Kwarata Littafi Na Daya Complete Hausa Novels
Reading file: Kwarata Complete.txt
Chapter 1 of 7
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIR*
*GABATARWA:•* _Yabo da godiya da'iman wa abbadan na Allah ne. Salati da sallama su ne na fiyayyen halitta, shugaban annabawa kuma jagoran manzanni Annabi Muhammad, da iyalansa da sahabbansa baki daya._
*Shafin farko sadaukarwa ne ga kungiya mai albarka da marubutan cikinta, BRILLIANT WRITER'S ASSOCIATION Allah ya kara hadin kai.*
*Bazan manta da ku ba aminan albarka ina alfahari daku saina tunaku ko ina a bakin kura* ðŸ†
*HALIMATU SADIYYA* _{{ My Leema }}_
*HABIBA IDRIS* _{{ Hubbie }}_
*HAUWA'U USMAN* _{{ Smasher }}_
*MAIMUNA O . G*
_Gaba daya littafin nan sadaukar ne gareku,_
*ASMA'U ZAYYAN* _{{Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 1
^^Shekaruna goma sha bakwai cas a duniya. Babana yana da mata hudu da "ya "ya hamsin da bakwai.^^
Mahaifina ya kasance dan auri saki ne, bakin abinda kunne na yaji mahaifina ya auri mata ashirin da takwas.
Babana ya kasance talaka ne baya da wata sana'a wadda ta wuce "yan bige bige, ya gwanance wurin iya karya sannan kuma babu abinda kware dashi sai cin bashi.........
Talaka ne amma baya saka sutura irin tasu, idan kika gansa zaki rantse da Allah yana iya kyautar naira miliyan biyar, yasan dadin kudi sosai amma a sutura baya tausawa naira.
^^°Baya da gidan zama haka kuma baya da fili ko taki daya, munyi zama a anguwanni da dama sosai wanda duk anguwar da muka sauka suna mana lakabi da gidan inna ratata, ko kuma suce gidan yawa...
Baya da aiki sai shaye shaye sannan kuma duk gidajen cacar dake garin katsina babu inda ba'asan shi ba, ya saka kansa caca wanda ake kira da nigerful, caca ce wacce take cinye tattalin arziki kuma ba kananan talakawa keyinta ba sai masu kudin gaske saboda idan har za'a buga wasan cacar mahaukatan kudine ake zubawa.
Baya bayar da abinci haka kuma babu abinda ya damesa da rashin lafiyar "ya "yansa ko matansa, idan dai caca tayi masa dadi zai siyo kwanon shinkafa daya da kuma rabin doya,
Da safe idan zai fita zai bayar da kudin kalaci ko wane daki naira talatin babu wani abinda ya damesa da yawanku.
{}{{{}}} Wata rana can wurin wasan caccarsa aka cisa, amma baya da kudin da zai biya daga cikin abinda aka saka masa, dan haka suka cire masa sutura, tun daga inda ya buga wasan har zuwa gidanmu daga shi sai gajeran wando haka ya ratso mutane saboda tsabar shi tantirine har ya iso gida.
Babu ruwansa da tarbiyar dan sa ko yar sa, shi yasa muka mayar da gidanmu kamar gidan karuwai, domin dai kowa abinda takeso shi takeyi dan babanmu yace sana'a itace tafi cancanta ga duk diyar daya haifa, ya daina biyan kudin haya yace mu zamu rika biya tunda kowa ya kawo karfi, dan haka duk yayuna suka tashi dan neman na kansu kowa ya kama sana'a amma banda ni,
Abinda yasa kuwa shine, lura da irin kyawun da Allah yayi min, karkuyi tunanin kyawu na wasa ko ku lakaba abin da shirme ni nake gaya muku haka, bawai a gidanmu ba gaba daya zuri'armu babu yarinya mai kyau da daukar hankali kamar nawa....
Ina da kyau fiye da tunanin mai tunani, ina da diri daidai irin wanda maza ke so, ina da babban kugu sannan kuma Allah ya bani baiwar iya murzasa.
Haka kuma ina da cikar kirji ina da manya idanuwa sannan ina da fari irin na fulanin asali, gaba daya zuri'armu babu mai haske na, idan na shigo taro mata sun gama wali haka kuma babu macen da zata kara tasiri harsai na bar wurin.
Ni "yar gayu ce, na iya wanka kuma na iya shafa turare gaba daya bani da tsara idan na ziyarci wuri kamshina zaiyi ta kasancewa a wurin, haka kuma idan na barsa turarena zai dade bai daina tasiri ba, sannan duk gidanmu babu mai ilimin addini na wanda na samesa ta dalilin mahaifiyata saboda nayi sauka kuma bakin gwargwado nasan hadissai amma gaba daya zuri'armu babu mai barna irin tawa, ga sani ga barna dan duk yanda nake dakai a danginmu idan har na kwallafawa raina saina bata ka tou fa lallai saina bata maka rayuwa.
Ku kasance dani a cikin littafin *KWARATA* domin jin wannan wane irin ubane ita kuma wace irin diya ce ? Kuma a cikin ita da uban waye yafi tantiranci ? Domin dai ni sana'ar da na zabawa kaina itace *KARUWANCI* danni a gani na itace sana'ar da tafi saurin kawo kudi.
Babana mahaifi shine mutum na farko daya fara budemin lasisin karuwanci, domin dai a wurin wasan cacarsa yayi kyauta da budurcina, wannan dalili yasa na zabi sana'ar karuwanci, shine ya fara ni kuma naci gaba da kasancewa da wasan domin dai masu iya magana sunce so da yawa kana koyawa mutum abu amma saiya fika kwarewa.
Ni babban kamfani ce kamar yanda ake sakawa a jikin kayan masarufi ace ingrediants to nima ina da nawa ingrediants in, kamar yanda company yake sarrafa abubuwa to nima company ce mai zaman kaina.
Wannan labari a kiyayi juyashi ta ko wace siga domin yin hakan babban kuskure ne , ba kagoshi nayi ba a haka ta fadamin shi domin ina so ya zama izina ga matan aure,
{{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}} {{{}}}
Baba da Allah ka bamu naira goma zamu cika mu siyo magi,
Ba tare daya kalleta ba yace me zakuyi da magi ? Cikin in ina tace dama kanzo ne zamu kwada,
Naira biyar ya fiddo daga cikin aljihunsa, ya mika mata tare da cewa anshi idan kin samu kudin magin ki cika ki siyomin sigari......
Mahaifiyar ta dake tsaye tana daka kulin da za dasuci kwadon tace haba mai gida idan tana da kudin zata tambaye ka ? Itama bai kalleta ba yace wannan matsalarku ce keda ita, keni yi sauri ki kawomin sigarita jiranki nake ya fada tare da shashantar da maganar matar sa.
Fa'iza mahaifiyarta ta kirata tare da cewa ina zaki samo kudin ? Bai bari Fa'izar ta bada amsa ba yace samarinta zasu bata ? Ke kike ganin bata da kudi duk yaran nan da kike kallo sun fiki kudi , ke ki hadomin da lemu mai sanyi kafin mai samomin abincin da zanci ta shigo.
Fa'iza na kokarin fita daga gidan sukaci karo da Farida a bakin kofa, da yake gidan baya da zaure wanda ke wucewa ta waje ma zai iya hango na cikin gida, gidan kuma babu kaure sai labulen buhu da aka saka a jikin kofar,
Babu sahihiyar katanga sai fasashshin buloluwa da aka jera, wanda ko yaro karami ya wuce zai hango na zaune.
Fa'iza ganin Farida yasa ta tsaya tare da cewa, Farida da Allah ko kina da kudi ki rantamin na siyowa Baba sigari da lemu, anjima idan nayi awara zan baki, babu sauran kudi a hannuna duk na kasosu kasuwa canjin daya rage kuma nakai zubin adashe kinga lokacin biyan kudin haya ya kusa.
Dan murmusawa Farida tayi tare da cewa ai tunda kika ganshi can ya mimmike kamar gawar sababi yau bashi da ko sisi, dan haka ma wallahi bazan shiga gidan ba komawa zanyi.
Tun kafin Farida ta rufe bakinta ya fara kwarara mata kira amma tayi kunnen uwar shaggu dashi ta fice abunta.
Rungume na fito da magena sanye cikin kayan islamiyata, nasha nikaf dina kayana sun dauki guga sai zabgaga kamshina nake da turarena dana siya na naira hamsin wurin masu siyar da turaren dure.
Da sauri Baba ya tashi zaune tare da cewa Mamana barka da fitowa ? Murmushi nayi tare da cewa yawwa Babana barka da hutawa,
Yawwa Mamana za'a tafi neman ilimin ? Eh Baba na fada a takaice, mikewa yayi tare da cewa muje in rakaki, wannan shine dabi'ar mahaifina duk inda zan tafi indai yana gida tou fa lallai shine zaiyi rakiya,
A kofar gida muka hadu da Fa'iza sigarin ya ansa tare da cewa ki ajiye min lemun in dawo, shigewa tayi gida tare da cewa tom.
A tafiye muke yana zukar sigarinsa hankali kwance, Baba wai har yanzu baka samu kudin da zaka siyamin keken ba ? Na tambayeshi, magen hannuna ya ansa tare da cewa machine zan siya miki uwa ta gari.
Murmushin farin ciki nayi sannan nace Allah ya bada sa'a Babana , da amin ya ansa tare damin fatan alkairi dan mun iso bakin islamiya, magena na ansa na shige shi kuma yayi gaba.
Yau inacikin farin ciki, domin dai idan har Babana yacemin zaimin abu tou fa ko zai mutu sai yayimin, yana min san da duk duniya bayayi wa kowa irinshi, yana kaunata fiye da yanda yake san kanshi, yana so ya ganni a cikin farin ciki saboda ina da sunan mahaifiyarsa.
Yau ban wani yi karatu ba, hankalina ya tafi makarantar boko, na kagara gari ya waye dan injewa kawaye na da labari mai dadi zanyi sabon machine, nidai makarantar bokon haka nan nake zuwa dan ba abinda nake ganewa kaina fanko ne , a islamiya kadai Allah ya dafamin nake ganewa, amma a boko bana gane komai. Haka nan nake zuwa na dawo,
Koda na dawo gida na kasa boye farin cikina, amma babu damar na fada, uban da ya kasa biyan kudin haya taya zan fada zai siyamin machine ? Dan haka naja bakina nayi shiru, saboda nasan idan suka ganni da machine in zasuyi tunanin kanin Mamana ne ya siya domin shine yake dauke da hidimata.
Ina cire kayan islamiya ta na matsawa Inna sai ta bani kudi na siyowa magena kifi, bazan bayar ba shine amsar data bani , tare da hadamin da cewa itama kanta gari taci , saboda haka bataci kifi ba babu wanda zata siyama kifi.
Gaskiya Inna bazan iya ba "yar madara gari taci ba, nice sheda saboda kin hana kanki kin cida magen banza, inna ta bani amsa,
Tana fadar haka ta shige daki, na dade zaune a wurin ban samu mafita ba dan duk wanda ke gidanmu haushina yakeji kamar ya sakani wuta wannan dalilin yasa bana shiga sabgar kowa,
Saida na gaji da zama na tashi a wurin ganin ban samu mafita ba, daki naje na kwantar da "yar jinjirar mage na nabar gidan dan samo mata abinda zataci, gidane babu kayan dadi daga gari sai kanzo inama amfanin talauci, shi kuma Baba ko tsoron Allah bayayi yazo gaban kowa yaci kaza dan zalinci,
Amma duk wannan masifar Maman Fa'iza hada wani ciki ina tausayin dan nan da za'a haifa domin dai zai shigo rayuwar bala'e dama ya sani yayi zamansa baizo ba.
Haka nayi ta galbaro a cikin anguwa babu tsiyar dana samo, dole na hakura na dawo gida dan lokacin sallar magrib yayi,
Har bayan sallar isha'e Baba bai dawo gida ba, tunda naga ya wuce lokacin dawowarsa na sanyawa zuciyata salama tare da ba "yar madara hakuri, tunda ko mun tsaya jiransa bige zai dawo nasan yana can ya shawu iya shawuwa, mata hudu a gida amma yana neman matan waje. Tirrr da wannan hali.
Tunani barkatai a zuciyata, ciki kuwa harda tunanin yanda zamu wayi gari ba tare da bango ya fado mana ba, dan gaba daya gidan nan ya rube ga wani irin hadari sai bakin rai yake, lallai wannan ruwan yau idan ya kwace gaskiya akwai matsala.
Allah ka tsaremu da rayuwar talauci, rufe idona nayi domin inyi bacci addu'a nayi a fili cewa ya Allah ka tsare bayinka daga mutuwar katanga, kasa in kasance rayayya, in wayi gari cikin farin ciki, Allah ka shirya Babana ya daina abunda yakeyi,
Inna ta ansamin da amin, tare da cewa Allah ya tsare gaba daya gidan, ban mata magana ba dan haushinta nakeji ta hanani kudin da zan siyowa mage na kifi, wani busashshen garinta can ta ajiyemin kuma banci ba, nasan idan naje makaranta gobe Amisty zata kawo mana shayi da biredi daga gidansu, shi yasa kafin kekena ya lalace nake saka "yar madara cikin kwandon gaban keken mu tafi tare itama ta maida miyanta.
Da tunanin shayin gidansu Amisty nayi bacci, kuma dashi na tashi, tunda na farka naji yanayin garin da sanyi nasan jiya an kwana kwarara ruwa, dan haka tun kafin na sauko daga saman katifa nace Inna halan kin tara ruwan sama ?
Na tara, ai jiya banyi bacci ba saida na tabbatar na cika komai nawa da ruwa, cikin damuwa na kara jan yagaggen zanin da nake rufa dashi tare da cewa wallahi bana san wanka da ruwan sama sai jikinka yayi ta wani sulbi kamar ka kama maciji,
Banza tayi dani bata sake cemin komai ba, tsoki nayi tare da tashi ina mai mita cewa saidai kawai inyi sallah amma wallahi banyi wanka da ruwan sama, tsakar gida na fito rike da buta, ina maijin kyankyamin shiga bayinmu,
Danni tunin duniya nayi sallama dayin fitsari daga tsugune, ko zanyi bayan gida makota nake shiga, wanka kuma dama tsakar gida nake wanke jikina baya da cikina kawai nake wanke wa a cikin bayin, ina watsa ma jikina ruwa tsikar jikina tana tashi.
Dan gajeran tsoki nayi tare da daga labilen bayin na shiga, fitsari nayi na fito, a tsakar gida na wanke cinyoyina, nayi alwallah na dawo daki.
Tun ina sallah Babana yake kirana tare da cewa uwar masu gida kiyi sauri mun makara naga har 7:30am, bana so Baba yana bina makarantar boko saboda duk kawata daya gani sai ya bita gidansu ni wannan abun yanamin ciwo.
Tsaye na ganshi a kofar dakin mu yana daura agogo sai zuba kamshi yake yasha farar shadda sai daukar ido yake, murmushi nayi a zuciyata nace Baba kenan ko ba'aba ciki ba aba kaya,
Katsemin zance zuci yayi da cewa maida hankali Mama mu tafi, mikewa nayi ba tare da nayi magana ba naci gaba da shiri, a gaggauce na shirya, tare da shafa "yar madara nace zan rago miki, Babana ya rikemin jakar makaranta muka fito daga gida.......
_Gaba daya kaine sile, dan iska domin ni kai zan kira da kwarto, kaine silar rushewar rayuwata_
Cikin farin ciki muka fito daga gida, ina fadawa Babana yabi sannu karya bata jikinsa kasancewar ruwan daya kwanta saman kasa,
Cikin jin dadi muke tafe muna fira, har mun kusa fita bakin titi ya sheko da gudu tuki na rainin hankali, tuki na gadara, tuki na wulakanci da rashin arziki, tukun da basa kaucewa mutane saidai mutane su kwauce masa, duk lokacin da zai shigo anguwar nan haka yake shigowa idan ya taka mutum ya taka banza, ko dabbobi gareka saidai ka daure abunka amma badai maganar ka sakesu ba.
Tunda na hango motar nake cewa Baba dawo ta nan, amma kafin Baba ya hayo inda nake tuni yabi takan ruwan ya wuce shaddar baba ta koma brown, iya wuya raina ya baci kuma nayi alkawari ko zai kasheni tunda har ya tabomin Babana sai naci uwarshi a safiyar nan.
Da gudu nabi motar ina watse hannuwa na yanda ake zagi dakkuwa, ina zaginsa, shima Baba biyoni yayi da gudu cikin tashin hankali, yana Mamana dawo, wanda yayi nisa bayajin kira, a kofar gidanshi da yake kiwon dokunan shi anan Baba ya sameni ya rikeni, shi kuma ya fito daga motar da bulala dorina irin wacce ake dukan dokuna da ita.
Zagin dana taho inayi shi ya jawo hankalin mutane yasa duk mutane suka fito daga gidajen su, wanda ke waje suka iso wurin da muke dan ganin kwam,
Rikeni sosai Babana yayi tare da rufemin baki saboda yasan ban iya zuciya ba, shima abokansa da sauri suka rikeshi tare da cewa *Dikko* karka daketa dan Allah yi hakuri, Babana kuma cewa yakeyi ranka ya dade kayi hakuri don Allah bata san kaine ba,
Raina baci yayi ganin kamar mahaifina yana bawa yaron da haifa hakuri, dan haka na bambare hannun Babana daga bakina nace, nasan kaine kuma na zageka, ban kara maganar ba Babana ya wanka min mari.
Tunda nake a duniya magana mai daci ko muni Baba baya fadamin ita, yana tattalin rayuwata yana kaunata amma yau saboda wani sakarai ni Babana ya daka,
Ina cikin wannan bakin cikin Baba ya bashi hakuri da taimakon abokansa ya hakura suka ja banza suka shiga gidan da yake kiwon dokuna,
A raina na dauka alkawari yanda Baba ya dakeni saboda Dikko saina rama dukana a wurinshi...... Hannuna Baba yaja muka taho yana bani hakurin marin da yayi min, wai yayi haka ne saboda Dikko kar yayimin wani abu, saida ya sakani napep sannan ya koma gida,
Cikin bacin rai na tafi sch amma tabbas Dikko sai yaci kaniyarshi.........
{{{}}} {{{}}}
30/07/2019
Meelat Musa ce 🤙ðŸ»
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 2
Duk sanyi sanyin da akeyi saboda ruwan da aka kwana kwararawa a daren jiya hade da wani irin iska mai dadi amma Baba zufa yake kamar an tsare mai jegon da a saman gadon kara......
Cikin tashin hankali ya fara cire kayanshi yana dorawa a saman katanga, sai bakinshi dake motsawa babu wanda yakejin abinda yake fada saidai lokaci bayan lokaci yakan goge zufar data bulbulo daga jikinsa..
Ganinshi cikin wannan yanayi ya dagawa kowa hankali, gashi ya fita da farar shadda amma ya dawo da shadda kamar miyan goro,
Idan yana cikin yanayin fushi baya so kowa yayi masa magana haka kuma bayasan ganin kowa kusa dashi, mata da "ya "ya suka gane haka shi yasa babu mai shiga sabgarshi, idan yana cikin yanayin damuwa Sultana kadai ke zuwa wurinshi ta bashi hakuri kuma ya sauka saboda soyayyar dake tsakaninshi da ita,
Har na isa makaranta tunanin yi hakurin da Babana ya bawa jakin dana manta sunanshi nakeyi, sunanshi ya bacemin kwata kwata na manta sunan da aka kirashi dashi, nidai Allah yayi min jakar kwalwa, saboda ko "yan gidanmu ba dukansu nasan sunansu ba, amma na alakanta abun da yawan da muke dashi, yayin da wasu suke ganin rainin hankali ne......
Ko a aji naso na bawa Amisty labari amma na manta sunan wanda zan fada mata, Amisty itace kadai abokiyata duk a ajinmu, abinda kuwa yasa na zabeta tana da kokari sosai kuma idan ana jarabawa tana bani satar amsa,
Amisty irin yaran nan ne da idonsu ya waye tun suna cikin zanin jarintaka, bata da labari sai labarin maza, bata da aiki sai kallon B F, duk hotunan da zaka gani a cikin wayar Amisty hotunan tsiraici ne, walau nata walau na wasu, babu mai tarayya da ita saini kadai domin an dade da canfata cewar tana lesbian, nikam babu abinda ya dameni idan dai zata bani shayi nasha a tashi jarabawa ta bani satar amsa idan anyi rubutu nima tayimin a littafina shikenan banda wata damuwa.
Lokacin dana shiga aji har malami ya shiga ya fita, ga rubutu nan a saman allo, bana gane sunan subject haka nan kawai na kalli allon nadan basar tare da cewa ashe malam harya fita.
Da Eh kusan rabin ajin suka amsamin dan ina da masoya sosai, wasu saboda kyauna suke sona yayin da wasu kuma gashin kaina yake daukar musu hankali, okey shine abinda na fada kamar wata shegiyar baturiya dan itama okey din na dade ina koyonta a bakin Amisty dakel dai na samu ta zauna ram a cikin kaina, idan na fadi okey zakayi tunanin nasha turanci na koshi, amma babu abinda nake ganewa duk duniya sai sallolina biyar da Allah yasa na iyasu saboda nacin zuwa islamiya.
Ina zuwa mazauni Amisty tace yau ina kika baro mana Baban namu ? Wata irin faduwar gaba naji dan nasan Babana shima ba karamin tantirin dan iska bane, kodai itama Amisty Baba ya zagaya ne ?
Kinyi shiru, Amisty ta katsemin tunani na, maganata daukewa takeyi duk lokacin da ake tambayata abu, ina da nawar magana akan magana karama sai inja lokaci sosai, inayin in ina kadan wannan dalilin yasa ban cika yawan magana ba.
Dan gajeren murmushi tayi tare da matsawa, zauna tacemin tare da maida hankalinta akan allo taci gaba da kwafar note. Zama nayi tare da cewa wane malami ne ya shigo ?
Malama dai , wace malama ce ? Malamar English ! Me take koyawa na tambayi Amisty, turanci ta fadamin a takaice, murmushi nayi tare da cewa yarinya ai na gane dama dan inji idan zakiyi min karya.
Kedai kika sani, ni ciro littafinki na rubuta miki idan kin gama rainin hankalin naki, Amisty ta fada........ Bude jakata nayi sawon wani lokaci na kasa gano littafin da Amisty tacemin, tun ina dubawa a cikin jaka har na fito da duka littafan banga littafin turanci ba, dan gajeran tsoki nayi tare da cewa Amisty inajin nabar littafin a gida gaskiya.
Daukar littafin tayi domin shine a sama, ajiyar zuciya nayi dan nima ta gane wata jar wuya ce , nace da yake jiya nayi karatu na dauka na barshi a gida ne, tou kawai tacemin bata sake magana ba,
Haka malamai mata da maza sukaci gaba da shigowa har aka tashi daga makaranta, a bakin get din makaranta na tsaya ina jiran isowar Babana , tabbas nasan zaizo duk inda yake naji yana kusa dani yana zuwa bada jimawa ba.
Banfi minti 2 ba Babana ya iso cikin wata irin kafirar mota yanzu ma yasha wanka ya murza wata irin dakekiyar shadda, sai kasaita yakeyi, murmushin jin dadi nayi domin dai Babana ya kankaro min mutunci na idan yayo wanka saboda dan gayu ne na koyi a idon duniya.....
Cikin farin ciki na isa jikin motar na bude gidan gaba na wani kame abuna, zugar kawayena ne sukayo kanshi suna gaishe shi kamar yanda suka saba idan yazo daukata,
Dan murmusawa kawai yakeyi tare da karkacewa cikin izza ya jawo wasu irin "yan dubu dubu wanda shi kanshi baisan ko nawa bane , Amisty ya mikamawa tare da cewa ku saka kati.
Yana basu bai jira godiyar da suke mishi ba yaja mota muka tafi......, ba'a hana alkairi amma inajin bakin cikin abinda yakeyi, yabar gida da yunwa yazo waje yana alkairi, gida bai koshi ba yakai ma na waje banda gori da zagin iyayenmu babu abinda akeyi a cikin anguwa cewa Babanmu yana tsaye akanmu amma duk mu tsinannin Allah ne mu , haka zaisa ayi ta shiga da buhun na, na shinkafa gero masara katin katin na madara sugar da komai na sarrafawa idon duniya sun gani haka zai biyo dare ya kwashe abinshi yaje ya siyar wannan rayuwar zalinci ce, kuma bai sani ba kanshi kawai yake yaudara,
Kasa hakuri nayi nace gaskiya Baba ni kadaina zuwa daukoni makaranta daga yau, ba tare daya kalli inda nake ba yace miyasa Mamana ? Kawai banajin dadin abinda kake ne , me nakeyi wanda bai miki dadi ba ? Wannan kudin da kake bayarwa dama gida kabawa su Inna sukaci abinci gidan kowa yunwa ta kamashi babu mai wani sahihin abinda zaici maganar daya ce kullum daga gari sai kanzo.
Dariya yayi sosai tare da cewa Mamana kenan, aisu wannan mutane basa godiyar Allah, kima daina biye musu dan kona basu kudin cefane makalewa sukeyi, duk wanda kika gani a cikinsu daga mai tumaki goma sai mai shanaye babu adadi, idan na basu kudi boyewa sukeyi su hana ku abinci, suna can sun sayi dabbobi sunkai kauyika an boye musu, idan kuma kina magana akan abinda akayi ma wani kuma wannan halin shi ake kiran da hassada idan kikaga anyi ma mutum alkairi koya samu wani abu kikaji bakin ciki a zuciyarki shima hassada ne, kuma ita hassada tana cinye kyawawan ayyuka ne kamar yanda wuta takecin karmami, kuma yawan surutu yana sa mutum ya zama sakarai , ki daina hassada kuma bakinki shiru akan fadar wasu maganganu akaina idan kinki ji kuwa jahannama tsaye ko kina san ki shiga wuta ne uwar masu gida ?
A , a Babana, amma zan fadawa su Inna gaskiya su daina irin abinda sukeyi zalinci ne, abun tausayi Baba kaji yaran nan suyi ta kukan yunwa wallahi ni har tausayinsu nakeji, kyalesu Mamana kina iya fada musu gaskiya suji haushinki barsu da halinsu................Maganarsa ta kare ne a daidai lokacin da muka tsaya wata majalissa.
Fita muje, fitowa mukayi daga cikin motar muka tunkari taron dandazon mazan, kallo daya zakayi musu kasan cikakkin "yan tasha ne ko wannensu ya koshi da iskanci,
Gaishe su nayi tare da matsawa daga gefe na zauna, kai bata abincin nan taci mu wuce, Babana yayi maganar a daidai lokacin da yake zama,
Mikomin abinci akayi a cikin ci ka yada, { take away } gyara zamana nayi tare da juyawa inda babu mutane naci gaba da aiki, daga nan bansan abinda yaci gaba da faruwa ba, saidai naji hayani tayi yawa sosai anata bawa Babana hakuri ana rirrikeshi.
Cikin tsananin bacin rai yake cewa da Allah ku sakeni wallahi saina kwakwale mashi idanuwa tunda nayi rantsuwa saina makantashi duk cikar garin katsina babu wanda ya isa ya hanani aikata abinda nayi niyya, da sauri na tashi nayi wurin Babana ina bashi hakuri,
Abokin fadan Babana yake cewa, yo kai "ya "yan wasu nawa ka batawa rayuwa, saini kawai dan na kalli diyarka nace babban lambu zaka nunamin rashin kunya, cewa nayi zan shiga ciki ? Yabawa fa kawai nayi.... Sai kawai hankali ya tashi ?
Sanin kanka ne duk kasuwar data burgeni saina ci ta hanyar shiga inyi siyayya a cikinta, duk gidan giyar daya burgeni idan na shiga saina sha kwalba biyar karanci kenan idan banda kudi, haka kuma idan naga gidan karuwai zan shiga ne inyi ta ciyayyar abinda ya sawwaka ba tare dana gajiya ba,
Ka sani nima nasan haka, tunda saina gama nake ma gwanjon mata, banyi maka shamaki da matana ba haka diyana, kenan yanzu idan nace ka bani aron Sultana mu bata dare haka zakazo bakin kofa kayi tamin babatu ?
Da sauri Babana ya rufe idanuwan shi tare da kauda kanshi gefe guda, tunda ni bansan abinda ya assasa fitinar ba, tou miye b'ata dare ? Kila shaye shayen su suke nufi,
Jinjina kai Babana yayi tare da cewa kaci sa'a Mamana tana kusa amma zan maida ita gida na dawo na nuna maka karyar barikanci, yana fadar haka yaja hannuna mukayi gaba, har muka iso gida baiyi min magana ba, saida ya tabbatar na shiga gida sannan ya koma,
Da sallama na daga buhun kofar gidanmu na shiga, gaba daya gidan suna tsakar gida uwaye da yara, yaran mazansu da matansu sun gurfana gaban wani dakekin mutum bakikkirin da cikinshi kamar ace Allah saukeshi lafiya, ni a tunani na assembly ake musu saida naga Inna na tuna ba makaranta bace.
Saida nazo daidai inda suke nayi musu sallama kamar yanda na saba, ina kokarin wuce yace ke zonan, ban kalleshi ba kuma banzo ba haka kuma ban tsaya ba naci gaba da tafiyata na kusa shiga dakinmu naji yace waccan yarinyar ta raina mutane wallahi da nayi niyar yin hakuri amma na fasa sai kun tashi kunbarmin gidana.
Hayani ta kwace bakajin maganar wani duk maganar ta koma iri daya yi hakuri , Allah ya taimake ka Allah ya kara arziki ka taimaka dan Allah karka tashemu, kaji hauka akan wannan rubabben gidan suke wani hadashi da Allah yayi hakuri, Allah ma yasa ya tashemu nayi addu'a ta a bayyane,
Zainab ce ta tashi taje wurinshi tana wani irin karye karye, sai kace karyar gidan karuwa taga maza, magana tayi mishi babu wanda yaji abinda tace, saidai suka fita da mutumin, ganin tafiyarshi yasa kowa ya tashi yaci gaba da sabgar gabanshi,
Babana da Zainab bansan yanda suka kare da mutanen su ba, haka Dikko bansan inda yake ba, dan an dauki wani lokaci banji labarin yazo anguwanmu ba,
Kwanaki da dama sun shude, rayuwa tana tafiya babu abinda yayi gaba sai ci baya ake samu, amma ni na samu ci gaba na rayuwa domin dai Babana ya siyamin sabon machine kamar yanda yayi alkawari, a cikin matanshi kuwa maman fa'iza ta samu karuwa ta aihuwa, yanzu mun zama mu hamsin da takwas cas a gidanmu,
Zaune nake a kofar dakinmu ina yanke farce na, "yar kyakkyawar magena tana shan madara, Baba ne ya siyomin madarar da yawa nake bata danni yanzu na daina tausayin "yan gidanmu tunda na gane duk munafikai ne, Kuma Babana ina gani duk safiya yana basu kudi amma bansan ko nawa bane,
Kadangare ne ya fado daga saman bango fef, yana ganin mage ya ruga, ita kuma daina shan madarar tayi tabi kadangaren da gudu, nima binta nayi ina kiran "yar madara' dan bana so tana cin kwarika, kadangare ya rugawa mage, ni kuma nabi magen haka muka fita a guje mu dukanmu muna gudu a tsakar santa....
Shima a guje ya shigo kamar yanda ya saba, ganin yanda mutane ke rike yaransu, masu tumaki na kamawa hakan ya tabbatar min dashi dinne ya sake dawowa,
Nima kokarin kama "yar madara nakeyi, amma kafin in isa wurinta tuni dan iskan yabi ta kanta da mota ya wuce, jininta yayi tsartuwa a saman fuskata, yana wucewa na ruga na durkusa wurin magen, saida tayi miyau.......... Sannan ta daina motsi, wata irin ashariya na babba tare da kurma wani irin ihu dan naji bakin cikin takata da mota da akayi.
Cikin kuka na nufi inda yake, dama ina jiran zuwan shi saboda marin da Babana yayimin ta dalilinshi, shima din jirana yakeyi saboda zagin da nayi mashi waccan ranar, kowa yana jiran kowa,
Bayan yayi parking ya fito ya zauna saman bayan mota, yauma bulalace a hannunshi yana wasa da ita, sai wani cin cingom yake sai kace karuwa...
Abokan da yazo dasu waccan ranar yauma sune ya dawo dasu, mutum biyu tsaye a gefen damarshi biyu a haggunshi daya kuma tsaye ta gabanshi ya dade da bakin glashi,
Lafiyayen kato ne mai kirar "yan dambe, singileti ce a jikinshi sai wani maski maski yakeyi kamar anyi mishi wanka da mai, dan nesa dasu na tsaya tare da cewa a cikinku waye yake tuka motar nan ? Na nuna motar da hannuna,
Nine nan, mai kirar "yan dambe ya bani amsa, sannan yaci gaba da cewa ko wani abu ya faru ne ? Saida na kalleshi sama da kasa sannan nace da Allah mi yasa ka takamin mage ? Nayi maganar cikin sanyin murya, bashi ne ba nine na taka ta, kema idan kika tsaya a hanya gobe haka zanbi ta kanki in wuce kinji ko an mata, duk shi Dikko yayi maganar.
Mai kirar "yan dambe ya anshi maganar cewa, ubangida na yanajin dadi yayi da yaga yana wulakanta talaka irinki, yana farin ciki idan ya zauna daga nan muka fara watso kayanku daga cikin kangon can, da nayi niyar murde miki wuya ki mutu , mutuwa irin ta beraye a ranar da kika wa mai gida rashin kunya, abu daya yasa ban kasheki ba kasancewar ke ba kowa bace,
Murmushi yayi tare da cewa ta hanya mafi sauki za'ayi miki hukunci, juya kisha kallo, juyawa nayi a hankali dan inga abinda yake so na gani, babu gidanmu tuni wurin ya koma fili, lokacin da na juyo babu su Dikko babu alamarsu dan tuni sun jima da tafiya daga wurin.
Salati nayi tare da tunkarar inda "yan gidanmu suke tsaye cirko cirko domin babu abinda aka bari suka fitar dashi komai an danneshi cikin kasa, sai motaci dake ta kwashe kasar wurin,
Ina zuwa kusa da Inna da zumar tambayarta abinda ya faru ta rufeni da duka tare da cewa miya hadaki da Dikko kin dauko mana fitina kin jawo mana masifa Allah kadai yasan karshen wannan masifar.
Cacai cacai kowa hayani yakemin a saman kai babu damar a dakeni Babana yaba mace rasid'i, ke kuma diyar gida kimin magana kijawa uwarki masifa, dan haka abinda kawai suke cewa miya hadani da *DIKKO ?* ................
{{{}}} {{{}}} {{{}}}
31/07/2019
Kubi sannu ku kasance da wannan labari,
Taku a kullum Meelat Musa 🤙ðŸ»
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 3
Saida na gama kallesu daya bayan daya sannan nayi murmushin takaici da gefen bakina, kallon inda gawar "yar madara take na kalla wani makoko yazo ya tsamin a makoshi wanda ko yawun zan hadiye sai naji kamar lumfashi na zai dauke.
Dikko......................! Saida na jinjina sunan a zuciyata da kuma bakina, sannan na kalli dandazon taron ahalin gidanmu, nu na su nayi da dan yatsa manuni, sannan na dafa daidai kirjina da hannun haggu na , zanyi magana sai kuma maganar ta kasa fitowa dan bana iya magana a cikin yanayin bacin rai..
Wuri na samu na zauna ina ta sauke ajiyar zuciya, tsinuwa da zagi da Allah ya isa bansan iyakar adadin dozinan da suka saukemin ba, zagin ne dai kawai amma nasan bazan daku ba,
Har yanzu babu wanda nayi ma magana kuma babu wanda na sake kallo, zama nayi na sauke kaina kasa, yayin da wasu suka gaji da tsayuwa suka durkusa wasu kuma suka bazama neman gida, dan su zasu nemo shi dan ko sun tsaya jiran Baba ko yazo bazaiyi wani abu ba,
Bayan sun zauna ne sukaci gaba da tattauna maganar abinda Dikko yayi, ashe tun waccan ranar zagin da nayi masa ranar da zamu tafi makaranta tare da Babana bayan an bashi hakuri ashe baiyi hakuri ba.
Da zai jira har na dawo daga makaranta ya takeni da mota ya wuce abinshi, tou bayan ya fito daga gidan da yake kiwon dokuna yaga Babana ya fito daga gidanmu,
Shi Dikko mugune na gaskiya da gaskiya, duk duniya babu abinda ya raina yake kyankyami irin talaka, Dikko baya dariya haka kuma baya murmushi kullum fuskar nan tashi a hade take kamar hadarin tsakar dare,
Bakya ganin dariyar shi kwata kwata, idan kuwa har Dikko yayi murmushi tou tabbas yaga cuta, idan kuma yayi dariya tou tabbas ku idan kuka ga abun sai kunyi kuka saboda tsabar tausayi. Danshi sai yaga mugunta yake dariya.....
Bayan Babana ya wuce, Dikko ya kalli gidan ya sake masa kallo babu abinda baya gani na gidan daga nan waje inda yake tsaye,
Kallon rainin hankali yayi ma gidan tare da bata fuska ya juyar da kai ya kalli daya daga cikin wanda suka zo tare sannan ya kalli agogon hannushi yace waye shi.... Ya nuna Babana da gidanmu...
Bai tsaya yin magana ba ya bazama cikin anguwa, a cikin kankanin lokaci yaje ya samowa Dikko duk wasu bayanai daya kamata akanmu da rayuwarmu,
Jinjina kai Dikko yayi bayan yaji komai tare da cewa karta mutu, amma barsu na jikatasu zata gane Dikko ba sa'ar ubanta bane daga wannan rana tsoron Dikko zai shiga zuciyarta maza a nemo min mai gidan daya basu hayar gidan, dan gajeren tsoki yayi tare da cewa talaka banza a banza, za'a nuna mata su kudi jigo ne masu nuna ishashshen iko. Daga wannan rana zata gane mai kudi ba'ayi masa hawan kasa,
Cikin anguwa ya sake komawa dan binciken mai gidan da muke haya, aka fada musu anguwar da yake zama, da kuma wurin da yake zama dan kasuwancin shi,
Bayan sun gama daukar duk bayanin da suke bukata, sukayi tafiyarsu, ashe Dikko gidan da muke haya yaje ya siya, kuma mai gidan da muke haya yace wa Dikko Babana baya biyan kudin haya tuni yayi niyar tashinmu sai wata yayata take biyanshi kudin haya daga cikin kaddarar rayuwarta,
Tun wannan ranar Dikko ya biya kudin gidanmu, bayan ya biya tafiya ta kamashi, saida yayi wata biyu baya nan, shine fa yana dawowa babu notice kawai yasa aka rushe gidan......
Ajiyar zuciya na sauke bayan na gama jin duk bayanan su, yanzu ita Zainab zuwa takeyi anayin iskanci da ita kenan ? Amma ta bata wayanta,
Yawwa an samo gida ku taso mu tafi, gaba daya sowar farin ciki suka dauka tare da mikewa suna cewa a ina gidan yake ? Gidan Alhaji Sabo ne yace mu zauna dan yaji abinda ya faru damu kuma ya tausaya mana sosai, amma duk watan duniya yace zamu rika biyan dubu goma,
Eh hakan yayi babu wani damuwa, ku tashi mu tafi, yeay yara da manya sukayi ta shewa muka tafi dukanmu yayin da wasu ke cewa dan uwar Dikko yazo ya anshi wannan idan ya isa.
Haka muka koma gidan Alhaji Sabo dake makotan gidanmu da Dikko ya siya, bamu da komai haka muka shiga gidan, kowa daga ita sai kayan jikinta,
Nidai har yanzu banyi magana ba, abun duniya duk ya dameni kuma babu wanda yabi ta kaina ko Inna bata sake shiga sabgata ba sunyi ayari wuri daya ana ta shawarar yanda za'ayi a samo kudin Alhaji a bashi dan ya basu daga yau zuwa jibi su kawo mishi kudin shi.
Har safiya basu samu mafita ba, haka kuma Babana bai kwana gida ba, bansan yanda akayi ba suka shiga suka fita suka bawa Alhaji kudin hayarshi ba,
Kwanan mu hudu a sabon gida Baba yazo gidan, bai tambayi yanda akayi muka dawo ba haka kuma baibi takan kowa ba zance ya akayi aka biya kudin haya ba, haka kuma baiyi ma kowa magana ba saini daya,
Uwar masu gida lafiyar ki qalau kuwa ? Lafiya qalau Baba na amsa masa, yace kwana biyu bakije makaranta ba har kawarki ta tambayeni ko lafiya ? Nace mata lafiya qalau gaskiya, kinsan nima bana nan naje Abuja,
Allah sarki na fada, tou miya hanaki zuwa makaranta ne ? Ya sake tambaya na, saida na tattara bakina sannan nace Baba ai an rusa gidan, komai namu kuma an tattarashi an kwashe anje an zubar, banda kayan makaranta da littafai,
Wayyo Allah Mamana, taso muje waje muyi magana, mikewa nayi nabi bayanshi, yana gaba ina binshi har muka fita kofar gida,
Wuri muka samu muka zauna, muna zama Babana yace in fada masa dame dame nake bukata ? Nace masa ko kayan sakawa dukanmu gidan bamu da, kowa kala daya yake dashi, amma makota sun dan tattara mana kaya, murmushi yayi tare da cewa wallahi Uwar masu gida bata saka kwancen kaya, na dawo garin nan jiya da kudi fiye da tunaninki Mamana,
Tunda naji abinda ya faru tsakanin shadda da yadi da boyal saida na siya kusan kala arba'in, takalmi da agoguna da hulana duk babu abinda ban siya ba, kayan suna can na kai dinki,
Tsare Babana nayi da ido, a zuciyata kuma ina ganin rashin adalci irin na Baba, amma Baba bakada imani iyalinka na nan suna neman abinda zasuci karma ayi maganar wurin zama amma kai har lokacin siyan kaya kake yi Baba......? Duk a zuciyata nake wannan tunanin.
Mamana, ya kira suna na, kallonshi nayi ba tare dana ansa ba, tunanin me kikeyi ? Bayan gani a duniya ! Idan har ina nan a raye baki da matsala nayi miki alkawari zan kula dake zan kange miki duk wani bakin ciki da damuwa, idan dan maganar kayan makaranta ne da littafai zan siyo miki komai ma ki daina damuwa, zan miki duk abinda kike so dan kiyi farin ciki Mamana , wallahi da ina da iko ko kuda da sauro da ban barsu sunzo wurinki ba, haka nake alfahari da aihuwarki farar mace lantarkin ciki gida, da nasan zan haifeki wallahi da ban tara wannan yame yamen "ya "yan ba,
A ranar da aka aifeki a ranar naci makudan kudade a wurin wasan caca , tun daga ranar na gane ke mai sa'a ce, wannan dalilin yasa nasa miki sunan mahaifiyata ya karasa maganar yana murmushi, sannan yaci gaba da cewa zuwanki yasa talauci ya guji rayuwata, shi yasa na tattara miki buri da yawa domin nasan kedin mai arziki ce.
Yana fadar haka yace tashi muje, tashi nayi nabishi, yauma cikin wata zakanyar mota muka shiga, ta gaji da haduwa sai sanyin A C ke tashi ga kamshi mai dadin shaka, Babana fa dan gayu ne gashi da wayewa kuma yana da kalar burgewa amma babu halin kirki.
A daren nan saida Babana ya tabbatar duk abinda zan bukata ya siyamin, sannan muka wuce wurin dinki, tela ya aunani Baba ya biya kudi muka dawo gida,
Tunda muka dawo matarshi Mariya ta tada hankali ta fara zagina tare da aibatani, bata san Babana yana tare dani ba da batamin ba, yana shigowa cikin gida yace mata ta tafi ya saketa, maimakon Mariya tayi farin cikin sakin kawai sai ta kama kuka, dani Babana ke aure ya sakeni wallahi sai nayi farin ciki sosai na rabu da rayuwar wahala,
Amma Mariya saita durkushe tana bashi hakuri, wallahi ko sauraren ta baiyi ba, anyi an gama domin Babana idan ya saki mace ya gama da ita har abadan duniya baya maimaita mace idan har ya riga ya rabu da ita, dan yace ko sitira sawa daya yake mata mace kadai yake ma maimaici a rayuwar shi, shi yasa idan har ya saki yake mantawa da babinta a rayuwarshi.
Fita yayi yabar gidan, Mariya kuwa kuka takeyi kamar zata mutu, wallahi ta bani tausayi sosai dandai ba hurumi na bane dana bashi hakuri kuma tabbas nasan zai hakura amma ba ruwana tunda ba hurumi na bane, kuma nasan tsakanin gobe da jibi tabbas saiya karo aure.......
Zaune muke lafiya a gidanmu, rayuwar dai tana nan kamar kullum kowa shi yake cida kanshi, gaba gaba dai yayuna sun fara harkar barikancin su har a cikin anguwa, saboda Baba baya tsawa tawa dan yaga dama ma ya kwana biyar ko sati baya gida,
Bayan sakin Mariya da sati daya Baba ya auro wata "yar fiririyar yarinya wacce zata tsaya iyakar sa'ata, kankanuwar yarinya itama mai zubin karuwai, wankan tarwada ce kallo daya zakayi mata kasan ta gaji da fekewa da bari...
Idan kayi mata magana saita wani yamutsa fuska sannan zata daga idonta dakel tayi maka magana, kai nidai sam tsarinta bai burgeni ba haka kuma bata wani shiga raina ba, dan bata da kunya ko ta misali, caccakakkar "yar iska ce , tasha iskanci ta koshi, amma anyaBaba auro yarinyar nan yayi kuwa ?
Rayuwata nakeyi cikin farin ciki, bani da wata damuwa shi yasa bana gane abinda kowa yake ciki a gidanmu, idan na fito daga dakinmu sai dare nake komawa saboda Innata bata san gani na, dan kishiyoyi sun tisota a gaba da habaici saboda ni, Babana yana kula dani sosai baya barina shiga damuwa, ina zuwa makarantar boko da islamiya , amma boko gugar kaya kawai nake inje, islamiya kadai nake da fahimta.
Tafiye nake a cikin nikaf ina, sauri kawai nake na isa gida saboda hadarin daya taso, sai wani irin iska akeyi mai hade da kasa, walkiya da cidar hadari duk sun karade sararin samani, tunda na biyo santar nan banci karo da kowa ba har na iso inda nake tunanin nan ne gidanmu,
Kamar yanda nayi hasashe haka na yanki hanya domin shiga gida dan bana ganin gabana saboda kasar data shigar min ido, na daga kafata in taka sumintin kofar gidan naji wayam, kara mika kafata nayi dan a tunani na ban tako daidai ba, kamar yanda naji daga farko yanzu ma haka naji,
Da sauri na bude idona dan inga lafiya ? Filin wurin kawai na gani kamar ba'a taba gini a wurin ba, salati nayi na sanar da ubangijina to ina "yan gidanmu suka tafi ?
Makota na shiga na tambayi inda "yan gidanmu suke, aka cemin Alhaji Sabo ya canza mana gida kafin wata ya kare mu tashi, tambayar dalilin tashin da rusa gidan da akayi nayi amsar da aka bani itace, *Dikko* ne ya siyi gidan amma wannan karon anyi ma kowa uziri ya fita da kayanshi.
Bance komai ba saidai na sake tambayarta ina gidan yake ? Kwatanci tamin gida na like da gidan da aka rushe nan muka koma, ban sake cewa uffan ba na nufi gidan.
Daki daya ne tak a gidan saboda haka kowa yana zaune cikin barandar dake tsakar gidan, sallama nayi amma babu wanda ya ansa min sallamar har Innarmu, nima ban sake sallamar ba na samu wuri na zauna tare da jan bakina na kameshi,
Dukanmu a tsakar gida muka kwana yayin da wasu suka kwana a zaure, babban gida ne sosai amma daki daya ne ya gina shima ajiye ajiye yake a cikinsa, gari na wayewa na shirya na tafi makarantar boko, Baba bayanan sun tafi gasar caca, dan bai fadawa kowa sunan garin daya tafi ba, ni kadai yayiwa bankwana.
A makaranta Amisty ta lura ina cikin damuwa, dan haka ta tambayeni abinda ya dameni, ban fada mata ba, saidai nace mata da Allah waye Dikko a garin nan ?
Hmm su Amisty idon duniya saida tayi masa wani irin kirari sannan tace miya hadaki dashi ne ? Nace mata kawai dai labarinsa nakeji shi yasa nake san sanin koshi din waye.
Abinda Amisty tacemin shine, yanda kike takama Babanki yana masifar sanki da kaunarki dan dole wannan misalin da kanki zanyi shi idan ba haka nayi miki ba tou fa lallai nasan baza ki gane ba,
Dikko d'a daya tak a wurin mahaifin shi, yana da yayu mata sosai saboda suna da yawa gidansu suma, amma basu kai gidanku yawa ba, abinda yasa kuwa aka tara yawa a gidansu saboda san haihuwar d'a namiji da basu samu ba,
Akan Dikko ya samu namiji daga shi kuma har zuwa yau din nan ba'a sake haihuwar namiji ba, Dikko gaskiya yana da kirki kuma shi ba dan iska bane amma gaskiya baya san raini,
Yana da alkairi sosai amma shi baya dariya haka kuma baya murmushi, ni bayan wannan bansan komai ba haka dai kawai naji ana fada a gari,
Gyara zama nayi tare da tambayarta shi kuma waye ubanshi ? Murmushi Amisty tayi sannan tace da Allah karki dauki ne wake da shinkafa mana, Dikkon ne a katsina baki san waye ubanshi ba ? Wallahi ban sani ba, na bata amsa, tashi tayi ta barni a wurin dan ita a tunanin na sani jan zance ne.
Har muka tashi makaranta Amisty bata fadamin ko waye uban Dikko ba, ni kuma ana tashi makaranta ban tsaya komai ba na nufi gida tunda nasan Babana baya nan,
Tunda napep ta ijiyeni, na hango kofar gidanmu daddabe da mutane, Dikko yana zaune a saman gaban mota ya kwantar da bayanshi saman gilas din motar kafarshi daya saman daya, ya tallabo kanshi da hannayen shi, kamar kullum yauma cingom yake ci, kananan kayane jikinshi ya dode da gilashi mai saukin duhu.
"Yan gidanmu sun daddabe shi suna bashi hakuri amma ko inda suke bai kalla ba bare su sa a ransu zaiyi magana, sai waso mana kaya akeyi daga cikin gida, yayin da "yan zaginshi ke cewa ai tunda har kuka tabo mai gida a garin nan sai kun rasa gidan zama, wannan dinma ya siyeshi idan kunyi zuciya ku gina naku talakawan banza kuna jayayya da masu katsinar gaba daya,
Inda jakar islamiyata take naje na duka na dauka, na koma gefe nayi tsayuwata tunda ko nayi magana babu wanda zaimin magana kowa haushi nake bashi,
Wani dattijo ne shima makoci ne , yace ni inje in bawa Dikko hakuri duk saboda abinda nayi masa yake ta wannan saye sayen gidanje, dan gajeren murmushi nayi tare da cewa Baba kenan aini wancan dan iska nafi karfinshi wallahi baikai matsayin da zan kalleshi ba bare har na bawa banza hakuri, idan kuma har ka tilasta naje to lallai ina zuwa zan jawo dan iska ya fado kasa,
Lallashi na dattijon nan ya farayi akan lallai sai naje na bawa Dikko hakuri, a lokacin har an gama fito da komai namu an fara rushe gidan.
01/08/2019
🤙ðŸ»
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 4
Ya uzura min sosai akan naje na bawa Dikko hakuri dan haka na tunkari wurin kai tsaye zuciyana tana min tsake tsaken mugunta iri daban daban.
Cike da bacin rai na isa wurin, kamar yanda na fadawa tsohon nan zanyi haka kuwa nayi, dan ina zuwa na kamo kafar Dikko da zumar na fadar dashi kasa ya karya kashin baya,
Amma ina, dan ina riko kafar shi daya, ya tattakura yakai min halbi da dayan kafar da ban rike ba, hanci baya raina duka lokaci guda jini ya ballemin kamar an yanka kosashshiyar kaza,
Yana halbina ya diro daga saman motar shima ashe yayo dagon muguntar shi yana neman inda zan sauketa ya huta, ganin jini yana bimin baki har yana digowa kasa yasa hankalina ya tashi,
Sosai nayo kan Dikko, yaranshi suna kokarin rikeni yace su barni yanzu zai koyamin hankali yanda idan na ganshi da gudu zan canja hanya.
Daga nesa mutane suka fara bashi hakuri dan babu wanda ya isa yazo kusa dashi, babu wanda ya kalla bare kayi tunanin ko zai saurare ka, kusa dani ya matso sosai, yasa hannuwan sa biyu ya riko min fuska, sai yanzu nakejin halbin da yayi min yake ratsa duk ilahirin cikin kokon kaina, gaba daya jikina ya saki ya koma kamar ba nawa ba,
Sama sama nake ganin Dikko har yanzu bai daina cin cingom in da yakeci ba, saida yayi min kyakkyawan riko sannan ya cire gilashin dake fuskarshi ya kalleni ido cikin ido sannan yayi dan kyakkyawan murmushi, wanda ke nuni da mugunta ta tashi...
Sai mun sake had'ewa an mata...yana fadin haka ya k'uma min kanshi da nawa wuri daya wanda haka yayi sanadiyyar daukewar gani na gaba, amma har zuwa wani lokaci goshina da nashi yana hade wuri daya,
Bai sakeni ba saida ya tabbatar na tafi suma, dan tabe baki yayi tare da dage girarsa ta dama sannan ya sakeni ya zura hannuwansa cikin aljihu ya nufi motarsa dashi da tawagarsa suka bar anguwarmu.
Ni kuma na fadi kasa somammiya, Allah sarki dan uwa mai dadi duk "yan gidanmu basu ji dadin abinda Dikko yayi min ba, sun tausayamin iyakar tausayi gashi babu mai kwandalar da za'a kaini asibiti, saidai aka samo kankara aka rika dandan na min a goshina tunda habo ne nayi,
Abokin Babanmu shi yaji labarin abinda ya faru damu, yana da wani gida na Alhaji Sabo da aka saka a caca ya ciwo gidan, shine ya bada makullin gidan aka kawo mana yace mu bude mu shiga,
Daukata sukayi suka shiga hadani tare da bani kulawa ta musamman, amma duk abinnan saida nayi sati daya kafin na dawk daidai,
Babana har yanzu bai dawo ba kuma bamuji labarinsa ba ko ta waya, kuma har yanzu ban yadda na sake fita ba koda zaure saboda zuwa wannan lokacin bana san ganin Dikko ko inuwarsa,
Gaba daya na jingine islamiya da wata bokon banza, daga tsakar gida sai daki, idan ina tsakar gida naji karar mota ma daki nake komawa,
Satinmu ukku a gidan abokin Babanmu Baba baizo ba, kuma baiyo aike ba, shima kuma wannan gida da muke ciki Dikko ya siyeshi, ba'a gidan kadai ya tsaya ba duk gidan da yasan na hayane a anguwar saida Dikko ya sayeshi duk sun zama mallakinsa, tashin hankali da damuwa kowa ya shiga,
Saida abokin Baba yazo yake fada mana cewa an kama Babanmu yana can an kulleshi saboda ya ranci miliyan biyar din wani abokinsu bai bashi kudin ba, shine ya kaishi wurin hukuma suka tsareshi,
Kowa ya jinjina miliyan biyar saboda babu wanda yasan abinda Baba yayi da kudin nan, shiba gida ba, ba mota ba ba fili ba, haka kawai ya saka kanshi rikicin duniya.
Inna na kalla data zabga tagumi tana d'igar da hawaye, cikin yanayin tausayi nace Inna wai da zaki auri Babana bakuyi binciken halinsa ba kafin auren ku? Banza Inna tayi dani bata bani amsa ba, tsoki nayi tare daci gaba da cewa muma mata muna da matsala yayin da muka hangi tilin dukiya da babbar mota hankalinmu, ganinmu da kuma tunanin mu sukan b'ace , idan aka samu kwadayayyar zuciya sai kuma takai mutum ta baroshi, kamar dai ku duk zuciyoyi ne da kwadayin duniya suka kawo ku nan suka barku, kiyi ta addu'a kema Allah sa ya sakeki ki huta. Kunga mutum da arziki bakusan taya yai ya samu abinsa ba,
Inna dai bata tankamin ba, muka fito domin "yan gidanmu sunce muzo mu tafi wata primary school dake bayan gidanmu mu kwana tunda dare yayi kafin mu samu gidan zama, duk muna tsaye a tsakar gida dan Dikko yace wallahi idan muka kara cikakkun mintina biyar saiya kunna mana wuta,
Cikin kyarmar jiki nacewa Maman Fa'iza "yan uwan Babanmu basu da kirki kowa ya zura masa ido dashi da iyalanshi sai wuta mukesha babu mai roka mana sassabci a rayuwarmu, ansa daya ta bani itace, ai babu ubanda yasa shi aure auren kuma basune suka sa duk yayi cikunnan ku aka haifo ku duniyar ba.
Haka tayi ta surutai marasa dadi na bad'ala da rashin kamun kai har muka fita gidan muka tafi makarantar, koda muka fito motoci sunkai biyar masu zafi tsadaddu masu burgewa da daukar hankali, an haska fitilinsu duka, amma yau babu Dikko dan naji suna magana cewa mai gidansu yayi tafiya baya k'asa amma ya umurcesu da su tabbatar bamu kwana gidan nan ba, idan mun fita mun huta idan bamu fita ba a kunnawa gidan wuta, wannan shine sakon da Dikko ya aiko dashi,
A makarantar mukaci gaba da zama cikin azuzuwa, { Classes } idan dalibai sunzo zamu fita waje idan sun gama suka tafi zamu koma mu zauna, ni na gaji na fadawa matan Babana waisu basu da gidan iyayensu ne ? Wannan wulakanci ai ya isa haka, kowa ta tafi gidan ubanta ta huta mana, ai fa yak'ai yak'ai kamar zamu cinyeni d'anyata saboda tsabar masifa, dole naja d'an bawan Allahna nayi shiru.
Satinmu daya kullum sai an koremu kamar karnuka kuma kullum bama tafiya sai mun dawo, da safe kuma su tura yaransu su shiga bara cikin gari, rayuwa dai wulakantattar rayuwa mafi muni da k'ask'anci, Babana baya da adalci kuma baya da imani hakika zai tadda Allah, domin wannan zalincin yayi yawa.
Ranar da muka cika kwana takwas aka koremu da karfin bala'e mukabar makarantar malaman suka kara da cewa gwamnati bamu ta ginawa makarantar nan ba muje can musan inda zamu zauna amma ba makaranta ba, suka kara jaddada mana idan suka sake ganin wata wallahi sai sun kaita an kulleta wurin "yan sanda,
Nanfa Allah ya bamu sa'a cikin malaman wani ya ji kanmu ya bamu kyautar fili dan mun fada musu matsalar mu, shi kuma ya tausaya mana, saifa suka fara yahani akan fili yayin da kowa ke cewa saidai a siyar da filin a raba kudin aba kowa,
Yayin da wasu ke cewa ayi hakuri a zauna, masu cewa ayi hakuri a zauna sun rinjayi wanda keso asiyar, dan haka dole suka hakura, muka dinguma zuwa fili, bayan munje akayi tamalmala ta malmala aka siyo buhunna dasu aka zagaye gidan ,
Wannan fili dai bazai ansu a wurin Dikko ba, nima ganin mun samu mazauni hankalina ya komawa tunanin Babana,
{{{}}} {{{}}}
Bayan wasu kwanaki,
Rayuwata nakeyi cikin jin dadi, nidai Allah ya taimakeni bana bara saboda kanin inna yana kawo mana dauki da abinci, kunsan idan mace ta koshi tou fa lallai bata da aiki sai iskanci da rashin kunya, toni dana koshi nawa iskancin Dikko kadai yake nema ido rufe, kullum ina bisa hanyar zuwa tsohuwar anguwar mu, haka zan hau napep kamar duka kenan saina tabbatar mun kusa zuwa sai in dire abuna, wasu basajin fita ta wasu kuma suna gani idan suka bini basu kamoni ba saidai suyi min Allah ya isa, nima na fara dauko kadan daga cikin dabi'un Babana.
Yauma direwa nayi, da gudu nasha lungu na shige wani gida, zaure na tsaya saida na huta sannan na tattaro natsuwa na shiga ciki da sallama,
Cikin sakin fuska matar ta ansa min, wuri na samu kasa na zauna ina gaisheta, ta ansa lafiya lau, shiru nayi zuwa wani lokaci nace mata hajiya dan Allah kin iya rubutun wasika ? Murmushi tayi sannan tace niko na iya rubutun wasika, nace tou don Allah kitaima min mijin Yayata ne suka rabu shine yayi mata shegen duka ya raba mata kai da tab'arya tana can asibiti rai hannun Allah, kuma sai rubutun zagi yakeyi yana aikowa gidanmu, shine aka rubutomin ansa na maida mishi kuma takardar ta fadi, ni kuma idan na rubuta sabuwa zai gane rubutu na ne , amma ki taimakamin don Allah, ni na karanta wasikar kuma zan iya fada miki yanda take kiyimin rubutun nakai mishi don Allah........!
Ba tare da tunanin komai ba tace tou, daki ta shiga ta dauko jakar makaranta, da gani ta yara ce , a ciki ta dauko biro da paper tace min bismillah, duk ba tare da tayi wani dogon binkice ba ko yin nazarin yin hakan me zai haifar daga baya.
Ni ko dadi naji sosai a zuciyata , tunda ni bazan iya rubuta uwar komai ba, amma nayi farin ciki sosai domin dai yau zanci uwar Dikko kafin in fara kashe dawanki dan iska. Bayani na farayi ta fara rubutawa,
_Ka fita daga rayuwarmu yayin da ni kuma yanzun nakejin farin cikin shiga taka rayuwar, salon ka yana da matukar burgewa dan marasa tarbiyya, taya zaka fara rashin tarbiyya kuma ka gaji da sauri haka ? Ko kudin sayen gidajen ya kare ne ? To tunda kudin sayen gidaje ya kare nasan zakayi kokari ka samo kudin sayen dokuna, ina mai farin cikin sanar dakai daga yanzu d'innan har zuwa ranar da zaka bar zaman anguwar nan farin ciki zai bar zuciyarka, kuma zaman anguwar nan zai haramta a gareka kamar yanda ka haramta mana zama a cikinta, zanyi ta kashe dokunan ka harsai ciwon zuciya ya kama ka idan ka fasa kai ba d'an Babanka bane............_
_Sultana ce, Allah ya bawa mai rabo sa'a, idan kaje Islamiya kace amin......_
Mikomin tayi bayan ta kammala rubutawa, godiya nayi mata sannan na fita, nayi tafiya mai dan nisa ina kokarin bi hanyar da zata sadani da tsohuwar anguwarmu na hango Dikko ya sauko daga saman doki......,
Jar riga ce a jikinshi amma ba irin ja d'innan ba ja mai kyan kallo, sai jar hula akanshi irin wacce matasa ke gayu da ita, fesin cap, bakin wando ya saka wanda suke kira 3quater da rufaffin takalmi, sai bulalar da ake dukan doki a hannunshi, daga gani dai daga kilisa suka dawo,
A fili nace shege mai kama da mata, cin cigom kamar tsohuwar karuwa, duk'awa yayi k'asa ya d'auki wani abu wanda ban iya ganewa ba, bayan ya d'auka ya koma saman dokin yayi mishi diddige tare da tsuke bakinshi irin yanda ake kora doki yayi gaba,
Da gudu ya wuce ya wani d'an jirge saman dokin yayi kyau sosai bazan mishi haddasa ba gaskiya, ci gaba nayi da tafiya, kafin in ida isa wurin kuma naga ya wuce da gudu cikin mota kura tabi bayan motar sosai kamar guguwa ta taso.
Hamdala nayi domin na samu damar farko da zan kashe doki d'aya daga cikin dawakan Dikko, saboda nasan wata mugunta d'aya da ake ma doki, ba'a ba doki ruwa idan aka dawo dashi daga yawo, idan aka bashi ruwa a wannan lokacin tou cikinshi k'ullewa yakeyi ya mutu.
Nikaf ina na ciro na saka tare da gyara tafiyata na tun kari gidan kai tsaye, a kofar get in gidan nayi ma mai gadin gidan sallama, ya ansa cikin sakin fuska, nace mishi dama wani mutum ne da jajayen kaya a jikinshi yace in turo mishi kai yana can yana jiranka..... Na nuna mishi hanyar da Dikko ya wuce da hannuna ,
Cikin sauri ya wuceni ya tafi, yana wucewa na shiga cikin gidan, doki d'aya ne kad'ai wato shine dokin da Dikko ya dawo dashi, an d'aureshi a gefe kuma an cika bokiti da ruwa an ajiye shi kuma dokin yana ta bubbud'a hanci yana maida numfashi,
Da sauri na kinkimi bokitin ruwan nakai gaban dokin na ajiye, aiko ina ajiyewa ya duk'ar da kanshi yaci gaba dashan ruwa, a daidai lokacin da mai gadi ya shigo dan yabi hanya baiga Dikko ba ya dawo,
Kay kay kay ba'a bashi ruwa yana k'ok'arin isa dan d'auke ruwan na tareshi tare da cewa anshi yace ka ajiye mishi wannan takardar idan yazo da daddare zai karb'a, bai tsaya ansar takardar ba kuma baimin magana ba ya wuce,
Murmushin nasara nayi daga cikin nik'af ina sannan naje na ijiye masa takardar a saman kujerar da yake zama na wuce abuna.
Kafin ya isa tuni doki ya shanye ruwan dana ajiye mashi, sai dai abinda ba'a rasa ba, cikin tashin hankali ya ciro wayarshi daga cikin aljihu ya fara kiran wayar Dikko,
Mai gida kazo akwai matsala dokin daka dawo dashi yanzu, gashi nan zai mutu, yana fad'in haka ya kashe wayarshi,
Cikin k'ank'anin lokaci Dikko ya iso, a k'ofar gidan yayi parking ya fita da sauri ko murfin motar bai tsaya rufewa ba, lokacin daya shiga cikin gidan tuni dokin ya kwantar da kanshi k'asa yana ta zabura irin na fitar rai.
Meya faru haka ne ? Dikko ya tambayi mai gadin shi ! Cikin daburcewa ya fad'awa Dikko duk yanda mukayi dashi , sannan ya d'ora da cewa ga takardar can daka bata ta kawo ta ajiye, ajiyar zuciya Dikko yayi tare da furta wace ce ita tayimin k'arya ?
'Daukomin takaddar kila tana da wata manufarta a ciki, d'aukowa yayi yakai mishi, ya warware ya duba, cimimiye takardar Dikko yayi bayan ya gama karantawa ya dink'uleta wuri d'aya sannan ya jinjina kanshi, ya fito da sauri daga cikin gidan,
Wurin motarshi ya tsaya, tare da kaima gaban motar duka sannan yace wallahi cikin k'ank'anin lokaci duk inda "yar iskar yarinyar nan take cikin garin nan ku d'auko min ita, yana fadi haka ya shiga mota yaja fa fafa ya tafi kamar zai tashi sama.......
Har yayi nisa ya dawo, har yanzu mai gadin bai koma cikin gidan ba yana nan tsaye a wurin, yanzu daya dawo bai fito ba ya sauke glashin motar shi sannan yace, ku kawota wurina zan nuna mata nid'in d'and'an Babana ne wallahi wallahi wallahi sai tayi nadamar zuwanta duniya.
Yana fad'in haka ya juya a guje ya tafi, lallai da ganin yanayin shi gaskiya ranshi a b'ace yake, tabbas idan har aka kamoni aka kawai Dikko ni a cikin wannan yanayin lallai Dikko kasheni zaiyi,
Lokaci d'aya jikina ya d'auki kyarma naji fitsari ya kamani sosai, "yan hanjina suka juya ai bansan lokacin dana bar wurin ba, cikin tashin hankali na hau napep na nufi filin gidanmu, tun kafin mu isa na dire nayi gida da gudu........
Da sallama na shiga, Babana na gani zaune dashi da abokanshi kuma sune suka amsa min sallama, cikin farin ciki ya kalleni tare da cewa daga ina kike Mamana ?
Cikin inda inda na sosa kaina tare da cewa daga gidansu k'awata nake, murmushi Babana yayi tare da mik'ewa yace muje waje muyi magana, naso nayi masa gardama dan gani nakeyi kamar idan na fita zanga Dikko k'ofar gidanmu,
Muna fita na fara tambayar shi ya akayi ya dawo ? Yace min su Bello sukayo belin inshi, akwai wani wasan caca da za'ayi an saka naira miliyan hamsin kin san na kware sosai a wasan caca babu wasan cacar da za'ayi a ci ni saidai ni in ciwo shi yasa ake min hassada.
Gyara tsayuwar shi yayi tare da d'an jan dogon hancinsa, sannan yace Mamana kinsan ba'ayin wasan caca a bashi sai an saka k'addara, bani da k'addara sai kayan sakawata, na saka amma ance ba'asan sutura, tou Bello ya bani shawara wai in sakaki a matsayin k'addarata,
Cikin rashin fahimta nace Baba kamar ya za'a sakani a matsayin k'addara bayn nima banda komai... Murmushi yayi tare da cewa Mamana kenan ai kuwa kece ma mai komai domin keda kanki kece babbar k'addara ta shi yasa na zab'eki a cikin duk "ya "yan hamsin da takwas dana aifa.....
Kiyi hak'uri kawai ki yadda duk wanda yazo ya tambayeki kece k'addarata kawai kice Eh, danni na yadda da kaina babu ubanda ya isa ya ciwo uwata a wasan caca saidai ni inciwo uwarshi wallahi, Mamana ki yadda da Babanki nayi alk'awari baza a samu matsala ba, ki yadda dani kinji Uwar masu gida, ya k'arasa maganar yana mai rik'e duka hannaye na duka biyun yayi kalar tausayi.
Tou Babana idan aka tambayeni zance Eh kawai ko ? Yawwa Eh zaki ce kawai ya wadatar, insha Allah gobe kamar yanzu muna cikin kud'i kuma ga Uwata a tare dani, ya k'arasa maganar cikin farin ciki, murmushi nayi mishi sannan muka koma cikin gida dan in fad'awa su Bello na yadda..........
Allah yasa muyi juma'a lafiya, ubangiji ya sadamu da alkairan dake cikin wannan juma'a mai albarka, mugun ji da mugun gani tsaka mai wuya ubangiji ya tsare daga garesu, Allah ya karemu da jin kunyar duniya da lahira. Am3n,
Jamila Musa ce 🤙ðŸ»
02/08/2019
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 5
Muna shiga ciki tun kafin mu k'arasa inda suke zaune Baba ya fara cewa tou gata nan ku tambayeta kuji, a daidai lokacin da muka iso gabansu.
Ina k'ok'arin durk'usawa Bello yace a , a basai na zauna ba in tsaya a tsaye akwai abinda yake dubawa.
'Dan b'ata fuska Babana yayi tare da cewa kamar ya kana duba wani abu ? Ai a cikin sharud'd'an babu maganar wani dube dube, dan haka kabar yarinya ta zauna ka wani daina yi mata kallon k'urulla saboda rake ba sa'ar tsoho bane ba, dan koya bada kudin sa ya siya saiya ajiye tunda baida hak'oran cizawa, ya k'arasa maganar cikin sigar duniyanci.
Murmushi Bello yayi tare da cewa, ai zamani tafiye yake da ci gaba ko ba'a tauna ba a tsotsa, d'an b'ata rai Babana yayi tare da cewa, kaga da Allah mubar wannan maganar muyi abinda ya had'amu, ya k'arasa maganar cikin nuna rashin jin dad'in zancen nasu.
Gyara zama Bello yayi tare da cewa, haba Aliyu kasanni fa farin sani, kuma haka nima nasanka ciki da wajen ka, wane dare ne jemage bai gani ba ? Na hau tudu nabi ta gangare, kasan ko inacin kwarika wannan kwaron yayi min k'ank'anta shi yasa kaga bana cin shinge saboda na raina girmanshi duk da kuwa yana da mai sosai nafi gane kura ko da kuwa an soyata babu magi ba gishiri, kalmar dai d'ayace ake kira amma wurin hidimar da banbanci karka samu damuwa yaro ne sabon jini kuma bak'one a harka, yasan dad'in komai a duniya amma har yanzu baisan dad'in mace ba shi yasa kaga inata k'ara dubawa dan bana san a samu damuwa,
Dariyar mugunta yayi tare da cewa , wash ashe na manta malamar Babanta jarumin gaske ne a harkar wasan caca, Shima Babana murmushi yayi amma da ganin murmushi kasan na b'acin rai ne, yace Bello kenan, shiga ramin kura ba abu ne mai sauk'i ba, idan har kaga na fad'i a wasan cacar nan tabbas duk wanda yayi k'ok'arin kusantar min Mama saina ga bayanshi, wannan shine sharadi na,
Bello kuma cewa yayi kar muyi haka dakai Aliyu yaron nan d'an rigima ne, mu daina wannan maganar kawai dai muyi fatan Allah yaba mai rabo nasara, kallona yayi tare da cewa kin amince ? Jinjina kaina nayi tare da kallon Babana sannan nace na yadda............ Dariya Bello yayi tare da cewa magana ta k'are mata tacewa mijinta shege,
Kafad'ar Babana ya daka tare da cewa Aliyu muje, juyowa yayi ya kaleni tare da cewa yarinya ki shirya, idan kinga Babanki tou fa lallai an ciki a wasan caca, idan kuma kika ga Bello tou Babanki ya cinye matashin nan, ganinmu shine zai tabbatar miki Babanki yaci caca mu kuma munzo miki murna ne, suna fad'in haka sukayi gaba abunsu,
Bayan tafiyarsu ina zaune suku suku dani kamar asirin mayya ya tonu, ni ba Babana ne damuwata ba Dikko shine tashin hankalina, yace duk inda nake a gano ni, sai yanzu na gane na tafka babban kuskure dana rubuta suna na a jikin takarda, lallai na cika babban dak'ik'iya.
A b'an garen Dikko kuwa nema na sukeyi kamar rai da mutuwa, babu wanda yasan inda muka koma, daga makaranta prymary babu wanda ya sake jin labarinmu,
Rashin gani na yasa suka fara ba Dikko hak'uri, amma fur Dikko yace wallahi kafin sha biyun dare sai an nemoni idan har ba'a ganni ba zai iya sargafe kanshi ya mutu,
Duk iyakar yanda suka so Dikko ya hak'ura ya k'iya, ba nemoni bane wahala a wurinsu suna tausayin irin a zaftuwar da zanyi a wurin Dikko, dan ya fad'a musu ba mutuwar dokin ya b'ata masa rai ba, d'an marasa tarbiya dana kirashi dashi, bama shine baida tarbiyar ba iyayenshi ne basu da tarbiya abinda nake nufi kenan,sai kuma idan ya fasa shi ba d'an Babanshi bane. Wannan sune munanan kalamai masu muni da suke ta zungurar zuciyar Dikko.
Dikko yana da zuciya sosai, kuma fushin shi baya da kyan gani, idan ya nace akan abu sai yayi babu wanda ya isa ya hanashi, idan yace bayayi babu wanda ya isa ya tursasa masa yayi abinda baisa kanshi ba.
Yau Dikko yana cikin matsanan cin b'acin rai, yayin da ni kuma nake cikin fargaba da tashin hankali, dan yanayin dana ga Dikko d'azu ya bani tsoro,
Duk wanda yaji wannan abun yasan nice bani da gaskiya, domin ni naje har inda yake na jawoshi fad'a, ya Allah ka rabani da Dikko daga yau insha Allah bazan sake janshi fad'a ba, ka mantar mishi dani a rayuwarshi kuma ka bashi hak'uri a zuciyarshi, ya daina nemana,
Misalin 10:45pm Babana ya dawo gida, dashi da abokinshi Bello a lokacin har nayi bacci Baba yasa a tadoni in samesu kofar gida......
A waje na samesu, gaishe su nayi tare dayi musu sannu da zuwa, Bello kad'ai ya ansa amma Babana ya kasa magana, Bello ne ya fara magana kamar haka.
Maryam, wannan shine sunan da Babana ya sakamin, wato sunan mahaifiyar shi, darajar wannan suna ne yake kirana da Uwar masu gida ko yace Mamana, Bello yaci gaba da cewa an samu matsala mahassada suka cuci Babanki bandai san yanda abun ya faru ba gab da za'a fara wasa kwalwarshi ta juya, ba buk'atar dogon bayani kawai dai Aliyu ya fad'i wasa.
Tou idan ya fad'i sai kayi ya ya kenan ? Na tambayi Bello, sai zamu tafi dake wurin wanda ya ranta masa kud'in, dan a can basu yadda da ansar mace ba, sai wani ya buk'ata dan haka ya bada kud'in yace a kawo mishi ke,
Waye shi ? Na sake tambaya, a tak'aice ya bani amsa cewa idan kinje kin ganshi, zan k'ara magana Babana yace Mamana babu abinda zai faru kiyi hak'uri kuje dan bana tunanin akwai wanda ya isa yayi miki wani abu a cikinsu saboda sun san waye ni, na bud'e bakina zan sakeyin magana a karo na biyu, wanda Babana ya sake tare min numfashi na da cewa idan dai har kare zai iya farautar kura tou lallai wani abu zai iya shiga tsakaninku, idan kuwa kare bazai iya ba tabbas zasu dawo dake, dan duk rashin kunyar kare ta gida ce, bishi kuje.... Yana fad'in haka ya juya da zumar shiga gida,
Da gudu nabi bayan Babana na rik'e hannunshi ina kuka nace haba Babana laifin me nayi maka zaka sayar dani ? Cikin kulawa ya kalleni tare da gogemin hawayen da suka zubo saman fuska ta sannan yace, baki sawuwa Mamana saboda nima bada kud'i nasiyo ki ba, haka kuma bakya satuwa tunda Allah shine ya azurtani dake, hak'ik'a kuma baza ki ciwo ba ta sanadiyar wasan caca ko kun tafi sai kun dawo, dan haka ki zama d'iya mai biyayya a gareni,....
Baba.....Mamana ya fad'a kafin nace komai, yaci gaba da cewa, so guda d'aya ne tal a zuciyar ko wane d'an adam, amma shi wannan san a duniya za'a kasa shi kaso mutane so adadin haka, uwa, uba, d'a da kuma mata, banda uwa banda uba, kuma ni Allah bai d'oranmin ciwon son "ya "ya ba, bare mace da ban d'auketa a bakin komai ba, wannan son nawa gaba d'aya kece na martaba ki dashi saboda ki zamo d'iya mai sharewa Babanta damuwa. Sakin hannu na yayi tare da cewa sai kun dawo, yana fad'in haka ya shigr gida.
Inaji ina gani suka tasa k'eyata gaba suka sakani mota mukabar k'ofar gidanmu, tafiya mukayi mai nisa sosai, sannan Bello da abokinshi daya taho dashi suka fara magana,
Bello yace, alhamdulillah na zurashi rami na gama, kasan Aliyu yana tak'ama da tasha ni kuma zan k'ure mishi tashi tashar shi dan abinda yayi min bazan manta dashi ba nima saina rama akan wannan d'iyar tashi daya d'auka san duniya ya d'ora mata,
Bello yaci gaba da cewa nine na bada kud'in nan cas saida na ajiyesu sannan akayi caca, bana asara zan kaita inda za'a bani kud'ina har a d'ora mani riba, ina tsoron wai wai da bayan da Aliyu zaiyi wallahi da nine zanyi mata kaca kaca da rayuwa amma yanzu zan kaita wurin gwamnati idan zai iya yayi fad'a da hukuma in gani.
Ai kaji shi wai Allah baisa mishi ciwon san "ya "ya ba, nima shi yasa ban zab'i ko d'aya daga cikinsu ba dan nasan duk wacce na d'auka abin bazai mishi ciwo ba, nima ina so in dasa masa irin tabon daya dab'a min a zuciyata wanda bansan ranar da zai gogo ba,
Ajiyar zuciya Bello ya sauke tare da cewa da Allah sake kiransu ni fa ba abinda ya dameni da wani fushin banzar shi, dan ba fushi yakeyi ba ko mutuwa akayi mishi ni kawai tafiya zanyi idan munje can ayita ta k'are, abokinsa yace to idan masu gadi suka hanamu shiga fa ? Daina min ma wannan bak'ar fatar taka da Allah, duba min magungunan nan Allah yasa ban zubar dasu ba wurin wancan sakaran, wata "yar k'aramar leda ya d'auko ya mik'a ma Bello tare da cewa gasu nan, dariya Bello yayi sosai tare da cewa kasan bak'one dole saida "yan rakiya,
A daidai lokacin daya fara magana a waya, nifa dama basai yana harkar mata ba, to dama banda abinka duk wanda kaga yana harkar mata ai koya yayi, nifa taimaka min zaiyi kuma na taimakeshi, saurara ka taimaka mana kazo ka shigar damu gidan idan muka shiga duk nasan yanda zanyi da Allah, tou babu damuwa gamu nan isowa ba jimawa, haka yayi wayarshi har ya gama, yakan d'auke maganar sa danjin abinda abokin wayar tasa zai fad'a, yana fad'in haka yaja motar muka tafi.
Ni kuma tunanin abinda Babana yayi masa kawai nakeyi wanda har yasa zaiyi ma Baba ramuwar gayya, ina tunani naji yana dariya tare da cewa an fad'a maka ni sakarai ne ? Ai kaima kasan baiyi cacar ba dan ubanshi dasai yaci, mugu ya saki baki ya lashe kud'i mu kuma muka lashe "yar sa, dariya ya k'arayi sosai tare da kaiwa sitiyari duka yace kud'i na biya malamai suka sa banza wasi wasi....... Amma ai kasan Aliyu maye ne da yayi wasan caca da gaske dasai ya lashe kudin nan kamar yadda karuwa ke lashe sabon harka..........
Ya kuma sabon harka ? Su sai suyi ta magana juyayya wanda sai su "yan bariki kad'ai suka isa su fassara yaren, ina ne nan kuma ? Na tambayi kaina yayin da muka tsaya gaban wani k'aton get, ga jami'an tsaro masu yawan gaske kowa ya kame da bindiga takai tsawo na, za'a fara magana wani daga cikin mota yace barsu su shiga tare muke,
K'arfe ne aka d'age mana muka shige saida mukayi tafiya mai d'an nisa sannan muka tsaya, daidai da daidai kowa yana zaune cikin mota wanda ya shigo damu yace, Bello bana so nayi maka gardama ne kaga kamar wani abu amma na rantse maka da girman Allah Dikko baya neman mata,
Wani irin tashin hankali naji yayin da naji an kira sunan Dikko sai yanzu na tuna da Dikkon da zaici uwata, hankalina na mayar a wurin Bello dake cewa kai ai sakaran banza ne idan zai nemi mata shawara zai maka ? Ai ba'a shedar namiji akan mace, murmushi mutumin yayi tare da cewa Bello na rantse maka da girman Allah har al-qur'ani zan iya dafawa Dikko bai harka mata,
Tsoki Bello yayi tare da cewa muje idan zaka raka mu dare nayi, jinjina kai yayi tare da cewa muje, yana gaba muna biye dashi saida muka wuce get ukku kafin mu isa, kuma duk inda mukaje jami'an tsaro ne har muka isa bakin wata k'ofa, dukkannin mu anan mukayi parking, kulle min ido da hannu Bello yayi bayan mun tsaya.
Rufe motar yayi da makulli sannan suka shiga ciki, wurin zama aka basu tare da cewa su jirashi yana zuwa, sunyi zaman daya wuce mintuna talatin sannan Dikko ya fito cikin tsananin b'acin rai dan har yanzu maganganun Sultana caccakar masa zuciya sukeyi, kuma ma koba komai dama shi Dikko ba ma'aboci sakin fuska bane,
Gaishe shi sukayi, da kanshi kawai ya ansa gaisuwar tare da tsare su da ido, mutumin daya kawomu shine ya d'urkusa gaban Dikko yayi masa magana k'asa k'asa wanda babu wanda yake iya jiyo abinda yake fad'a,
Kallo su Bello Dikko yayi tare da cewa da Allah kuyi hak'uri ita rayuwa sannu ake binta, babu wanda yasan abinda anjima zatayi bare kuma gobe, kar kace zakayi ramuwa akan duk abinda akayi maka wannan ba d'abi'a bace mai kyau, halin mutunan kirki sukan manta da duk wani abu mara kyau da akayi musu, ka zama mai yafiya akan ko wane irin mutum idan yayi maka laifi, kaima sai Allah ya gafarta maka, miliyan nawa ne ka kud'in ? Dikko ya karasa maganar tare da tambaya,
Cikin kwantar da murya Bello yace miliyan biyar ne na zuba, Dikko yace tou kai Sani kuje dashi ka bashi miliyan goma, a rik'a hak'uri kaji bawan Allah, gyara zama Bello yayi tare da cewa kayi hak'uri gaskiya ni ko miliyan d'ari zaka bani wallahi basu ne gabana ba a yanzu kawai so nakeyi ka ramamin abinda ubanta yayi min.
'Daure fuska Dikko yayi domin duk cikin k'arfin hili yake magana, shi duk duniya babu abinda ya tsana irin mutum yace ya wulakanta shi, danne zuciyarshi ya sakeyi tare da cewa kayi hakuri gaskiya Dikko baya neman mata,
Kayi hak'uri ranka ya dad'e ka ganta ko so d'aya ne nasan zatayi maka, kai jeka taho da ita da sauri, duk Bello ya fad'a ba tare daya bari Dikko ya sake cewa komai ba danshi Dikkon ma harya gaji da magana yayi shiru.
Kamar wata b'arauniya haka ya jawoni har yanzu idona a rufe yake, lallausar kafet in dana taka da wani sanyi mai shiga jiki sai wani irin daddad'an k'amshi mai dad'in shak'a naji, hakan ya tabbatar min an kawoni inda za'aci mutunci na, har yanzu banyi magana ba amma idona ya cika da hawaye dan da ba'a rufemin idona ba babu abinda zai hana na cika d'akin da kuka.....
A gaban Dikko aka durk'usar dani, amma shi ya kauda kanshi gefe d'aya bamu yake kallo ba, hankalin shi yana kan T V danma baya so ya kalli ko wace ce aka kawo dan babu zuciyar wanda shed'an bazaiyi wasa da ita ba,
Bud'e min fuska akayi da sauri na bud'e duk girman idanuwana na fara kalle kalle, innalillahi na fad'a a fili a lokacin da idonuwa na sukaci karo da *Dikko* tare da fara k'ok'arin mik'ewa,
Har yanzu Dikko bai juyo ba, dan haka nayi shiru dan karyaji magana ta, hijabin jikina suka ciremin da hular da na saka saman kaina, sannan aka turani saitin inda Dikko ke kallo, gaba d'aya kunya ta kamani dan haka na duk'ar da kaina k'asa,
Dikko bai kalleni ba, kuma baiyi magana ba, inaa tsaye a wurin kaina na kallon k'asa hannuwana kuma suna d'aure ta baya na, ina tsaye a wurin shima Dikko bai dainaa kallon T V ba dan har yanzu bai kalleni ba bare na tabbatar daya ganeni ko bai ganeni ba,
Shiru kowa yayi babu wanda ya sake magana har kusan tsawon awa d'aya, Bello ya gaji yace ranka ya dad'e zamu koma, yanzu ma kai ya jinjina ma Bello , matsowa Bello yayi a kusa da Dikko ya ajiye ledar daya zo da ita sannan yayi magana banji abinda yace ba, amma wannan karon Dikko bai ko motsa kanshi ba, fita sukayi suka tafi, shima wanda yayo mana jagora bin bayan su Bello yayi Dikko yace idan ka fita kaja man k'ofar,
Cikin girmamawa yace tou, yana fita yaja k'ofar gam wanda rufeta yasa naji wani irin tashin hankali na saki baki na fara kuka da dan Allah kayi hak'uri kar muyi haka dakai, mugu kenan yaji mugunta dan haka ya fara murmushi, ashe ma yafi kyau idan yana murmushi,
'Dan wasa yayi da idanuwan shi sannan yad'anyi motsi da kanshi kamar yaji kid'a, saida ya k'ara k'ayataccen murmushi sannan ya d'aure fuskarshi kamar baisan miye dariya ba, ya tsareni da idanuwanshi masu sa mutum yaji yanajin fitsari, da sauri na mayar da kaina k'asa gabana yana ci gaba da bugawa.
Wayarshi ya d'auka yayi danne danne sannan ya k'ura mata ido, d'an tab'e bakinsa yayi a daidai lokacin daya kara wayar a kunnen shi yana cewa duk duniya me mace "yar matshi ya ta tsana ayi mata ? Kallona yayi sosai sannan yace 16 zuwa 17, mai maganar a waya ya dad'e yanawa Dikko bayani, murmushi Dikko yayi har saida kyawawan hak'oransa suka fito sannan yace yayi tare da ajiye wayar,
Mik'ewa yayi bayan ya gama wayar ya kulle k'ofar da makulli ya tafi dashi ciki ya barni anan falo tsaye kamar wata gunkiya,
Bayan kamar wani lokaci mai tsayi ya dawo, inda ya zauna da farko a wurin ya sake zama sannaan yace min zo nan, babu musu naje gabanshi na durkusa kamar yanda naga anayi mishi,
Ya sunanki ? Suna na Sultana, da Allah me kike so nayi miki wanda zai tabbatar miki dani d'an Babana ne, shiru nayi bance komai ba, gyara zamanshi yayi tare da mik'e k'afarshi ya taka saman kafad'a ta, yace ina saurarenki.
Kayi hak'uri don Allah sharrin zuciya ne, to kinga kin kasa ba zuciyarki hak'uri a lokacin dana b'ata miki , ni yanzu waye zai ba tawa zuciyar hak'uri ?
Kayi hak'uri don Allah insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba, kayi hakuri don Allah, kwantar da kanshi yayi jikin kujera yana nazari har yanzu k'afarshi tana kan kafad'ata, ba tare daya taso ba yace gaskiya kamar zan hak'ura amma na fasa,
Dan Allah kayi hak'uri, tasowa yayi tare da cewa wallahi bazanyi hak'uri ba yau zan nuna miki cewa ni d'an Babana ne, kuma da kanki zaki sheda ya iya haihu a daren nan zuwa safiya zaki anshi hukunci mafi munin hukunci, zan baki mamaki kuma zan nuna miki Dikko ba sa'an wasan yara bane, zan biga tambarina a zuciyarki za kiyi ta kuka daga yau har zuwa ranar mutuwar ki, yanayin farin ciki ko damuwa duk wanda kika shiga wallahi baza ki manta da Dikko ba a rayuwarki, dani dake kinga saiki fad'amin waye ciwon zuciya zai kama.....
Ka rufamin asiri, ke yarinya ya fad'a tare da takamin bakina da k'afarshi, da sauri na janye fuskata gefe guda tare da goge bakina da kafad'ata, kam balasti kafatace kike gogewa baki ? Tou bari kiji in fad'a miki wannan k'afar tafi ubanki tsafta, tafi uwarki ni kuma nafiki banza kazamiya d'iyar d'an caca, saboda san duniyar da bata da tabbas ubanki ya anshi kud'i ya bada ke, mutunci da ko wace "yar mutunci da iyayen mutunci suke tattalawa amma ke ya siyar dan biyan buk'atarshi,
Da sauri na kalli Dikko raina amatuk'ar b'ace nace gaka babban d'an iska da zakayi fasik'anci dani a cikin gidanku, ni ba fasik'i bane yarinya ki tambaya kiji ni babu mata a tsarin rayuwata shi yasa bana sabgarsu, amma kedai yau sai nayi miki kaca kaca wallahi yanda ko sunan Dikko kikaji sai kinyi fitsari, ya kara sa maganar tare da sake maida k'afarshi ya takamin baki,
Sake janye k'afar nayi daga bakina na k'ara juya kaina gefe, dariya Dikko yayi tare da sauko kafarshi saitin k'irjina ya taka tare da tura babban d'an yatsan shi cikin riga ta sannan yaja da k'arfi, b'earr k'arar yagewar rigata, cika idona yayi da hawaye kuma ga hannu na d'aure ta baya, dan girman Allah kayi hakuri karka ciremin kayana,
Sai k'ara tattakani yakeyi, gajiya nayi da iskancin shi nace sakaran banza kwance min hannuna na kaga yanda zanci k'aniyar ka a daren nan,
03/08/2019
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 6
Idan na kunce ki zaki iyamin wani abu kenan ko ? Eh na fad'a cikin kwarin guiwa,
Murmushi yayi kad'an da gefen bakinshi sannan ya kuncemin hannu na, mik'ewa nayi da sauri na d'auka hijabina na saka, sannan nayi hanyar fita da gudu,
Dukan k'ofar d'akin na farayi tare da kwarara ihu a kawomin d'auki, Dikko bai sake bi takaina ba ya tashi ya shige ciki, dan yasan inda nake ihuna banza ne kururuwata wofi...
Alwallah yayi bayan ya shiga yai kwanciyar shi, duk abinda Dikko zaiyi bayayin shi kai tsaye zai dad'e yana tunani idan yayi abun bayan wani lokaci me zai haifar mishi ? Yana duba duk abinda zaije ya dawo kafin ya aikata.....
Ni kuma gajiya nayi da doke doken k'ofa na zauna a wurin saboda har muryata ta shak'e tama daina fita sosai, a wurin na zauna har asuba banyi bacci ba ina zaune,
Koda asuba a gabana Dikko ya fito da jallabiya brown a jikinshi da hula fara wacce ake cema tashi da kwakwa hannun shi d'aya a aljihu d'ayan kuma rik'e da makulli, bud'e k'ofar yayi da makullin ya fita, kuma yana fita yasa makulli ya rufe ta waje,
Nima tashi nayi na shiga ta hanyar dana ga Dikko yake bi yana tafiya, hanyace doguwa sosai ta tafi d'od'arar tasha tayils sai kyalli yakeyi mai d'aukar ido, sai tukwanen shukoki da suka sakani tsakiya, wato wasu a gefen damata wasu a haggu na,
Ina zuwa k'arshe naga hanya ta rabu biyu, daidai bangon da hanyoyin suka rabu kuma anyi rubutu wanda bansan abinda aka rubuta ba, saidai zuciyata ta gargad'eni da na tsaya karna fad'a inda zan kashe kaina.
Dole naja na tsaya daga nan, zama nayi a wurin, ban wani dad'e da zama ba Dikko ya dawo, a daidai inda nake zaune yace taso muje ya fad'i maganar ba tare daya tsaya ba,
Da sauri na tashi nabi bayanshi dan zuwa wannan lokacin zuciyata ta tabbatar min babu abinda Dikko zaimin, yanayin shi abinda na lura yanayin abu na mutuntaka, yana da ruwan mutanen kirki kila zai tausaya min.
Allah ka azurtamu shine abinda na fad'a a zuciyata yayin da na shiga d'akin Dikko, banda cikakkiyar natsuwa a wannan lokaci shi yasa ban wani damu da abinda d'akin yake ciki ba, saman kujera ya zauna tare da cewa ga wurin wanka can ya nunamin da hannunshi,
Ki fara wanka sannan kiyi alwalla, zaki ga ruwa yana nan na zuba miki dan karki je kiyiwa mutane kauyanci, a inda ruwan yake anan akeyin wanka kuma karki sake kimin fitsari a ciki,
Banza nayi na kyale d'an iska na shige, saida nayi fitsari na a inda yace baya so sannan nayi wanka nayo alwallah na fito, wurin da zanyi sallah ya nunamin ina kabbara sallah ya shiga toilet in,
Jinjina kanshi yayi sannan ya fito ranshi a matuk'ar b'ace , ko ya akayi ya gane nayi fitsarin oho ! Rashin sani ashe ya gwada ni ne yaga idan ya kyaleni bazan sake mishi rashin kunya ba, idan ya tabbatar banyi fitsarin ba zai fitar dani na tafi gida,
A fili yace shawar dare zan d'auka kawai, ledar da Bello ya ajiye mishi jiya itace ya d'auka ya fita, ashe maganin maza ne a ciki, Bello yace masa duk wanda yayi masa a ciko tou shi zaisha guda d'aya, shi kuma a nashi tunanin ko wanne zaisha guda d'aya a ciki,
Duka magungunan nan babu wanda Dikko baisha ba, bayan ya gama sha ya shigo, a lokacin na gama sallah ina zaune wurin da nayi sallah, gyara labuleye ya farayi lokaci guda duhu ya fara bayyana a d'akin, kashe hasken fitilar dakin yayi lokaci guda yanayin d'akin ya koma kamar dare,
Bansan ya taho ba saidai naji an rik'oni cikin duhu, saida ya rik'eni sannan ya mik'ar dani tsaye amma baiyi magana ba, fitilar wayarsa ya kunna sannan ya sakata a aljihun gabar rigarshi,
Kamo fuskata yayi a bakina ya cuccusa min wani abu sannan ya nad'e bakin da salitaf, hijabina da zanin jikina ya cire ya zubar awurin, ganin da gaske yake yasa naji wani irin k'arfi yazo min na kwace na fara kai duka ba tare da nasan inda yake ba saboda duhun da d'akin yayi,
So d'aya na sameshi kawai ya rik'e hannuwana duka yace ni kika daka ? Waye yace miki ana dukana ? Murd'e min hannu yayi saida yayi k'ara sannan yace ko a gidanmu ba'a tab'a dukana ba kuma babu mai min kallon banza kowa so yake ya kyautata min dan insan dashi. Ke kuma kimma samu Dikko a arha har wani kai mishi duka kike ? Zanyi maganin rashin kunyarki yanzu nan.
Hannun daya murd'e shine ya jani dashi har zuwa bakin gado, jefani yayi saman gadon zuwa wannan lokacin ko motsin kirki bana iyawa saboda murd'ewar da yayi ma hannu na, shima jallabiyar shi ya cire tare da hawowa saman gadon.
Gaba d'aya Dikko ya zare hankalinshi da tunaninshi ya fita daga jikinshi, babu wani sauk'i bare tausayi ya nufi hanyar masar ba tare da tunanin komai ba,
Wata irin gumza nayi a lokacin da Dikko ya shigeni, jikina yana kyarma saboda azaba nasa hannu na mai lafiya na kware abinda ya rufemin baki, nace kaji tsoron Allah karka b'atamin rayuwa ka rufamin asiri dan girman Allah, ko saurare na baiyi ba, da hannu na mai lafiya dashi na fara yagushin Dikko tare da cizo, nayi kuka na bashi hak'uri amma kamar an watsa ruwa a k'asa, dan gaba d'aya tunanin Dikko ya b'ace saboda duk abinda nake masa bayaji, cizo da yagin ma kamar ina yagin karfe kwata kwata bayaji.
Tun ina iya Allah ya isa, cizo yagi har k'arfina ya k'are na gaji na daina bai barni ba, wata irin azabtuwa nake sha wadda tunda nake a duniya ban tab'a jin irinta ba, haka kuma bazan iya musulta girman azabar ba, wai yau nice akayi ma fyad'e, wannan bala'in ne Zainab ke zuwa ai mata a bata kud'i ?.......
Wurin kamar kimanin 12:45pm dukan k'ofar d'akin Dikko akeyi babu sauk'i, kuma har zuwa wannan lokacin Dikko bai kyaleni ba, na suma na dawo bansan adadi ba, baida niyar bud'e k'ofar kwata kwata, magana mai dukan k'ofar ya farayi cewa wai har me kakeyi ne baza ka bud'e k'ofar ba.
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, yai ta maimaitawa, tare da sauka daga saman gadon, ta jikin tagar d'akinshi ya lek'a a bayyane yace Dady......
Gajeran wando ya saka sannan ya kunna fitila, jawoni yayi daga saman gadon ya sauko ni k'asa sannan ya bud'e loka na bedsite ya d'auko gishiri, saida ya cikamin bakina da gishiri sannan ya zubamin ruwa a baki na hakan ya bawa gishirin damar narkewa yaci gaba da gangarawa cikin mak'oshina.
Dakel na bud'a idona na kalli Dikko, tsoki yayi tare da cewa munafikar Allah bari kallona dan uwarki..... A hankali na maida idona na rufe, k'asa yajani har muka fito daga d'akin kuma har yanzu ba'a daina dukan k'ofar d'akin ba,
Wani d'aki daban ya kaini ya ajiyeni, sannan ya kulle da makulli, saida ya goge inda jini ya b'ata daya jawoni sannan ya koma d'akin daya b'atamin rayuwa, zanin gadon ya cire ya tafi toilet dashi,
Bai wani dad'e ba yayo wanka ya fito, saka kayanshi sannan ya bud'e k'ofar, hannu Dady ya mik'a wa Dikko suka gaisa yace masa Babana baka tashi ba ? Na tashi..., tou lafiya baka shigo ciki ba ? Me yake damunka ne ? Ba komai Dady, sosai Dady ya sake kallon Dikko sannan yace mu shiga ciki,
Duk yanayin fuskar Dady ya canja zuwa na damuwa, jan Dikko yayi suka zauna har yanzu yana rik'e dashi a jikinshi yace Babana fad'amin abinda yake damunka, Dady nace babu, to miya hanaka shiga ka gaisheni, ba komai, tab'a jikin Dikko yayi cikin damuwa yace tou mi yake maka ciwo ? Kanka ne ? Ko bacci kake ji ?
Shiru Dikko yayi duk abun duniya ya dameshi, Dady kad'ai yaketa ma Dikko sannu, yana san Dikko fiye da yanda kowa yake san d'anshi, yana tattalin Dikko ko ina Dady baya san Dikko yana zuwa dan duk fitar da Dikko keyi Dady baisan yana fita waje ba, yana lallab'a Dikko sosai gani yakeyi kamar Dikko zai mutu ya barshi, kullum addu'ar shi Allah ya k'ara kare mishi Dikko ya shirya shi ya albarkaci rayuwarshi, saboda d'a d'aya tsotsai gareshi. Yana da "ya "ya sunkai sha biyar amma duk mata ne Dikko ne kadai na namiji a gidanshi.
Taso muje, Dady ya fad'a tare da dafa kafad'ar Dikko suka fita, cikin gida suka shiga, tunda suka shiga k'annen shi suka fara cewa Yaya munce ma Dady lafiyar ka qalau yace saiya ganka zai fita, kallonsu kawai yayi amma baima kowa magana ba, suma basu damu ba tunda halinsa ne shariya, sai kayi ta mishi magana ya kyaleka kamar bayajin ka.
Gishirin da Dikko ya zubamin a baki nake ta tofarwa amma rabi ya riga ya gama shigewa cikin cikina, kuka nakeyi mara sauti, duk ilahirin jikina ciwo yakemin, ga kaina kamar zai fashe saboda rashin bacci da kukan da nayi.
Haka na yini zubur babu Dikko ba labarinshi, ga ciwo da nakeji a k'asana kamar zai fita saboda azaba, kuma d'akin da nake babu toilet a ciki duk sallolin da akayi na yinin ranar nan inajinsu amma tun sallah asuba ban k'ara wata sallah ba.
Sai dare sosai Dikko ya bud'eni, shigowa yayi yana waya, wallahi dawowa ta kenan naje Abuja kwata kwata na manta da yarinyar nan saida nayi alwalla zanyi sallah magrib ta fad'omin a rai, ko Dady basai na dawo ba kuma ina ajiyeta zan koma , ....... A , a, 06:30am ne, ai bana so Dady yaji ban tafi ba kasan yanzu sai ya shiga damuwa, bada driver nake ba, tou kudai ku sakani addu'a , yana gama wayar yace ke da Allah tashi muje, munafika kinja min tafiyar dare, daka min tsawa yayi tare da cewa ki wuce mu tafi kina b'atamin lokaci dare yana karuwa,
K'iri k'iri na kasa tashi, kaina sai juyawa yake ga wani irin amai dake kai kawo tsakanin zuciyata da cikin cikina, jiki na yana kyarma nace masa bana iya tashi..... Na k'arasa maganar hawaye na zubomin daga cikin ido na,
Zan tafi idan kin tashi kin basu labarin abinda ya kawo gidan nan ni kinga tafiyata, ya juya zai tafi nace dan Allah zan tashi, juyowa yayi ya kalleni sannan yace tou taso ya fad'a cikin sigar lallashi,
Dakel na iya tashi amma a duk'e nake na kasa mik'ewa tsaye, yanayin fuskar shi ya nuna tausayi, akwai zafi ? Ya tambayeni, banza nayi dashi bance masa komai ba, murmushi yayi tare da cewa ki sameni ta baya, kuma kiyi hankali karda a ganki,
Dakel nake tafiya har nafito, a lokacin harya d'auko motar daga inda ya ajiyeta, ina k'ok'arin shiga yace in tsaya kar in b'ata motar, ciki ya koma ya sake gyaggyara inda na b'ata sannan ya d'auko wani k'aton zani ya taho dashi, inda zan zauna ya shimfid'a sannan yace shiga,
Shiga nayi na zauna ya rufe k'ofar tare da zagayawa shima ya shiga, waya ya kira yace gani nan zan fito bud'e min get in, yana fad'a ya ajiye wayar ba tare daya kashe ba,
Da gudu yaja motar kamar zamu tashi sama muka tun kari hanyar fita, a daidai get ya tsaya sukayi ta masa addu'a da fatan alkairi ya amsa da amin sannan muka fice, hanyar filin gidanmu ya nufa, babu mota ko d'aya a hanya bare machine haka ya tabbatar min da dare yayi sosai,
Lokaci lokaci nakan goge hawaye, tare da Allah ya isa zuciyata, saida ya kusa zuwa gidanmu ya tsaya yace ke sauka haka nan, kama murfin motar nayi sannan na kalli Dikko nace Allah ya isa ban yafe maka ba mugu azzalimi d'an isa mai bakin mata, murmushi Dikko yayi sannan yace ngode,
Kuma ko zaka mutu bazan tab'a yafe maka ba, Dikko yace tou, in Allah ya yadda saika had'u da tashin hankali a hanya, bazan had'u dashi ba in Allah ya yadda, tsoki nayi tare da bud'e motar na fita, tillomin zanin dana zauna akai yayi a daidai lokacin da nace kuma wallahi sainayi k'arar ka, babu damuwa ina jiranki, azzalimi , murmushi yayi tare da cewa naji ba komai duk abinda zaki ce ki fad'a nidai nasan na more miki har abadan duniya, gwallo yayi min tare da jan motarshi ya barbad'eni da k'ura.....
Wani irin bak'in ciki ya kamani nayi wani irin ihu daga nan ban sake sanin inda kaina yake ba saidai na farka na ganni kwance a gadon asibiti, an d'aure hannuna wanda yaji min ciwo, anmin dinkuna a k'ark'ashi na,
Zainab itace ta zauna tare dani a asibiti dan Inna tunda taji abinda ya faru tayi tafiyarta tace ta gama auren Baba har abadan duniya,
Sati na d'aya a asibiti aka sallame mu muka dawo gida, Babana kuma kunya tace ta koreshi babu wanda yasan inda ya tafi, tunda na dawo na samu labarin Inna ta tafi ban wani ji sha'awar binta ba, na hak'ura na zauna cikin "yan uwana.
Naje nayi k'arar Dikko wurin "yan sanda abinda ma na fahimta sumo so suke suyi irin abinda Dikko yayi dani, dan haka na hak'ura na dawo gida.
Babu ranar da zata zo ta koma ga Allah ban fad'owa Dikko a rai ba, ya shiga damuwa da tashin hankalin abinda yayi min, yaji bak'in ciki tare da tambayar kansa mi yasa yayi zina ? Mi yasa nayi ? Mi yasa,.....????
Wani lokaci haka zai zauna yayi ta kuka yana mai jin bak'in ciki da nadamar aikata abunda yayi, ya tambayi kanshi so babu adadi wai miye amfanin abinda yayi ? Yin hakan meya haifar ? Dadin me yaji ? Wane rayuwa yarinyar mutane zata shiga? Mi yasa saishi ne Bello ya zab'a ya farkewa Sultana mutunci ? Tabbas ya yadda ya zama babban mahauci iliminshi baida wani amfani baida banbanci da jahili,
Kullum addu'a Dikko yakeyi Allah ya yafe mishi akan abinda yayi min,zuwa wannan lokaci ya fara tunanin ko ya sanar da Dady abinda ya faru kila zai bashi shawara tunda babu abinda suke b'oyewa juna,
Ko isashshen bacci Dikko baya samu, daya kwanta shashkar kukana yake tashin shi daga bacci, a fili yayi magana cewa baiwar Allah kiyi hak'uri ni wannan na d'auke shi matsayin k'addara tunda nake a rayuwata Allah ma ya kulle min idona da zuciyata akan mata,
Wallahi ko labarin mata bana so anayi a gabana, ban tab'a zina ba kuma wallahi ban tab'a jin sha'awarta a zuciyata ba, Allah yayi min kyankyami da tsoron sab'a masa , amma ya akayi banji kyamar yarinyar nan ba, na sab'awa Allah mi yasa na kasa control in zuciyata mi yasa wai..........? Dan Allah ki fita daga rayuwata ki barni, kiyi rayuwarki inyi tawa, hawaye ne suka sake tsirarowa daga cikon idonshi, cikin kuka yace ya Allah na rok'eka dan arzik'in annabi Muhammad S. A. W ka mantar min da lamarin yarinyar nan daga zuciyata, ka hanata zuwa man cikin bacci ta daina min wobuwa idan ina cikin mutane wallahi ina iya haukacewa,
A b'angare na kuwa, zuwa yanzu na shafe babin Dikko a rayuwata, akwai wani d'an uwanmu da yake so na, kuma yayi alk'awarin aurena dama tunda ya fara zuwa Baba yace mishi ya bashi ni amma babu maganar zance kawai dai idan na isa aure zai aura mishi ni.
Shima yaji labarin abinda ya faru dani, kuma yazo wurina, ya tambaye ni da gaske ne ko wasa ? Da farko naso na b'oye masa, amma daga baya kawai na fad'a masa gaskiya, yacemin tou shi gaskiya bazai iya aurena ba inyi hak'uri, ban wani damu ba nace Allah yasa haka shi yafi min alkairi a rayuwata.
A hankali magana ta fara zaga gari, anyi min fyad'e kuma wanda yayi min fyad'e d'in ba'asan ko waye ba, amma asibiti sunce ina da cutar H I V, duk abinda na tab'a a gidanmu babu mai k'ara amfani dashi, duk wacce na zauna kusa dashi sai ya tashi, idan na fito mutane da sun ganni sai su dare....
Ko a familyn mu kowa baya shiga sabgata, kyara da tsana ake nunamin kamar mayya, ga mahaifiyata tayi tafiyarta garinsu, Baba bansan inda ya tafi ba, na rasa abinda yake min dad'i a duniya, banda mai bani abincin da zanci duk wanda naje wurinshi saiya koreni, azaba ta isheni na fara sana'a babu mai siye,
Koda naje na fad'awa Amisty abinda rayuwata take ciki da fyad'en da aka min amma ban fad'a mata Dikko bane ba, shawara d'aya ta bani, shawarar kuwa itace, sana'a d'aya zanyi inyi arzik'i ba H I V gareni ba ko kabari ce ni sai an shigeni,
Wace sana'ace ? Murmushi Amisty tayi tare da cewa zan kaiyi wurin uwar d'akina in yankar miki form zata baki lectures, lokaci guda zaki goge idonki ya bud'e zaki ga yanda maza zasu rik'a layi akanki,.....
Idan sunyi layin me zan basu ? Abinda kika bawa wanda yai miki fyad'e,...............
Taku a kullum.
*JAMILA MUSA*
03/08/2019
Ku kulle marecen ku da wannan..........
Ku biyoni sannu a hankali danji dalilin da yasa na kira wannan labari da *KWARATA* nazo kuma nayi masa in kiya da *KALU BALE GARE KU MATAN AURE.............*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
*_Ina miki sannu da gajiya fatan kin koma gida lafiya ? Ngode sosai Allah ya bada ladar zuminci ya kuma hutar da gajiya RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE_*
🅿 ------ 7
Haba Amisty wannan ai ba mafita bace, Sultana kenan wannan kuwa itace babar mafita, domin mazan yanzu yawancin su yanda kika san kura da nama haka suke akan mata, d'aid'aikun su ne Allah yatsare su, sai kuma wanda suka had'u da jajirtaccin mataye.
Ni nan da kika ganni Sultana nasan abinda nakeyi kuma haka nasan irin mazan da nake tarayya dasu, banajin kunya asan ni "yar iska ce haka kuma bana b'oyon iskancina dan ta haka ne kad'ai za'a san ni karuwar gidan ce har na samu costomers.
Na samu dubban kud'ad'e ta hanyar karuwanci ban san adadi ba, dubu goma dubu ishirin ga kud'ina kuma inji dad'i abu na babu wanda yaji ba wanda ya gani, in rik'e babbar waya irin wacce nake so haka kuma in d'inka sutura da talakalmi da jaka, abu d'aya yasa ban sayi motar hawa ba saboda bana so Baba ya harbo jirgina da wuri amma badan babu ba,
Gyara zama nayi tare da tattara hankali na wurin Amisty, nace to ke mi yasa kike sha'awar karuwanci ne ? Murmushi tayi sannan tace gaskiya daga kalle kallen B F tun inajin tsoron abun har ya fara bani sha'awa,
Tsare ta nayi da ido sannan na tambayeta a ina take samu ? Tsoki tayi tare da cewa tambaya kamar "yar jarida, idan zakiyi na had'aki da wani mak'ocinmu sakaran banza baisan darajar kud'i ba, kije yai miki yaimin muci gaba da k'wak'wale banza tunda matar tasa sakaryar banza ce, kud'i gareshi na tashin hankali amma matar bata wani iya sauk'e hak'k'insa kinji yanda yake tona mata asiri ? Gata da kyau kamar ita tai kanta amma kyan ya zama hoto tunda mijinta ke neman mata.
Tou ke Amisty ya akayi kuka had'u kuma ya akayi yasan kina neman maza ? Hmm yarinya kenan ! Amisty tace min sannan taci gaba da cewa....... Gidan nake zuwa ita kuma bata da wani sirri bud'e take shegen surutu kamar an sakawa radio sabon battery,
Kullum naje sai ta bani labarin mijinta d'an jaraba ne, da a tunani na mafad'aci ne, sai nace mata niko sai naga yana da kirki sosai bashi da wata damuwa, sai tacemin ba fad'a na baki ba jaraba kullum zai nemeni daga dare zuwa asuba yakai sau biyar.
Cikin rashin fahimta na tambayeta, ban gane ba..... Tamin bayani na gagara fahimta shine ta fahimtar dani ta hanyar nunamin vidio a wayarta,
Tana kunna min ta tashi dan zuwa duba girki, ni kuma tuni dama na fara iskanci na amma a lokacin ban dad'e da farawa ba, dan haka tana tashi na sace number mijin a wayarta, tunda iskancin kawai nakeyi a lokacin amma bansan fa'idar abun ba......
Tana madafar abinci naje na bata wayarta nayi mata sai anjima, ina fita ba gida na tafi ba kawai na sharce wurin uwar d'akina, wadda nace miki zan had'aki da ita kema ta mayar dake gahurtacciya kuma abun kwatacce a harkar barikanci. To ita naje ta sake bani haske a harkar, dan haka ina dawowa gida na fara tura masa sak'on gaisuwa ta whatsApp.
Shareni yayi bayan yaga sak'on baiyi reply ba, ni kuma na nace na kwakwafe banyi zuciya ba naci gaba da aika sak'on, kusan sati biyu babu wani bayani, dan haka na fara tura mishi da irin vidios in B F da nake kallo na tura mishi masu zafi da yamutsa tunani dan wani lokaci sai yakai 1:30am yana online.
Wai wace ce ? Ya tambayeni bayan yaga vidio inyi, nima basar wa nayi ban bashi amsa ba na sauka online, ina sauka yana kirana a waya..... Murmushi nayi a bayyane nace ashe kuwa mayen ne ? Mu zuba dani dakai..... Kuma ban d'auki wayar ba,
Text ya turomin ta inbox, kamar haka....
_Wai wace ce ke ? Ki hau Online muyi magana don Allah !_
_Ai nayi fushi nima....._
Shine amsar dana bashi,
_Kiyi hakuri don Allah ki hau online muyi magana_
Shareshi nayi na kashe wata duka nayi kwanciyata...... Saida na kwana biyu wayata na kashe, ranar dana bud'e wayar kuwa sak'onsa ne yai ta shigo babu iyaka, wasu na duba wasu kuma na share.
Ko online dana hau sak'unan sa birjik, dan haka naci gaba da tura vidion iskanci, kuma idan natashi sai tsakar dare nake turawa, jakar tana can tana bacci,
A hankali ya saba dani, amma ban fad'a mishi kaina ba, yau da gobe bata bar komai ba, har na tambayeshi dalilin da yake kai tsakar dare yana chat, kawai cewa yayi yana da damuwa da iyalinshi, bata bashi hak'k'inshi wai tace yawan sex da mace yana sa tayi saurin tsufa....
Amsar dana bashi itace, ya barta can ta k'unshe abunta har yayi wari, indai yana da buk'ata tou ni zan rik'a bashi nawa duk lokacin daya buk'ata, kinji shine fa idan bata nan nake zuwa gidan muyi komai namu cikin sirri.
'Dan gajeren murmushi nayi sannan nace Amisty kenan...... Idan dai har bin maza zanyi tou pha tabbas babu macen data bini ilimin iskanci, kinji hausa suna cewa d'an gado saiya zarta, nawa ba kalar naku bane, saboda naku iskanci mai arha kukeyi, tunda har banji kunyar mahalicci ba na tsab'a masa babu abinda zaisa naji kunyar wani banza,
Hannu na nakai saitin prvt prt ina sannan nace idan dai wannan ne abinda maza suke buk'ata ni kuma duk saina halaka da yawansu dashi, kallon Amisty nayi sannan nace, babu wanda ya koya min saishi d'aya, ban fara ba shine ya fara, ban iya ba yayi da k'arfin bala'e, ba'ayi da zafi yayi min saboda k'eta, ke Amisty karki manta a caca aka sakani duk saboda talauci idan har ban tara kud'i ba ta sanadiyar karuwanci nayi suna a duniya lallai ni ba d'iyar Aliyu Binnaa bace,
Tunda har ya bada budurci na saboda san duniya ni kuma zanci gaba da basu su bani dan na tara mishi abunda ya buk'ata,
Amfanin zunubi roma Amisty, tunda zanyi kawai zanyi amma babu fashi, saidai ki sani akan sab'awa Allah babu namijin daya isa yaga ko pant ina da naira dubu goma ko ishirin, kud'in shigar ciniki naira dubu d'ari ne shine harajin da na yankawa duk mai sha'awar yin iskanci dani, idan kuma zaka shiga gidan dubu d'ari biyar, idan har haka yayi tou na siyar idan haka baima mutum ba tou ya tattara buk'atarshi ya koma,
Amma tabbas duk namijin da yace zaiyi, saiya bada dubu d'ari, idan na yadda yayi idan kuma ban amince da dashi ba zai koma, amma dubu d'arinshi tazo kenan kamar gawa tazo lahira.
Ki sani bana iskancin wahala, kuma bana iskancin cini incin tuwo, zan zauna gida bazan bar k'asata ba amma zan zama tarihi a duniyar nan, ki fad'awa uwar d'akin taki cewa ina gayyatar ta shigowa k'ungiyata da nake fatan kafuwarta daga yanzu zuwa ranar da numfashina zai k'are, ki sanar da ita cewa ni banda ilimin boko amma akwai na tsoron Allah kuma sanin ilimin bazai hanani bujire masa ba, nasan hukuncin mazina daga wacce tayi aure har wacce bata tab'a ba, hukunci kisa ga masu aure, bulala ce ga irinmu "yan mata, to anan duniya zan sameta ko sai naje can ? Duk na sani, kuma nasan a ina ake amso su, mik'ewa tsaye nayi tare da dafa wa Amisty kafad'a sannan nace bana buk'atar shiriya, kuma bana so a tausaya min, daga yanzu zuwa lokacin da zan gama kammalawa........, *BARIKI ASSALAMU ALAIKUM*
Murmushi nayi sannan nace wa Amisty suna na , MARYAM ALIYU BINNA, na bud'e k'ungiyata daga yanzu, idan kina sha'awar shiga bisimillah, na barki lafiya......... Ina fad'in haka ban sake magana ba na juya na fita daga gidansu......
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, shine abunda Dikko ya fad'a adaidai wannan lokacin, tare da cewa Allah na tuba.......... ðŸ™ðŸ»
Ina fita na tare napep nace malam ka kaini kambarawa, can ne anguwar da muke zama. Abinda zan bashi ya fad'amin bayan ni ban tambayeshi ba,
Shiga nayi yaja muka tafi, duk inda yaga fasinja ya tsaya zai d'auka cewa nakeyi muje bana so ka d'auki kowa, har muka iso filin gidanmu da yasha ado da darnin kara......
Ina fita na wuce abuna, malama kud'in fa ? Juyowa nayi tare da ce masa nawa ne ma ? 250, murmushi nayi tare da kallonsa k'asa da sama sannan nace naci na Allah bud'a, da kuma tsarinka yamin dana baka wani abu ka kalla sai kayomin ciko,
Fitowa yayi daga cikin napep d'in yana fad'in ke zanci uwarki ko ki bani kud'ina, murmushi nayi tare da cewa tayi maka tsufa...... Ina fad'in haka nayi gaba abuna, haya haya ya fara hayani tare da ci gaba da d'uramin zagi irin na "yan tasha. Ja nayi na tsaya ba tare dana juyo ba.
Saida ya gama zage zagensa sannan naci tou ka zagi kud'inka, kuma naci na cinyesu duk garin nan inga mai amsar su wurina, kaina yayo da zumar kaimin duka, nace ka dakeni ka dako ma kanka bala'e da kabi ta hankali daka tsira amma tunda iskanci ne abun dani dakai dan iska ka fasa,...
Wani mak'ocinmu ne yazo wucewa, na fashe da kuka tare da cewa malam lawal kaga wannan shine yayi min fyad'e, dama nace muku ina ganeshi, yana jin zance fyad'e ya ruga zai nufi napep malam lawal ya fara a kawo d'auki, a tak'aice dai kafin ya bar anguwar bayan yaci shegen duka saida aka fasa mishi gilashin mota na gaba sannan suka k'wak'ule masa cini kin da yayi yabar anguwar a wahalce......
Yana tafiya na shiga gidanmu natashi masifa cewa sai an siyar da filin nan an bani hak'k'ina, yanda na birkice lokaci guda ya bawa al'ummar anguwarmu mamaki, an nuna min cewa ayi kud'i wa filin sai a fitar min da kud'ina su kuma su zauni fili, nace bansan wannan zance ba duka nake so a siyar uban kowa ya kama gabanshi,
Tambayata akayi me zanyi da kud'in ?Babu kunya bare shakku nace, karuwanci zan fara shi yasa nake so a siyar a bani kud'i na naje na siyo kayan da zan zama karuwar......
Gaba d'aya wurin salati aka d'auka ! Yayin da wasu dattawa suka fara sulalewa suna barin wurin, ni kuma na shiga cikin gidan naci gaba da yanyara ruwan iskanci na san raina,
Bayan kwana biyu mak'ocinmu ya kawo kud'in filin gidanmu domin shine ya siya, aka raba aka bani nawa, sallama nayi musu tare da cewa kuyi k'ok'ori kuna ziyarta na domin inaji a jikina nan da kwanaki kad'an zanyi muku wahalar gani.......
Babu wanda ya bani amsa, murmushi nayi tare da tafiyata dan dai nasan nasha dasu.... Nima bak'in ciki yasa nace duka filin za'a siyar dan kar na shiga gararin rayuwa ni d'aya kowa ya lalace dan zuwa yanzu gaba d'aya na koma kamar wata kafira dan babu sauran tausayi a zuciyata......
Bakin titi na fito na samu mai abin hawa, inda zanje ya tambayeni........... Shiru nayi na wani lokaci sannan nace masa gidan karuwai zaka kaini,
Kallona yayi sosai sannan yace ina ? Nasan yaji sarai iskanci ne yasa ya sake tambayata, dan haka nace gidan da "yan iska ke zama wanda suka gagari iyayensu,
Jinjina kai yayi amma baiyi magana ba, ko har yanzu baka gane ba ? Na tambaye shi ? Shiru yayi baicemin komai ba, ni kuma nace tou ina nufin inda maza da mata ake had'uwa ayi bad'ala, kallona yayi cikin yanayin tausayi sannan yace ke yarinya ki rufawa kanki asiri rayuwar bariki tafi k'arfin ki, aure shine yafi dacewa da rayuwarki,
Kai malam zaka kaini ko kuwa dai ? Tashin napep inshi yayi tare da cewa Allah ya shiryaki, amma nikam bana kaiki gidan karuwai, tsoki nayi tare da cewa jeka d'an munafika shege marar rabo... Gaki nan katuwar marar rabo duniya da lahira, indai mazan bariki ne sai sun kasheki murus kin kasa morawa rayuwarki, dan mace bata kashe namiji saidai ya kashe ta, baki san dafin namiji ba da baki hayewa mazan zamani ba kin koma gida, basu da imani haka kuma basa tausayi tunda sun san kud'insu suka biya, tou fa basa sassafta wa kamar mai gidan haya ne da "yan haya, tunda sun san ke ba tasu bace hawa d'aya zuwa biyu zasu tashe ki aiki kina kallon maza suna kallonki amma dan uwarki bazasu ciwu gareki............ Yana kaiwa nan yaja napep inshi yayi gaba.
A bayyane nace komi zakace kaje kace saina zama cikakkiyar karuwa, kuma ni karuwanci nawa mai aji zanyi ba irin wanda kowa yake tunani ba.
Bai dad'e da tafiya ba na samu abin hawa, kuma na fad'a masa gidan karuwai zai kaini, yace min na ina gidan karuwai d'in ? Nace inda fek'ak'k'un suke can zaka kaini, shigo muje, shiga nayi yaja muka tafi.........
05/08/2019
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
*_Ku nemi naku fitowa ta farko daga shahararriyar kungiya mai san farin cikin makaranta wato BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION, sabon salo ne daga shahararrin marubuta biyu, MAI JIDDA daga alkalamin MARYAM MUHAMMAD HASSAN, MAFARKIN NANAH, sabon sauyi na SA'ADATU LAWAL maman ilu, kar ku sake ku bari a baku labari......_*
*_ZAINAB ATTAHIRU B ' K sakonki yazo gareni ngode sosai ina miki fatan alkairi, ki kasance cikin farin ciki da kwanciyar hankali har a busa kaho............_*
🅿 ------ 8
Tafiya mukeyi daga ni harshi babu wanda yayi ma wani magana, saini da a zuciyata nake ta addu'a, Allah na rok'eka ka bani farin jini ka zubamin kwar jini kasa na rik'a bud'ewa mutane ido duk wanda yayi ido dani, Allah kasa wannan kyawun nawa ya zamar min babban jari, kasa nayi suna sosai a harkar karuwanci.
Tafiya mai nisa mukayi har muka iso k'ofar gidan, sai yanzu yayi magana cewa ranki ya dad'e anzo, ba tare dana fito ba nace masa, malam ya sunan anguwar nan ne ...... ?
Sanin da nayi ma anguwar a da yanzu karuwai sun canja mata suna, gidan na sani ba sunan wurin ba, ki sauka ki bani kud'ina sauri nakeyi.
Ina k'ok'arin fitowa nace kasan kana sauri ka bari aka haife ka ? Ka iya tafiya domin dai ni d'abi'ata idan nahau abin hawa gaskiya bana iya biyan kud'i, amma Allah ya taimaka sauka lafiya !
Fitowa yayi daga cikin napep in ya fara ke bansan rashin kunya bani kud'i na ko in wulak'anta ki a wurin nan, d'an gajeran murmushi nayi tare da cewa banda haukar ka wanda ya fito bariki ai baya tsoron wulak'anta, ai ta wulakanta ta kare tunda har na fito daga gidanmu na taho yawon karuwanci........!
Shiru yayi ya rasa abin cewa, dan haka nace ko kana da sauran magana ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa jeki kya gani...... Dariya nayi sosai irin ta cikakkin "yan duniya na kashe dariyar da rangad'a gud'a, sannan nace shege kaji uwar bari ko ?
Tou babu uwar da zan gani dan duk wani gagararren d'an iska dake fad'in garin katsina nice uwarshi nice ubanshi, duk wani kangararren dan iska da "yar iska da iyayensu sukace jeku kun gani, to wallahi idan suka taho ni zasu gani.....
Sauk'i ya nemar min sannan ya koma cikin napep inshi, yana k'ok'arin tashin ta nace malam dakata, tsayawa yayi yana kallona, kana da waya ne ? Rik'e waya ai sai ke da kika fito neman haramun, to naji ba komai, kadai ganni sosai ko ? Kuma zaka iya ganeni gobe idan mun had'u, tsoki yayi sannan yace taya zan manta da fuskarki azzaluma kawai, yawwa ina so dama ka gane ni gobe idan ka ganni, ni suna na Sultana idan kayi gaba ka bada labarina dan ina san cikin d'an k'ank'anin lokaci suna na ya zagaya kaf fad'in garinnan, sauka lafiya.......... ! Ina fad'in haka na shige gidan karuwai,
Tun a zauren gidan na farajin kuruwar wata karuwa, karuwinta ne yake dukanta da belt kamar uba yana hukunta d'iyar sa, babu ji babu gani yana dukanta yana cewa dan ubanki sai kin bar gidan nan, wallahi na gama zama dake, d'an murmushi nayi a bayyane nace Allah sarki duniya yayin da wasu ke shigowa yayin wasu ke fita,
A hankali nabi gidan da kallo ga mutane nan iri iri, yayin da wasu ke caca, wasu na lido, wasu na shan sigari yayin da wasu ke kwance saman jikin maza babu kunyar Allah bare tsoranshi, wato abinda dai na lura duk abinda kake so shi kakeyi babu mai ce maka dan mine ne ......?
K'arewa gidan kallo nayi sosai, d'akuna ne k'asa da sama, bene ya zageye k'asan gidan yayi masa rumfa sai yanayin gidan ya tabbata kamar irin hadari ya taso. Wani irin ihu na zabgaga tare da kashe ihun da gud'a, wanda haka yayi sanadiyyar jawo hankalin duk wanda ke cikin gidan na waje da wanda ke d'aki babu wanda aka bari kowa saida ya fito....... Kirari na fara kwararwa bari ba tare dana kalli dandazon mutanen dake kallona ba.
Bariki ba'ayi miki tilas babu wanda ya rako wani kowa da k'afarshi yazo kuma in yaji wuya shi zai koma, baki duba mai kyau ko mummuna, haka kuma babu ruwanki da maye ko mayya mai lafiya da mai cuta duk wanda yazo kina da masaukinshi, baki san inda kowa yake ba amma kowa yasan inda kike, gani nazo ki sakamin albarka, baki da tabbas bariki haka nima bani da tabbas, matsalar ubace ta kawoni amma ina tare da had'ari guda d'aya, bana san shiga sabgar kowa karki sake ki bari wani ya shigo rayuwata, ilimi nazo d'auka a cikinki amma ni nafiki rashin tabbas, ina da masaukin kowa amma banda na mata.....duk namijin da uwarshi ko ubanshi yace jeka ka gani tabbas idan yazo ina da masaukin shi nima,
Kija da'irarki ki bani tawa, bana shan sigari bana cin goro, abu d'aya ya kawoni shi zanyi na koma, bansan bincike haka kuma bana san bin kwakwaf, kar ku sake naji bakin wani nan, idan ba amsa zai bani ba, kuma magana d'aya nake so ta fito bakinku akwai ko babu, itace amsar da nake so a bani, tambayata itace kawai d'akin zama ko nayi gaba.........?
Wani daga can saman bene yace ke "yar cakulkula dake har kin san dad'in namiji ? 'Daga kaina nayi sama na kalleshi sannan nace daga ganinka gidan haya aka haife ka, kaine matsala da kanka bakaji abinda nace ba ? Akwai ko babu kawai nake so naji.
Daga bayana wani yace ki bashi amsar tambayar shi mana sai mubaki taki, murmushi nayi sannan na d'aga kaina sama na kalleshi tare da cewa, duk tayar abun hawa sunanta taya, amma kaga tayar daf tafi ta jirgi girma amma abinda jirgi zai d'auka daf bata iya d'auka, jirgi ya d'auke ka kuma ya d'au kayan ka, kamar dai kai kaga ga jibgegiyar mace a gefenka, amma a zahirance gwaram ce tunda har ka samu damar fitowa, saboda haka k'aranta ba matsala bace, abinda wata motar ta kasa sai kaga machine yayi.
Tabbas muna da masaukin ki, d'aki d'aya 5k ne a wata haka kowa yake biya sai kuma zaki bayar da kyautar dare d'aya ga mai gidan wannan shine tsarin wannan gida me kika ce ?
Wannan ba damuwa bace amma nima ina da nawa tsarin na basu amsa, muna saurarenki suka bani amsa, gyara tsayuwa nayi sannan naci gaba da cewa ina da ranakun aiki ina da na hutu, yau da gobe da jibi daga nan har zuwa k'arshen satin nan babu maganar kwanciya da ko wane na miji amma zai yadda daga nan zuwa sati na gaba.........? Nayi musu haka ne dan ni kwana ukku kad'ai zanyi na k'ara gaba abu d'aya zuwa biyu nazo koya kad'ai a gidan karuwai kuma a raina bazan biya kud'in hayar ba haka na yanke..
Na saman benan yace min mi yasa kike da wannan tsarin haka ne An mata.......? Wata irin fad'uwar gaba naji tare da kallonshi da sauri domin ya kirani da irin sunan da Dikko yake kirana dashi, janye zance Dikko nayi a raina sannan nace idan har ruwa ya kare a cikin tanki ko ka tara abun ibar ruwa baka samun komai haka nan zaka gaji da jira ka d'auke, amma idan aka bari ya taru kana tarawa zai cika ma duk abinda kake buk'ata, to nima haka take daga gareni karfina ya k'are dan na kwana ina aiki saboda haka a barni na huta na kwanakin dana iba,
Murmushi yayi tare da cewa gaskiya ku bata d'aki tabbas muna da masaukin ki a gidan nan, sakaran banza na fad'a a cikin raina nace otiho dakai baka tsan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, duk shelar da nayi na ce bariki tafini tabbas ka gagara ganewa da gaanin wannan sha ka tafi ne, fuska ta d'auke da mugunta nace mashi idan an bani d'akin kai ka biya kud'in sannan kuma ka bani rance dubu d'ari, tukuicin d'aki zaka kwana biyu kana morewa dani nima daga cikin irin baiwar da Allah ya bani, dubu d'arin ka kuma da kud'in d'aki duk zan baka su idan na fara kasuwa......
Ba damuwa a bata d'akin sama lamba 59 ya fad'a cikin zaguwa, ga *kwartuwar* shi gefe ya manta da labarinta, hawa sama nayi aka nunamin d'akin, makulli aka bani na bud'e na shiga ina shiga na kulle d'akin ta ciki.
Dudduba d'akin nayi bayan na shiga, falo ne sai d'akin bacci madafar abinci da bayi, d'akin bacci katifa ce irin ta "yan bodyn sch, falo tayils ne babu kujeru sai kafet, k'arewa d'akin kallo nayi sannan na koma jikin tagar d'akin na fara kallon yanda *karuwai* suke rayuwarsu.
Ina tsaye na fara tunanin fuskar da tacemin An mata, ina k'ok'arin tunoshi kwalwata ta fara jakkancin data saba, a bayyane nace ki saurara kar kimin haka don Allah rayuwa mai had'ari na kawo kaina ki tausamin ki sanar dani ko waye waccan, kwana biyu kad'ai zanyi nabar gidan nan amma ina so ki sanar dani ko waye shi d'in......
Bugawa zuciyata tayi tare da cewa abokin Dikko ne wallahi, shine ya raka abokin Babanki aka kaiki wurin Dikko....... Kamar kasuwa haka zuciyata da kwalwata suka fara gardama hayani ke tashi daga cikin kwalwata da zuciyata, yayin da kwalwata ke cewa bashi ne ba zuciyata tana cewa tabbas wallahi shine, kyarma jikina ya farayi gaba d'aya d'akin naji yana juyamin, kamar ana jijjiga ni naji anayi dan haka da sauri na dafa bango na zauna k'asa tare da fara karanto duk addu'ar data zo bakina......
Bayan na samu natsuwa ne, na dafa daidai saitin zuciyata da kwalwata sannan nace idan nayi muku wani laifi da Allah ku gafarceni amma ku daina dakushe wa ku barni nayi komai cikin hikima kamar yanda na tsara zanyi. Kuyi hakuri ku daure ku bani gudamwa.
Kwana na biyu a gidan karuwai ina koyon abinda yakaini, safe rana dare wannan d'an iskan yake kawomin abinci, a yanda nayi niya yaune zan tafi amma na fasa tafiya sai naga mai gidan bene....... Wato mai wannan gidan na karuwai.
Da daddare misalin 9:30pm na sauko k'asa na samu wuri daga gefe na zauna banma kowa magana ba haka kuma babu wanda na kalla amma hankalina gaba d'aya yana wurinsu,
Murmushi nayi a lokacin da naji wasu *kwarata* na ciniki, kallarni sama da k'asa kaga zubina ai kasan nafi k'arfin ka kwanta dani kace 1k zaka bani, yo wace kala gareki ni keda bakin masai baku da banbanci a wurina tunda kowa ma zuwa yakeyi ya hau ya kama gabanshi, ina ma laifina da zan baki 1k idan haka yayi miki in bayar idan baki yadda ba naje wurin Umma.
Mai makon naga taji haushi sai kawai tayi dariya tare da cewa shege kenan, to kawo dubu d'in, d'an sosa kansa yayi sannan yace kai nama manta dubun zan siya ma iyalina biredi wallahi kuma machine ina baida mai amma bari dai in bada dari biyar, batayi zuciya ba tace to kawo dari biyar in, bata yayi suka shiga cikin d'akin.....
Tsoki nayi tare da ganin wallan matan aure, kuna gida kwance mazajenku suna nan wurin sakarkarin matan da basu kaiku komai ba, kuna can kuna girman kai da kunyar banza da sakarci aje a yayo cuta a cusa muku babu gari babu dalili.
Me Allah ya rageku dashi ? Me karuwa take dashi wanda Allah bai baki ba ? Naki ma yafi nasu daraja tunda ke ta hanyar bautar Allah zaki mik'ashi kuma Allah ya baki lada, amma matar malam bahaushe tanajin kanta yai mata girma ji takeyi idan ta nunawa mijinta tana buk'atarshi kamar zai rainata, wata ma macen idan bashi ya nemeta ba saidai ayi ta zama a haka, to ya nemiki jiya shekaran jiya kullum har "yar basirar dake gareshi ta kare, ko kuma sai yazo kwanciya dake ki tashi hankalinshi ki tado fitar da kila anyi sati ko wata da yin abu saboda ke kawai za'a kwanta dake, kin b'ata mishi rai yaji gaba d'aya abun ya fita a kanshi ko kuma yayi shi ba cikin natsuwa ba, da kanki kike jefa kanki halakar da babu mai iya fitar dake sai Allah , daga haka sai shedan ya fara doka masa gangar sa ya barki yaje ya nemi na banza, dan babu zuciyat wanda shed'an baya wasa da ita.
Idan kika had'u da muguwar mace sai ta rabaki da mijin fafur ki kasa gane kanshi, daga nan sai ki fara tattara kaya ke a dole kinyi yaji. Idan an tambayeki abinda ya had'aku ki fara cewa baya dawowa gida da wuri, idan kin kawo abinci baya ci, idan kinyi kwalliya baya yabawa, bayan duk kece babban da kika jawo ma kanki wannan damuwar........... Mudai je zuwa zamu gano masu laifin tsakanin matan da mazan su waye masu matsala......
Ina zaune a wurin har 12:30am bai fito ba, tou me akeyi haka har yanzu wanda ba'a gama shi ba ? Duk gorin da yayi mata na had'a mata k'addarar ta da bakin masai batayi zuciya ba.
Lallai bariki bariki ce, mutanen cikinta suma sun barikantu kodai taji haushin abun bata wani nuna mishi damuwa ba, ina nan zaune a wurin har mutumin da nake tunanin mutumin da nake tunanin yana tare da Dikko ya shigo,
Da fito ya shigo babu sallama sai gyara wando yakeyi kamar wani sabon shigar *kwartanci* kallona yayi tare da cewa har yanzu baki bacci ba ? Nima irin yanda naga *karuwai* sunayi idan zasuyi magana nayi, d'an kashe idanuwa nayi cikin sigar bariki sannan nace banyi ba, to me kike jirane ? Kud'in da zaka bani ina so na shiga kasuwa gobe zanyo siyayya kasan jibi nake komawa bakin aiki na......
Murmushi yayi saboda yasan shine farkon layi idan na fara iskanci, kina da account ne ? Ya tambayeni ?Banda shi, to da safen zan baki idan naje wurin mai gida na, Allah ya kaimu nace tare da mik'ewa na fara tafiya cikin *kwartanci* sakaran banza ya bini da kallo, zakaci ubanka idan na gano ku, jibi kamar yanzu kana nan zakayi baccin bak'in ciki dan zan b'ace muku b'at kamar jirgi a cikin gizagizan sararin samani............
07/08/2019
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
*_Ku nemi naku fitowa ta farko daga shahararriyar kungiya mai san farin cikin makaranta wato BRILLIANT WRITERS ASSOCIATION, sabon salo ne daga shahararrin marubuta biyu, MAI JIDDA daga alkalamin MARYAM MUHAMMAD HASSAN, MAFARKIN NANAH, sabon sauyi na SA'ADATU LAWAL maman ilu, kar ku sake ku bari a baku labari......_*
*_ZAINAB ATTAHIRU B ' K sakonki yazo gareni ngode sosai ina miki fatan alkairi, ki kasance cikin farin ciki da kwanciyar hankali har a busa kaho............_*
🅿 ------ 8
Tafiya mukeyi daga ni harshi babu wanda yayi ma wani magana, saini da a zuciyata nake ta addu'a, Allah na rok'eka ka bani farin jini ka zubamin kwar jini kasa na rik'a bud'ewa mutane ido duk wanda yayi ido dani, Allah kasa wannan kyawun nawa ya zamar min babban jari, kasa nayi suna sosai a harkar karuwanci.
Tafiya mai nisa mukayi har muka iso k'ofar gidan, sai yanzu yayi magana cewa ranki ya dad'e anzo, ba tare dana fito ba nace masa, malam ya sunan anguwar nan ne ...... ?
Sanin da nayi ma anguwar a da yanzu karuwai sun canja mata suna, gidan na sani ba sunan wurin ba, ki sauka ki bani kud'ina sauri nakeyi.
Ina k'ok'arin fitowa nace kasan kana sauri ka bari aka haife ka ? Ka iya tafiya domin dai ni d'abi'ata idan nahau abin hawa gaskiya bana iya biyan kud'i, amma Allah ya taimaka sauka lafiya !
Fitowa yayi daga cikin napep in ya fara ke bansan rashin kunya bani kud'i na ko in wulak'anta ki a wurin nan, d'an gajeran murmushi nayi tare da cewa banda haukar ka wanda ya fito bariki ai baya tsoron wulak'anta, ai ta wulakanta ta kare tunda har na fito daga gidanmu na taho yawon karuwanci........!
Shiru yayi ya rasa abin cewa, dan haka nace ko kana da sauran magana ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa jeki kya gani...... Dariya nayi sosai irin ta cikakkin "yan duniya na kashe dariyar da rangad'a gud'a, sannan nace shege kaji uwar bari ko ?
Tou babu uwar da zan gani dan duk wani gagararren d'an iska dake fad'in garin katsina nice uwarshi nice ubanshi, duk wani kangararren dan iska da "yar iska da iyayensu sukace jeku kun gani, to wallahi idan suka taho ni zasu gani.....
Sauk'i ya nemar min sannan ya koma cikin napep inshi, yana k'ok'arin tashin ta nace malam dakata, tsayawa yayi yana kallona, kana da waya ne ? Rik'e waya ai sai ke da kika fito neman haramun, to naji ba komai, kadai ganni sosai ko ? Kuma zaka iya ganeni gobe idan mun had'u, tsoki yayi sannan yace taya zan manta da fuskarki azzaluma kawai, yawwa ina so dama ka gane ni gobe idan ka ganni, ni suna na Sultana idan kayi gaba ka bada labarina dan ina san cikin d'an k'ank'anin lokaci suna na ya zagaya kaf fad'in garinnan, sauka lafiya.......... ! Ina fad'in haka na shige gidan karuwai,
Tun a zauren gidan na farajin kuruwar wata karuwa, karuwinta ne yake dukanta da belt kamar uba yana hukunta d'iyar sa, babu ji babu gani yana dukanta yana cewa dan ubanki sai kin bar gidan nan, wallahi na gama zama dake, d'an murmushi nayi a bayyane nace Allah sarki duniya yayin da wasu ke shigowa yayin wasu ke fita,
A hankali nabi gidan da kallo ga mutane nan iri iri, yayin da wasu ke caca, wasu na lido, wasu na shan sigari yayin da wasu ke kwance saman jikin maza babu kunyar Allah bare tsoranshi, wato abinda dai na lura duk abinda kake so shi kakeyi babu mai ce maka dan mine ne ......?
K'arewa gidan kallo nayi sosai, d'akuna ne k'asa da sama, bene ya zageye k'asan gidan yayi masa rumfa sai yanayin gidan ya tabbata kamar irin hadari ya taso. Wani irin ihu na zabgaga tare da kashe ihun da gud'a, wanda haka yayi sanadiyyar jawo hankalin duk wanda ke cikin gidan na waje da wanda ke d'aki babu wanda aka bari kowa saida ya fito....... Kirari na fara kwararwa bari ba tare dana kalli dandazon mutanen dake kallona ba.
Bariki ba'ayi miki tilas babu wanda ya rako wani kowa da k'afarshi yazo kuma in yaji wuya shi zai koma, baki duba mai kyau ko mummuna, haka kuma babu ruwanki da maye ko mayya mai lafiya da mai cuta duk wanda yazo kina da masaukinshi, baki san inda kowa yake ba amma kowa yasan inda kike, gani nazo ki sakamin albarka, baki da tabbas bariki haka nima bani da tabbas, matsalar ubace ta kawoni amma ina tare da had'ari guda d'aya, bana san shiga sabgar kowa karki sake ki bari wani ya shigo rayuwata, ilimi nazo d'auka a cikinki amma ni nafiki rashin tabbas, ina da masaukin kowa amma banda na mata.....duk namijin da uwarshi ko ubanshi yace jeka ka gani tabbas idan yazo ina da masaukin shi nima,
Kija da'irarki ki bani tawa, bana shan sigari bana cin goro, abu d'aya ya kawoni shi zanyi na koma, bansan bincike haka kuma bana san bin kwakwaf, kar ku sake naji bakin wani nan, idan ba amsa zai bani ba, kuma magana d'aya nake so ta fito bakinku akwai ko babu, itace amsar da nake so a bani, tambayata itace kawai d'akin zama ko nayi gaba.........?
Wani daga can saman bene yace ke "yar cakulkula dake har kin san dad'in namiji ? 'Daga kaina nayi sama na kalleshi sannan nace daga ganinka gidan haya aka haife ka, kaine matsala da kanka bakaji abinda nace ba ? Akwai ko babu kawai nake so naji.
Daga bayana wani yace ki bashi amsar tambayar shi mana sai mubaki taki, murmushi nayi sannan na d'aga kaina sama na kalleshi tare da cewa, duk tayar abun hawa sunanta taya, amma kaga tayar daf tafi ta jirgi girma amma abinda jirgi zai d'auka daf bata iya d'auka, jirgi ya d'auke ka kuma ya d'au kayan ka, kamar dai kai kaga ga jibgegiyar mace a gefenka, amma a zahirance gwaram ce tunda har ka samu damar fitowa, saboda haka k'aranta ba matsala bace, abinda wata motar ta kasa sai kaga machine yayi.
Tabbas muna da masaukin ki, d'aki d'aya 5k ne a wata haka kowa yake biya sai kuma zaki bayar da kyautar dare d'aya ga mai gidan wannan shine tsarin wannan gida me kika ce ?
Wannan ba damuwa bace amma nima ina da nawa tsarin na basu amsa, muna saurarenki suka bani amsa, gyara tsayuwa nayi sannan naci gaba da cewa ina da ranakun aiki ina da na hutu, yau da gobe da jibi daga nan har zuwa k'arshen satin nan babu maganar kwanciya da ko wane na miji amma zai yadda daga nan zuwa sati na gaba.........? Nayi musu haka ne dan ni kwana ukku kad'ai zanyi na k'ara gaba abu d'aya zuwa biyu nazo koya kad'ai a gidan karuwai kuma a raina bazan biya kud'in hayar ba haka na yanke..
Na saman benan yace min mi yasa kike da wannan tsarin haka ne An mata.......? Wata irin fad'uwar gaba naji tare da kallonshi da sauri domin ya kirani da irin sunan da Dikko yake kirana dashi, janye zance Dikko nayi a raina sannan nace idan har ruwa ya kare a cikin tanki ko ka tara abun ibar ruwa baka samun komai haka nan zaka gaji da jira ka d'auke, amma idan aka bari ya taru kana tarawa zai cika ma duk abinda kake buk'ata, to nima haka take daga gareni karfina ya k'are dan na kwana ina aiki saboda haka a barni na huta na kwanakin dana iba,
Murmushi yayi tare da cewa gaskiya ku bata d'aki tabbas muna da masaukin ki a gidan nan, sakaran banza na fad'a a cikin raina nace otiho dakai baka tsan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, duk shelar da nayi na ce bariki tafini tabbas ka gagara ganewa da gaanin wannan sha ka tafi ne, fuska ta d'auke da mugunta nace mashi idan an bani d'akin kai ka biya kud'in sannan kuma ka bani rance dubu d'ari, tukuicin d'aki zaka kwana biyu kana morewa dani nima daga cikin irin baiwar da Allah ya bani, dubu d'arin ka kuma da kud'in d'aki duk zan baka su idan na fara kasuwa......
Ba damuwa a bata d'akin sama lamba 59 ya fad'a cikin zaguwa, ga *kwartuwar* shi gefe ya manta da labarinta, hawa sama nayi aka nunamin d'akin, makulli aka bani na bud'e na shiga ina shiga na kulle d'akin ta ciki.
Dudduba d'akin nayi bayan na shiga, falo ne sai d'akin bacci madafar abinci da bayi, d'akin bacci katifa ce irin ta "yan bodyn sch, falo tayils ne babu kujeru sai kafet, k'arewa d'akin kallo nayi sannan na koma jikin tagar d'akin na fara kallon yanda *karuwai* suke rayuwarsu.
Ina tsaye na fara tunanin fuskar da tacemin An mata, ina k'ok'arin tunoshi kwalwata ta fara jakkancin data saba, a bayyane nace ki saurara kar kimin haka don Allah rayuwa mai had'ari na kawo kaina ki tausamin ki sanar dani ko waye waccan, kwana biyu kad'ai zanyi nabar gidan nan amma ina so ki sanar dani ko waye shi d'in......
Bugawa zuciyata tayi tare da cewa abokin Dikko ne wallahi, shine ya raka abokin Babanki aka kaiki wurin Dikko....... Kamar kasuwa haka zuciyata da kwalwata suka fara gardama hayani ke tashi daga cikin kwalwata da zuciyata, yayin da kwalwata ke cewa bashi ne ba zuciyata tana cewa tabbas wallahi shine, kyarma jikina ya farayi gaba d'aya d'akin naji yana juyamin, kamar ana jijjiga ni naji anayi dan haka da sauri na dafa bango na zauna k'asa tare da fara karanto duk addu'ar data zo bakina......
Bayan na samu natsuwa ne, na dafa daidai saitin zuciyata da kwalwata sannan nace idan nayi muku wani laifi da Allah ku gafarceni amma ku daina dakushe wa ku barni nayi komai cikin hikima kamar yanda na tsara zanyi. Kuyi hakuri ku daure ku bani gudamwa.
Kwana na biyu a gidan karuwai ina koyon abinda yakaini, safe rana dare wannan d'an iskan yake kawomin abinci, a yanda nayi niya yaune zan tafi amma na fasa tafiya sai naga mai gidan bene....... Wato mai wannan gidan na karuwai.
Da daddare misalin 9:30pm na sauko k'asa na samu wuri daga gefe na zauna banma kowa magana ba haka kuma babu wanda na kalla amma hankalina gaba d'aya yana wurinsu,
Murmushi nayi a lokacin da naji wasu *kwarata* na ciniki, kallarni sama da k'asa kaga zubina ai kasan nafi k'arfin ka kwanta dani kace 1k zaka bani, yo wace kala gareki ni keda bakin masai baku da banbanci a wurina tunda kowa ma zuwa yakeyi ya hau ya kama gabanshi, ina ma laifina da zan baki 1k idan haka yayi miki in bayar idan baki yadda ba naje wurin Umma.
Mai makon naga taji haushi sai kawai tayi dariya tare da cewa shege kenan, to kawo dubu d'in, d'an sosa kansa yayi sannan yace kai nama manta dubun zan siya ma iyalina biredi wallahi kuma machine ina baida mai amma bari dai in bada dari biyar, batayi zuciya ba tace to kawo dari biyar in, bata yayi suka shiga cikin d'akin.....
Tsoki nayi tare da ganin wallan matan aure, kuna gida kwance mazajenku suna nan wurin sakarkarin matan da basu kaiku komai ba, kuna can kuna girman kai da kunyar banza da sakarci aje a yayo cuta a cusa muku babu gari babu dalili.
Me Allah ya rageku dashi ? Me karuwa take dashi wanda Allah bai baki ba ? Naki ma yafi nasu daraja tunda ke ta hanyar bautar Allah zaki mik'ashi kuma Allah ya baki lada, amma matar malam bahaushe tanajin kanta yai mata girma ji takeyi idan ta nunawa mijinta tana buk'atarshi kamar zai rainata, wata ma macen idan bashi ya nemeta ba saidai ayi ta zama a haka, to ya nemiki jiya shekaran jiya kullum har "yar basirar dake gareshi ta kare, ko kuma sai yazo kwanciya dake ki tashi hankalinshi ki tado fitar da kila anyi sati ko wata da yin abu saboda ke kawai za'a kwanta dake, kin b'ata mishi rai yaji gaba d'aya abun ya fita a kanshi ko kuma yayi shi ba cikin natsuwa ba, da kanki kike jefa kanki halakar da babu mai iya fitar dake sai Allah , daga haka sai shedan ya fara doka masa gangar sa ya barki yaje ya nemi na banza, dan babu zuciyat wanda shed'an baya wasa da ita.
Idan kika had'u da muguwar mace sai ta rabaki da mijin fafur ki kasa gane kanshi, daga nan sai ki fara tattara kaya ke a dole kinyi yaji. Idan an tambayeki abinda ya had'aku ki fara cewa baya dawowa gida da wuri, idan kin kawo abinci baya ci, idan kinyi kwalliya baya yabawa, bayan duk kece babban da kika jawo ma kanki wannan damuwar........... Mudai je zuwa zamu gano masu laifin tsakanin matan da mazan su waye masu matsala......
Ina zaune a wurin har 12:30am bai fito ba, tou me akeyi haka har yanzu wanda ba'a gama shi ba ? Duk gorin da yayi mata na had'a mata k'addarar ta da bakin masai batayi zuciya ba.
Lallai bariki bariki ce, mutanen cikinta suma sun barikantu kodai taji haushin abun bata wani nuna mishi damuwa ba, ina nan zaune a wurin har mutumin da nake tunanin mutumin da nake tunanin yana tare da Dikko ya shigo,
Da fito ya shigo babu sallama sai gyara wando yakeyi kamar wani sabon shigar *kwartanci* kallona yayi tare da cewa har yanzu baki bacci ba ? Nima irin yanda naga *karuwai* sunayi idan zasuyi magana nayi, d'an kashe idanuwa nayi cikin sigar bariki sannan nace banyi ba, to me kike jirane ? Kud'in da zaka bani ina so na shiga kasuwa gobe zanyo siyayya kasan jibi nake komawa bakin aiki na......
Murmushi yayi saboda yasan shine farkon layi idan na fara iskanci, kina da account ne ? Ya tambayeni ?Banda shi, to da safen zan baki idan naje wurin mai gida na, Allah ya kaimu nace tare da mik'ewa na fara tafiya cikin *kwartanci* sakaran banza ya bini da kallo, zakaci ubanka idan na gano ku, jibi kamar yanzu kana nan zakayi baccin bak'in ciki dan zan b'ace muku b'at kamar jirgi a cikin gizagizan sararin samani............
07/08/2019
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 9
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, itace kad'ai abinda Dikko yake ta maimaitawa a cikin wannan tsalelen dare,
Juyi yakeyi sosai a saman gado sai kace macen da ciwon ciki ya taso ta gaba, kifa kanshi yayi a saman lallausan bargon dake kusa da kanshi ya goge hawayen dake bi masa idanuwa.
Allah na tuba..., ya fad'a a bayyane tare da gyara kwanciyar shi, girgiza kanshi yayi , yayin da zuciyarshi da kwakwalwar shi suka hasko mishi abinda yayi ma Sultana, a hankali ya lumshe idanuwanshi na tsawon lokaci sannan ya fad'a a bayyane baiwar Allah baki dace mahaifi ba,
Sai kuma Allah ya jefoki a rayuwar Dikko yayin da nake nemanki, kika zo a daidai lokacin da na d'auki hud'ubar shaidan , Allah ya baki hak'uri kinji, ya k'arasa maganar tare da bud'e idanuwanshi duka da sukayi jajir saboda kuka........
Ko ina kike ? Me kike yi yanzu ? Wane irin bak'in ciki kikeji idan kika tuna dani ? Ki zama mai yafiya a rayuwarki, manta da Dikko ki fuskanci rayuwa, ina nan ke kuma ina ki ke .....?
Ina gidan karuwai,.... Ina shiga d'akina na mayar da k'ofa na rufe, ya zama lallai na gano waye mamallakin wannan gidan, sannan idan har na karb'i dubu d'ari a hannun wancan garan me ya kamata nayi da ita ne ? Ansar kud'in sune wahala Sultana anso su tuk'una idan suka zo hannu ba'a rasa abinda za'ayi ba, wannan shine shawarar da zuciyata ta fad'amin.
Ajiyar zuciya na sauke tare da hayewa saman "yar k'aramar katifata na kwanta bacci.
Da safe ina tashi sallah asuba nayi, na dad'e ina zaune a saman abin sallah ina addu'o'i na neman tsari d'aukaka farin jini da kuma k'war jini a harkar bariki.
Sai 7:00am na tashi daga saman abin sallah, toilet na shiga nayi wanka, ina fitowa na shirya a gaggauce domin akwai inda nake so naje.
Ina gama shirina na fito sanye cikin hijabina, sai nik'af dana dabkakawa fuskata, ina rufe d'akina mai kirana da irin sunan da Dikko yake kirana yazo.
A k'ofar d'aki muka gaisa daga gaisuwa ban sake masa magana ba naci gaba da rufe d'akina.
An mata ina zakije haka da safe ? Ban kalleshi ba nace zanje wurinka ne dama, murmushi yayi tare da cewa kuma gashi nima nazo wurinki yake nan .?
Babu wani damuwa zamu iya maganarmu anan, mudai shiga daga ciki zaifi ko ? Ya fad'a yana kallo na, gyara tsayuwata nayi tare da cewa kayi hak'uri gaskiya na fito bazan koma ba, yana k'ok'arin bud'e bakinshi yayi magana nace kayi hak'uri da Allah bana san magana tayi tsayo na wuce, ina k'ok'arin tafiya yace d'an tsaya kiji mana.
Tsayuwa nayi ba tare dana juyo ba, am dama cewa zanyi idan kina da hali anjima zamuje wurin Alhaji yace yana san ganin ki, ba tare dana juyo ba nace wane Alhaji ne ? Mai gidan nan, na bashi labarinki shi kuma ya matsa saiya ganki.
Saida nayi shiru na wani lokaci sannan nace wurin k'arfe nawa zamu je kenan ? Yanzu ma dan zaki fita da munje saboda ba'a gida ya kwana ba yana nan bayan gidan nan yana tare da bak'i da sukazo wurinshi manyan alhazawa ne masu kud'i da suka ansa sunansu a kud'i, d'an mugun murmushi nayi a cikin nik'af ina sannan nace tou kai ya maganar kud'in da zaka bani ne ? Suna cikon mota muje, murmushin zalinci nayi irin wanda naga mugu Dikko yanayi sannan nayi gaba abuna ya biyo bayana.
Cikin motarshi ya d'aukeni, muna shiga cikin motar na yaye nik'af ina tare da kallonshi sannan nace niko na tambaye ka mana ? Tambayarni mana ya fad'a a daidai lokacin daya fara tafiya da mota.
Shiru nayi ban sake magana ba, shine ya gaji da shirun yace kinyi shiru kuma ! Ey zan tambaye ka amma ba yanzu ba dan na d'auka ne baka san tambaya da surutu ne kamar yanda nima bana so, amma tunda ka bani izini zan rik'a tambayarka a duk lokacin da tambayar yazo min, amma dai ya sunan ka ...?
Murmushi yayi sannan yace suna na Umar, gyara zama na nayi tare da cewa me yasa Babanku yasa maka suna Umar ne ? Dariya yayi sosai tare da cewa sunan ubangidan shi ne,
Zaici gaba da rattafo min bayani na dakatar dashi ta hanyar cewa barmin bayanin haka nan zan tambayeka wani lokaci, babu gardama ya kame bakinshi ta hanyar yin shiru....
Har muka isa bakin get in gidan babu wanda ya sake magana daga ni harshi, horn yayi mai gadi ya bud'e mana muka shiga, gida ne had'ad'd'en gida na "yan gayu yasha ado da shuke shuke na filawowi, daga gefe kuma wasu irin lafiyayun dawakai ne tsabtatacci kuma k'osashshi aka d'aure sai tattabaru masu kyau wanda suke sauka k'asa lokaci lokaci su kuma tashi sama firrr lokaci lokaci....
Gaskiya dokunan sun burgeni sun kuma bani sha'awa, amma dana tuna da Dikko yana san doki yana k'aunar doki a rayuwarshi sai kawai naji dawakan nan sun fita a raina, saima zuciyata ta fara tunanin taya zanyi in kashe su, domin na tuna cewa Dikko ya fad'a cewa yana san doki ko ba nashi bane, lallai ni kuma na tsani dawakai.. Muje Umar ya fad'a da yaga banda alamar fita daga cikin motar.
Fitowa nayi tare da cewa Umar waye yake kiwon dokuna ? Wallahi na uban gidan Alhaji ne, ya bani amsa ne a lokacin da muka fara tafiya, tou shi Alhajin duk kud'inshi kenan yana da ubangida shima ? Na tambayi Umar, Umar yace Eh mana ai ubangidan nashi shine duk wata k'aryarshi, shine ya d'aure masa k'ugu shi ya tsaya masa saida ya tabbatar Alhaji ya zauna saman k'afafuwanshi , gaskiya mutumin kirki ne sosai, da yana harkar mata na tabbata idan na had'aki dashi yarinya kin warke, bake ba talauci, ke bake ba kaf zuri'arku da talauci ya k'are.
Maganar Umar ta k'are ne a daidai lokacin da muka shiga palon gidan, k'aton palo ne mai girman gaske, sai wata irin dakekiyar tv tunda nake a rayuwata ban tab'a ganin tv mai girmanta ba, ko da yake ma ina naje ina na sani a wannan lokaci ? Saifa gidansu Dikko shima naga tashi tv n babba ce amma banda natsuwar gane wacce tafi girma,
Bin palon nayi da kallo, d'an rumtse idona nayi na bud'e tare da k'ara d'ora idanuwana a saman hotunan dake palon, tabbas idan ban manta fuskar Dikko ba wannan shine Dikko, mutumin dana tsana nake san ganin bayanshi komin daren dad'ewa, dan ina sayen gida wa Babana Dikko shine mutum na farko da zan fara sabautawa rayuwa a duniya......
Muje suna ciki, Umar ya fad'a tare da katse mun tunani na, sauke nik'af ina nayi na rufe fuskata sannan nace mu koma gida, zai tambayeni dalili nace kawai mu koma zamuyi magana dakai daga baya. Haba Sultana har mun shigo wuri zaki ce mu koma.... Kallon Umar nayi sannan nace tunda nazo da kaina ai kasan zan sake dawowa ko ? Ina fad'in haka nayi gaba abuna......
Ina fitowa idanuwana suka cika da hawaye, tun ranar da Dikko ya ajiyeni a k'ofar gidanmu ban sake tunaninshi ba sai ranar da Umar ya kirani da An mata, ban sanka Dikko na tsani duk sunan daya fara daga kalmar D insha Allah ni zan zama ajalinka..... Kuma ta hanyar da kabi ka azabtar dani to nima ta hanyar zanbi in rama abinda kamin, yanda ka somar dani ni kuma saina kasheka.... Babana yaci darajar mahaifi na ne shi, zan tara masa dukiya ta hanyar karuwanci zaici yaci bulus amma wallahi kai Dikko bakaci banza ba.....
Fitowar Umar yasa na saita kaina, na bud'e mota na shiga domin ya bud'emin ita tun lokacin daya fito, zakuji dalilin da yasa na fasa shiga ciki, Umar kad'ai yasan fuskata kuma yau ya zamar min wajibi nabar gidan karuwai domin wannan kwanakin sune kwanakin dana iba zanyi a gidan karuwai, na ga abinda nake so na gani, naji na kuma gani nima zanyi gaba dan nima in dogara da kaina.
Muna fitowa yayi hanyar gida nace dakata ajiyeni nan, ina zakije ne ? Ya tambayeni , ban bashi amsar tambayarshi ba nace masa ga makullin d'akina kasa a gyara man, bani kud'in nan zanje in had'o makaman yak'i.....
Miye makaman yak'i kuma ? Ba tare dana kalleshi ba nace ai kasan ba'a shiga gida dole saida sallama, gida ba shara ai baya dad'in zama, na ciki bai san akwai na waje ba idan baya kwankwasa ba, to haka bazai yuwu ba wani yaci abinci yace kai yaci mawa, kaidai bani kud'i kaji idan na dawo zan baka bayani,
Kud'in ya d'auko ya bani, bayan na ansa nace samu wuri ka rubuta min number ka idan zan dawo zan kiraka kazo ka taho dani, yo ina wayarki ne ? Banda waya amma ka rubuta min zan samu aro na kiraka, rubuta min yayi a jikin takarda ya mik'omin, ansa nayi na fita daga motar tare da cewa sai munyi waya...
Saida na daina hango Umar sannan nima na ibi tawa hanyar na shiga duniya......,
Tafiya nayi mai tsayi ba tare da sanin inda zanje ba sannan na tsaya wani shago na samu aron waya, lambar Umar na basu nace da Allah su saka a waya su kirashi, ansa mai shagon yayi yasa lambar ya kira, babu wani b'ata lokaci aka sadani da Umar...
Sultana ce, na fad'a a lokacin da Umar yace hello, Oh kin gama ne ? Ya tambayeni, maimakon na bashi ansa saina kece da dariya kamar hauka sabon kamu..... Meya faru ne ? Inji Umar, saida na gaji da dariya dan kaina sannan nace darasi.
Yau na tabbatar ni bariki ta fini tabbas na tafi na barka, wannan makullin d'akin daka bani ne shine na dawo muku da kayanku, amma zan baka sak'o a wurin Dikko tunda kasanshi , ka fad'a mishi cewa Sultana tace zasu gauraya........ Ina fad'in haka na yanke wayar na mayar da ita ga mamallakinta nayi gaba abuna....
Wata irin zufa ta ketowa Umar mai makon salati sai ashariya, ya fara luk'ak'a zagi tare dayo waje da gudu, yana cewa amma lallai yarinyar nan ni zata danfara, wato wani bazaici abinci yace kai yaci ma ba, wato nine abinci itace bakin ni zakici ki gudu ? Kuma har kike wani cewa mai gida Dikko zaki gauraya dashi ? Kai wallahi idan na yadda shege ne ni, kuma yanzu zan kira Dikkon zaki ci kutumar ubanki, kici dubu d'ari zanci miliyan daga jikinki.
Jikinshi na kyarma ya fara kiran wayar Dikko har ta tsinke bai d'auka ba, k'ara kiranshi yayi bai d'auka ba, ci gaba yayi da kiran wayar babu k'ak'k'autawa, saida ya kira Dikko yakai sau goma sannan miskilin ya d'auka wayar.....
Ya akayi ne ? Shine tambayar da Dikko yayi ma Umar, cikin tausasa lafuzzan shi yace ranka ya dad'e kasan wata yarinya Sultana..... ? Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un Dikko ya fad'a a ranshi lokacin da aka ambaci sunan Sultana,
Me ya faru ne ? Dikko ya tambaya ? Umar yaci gaba da cewa ranka ya dad'e yarinyar nan "yar damfara ce, tazo nan gidan "yanci ne , gidan karuwai suke cewa gidan "yanci, dan idan aka kira karuwai d'in haka abun babu dad'in ji. Shi yasa su gogaggin "yan bariki suke kiran gidan da gidan "yanci.
Wata irin zufa ta tsatstsafowa Dikko amma yayi shiru yana sauraren Umar, ranka ya dad'e kwananta hud'u a gidan "yanci shine yau ashe ta shirya guduwa ta raina min hankali ta ansar min kud'i dubu d'ari akan zata bani tukuici, { zasuyi iskanci } shine ta gudu, wai kuma saboda ta d'aukeni sakarai wai tayomin waya in fad'a maka wai zata gauraya dakai.
Saida Dikko ya goge zufa sannan yace yanzu kayi hak'uri zan biyaka kud'inka, ai ranka ya dad'e ni ba kud'in bane yafi damuna mummunar maganar data fad'a a kanka ne, bayan zata gauraya dani tace maka wani abu ? A , a batace komai ba, amma ina ruwanta dakai ? Tana da dalilinta na fad'in zata gauraya dani, ka fita harkar yarinyar nan zan tura maka kud'inka karka ma sake kace zaka sake tashin wata magana kuma karka sake ka nemeta ,
Umar yace mai gida zafa ta gaura dakai ? Ka kuwa san abinda gauraya take nufi ? Dikko yace ta gaurayo dani d'in ina ruwanka ? Kaine tace zata gaura ko ni ? Shiru Umar yayi, tsoki Dikko yayi da niyar kashe waya, Umar yace ranka ya dad'e nidai idan kaine zaka biya kud'in nan na yafe maka su, Dikko yace ita zaka yafewa bani ba tunda ni banci maka ba, taci albarkacinka na yafe mata, na gode shine abinda Dikko ya fad'a tare da kashe wayarshi.
Miye tsakanin Dikko da Yarinyar nan ? Shine tambayar da Umar yakewa kanshi wanda ya rasa mai bashi amsar tambayar, tou yaushe mai gida ya fara harkar mata ne ? Dariya yayi tare da cewa shegiya duniya mata bala'e ne wato duk musulinci mutum da kawaicinshi babu uztaz babu mahaukaci kowa dai yasan darajar ku, ai dole nake yafe dubu d'ari nasan wasu miliyoyi ne zan ansa, inama zanga yarinyar nan da na tambayeta miye tsakaninta da Dikko.
Mi yasa zakiyi haka ? Me zaki tsinta a harkar karuwanci banda wahala ? Me kike so ne ? Me kika rasa ? Kud'i ba damuwa na bane da zan ganki da na wadaki da dukiya har sai kin rik'ajin kyankyan kud'i, k'amshisu ma idan kikaji saiya rik'a tayar miki da zuciya, ke kuma duniyar kike so ? Jinjina kanshi yayi tare da cewa Allah yasa miki natsuwa ki dawo daga rakiyar shaidan. Allah ya had'ani dake Sultana in baki hak'uri in kuma nemi yafiyarki,
Mutane sunamin bahaguwar fahimta, yanda kike kallona ba haka nake ba, kuna min wani tunani na daban bayan ba haka Dikko yake ba,
Duk abinda ya faru tsakani na dake wallahi ina ganinshi ne kamar wasa, banso haka ba, bansan ya akayi nima na koma kamar wani sakarai ba wallahi, Allah ya tsareki fad'awa halaka, idan har kika fad'a harkar karuwanci na cuci rayuwata da zuri'ata da banma fara tunanin auren ba.
Farin ciki kamar in tashi sama yau gani ga naira dubu d'ari, kud'i suna da dad'i gaskiya da farko dai saina ci kaza, sannan na gano wani abu d'aya da maza suke so a tattare da mata, suna san k'osashshiyar mace, suna san tsaftatacciyar mace, suna san mace mai aji suna san mace ma'abociya k'amshi macen data iya soyayya da tattali, ina zan nufa yanzu ? ..........
16/08/2019
Da Allah kuyi hakuri rasuwa akayi min ne kukaji shiru da dad'ewa haka,
Ina ma kowa barka da sallah, Allah ya maimaita mana yasa muna da rabon ganin na bad'in bad'ad'a, amin. Barka da sallah.
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 10
Lallai idan nayi shiru da maganar nan ban fad'awa mahaifin Dikko ba nan gaba ya gano wani abu lallai zan fuskanci baraza na dagani har mahaifina, kila ma ya kora mu, ya zama wajibi naje na fad'a masa halin da Dikko yake ciki, in yaso zaiyi bincike abinda ya had'ashi da ita yarinyar, Umar yake magana duk abin yazo ya dameshi yana mamakin abinda ya had'a Dikko da mace har take fad'ar zata gauraya dashi.....
Dikko mai zafi akan mata, ya akayi ya koma mai sanyi ? Wuta ne mai tsananin k'unar gaske ga duk macen data matse masa, babu abinda ya tsana duniya irin mata, amma wai shine yake godiya akan mace... Wace ce ita ? Miye tsakanin su ne.... ? Kayi shaye sheyenka ne Umar shi yasa ka manta wace ce Sultana.....
Tsohuwar anguwarmu ta farko na koma, inda Dikko yayi ta siye siyen gidanjen da muke kamawa haya, gida mai sauk'in kud'i na samu na kama d'aki d'aya, bayan na biya kud'in d'aki na tafi kasuwa dan siyo d'an abinda ba'a rasa ba na amfanin yau da kullum.
Na dad'e sosai a kasuwa, saboda duk abinda nasan zan nema saida na tabbatar na siya saboda ni rayuwata ta duniya babu abinda na tsana irin aro, bana san na takura shi yasa zanyi k'ok'ori na bada k'addarata dan na samu kud'i.......
Umar durk'ushe a gaban mahaifin Dikko, hada wani hawayen munafirci kanshi a k'asa kamar sabuwar amarya a daren farko, Dady kuwa gaba d'aya yanayin fuskashi ya sauya zuwa damuwa bayan ya gama jin duk maganar da Umar yazo da ita, shi baya hana Dikko yayi magana da mata bane ko wani abu a , a shi baya so dai ya shiga damuwa har wani abu yazo ya sameshi, kuma idan yayi ma Dikko maganar aure sai yace shi yaro ne a bari saiya k'ara girma, ga Umar kuma yazo ya fad'i k'arya da gaskiya dandai kawai a bashi wani abu, wannan fada ce ko kuwa maulace ? Kallon Umar Dady yayi sosai sannan yace kirawo min shi....
Umar ya kira Dikko yafi so a irga amma bai d'auki wayarshi ba, ganin haka yasa Dady ya fara kiran Dikkon da kanshi, shima bai d'auka ba, jinjina kai Dady yayi tare da turawa Dikko sak'o kamar haka....
_Babana idan ka gama abinda kakeyi ka kirani._
Umar kuwa yana tashi daga wurin Dady ciki ya wuce inda iyayenshi suke, a gidan su Dikko Umar da iyayenshi suke zama, suna a k'ark'arshin su Dikko ne, kuma Umar shine mutumin da yayowa Bello jagoranci aka kawoni wurin Dikko, ni da dare na ganshi amma Allah yasa na ganeshi duk da jakanci na, amma shi ya kasa ganeni kwata kwata....
Umar bai dad'e da tashi ba kiran Dikko ya shigo cikin wayar Dady..... Da farin ciki Dady ya d'auki wayar tare da cewa ina ka shige ne ? Ko kana tunanin surukata ne ? Ya fad'i maganar cikin sigar zaulaya, d'an gyaran murya Dikko yayi tare da cewa barka da yini, ya gaishe da Dady dan kauda waccan maganar.....
Ansawa Dady yayi suka gaisa cikin farin ciki da soyayya irin na d`a da mahaifi. Bayan gaisuwa Dady ya tambayi Dikko labarin yarinya da Umar yazo mishi da ita, miye tsakaninsu kuma miye gaskiya labarin ...? Dady ya k'ara da cewa banso soyayya tayi min wasa da rayuwata, domin duk abinda ya tab'a hanci ido ruwa yake, tou duk abinda ya tab'oka ni ya shafa.
Me ya had'aku har take zaginka ? Gyara zama Dikko yayi sannan yace ba komai, kuma ma ai bata zageni ba Dady, duba Babana yaushe ka fara b'oyemin abinda ya shafeka ? Ni zaka juyawa baya ? Me zaka b'oyemi bayan kasan ni bana b'oye maka komai ? Fad'amin abinda ya dameka muyi damuwar tare.....
Shiru Dikko yayi na wasu mintoci yak'i yayi magana, Dady yace kai nake saurare Babana kaji tsoron Allah ka fad'amin abinda yake damunka idan har kana so nayi bacci a daren yau.....
Har yanzu Dikko baiyi magana ba kuma bai kashe wayar ba, Dady ya k'ara cewa ka daiji tsoron Allah ka fad'amin gaskiya k'arya ba halinka bane kuma masu sunan manya basa fad'ar abinda ba gaskiya ne ba, gaskiyar mahaifina da amana irin tashi yasa na saka maka sunanshi saboda kwad'ayin kaima ka zama mai gaskiya da amana kamarshi, kuma ina fatan ka zama mai adalci ko bayan bana duniyar nan..... Ina so ka zama jigo ga "yan uwanka ka tausaya musu ka karb'i damuwarsu ka sakasu farin ciki karka barsu suyi kukan rashin mahaifi, inaji a jikina bazan dad'e duniya ba, nayi kuka kuma na shiga damuwa rashin samun d`a namiji, sai kuma nayi farin ciki a lokacin da Allah ya azurtani dakai...
Idan kaga na damu da nasan abinda yake damunka saboda in d'oraka hanya idan naga zaka sauka daga saman layin gaskiya, ina fad'a maka tawa damuwar ne dan ka gane abinda duniya take ciki.
Me ya had'aka da yarinyar mutane take zaginka ne Babana ? Cikin kame kame yace Dady nifa ba zagina tayi ba, kuma ma yake maganar cewa tana min rashin kunya a ina akayi haka ? Ni ba ruwana da ita sab'ani ne kawai muka samu kuma ma ai abun ya wuce....
Saidai inayin mafarkinta idan ina bacci, inajin damuwa ne idan na tuno da ita, sai kuma inji kamar tana kiran suna na wani lokaci, kuma sai inji kamar tana tare dani, inajin kamar numfashinta a jikina sai kuma shashshekar kukanta tana dai zuwa min sosai a ranaku da dama, shi yasa ma nake d'an tunani, amma bayan haka banda wani damuwa da ita.
Tou soyayya kakeyi da ita ne ? Dady ya tambayeshi, no ba soyayya kawai dai rashin kunya tamin sai nayi maganin bakin tsiwa, kamar ya dady ya sake tambayar Dikko, shiru Dikko ya sakeyi ya kuma rasa abin cewa.
Kai nake saurare, Dady ya fad'a, kwashe komai Dikko yayi ya fad'awa dady amma bai fad'a masa labarin wani abu ya shiga tsakaninshi da Sultana ba, kawai dai yace ya sissiye gidajen da suke haya ne, a haka aka tsaya ba maganar yayi wani abu da ita.
Nasiha Dady yayi ma Dikko kamar yanda ya saba, yace yayi ta addu'a, kuma zasu tayashi har Allah yasa ya manta da labarin Sultana a rayuwarshi, godiya Dikko yayi ma Dady sukayi sallama.
Haka kuwa akayi domin dai Dady ya mik'e tsaye yasa ayiwa Dikko rok'on Allah dan shi a tunaninshi Sultana aljana ce, ko kuma mayu ce ko tanawa d`ansa asiri ne, dan haka Dady ya tsaya akan k'afafuwanshi saida ya tabbatar Dikko ya manta da labarin Sultana a rayuwarshi sannan hankalinshi ya kwanta...........
Wannan kenan...........
***
_{ kalu bale gareku matan aure.......... }_
Gidan da na kama haya gaba d'aya gidan matan aure ne babu zawara ko d'aya haka babu budurwa idan bani ba........
Kowa da mijinta daban babu wacce ta had'a miji da wata, abinda na fuskanta da rayuwar mazauna gidan kowa yanayi ma d'an uwansa kallon hadarin kaji ne, babu wanda yake san kowa sai zazzafar bak'in ciki da jin zafi da gasa da kowa yake nunawa abokin zamanshi ido biyu kunne tsaye babu kunya bare kawaici.
Gidan babu katsari kuma bashi da saiti kowa yaga dama shigowa yakeyi, sai a tara dandazon taron mata ayita maganganun sakarci da rashin kamun kai, shi yasa zawarun anguwar da "yan mata wanda suka bushe fitilarsu suka maida gidan dandalin sauke lalatarsu.
Suna da wata d'abi'a d'aya dana lura da ita ta wasan banza, kuma basajin kunyar nuna tsiraici wa junansu, ma'ana kamar irin cire riga da bra a lokacin fira, irin wancan tace amma wance gaskiya kinfi wacce nono, basajin kunya sakin maganganu na sakarci da fallasa sirin mazajensu.
Duk da ni yarinya ce mai k'aranci shekaru a cikinsu na raina musu wayau gaskiya, kuma na d'aukesu wawaye idan naga dama zan basu shawara kuma idan suka d'auka zata musu amfani, amma gaskiya banga dama ba, haggu zanyi amfani da ita dan ni yanzu ba shiriya nake so ba lalacewa itace na zab'a kuma duk wanda naga zai lalace saina kama mishi ya lalace, dan nayi alk'awari saina kafa tarihi a garin katsina, ina so in zama cikakkiyar karuwar da sai suna na ya shiga cikin sahun "yan iska a duniya, dan bazan yadda nayi karuwanci wahala ba.
Kujerata na d'auka na nufi k'ark'ashin bishiyar da ake zaman majalisar, ina k'ok'arin kafa kujerata zan zauna wata zawara tace ke Sultana tashi nan ba wurin zaman yara bane ba kinji.....
Gaba d'aya suka shek'e da dariya tare dayin gud'a, { ayyuri yuri yuriiiiik.... } aka kashe, murmushi nayi tare da ajiye kujerata na zauna, ba tare dana kalleta ba nace dan anyi ciwo an warke ai ba'a ba mutuwa haushi ba, abinda kike takamar an baki nima naci irinshi, tou me za'a b'oyewa ruwa bayan babu inda bai shiga, ansha kuma anyi wanka dashi aikuwa kinga farin wata ba bak'on dare bane ba.
Duk macen dake wurin saida ta kalleni, murmushi nayi irin na "yan duniya tare da d'aga girare na duka nace muci gaba da zance ai abokin cin mushe ba'a b'oye mishi wuk'a.
Sama sama dai akayi firar wannan rana babu wani labarin ci gaba da guda guda kowa ya sab'e duk wanda ba gidan yake ba yayi tafiyarshi aka barmu iyakarmu "yan gidan.....
Bayan sun fashe ne kowa ta tashi ta fara aikin gabanta tunda masu labarin iskancin sun tafi, dan haka sukeyi idan dai ana wannan firar jarabar babu macen dake motsawa, idan kuwa d'anta zaiyi kukan mutuwa bata kulashi.
Maganar sallah kuwa saidai a mik'ata a jimlace, wai sai an gama zance duniya za'aje ayi alwalla lokacin za'ayi azahar la'asar magrib isha'i, wata ma idan ta makara bata tashi sallah asubahi ba, har gari ya waye tou duk wacce ta fito ta samu an fara fira tou wannan sallah sai anjima za'ayi ta, nan mace zata jibge kamar asara ayita kiraye kirayen "ya "yan dan ubanki baza ki kawomin kaza ba,
Saida kowa ya tashi sannan nima na d'auki kujerata nayi d'akina, buta na d'auko nazo nayi alwallah magrib na shige tare da rufe k'ofata ba kuma zan sake fita ba sai Allah ya kaimu gobe lafiya.....
Dan babu abinda banda shi a cikin d'akina na masarufi, ina da indomie ina da kayan tea kuma ko wane lokaci flarks ina cike yake da ruwan zafi, saida nayi sallah isha'i tare da addu'o'in samun d'aukaka kamar yanda na saba a duk lokacin da nayi sallah.
Bana buk'atar komai domin banajin yunwa, a inda na gama sallata a wurin nayi kwanciyata, ban dad'e da kwanciya ba bacci yayi gaba dani.....
Can cikin bacci naji hayani wanda tak'i k'arewa muryar Nana sama sai zabgaga ashariya takeyi tare da cewa auren ka ko auren wahala, auren cida kai niba ga gidan gayu ba na bige ga zaman haya, har kunya nakeji k'awayena su san inda nake dan darajata da nasabata ta wuce in aureka haka nan Allah ya had'ani da wannan auren k'addarar da k'aranci shekaruna duk kabi ka bigar dani na koma wata abun tausayi, tou wallahi idan kaga yau na kwana dakai saika biyani duk bashin daka san inabinka....
Ajiyar zuciya na sauke tare da kallon "yar agogon dana mak'ala a jikin bangon d'akina 11:45pm, maida kallona nayi wurin da Nana da mijinta dake rik'e da wandonshi yana mata magana amma bana iya jiyosu....
Zazzaga Nana tayi tare da cewa wallahi ka mutun ba abinda ya dameni idan ma ka mutu ko ka sakeni ai dubunka suna can suna jirana, magana ya sakeyi still banji abinda yace ba, Nana kuwa ta sake d'aga murya cewa bazan koma d'akin ba, kamata yayi da kokowa yana k'ok'arin turata cikin d'aki, d'an gajeran tsoki nayi tare da tirr da Allah wadai da wannan hali....
Bansan yanda suka k'are ba na koma nayi kwanciyata naci gaba da bacci na. Tunda na kwanta ban sake farkawa ba saida aka fara kiraye kirayen sallah asuba......
17/08/2019
*JAMILA MUSA*🤙ðŸ»
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 11
Tashi nayi na fito nayi alwallah, bamma kowa magana ba na koma d'akina... Kuma koda na gama sallah kwanciya na k'arayi dan inajin gajiya sosai ga kuma bacci.
Amma k'iri k'iri baccin ga yak'i zuwa, hankalina da tunani na gaba d'aya ya tafi ina tunanin irin yanda Nana ta tozarta mijinta daren jiya a cikin bainannasi, miji da yake da daraja yake da matsayi yake da mutunci abin tattalawa idan Allah ya baka, ubangiji ya rataya ma Nana rigar arzik'i amma tana k'ok'arin yagata ta ratayawa kanta rigar wahala, idan har Nana ta fito daga gidan mutunci ko a gaban d'iyanta batayi wannan iskanci ba amma shine har ta fito tsakar gida kuma gidan ma na haya dan ta nunawa mutanen gidan cewa ita ta hana mijinta hak'k'inshi.
Gaskiya abinda wasu matan sukeyi bai kamata ba, duk yanda akayi a zaman jiya aka rud'awa Nana tunani, ashe kuwa idan har zaki biye ma labarin "yan iskan mata babu ranar da hankalinki zai kwanta a gidan aure, su basuyi auren ba kuma su hana masu zaman auren suyi aurensu, sai su rud'aki da zance babu labarin k'arya a samu a kakkab'oki sai kin fito daga gidan mijin kizo kiga labari yasha banban.....
Maganar Karima najiyo tana cewa jama'an gida ku fito majalissa d'inki duniya ta fara tattaruwa, ga A' i nan ta taho da labari, Nana tace ai bama labari kad'ai tazo dashi ba naga ta shigo da leda duk "yanda akayi daren jiya anci kaza mu ta ragowa sauran, kaji jakka sai kace rainon mayu dan ubanta.
Hayaniyar matan gidan naji da alama kowa tayo waje, agogo na kalla naga duka 6:22am, gaskiya dai hakan bai kamata ba da zasu yadda dana basu shawara amma bara nima na fita wajen mu gani....
Nana na gani tana wanke fuskarta tare da cewa ai ilimi yafi sallah ita sallar bara a jingineta idan na gama d'aukar darasin nayi ta daga baya.....
Kallonta nayi k'asa da sama amma banyi mata magana ba, duk yanda akayi Nana uwayenta jahilai ne, wata zuciyar tacemin karki zargi iyayenta Sultana wallahi kina iya ganin babu laifinsu d'a nawa kake ba tarbiya idan yaga ba idonka ya barbad'ar da ita yayi wanda yake so.
Ina isa inda kowa yake na kalli A ` i, nace gaskiya ki daina yo mana sabko duk fa masu gidan basu fita ba kawai sai ki baro gidanku kizo ki hana mazajen wasu baccin safe ? Irin haka da kukeyi gaskiya bai kamata ba, kallon Nana nayi tare da ci gaba da cewa gaskiya kuma matan gidan nan kuna da naku laifi da kuna zamanku a wurin mazajenku baku fito ba babu wacce zata rik'a dako muku sammako ta hanaku samun ladar kwanciya a jikin mazajenku.....
Nana zatayi magana A ' i tace barta in bata sani ba a fad'a mata, kallona tayi tare da cewa ke Sultana kinsan makaho idan yana kashi baisan ana kallonshi ba sai an tsokalo d'uwawunshi, munsan tal munsan sal abu d'aya yasa bazan gaya miki ko waye ubanki ba da rayuwar gidanku amma yau dana bud'e miki zani cikin kasuwa.
Ke harma kina da bakin da zaki zo ki wani ce an hana mazan wasu bacci , ina kika san wannan keda uban naki ma ko gidan bai kwana..... Murmushi nayi ba tare dana nuna naji zafi akan tabo Babana da tayi ba nace.....
Ai duk ubanda ya ganni yasan ubana zauna gida ne, ko bai kwana ba kinsan yayi k'ok'ari kuma ya fita hak'k'in mata tunda har ga sakamakon mu ya fito, duk namijin daya zauna gida ai soko ne tunda babu k'ashin zuciyar da zaisa ya fita neman abinda zai ba iyali, niko zuciyar ubana tsaye take wurin nema ya nemo aci asha kuma ko bai kwana gidan ba da safen idan ya dawo suma matan gidan zai basu hak'k'insu kinga kuwa dan bai kwana ba ai ba aibu bane ba tunda dai abinda suka aure shi danshi d'in ai yana basu bai hanasu ba.
Saboda mata da yawa wannan abun dake kika raina su sunsan darajarshi, wasu matan kuwa zasu iya hak'uri da talaucin namiji amma wannan abin d'aya da kike magana akanshi basu yadda su rasashi ba, wata macen kuma mijinta ya daketa ya hanata abinci amma idan dai zai kwanta da ita ta samu gamsuwa zatayi hak'uri taci gaba da zama dashi a haka tasan arzik'i na Allah, amma wata ita ba shi take mawa ba rayuwarta da tunaninta ya tafi wurin tunanin neman duniya, kamar dai ni dake kinga ba abun ya fiddo mu ba kasuwanci muka d'auke shi, tou haka matan gidan nan suke su ma, da mazajensu masu kud'i ne ko sunyi wani abun wani sa d'aga k'afa dan duk yanda ka raina d'an tsintsu bakacin shi da gashi, namiji ya sakarwa mace ragamar gida ai dole ta koma mijin shi ya zama matar, amma duk da haka dai ki sani Allah ba ruwanshi da kin nemo kinba miji tunda hak'k'in cida da sha sutura da wurin zama lafiya da ilimantar wa duk saida ya d'auki alk'awarin zaiyi a gaban waliyyanki ,
To tunda anyi auren kin gane bazai iya ba ai sai a raba auren ki huta amma bawai ki zauna kiyi ta yayar ma kanki zunibi ba, zaiyi wuya kiji mace taje gidansu takai k'arar mijinta yana basu abinci so d'aya a rana.
Amma mafi yawancin mata namiji ya hanasu hak'k'insu ko baya gamsar dasu sai kinji sunyi tsegumi, aba k'awaye labari aba mak'ota labari aminiya da duk wanda kike hud'd'a dashi sirrin mijinki fallashshe ne, tou wa kikayi mawa ?
Nidai shawara ce idan ta muku zafi sai kuyi hak'uri, amma ya kamata ku rik'a sirrinta sirrin mazajenku domin dai wannan sirri ba abin yayad'awa bane shi yasa yake rufaffen sirri ko an shiga d'aki sai an rufe k'ofa....
Tsoki Nana tayi tare da cewa mu idan zaki zauna kiji ki zauna idan bakiji ki k'ara gaba, Karima tace da Allah kyaleta tafi ma mill tsayuwa bamu fasa zancenmu, ke A ' i albishirinki ....! Saida A ` i ta harareni sannan tace goro,
Jiya fa Audu yaci ubanshi da gudu ya biyo Nana har tsakar gida, kallon Nana tayi tare da cewa kai jiya fa Nana tayi bala'i gidan nan , can naji gurnanin munafiki kamar an kwacewa mahaukaciya diyarta.....
Ke Nana bada dai labari da kanki kinsan masu iya magana nacewa wak'a bakin mai ita tafi dad'i, mu na waje muka gani bamu kalli na d'aki ba.
Tab'o ledar hannun A ` i tayi tare da cewa da Allah idan dai namu ne ki bamu mu cinye sai miyau na yake tsikewa, mik'a musu tayi "yan iska masu kama da maguna suka rarraba suka cinye, Nana na cewa dan Allah A ` i ki kawo min ice cream rabona da insha shi tun ina budurwa,
Karima ta katse ta da cewa haba da Allah bamu labarin Audu ki daina wani zancen ice cream, lashe hannunta tayi sannan ta fara cewa, in fad'a muku tunda na ganshi ya shigo da leda nasan dole yana buk'ata...
Ajiye ledar yayi a gefe na tare da cewa karfa kiyi bacci, inajin yace kar nayi bacci nasan tafiye yake da damuwarshi, saida na bari ya gama abinda yakeyi tsaf yazo ya hawo ta bayana yana wani shashshafoni na fara mutsirniya, cikin raunanniyar murya magana mai fitar da numfashin wahala yace kar muyi haka dake Nana yau kusan sati biyu kenan kina hanani hak'k'ina bakyajin tsoron fushin Allah ya sauka kanki ......?
Aiko na b'ata rai nace gaka k'atoton wanda fushin Allah zai saukar mawa , ai idan dai har kaga ka kwanta dani tou wallahi sai ka biyani duk bashin da nake binka..... cikin rawar jiki ya fara k'ok'arin juyoni yana cewa kiyi hak'uri Nanata wallahi ba'ayimin biyan bashin ba, kuma banyi ciniki sosai ba yau abinda na samu gashi nan na biya na dafo miki indomie, tsoki nayi tare da cewa ai sai ka cinyeta ka kwanta kayi bacci.
Haba Nana idan dai har kika ga anci ko ansha saida natsuwar ci, ina tare da babbar yunwar da abinci bazai gusar min da ita ba kin sa na zama wani susutacce na zama kamar wani tab'ab'b'e banda natsuwa bare kwanciyar hankali kiyi hak'uri don Allah yauma karki ce zaki hanani....
Ai ban gama jin zancenshi ba na duro daga saman gado nayo waje..... Ni kuma naji tana wannan haukan shi kuma ya jata suka koma d'aki. Murmushi nayi tare da cewa kin burge Nana.... Tou me ya faru bayan kun koma d'akin ne ?
Tunda na lura basa san gaskiya shi yasa nima zan biye musu mu zama riftattun gaba d'ayanmu, Nana tace ai koda ya maidar dani d'aki da k'arfin tsiya babu abinda na yadda ya shiga tsakani na dashi, yayi magiyar yayi nacin kuma ya jaraba ansa ta k'arfin tsiya amma ya gagare shi, dole ya hak'ura ya fita baima kwana gidan ba......
Dariya nayi tare da cewa tou ina kike tunanin ya tafi Nana ? Yo can shi ta matse mawa koma gidan uban waye ya tafi bai dameni ba wallahi saiya biyani bashi na ko zaici gaba da kwanciya dani.
A ` i kuwa cewa tayi kwarai Nana karki sake ki yadda ko gidan haya kake zaune kud'in wata ya k'are idan baka biya ba no uziri tashinka akeyi, ya baki idan babu kullum yaita kwanan hak'uri, gaba d'aya suka bushe da dariya...... Banda ni da nabi Nana da kallon tausayi !!!
Mijin Karima ne ya fito cikin kunya yana san ya shiga bayi amma kunya ta hanashi fitowa dan yanzu mun k'ara yawa, daya d'aga labule ya hangomu sai ya koma, k'arshe dai hak'ura yayi da wanka yasa rigarshi yabar gidan.....
Fira akaci gaba dayi tunda muka zauna har zuwa yanzu babu macen data tashi koda wasa, ganin rashin aikin yin nasu bashi k'arewa yasa na tashi dan ina da wurin zuwa anyi firar dare dani idan banyi baccin wuri ba,
Saida na share d'akina na gogeshi tass na kunna tsintsiyar k'amshi sannan na zuba ruwa naje nayi wanka, ina fitowa na shirya saida na gama shiri na sannan nasha ruwan tea ko biredi babu ina gamawa nayi ma mutanen gida sallama tare da rufe d'akina nayi gaba abuna.....
A zaure na sauk'e nik'af ina na fice daga gidan tare da addu'ar yo babban kamu idan na fita, A ` i na gani tsaye da wani amma bansan ko waye ba, ni mamaki ma ya kamani dan bansan lokacin da A ` i ta fito daga gidan ba...
Har zan wuce naji tace ina zuwa haka Hajiyata ? Yaye nik'af ina nayi tare da rage girman idona na dama nace farauta zanje kinsan sai ka gane girman gida kake sanin ta inda zaka fara shara.... Murmushi A ` i tayi tare da matsowa kusa dani ta d'an rik'o k'uguna da hannu d'aya, sannan tayi min wani irin kallo wanda ni bansan abinda yake nufi ba......
Saida ta wani yi k'asa da murya sannan tace da ganinki zakiyi tunon asiri amma ina gargad'inki da ki rik'awa bakin linzami ta k'arasa maganar tare dayin murmushi, bud'e idanuwa nayi dukansu wanda idan har na d'an ragesu na bud'esu lokaci d'aya nasan ina k'ara kyau kuma mutane sunsha fad'amin haka.
Kallonta nayi da duka idanuwana sannan nace dama tunda kike kin tab'a ganin mazinacin da yayi sirri ? Miya had'a karuwa da sirri dama ? Ai da amana da kunya da sirri da gaskiya duk karuwa bata dasu, kunya tana tasowa ne daga b'oye tsiraici tou ban b'oyeshi ba zan bud'ashi wa duk wani mai kud'i ya gani, kinga nan rashin kunya ta fito, daga inda babu kunya kinga babu imani duk mutumin da baida imani kuma bashi tare da rahmar Allah, ina bud'ewa ga maza, namiji kad'ai ya isa ya gani yasha kuma ya tab'a dan haka sakarmin k'ugu daga yau karki kuskura ki sake tab'amin jiki, idan har na baki sha'awa tou ki zama namiji kizo da dubu dari shidda sai in baki duk abinda kike gani a jikina ya burgeki, na k'arasa maganar tare da sauke hannunta a jikina....
Kallona A ` i tayi tare da cewa ai duk saurin anguwar zoma ta bari a haihu ? Duk saurinki kin bari kiji uzirin da nazo dashi..... Bud'e k'ofofin hancina nayi sannan nace ai tunda har aka tanaji aikin ungozance ansa haihu tana zuwa kinga kuwa duk daren dad'ewa amfaninta zaizo. Tou ni bana jira idan na gani saina tanka na dakatar dake ne tun kafin cikin ya samu bare kisa ran ansar haihuwar....
Na sanki cikinki da waje, duk macen dake gidan nan nasanta kuma tun ranar da na kwana na gama karatun halin kowa, kwalwa ta gane inda mutum ya dosa Allah ya bani amma bai bani kwalwar gane rubutu da karatu ba, ina iya gaya miki duk macen dake lesbian a cikin gidan nan , kuma ina gane duk macen da namiji ya kwanta da ita ba tare da na sani ba, ki kiyayeni ina da had'ari ne mai girma domin nima kaina tsoron kaina nake, ki fita idona tun kafin inyi miki terere.......
Shiru A ` i , tayi ta kasa magana..... Murmushi nayi tare da dafa kafad'arta nace yawwa kisan wani abu gaskiya ni bana gaba da mutum ina so abun nan ya tsaya iya mu biyu, zan wuce ki gaishe min da mijin Nana kuma bazan bata labari ba , ina fad'in haka nayi gaba abuna.....
Cin amana da rana k'iri k'iri wannan fa shine an raka zomo rami an dawo.... A ` i takai Nana ta barota gashi kuma tana tare da mijinta, kila ma jiya da yayi zuciya da Nana wurin A ` i ya tafi ya kwana, tabbas ma can yaje tana nan tana haukan banza mijinta yaje ya siyo ma k'atuwar banza kaza taci ta rago musu....
Zuciya ta ce tace Sultana kiji tsoron Allah zato zunibi, tsoki nayi tare da cewa wannan ai ba zato bane abinda yake filin Allah kowa yana gani dandai kawai gaskiya bata fad'uwa, sudai suka sani amma idan tayi tsami kowa yaji.
Napep na tare na fad'a mishi inda zanje, ciniki mukayi na shiga yaja muka tafi. Yau babu inda zan sauke zango sai wurin Alhaji mai gidan "yanci, wato inda Umar yakai ni da farko ban shiga ba na dawo, dalilina na haka kuwa yanzu zakuji.......
18/08/2019
*JAMILA MUSA Ce* 🤙ðŸ»
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 12
Abinda yasa banbi Umar mukaje gaban Alhaji saboda na shirya lafiyayyar yaudara da zanyi masa, sana'ar karuwanci tayi min kad'an gaskiya dan haka dole sai na had'a da sata, shekaru biyu kacal zanyi a cikin wannan mummunar d'abi'ar, ina so na shigewa Alhaji sosai a rayuwa idan ya saba dani zan kunce dawakan Dikko duk in siyar dasu, nasan duk doki d'aya za'a siya da kud'i masu yawan gaske.
A wancan lokacin da munje tare da Umar Alhaji yaga fuskata tou kud'in Umar da nayi wayau na kwace masa tou Umar zai koma ya fad'awa Alhaji cewa wannan yarinyar b'arauniya ce ayi hankali da ita...
Bani da tabbas kuma bani da alkibla nima kaina tsoron kaina nake bansan abinda yake damuna ba umarni kawai zuciyata ke bani ni kuma ina biye da ita.....
A k'ofar gidan Alhaji napep ya sauke ni, kud'inshi na bashi ya wuce nima na shige ciki, kaina tsaye na tunkari gidan babu wani tsoro fargaba bare kuma jin kunyar kowa amma har yanzun ban cire nik'af ina ba.....
Ko mai gadi baiyi yunk'urin dakatar dani ba domin dai yasan mata abokan hud'd'ar ubangidan nasa ne... Hanyar da Umar yabi dani hanyar nabi naci gaba da tafiya har na shiga cikin palon gida....
Saida na shiga cikin palon na cire nik'af ina, d'an kallon palon nayi sannan na kallo inda hotunan mak'iyi Dikko yake raina ya b'aci sosai tsinan ne duk shine silar rushewar gidanmu kowa ya bazama ya shiga duniya, duk da bai sissiye ba da muna zamanmu cikin farin ciki, idan dai kud'i yasa kayi mana haka nice zan mayar dakai talakan k'arfin da yaji, uhum da kinsan waye Dikko da baki ce haka ba .....
Sallama na kwarara daidai yanda nasan za'a iya jiyoni, daga ciki naji ance shigo mana ! Inda naji sautin maganar ya fito nabi na shiga, kwance mutumin yake saman gado ya wani baje sai kace anyi b'arin asara...
Kallo d'aya nayi masa tare dayin murmushi na zauna a gefen gado, kuma nayi karatunshi tun shigowa ta bakin gwargwado kuma na fahimci wasu d'abi'u nashi, da gani zaiyi sauri fushi kuma yana da saurin sauka, yanayin shi ya nuna abun duniya bai rufe mishi ido ba, amma wannan da ganin idonshi mayen mata ne lallai wannan idan ya dafi mace aradu mai ansarta sai Allah...... !!!
Alhaji barka da yini, cikin sakin fuska ya amsa min da cewa barka dai malama ya kike ? 'Dan gyara zama na nayi tare da cewa lafiya qalau ya aiki ? Kallo na yayi tare da cewa ki ganni kwance kuma kice min ya aiki ? Murmushi nayi tare da cewa ai na kwance kuwa shi yasha aiki Alhaji inba ba'ayi tuk'in zaune ba ai anyi na kwance....
Kallo na yayi tare dayin dariya irin tasu ta gogaggin "yan bariki sannan yace wace ce ke ? Kama kaina nayi tare da tattaro natsuwa ta dan ni nawa ba kalar nasu bane, saida na tattaro class ina sannan na d'an rage yawan fara'a , suna na Maryam Aliyu Binna........ Amma anfi sani na da Sultana.
Talla na kawo maka da fatan zaka siya ? Na k'arasa maganar tare da kashe mishi ido d'aya.... Dariya Alhaji yayi tare da gyara zaman belt inshi sannan yace yarinya me kike siyarwa ne ?
K'addara......... !!! Kasan kowa da irin tasa k'addarar haka kuma kowa da irin k'addarar da yake siyarwa, idan talauci ya ishi mai rai yakan siyar da duk wasu abubuwa nashi daya siya ya adana, manoma sukan b'oye hatsi yayin da sai yayi tsada suke siyarwa, dillalai kuwa sukan adana k'addara ta k'asa sai tayi kud'i su siyar, macen da kud'i suka kama idan tayi ajiyar d'an kunnen zinari zobe ko awarwaro wannan talaucin zaisa ya ziyarci kasuwa, yayin da duk macen da tasan ciwon kanta take k'ok'arin adana tata k'addarar da Allah ya bata kyauta sai taje gidan mijinta,
Ni kuma talauci ya dameni ba gidan zama bare motar hawa, kuma ban ajiye hatsi ba ban aje gold ba, shi yasa na d'auko nawa mutunci zan siyar amma sai na lura babu wanda zai siya da daraja idan ba kai ba, dare d'aya tak zaka more amma farashin farko kuma ba tayi miliyan d'aya ne,
Ka ganni dai a fuska gwanin burgewa, masana sirrin mata sunce duk macen data cika muni zaiyi wuya tayi wani armashi, sai kuma sukace kyakkyawar mace kuma wannan riba biyu ce harda gyara ma, karfa kaga kamar ina yaba kaina ne fuskar gida ba itace take nuna tsarin sa da haduwar sa ba, sai an bud'e an duba ake ganewa....
Duk mota sunanta mota amma wata motar bata kai mota ba, tou haka take ga mata duk mace sunan ta mace amma wata macen muna mata ce..... Na k'arasa maganar tare da kallon Alhaji nayi masa kyakkyawan murmushi mai tattare da jan hankali. Saida na kauda kaina sannan nace amma ina da sharadi d'aya , idan anyi ba'a sake maimaici wannan shine sharad'in kasuwata idan zaka zuba hannun jari bisimillah, na mik'a masa hannu na da niyar mu k'ulla alk'awari....
Gyara kwanciya Alhaji yayi da niyar magana amma na lura da yanayin fuskarshi kamar bai yadda dani ba, dan haka na tare maganarshi da cewa karka cuci kanka wannan harka duk taimakekeniya ce , ka bani gishiri in baka mand'a , kaga masanya ce za'ayi fa ni wannan ba matsalata bace kud'in ne kawai damuwa ta, ka yadda na rana d'aya tak 👌ðŸ»........
Kallo na Alhaji yayi tare da cewa tou ai ked'in ce kin tsananta miliyan d'aya fa..... Kin kuwa san girman miliyan Sultana ? Idan na baki ita ina zaki zuba ta ? Waye zai d'aukar miki ita ? Me zakiyi da ita kuma ? Ajiyar zuciya na sauke tare da cewa, wurin zubata da d'aukarta da abinda zanyi da ita duk ba huruminka bane ba, kayi kawai ka bani idan kuma baya yuwuwa in hak'ura inyi gaba kila na dace.......
Tashi yayi zaune tare da tattaro duka hankalinshi gareni sannan yace karki k'i fad'amin, kika sani ko zan iya miki maganin damuwarki ne ? Kuma kike maganar miliyan d'ayan d'aya kika sani ko in baki abinda yafi miliyan d'in ? Ni kud'i ba matsalata bane amma ina san sirri dan duk wannan harkar da kikaga inayi gaskiya banayinta da d'anyar kwalwa saboda gudun b'acin rana.....
Alhaji kenan idan na fahimta kallon yarinya kake min ko ? Tabbas a zahirance ni yarinya ce amma a bad'ini ni mai tunani ce, babu wanda ya koyamin yanda ake bariki ni na koya da kaina, ban yadda da zama k'ark'ashin kowa ba nima saboda gudun b'acin rana, "yanci na, mutunci da kowa yake tak'ama dashi ya siyar akan kud'i k'alilin k'arshen wulak'anci da tozarci mak'iyina da bana k'auna shine ya taka ruwan ciki na, a cikin gidansu ya keta min hijabin da nake ta boyewa shine yayi mata kaca kaca.... Shiru nayi saboda idan dai har naci gaba da magana zan iya kamo sunan Dikko in d'ura wa uwarshi zagi.
Hak'uri Alhaji ya bani tare da jawoni jikinshi yace kiyi hak'uri ku matan ne baku da amana sai a had'a kai daku a cuci mutum, murmushi nayi tare da cewa ai ko zanyi cuta bana tsaya inda aka sanni ba, kana dai da kud'i kusa dakai dan bana amfani da banki danma karka wani ce zaka turamin.....
Cikin raunanniyar murya yace karki damu Sultana d'akin nan cike yake da kud'i, zan sake magana ya had'e bakina da nashi wuri d'aya labari ya fara canja salo.....
Murmushin mugunta nayi tare da bawa Alhaji duk abinda nasan zaisa ya samu natsuwa.... Ya dad'e yana gurje kud'inshi kuma ban waniji wata damuwa ba, har saida ya gaji dan kanshi ya kyaleni.
Sauka yayi daga saman gado ya nufi toilet ni kuma ina nan kwance, yana shiga na zaro wayata dana soke a jikin gado wanda duk abinda mukayi da Alhaji saida na d'auka, dariya nayi bayan na gama kallo sannan na mayar da wayata cikin jaka...
Kafin Alhaji ya fito har na gama saka kayana na maida nik'af ina na zauna bakin gado.... Ina jiran fitowarshi ! Bai wani dad'e ba ya fito da sauri ya nufi wurin wayarshi saboda tun dazu ake kiranshi banyi gigin dubawa ba saboda ko na duba bana gane suna....
Kayi hak'uri mai gida shine dai abinda yake ta maimaitawa, bansan abinda abokin wayar yace mishi ba naji yace Eh an basu ranka ya dad'e , tou insha Allah, Allah ya tsare ubangijj ya k'ara taimakawa. Sallama sukayi dashi Alhaji ya ajiye waya sannan ya kalloni tare da cewa ke yanzu ya zamuyi ne ?
K'afa d'aya a saman d'aya na d'ora sannan na ajiye hannuwa na ta baya nace bani zakayi in wuce marece yanayi, tou baza kiyi wanka ba ? 'Dan girgiza k'afata nayi sannan nace bana sauke najasa a wurin da bai kamata ba ka bani kawai na wuce.....
Tou waike taya zaki d'auki miliyan d'aya ne ? 'Daga nik'af ina nayi tare da cewa karfa ka raina min hankali ka bani in wuce kana b'atamin lokaci kaji.... Murmushi yayi tare da cewa ya zaki d'auki zafi da wuri haka ? Tou ya zakiji idan na hanaki kud'in nan, murmushi nayi tare da cewa kai kuma ya zakaji idan ka samu hotunan vidio abinda mukayi a yanar giza gizo ..... Na k'arasa maganar ina masa kallon rainin hankali.
'Daure fuska yayi tare da cewa sai in kashe ki, murmushi nayi da gefen bakina tare da cewa tou da suka shiga duniya kuma ya zakayi da duk wanda ya gani ? Ta ina zaka bi ko gogesu a cikin wayar kowa ? Akwai "ya "ya akwai surukai ga kuma matanka abinda kake b'oyo tou gashi a cikin wayar "yarka ko d'anka tou ya zakayi dasu.........
Zufa ta keto mishi sosai, dariya nayi tare da cewa tou goge ai haka ma bazata tab'a yuwuwa ba, kawai nima nayi maka barazana ne kamar yanda kake neman hanani kud'ina, kaga abinda bazai yuwu bane bani na wuce,
Ya kama kanshi sosai dan haka yace zan baki dubu dari biyar yanzu anjima ki dawo ki amsa sauran, gaskiya idan na tafi bana dawowa ka bani kawai sai mu rabo lafiya, tou wai babu zan baki ? Nace itama babun idan tana kamuwa ka bani ansa zanyi ba cemin kayi d'akin ka cike yake da kud'i ba ?
Mutum cikakke mai arzik'i kamar ka ai bai kamata ya rik'a d'aga murya ba akan miliyan d'aya kacal ba, miliyoyin da suka tafi babu dalili baka san iyakarsu ba bare wannan idan ka bada ita ai kasan ta inda tabi ta wuce...
Dubu d'ari biyar ya bani yace muje in baki sauran suna cikin mota, cikin jakata na zuba dubu dari3 muka fita dubu dari biyu na hannu na, muna zuwa ya bud'e mota ya bani sauran kud'in, bud'e gaban mota nayi na shiga tare da cire kallabin kaina na d'auresu a ciki nace ka ajiyeni bakin titi....
Baimin magana ba ya tada mota muka tafi, saida muka tsaya inda zai saukeni nace da Allah rubutamin number wayarka, har yanzu baiyi magana ba ya ciro biro a gaban aljihunshi ya rubutamin a jikin takarda ya bani,
Nima ban sake magana ba na bud'e mota na fita, napep na tare dan zuwa gida, a k'ofar gida ya saukeni na shige, da sallama na shiga gidan sannan na wuce d'akina ina shiga na ajiye kud'in na zuba ruwa na tafi dan tsarkake jikina banyi ko azahar ba kuma ga la'asar ta kusa..
Saida na gama sallolina sannan na dafa indomie naci, bayan na gama na zazzage buhun kayana na zuba kud'in a k'asa sannan na d'auki kayan na maida daga sama, fitowa nayi tsakar gida na nufi majalissar matan aure....
Barkan ku da hutawa mata masu duniya, Karima tace wai ke duk yau ina kika shige ne ? Ban bata amsa ba na canja tambayar da cewa yau kuma zawarawan anguwar nan dame suka zo mana ne ?
Karima tace ai gasu nan sai ki zauna ayi dake, zama nayi saman takalmana sannan na kalli inda Nana take kwance a saman cinyar A ` i wai tana kakkab'e mata dandirof,
Karima kuma sai cewa takeyi Allah dai ya tsinewa talauci albarka, kullum a rasa abinda za'ayi ta baka sai tuwo maganar d'aya dai tuwo tuwo babu wani ci gaba kullum zance kenan, shi yasa gani nan kullum sai bushewa nakeyi ina k'armashewa kamar mai cutar kanjamau.
Niko da bani da zuciya nace aiko Karima ki godewa Allah, domin dai Allah yayi miki rufin asiri ke kin raina tuwo ko ? Na tambayeta, bata bani amsa ba naci gaba da cewa yo aike cin tuwo yanzu basai wanda Allah yaso yake ci ba ? Da safe kina dama d'an kokonki da rana idan Allah ya hore zakiyi d'an wanke ko teba wata rana ma har taliya kuke dafawa, da daddare kuyi tuwo kuci ku k'oshi keda "ya "yanki kuma duk daren duniya naga sai mijinki ya shigo miki da fura, tou ina laifi ? Aike tsakaninki da Allah saida kice Alhamdulillah bawai ki zauna kiyi ta tsinewa talauci ba ai ina ganin haka kamar rashin godiyar Allah ne.....
Saudatu tace, { itama ba'a gidan take ba shigowa takeyi } ai rayuwa tana san canji kullum abinci d'aya an kama dindindigau kamar kukan mutuwar uwa, ai ya kama a samu sauyi mana Sultana.
Nace haba Saude ai duk namijin da kikaga ba'aci mai dad'i a gidanshi ba tou baya dashi babu namijin da yake so a tsarewa iyalinshi, Saudatu tace ai wallahi k'arya ne mijin Karima yana da kud'in da ko naman rago saiya ciyar da ita dashi, dandai kawai had'in fad'a baida dad'i amma wallahi dasai na fad'a mata abinda yakeyi da kuma inda yake kai kud'in nashi , ita ya rainawa wayau ya barta nan tana ta sassak'ar tuwo sai kace matar ladar noma.
Daga wannan maganar har Karima ta kawo wuya, ta fara zazzaga luk'a luk'an zagi tana cewa ai da ganin biri yayi kama da mutum tsakanina da Nuhu sai Allah ya isa ban yafe mishi ba, kuma zai dawo gidan ya sameni saina ci uwarshi....
Kallon Karima nayi tare da cewa idan dai kuna biye ma zawarawan anguwar nan wallahi duk sai sun kashe muku aure, baku san maganar d'auka ba baku san abinda kuke fad'a musu ba ku biye musu su kaiku su baroku, su basuyi aure ba kullum suna biye daku suna halakar daku,
Karima tace ai wallahi Sultana na yadda da maganar Saude saboda rabon da muyi kwanciyar aure dani da Nuhu yau anfi k'arfin wata d'aya, dama idan ba neman mata yakeyi ba ai kema kinsan abunda bazai yuwu bane ba....
Tsoki nayi tare da cewa ai wallahi saina fad'a miki ko zatai miki zafi, ba Nuhu ba wallahi koni dakel nake iya zama kusa dake, mace da aka santa da gayu da kwalisa da k'amshi da tsafa da tsaftacewa tou ku matan gidan nan ba haka kuke ba, kullum safiya kunzo kun jibge a k'ark'ashin inuwa ba wanka ba wanke ido babu sallah bare salati, baki cuwai cuwai ba abinda kuka sani saidai inuwa ta k'are ku ja tabarma ku k'ara gaba,
Kun fito tun kafin mazajen ku su fita daga d'akin ku kun rigasu fitowa, yara sun kwana zabga fitsarin kwance baku tsaya kun gyara kun wanke ba, yanda namiji yabar d'aki haka zai dawo ya taddashi, baku iya magana da mazajenku ba kuna ma mazanku magana muryarku ta kere tasu mace da aka sani da sanyi, kina ma miji magana tsawa tsawa kamar yaron gidanki, duk daren duniya idan Nuhu ya dawo sai yayi wanka ya tsaftace jikinshi a haka zai rungumeki ki b'ata mishi wanka ?
Kalli kanki Karima ji k'afafuwanki waike matar aure ! A haka har kike tunanin namiji zai samu kwanciyar hankalin da zai baki natsuwa ? Aini wallahi ko toilet na shiga mara tsafta banda natsuwar da zanyi komai a cikinshi wuta wuta zan fito dan kar in d'aukowa kaina cuta, gashin hamatarki ma kad'ai wallahi abin zubar da yawu n....... Mik'ewa Karima tayi tare da kaimin duka dan uwarki ni kike cewa kazama ce ?
Rik'e mata hannuwa nayi duka tare da cewa saurara kiji ni bance miki k'azama ba kawai dai ina fad'a miki matsalarki ne, amma kiyi hak'uri ni ba'a fad'a dani gaskiya ce baki so kuma daga yau na daina insha Allah, amma duk da haka zan baku shawara d'aya dake da Nana wala Allah tayi muku dad'i wala Allah tayi muku zafi Nana tace ki rik'e banzar shawararki kila ta miki amfani can gaba..... Murmushi nayi tare da cewa tou ba damuwa na gode amma kuma ku sani bazan daina zaman majalissar nan ba, yanzu ma sallah magrib zanyi na dawo...
Babu wanda ya bani amsa dan haka naje na d'auk'i buta ta naje nayi alwallah, saida nayi sallah isha'e sannan na fito majalissar su......
19/08/2019
*NICE DAI...*
*JAMILA MUSA...* 🤙ðŸ»
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 13
Sallama nayi musu amma babu wacce ta amsamin, na maimaita sallamar har sau ukku amma dukansu babu wacce ko kallona tayi bare nayi tunanin zasu amsa min, murmushi nayi tare da cewa aikin banza kare da gudun layya.
Wuri na samu na zauna, ina zama gaba d'ayansu suka tashi suka bar wurin aka barni zaune ni d'aya kamar mayya, banji wani damuwa ba haka banji bak'in ciki ba domin dai nasan gaba d'ayansu nafi su ta ko ina da ko ina, tunda kuwa nafi su ai babu dalilin ni na biye musu muyi gaba, bawai dan ban iya ba na iya kuma idan na fara nawa bashi da kyau....
Ban tashi a wurin ba na haska wayata na fara kwafar lambar Alhaji daga saman takarda zuwa cikin wayata da nayo mishi vidio, nafi minti biyar ina rubutawa karantawa ne dai bana iyawa amma ina kwafar abu, idan kuwa zan kwafa da guda guda nake d'aukarshi, kuma zansa a bud'emin whatsApp amma ya zamar min na "yan gaisuwa saidai duk wanda zanyi magana dashi inyi masa voice note, na ajiye number shi a wayata, abinda na saka mishi shine lamba 1
Mik'ewa tsaye nayi tare da cewa bak'in ciki da fushi ba naki bane Sultana tunda kina da aikinyi, d'aga muryata nayi tare da cewa waye yake san k'amshi mu bashi turare ? Tou tabbas maik'o saidai a barwa balangu ansha gaban mai tsiri......
Kujerata na d'auko na zauna k'ofar d'akina tunda na lura suna neman su haramta min zaman tsakar gidan ne kuma aradu basu isa ba, watsa kunnuwa na nayi ina jiyo firarsu k'asa k'asa bana iya cewa naji abinda akace duka ba amma da yake Saude bata iya maganar sirri ba, bama itama ba duk matan gidan ga haka suke, ji nayi tana cewa ai wallahi ki had'ani dashi in nemi taimako....
Daga inda nake zaune nace hattara dai matar aure, idan dai an ciza a busa, ki kiyayi duniya da rayuwar mutanen cikinta, ita duniya da kika ganta juyi d'an magwaro takeyi yayin daya fad'i k'asa zai kwaso k'asa da tsakuwa, idan kika wanke zak'in zai fita idan kuma kika sha baki wanke ba zaki ci da k'asa duniya tafi karfin kowa, wanda yafiki iskanci yazo yayi ya koma ki kama kanki kuma kiyi k'ok'ari ki koma gaban Allah kina mai kamanta gaskiya, amma na horeki da ki kiyaye darajar aurenki tun kafin duniya ta juya miki baya....
Cikin hayagaga Nana tace ai ba tsoronki akeyi ba a gabanki ma za'ayi maganar dan kutumar ubanki idan kin isa ki hana wani abu in gani, tirr na fad'a tare da cewa kutumar ubana tafi k'arfin kaff zuri'arku wallahi, saboda ko da yake raba kutumar wa mata badai irinku masu tsamin daud'a ba...
Kaina Nana tayo da gudun bala'i kafin ta iso na d'auki kujerata na rik'e nace wallahi kika kuskura kika iso nan saina raba miki kai gida biyu, tsoro ya hanata ta iso taja tayi tsaye, tsoki nayi tare da cewa k'aryar rashin kunya sakarkarin banza daku, insha Allah ko gani nayi zaku shiga wuta saina watsa muku fetir, ina fadin haka na shige d'akina na kyale jahilai, dan gaskiya na lura wallahi jahilci ne kawai yake cizar musu kwalwa, inma banda b'atar basira matar aure za'a kai wurin wani namiji ta nemi taimako.....
*** *** ***
Sati na d'aya kenan bana shiga safgar kowa a gidan da nake haya, ni dama fil'azal magana bai dameni ba, shigowa na ma gidan nan ne naga har na iya surutu idan dai har magana da sune zaisa su raina ni har kowa yake k'ok'orin magana kad'an ya dakeni tou na fita sabgarsu danni ina da wata irin zuciya da idan har na gama da abu tou fa tabbas na shafe labarinsa a babin rayuwata, niko nace hada Dikko Sultana ?
Cikin kud'in da Alhaji ya bani na shiga kasuwa na kwankwaso tsadajjiyar sutura, na siyi kaya na kece raina, gyale takalmi jaka turaruka mayuka na shafawa irin ya wayayyun mata, agogo sark"a da "yan kunne "yan hannu zobuna saida na tabbatar nima na zama gogaggiyar mace ta sahun farko a fanni sutura.
Sannan naje nakai dinki wurin telan da nasan shima yasan hannunshi, kuma da naje kai d'inkin na fad'a mishi cewa irin d'inki karuwai nake so yayi min, nace yamin d'inkin dako tuk'i namiji yakeyi idan na wuce saiya dakaya saiya manta da kan sitiyari yake ya tsaya ya kalleni, mukayi tsada dashi na biyashi kud'inshi tare da sharadin idan fa ya lalatamin kayana wallahi saiya biyani, yace kuma yaji ya yadda.
Na gyara d'akina sosai nasa kayan kallo na sake katifa mai kyau na saka ledar tsakar d'aki na saka fanka amma ta k'asa, na kuma k'ara biyan kud'in haya daga lokacin da suka k'are daga lokacin zan siyi gida haka shine tsarina na gaba... Saina sayi gidan zama sannan zan sayi mota kuma duk zakuji ta inda kud'in zasu rik'a fitowa babu b'ata lokaci....
Hankalina kwance banda wata damuwa, banda rashin ci haka kuma babu rashin sha, cikin "yan kwanaki k'alilan na fara sauyawa, k'oshi babu abinda ya bari dan duk daren duniya sai naci nama abinda nake so ci nake ci kuma duk abinda naga dama shi nakeyi babu mai kwab'a kuma babu mai kyahra, jikina kuwa yasha mayuka gani bana jin wahalar wanka dan ko agwagwa bata kaini san ruwa ba, ya jama'a ku tayani hasko kyau ya had'u da gayu, ku tayani ganin gayu ya had'u da wanka, ku tuno wanka ya had'u da k'amshi...... Wuta Sultana lokacina ya fara...... Kalu bale gareku k"azaman mata.....
Kwance nake saman katuwar katifata da tasha shinfid'a da tsaftataccen zani, { bedsheet } iskan fanka sai kad'ani yake ta ko ina, ga wani ni'imtaccen k'amshi dake tashi daga d'akin har jikina, yanzu tunani na bai wuce in addabi Bello ba abokin Babana.....
Dan yanda ya haramta wa Babana wali a cikin garin shi, inda aka haifeshi ya girma a ciki yayi iyali, amma ya gudu ya bar "yan uwa da "ya "ya da matanshi tou shima katsina zata haramta yayi wali a cikinta, idan kuma yayi iskanci saiya d'aure kayanshi yabar birinin katsinar gaba d'aya....
Hannu na, na saka k'ark'ashin katifa na jawo wata "yar k'aramar kwalba dana anso hannu wani d'an daba, ya fad'amin sunan abun amma wallahi kafin inzo gida har na manta, abun fesawa gareshi kamar na turare, kud'i na bashi ya siyomin nace mishi abinda idan na fesawa mutum kawai zai kama bacci babu b'ata lokaci shine ya kawomin shi....
Tashi nayi na rufo d'akina dan ina so in gwada inga ko abun yanayi, saman katifa na kwanta sannan na fesa shi a fuskata..... Luuu wani bak'i na gani ya gittamin daga nan ban sake sanin inda kaina yake ba saida 11:30am tayi.....
Salati nayi tare da godewa Allah dana farka na ganni a duniya, d'auko kwalbar nayi tare da sunbatar ta, tabbas kece abokiyar tafiyata, amfani biyu zakimin daga Bello sai Dikko daga nan aikinki ya k'are zan yadaki shikenan.....
Wanka naje nayo tare da d'auro alwalla nazo nayi sallah asuba da ban samu nayi ba, ina gamawa na hau shiri domin yau ba abinda zai dawo dani gida sai nayi ido ido da Bello kuma saina tabbatar da k'udurina akanshi.....
Mai da powder na shafa sai kwalli dana shafawa idona, ban shafa jan baki ba saboda bakina baya buk'atar shafe shafe sai kuma lura da nayi da irin manyan mata mawuyaci kuga sun daddab'awa fuskarsu irin abinda muka shafawa, irinsu jagira aishadow duk basa shafawa shi yasa idan suka shiga wuri suke fita daban, bana buk'atar bilicin koda na kasance ni b'aka ce shima ku lura da kyau bilicin na maciyata ne, d'iyan masu kud'i basa shafe shafe mayuka gaskiya....
Doguwar rigar shadda getzner na saka bak'a, kuma tayi matuk'ar martabani domin dai ta zauna min a jikina ciff na d'aura d'an kwalina coge, na kawo gyale na ida kafe wankan dashi komai dai dana san zai martabo min mutunci na saida na saka a jikina, sannan na yayyafa ruwan turare nayi gaba...
Tun kafin in fito k'amshin turarena yakai tsakar gida, a lokacin dana fito ina rufe k'ofar d'akina kuma gaba d'aya hankalin duk wanda ke gidan saida ya dawo kaina, ina rufe d'aki na saka makulli na a jaka na wuce abuna banma kowa magana ba... Da kallo suka bini domin dai sun gane kura ba sa'ar kare bace ba.....
Tunda na fito gida har nakai bakin titi na zama abin kallo ga jama'a , ban damu dasu ba domin dai duniyar yanzu gaba na bata ba baya ba.....
Napep na tare na fad'a mishi inda zai kaini na shiga muka tafi, cikin "yan mintoci kad'an muka isa, na sauka na bashi hak'k'inshi, majalissar ciki take kamar zata fashe saboda yawan dandazon mazan dake cikinta, ina fitowa napep duk wanda ke wurin idonshi ya dawo kaina...
Banji fargaba ba haka kuma ban daburce ba, banji bazan iya tafiya ba dan ana kallona duk wani bargaba da kunya ko tsoro duk basa tare dani a wannan lokaci, tafiya na farayi zuwa wurinsu na k'addara ma kawai ba maza bane mata ne....
Tsofaffin banza tun daga yanayin kallon da sukemin zaku gane duk sun fad'o rami, kallon tarko suka faramin kamar mage ta ritsa bera. Sallama nayi musu yayin dana isa wurin, kusan gaba d'ayansu saida suka amsa kamar ana biyawa dalibai karatu....
Nima kujera naja na zauna sannan na gaishe su, duka suka amsa cikin sakin fuska, inda Bello yake zaune na kalla tare da cewa Baba wurinka nazo , tou yace amma ban ganiki ba, sadda kaina k'asa nayi sannan na d'an murmusa cikin sigar bariki nace d'iyarka ce ta wurin Aliyu Binna...... Na k'arasa maganar tare da d'ago kaina na kalleshi da kyawawan idanuwa na da suka sha da ado da kwalli nakai karshen maganar tare da d'an sassauta kallo na, sannan na bud'e idanuwan dukansu,
Yashe baki yayi yana dariya kamar yaga wawan zama, sannan yace ahaf tou tou Uwar masu gida ce ? Murmushi nayi tare da cewa Eh, kinyi aure ne ? Ya tambaye ni ? Da kaina na bashi amsa cewa A , a, tou kina ina ne haka ? Ba tare dajin kunyar kowa ba nace ina bariki ne ? Dariya yayi sosai tare da cewa "yar gari kenan yarinya ta gane makoma.....
Nima dariyar duniyanci nayi harsai da kyawawan hak'orana suka bayyana idan dai nayi irin wannan dariya ni kaina nasan tana k'ara min kyau sosai sannan na kalleshi nayi murmushi sai kuma na kama kaina, kallon maita ya bini dashi kamar ya cinyeni a bakin titi sannan yace ina kike zama haka ne ? Ina nan tsohuwar anguwarmu daka sani dai....
Tou taso mana ya fad'a tare da mik'ewa, a raina nace wato tunda na zama karuwa bari a bini a lalace ! Zakaci ubanka domin nima kaina tsoron kaina nakeyi, duk a zuciya ta nayi magana....
'Daukar kujerata nayi muka matsa gaba, zama nayi na d'ora k'afa d'aya saman d'aya sannan nace ya ake ciki Baba ? Am tou aike zan tambaya kinga tunda ga gida ai ba'a kai k'aruwa waje ba....
'Dan gajeren murmushi nayi sannan nace gaskiya kam, amma yanzu kana da mota kuwa ? Eh akwai mota hannuna mana, wace iri ce ? Na tambayeshi yana k'ok'arin fad'amin nace dakata ma barshi kawai kasan ko ka fad'a bazan rik'e ba zan manta ne ,
Duk'owa yayi kusa dani waini zai tambaya yanda muka k'are da Dikko kwanaki, dariya nayi sannan nace ai Dikko ba abinda yayi min kuna tafiya yasa aka dawo dani gida, tsoki Bello yayi tare da cewa kaji sakaran banza wannan tunjumemiyar mace ya bari baisha ruwa ba ?
Murmushin mugunta nayi tare da d'aga girarena nace kila bayajin k'ishirwar ne, tou waike kawai sai kika fara bariki abunki ? Nace sosai ma, tou ya akayi kika zab'i wannan harkar bayan baki san yanda abubuwan suke ba ? Duk zan baka bayani idan kana da wurin saukeni mu tafi kaji komai....
Tou ina zuwa, ya fad'a tare da tafiya wurin abokansu, sallama yayi musu tare da cewa zai dawo da daddare duk zasuji bayani, wani ne daga can yace kayi min register idan ka gama ina layi nima.... D'iyar abokinku maimakon kuyi k'ok'arin d'orani hanya A , a, saidai kuyi k'ok'arin k'ara dilmiyar dani....
A mota ya d'aukeni muka tafi, ko a hanya sai wani kyarma yake yana k'ok'arin kai hannunsa cikin rigata, kallonshi nayi tare da cewa saurin me kakeyi haka ne wai ? Ban bari ya bani amsa ba naci gaba da cewa ko da kayi tunanin yau zaka sameni ? Yace a , a nace tou kasa ma ranka natsuwa har muje inda zamu baje kolin iskancin namu muci karenmu babu babbaka babu wanda yaji kuma babu wanda ya gani...
Kyah kyah kyah ya kyalkyale da dariya tare da cewa gaskiya ne Uwar masu gida, kunji ihu kura ta samu nama, wannan dariya itace yayi shi ya samu Sultanar banza zaije ya gurji banza a tunaninshi, baisan ni nafi shi iya iskanci ba domin dai ni naci uwarshi nasha ruwan kanwa maganin kwarnahin ciki....
Har muka iso ban sake magana ba, horn yayi mai gadi ya yaye mana get muka shige ciki, parking yayi sannan yace muje, kai jama'a kuji rashin kunya don Allah dan kwatawalci d'iyar abokinka, uhum cije lebona na k'asa nayi sannan nace masa rubutamin number wayarka don Allah a takarda, yo baki da waya ne ? Ya tambayeni cikin gatsali, murmushi nayi sannan nace aini ko a cikin kwarin k'arama ce har yanzu da sauranmu kafin mu gama nuna Baba....
Hahaha a haka ma baki nuna ba ? Nace yo dana nuna ka ganni a napep baki da dama yace tare da fara rubutamin number wayarshi, mik'omin yayi bayan ya gama, yana k'ok'arin fita nace ka sallameni kafin mu shiga mana.....
Dubu biyar ya mik'omin , ansa nayi tare da jujjuya kud'in nace ashe gara da bamu shiga ba, yo Baba banda abunka wannan ai ko kud'in fira baka biya ba, zaro ido yayi tare da cewa dubu biyar ? Ke kin raina dubu biyar ? Murmushi nayi tare da cewa tou turaren dana shafa idan akace maka kayi tukwuici ai kasan nafi k'arfin ka bani 5k , koni ai nayi kyautar dubu biyar wallahi, ka bani kud'i masu yawa idan kana bani kaji malam....
Daga gaban motarshi ya jawo wani wuri kud'i na gani kamar in zabgaga ihu saboda yawansu , saida na gani sannan ya maida ya rufe kin gansu nan kud'in da zamuyi caca ne na had'a gobe na k'ara miki ki anshi 5k in mana...
Babu gardama na ansa muka fita daga motar dukanmu muka shiga ciki, saida ya rurrufe ko ina mu kuma mukayi ma junanmu masauki saman gado..
K'ik'iy k'ik'iy ya cire riga ya cire wando, jakata na bud'e na d'auko kwalbata sannan nayo wurinshi cikin karairaya, yana k'ok'arin rungumata nayi ma shege feshin maganin sauro, babu b'ata lokaci ya tafi bacci rik'eshi nayi har yakai k'asa sannan na cire mishi gajeren wandonshi na dauki d'an iska hoto, nayi mishi kuma vidio ko ina saida na d'auka, bayan na gama na janye shi daga saman hanya, saida na lalube aljihunan shi kaf sannan na zauna gefen gado na shigar da numbershi cikin wayata, bayan na gama na ajiyeshi da lamba 2.
Makulin motar na d'auka da jakata na bud'e d'akin na fita, cikin mota na koma saida na kwashe kud'in nan kaff sannan na rufe na maida makullin kusa dashi na ajiye, fitowa nayi na tunkari hanyar fita daga gidan, dubu biyar d'in daya bani itace naba mai gadin gidan kyauta, yana ta godiya na wuce abuna ban tsaya saurarenshi ba na fice daga gidan abuna..........
20/08/2019
*JAMILA MUSA...*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 14
Saida ma na fita daga gidan nakejin wani irin bak'in ciki ya tokaremin zuciyata, wallahi dana iya mota saina taho da motar Bello, zanje gida na jira zuwan shi domin dai nasan nabar baya da k'ura babu yanda za'ayi ya barni na ci kud'in nan , murmushi nayi sannan nayi magana a bayyane cewa Allah ya kawo ka lafiya Baban kwali Baban tusa.....
Ban tsaya wasa ba haka kuma banyi gigin biyawa gidan kowa ba na yanki santa na fara neman gidan da nake kwana....
Tafiya mai zurfi nayi kafin na fito bakin titi, Allah kuma ya taimakeni ina fitowa na samu abin hawa ban wani b'ata lokaci ba, ko ciniki ban tsaya yi ba na afka nace muje.
Inda zamuje ya tambayeni, ni kuma na fad'a masa yaja muka tafi, raina fes zuciyata dunk'ule da farin ciki na isa gida, ko mai napep 1k na bashi yayi ta zabgaga min godiya tare da jawo addu'o'in samun nasara a rayuwata...
Godiya nayi masa sannan na shiga gida da sallama kamar yanda na saba bawai dan zasu amsa min ba, a , a, inayi ne dan fita hak'k'in musulinci, kai tsaye k'ofar d'akina na tsaya na ciro mukulli na bud'e na shige abuna....
Saida na fara adana kud'ina a ma'adana mai sirri sannan na fara neman abinda zanba baba uban ba'u, { ciki } saida na d'ora girkin abinda zanci sannan na fita nayo alwallah dan ganawa da mahalicci na...
Bayan na fito daga bayi ne naji su Saude suna fira kuma ga dukkan alamu zance Dikko ne sukeyi, da wutsiyar ido na kalli wurin, wata bak'ar cikakkiyar buduwarce na gani tsaye, amma ban tab'a ganinta ba sai yau, kallo d'aya zakayi mata ka tabbatar tanaji da hutu domin ta huta d'in, duk inda ta fito yarinyar can d'iyar wani attajiri ne...
Fasa alwallar nayi na tashi na koma d'aki na kashe d'an gass d'ina na d'auko asawaki dan inaso inji inda labarin nasu zai tsaya, dawowa nayi na zauna ban kalli inda kowa yake ba kuma banyi ma kowa magana ba na tusa buta a gaba naci gaba da gogo asuwaki a bakina....
A ` i ce ke cewa kai amma gaskiya Hafsat baki da hankali ai da ki nemi d'an mai kud'i da asiri gara ki tafi tsirara kawai ki huta, kina ganin ubanshi banza ne ? Wannan Dikkon da kike gani tun yana ciki an gama dafashi da asiri yanda Babanshi yasha wahala kafin ya samu namiji kina ganin daya sameshi da wahala zai barshi ne yai ta yawo figifigi a duniya ba tare da an bashi dafa'i ba ? Kai wallahi kimayi hak'uri ,
Cikin muryar sakataccin "ya "ya tace no ai da ina kiranshi wani lokaci yana d'aukar wayata amma yanzu ya daina d'auka kwata kwata, da sauri na d'aga kaina na kallesu sai kuma na basar kamar ina kallon wani wuri, wato ita tana ma da number Dikko, tunani na farayi yanda wayarta zata zo hannuna na, ba ansar wayarta zaimin wahala ba yanda zan gano sunan Dikko shine wahala a wurina....
Kawai gaba d'aya tunanina ma har ya tashi daga d'aukar number, kawai harma na hango gani nan na d'auko tsiraicin Dikko na balbad'a a social media, tabbas Dikko saina had'a shagalin partyn wulak'anta mishi rayuwa.... Tunani na ya dawo ne a lokacin da naji Saudatu na cewa aiko ki dage yarinya dan nan da shekara d'aya Dikko baya rik'uwa, tunda shi dama bai dogara da kud'in gidansu ba gaskiya Dikko yana da sa'ar rayuwa idan kika auri shi kin more rayuwa domin dai cikakken namiji ne...
Banyi musu magana ba dai naci gaba da goge hak'ora na, wayau sukayi ma Hafsat suka amshi kud'i masu yawa a hannunta da sunan za'ayiwa Dikko asiri, ci gaba da tattaunawa sukayi amma hankalina baya wurin firarsu ya tafi wurin karatun halayyar Hafsat, tab'e bakina nayi a bayyane nace itama dai "yar mad'igon ce { Lesbian }
Kallona tayi nima na watsa mata mayatattun idanuwana masu sa mutum ya rikice na k'ura mata su sosai domin ina so ta yabani idan har ta shigo hannu na nice zan koya mata barikin da zata kawo min Dikko k'asan k'afaafuwana nima in rama wulak'anci da yayi min dan nayi alk'awari nima sai Dikko ya lashi k'afata kamar yanda yasa na lashi tashi...
Shegiya ta kuwa daskare ta kasa barin kallona, kyakkyawan murmushi nayi mata tare da cewa sannu ko ? Na k'arasa maganar tare da d'an wasa da idanuwana... Murmushi tamin tare da cewa ya kike ? Ban bata amsa ba naci gaba da alwallata...
Ina gamawa ban sake bi ta kansu ba nayi d'aki inajin tana ta magana amma na basar da ita, nadai juya ta ganni maza ma sun gani sun rikice ina ga mata mayun mata kuma ?
Ina shiga na kunna gas ina na kabbara sallah. Bansan yanda suka k'are ba, amma nasan tabbas saita dawo saboda taga ina da irin k'addarar da suke nema...
Bayan na gama sallah na zuba abinda zan dafa a tukunya sannan na zuba ruwa na tafi wanka, lokacin da nayi wanka na dawo har ya dahu, dan haka kashe gas ina nayi sannan na shafa mai da powder, d'aurin gaba nayi sannan na zuba abinci na naci gaba daci....
Bayan na gama duk abinda nake na kunna kallo, sannan na saka kayan bacci na koma saman katifa na kame kamar d'iyar wani shege... Kai gaskiya inajin dad'in wannan rayuwa tawa, saida na kwanta sannan na bud'e data ta, lamba d'aya na gano bayan na ganoshi na tura mishi vidion dana d'auko , tare dayin voice note na tura mishi. Ina turawa na sauka online na kashe wayata gaba d'aya, na kashe kallo na rufe d'akina nayi kwanciyata.......
Tashin hankali shine kalmar da Alhaji ya fad'a a lokacin da yaga vidion dana tura mishi, wata irin gagarumar zufa ta yayyafo mishi a lokacin da ya saurari voice note ina, tashi yayi tsaye cikin tsananin tashin hankali ya rasa gane a wace rayuwar yake rayuwar mutuwa ce ko ta duniya ?
A gefe kuma wayarshi ce take ta kwarara ihu, lambar mai gida Dikko ce keta tsalle babu k'ak'k'autawa amma Alhaji yau kam bata Dikko yake ba, saida kiran ya tsinke sannan Alhaji ya sake kunna maganar Sultana yana sauraro, ga abinda take cewa....
_Ina mai farin cikin sanar dakai wannan mummunan labari, d'abi'a na ne yin albishir da farin ciki yayin fad'ar abu mai munin gaske, kuma nakanyi farin ciki yayin fad'ar abun farin ciki, wannan vidion dai dani dakai ne a ciki kuma kaga irin bad'alancin da muke aikatawa a ciki, nidai banajin komai idan wani ya gani domin ni iyayena tuni sun sallama ma duniya ni, saboda haka ni duniya itace uwata kuma itace ubana, idan na yad'a wannan vidio banajin komai tunda biye nake da mutanen cikinta ina basu, nayi tunanin maidashi faifayin filet na sidi dan in siyar na samu kud'i , sannan kuma in watsashi a yanar giza gizo dan inyi suna, kai kuma kana da dama d'aya tak data rage maka, idan har ka bani naira miliyan d'aya nayi maka alk'awari zan goge shi sai in hak'ura basai nayi suna a duniya ba...... Idan kuma baka dasu in turawa "ya "yanka ko suna da kud'in fansar ka ! Sultana, Sultana ce yarinyar mai dogon zamani, idan kuma kace zakayi gigin sako hukuma a ciki na riga dana turama k'awata nace da taji an kamani firr zakaji su sun watsu a duniya kamar saukar tsuntsaye. Ka huta lafiya habibinah muah_ 💋
Goge zufa Alhaji yayi tare da cewa Allah ka tsinewa yarinyar nan albarka, shegiya tsinanniya ubanta da uwarta basuyi addu'ar kwanciyar aure ba yayin da zasu kwanta Allah ya basu cikin d'ebabbar albarkar yarinyar nan, a daidai wannan lokacin kiran Dikko ya sake shigowa.
Jiki a sanyaye Alhaji ya kalli wayar tare da cewa mai gida kayi hak'uri wannan abun kunya ina za'a dashi na watsu cikin duniya ina zina, abun bak'in ciki da d'iyar da nayi d'iya da ita, garin ciye ciye na har naje na ciwo ma kaina bala'e, kila sai ta k'arar da arzik'ina, kuma tace idan na fad'awa hukuma taba k'awarta vidion zata yad'ashi wannan shine ciwo ya riga ajali zuwa...
Kuka Alhaji yayi tayi tare mitar ya shiga 3 ya bani ya lalace, wannan labarin abun kunyar waye ma zai fad'a mawa bare kuma yasa ran zai samu wata sahihiyar shawara, kai ya bani ya bani ya bani........😰🙆ðŸ»â€â™‚ðŸ˜, a daren nan Alhaji baiyi bacci ba kuma baibi kiran Dikko ba, wayar Sultana kuma ya kirata yafi so adadin yawan dutsinan da ake jifar shedan dasu amma maganar dai d'aya ce cewa a kashe.......
Da safe , tunda nayi sallar asuba na koma bacci, can cikin bacci naji ana dukan k'ofar d'akina, addu'ar tashi daga bacci d'auke a bakina bayan na gama nace waye ? Na tambaya cikin muryar bacci tare dakai idona saman agogon dake lik'e a saman bangon d'akina k'arfe 10:36am, cikin muryar murna Nana tace "yan sanda aka d'auko miki Sultana....
Murmushi nayi tare da jawo wayata na kunna sannan nace ma Nana da Allah kije kice waye ya d'aukomin "yan sanda ? Cikin farin ciki ta koma zaure sannan ta tambayi d'an sanda waye yake k'arata ?
Fad'a mata yayi tayo cikin gida da har yanzu tanajin dad'in k'arata da akayi, a bakin k'ofar d'aki ta tsaya sannan tace wai abokin Babanki Bello, jinjina kaina nayi tare da cewa tou ina fitowa....
Data na bud'e na nemo lamba 2, hotunan dana d'auke shi jiya na tura mishi tare da yin voice note na antaya ma banza, ina gamawa na kashe wayata, saida nayi wanka naci gayuna na watsa turare na d'auku iyakar yanda hankali baya tunani duk wanda ya ganni saina burgeshi, fitowa nayi banma kowa magana ba na tunkari zaure, dan zuwa wurin hukuma a yanayin talauci yana jawo ma mutum raini....
A k'ofar gida na samu d'an sandan nan ya gama shak'e b'acin rai daga gani yana jira muje can yaci uwata, a yangance na fito cikin aji na kalleshi tare da cewa "yar labai barka da aiki......
'Dan sakin fuska yayi tare da cewa yawwa, gaishe shi nayi tare da ce masa nice Sultana, kallona yayi sama da k'asa sannan yace tou hajiya muna gayyatarki zuwa ofishinmu ai anyi miki bayanin mai k'ararki ko ? murmushi nayi tare da cewa babu damuwa muje amma Allah yasa ba'a cikin motar "yan sanda zaka d'aukeni ba, murmushi yayi tare da cewa ai hajiya napep zamu shiga, ajiyar zuciya nayi cikin sigar jan hankali sannan nace tou ai har naji natsuwa.
Napep muka hau muka nufi c p s , kuma nice na biya kud'in 1k ne na bayar kuma daya anso canji nace ya rik'e yasha ruwa, tunda muka fita a napep gaba d'aya wurin saida hankalin kowa ya dawo kaina, na farko dai ga wanka ga gayu ga k'amshi uwa uba kyau Allah yayi min kyawun da mutum baya gajiya da kallona, ga gashina na tik'ashi nayi mishi wani irin parking irin na wayayyin mata, baka isa ka rainani ba ko waye kai domin sitirar dana saka ita kad'ai ta isa ka gane ni ba sa'ar wasan yaro bace ba.....
Ofishin d c o muka nufa, a ciki na samu Bello zaune tare dashi da wasu abokan Babana, sallama nayi sannan na gaishesu dukansu cikin kyakkyawan yanayi, bayan mun gaisa nima na samu wuri na kame kamar yanda naga kowa yayi.....
Kallona d c o yayi bayan ya gama karanta wata takarda dake gabanshi sannan yace Maryam miya had'aki da Bello ne ? Murmushi nayi tare da gyara zamana nace ranka ya dad'e ai Baba Bello abokin kasuwanci ne, halak'a ta mutunci ne a tsakani na dashi bayan wannan babu komai....
D C O yace tou jiya ina kika had'u da Bello ne ? Ranka ya dad'e majalissar su naje gaishe su, bayan mun gaisa kuma ya tambayeni nayi aure nace masa A , a, yace yanzu ina nake zama ? Nace masa ina zama a tsohuwar anguwarmu daya sani, ya tambayeni ko ina kasuwanci ne ? Nace masa Eh yace me nake siyarwa ranka ya dade nace masa karuwanci nakeyi, tsakanin mai saye da mai siyarwa ai babu fushi anan muka daidai suka d'aukeni muka tafi wani gida, nuna yawan duka abokan Babana nayi sannan naci gaba da cewa ranka ya dad'e dukansu nan babu wanda baiyi ba kuma duk saida suka k'ara zagayawa "yar labai, kuma gasu nan ka tambayesu idan nayi musu k'arya. Kuma cikon kud'in ma har yanzu basu bani ba..
Kowansu zaro ido yayi tare da dafa k'irji cikin yanayin mamaki yace ke mune mukayi iskanci dake ? 'Daure fuskata nayi kamar gaske nace aini banajin kunya tunda dai banji tsoron Allah ba nayi zina wallahi banajin kunya gaban kowa in fad'a nayi, kunyi mana ko k'arya zan muku ne ? Lokacin da bakuyi ba nace kunyi ?
Gaba d'aya wurin hayaniya ta tashi har bakajin bakin wani, d c o ya dakatar dasu tare da cewa suyi mishi shiru, bayan kowa yayi shiru ya kalleni sannan yace ke Sultana Bello yana tuhumarki kud'in shi da kika d'auka. Cikin natsuwa nace wasu iri kud'i kuma ranka ya dad'e ?
Bayani d c o yaimin kamar yanda na sani, jinjina kai nayi tare da cewa idan sun gama k'arata nima zanyi k'ararsu saboda b'atamin suna da sukayi, ranka ya dad'e a gaban idon waye na d'auka kud'in ne ? Nifa bana sata amma ina neman maza gaskiya, duk abinda nakeyi bana jin kunyar asan inayi domin dai duk sana'a sunanta sana'a, idan ma na d'auka aka tambayeni idan nasan na sata kawai zan dawo musu da kayansu in basu hak'uri tunda karuwanci da nakeyi ai ban b'oye ba na fad'a tunda ba abun kunya bane....
Tambayar Bello D C O yayi ko yana da wata sheda ne ? Baida ita tunda an tambayi mai gadi yace shidai bai ganni cikin mota ba, duk iyakar binciken da akayi dan asamu wata sheda babu ita, dan haka aka rubuta takarda cewa an janye k'ara, bayan an gama rubutu aka bani na saka hannu da larabci nayi sigining ina, an mik'e za'a tafi nace ma d c o naga fa sunamin wani kallon hadarin kaji sufa fita ido na, d c o yace ai duk an rubuta, nace to ranka ya dad'e cikon kud'ina kuma sai yaushe zasu bani ?
Hak'uri d c o ya bani tare da nunamin tunda anyi masa sata inyi hak'uri inma barshi da ramuwar biyan kud'in mutane, babu kunya ba komai nace kenan ni yanzu ranka ya dad'e sunci banza ? Duk wanda ke cikin office in saida ya kalloni, nace ranka ya dad'e kafa duba lamarin nan gaskiya ni ba'amin adalci ba, shiru wurin yayi wutar kowa ta d'auke, murmushi nayi tunda basu da amsa nace nawa ake yankar sammaci ? Sammaci ma ake cewa abin ko miye ?
A kotu ake yankar sammaci d c o ya bani amsa tare da fad'amin abinda ake kiran nasu da turanci, oho dai da yake kan baya ganewa kasa maimaitawa nayi saidai kawai nace nawa ne ? Kud'in aka fad'amin na bud'e jakata na bada sannan nacewa d c o ga wanda nake k'ara nan Bello ina tuhumarshi akan b'atar mahaifina daya tafi babu wanda yasan ina yaje..........
21/08/2019
*JAMILA MUSA...*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 15
*_Had'inkai group ina tare daku aminan albarka, Allah yabar so da kauna ubangiji ya k'ara yadda da aminci, HALIMATU SADIYYA {{ Leema }} HABIBA IDRIS {{ Hubbie }} HAUWA'U USMAN {{ Smasher }} MAIMUNA O . G {{ Aunty Munari.... }} muna tare_*
*_Mrs Abdul-aziz ina godiya sosai da dogon sharhi kuma ngode sosai page 14 na baki shi kyauta...._*
Lahaula walakuwata illah billah, kiji tsoron Allah ke uwar masu gida a ina na b'atar da mahaifinki ? Sharri zaki min ? Kiji tsoron Allah in babu nan akwai ranar hisabi duk wanda yaci zalin wani daidai da kwayar zarra ubangiji bazai barshi ba, ki daina ganin kin samu dama ta tak'in lokaci yasa ki manta da rayuwar gaba, karki biyewa zuciya ki kafa abinda zaisa kiyi nadama wata rana.....
Gaba d'aya jikina yayi sanyi tsoron Allah ya kamani nasan k'azafi da sharri ba abu ne mai kyau ba, kuma addini na bai koyar dani haka ba, amma d'an kamewa na sakeyi sannan nace ni rayuwar dad'i baza ta tab'a zama takaitacciya a wurina ba, jin dad'i na d'aura insha Allah daga nan har zuwa ranar da numfashi na zai k'are, ina Babana yake wai ina ka kaishi ne............?
Cikin nadama Bello yace na rantse da ubangiji daya bani aron lumfashi ya bani aron lafiya nake ganinki nake kuma saurarenki ya bani hankali da tunani idan nasan inda mahaifinki yake Allah ya tsinemin albarka. Wallahi Uwar masu gida bansan inda ya tafi ba na rantse miki da girman Allah. Tausayi ya bani yana rantsuwar yana wani kwantar dakai kamar an ritse macen da tayi cikin shege ta haihu kuma ta kashe d'an....
Kallon D C O nayi tare da cewa "yar labai shikenan tunda yayi rantsuwa baiyi ba kawai na janye, zan iya tafiya ? Na tambayi D C O, cewa yayi na zauna zamuyi magana, zama nayi su kuma su Bello aka sallamesu suka tafi ni kuma naci kud'in banza Ehe....
Ta wutsiyar idona na kalli d c o bayan fitarsu Bello domin ina son na gano tashi manufar a kaina, murmushi nayi bayan na gama fahimtar shi, a bayyane nace lamba 3 tazo kenan, ajiyar zuciya ya sauke tare da tattaro duka hankalin shi wurina yace ranki ya dad'e ya hak'uri da jama' a ? Kallonshi nayi ba tare da nayi magana ba domin wallahi tsarin bakinshi kwata kwata bai burgeni ba. Amma ba komai zan hak'ura nayi maleji dashi haka nan saboda idan na taro watan aug zai gina min gada nabi na wuce ba tare dana sha k'ashin ruwa ba....
Wayan cewa nayi tare da gyara zama na nace Allah dai yasa aiki zaka d'aukeni mai girma d c o, murmushi yayi tare da komawa ya kwanta saman kujerarshi irin masu juyawa d'in nan, sannan yace wai gida zan saukeki idan ba matsala, d'an yamutsa baki nayi tare da cewa na gode amma ni ba gida zanje ba...
Ina zakije haka da rana ? 'Daure fuska nayi dan ya fara cika min ciki nace wurin aiki zanje, wane irin aiki ? Tsoki nayi tare da cewa kai komai sai anyi maka b'aro b'aro kake ganewa ko ? Tou abokin lalata zanje nema.....
Murmushi yayi tare da cewa ke bakya gajiya ? Cikin wuta wuta nace ka tab'a ganin inda mutum yake rayuwa babu abinci ? Yace a , a, nace tou ni da kud'i da karuwanci sune abokan rayuwata, domin sai nayi nake samu sannan naci nasha na kuma d'aura har in fito na burge abokan harka , idan kuma kaima d'an hannu ne karka wani cuci kanka kawai kayi magana idan kajira sai an maka tayaki tou fa lallai zaka kwana da yunwa, amma kayi hak'uri da tambayar da zan maka tsakanin ka da Allah nawa ne albashin ka...... ?
Kallona yayi tare da cewa hajiya maryam kenan , miya shafi albashi da harkar bariki ne ? Bai shafa ba amma ni ina duba nasabar namiji da cancantar shi kafin wata sahihiyar mu'amula ta shiga tsakani na dashi, dan duk wanda ya jawo maganar aure a rayuwarshi tabbas ya tara abun hidima, bata yuwuwa na biye maka ka k'ok'ar dani ba tare da ka sake bani kud'in da zan sabon fenti ba, dan kai kanka da ban d'aukar maka ido ba duk yanda nake barikin baza ka taya ba,
Kallon agogon dake d'aure a tsintsinyar hannu na nayi tare da cewa zama wuri d'aya tsautsayi inji kifi, malam d c o zan wuce ka rubutamin number ka a jikin takarda idan ayyuka sukamin sauk'i akwai dawowa......
Babu musu kuma ba tunanin komai ya d'auki biro da takarda ya gwagwad'amin number wayarshi, ansa nayi tare da mik'ewa tsaye sannan nace sai ka jini, baki bari mu tafi in ajiye ki ? Ya tambayeni, juyawa nayi na fara tafiya tare da cewa ban hawa mota sai napep a daidai lokacin dana fice daga ofishin....
Ina fitowa wuri na samu na tsaya, wayata na fiddo nayi saving in no d c o da lamba 3 , sannan na kira wayar Alhaji, babu b'ata lokaci ya d'auka tare da cewa ranki ya dad'e tun jiya inata kiran ki wayarki a kashe ko yau da safe ma na kira a rufe.... Ban bashi amsa ba nace kawomin kud'in yanzu nan ina nan c p s ina jiranka kuma karka b'atamin lokaci, ina fad'a na kashe wayata......
Lambar Bello na kira amma bai d'auka ba, daga kira d'aya nima ban sake kira ba, domin dai nasan idan yaga abunda na tura mishi shi da kanshi zai nemeni, k'ok'arin maida wayata nake cikin jikka naji ana cewa shegiya k'awata kece kika koma wata hajiya haka ? Da sauri na d'ago kaina domin jin muryar Amisty da nayi...
Cikin farin ciki muka rungume juna, bayan gaisuwa sai kuma muka shiga firar duniya, yayin da nake tambayarta wane ci baya ta samu na bariki naga har yanzu bata fara hawa mota ba, ajiyar zuciya Amisty ta sauke tare da cewa kinsan mazan babu kud'i hannunsu kullum tsuwwa da kukan babu......
'Daure fuska nayi tare da cewa waye ya fad'a miki ana hawan jirgin sama bashi ne ? Ai filin jirgi ma baka shigarshi dole sai kana da tikitin tafiya, haka nan kike basu suna hayewa basu baki kud'in mai, tou ina uwar d'akin taki ne ko bata nan bata fad'a miki illar maza ba ? Haba Amisty idan baki ridowa da yawa wallahi bariki kasheki zatayi, niko kin ganni nan ni zanyi gwanjo bariki kafin ta wurgar dani gefen titi, kinsan bariki bata da tabbas d'auka da ajiyewa gareta, ni zan kashe bariki bazan yadda ta kashe ni ba, zanyi amfani da talata ta kafin laraba ta, ta riskeni, wannan uwar d'aki taki k'atuwar jahila ce batayi karatun komai ba haka nan ta tara yawan dalibai, har yanzu kuna da dama ki nemi canji makaranta ki dawo makaranta ta zan baki ilimi akan namiji, kud'i kike so ko suna ......?
Horn Alhaji yayi da mota wanda tun d'azu yakeyi amma magana ta hana na saurareshi, juyawa nayi tare da nuna mishi da hannu ina zuwa, ni kuma naci gaba da magana da Amisty, wata matace ta fito daga ciki tayo wurinmu kuma ga dukkan alama tare suke da Amisty, gaisawa muka yi yayin da Amisty ta fara tambayarta ya aka k'are, basu bani labari ba suna ta maganar ne cikin munafinci, ni na fahimta suna magana ne kamar tayi ciki..
Datsar maganar nayi da cewa keko ya akayi kikayi cikin shege ? Gaki a fuska kamar wayayya taya akayi haka ta faru ? Ita kuma a tunaninta Amisty ta fad'amin dan haka tace kin gane ni bawai cikin bane matsala a, a mijina yau watanshi bakwai baya nan kuma ga ciki wata hud'u, kuma nayi a zubar da cikin shi wanda yayi cikin yace wallahi bazai yadda ba saboda bai tab'a haihu ba, idan wannan abu ya fito ai kinsan akwai matsala.....
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un na fad'a tare da cewa ke matar aure kike zina ? Hasbinallahu wa ni'imal wakim, amma kinyi k'atuwar asara, kallon Amisty nayi tare da cewa zance zaune ba na tsaye bane idan kuna neman taimako ku sameni gida, ina nan tsohuwar anguwarmu idan kika shigo ki tambayi gidan da nake haya za'a kawoki, ina fad'in haka nayi wurin motar alhaji ina zuwa na kama na bud'e na shige nace muje...
Har muka isa gida banyi ma Alhaji magana ba domin ni yau naga macen da tafini kafirci kina k'ark'ashin bautar aure amma kina aikata sab'o, wannan wai wane irin zamani ne muke ciki lallai ya kamata nasan ita kuma wane rud'un duniyar ne yaja mata neman mazan waje ga nata mijin da yake hak'k'inta amma ta tsallake shi ta tafi wurin na wasu , gaba d'aya jikina yayi sanyi kuma na dawo daga rakiyar duniya....
Ansar jakar da Alhaji ya zubomin kud'i nayi tare da direwa daga motar, zaiyi min magana nace mishi muyi waya kawai nayi gaba abu na, lokacin dana shiga gida bana ko ganin gabana saboda bak'in ciki da kishin aure, d'akina na bud'e na shiga, saida na adana kud'ina sannan naje nayo alwalla nayi sallah azahar, yinin ranar haka na yini sukuku kamar wata mara lafiya, koda nayi sallah isha'i kwanciyata nayi , duk yau banda ruwan shayi babu abinda ke cikin cikina, haka na kwanta da tunani iri iri, ko bacci nayi na farka abun yakan fad'omin a rai har gari ya waye da tunanin matar nan a zuciyata..
Da safe bayan nayi kalaci na gyara d'akina naje nayi wanka na shirya cikin doguwar riga ta atamfa da tasha d'inki buba, hula mai raga { net } na saka kaina na fice tsakar gidan....
Kujera na sa a k'ofar d'akina na zauna tunda fitowa wajen ya zamar min dole, kallon inda Karima take nayi sannan na maida kallo na wurin Saude dake zaune saman turmi, babu ko breziya jikinta kuma babu kaya sai siket ondie da taja saman kirjinta, amma komai na halittar ta babu abinda ya b'oye duk a bayyane yake.....
'Dauke idona nayi gefe na kallo inda Nana take kwance A ` i tana durk'ushe ta duk'a samanta sosai suna k'ushin k'ushin, jinjina kaina nayi sannan na sake kai idona wurin Saude nace ke Saude wai da Allah in tambaye ki ?
Murmushi tayi tare da cewa tambayarni kanki tsaye, b'ata rai nayi sosai sannan nace nan gidan ubanki ne wai da zaki zo ki rik'a zama mana tsirara dan baki da kunya ?
Gaba d'ayansu dariya sukayi ,sannan Saude tace tou ke mai tambayar gidan ubanki ne ? Ni nan ba gidan ubana bane amma ya zama na ubana tunda na biya kud'in haya, d'aki d'aya na kama amma ina da hurumin da zan sauke ubana a ciki, ke ko fa ? Nana ta anshi maganar da cewa yanda kike tak'amar kin kama haya muma kamawa mukayi kuma muma muna da hurumin da zamu kawo mutanen da muke so su zauna tare damu, kedai kawai kice kina so ayi dake.
'Dan gajeran murmushi nayi tare da cewa duk wanda yaci naman arne tabbas zai iya cin mushen alade , banda abinki miya had'a makaho da ganin wawan zama ? Ni bana iya cin naman jaki amma idan na samu doki zanci duk da an yanka shi nasan wata rana zanyi hazaka, ko banyi gudu ba tabbas nasan zanyi tafiya, magana ce na fad'a miki a jimlace idan kina da ilimi sai ki warwareta banzanye da ku masu wahalallen bariki.....
Gaba d'aya wutar kowa d'aukewa tayi sukayi shiru babu wanda tace komai, murmushi nayi tare da cewa ba'a bariki dole saida ado kuje ku ibi ruwa kuyi wanka kusa toka ku wanke baki ko ya rage k'annin koko, daga haka ban sake ma kowa magana ba kuma suma babu wanda ya sake cewa komai,
Bayan Alhaji ya bani kud'i ya dad'e k'ofar gidanmu ya kasa tafiya, hankalinshi a tashe saboda yaso yayi magana dani na goge vidion nan kuma yaji ina na dosa ? Amma samsam ban saurare shi ba, kuma yasan lallai saina sake tambayarshi wasu kud'in tunda akwai vidio a hannuna ban goge ba,
Rasa yanda zaiyi yayi zuciyarsa ta yanke mishi kawai ya fad'a wa Dikko komai yasan babu mai iya magani na saishi amma fa a nashi haukar , d'aga waya yayi ya kira Dikko kuma har zuwa wannan lokacin yana k'ofar gidanmu bai tafi ba.
Bayan Dikko ya d'auki waya Alhaji ya gaishe shi cikin girmamawa kamar yanda ya saba, Dikko ya amsa shima cikin mutuntawa, dan a haife Alhaji ya haifi Dikko amma igiyar naira tasa yana k'ark'ashin Dikko kuma k'asan k'asa ma, dan ubangidan Alhaji na ainahi shima yaron Dikko ne na biyu, tou abinda yasa Alhaji yake kiran Dikko kai tsaye saboda yanajin dad'in yadda yake kularmishi da dokunan shi, shi yasa shi Dikko da kanshi ma ya anshi number Alhaji ko wata matsala ta taso ga dokunan shi, dan dama ubangidan nashi na farko kafin yasan Dikko wurin kula da dokuna ajiye shi Alhajin....
Alhaji yace mai gida kayi hak'uri don girman Allah wallahi jiya daka kirani ina cikin yanayin da bazan iya magana ba, cikin jimami Dikko yace meya faru haka ? Wato ranka ya dad'e ina cikin tashin hankalin dana zab'i mutuwa ma da rayuwa, salati Dikko yayi tare dayin murmushi domin shi yaji mugunta, sannan yace Alhaji duk dad'in duniyar wato tai maka d'aci ko ? Alhaji yace Eh wallahi ranka ya dad'e, Dikko yace tou Allah ya kyauta...
Da sauri Alhaji ya fara bayani wa Dikko dan yasan daga Allah ya kyauta kawai zai kashe wayarshi ne yasan baya doguwar waya, ranka ya dad'e wato wallahi wata yarinya ce muka d'an keb'e da ita, tou wallahi bansan yarinyar nan ta shirya sharri ba, ashe duk abinda mukayi ranka ya dad'e tana d'auka cikin waya ban sani ba, tou ta rik'e vidion sai wahalar dani takeyi tana ansar kud'ad'ena, yauma na bata kud'i kuma a police station nakai mata kud'in inaji wani ne ya d'aure mata gindi take iskanci a garin nan....
Murmushin mugunta Dikko yayi tare dayin kamar bai gane ba, yace wane irin vidio ne ? Gyara zama Alhaji yayi tare da goge zufa yace wato ranka ya dad'e harka daice irin wadda muka saba, Dikko yace wadda ka saba dai , wato ka samo daidai dakai ko ? Tou turomin vidion in gani ya fad'i maganar cikin sigar zaulaya, Alhaji yace ranka ya dad'e vidion fa irin na kafirawan nan ne masu d'aukar tsiraicinsu suna yayad'awa a duniya.......
Dikko yace tou banda abunka kace taje ta yad'a ba hada ita a vidion ba ? Alhaji yace ranka ya dad'e ina za'ayi wannan abun kunya tsiraicina a yanar giza gizo cewa tayi fa har "ya "yana zata tura su gani, Dikko ya gaggab'e da dariyar mugunta tare da kashe wayarshi, irin wannan abun Dikko kadai yake ma dariya a duniya, duk abin burgewa ko na nishad'i Dikko baya mishi dariya kuma baya murmushi idan kaga murmushin shi ko dariya yaji ko yaga k'eta, amma kai kana iya ganin abinda zai baka tausayi kayi kuka wallahi Dikko sai yayi mishi dariya saboda tsabagen shi cikakken mugune....
Cikin sanyin jiki Alhaji yaja motarshi ya tafi, Dikko kuwa saida yasha dariyarshi ya gaji sannan ya sake kiran Alhaji, bayan ya d'auka yace tou waikai kawai sai tayi maka vidio ? Alhaji yace Eh ranka ya dad'e Dikko ya sake shek'ewa da dariya sannan yace kai amma wallahi yarinyar nan tantiriya ce ta fad'a a duniya,
Dikko yace tou yanzu me kake so nayi maka ne ? Alhaji yace ranka ya dad'e so nake kayi min maganinta, dariya Dikko yayi sannan yace nima so kake ta d'aukeni ? Cikin biyayya Alhaji yace haba ranka ya dad'e kada Allah ya had'aka shegiyar yarinyar nan.....
Dikko yace aini ko ta had'u dani bata da yadda zatayi dani, nidai bana neman mata kuma bana sabgarsu bana shiga huruminsu gudun raini, kayi hak'uri insha Allah zanzo katsina jibi idan Allah ya kaimu zata goge vidion dan wahala, ranka ya dad'e ai tace ta turawa k'awarta ne, Dikko yace k'arya take kadai jira zuwana .....
Godiya Alhaji yayi sannan sukayi sallama da Dikko,
Murmushi nayi a daidai wannan lokacin sannan nace duk mai niyar yin magani na nice zanyi maganin d'an banza, zomon bana shike maganin karen bana, maganin d'an iska kuma karen maguzawa, dani dakai dashi mu zuba duk wanda ya fasa yaci k'aniyarshi.......
Sallamar Hafsa ce da wasu zugar tantiran mata, a ciki kuwa harda Amisty, kila sunzo ne suci min uwa tunda nace uwar d'akinsu k'atuwar jahila ce, oho koma dai miye su shigo ina jiran isowarsu wurina inji su kuma da wace suka zo................???
22/08/2019
Taku a kullum mai san farin cikinku wato .
*MEELAT MUSA*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 16
*_Bandai ji komai ba , 71 , 29 babu damuwa zamu rama muma..._*
_____```^^=°°--- Basarwa nayi tare da d'auke fuska ta daga dubansu, mutum dai bai isa yazo har gidana ya dakeni ba, kallon banza ko maganar banza mutum yamin wadda batamin ba wallahi ina da Lamba3 d c o zaici k'aniyar mata....
A daidai lokacin da suka iso gabana maganar zuci ya k'are, Amisty ce tace wurinki fa muka zo kina yi kamar baki ganmu ba, saida na gama kallesu tsaf sannan nace sannunku da zuwa tare da mik'ewa zan shiga d'aki dan d'auko musu tabarma...
Gaba d'ayansu rufa min baya sukayi suma suna k'ok'arin shigamin d'aki, ja nayi na tsaya tare da tambayarsu ina zasu je ? Amisty tace ciki zamu shiga ? Murmushi nayi tare da cewa kuyi hak'uri ku jirani ni bana kai mata cikin d'akina...
Hafsa zatayi magana Amisty ta dakatar da ita, kallonsu nayi tare da cewa barta ta fad'i cikinta, Amisty tace barta kawai d'auko mana kedai, munafikin murmushi nayi tare da juyawa na shige cikin É—aki, domin ita Amisty tasan wace ce ni, tabarma na d'auko nazo na shimfiÉ—awa banza nace su zauna...
Dukansu zama sukayi lokaci ɗaya, su A ` i da Saude Nana da Karima duk suka taso suka dawo ƙofar ɗakina, nima zama nayi tare da cewa meke tafe daku ne ? Na ƙarasa maganar tare da kauda kaina gefe ɗaya....
Amisty tace Sultana ke kikace mu sameki gida ! Kallonta nayi tare da cewa sai akayi ya ya ? Amisty tace ai shine muka zo ! Kallon tantiran mata nayi sannan na maida hankalina wurin Amisty nace da Allah daga yau idan zaki zo wurina kidai min kwashe kwashe , da sauri Amisty ta kalleni sannan tace haba Sultana mi yasa haka kuma ?
Kai tsaye nace kinsan bana san munafirci kuma ban tare da munafikai, waccan bak'ar yarinyar da kika gani na nuna Hafsa budurwar Dikko sannan naci gaba da cewa gaskiya aminci take da mak'iya na saidai ta zab'a ni take so ko su A ` i , murmushi Hafsa tayi tare da kallona sosai ni kuma na d'an gyara zama yanda zan d'aukar mata hankali sosai, saboda ina so na rabata tarayya dasu A ` i idan ina tare da Hafsa suma suna tare da ita riƙa zugamin ita zasuyi har su hanani na cimma buruni tunda na lura ita Hafsa doluwa ce kuɗinne kawai ba wayau sai tsabar neman matan bala'e. Kwazzaba tasa har bata iya tantance kifi bata gane kwad'o,
Cikin ruÉ—ewa Hafsa ta fara magana irin ta "ya "yan masu kuÉ—i, kin gane Sultana nifa ba abokaina bane kawai gaisawa mukeyi sai kuma wata huÉ—É—a tamu data haÉ—amu amma ba komai tsakaninmu gaskiya,
Ɗaure rai nayi tare da cewa nifa ba abinda ya haɗaku nake so na sani ba cewa nayi kawai ki faɗa ni zakiyi abokiya dani kibar su A ` i ko kuwa su A ` i kika zaɓa, Hafsa tace haba aike tawa ce kuma ina tare dake, murmushi nayi tare da cewa magana ta ƙare mata tacewa mijinta shege...
A ` i zatayi magana nace dakata malama ta bakin gulbi, ki taka sannu da lafiya kafin insa a ɓatarmin dake cikin garin nan, nuna yawan su Amisty nayi tare da cewa nan da kika gansu duk dalibai na ne, zan fara basu karatu daga jibi idan Allah ya kaimu, na kafa ƙungiya ta mai take *kwarata* duk wacce kika gani anan mabuƙaciya ce, zan haɗa ne zanba mace namiji idan an sallami mace zata fiddani, zan haɗa mata da mata amma a tafiyata ban tafiya da taron banza, sabbin ɗalibai ku na ɗaukeku kyauta basai kunyi register ba, amma daga ba yanzu ba duk wacce zata shigo cikinmu saita ajiye dubu talatin kuɗin register haƙƙina neman maza da mata masu abun hannunsu....
Miƙa hannuna nayi tare da cewa duk wanda yake tare dani ya ɗora hannunsa a saman nawa, kowa ɗora hannunshi yayi harsu Nana matan aure ba'a barsu a baya ba, ku ɗauki alƙawari babu cin amana , gaba ɗaya suka amsa munyi alƙawari bazamu ci amana ba, nace kuyi alƙawari zaku zama ɗalibai masu biyayya, munyi alƙawari zamu zama ɗalibai masu biyya nace idan kun samu ina nan ko bana nan zaku ajiyemin nawa kason, shima suka maimaita, sannan nayi addu'a tare da neman Allah yasa albarka a cikin wannan ƙungiya tamu mai albarka wanda nayi ma laƙabi da *KWARATA* saboda dukanmu lalatacci ne ,
Bayan an gama nace tou kowa ya tashi ya tafi nima zan fita inda fuskar jama'a take na samu gida na siya idan kuɗina yakai, idan basu kai ba kuma zamu kama shago, wannan shago zai zama nan ne kowa zataci gayu da safe taje ta zauna, yayin da zamu kafa ƙaton allonmu ya kalli al'umma, za'a rubuta a gaban shagon ko gidan tambarin *KWARATA* idan ma baka iya ba kazo za'a koya maka.
Zamu rubuta a jikin takarda mukai kuma a buga mana su da yawa, ni zanbi manya ofisoshi da kasuwa da kuma kamfaninika da inda "yan siyasa ke zama saina zabo mana manyan alhazawa sai mu raba musu, duk wanda ya gani ya karanta dama ga number wayata nan a jiki, ku kuma kuna shago kunsha wanka kunayi kuna ƙara powder da jagira ina binku ina muku wanka da turare, da mutum yace zaizo zance ya iso akawai kaya a ƙasa, yana shigowa ya ganku wayyo shikenan labari zai canja salo, ni kuma ina da wata dabara ɗaya amma bazan faɗa muku ba saboda karuwa bata da amana,
Nana tace tou mu da muke da aure fa ? Kallon ta nayi ƙasa da sama sannan nace duk iskanci da kukeyi keda A ` i sai yanzu kika tuna Allah ? Tsoki nayi tare da cewa tunda na lura kema kinasan duniyar sai in ɗaukeki aiki ki riƙa sharewa kina gogewa, ke kuma Karima idan mijinki ya barki zan zuba miki kayan mata da maza na gyaran harka duk wata zan baki dubu biyar ko anyi ciniki ko ba'ayi ba, amma idan mijinki ya barki fa.
Tun kafin in rufe bakina Karima tace koma bai barni sai naje wallahi, dubu biyar fa ? Ina nan kullum zaune gida naira hamsin ma wahala take min , kuma Sultana ki rubuta a jikin takarda duk wanda zaizo ya taho da kaza kinga idan anci an rage ai muma zamu maida miyanmu.....
Kallon Karima nayi sannan nace kazar Lbura'uba, an faɗa miki *kwartancin* wahala zamuyi ? Kudai kuyi ta addu'a a samu bakin titi, addu'a sukayi tayi Allah ya taimaka ya bada sa'a, daga ƙarshe dai kowa ya kama gabanshi, nima na kulle ɗakina na fantsa ma cikin gari...
Ina bakin titi tsaye naji wayata tana ta kururuwa dan haka dole na dakata, fiddota nayi na duba dan ganin mai kirana, Lamba 2 wato Bello kenan, É—auka nayi tare dayin sallama, bayan ya ansa na gaishe shi, bai ansa gaisuwar ba yace ke Uwar masu gida hotuna na gani ?
Amma ai ka gane ko waye a jikin hotunan ko ? Eh nine , tou kuÉ—i zaka bani naira budu É—ari biyar nan da gobe idan Allah ya kaimu idan kuma kace babu sai ina watsa su duniya kowa ya kalla kyauta.... ÆŠanka da matarka da abokanka duk suna kwance a saman gado zasusha kallo abunsu...
Sirikinka da surukarka zasusha kallon siriki tsirara... Tou nabarka lafiya, ina faÉ—in haka na katse kiranshi, ina duba yanayin samun mutum kafin na yanka mishi haraji, Bello baida ko sisi kuma baida wata sana'a data wuce caca, kuma caca ba kullum akeyinta ba, gashi kuma na sace kuÉ—aÉ—anshi kaff da na gani a mota ba damuwa na bane nidai kuÉ—i kawai, ina gama waya da Bello na kira lamba3 wato d c o, mai girma É—an sanda yarinyar jiya ce, Maryam Sultana Aliyu Binna, ya garin ? Haka nayi masa bayani bayan ya É—auki wayata....
Hajiya ya kike ? Lafiya qalau kana ta ina haka ne ? Yace naje ganin gida ne baby, cikin salon cuta na kwantar da murya ƙasa ƙasa nace kuma "yar laɓai maimakon ka kirani inyi rakiya ? Murmushi yayi sannan yace wallahi nima tafiyar bazata ce wife ina ce bata lafiya, tou lallai wannan kuwa da sa'a take wace ce ita, dan bansan abinda wife in take nufi ba, dana dangantata da mace saboda naji yayi magana da sunan jinsin mace ne, yace wife itace ba lafiya,
D c o yace matata nace, danshi yanda yake kallon wayewa ta ya É—auka wata shegiyar baturiya ce, danaji yace mata nace ai shine nace wannan tana da sa'a, da kaji kuma nace wace ce ita ina tambayarka amarya ne ko uwar gida ?
D c o yace ai mata ta ɗaya ce, nace tou yayi kyau yaushe zaka dawo ne ? Zan dawo amma sai ta samu sauƙi, to Allah ya sawaƙe ya bata lafiya, d c o ya amsa da amin mukayi sallama.....
Lallai duk yanda akayi wannan matar tashi tasan damarta ne, idan ta riƙe d c o sosai taya zamu samu wani abu a wurinshi ne to ? Wato ita munafika nufinta ita ɗaya zataci ? Taci gidansu bari dai d c o in ya dawo bata ƙara ganinshi dan ubanta ba rashin lafiya ba ko mutuwa tayi sai anyi jana'izarta baije ba....
Napep na hau na nufi gidan Alhaji marenin wayau na, tsoho ya tsufa amma zuciyar bata mutu ba, buɗe na samu gidan dan haka na banka kaina tsaye na shiga, babu dawakuna ko guda ɗaya duk an fitar dasu an share gidan ƙwal gwanin burgewa, sai cire yana akeyi ana wani kakkaɓe kakkaɓe get in gida sai wanke shi akeyi ana goge duk inda yayi ƙura....
Cikin masu sharar na tamabaya lafiya ko Alhaji ya tashi ne ? Yace lafiya qalau bai tashi ba ubangidan shi ne zai dawo gobe, tsoki nayi tare da cewa shine ake ta wani share share ? Yace Eh , Dikko ko ? Na tambayi yaron yace Eh ai ance ma ya iso yana Abuja ko zasuyi me ne ne ? Amma dai naji ance jirgin safe zaibi yaje kano akwai abinda zasuyi sannan zai shigo katsina....
Jinjina kai nayi sannan nace tou shi ina Alhajin ne ? Ai sun tafi kano taroshi, daga nan har kano suka tafi su taho dashi saboda tsabar basu da aikinyi ? Yaron yace ai ba rashin aikinyi bane ba hajiya duk abinda kika ga sunayi dan sun san zasu samu, Alhaji fa baya saida fari baya saida baƙi kiwon dokuna yake amma kiji irin dukiyar dake gareshi, sun san suna samu da D ---K ɗin ne shi yasa suke laƙafe dashi, da yana nan da baya nan kuɗi suke samu kamar tashin hankali...
Tou zan tafi kawai mayi waya dashi, jakata na buɗe nayi ma yaron alheri godiya yayi tayi tare da cewa Allah ya kareki ya ƙara arziƙi hajiya ubangiji yasa kifi haka Allah ya ƙara lilka darajarki ngode sosai. Ban saurareshi ba nayi waje abu na,
Gida na koma saida nayi sallah isha'e sannan na fara nazari akan Alhaji abinda zance masa kawai ya bani mota da gida sai in fita daga harkarshi, dan ni duk inda zanji ƙamshi ko labarin sunan D ---K na tsani wurin tsakani da Allah bana san Dikko na tsani rayuwarshi wallahi, amma idan har Allah yayi min cikakken arziƙi saina wulaƙanta ma Dikko rayuwa,
Wani irin baƙin ciki naji yana tasomin hawaye ya cikamin ido na abinda ya faru tsaƙanina da Dikko ya dawomin sabo fil a zuciyata, zuciya ta tace min ƙaryane baza a fita daga harkar Dikko ba sai na halakashi, kamar mai aljannu lokaci guda na burkuce nayi nayi na saita kaina amma na kasa wuƙa na ɗauko tare da kwarara wani irin ihu nace wallahi saina kashe ka........ Na ƙarasa maganar cikin kururuwa.
Duk wanda ke gidan nan babu wanda baiji ihuna ba, da gudu Nana da Karima sukayo ɗakina amma banda su A ` i saboda yau da wuri suka tafi gida. Lokacin da su Nana suka shigo duk na yanyanki wasu wurare na jikina da wuƙa, abin ya tada musu hankali dakel suka riƙeni suna tambayata waye Sultana kallon Nana nayi cikin kuka nace wallahi saina kashe shi gobe zai shigo katsina bana ko ƙaunar jin irin sunanshi a rayuwata....
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, shine abinda Dikko ya faɗa a daidai wannan lokacin tare da janye ruwan dake gabanshi, hankalin kowa yayo kanshi tare da tambayar lafiya ranka ya daɗe ? Dafa ƙirjishi yayi tare da cewa gabana ke faɗuwa babu gaira babu dalili.
Duk kusa dashi suka matsa suna mishi sannu, kallon babban yaronshi yayi sannan yace maza kiramin gida, ɗaukar waya yayi ya kiro dadyn dikko, babu ɓata lokaci dady ya ɗauka D --- K babu ko gaisuwa yace Dady lafiyanka qalau kuwa ? Murmushi Dady yayi tare da cewa mi kuwa zai sameni ? Bayan ina nan zaune cikin iyalina muna farin ciki saboda zuwanka ! Dikko yace Dady karka ɓoyemin dan Allah miye ? Dady yace tsaya ma kaji, saida ya haɗa Dikko da kowa yayi magana sannan yace kaji ko ?
Ajiyar zuciya Dikko yayi kamar wanda yasha kuka ya ƙoshi sannan yace kawai haka nan naji gabana yana faɗuwa, Dady yace saboda zaka ga ganni ne, kayi ta addu'a Allaah ya tsare kuma kayi bacci da wuri, jinjina kai Dikko yayi tare dayi ma Dady sallama suka ajiye waya....
Dakel su Nana suka lallasheni nayi shiru, Karima tace inyi ta addu'a don Allah sharrin shaiɗan ne, nace tou amma har yanzu ban daina baƙin ciki ba, saida suka tabbar hankalina ya kwanta sannan suka tafi bayan sunsha fama na faɗa musu ko waye naƙi faɗa musu...
Suna fita na rufe É—akina nayi addu'a na kwanta bacci,
Da safe kuwa misalin 12:45pm na fara gwagwaÉ—awa Alhaji kira, bawan Allah banda zufa babu abinda yake haÉ—awa, idanuwanshi sunyi jajir saboda tsabar tashin hankali duk wanda ke wurin saida Alhaji ya bashi tausayi duk da babu wanda yasan abinda yake damunshi, amma banda Dikko dakeyin kyakkyawan murmushin dake fito masa da tsananin kyawunshi, da yasan yanda yakeyin kyau idan yanayin murmushi daya dawwama yanayin fara'a, duk da ko baiyi murmushi ba yana da kyau sosai gaskiya, taunar rainin hankali yake ma cingom in bakinshi sannan yace wai har yanzu ta hanaka ka huta ne ?
Kamar Alhaji yana jira yace Eh ranka yadaÉ—e, Dikko yace bani ita, Alhaji yace ai kiran ya tsinki, É—aure fuska Dikko yayi sannan yace kirawo min ita...............
23/08/2019
*JAMILA MUSA* 🤙ðŸ»
Ina mana barka da juma'a,
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 17
_Don Allah kuyi haƙuri mu dukanmu mubi labarin nan a hankali, wannan labari na faɗa muku yanda yake, an rage wasu abubuwa ne wasu kuma an gyara su, labarin yana da yawa sosai ba'ayi komai ba yanzun muka fara wasan , kuyi haƙuri muje a hankali, ni jamila musa nake cewa asha karatu lafiya...._
Gajiya nayi da kira ba'a ɗauka ba dan haka na haƙura banyi yunƙurin sake kira ba, ina ƙoƙarin ajiye wayata kira ya shigo a cikin wayata mamaki ya kamani sosai ganin kiran Alhaji, taya zai kirani bayan ni na kirashi da kaina bai ɗauka ba ?
Haka nan naji tsikar jikina ta tashi zuciyata namin wasi wasi lallai akwai wata ƙullallah da ake son ɗaura min, duk yanda akayi wani baƙon lamari zai faru tou amma bansan ko miye ba, kashedi zuciyata tamin tare da hanani ɗaukar wayar, sau biyu aka kira ban ɗauka ba dan haka suka haƙura basu sake kira ba...
Kallon Alhaji Dikko yayi sannan yace yarinyar nan zata kai shekaru nawa ? Saida Alhaji ya kwantar da kai cikin biyayya sannan yace baza ta wuce sha shidda zuwa sha bakwai ba, D --- K yace tou wallahi wannan yarinya tasan abinda takeyi kila shekarunta ya wuce yanda kake tunaninta tana abunta da lissafi, amma baka taɓa kiranta a waya ba ko ... ?
Alhaji yace Eh gaskiya chat kaÉ—ai mukeyi da ita, sai ranar da ta turomin vidion nan shine na kirata, amma daga ranar ban sake kiranta ba saidai ta kirani, Dikko yace tou jikinta ya bata ba kaine kake kiranta ba shi yasa bata É—auka waya ba, amma nasan zata kiraka zuwa anjima zatayi tunanin wayar ta koma hannunka, ajiye wayar yayi a gefenshi suka ci gaba da abinda sukeyi..
Ina ajiye wayar kiran Bello yana shigowa, ɗauka nayi bayan mun gaisa yace min Uwar masu gida nifa har yanzu ban samu kuɗin da kike magana ba, jinjina kaina nayi tare da murmushi nace kanajin wasa bazan iya tura hotunan ka ba a yanar giza gizo ko ? Tou wai babu zan baki ne ? Cikin faɗa yace tou banda su ko satowa zanyi in baki saboda inajin tsoronki to ki turawa uwar yanar giza gizo dan kutumar ubanki ko an faɗa miki tsoronki nakeji ko inajin tsoron a ganni tsirara, idan baki sani ba har gasar fitowa tsirara nayi daga ƙofar gida na har bakin masallacin juma'a naje ranar juma'a babu kaya a jikina na dawo, ni zaki ɗauka hoto kimin hauka ? Tou bake ba ubanki ma nafi ƙarfinshi ki riƙe kiyi ta kallo mtsw ya kashe wayatshi....
Murmushi nayi tare dabin wayar da kallo, har zan haƙura wata zuciyar tace wallahi ƙarya yakeyi bai wani fita tsirara ba idan kika fahimci maganar shi ta farko a sadudance yayi miki magana, karki sauƙaƙa mishi number wayar matarshi zaki fita ki samo ki tura mata zata bashi labari, idan kin tura mata ni na sani sai ya kiraki, idan ya kiraki sai kice kin turawa ɗanshi ma, shi kuma ɗan ba hoton za'a tura mishi ba voice note za'ayi mishi da wasu maganganu masu zafi zuciya zata tunzurashi yayi ma baban magana, tashi dai ki fita duk ki samo numbobinsu ki dawo sannan musan abunyi...
Bello kuma shida abokinshi suka kashe sannan yace na faɗa mata, abokin yace tou yanzu zata shafa maka lafiya kaga kun rabu lafiya zata gaji da ajiyar hotunan ta gogesu, Bello yace ni tsoro na ɗaya tace ta turawa wata ƙawarta hotunan fa, karka damu sun gaji su goge dan ubansu, dariya sukayi tare da ƙara kashe wa cikin duniyanci....
Ina fitowa daga wanka nace ba'asan tsiyar nasara ba sai zashi ganin gida, zakayi dana sanin hanani kuÉ—in nan, kila kuma rabona ne yake da yawa kuÉ—in zasu sake yawa.
Har na gama shiri da abinda nake saƙawa nake warwarewa, Nana na kwaɗawa kira ta kwararo da gudunta tazo, kallonta nayi sannan nace Nana aiki yamin yawa zan fita neman wurin zama sannan kuma zanje wurin wani Alhaji dake tamin rainin hankali, ai kinsan majalissar babana ko ? Nana tace Eh na sani, nace ai kinma san Bello abokinshi ko ? Nana tace sosai ma, tou lambar wayar matarshi da babban ɗanshi zaki kawo number wayoyinsu zan baki dubu ɗaya...
Yashe baki Nana tayi sannan tace godiya nake Sultana, wani sauran biredi da naman da naci jiya na rage na miƙa mata ansa tayi taita kwarara godiya harta fita, tana fita nima na tattara nawa ya nawa na fita nabar gidan...
A ƙofar gidan Alhaji napep ya sauke ni, wasu irin zuƙa zuƙa motoci tun daga ƙofar gida har cikin get in gidan, kuma yauma get ɗin a buɗe yake daga inda nake tsaye ina hango komai na gidan !
Matashin jiya daya faÉ—a min cewa Alhaji yayi tafiya shine yazo wurina da sauri ya gaisheni cikin girmamawa ansawa nayi cikin sakin fuska sannan nace gidan naku lafiya naga taron motoci ?
Lafiya qalau ubangidan nasu ne ya dawo ko gida ma baije ba ya fara da ganin dokuna, jiya da aka fidda dawakunan doki ɗaya ya kare a ƙafa shine ya fara da ganinshi kafin ya wuce.
D --- K ne ya fito daga cikin palon yana magana daga ganin yanayin maganar shi faɗa yakeyi, saida ya fito tsakar gidan sannan ya riƙe ƙugunshi da duka hannuwan shi biyu yaci gaba da magana amma bana iya jiyo abinda suke cewa saboda tazarar dake tsakaninmu.
Zubinsu da yawansu ya bani tsoro gasu ƙosasshi, inda Dikko yake tsaye na kalla, gaskiya Dikko ɗan gayu ne wankakken namiji yasha wanka ya ƙoshi tsaftatacce dashi ya cika ya fito cikakken namiji har wani gemun rainin hankali ya ajiye kamu ɗaya gaskiya duk da bana ƙaunar shi jarumin namiji ne duk inda mace take san namiji Dikko yakai tsakani da Allah zan faɗi gaskiya, domin Allah Dikko yana da kyau mai burgewa da ɗaukar hankali , sauke hannunshi ɗaya yayi daga riƙon da yayi mishi ya saka a aljihu ya ciro ibadar tashi, ya ciro cingom in daga cikin takardar shi ya jefa a bakinshi sannan suka fara taho wurin motocinsu...
Murmushi nayi kaɗan yayin da wani sashe na zuciyata yake cewa kira sunanshi idan ya juyo ki caccakawa uwarshi zagi komai zai faru ya faru idan ma ta tafasa ta ƙone, yayin da wani sashe na kwalwata yake bani shawara cewa duk abinda zakiyi kisa nazari da lissafi kiyi ma takonki linzami mai kyau duk daren daɗewa Dikko sai kinci ubanshi.
Zuciyata tace kiyi masa magana dan ya tunaki kuma yasan kina nan kuma ki faÉ—a masa cewa zaki ci ubanshi idan babu yau akwai wata rana....
Sallama nayi da matashin daya faɗa min Dikko ne yazo sannan na wuce ciki, a lokacin dana isa wurinsu tuni D --- K ya zauna cikin mota ana ƙoƙarin rufe masa mota na riƙe murfin motar ,
Kowa kallo wurin hannun daya riƙe murfin mota yayi dan ganewa idonsa ɗan rainin hankali daya isa yayi wannan iskancin, kwantar da kaina nayi saman murfin motar cikin tausasashshiyar murya nace Dikko, kallo na yayi tare da cewa na'am ya tsareni da idanuwa, shiru na wani lokaci ya ratsa wurin bai daina kallona ba kuma nima ban daina kallonshi ba haka kuma babu wanda yayi mana magana...
Nice na fara cire idona daga kanshi dan idan har ina kallonshi tou lallai babu abinda zai hana in burma mishi wuƙa, kaina yana kallon ƙasa nace ka kuwa gane ni ? Na ƙarasa maganar tare da ɗago fuskata amma ban sake kallon idonshi ba...
Cikin ɓacin rai yace Al ' Ameen mtsww muje ya faɗi maganar tare da jan murmufin motar da ƙarfi ya rufe, zuciya bata da ƙashi ganin Dikko zai maidani sakara yasa na dunkule hannuna na kaiwa gilashin motar duka saida ya tarwatse , jini kuwa yace gashi nan zuwa...
Duk da haka Dikko baiyi niyar tsayawa ba saida nace kai ƙaramin ɗan iska yau itace rana ta ƙarshe a gareka kamar yanda na dasa lissafin kwanaki mutuwarka , idan har kayi nasarar guduwa ina nan tafe gareka sai ka ɗanɗani azaba kwatankwacin irin wacce ka ganamin baka da aiki sai cin cingom kamar wata karuwa sakaran banza daƙiƙi ɗan gidan matsiy......
Wanda aka kira da Al " Ameen shine ya ɗaga hannunshi da niyar kwarara min mari Dikko ya riƙe hannunshi tare dayin murmushin mugunta yace waye yace maka irinsu ake duka ? Tsaya daga gefe kaga maganin ta, Allah ɗaya nake tsoro amma yau dasai nayi mata allurar natsuwa, amma ka barta nayau zan mata kaɗai idan na sake ganinta tou nasan abinda take buƙata, Al ' Ameen yace mai gida ka sakeni in koya mata hankali, murmushin mugunta Dikko yayi tare da cewa bari in bata abinda ta roƙa...
Sakin hannun Al ' Ameen yayi sannan ya matso kusa dani, ɗan kauda kanshi yayi gefe kamar yana nazari fuska a ɗaure ya juyo ya kalleni ni juyowar da yayi gaba ɗaya wurin kowa ya juya baya, hannuwana ya haɗa duka biyun ya maidasu ta baya ya riƙe, hannu ɗayan kuma ya riƙe fuskata, ƙasa ƙasa yayi magana cewa.
Naga dai kina san cingom in nan kinsan kwanaki da muka haɗu ban "yan maki shi ba, kuma sai kiyi ta abu babu kawaici a gaban jama'a sai kiyi ta wani zalamar Dikko kuma ko an baki ni nayi miki yawa ba inda zaki je dani dan ruwa ba sa'ar kwando bane, kina da daraja ɗaya a wurina kuma albarkacinta kike ci amma wallahi dasai na nuna miki ni tantirin ɗan iska ne, darajar tasa kawai bazan wulaƙanta ki ba, amma idan kina neman rainin hankali da tsantsagwaron rashin mutunci daga kaina an rufe littafi.
Tattaunawa yayi cingom in cikin salon jan hankali saida ya busa cingom in yanda ake cewa kwai, sannan ya kalleni da wani iri salo sai kuma yayi murmushi da gefen bakinshi, hannun daya riƙe min fuska ya ciro cingom in sannan ya tura minshi cikin bakina, tuf tuff na fara tofar da cingom in , murmushi yayi tare da rufemin baki yace ai ƙarya kikeyi sai kinci....
Iya ƙoƙari nayi na tofar yaƙi fita ga kuma ya riƙe min hannuwa duka, daidai saitin maƙoshi na yayi min wani duka wanda yasa dole saida na haɗi cingom in, dariya yayi sannan ya sakeni tare da turani baya yace sai mun sake haɗewa an mata....
Tangal tangal na tafi kamar zan faɗi su kuma suka shige motocinsu suka tafi aka barni a filin tsakar wurin daga ni sai Alhaji, dakel na iya haɗiye yawun bakina saboda azaba da raɗaɗin da maƙoshina yakemin saboda nushin da yayi min.
Kallon hannu na nayi da jini yake ta É—iga sannan na kalli Alhaji nace kaini asibiti, cikin damuwa yace muje, dani dashi muka nufi wurin motarshi muka shiga gaba É—ayanmu muka nufi asibiti,
Muna zuwa babu wani daÉ—ewa akamin diresin , bayan an bincike hannun kaf ko akwai wani gilashin a ciki, magunguna aka bani sai kuma allurai da akayi min duk Alhaji ne ya biya kuÉ—in bayan an gama komai ya É—aukeni muka tafi gida !
A ƙofar gida yayi parking duk muna cikin mota daga ni harshi, shiru mukayi na wani lokaci sannan Alhaji yace hajiya dan girman Allah ki goge wannan vidio dan darajar manzan Allah S. A. W, ki taimaki rayuwata ki goge don Allah, badan halina ba,
Ajiyar zuciya nayi sannan nace tou nima ka taimakeni dan darajar manzan Allah S. A. W dani dakai duk mu taimaki juna daga yau nayi maka alƙawari zan goge vidio sannan kuma zan fita rayuwarka babu dawowa...
Tattaro hankalinshi yayi wurina sannan yace faÉ—amin me kike so idan har ina da hali zan miki ! Ba tare dana kalleshi ba nace mota kawai zaka bani daga ita na rantse maka da Allah na fita sha'anin ka vidiwo kuma zan goge...
Goge zufa Alhaji yayi sannan yace wace iri kike so ne ? Ni bansan mota ba amma dai mai kyau nake so, kallon motarshi yayi sannan yace kina san wannan ? Ba tare da ɓata lokaci ba nace Eh tamin kuma ina santa,
Alhaji yace tou na baki ita, kina da wurin ajiyarta ne ? Yanzu ma zan ajiye miki ita insa azo a tafi dani amma ki goge hotunan nan dan Allah, karka damu zan goge wallahi, a , a nidai ki goge a gabana don Allah, tunda nace zan goge ai zan goge, Alhaji yace tou bayan wannan sai me ?
Abu na gaba ina so ka faÉ—amin waye Dikko ? Miye asalinshi waye babanshi a garin nan ? Wane irin matsayi gareshi kuma wane dalili ne yasa yake É—agawa ta rayuwa ina san ka faÉ—amin asalin Dikko da kuma tarihin rayuwarshi.....
Gyara zama Alhaji yayi sannan yace fara bani mazaunin motarki na ajiye ki goge vidio sannan sai muyi magana kinga lokacin ina cikin natsuwa, ba damuwa na faÉ—a tare da buÉ—e mota na fita na shiga cikin gida !:',
Kuyi haƙuri don Allah yau ina can gidan uwar ɗakina nima inacin shagali da miyar mutunci, wurin uwar ɗakina wato *RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE* ina alfahari dake uwar ɗaki ɗaya tamkar da dubu banda kamarki kuma kina da matsayi na musamma a zuciyar *MEELAT MUSA*.....
24/08/2019
*JAMILA MUSA CE...*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 18
*_KOMAI DADIN DUNIYA KIYAMA TA FISHI , daga alƙalamin Ummerherny Nerserllerh idan kika bari aka barki baya bazan baki labarin wannan ƙayataccen labari ba wanda ya fito daga alƙalamin haziƙar marubuciyar zamani, Allah ya taimaka surukuta yasa a kammala lafiya amin..._*
Ina shiga gidan ko sallama banyi ba yaro ya shigo da saurinshi wai ance Sultana tazo Alhaji yana kiranta , Nana ta fara miya sameki naga hannunki a É—aure ... ? Duk hankalin su A ` i ya tashi sunga uwar É—akin kwarata hannu da É—amara, murmushi nayi tare da cewa yawwa A ` i da Allah inda zan ajiye mota nake so nayi maganar dan kauda tambayar abinda yaji min ciwo, Hafsa tace ina motar take ne ?
Ba tare dana kalleta ba nace tana waje, dan haushin Dikko ya fara shafar Hafsa saboda soyayyar da take mishi bana san Dikko haka kuma bana soyayya wa duk wanda yake ƙaunar Dikko, Hafsa tace sai in ajiye miki a gidanmu, ban bata amsa ba nabi yaron muka koma waje...
Motoci biyu na gani a ƙofar gida , wurin motar Alhaji na tsaya daidai saitinshi sannan nace gani, wani wuri ya buɗe ya tattaro wasu takaddu ya bani ansa nayi naɗan basar ina kallo a zahirance karatunsu nakeyi amma wallahi a baɗinance bansan ko na miye ba...
Fitowa yayi daga cikin motar ya bani makullin tare da cewa ga motar nan zanje mai gida yake kirana dana gama zan dawo insha Allah amma ki rufamin asiri Sultana ki goge vidion nan don Allah, wallahi karkaji komai Alhaji zan goge amma kaÉ—an bani na kati plz, yace ina zuwa bara in gama tattara tarkacena a motar nan...
Komai nashi ya kwashe a mota ya zuba cikin motar dana gani, bayan ya gama ya ciro wayarshi yace kalli ki gani, kallon wayar nayi yace kinga na goge nawa ko ? Nace Eh nima zan goge insha Allah, godiya yayi sannan ya bani kuÉ—i amma basu da yawa yace idan ya dawo anjima insha Allah zai bani tukuicin goge vidio, godiya nayi masa sannan mukayi sallama ya shiga mota tare da cewa karfa kiyi wasa da takardun motar nan ki adana su kinji ko ? Sai yanzu na gane abinda takardun suke nufi godiya nayi masa suka wuce ni kuma na koma gida...
Ina shiga gida Hafsa na ba makullin nace kije ki ajiyemin zan ɗauko ta ƙarshen satin nan insha Allah, ansar mukulin tayi taci gaba da maganar ta, kallonta nayi sannan nace saurara kiji, kije ki ajiyemin mota ki dawo, tashi tayi ita dasu Saude suka tafi ni kuma na shiga ɗakina, ban daɗe da shiga ba Nana ta shigo tare da bani number matar Bello amma bata samo na ɗanshi ba , ansa nayi da nayi niyar bata 500 sai wata zuciyar tace kawai in bata 1k in ka nema ma ka samu ai arziƙi ne...
Jakata na buɗe na bata 1k nayi godiya, itama godiya tamin ta fice a ɗakin, tana fita na kulle ƙofa na kwanta saman katifa na fashe da kuka mara sauti , duk duniya babu wanda ya taɓa wulaƙanta ni kamar Dikko nice zai bawa cingom in bakinshi da yawun bakinshi na haɗe a cikin cikina , duk duniya babu abinda yakai miyau saurin sadar da shaƙuwa, shi yasa masu wayau ko bariki suke basa yadda suna haɗa bakunansu da na wasu, waccan ranar bai haɗa bakinmu ba amma shine yau ya ciro abu daga cikin bakinshi ya bani, yana da wata manufa ta daban shine dalilin da yasa yace ma Al ' Ameen bara suga magani na, wato wannan dalilin ne yasa kowa ya juya mana baya ko ? Saida na goge hawaye na sannan nace ƙarya kakeyi yawun bakin ka bazai taɓa zama hukunci a gareni ba...
Nayi kuka har na gode Allah daga baya kuma bacci ya kwasheni wanda bansa lokacin daya zo ba kuma baiyi shawara dani ba,
Washe gari koda na tashi nayi sallah bacci na koma bayan na gama kwashewa Dikko karama , misalin 09:30am Alhaji yasa aka kirani a waya, bayan na É—auka nayi sallama dakel Alhaji ya amsamin sallamar cikin nishi yace Sultana ina federal medical center { F M C } saida ya sake yin nishi cikin yanayin wahaltuwa sannan yace ina nan Accident & Emargency kizo yanzu don Allah inasan zanyi magana dake....
Har a zuciyata banji daɗi ba cikin muryar tausayi nace kayi haɗari ne ? Hawaye ya gangaro masa daga cikin idonshi yace kizo dai dan bana tunanin zan ƙara awa ɗaya a cikin duniyar nan....
Subahanalla da Allah ka daina wannan maganar gani nan zuwa insha Allah, cikin rawar jiki na kashe wayata, da sauri na sauko daga saman katifa na zuba ruwa, a gaggauce naje nayo wanka tare da wanko bakina, mai fauda da kwalli kaɗai na shafa, baƙar riga ta jallabiya na saka na yana gyalen a saman kaina na zagoyo dashi har gashin kaina saida ya fito ta ƙasan gyalen jallabiyata, gilashi mai saukin duhu na saka sannan na wanke jikina da turaruka masu sanyi ƙamshi, masha Allah na faɗa a lokacin da naga kaina a cikin madubi, nayi kyau sosai na fito kamar baƙuwar balarabiya a nigeria,
Wayata na É—auka da jakata, na fito ina tsaye ina kulle É—aki Hafsa ta shigo, ita É—aya ce babu abokan nata su Saude, su Nana ma duk basa tsakar gida, É—an gangarowa tayi da wani irin salon tafiya, ta wutsiyar idona na kalleta sannan na É—aure fuskata na kallota dukanta a daidai lokacin dana gama rufe É—akina...
Wow uwar ɗakin karuwai kinyi kyau fa kamar dai ba'a mutu ba, share maganar nayi tare da cewa da mota kika zo ne ? Eh ta faɗa tare da bina da kallon cin wanka , gaba nayi tare da cewa muje ki saukeni f m c biyoni tayi muka fito a tare, a ƙofar gida muka haɗu dasu A ` i hada Amisty da Saudatu....
Amisty tace wurinki zamuje munji shiru har yanzu, kuma mun rubuto takarda an tsara jaddawalin yanda zai ƙawatar ya kuma tafi da hankalin maza gaki kuma zafi fita, buɗe gaban mota nayi na kame sannan nace ku shigo muje kuma, baya suka shiga, Hafsa kuma ta zauna mazaunin tuƙi taja muka tafi....
Saida muka fara tafiya sannan nace karanto min ina saurarenki, Amisty fa tasan komai tasan bana ganewa bana rubutawa kuma bana iya karantawa amma sai tace kidai duba ki gani Sultana, basar da ita nayi tare da miƙa hannuna ta baya na anso takarda ko buɗewa banyi ba na ajiye shegiya ban sake bi ta kanta ba kuma ban sake magana ba har muka isa asibitin...
Wani irin tuƙin ganganci Hafsa tayi tare da sakin sitiyarin saboda taga D --- K , a tare muka iso dasu sai leƙawa take tana kiranshi, wato abinda na fahimta idanma ka nunawa mutum ka damu dashi sai yayi ta ɗagawa, kallon Hafsa nayi tare da cewa ke kuwa baki da aji a haka kike tunanin zan riƙa haɗaki da zafafan mata babu class, raina ya ɓaci sannan nace uban waye Dikko da kike ta hauka kina kiranshi mutane suna kallonki kamar wata zararriya....
A daidai lokacin da muka fito mu dukanmu daga mota shima Dikko ya fito kuma yaji zagin da nayi masa , bai kallemu ba yayi gaba ana take masa baya nima gaba na shiga su Hafsa suka rufomin baya, murmushi Dikko yayi a daidai lokacin da muka tsaya bakin ƙofar ɗakin kowa da muƙarrabenshi a bayanshi, kallona Dikko yayi tare dayin murmushi sannan yace zaki ci ne an mata yayi tambayar tare da ɗaga gira ? Ya ƙarasa maganar tare dayimin wani irin kallo mai tattare da mugunta, yaci gaba da cin cingom inshi cikin salon jan hankali gemunshi yana motsawa a hankali cikin salon ɗaukar hankali , murmushi nayi saboda gaskiya yanayin da yayi ya burgeni, ƙarshen harshenshi ya kawo cingom in yayi wasa dashi a daidai lokacin da aka buɗe mana ƙofa duk muka shiga, daga waje bai sake kallona ba kuma bai sake murmushi ba babu magana har muka isa gaban gadon Alhaji...
Duk matan da muke tare ihu muka farayi saboda tsoron yanayi da Alhaji yake ciki yayin da wasu suka nufi hanyar fita, dani da A ` i aka bari yayin da A ` i ta duƙushe tana kuka ni kuma na cire gilashi na wurgar a gefe na rufe idanuwa na naci gaba da dire dire ina kuka saboda na kasa gaba na kasa baya....
Shi kuma Alhaji burinshi inje wurinshi in taimaki rayuwarshi na goge vidio sai kirana yake cikin dasasshiyar murya da yayi magana sai jini ya kwararo , Dikko yace ya daina magana amma yaƙi saurarenshi Sultana kawai yake kira,
Kusa dashi Dikko ya ɗuka sannan ya tambayashi me zan mishi ne ? Hawaye na zuba a idon Alhaji yace ma Dikko ya rufa mishi asiri ya kawoni wurinshi magana zamuyi ta sirri, Dikko yace faɗamin na faɗa mata kaga ta firgita wani abu zai samunta, cikin wahaltacciyarar murya Alhaji yace kayi min wannan arziƙin na sauran mintunan da suka ragemin a duniya lokacina yana tafiya zan iya mutuwa ko wane lokaci, yanda yayi maganar ne yasa Dikko ya kallo inda nake tsaye ina ta direre kamar anyi ma lafiyayyan diko allurar hauka.
ÆŠauke idonshi yayi daga kaina sannan ya kalli zugar daya zo da ita, Al ` Ameen ya faÉ—a cikin wani irin yanayi kamar bashi ne yayi maganar ba, gaba É—aya waje suka fita harda A ` i aka fita, inda gilashina yake Dikko yaje ya É—auko sannan yazo kusa dani, ta gaban rigata ya jawo ya sagala gilashin sannan yace buÉ—e idonki, jikina yana kyarma na buÉ—e na kalli Dikko, dakel ya haÉ—e yawun bakinshi sannan ya tofar da cingom in bakinshi gaba É—aya yanayin Dikko ya canza É—aure fuska yayi sosai sannan yace miye tsakaninki da mara lafiyar nan ? Miye dalilinki na zuwa ganinshi ? Me kikaje yi gidanshi ? Kema "yar iska kike so ki zama ko ?
Cikin gatsali nace Ey "yar iska zan zama ina ruwanka da iskanci na ne ? Jinjina kai yayi tare da cewa Allah ya sawaƙe wuce muje yana kiranki, tirjewa nayi tare da juya zan fita da gudu ya riƙoni yace ai ƙarya kike sai kinje, har gaban Alhaji ya jani ya kaini sannan ya zaunar dani saman kujera ya tsaya ta bayana yace gata nan me tayi maka ne ? Ko kaima taci kuɗinka kamar yanda taci na Umar ?
Ɗaga kaina nayi na kallo Dikko ɓacin rai kwance a cikin idonshi zare min idanuwa yayi tare da cewa bari kallona kar fashe miki kwayar ido wallahi, jiki a sanyaye na sauko kaina daga kallon da nake ma Dikko naci gaba da kallon Alhaji ina kuka, dafo kujerar yayi ya duƙo kusa dani sosai saitin kunne na yace na rantse da girman Allah idan na gano akwai wani abu tsakaninki dashi saina kashe ki, ya faɗi maganar tare da shaƙemin wuya sosai na fara ƙoƙarin ƙwalƙwale hannunshi na kasa, tun ina iyawa har nasa wani abu na fara halbe halbe har na faɗo daga saman kujera Dikko bai saki wuyana ba naci gaba da halbe halbe, yanda nake halhalbe ya jawo hankalin mutane suka yo kanmu amma an kasa cire hannun Dikko daga wuyana,
Hayani tayi yawa sosai wanda yasa su Al ` Ameen suka shigo ciki da gudu amma wallahi duk yawan mazan nan suka kasa ɓanɓareni daga hannun Dikko harsai dana suma, riƙe Al ` Ameen yake da hannun Dikko yana cewa don girman Allah mai gida ka ƙyale yarinyar nan karta mutu, zaro jajayen idanuwan shi yayi kamar yaci mutuwa yace fita idona Al ` Amenn ya faɗi maganar yana fitar da wani irin lumfashi kamar ranshi zai fita, Al ` Ameen kuwa ƙin sakin hannun Dikko yayi saboda tunda yaga Dikko a wannan yanayin yasan komai zai iya faruwa....
Yace mai gida karta mutu, Dikko yace ta mutu idan ta mutu kaine ka kashe ta ko kaine zakayi azumi ? Ya ƙarasa maganar tare da kwalalo idanuwanshi waje , sannan yace duk abinda ya faru da ita nine ya ƙarasa maganar tare da nuna kanshi, haƙuri akayi taba dikko dakel aka samu ya sakeni ,
Bakin gadon Alhaji ya koma ya ɗauki wayarshi iyakar bincike Dikko yayi bai samu komai ba, kuma number na dama Alhaji baiyi saving ba, jerin kira ya dawo yaci gaba da binke, saida ya gama sannan ya ajiye wayar , kallo gadon da nake kwance yayi har an sakamin ƙarin ruwa da taimakon Al ' Ameen dayayi tsaye yace a bani taimakon gaggawa,
Kusa da Al ' Ameen yaje tare da cewa bani makullin mota, cikin girmamawa ya É—auko ya bashi baiyi mishi musu ba saboda yasan Dikko baya san gardama idan yace ayi kawai ayi mishi idan yace a bari barin kawai za'ayi sai a zauna lafiya,
Cingom ya ciro daga aljihu ya ɓanɓare ya saka bakinshi yaci gaba daci, Al ' Ameen kuwa bin Dikko yayi da kallo harya fita daga ɗakin yana mamakin hali irin na Dikko zuciyarshi tayi yawa idan ya burkuce wani lokaci kamar bashi ne yakeyi wasu abubuwan ba...
Ta jikin window ya leƙa Dikko, har ya shiga motar yaja ya tafi cikin tuƙinshi na ganganci wanda baya kaucewa kuma baya ɗagawa kowa ƙafa idan ya tafi sai yakai inda zaije hankalinshi yake kwanciya, Allah ya tsare hanya Al ' Ameen ya faɗa tare da dawowa wurin gado na ya tsaya, su Hafsa da Saude da A ` i da Amisty sunyi jigum kowa yana jiran farfaɗowa ta yaji abinda ya haɗani da D --- K......
Dikko kuwa tuƙi yake amma yana tunanin maganar Alhaji ranka ya daɗe wato wallahi wata yarinya ce muka ɗan keɓe da ita , tou wallahi bansan yarinyar nan ta shirya sharri ba, ashe duk abinda mukayi ranka ya daɗe tana ɗauka cikin waya ban sani ba....
Dukan sitiyari Dikko yayi tare da cewa tabbas yacemin yarinyar nan shekarunta bazai wuce 16 zuwa 17 ba daidai saitin zuciyarshi ya daka tare da cewa kece .... ?
Akan titi duk ƙurewar wuri Dikko ya juya kan sitiyarin mota ya koma baya ba abinda ya dameshi da halin da wani zai shiga kanshi kawai yakeji amma baya sauraren talakawansu, da gudu ya ibi shararra ya komo asibiti, a lokacin su Al ' Ameen sun fito zasu tafi ganin Dikko ya dawo yasa Al ' Ameen ya dawo cikin ɗakin da gudu yasa aka ɓoyeni, danshi Alhaji tuni Allah ya anshi rayuwarshi har an tafi da gawarshi, duk zunubin da Alhaji ya cacumar ma kanshi an samu wani marar rabo a lahira ya dira gidanshi yayi mishi caccakar wulaƙanci aka kawoshi asibiti dan ceton rayuwarshi Allah yasa ikar ibar da yayo kenan, Allah ya jiƙanshi yasa mu cika da imani ubangiji ya kyautata namu ƙarshen idan ajalinmu yazo...
Ana ɓoyeni su Al ` Ameen suka fito, a waje suka haɗu da Dikko yana ƙoƙarin shiga suka faɗa mishi mutuwar Alhaji ni kuma an canja min asibiti, Allahu Akbar Dikko ya faɗa tare da cewa ubangiji ya ƙarɓi baƙuncinka Muntari Allah ya kyautata tamu bayan taku, da Amin kowa ya ansa sannan suka tafi a tattare baki ɗayansu...
25/08/2019
Taku a kullum
*MEELAT MUSA...*
⚜ *BRILLIANT WRITERS ASSO* 🖊
_-{{Pen of freedom, home of exceptional and magnificent writers}}-_
*KWARATA*
_{{Kalu bale gareku matan aure}}_
*JAMILA MUSA* _{ meelat musa }_
_Sadaukar wa gareku,_ 👇ðŸ»
*ASMA'U ZAYYAN* _{{ Asmeenat }}_
&
*RABI'ATU AMINU MAMMAN DEE*
🅿 ------ 19
Har yanzu kalar idon Dikko bai koma fari ba, idon nan jajir kamar yaci bala'e, amma a hankali yake washewa zuwa kalarshi ta ainahi, fuskar nan a murtuke ya jingina bayan shi da kujerar mota kana kallonshi kasan yana tattare da tsantsar damuwa.
Ɗan gajeren tsoki yayi tare da gyara zamanshi, hannunshi yakai ya shafe gefen fuskar shi, tunanin safiyar haɗuwarshi da Sultana ya fara dawo mishi sabo fitikil kamar yanzu ne abun yake faruwa, da sauri ya rumtse idanuwan shi tare da haɗe leɓunan sa wuri ɗaya ya danne su da haƙoranshi ta ciki, buɗe ƙofafin hancin shi yayi saboda lumfashin da yake shaƙa yayi mishi kaɗan ya buɗe ƙoƙofin hancin ne dan iskan ya yalwace shi.
Har suka isa gidan rasuwa Dikko bai sake ma kowa magana ba, tunda dama shi ba ma'abokin surutu bane, mota nayi parking ya fita cikin damuwa danshi dama kullum haka yanayin shi yake , farin ciki da ɓakin ciki duk yanayin iri ɗaya ne a wurin shi, babu wanda ya isa yasan lokacin farin cikinshi kuma babu wanda ya isa yasan lokacin da yake damuwa.
Tunda ya fito aka fara gyara mishi wurin da zai zauna dan zamanin ga mutane basa abu domin Allah basa darata girma shekaru da mutumci amma suna ba naira matsayi na musamma, Dikko yana da rashin mutunci amma alherinshi yasa mutane basa ganin rashin mutuncin nashi dan Allah yayi masa kyauta idan dai kukayi ido ido dashi tou tabbas zai baki kuma baya da kwauro idan zai bayar mai yawa yake baka, tou kyautar itace ta danne rashin mutuncin shi ga idanuwan al'ummar gari...
Sabuwar tabarma aka amso daga cikin gidan aka shimfida mishi, takalman shi ya cire ya taka tabarmar da safa, saida ya zauna sannan kowa ya zauna kuɗi suka fara nuna ikonsu domin masu neman asan dasu sukayi ta zubewa suna bada gaisuwa, saida ya jinjina kai dan shi kaɗai yasan tsutsar baƙin cikin dake lasar masa zuciya...
Wanda suka bawa duniya gaba ne suka fara bawa Dikko labarin yadda abun ya faru amma a zahirance yana jinsu amma a baɗinance hankali shi yana wurin Sultana so yake kawai a dawo jana'iza yaje ya ganota wallahi sai ta faɗa mishi miye tsakaninta da Muntari, inma banda take daƙiƙiya dan ta tona mishi asiri shine zai haɗa kirji da ita taje ita kuma ta haɗa da yaronshi...
Wayarshi ya ciro yayi "yan rubuce rubuce bayan ya gama ya tura, wayar shi ya maida aljihun gaban riga a zuciyarshi kuwa yana tunani Sultana ta gama barbaÉ—ashi a duniya kowa kallon É—an iska yake mishi,
Mikewa tsaye sukayi gaba ɗaya dan an fito da mankara, sai yanzu wasu keyin alwalla shidai yana da ita takalmin shi ya saka suka fita sarari dan sallatar gawar Alhaji Muntari , Allahu Akbar ubangiji kayi mana kyakkyawan ƙarshe hanyar dai ɗaya ce duk wanda yazo sai ya koma Allah kasa mu cika da imani idan ajalinmu yazo ameen....
A asibiti kuwa ina kwance cikin tsaka mai wuya, ina tafiya ne tsakanin rayuwa da mutuwa, duk wanda ya ganni saiya tausayamin ga hannu na naÉ—e da bandej wanda na fasa shi a jikin gilashin motar Dikko, su A ` i kuwa suna bani kulawa ta musamman tare da tattalina kamar mun fita ciki É—aya !
Tsaye suke zagaye jikin gado na hankalin kowa tashe, jami'an tsaro ne suka shigo gaba É—aya suka fatattaki su A ` i , kujerar da ake tura marasa lafiya aka É—auko aka É—orani a samanta suka tun kari hanyar fita dani daga cikin É—akin, wani irin ihu Saude tayi tare da cewa ina zakuje da ita ne ?
Basu saurari kowa ba suka fito dani, cikin mota aka sakani mazaunin baya sannan aka rataye ƙarin ruwan a jikin kujera yaci gaba da shiga cikin jikina,
A wurin suka bar kujerar duk suka shiga mota sukaja muka bar asibitin, kuka su Hafsa sukayi tayi tare da tambayar kansu wane irin laifi nayi wanda har hukuma bata ragamin ba ina kwance a gadon asibiti, sunsha kuka har sun godewa Allah daga ƙarshe suka haƙura suka tafi gida...
Daga maƙabarta Dikko basu dawo gidan rasuwa ba gida suka wuce kai tsaye, tun a get na biyu ya sauka tare da cewa zai shiga yayi bacci , Al ' Ameen yace ranka ya daɗe bara muje get in ƙarshe sannan mu sauke ka amma daga nan ai zakasha tafiya, ba tare daya kalli Al ' Ameen ba yace nan zan sauka ya ƙarasa maganar tare da kallon Al ' Ameen , tuba nake ranka ya daɗe Al ' Ameen ya faɗa tare da jan motar yayi gaba...
Saida ya daina hango ɓurɓushin motar sannan ya fiddo wayarshi yayi "yan lashe lashenshi sannan ya kara a kunnenshi , bayan wani lokaci yace kuna ina ne ? Magana na cikin wayar yayi sannan Dikko yace ku shigo ta get in baya, yana faɗin haka ya kashe wayarshi tare da kiran wata wayar kuma.
Ta baya ya dawo ya bi wata hanya daban , tafiya mai nisan gaske yayi wurin tsitt bakajin ƙarar komai sai motsin tafiyarshi tunda tsakuwowi ne baje a wurin irin wannan fararen wanda idan ana rana har kashe ido suke, idan ya taka sai kaji tsus tsuss ƙarar tafiyar shi ,
Wata hanya ya bullo sai gashi jikin wani makeken get, masu gadi yayi ma magana suka buɗe motarmu ta shigo cikin gidan, gaba yayi motarmu tanabin bayanshi saida mukayo nisa da get in sannan ya tsaya, shima matuƙin motar tsayawa yayi tare da fitowa Dikko bai mishi magana ba ya shiga mazaunin dirver yaja motar yayi gaba.
A bakin ƙofar falonshi yayi parking sannan ya fito yaje ya buɗe ɗakin, dawowa yayi ya buɗe baya inda nake kwance rai hannun Allah, ciro robor ƙarin ruwan yayi ya fara riƙewa sannan ya ɗaukeni ya shiga ciki, a falo ya kwantar dani saman kujera 3sieter saida ya gyara ruwan suka ci gaba da shiga sannan ya fita tare da rufe ɗakin ta waje...
Motar ya ɗauke daga bakin ƙofar falon sannan ya ajiyeta a inda suke ajiye motoci, motar ta gidansu ce kuma jami'an suma na gidansu ne yayi amfani dasu...
Dawowa yayi tare da rufe ɗakin sannan ya wuce ciki, wanka yayi ya cire manyan kaya zuwa ƙanana, falo ya dawo ya zauna yana jiran lokacin da zan buɗe idona ya haɗa partyn shagalin wulaƙantani,
Zama yayi saman kujera wacce take kallona, ba abinda yake tashin shi a wurin saidai yaje yayi sallah ya dawo, idan yazo ya zauna kuwa lokaci zuwa lokaci yakan kalli agogon hannushi sannan ya kalli inda nake kwance, waya kuwa idan an kishi saida ya duba kawai ya latse,
Ruwa ma daya ƙare shine ya cire min, bai daɗe da zama ba aka fara dukan ƙofar ɗakin, ɗan latse baki yayi tare da cewa waye ? Dikko buɗe nice, muryar yayarshi yaji miƙewa yayi yaje ya buɗe ƙofar suka shigo cikin falon tare,
Salati nayi a daidai wannan lokacin jin muryar Dikko da sunanshi da aka kira, wani irin abu naji ya daki zuciyata, na ƙara lafewa bamma yi gigin tashi ba haka kuma ban kuskura na buɗe idona ba, amma jikina ya mutu murus , zama yayi a saman kujerar da yake itama kusa dashi ta zauna saman hannun kujera sannan tace ina ka samo larabawan daji ? Ta faɗi maganar tare dayin dariya...
Banza yayi baice mata komai ba, dariya ta sakeyi tare da jan gemunshi sannan tace dan ubanka bakaji ina maka magana, tayi maganar cikin sigar zaulaya, tsoki yayi tare da cewa ni bana san irin abinda kikemin yayi maganar cikin haɗe rai kamar dai yanda ya saba, kaiji ɗan iska ni zaka ɗaure ma fuska ko mutuwa zakayi na faɗa maka bazan daina janka ba, duk wannan haɗe haɗen fuskar gabana aka haife saida ma nayi aure dan ubanka kazo duniya wane girma zakayi gabana, ko inda take bai kalla ba, kuma baiyi murmushi ba bare tasa ran zaiyi dariya, sansar wauta dai tayi ta nunawa da sakarci amma Dikko tunda yace mata baya san abinda take mishi bai sake magana ba saida ta ƙari rashin wayanta sannan ta taho inda nake kwance...
Ko kallonta baiyi ba dan hankalinshi ma yana kan wayarshi amma yana kallonmu da zuciyarshi, tsaye tayi gabana idona da jikina suka É—auki kyarma da sauri na buÉ—e ido na kalleta a tsorace sai kuma na kallo inda Dikko yake zaune amma yanzu bayacim cingom maido kallona nayi wurinta kawai sai na fashe da kuka....
Sai yanzu ya É—ago kanshi cikin tsawa yace ki rufemin baki, da sauri na haÉ—e kukan tare da rufe idona dan wallahi a halin yanzu tsoron Dikko nakeji dan na fara tunanin kila mahaukaci ne amma har yanzu jikina bai daina kyarma ba.
Juyawa yayar tashi tayi tai mishi magana da yaren arna { turanci } bansan abinda sukace ba, ɗan ɓata fuska yayi sannan ya ajiye wayarshi shima yayi mata magana cikin irin harshen da tayi masa, Allah ya bata lafiya ta faɗa tare da cewa zan koma wurin momy da Allah kayi ƙoƙari ka shigo, da kanshi ya amsa mata, saida ta ƙara kallona sannan ta kalli Dikko ta sakeyin magana da yaren ɗazu, kyakkyawan murmushi yayi sannan yace ngode ya faɗi maganar tare da ɗauko cingom ya fara ci, abinda na fahimta cin cingom in kila yana da ƙa'ida domin yafi amfani dashi a wasu lokutta wanda shi kaɗai yasan su...
Fita tayi daga ɗakin tare dajan ƙofar garam, har yanzu idanuwa na a rufe suke jikina kuma bai daina kyarma ba, tashi yayi yaje ya kulle ɗakin sannan ya dawo ya zauna, cikin kujera ya tura hannunshi ya zauro wata irin zureriyar wuƙa sai kyalli takeyi saboda sabinta,
Ke zo nan , kamar ina jira na tashi dan nasan babu wata ke a ɗakin sai ni, da sauri na isa gabanshi na durƙusa cikin tsoro na sauke kaina ƙasa, cikin natsatstsiyar murya yace kalli , ɗago kaina nayi na kalleshi amma ba ido cikin ido ba, cikin murya maisa natsuwa yace mi yasa bakijin magana ? Shiru nayi naci gaba da lissafin "yan yatsu na, bana san ina magana ina maimaitawa, raina yana sauri ɓacin ne , banda haƙuri zuciyata a kusa take ina tambayarki kawai ki bani amsa...
Mi ya haɗaki da Muntari kikayi mishi vidio ? Wata irin mummunar faɗuwar gaba naji kardai Alhaji ya nunawa Dikko vidion nan, Dikko kuwa ɗoro tsinin wuƙarshi yayi daidai saitin maƙoshina, wanda ya shaƙeni a gaban mutane lallai zai iya kasheni tunda babu mai ganinmu sai Allah, ina san ganin idonshi domin ta nan ne kaɗai zan iya gano idan Alhaji ya bashi labarin vidio,
Ɗan kartar min wuya yayi da wuƙar tare da cewa ke nake sauraro, cak na ɗauke numfashina tare da kallon kwayar idonshi sannan nace waye Muntari ? Na tambayeshi ne dan san gano ko gaskiya ne ? Da ƙafarshi ya takamin baki sannan ya halbi daidai saitin hancina har saida jini ya fita.
Ƙasa ƙasa yayo da wuƙar daidai saitin ƙirjina inda daya burma min ita tawa ta ƙare, cikin kuka na riƙe wuƙar tare da cewa to yanzu kuma laifin me nayi maka ? Na ƙarasa maganar hawaye na kwarara daga cikin idona, shima hawaye ne kwance a cikin kwayar idonshi cikin damuwa yace saki wuƙar kinji, sakin wuƙar nayi sannan yace zaki iya kasheni ? Cikin rashin fahimta nace kamar ya zan iya kisa bayan nasan ba abune mai kyau ba ?
Dikko yace tou mi yasa kika zaɓi zunubi mafi muni a rayuwarki ? Kin kuwa san illolin dake tattare da zina ? Kinsan bala'en ta kinsan matsalolin da take haifarwa ? Kina ƙaramar yarinyarki ki tunkari mazan bariki, kinsan bala'e kuwa irin na mazan bariki ? Kinsan haɗarinsu ? Mazan bariki basa taɓa jin tausayin macen bariki kuma basa tattalata basu san darajarta ba haka kuma bazasu taɓa raga mata daidai da ɗigon kwayar zarraba bariki ta fito kuma shi za'ayi da ita tunda sunsan idan sun lalataki gobe ma wata zasu nema, kinga kuwa da wannan bala'e da kika bashi gaba kawai gara ki sokawa Dikko wuƙa ki huta ya ƙarasa maganar tare da miƙomin wuƙar....
Kallonshi nayi amma banyi magana ba, murmushi yayi tare da ciro cingom in bakin shi yace na Æ™oshi ko zaki ci ne ? Banza nayi kamar banji ba , É—aga kafaÉ—un shi yayi tare da cewa kin huta 🤷ðŸ»â€â™‚, ya faÉ—i maganar tare da maida cingom inshi cikin bakinshi yabi ni da kallon rainin hankali,
Shiru na wasu mintoci sannan yace kinsan abinda yasa nazo dake gidan nan ? Keda ke gidanki idan kinyi magana tou na tankawa Dikko, ci gaba yayi da cewa anan kaɗai zanyi magana dake cikin natsuwa, ki daina hayemin kuma ki rage rashin kunya sannan ki taka a hankali duniya taƙaitacciya ce ga kowa amma babu kamar mace,
Ki taka sannu An mata ki faɗamin duk abinda kike so a duniyar nan ko miye zan miki kuma zan baki idan dai zaisa ki kwantar da hankali ki natsu, kuma ba yau kaɗai ba zan ci gaba da kyautata miki daga nan har ranar da numfashina zai bar gangar jikina zanci gaba da kyautata miki dan kiyi farin ciki , ke yarinya ce baki san komai na rayuwa ba, amma zan sake faɗa Allah ya baki sa'ar rayuwa da har kika shigo rayuwata sheɗan kuma ya samu galaba a kaina, tunda ni zina ba aikina bane ban taɓa ba tunda nake wallahi sai a kanki.
Kinsha dani kuma kin gama dani har badan duniya, kina da matsayi na musamman da bazai taɓa goguwa a zuciyata ba kuma kin shiga cikin babban tarihin da bazai taɓa gogewa ba a rayuwata har abadan duniya , duk wacce ta shigo kece farko, ni haɗuwata dake na barshi matsayin ƙaddara kuma bansan abinda ubangiji yake nufi da ita ba.
Daga ni harke babu wanda yasan abinda anjima zatayi bare gobe, amma ina riƙonki da Allah kiyi haƙuri kuma ki yafemin akan duk wani abu daya faru tsakanina dake, taɓe bakina nayi tare dayi magana ƙasa ƙasa amma baiji abinda nace ba, Eye ? Ya tambayani tare da yatsina fuska yace banji me kike faɗa ba ,
Kai tsaye na kalleshi tare da cewa bazan yafe maka ba har abadan duniya, jinjina kai yayi tare da cewa to ba komai Allah yasa rashin yafiyar shine alkairi a rayuwata, kina buƙatar wani abu ne daga gareni ? Ni bana san komai saboda baka da abinda zaka bani ni bakayi kuɗin da zaka taimakeni dashi ba har yanzu, bai sake magana ba, ya ɗauki wayarshi ya kira mutumin daya kawoni yace yazo ya mai dani gida...