na maraici, amma kina zarce ƙa'ida wasu lokutan, daughter farincikin ki muke fata shiyasa muke son aurar dake"

Gaba ɗaya Widad ta ɗauke kai daga kallon Daddynta zuwa wani sashin daban, tanajin ɓacin ran saboda wannan daƙiƙin talasurun Fahad ɗin yau Daddynta ke mata faɗa, ze gane bashi da wayo.

"dan haka whether you like it or not, i have took the final decision, ending of this month zuwa farkon wata na gaba zan É—aura Auren ki da Fahad"

Zare ido Ramlah tayi, taji zuciyarta kamar zata faÉ—o.

Fahad ya wani gyara zama ya kalli Alhaji Nasir yace  "sannan Daddy gaskiya yakamata ayi mata magana akan tasan yadda zata dinga gayamin magana, ta tauna ta kafin ta faɗeta dan sam bata da ɗa'a"

Miƙewa Widad tayi tsaye a fusace tace  "Over my death Body Daddy, wallahi da in auri wannan mara amfanin gara in kashe kaina, kai ka isa ka kalli tsabar idona kace a koyamin yadda zan magana, waye kai"

"Widad!!!"  mahaifinta ya kira sunanta tare da Miƙewa kamar ze kai mata duka.
Cikin zafin nama Yusuf ya miƙe ya shiga tsakanin Widad da mahaifinta ya girgiza kai yace  "Yallaɓai ayi mata afuwa dan Allah, baka saba yi mata magana haka ba karka fara yanzu karkasa zuciyarta tayi rauni, kowa ya juya mata baya, ka sauraretaba zata rasa dalilinta na ƙinsa ba"

Alhaji Nasir yace  "Amma Yusuf yakamata Widad tayi min haka a gaban mutane ta nuna ban isa ba?"

Girgiza kai Yusuf yayi yace "ba tayi haka dan Wulaƙanta kaba, ta tashi a environment ɗin da kowa yana da 'yancin faɗan abunda yake ra' ayinsa, karka ɗau hakan a matsayin ta Wulaƙanta ka, kayi haƙuri dan Allah kasan bata da lafiya"

Tuni hawaye ya wanke fuskar Widad ta kalli Daddynta karo na farko a rayuwar ta da yaƙi bin abunda takeso, hannayenta biyu ta haɗa tareda duƙar da kanta alamar neman afuwa, daga nan ta juya ɗakinta.

Alhaji Nasir ya nemi guri ya zauna, Bulama yace  "lamarin daughter se haƙuri, Allah ya shirya mana"

Hajiya Halima ta gyatsine baki tace  "wannan direban ne yake hure mata kunne take iskancin data ga dama, na rasa wace irin alaƙace tsakaninsu banda haka ana mata faɗa meye na tsoma baki? Kaima Yallaɓai harda kai da kake saka bare a al'amuran gidanka"
  Alhaji Nasir yace  "ba ruwan Yusuf, a irin taurin kai na Widad da irin haƙuri na Yusuf be isa ya hure mata kunne ba, sedai haƙurinsa ne yasa suke tare har yanzu, dan haka karki ƙara aibata shi ko ɗora masa laifi, kaimu Fahad zan shawo kan komai insha Allah"

Yusuf ya miƙe yayi musu sallama ya fice suka cigaba da tattaunawa.

Cakwakiyar gidan nan akwai sarƙaƙiya da ban mamaki, yana nan zaune ya dafe kai yayi shiru Bulama da Fahad suka fito zasu tafi, Bulama ya shiga motarsa direbansa ya ja suka tafi.

Fahad ya tako zuwa gaban Yusuf ya zauna yana fuskantar Yusuf yace 

"kaine direban Widad ko?"

Yusuf yace
"Eh nine"

"Naga kamar matsayinka a gidan nan ya wuce matsayinka na zahiri, zan ja maka kunne ne idan har kana shishshigi da iyayi ka kiyayi Fahad, dan bana barin duk wani abu daze kawomin cikas, matsiyaci kawai kalli rigar wuyanka wai har kaine zaka shiga maganar da bata shafeka ba"

Yusuf yayi murmushi ya miƙawa Fahad hannu yace "Assalamu Alaikum warahmatullah"

Fahad ya kalleshi yace "ni zaka miƙowa hannu kace mu gaisa, kasan koni waye?"

"haka Addini na ya koyamin, ban saniba ko zama a cikin turawa yasa ka manta hakan, rigar wuyana zata iya fin taka daraja in har da gumin halak na sameta, sannan nafi kowa sanin ko kai waye, ɗan adam ne da'aka samar daga Najasa wanda ƙarshena ni da kake kira matsiyaci da kai da kake ganin kanka wani ƙarshen mu ɗaya wato turɓaya kuma Abincin tsutsa, kana fuffukar ban san waye kaiba, kamar ba'a gabana mace ta keta ka ba ta Wulaƙanta ka, wulaƙanci mafi ƙasƙanci shine yadda ake cusa mata kai tana cewa bata sonka "

Galala Fahad yayi yana kallon Yusuf, sam be zaci Yusuf ya iya yanka baƙaƙen magnganu haka ba, Yusuf ya miƙe yace " ka kiyaye gaba, dan idan baki yasan me ze faɗa be san abunda za'a mayar masa ba, bana shkkar kowa se Mahaliccina, kana gayamin abunda beminba zan rama, ni yanzu damuwata be wuce yadda a dalilinka aka samun uwar ɗakina a damuwa ba, damuwarta tafi komai tsayawa a zuciyata"

************************************

"Akan me za'a ayi maka transfer bayan bamu sallami wannan mutanen ba? Waima waye yayi maka transfer ne haka ba shiri? Aknme za'a É—auke ka daga garin nan?"

Abbas yayi ajiyar zuciya yace " wallahi ranka ya daɗe ban san yadda hakan ta faru ba, Suleiman ya cemin daga sama transfer ɗin tazo, abun baƙin ciki aka maye gurbina dana bari da Yusuf, ni ina kyautata zaton shine yaje yasa akamin transfer dan ya gaji muƙamina, kuma da yake munafiki ne ya zo yana nuna damuwarsa akan transfer ɗin da'akayi min"

Saleh ya numfasa yace  "Abbas tabbas akwai babbar matsala wannan transfe da'akayi maka ba tare da samun binciken da Yusuf yayi ba, a ɗan ganin da nayi masa beyi kama da mugun mutum ba yana da nutsuwa, dan haka bashi da hannu a cikin transfer ɗin da'akayi maka, ni babban burina in samu binciken da yayi a hannuna in sallami wancan mutanen kafin su shiga target ɗinsu na biyu kuma na ƙarshe akan Widad, wanda target ne me hatsarin gaske"

Abbas yace  "nifa takaicina shikenan yanzu ba zan samu kuɗaɗen nan ba? Gaskiya na ƙallafa rai amma karka damu Yallaɓai, dukda zan bar garin nan dole a samu binciken da Yusuf yayi"

Saleh yace  "don't stress yourself i know what to do"

"Amma kana ganin rashin bada file É—in akan kari zesa kaima ka shiga cikin matsala?"

"babu wata matsala am also planning something, karka damu ni zan tafi duk yadda ake ciki zamuyi waya"

Daga nan suka yi sallama.

Sam Yusuf ya dena ganin Widad, hakan yasashi shiga damuwa sosai, hakan yaso ya shafi aikin da yake yi, ya damu sosai yaga halin da take ciki, bashi da hujjar shiga cikin gidan tunda ba nemansa akayiba.

Mutanen gidan dama ba wanda yake saurarar Yusuf, dan haka haka yake zuwa ya wuni ya tafi zuciyarsa cike da son sanin halin da take ciki.

Yusuf yana zaune yana tunanin yadda zega Widad dan yasan koba'a gaya masa ba Widad tana cikin damuwa.

Fitowar Alhaji Nasir dasu Hajiya Halima ne ya dawo da Yusuf daga tunanin da yake yi, Fuskar Alhaji Nasir akwai damuwa amma ya danne damuwar tasa yana ta fara'a.

Yayiwa Yusuf alama da yazo, Yusuf ya taso yazo, Alhaji Nasir yace  "Babban Yaya, airport za muje zamu ɗakko ɗana Anwar, ya kammala karatun sa"

Yusuf yayi murmushi yace  "Masha Allah, shima Yayan uwa ɗakina ne?"

Alhaji Nasir yayi murmushi yace  "Yusufa kenan, ai uwaɗakin ka bata da wa ba ƙani, Amma Anwar ma ɗana ne tunda na riƙe shi"

Yusuf yace  "ba da ita zamuje bane? Naga ita bata fito ba?" Yusuf yayi maganar cike da son sanin halinda Widad take ciki.

"Kasan tana fushi dani ne, ta dena zuwa inda nake ma, na ɗan ƙyaleta ne ta huta, har seta gane mahimmancin maganata"

Har Yusuf zeyi magana, Hajiya Halima tace "Kaga ka ishemu da surutu, muyi mu tafi kar jirginsu ya sauka yazo yana faman jira"

Alhaji Nasir yace  "Bimin shi a hankali Halima, Yaya nane a girmama shi ko dan sunan nasa"

Nura yana gefe ji yake kaman ya shaƙe Yusuf, ba'a taɓa ma'aikacin da Alhaji Nasir ke nunawa soyayya kamae Yusuf ba dukda mutum ne me girmama na ƙasanshi, tsabar abu yanzu Alhaji Nasir be fiye damuwa da Nura yaja shi a mota ba sedai Yusuf.

Gaban Mota Amal ta shige, yayin da su kuma suka shiga baya, Suna tafe a mota iyalan suna hira kamar ba abunda ke damunsu, Alhaji Nasir yana dauriya ne kawai, yayin da Yusuf ko uffan yakasa cewa hankalin sa na kan Widad.

Koda suka je airport sunyi A ƙalla mintuna talatin, sannan wanda suka zo dominsan jirginsu ya sauka, matashin kamarsa ɗaya sak da Amal, kana kallonsa kasan ɗan uwansu ne, da gudu sukaje suka rungume shi cike da farinciki, ya ƙaraso gaban Alhaji Nasir ya durƙusa ya gaishe shi.

Bayan sun gaisa ya kalli Yusuf ya miƙa masa hannu sukayi musabaha, da alama Anwar shi a nutse yake ba kamar 'yan uwansa ba, daga nan suka nufi hanyar gida, suna tafe kamar zasu fasa motar da hayaniya da shewa.

Har sukaje gida hirarsu kawai suke, amma alamu sun nuna Alhaji Nasir biye musu kawai yake, sun Sakkowa sukayi cikin gida yayinda aka bar Yusuf da kwaso akwatunan Anwar.

Suna shiga falo kawai Yusuf yaga Widad a zaune tana shan ruwan roba, sedai idanunta a kumbure suke, alamar kodai bata bacci kokuma kuka take yi, gaba É—aya Yusuf yaji babu daÉ—i.

Anwar yace  "Masha Allah, little queen ta girma Amma Daddy sha ka fashe ka bata dan yayi wuri ace tayi wannan girman"

Daddy yayi murmushi yace "gata nan tambaye ta, in da ragiwar sha ka fashe É—in kaima ta sammaka"

Ba tsammani Yusuf yaga Widad ta É—anyi murmushi, yayin da Hajiya Halima ta tsuke fuska tace "kaga muje ka wataa ruwa ka nemi Abinci"

Anwar yace  "bari Mummy in gama ganin lovely ɗin Daddyn ta inji dalilin da yasa ba tazo taroni ba"

Yai maganar yana ƙarasawa inda Widad take ya zauna, Alhaji Nasir kam part ɗinsa ya wuce yana murmushi saboda Anwar akwai barkwanci.

Ramla cikin tsawa ta cewa Yusuf "dalla malam ka ajiye kayan na ki fita, uban sa ido kawai"

"Karki kuma yi masa tsawa, na kuma gayamiki ba zamanki yake ba, idan kika ƙara hukuncin daze biyo baya ka iya ɓatawa kowa rai"  Widad tayi maganar ba tare da kallon Ramla ba.

Anwar yace  "Ramla baki kyauta ba, babu daɗi abunda kikayi fa"

A fusace Mummy tace  "dalla tashi ka wuce ciki, ina magana harda neman guri ka zauna"

Anwar ya miƙe yace  "Widad idan na fito zanzo mu gaisa sosai ki bani sirrin wannan girman naki"

"No need Anwar, yanzu ma mun gaisa yawan shiga harkata ka iya baka matsala da kai da Ahalinka, ina taya ka murnar kammala karatunka, Allah yasa al'umma su amfana"

Tai maganar tana miƙa masa hannu suka gaisa, from no where Yusuf yaji wani takaici ya tokare masa zuciya ganin abunda ya faru.

Mummy ta tasa ahalinta suka shige sashinta, aka bar Yusuf da Widad a falon har ya juya ze fita ya bar falon ya waiwayo, ba zato suka haɗa ido tai saurin ɗauke nata idon daga nasa, a hankali ya dawo ya kalleta yace  "Madam ko baki da lafiya ne?"

Girgiza masa kai tayi tace  "jirani a waje gani nan zamu fita" ya jinjina mata kai ya fita.

Cike da damuwa Anwar yace "Mumsy meyasa bakya son Widad ne? Me tayi mikine haka?"

Ramla tace  "yanzu daka dawo idonka ze gane maka ai"

"kar in sake magana ki samun baki, in bahaka ba sena tattakaki na gaya miki"

Ya maida hankalinsa kan Hajiya Halima yace  "Rayuwar ta abun tausayi ce, tana buƙatar kulawa meyw a ciki dan ki haɗemu gaba ɗaya kin nuna mata kamar ke kika haifeta"

Amal tace  "Taɓɗijan lallai baka san yarinyar nan da taurin kai kamar arnan farko ba, ba mutunci a lamuranta balle tausasawa bata ganin kowa da gashi waye za janyo ta a jiki?"

"Amla yaushe kika koma hakane? Gaba É—aya kun zama fitsararru"

"karka ƙara ce musu fitsararru na gaya maka, bazan riƙe yarinyar da zata nemi ta halakani da baƙinciki ba, bata da tarbiyya sam bata da ɗa'a, shikansa mahaifin nata bata ƙyaleshi ba, weekends ɗin nan Fahad yazo ganin ta za'a haɗasu Aure da shi da ubansa ta haɗa ta wanke su da rashin mutunci tsaf, ubanta ya kirata yayi mata faɗa nan ma ta sake kunyata shi a gaban mutane ta hanyar nuna masa be isa ba"

Cike da ɗimuwa Anwar yace  "wait ji nayi kamar kince za'a haɗata Aurw da Fahad, wani Fahad ɗin wai?"

"Fahad É—in Bulama mana" ta bashi amsa

A diririce yace "Mummy ta yaya haka zata farune? Ita tace tana sonshi? A zatona ai Ramla yake so"

Amla tace  "Ramla yake so, amma babansa da Babanta sukayi ƙarfa ƙarfa sukace zasu aura masa ita, tayi masa rashin mutunci amma yace ba gudu ba ja da baya seya aure ta"

Anwar yace  "Impossible wallahi sedai ayi biyu babu, Fahad yafi kowa sanin yadda nake son yarinyar nan danme zemin haka? Na tabbata da nine bazan masa haka ba, wallahi indai da raina Fahad be isa ba, sedai zumuncin namu ya watse"

"haka nima indai da raina baka isa ka aureta ba, sedai ka canza wata uwar bani ba, dan da hankalina É—ana baze auri dangin mahaukata gadon rashin tarbiyya ba"

Bin mahaifiyar tasa yayi da ido, tare da mamakin wannan magana data fito daga bakinta, be kuma cewa komai ba ya fice cikin hanzari.

Wata katafariyar ma'aikata sukaje, Yusuf yayi mamakin haɗuwa gami da tsaruwar ma'aikatar kamar ba'a ƙasa Nigeria ba, Widad ta dinga ratsawa Yusuf na binta kamar inuwa haka suka isa wani makeken Office.

Kai tsaye ba neman izina ta bankaÉ—a ofishin ta shiga, Bulama ne zaune da É—ansa Fahad suna dudsuba wasu file, Widad ta kallesu tana huci kamar mayuwanciyar Mesa.

"daughter lafiya kuwa?" Bulama ya tambayeta.

"Dole ka tambayi lafiya mana tunda kayi nasarar cusawa mahaifina ra'ayinka wansa yake barazana ga ratuwata, be taɓa fushi dani kamar wannan karon ba yana kallon hawaye akan fuskata amma ya kasa share min hawayen, ya barni tsawon kwanaki ina fama da ƙuncin zuciya "

Bulama yace " Calm down daughter, wannan fa duk ba abun zafi bane, ke kika kambama abun kika maida shi babba, meye laifin Fahad dan an Aure shi? Kuma daba'a aure a haifeki? "

" kai baka ga laifin ɗanka ba ni na gani, bashi da nagartar daze iya zama miji a gare ni, na tsane shi bana sonsa kuma bazan aure shi ba, sannan ka gaggauta zuwa ka janye wannan maganar daga gurin mahaifina ya dena fushi dani, fushinsa yana daga abunda ke jefa zuciyata cikin tashin hankali, be taɓa fushibdanibba se a dalikin wannan gurguwar shawarar taka, bazanyi aure ba ka janye wannan maganar idan ba haka ba Wallahi sena baka mamaki daga kai har ɗan naka"

"Ke jahila!" Fahad ya faɗa tare da yunƙurin kai mata mari, ganin yadda take wa mahaifinsa shouting, sedai ba zato yaji an riƙe hannunsa anyi gefe dashi.

"karka kuskura koda wasa ka kuma yunƙurin ɗaga hannu akanta, koda mafarki kake kaga hakan zata faru kayi duk me yuwuwa kaga ka farka da baccin dan mummunan mafarkine balle a gaske, sannan kasan da kalmomin da zakayi amfani gurin yi mata magana"

Yusuf yayi maganar cikin fushi da harzuƙa, wani irin kwarjini Yusuf yayiwa Fahad, dan a doke tsaf Yusuf ze bazar dashi a gurin.

Bulama yace  "ɗan samari kamar kana zaƙewa fa wasu lokutan"

Yusuf ya saki hannun Fahad cikin ladabi yace  "bahaka bane ranka ya dade, nayi ƙoƙarin hana faruwar tsamin alaƙar daze biyo baya idan har Alhaji Nasir yaji ɗanka ya dakar masa 'ya me"

Bulama yace "koda baka yi hakan ba ni zan É—au mataki Yusuf, bazan bari hakan ta faru ba sam"

Widad tace  "naso ka bari ya dakeni, in sa a nuna masa shi ba komai bane, in nunawa duniya da bazata yake rawa, duk wannan fuffukar da yake da sena nuna masa in ba Widad babu shi, kuma Auren nan dole a fasashi, nazo ne dama dan in muku gargaɗi na ƙarshe a janye maganar nan kafin rugujewar duk wata alaƙa dake tsakaninka da mahaifina"

Sosai Fahad ya dinga huci, a gabansa yarinya ƙarama take cim zarafin mahaifinsa.
Bayan fitarsu Widad, Bulama yayi shiru yana tunani, Fahad yace  "Daddy wannan wace irin dabbar yarinya ce me kyan ɗan maciji, bata da tarbiyya bata da ta ido Sam, ta dubi mutum kamar kai ta dinga gaya masa wannan maganganun, kana kallonta kuma Daddy"

Bulama yayi ajiyar zuciya yace  "daka sake ka daki yarinyar nan da tabbas yanzu wani zancen ake ba wannan ba, koda wasa karka kuskura kayi gangancin cewar zaka dake ta, ta wuce yadda kake tunani, tabbas ba dan inajin nauyin Daula ba da se an fasa Auren nan, dan ina ganin ƙiyayyarka a idonta wanda har hakan yake son ya shafeni"

Fahad ya daki teburi yace  "Nikuma ina sonta a hakan, zan Aure ta koda zata kashe kanta sena Aureta na wulaƙantata na nuna mata ita bakomai bace zanga wanda ze Nasara tsakanin ni da ita"

Bulama ya girgiza kai yace  "Fahad kenan kai kana tunanin zaka iya Wulaƙanta ta idan ka Aureta, dole kayi haƙuri da duk abunda zata aikata maka, zamuyi mata aurene dan samun nutsuwar ta ba dan a muzguna mata ba, shiyasa tun da fari bamu nemi wani bare sekai"

Gajeren tsaki Fahad yayi yaja kujera ya zauna tare da dafe kansa.

Kallonsa take yana tuƙi fuskarsa ɗauke da ɓacin rai, tunani take a duk lokacin da yaga wani na shirin cin zarafinta ko ɓata mata rai se yayi duk me yuwa ya hana faruwar hakan, a duk lokacin da take cikin damuwa zataga damuwa a fuskarsa, wanda ko ɓata masa rai tayi be fiye nuna damuwa haka ba.
Ajiyar zuciya ta sauke seda Yusuf ya juyo ya kalleta yace "lafiya kuwa?"

Ta jinjina masa kai alamar eh, haka suka koma gida ranta a matuƙar ɓace.

Anwar suka gani a harabar gidan, ya ƙaraso da sauri inda take yace  "Widad ina kika jene? Tun ɗazu nake dubaki a gidan nan ban ganki ba" yai maganar cike da damuwa.

Widad tace  "Anwar bana son daga dawowarka ka fara shiga cikin matsalolin gidan nan, zaka fuskanci fushin mahaifiyarka idan haraka cigaba da shiga harkata, am sorry amma kayi harkokinka inyi nawa please"

Ze sake yin magana tayi gaba ta shige ta barshi a gurin, ya kalli Yusuf yace  "ɗan uwa dan Allah meke wakana a gidan nan ne? Ni gaba ɗaya abubuwan mamaki suke bani"

Yusuf yace  "gaskiya nima ban sani ba, tunda nima banfi watanni huɗu da fara aiki a gidan nan ba, bakomai nasani ba, sedai damuwa na damunta sakamakon Auren da za'ayi mata, bata fiye son a shiga harkar ta ba idan tana cikin damuwa shine kawai abunda nasani"

"dan Allah wai dama maganar Auren nan dagaske ne?"

"Eh gaskene" Yusuf ya bashi amsa

"Impossible" Anwar ya faɗa da ɗan ƙarfi

"Ni Fahad zeyi wa haka? Saboda cin amana da wulaƙanci" Anwar ya girgiza kai ya koma cikin gida fuskarsa ɗauke da ɓacin rai.

Washegari da safe Yusuf ya shirya ya fita, seda ya fara biyawa gidan Abbas amma ya tarar baya nan, kamar yaje office amma ya fasa ya wuce gidansu Widad.

"Yusuf gimbiyar masu gida da kanta ta fito nemanka, da alama ka makara fa"

Yusuf yace  "wani abune ya ɗan tsareni, bari inje in ganta"

Murtalah yace  "tana lambu ita da tsuntsayenta da ƙanwarta wato kyanwarta"

Yusuf yayi murmushi ya nufi lambun, kamar yadda Murtalah ya gaya masa tana lambun ita da magenta Roux, magana takewa magen nata kamar da mutum take magana tana cewa

"Roux har yanzu Daddy yana fushi dani, gaba ɗaya duniya tamin zafi, ba wanda ya goyi bayana ko ya tausayawa halin da nake ciki, ba zan iyayiwa Daddy biyayya in Auri Fahad ba, ji nake kamar zuciyata zata tsaya saboda ɓacin rai, amma dole in san hujjar da zan gabatarwa Daddy da zesa a fasa Auren nan, am so much disturbed Roux"

Tana maganar tana shafa jikin magen, yayinda magen tayi luf a jikin Widad kamar tasan me take gaya mata, lokuta da dama Yusuf yana jin Widad tana hira da Mage, hirar da be taɓa jin tana yi da ɗan adam cikin mutuntawa da nutsuwa haka ba.

Ji tayi kamar ana kallonta ta É—aga kai suka haÉ—a ido da Yusuf, ta tsuke fuska tace "baka iya Sallama bane?"

"Ai idan nayi sallama bakya amsawa" ya bata amsa

"Se yanzu kaga damar zuwa ko?"

"Umma na taya aiki shiyasa banzo da wuri ba"

"shikenan, zamu fita yau ƙarfe tara"

"Amma ai tara ta wuce yanzu, sedai ta gobe in Allah ya kaimu"

"tara na dare" ta bashi amsa

"tara na dare kuma? Ina zamuje haka da daddare? Kuma mu dawo yaushe? "

Ba tare da ta kalli Yusuf ba tace "hmmm akwai ka da ƙwarin gwiwa, ƙarfin hali bin ƙwaƙwƙwafi da sa ido sekace ɗan Sanda ko wani jami'in sirri, za kayi kyau da Aikin ɗan sanda ko kuma fannin shari'a"

Wani abune ya tsarga tun daga kan Yusuf har yatsunsa na ƙafa.......

(INA BUƘATAR JIN SHARHINKU FANS, ME KUKE TUNANI NE AKAN WANNAN TURKA TURKA, INGA COMMENTS ƊINKU KO IN KOMA POSTING DA TSALLAKEN KWANA ƊAYA)

Share and share please
domin sharhi, gyara ko shawara
Ayshercool
07063065680

                      _*AƘIDATA*_
       

PERFECT WRITERS ASSOCIATION

(WE AIN'T PERFECT BUT WE ARE ALWAYS TRYING OUR BEST, TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS)

https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

*Story and written by*

_*AISHA HUMAIRA
(Daddy's girl)*_

The experience writer of
*ABDUL JALAL*
* WATA KISSAR.... (SAI MATA) *
And now
*AƘIDA TA *

I dedicated this book to my Mum
(Malama Nafisat Adam Muhammad) i love you mum

Haƙƙin Mallaka ⚠ : Littafin nan mallaki nane, tun daga sunan labarin zuwa abunda ya ƙunsa, ban yadda wani ko wata ya sauyamin ko yin Amfani da wani ɓangare na labarin ba ba tare da izinina ba, Nagode

https://www.wattpad.com/user/Ayshercool7724?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends

ELEGANT ONLINE WRITER'S

                         PART1
                                Page 20_21

Widad ta cigaba da cewa "da aikin shari'a zakayi zeyi wuya a iya kada kai, yakamata Alhaji Nasir yayiwa yayansa wani abu, yakamata ya nema maka makaranta ko dai horarwa akan aikin tsaro kokuma a nema maka aikin shari'a" ta ƙarasa maganar da wani ɗan guntun murmushi

Yusuf ya daskare ya kasa ko motsa É—an yatsansa 'Widad ta gano shine kokuwa?'

"Jeka in lokacin yayi kazo mu tafi"

Kasa motsawa Yusuf yayi, ya tasaya yana kallon Widad, ta É—ago ta kalle shi tace "ya dai naga ka tsaya? Meyafaru?"

Girgiza kai yayi ya juya ze fita, beji takuma cewa komai ba.

Tunani ne ya shiga zarya a zuciyarsa, kodai Widad tasan waye shine? Amma ya tuna da sharaɗinta bata yafewa wanda yayi mata ƙarya, a rashin yarda nan tata tabbas da tasan waye shi da tuni tayi maganinsa ta ɗau mataki akansa.
A hankali ya furta "Ubangiji Allah ka shiga lamarina, Allah yasa har in kammala aikin nan yarinyar nan ba zata ganoni ba"

*****************************

"Amma ni tabbas ba'ayimin Adalci a wannan lamarin ba, nida É—an uwana ku kusan halaka shi sannan ace bazan ganshi ba, wannan wane irin zalunci ne"

"zaka iya kiransa da duka abunda kaga dama, amma tabbas ba zaka ganshi ba, zamu ci gaba da ajiye shi a ɓoyayyen guri har se sakamakon binciken nan yazo hannun mu"

Saleh yace  "binciken nan bani na yake yi ba, kun san hukumar da sukeyi meze sa ku cigaba da azabtar min da ɗan uwa"

"saboda shi kaÉ—ai ne hujjar daze fallasa komai a kotu, kuma yana nan shirin tona mana Asiri dan haka gara muyi maganinsa"

Cike da damuwa Saleh yace  "to ai wanda yake ƙoƙarin samo min sakamakon anyi masa transfer ya kuke so inyi, ni ko ganinsa inyi shikenan"

Alhaji Musa yace  "baja da wannan damar Saleh, kayi abunda muka ce kawai"

A fusace Saleh ya miƙe ya bar gurin zuciyarsa na masa zugi, tabbas su Alhaji Musa masifa ne a rayuwarsa da ɗan uwansa.

Anwar a cikin ɓacin rai yaje ya samu Fahad a gida, Fahad na ganinsa yace  "Ohh God, Anwar ai namanta gaba ɗaya jiya zaka dawo am so sorry brother"

Jiki a sanyaye Anwar ya kalli Fahad yace "Am disappointed Fahad, dole kace ka manta jiya zan dawo, yanzu Fahad yarinyar dana daÉ—e ina mafarkin aura ita zaka aura?"

Ajiyar zuciya Fahad yayi yace "am sorry, nima bani nace ina son ta ba cusa min ita akayi akace sena Aureta dan anga tana da taɓun hankali"

"Fahad, Widad ba irin matan da za'a cusawa mutum bane, sannan idan har cusa maka ita akayi saboda taɓin hankali, ni ka barmin ita in aura tunda ni ina son ta"

"nice maka akayi bana sonta? Ko kuma so kake in kalli mahaifina ince zan bijirewa umarninsa"

Anwar yace "ni bahaka nake nufi ba amma nasani ka sani Baka dace da Widad ba, nasan halinka gaba da baya"

"kasan halina amma ka barni nake soyayya da ƙanwarka? Ko abun naka son zuciya ne?"

"son zuciya be wuce wanda ake shirin yiwa Widad ba, Ramla tasan dai dai tasan abunda take yi dan haka idan ta zaɓeka a matsayin miji ita taso hakan, Amma Widad fa Yarinya ce sannan...

"kaga Anwar ya isheni haka" Fahad yai maganar a tsawace

"Idan har ba so kake abotarmu ta samu matsala ba ka ƙyaleni, ka fita daga batun Auren nan"

"Idan kuma naƙifa?"

"Komai ze iya faruwa"

Anwar yace  "to sonake koman ya fary Fahad, naga baka gane rarrashi zan ɓullo maka ta inda ya dace"

Fahad yace  "Anwar karka kuskura kaje ka faɗi wani mummunan abu a kaina a gurin mahaifin Widad"

"Fahad dani da kai a ƙarƙashin kulawarsa mukayi karatu, ba abunda be mana na gata a rayuwa ba, bana jin Widad kanta ta moreshi kamar yadda muka moreshi, idan har aka lulluɓe kura da fatar Akuya ba muyiwa Alhaji Nasir Adalci ba, kaima kasan baka dace sa Auren 'yarsa ba"

"Amma Anwar kasan taimakawa zan in Aureta tunda mahaukaciya ce?"

"kabar taimakon naka mana, kaje ka auri Ramlah"

"Amma Anwar meyasa kake fifita Bare akan ƙanwarka? Idan har dagaske kake Ramla yakamata kace bazan Aura ba"

"Fahad ba goyon bayan bare nake ba, goyon bayan gaskiya nake kuma kaima ka sani"

Yana gama maganar ya fice a fusace cikin sauri.

**********************************
Ɓangarren Nurat kam lamarin mahaifinta yana bata mamaki, gaba ɗaya babu wanda ya gane inda yasa gaba daga ita har mahaifiyarta, ga ta'amali da wasu irin ƙarti da yakeyi wanda daka gansu zaka san ba mutanen kirki bane, suyita musu zirga zirga a gida, babu me ikon cewa uffan saboda duk tsoronsa suke ji.

Gefe guda kam tunanin Abokinta ya cika mata zuciya, zuciyar ta na matuƙar begen ta ganshi amma abu ya gagara, tasan ko giyar wake tasha bata isa taje gidansu Widad ba, tunda ta dena ɗaga wayarta tasan akwai wata a ƙasa haɗuwarta sa Widad ze iya haifar mata da matsala ne kawai.

Ba zata iya ƙirga adadin saƙonni da kuma kiran da tayiwa Yusuf ba, gefe guda kuma dai zuciyar ta na kwaɗai mata son sanin me mahaifinta ke ƙullawa wanda yasa shi yin mu'amala da wannan mutanen haka, suke ta musu sintiri a gida.

************************************

Anwar ne ya shiga É—akin Alhaji Nasir da Sallama, cikin sakin fuska ya amsa masa, sedai mahaifiyarsa tana tare da Alhaji Nasir É—in a wannan lokacin, fuskarsa ta nuna yana cikin damuwa kuma yana son yin magana ne.

Alhaji Nasir yace "shigo mana Anwar"

Anwar ya ƙarasa ya zauna a ƙasan carfet yana sunkuyar da kai, can yace
"Daddy, naji ka yanke wani hukunci, wai dagaske nan da ƙarshen wata zaka aurar da Widad?"

"eh hakane Anwar, halin ƙanwar taka ne se ita, gashi har yanzu ciwon ta yakan tashi, bekamata ace mamanku ta cigaba da ɗawainiya da ita ba, akwai buƙatar itama tayi Aure tunda ta girma"

"Amma Daddy kayi bincike akan wanda zaka bawan kuwa?"

Alhaji Nasir yace  "bafa wani ne ba, Fahad ne ba wai wani guri aka samo mata mijin ba, Fahad ne Abokin ka ɗan gidan Bulama"

Irin mugun kallon da mahaifiyarsa ke jifansa dashi ne yasa ya kasa cewa komai yace  "shikenan Daddy, Allah ya Sanya alkhairi ya kaimu lokacin"

Ya tashi gwiwa a saɓule yana kallon mahaifiyarsa ya bar ɗakina.

Alhaji Nasir yace  "Halima kaman akwai abunda yake damun Anwar amma ya kasa faɗa"

"ba abunda yake damunsa, naga dai kamar ya É—an damu ne da batun Auren Widad"

"ko dai yana sonta ne?"

Da sauri tace  "A'a kasan halinsa dai da tausayi, da yana son ta ai da tuntuni ya faɗa"

"hakane, aikam da ban bawa Fahad ba da Anwar zan bawa, dukda gaba É—ayansu 'ya' yana ne, amma wata kusan ai tafi wata"

"hakane kam, Allah ya wuce mana gaba"

Bayan ta sallami Alhaji Nasir, ta fito ta tafi É—akin Anwar, yana zaune a bakin gado ya dafe kai yana tunani, jin motsin shigowarta ne yasa shi É—agowa ya kalleta, Hajiya Halima tace
 
"kaga Anwar zuwa nayi in sake yi maka kashedi, wallahi tun wuri ka fita daga harkar Auren nan, wai ƙanwar uwarkace ita kota ubanka? Ka shiga hankalin ka na gaya maka"

Fahad yace "Allah ya baki haƙuri, Insha Allah zan kiyaye, amma dai Fahad be dace da Aurenta ba"

"da anyi magana ka iya bada haƙuri ai, ko waze aurawa ina ruwanka, shi ya haifeta ba in ya ga dama yaje ya aurawa kare ita mana ina ruwan wani?"

"Amma Mummy ya zakiyi da Ramla da take mutuwar son Fahad?"

"Ai magana ta ƙare tunda Fahad ze auri mahaukaciya, Allah ya bata wanda ya fishi seta haƙura"

"Amma ba kya tunanin yadda take son shi hakan ya haifar da matsala?"

"Kai rufemin baki, Allah ya tsaremu da matsala ina sake jan kunnenka ka fita daga sabgar yarinyar nan, in kuma kaƙi ji baka ƙi gani ba"

Anwar ya bita da kallo yayin da ta bar É—akin, ya girgiza kai tare da sauke ajiyar zuciya.

Yusuf yana zaune a mota yana ɗan danna wayarsa yana jiran fitowar Widad, be san ta taho ba kawai yaji ta buɗe motar, da sauri ya ɗago ya kalleta, wato abun nata kullum ƙara gaba yake, yau shigar tata tafi ta kullum muni, kamar yadda ta saba gaban mota ta shiga garin zama seda jikinsu ya gogi juna, amma kowannensu ya basar.
Shiru Yusuf yayi bece komai ba, ta ɗakko wayarta ta miƙa masa, ya karɓa ya duba, kwatancen idan zasuje ne ya sake duba agogon hannunsa ƙarfe tara daidai na dare, zuba mata idanun yayi yayinda itakuma take kallon wani gurin.
Ba zato yaji ta fizge wayarta daga hannunsa tace

"malam bana son kallo"

"Aikuwa kallo kin gamu dashi muddin da wannan shigar zaki fita" ya bata amsa

"shikenan cigaba da kallona karka fasa, wallahi kasa na makara zuwa inda zanje se nayi mummunan ɓata maka rai"

Ta faɗa in a very serious tone, haka yaja motar suka fita, gaba ɗaya jikinsa babu ƙwari yake tuƙin.

Yusuf be tsinke al'amarin ba seda yaga sun iso wani katafaren Club a cikin sabon garin Kano, kallon Widad yake yaga me zata yi ganin yadda zaratan karuwai da 'yan iska ke shiga suna fita a gurin.

Yunƙurawa tayi da nufin buɗe ƙofar taji yasa lock, ta kalle shi tace "buɗeni zan fita"

"kije ina?"

"inda ka aikeni" ta faÉ—a cikin fushi

Gyara zama yayi ya É—auke kansa daga kallon ta.

"magana fa nake maka"

"idan har na bari kika shiga wannan gurin a haka, ba yiwa kaina adalci ba kuma Allah ze kamani da laifin cin Amana"

"Dalla ka rufemin baki, ina ruwanka da nine? Ina ruwanka da rayuwata na gaya maka kadenamin shishshigi fa bana so, ina kunyar Daddy ne ba dan haka ba da tuni na daÉ—e da karta maka rashin mutunci"

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.