Complete Hausa Novels

Rabon Kwado Part 3 Complete Hausa Novel

Reading file: Rabon Kwado Part 3 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 22 of 22

page 51- 52

Da asubah muhammad yatashi ya yahada mata ruwa medan zafi yadda zai gasata sosai,sannan yazo ya dauke ta yana tabata ta farka amma setaki bude idanun ta seda tajita a ruwan zafin tukunnah ta gwalalo idanu zata kware baki kwanto da ita yay kan kirjinshi iya karfinta ta kankameshi tasa masa kuka harda magiya yakyaleta ta fita aruwan don yasa hannayen sa ya dannata dakyau kalaman dayake mata ne cikin kunnen ta yadauke mata hankali,seda ya tabbatar da ruwan yagama ratsata tukunna yasaketa yay alwala yafito yatafi masallaci don inya tsaya yimata wanka bazata bari bah ga time zata bata masa, a daddafe tafito tai sallah takoma kan bed din tanata rawar sanyi saboda jikin ta yasoma zafi sosai da alamu zazzabi ne ze kamata ta kudundune dakyau haka yadawo yasame ta hakanne yasashi dauko mata kaya yasa mata don zumbulelen hijab dinta datai sallah dashi ne a jikin ta se towel,be koma bacci bah yashiga kitchen yashirya musu abin karin kummalo, har kan bed din yaje yabata tea tasha da pain relief ta koma ta kwanci bacci me nauyi yay awon gaba da ita,
muhammad baccin da be koma ba kenan yay wanka ya shirya ya tafi gidan auntien tashi safiyya ko ince sirikar sa, 8 da dan wani abu lokacin daya shiga gidan 'yan adamawa sun gama shirun su natafiya safiyya sam fuskarta babu fara ah sabida bata kaunar rabuwa da 'yar uwarta daddy yanata lallabata don ko kadan bayason tasawa kanta damuwa, har suka tafi meenal batasan wainar da ake toya bah, gida ya rage daga twins se nabiha da safiyya se 'yan aikinsu gidan yay misu shiru da yawa duk sunajin babu dadi, daddy da muhammad kuwa hospital suka tafi gurin auntie suna zuwa suka sami asiya aminiyar ta agurinta, itama rayuwar ta abar tausayi takoma don tamkar mabaraciya haka ta dawo ashe tun tuni mijinta yasaketa, sakamakon makudan kudin data sace masa har prison seda tayi to fitowar ta kuma tanemi abokin shedin nata ta rasa yagudu da kudin iyayenta bawani karfine dasu bah saboda hakane gaba daya rayuwar ta ta lalace se kuka take ganin yadda itama rayuwar aminiyar ta ta takoma.

(Rayuwa kenan ita dama duniya haka take Allah yana arawa mutum dama ne, Allah kasa mudace duniya da lahira)

To bangaren amarya nanah kuwa da yousep tun randa aka kaita gidan yashiga dakin nata bekara lekataba ranar mah dokoki ne ya shimfida mata su, idan kadaici ya isheta ne zata je gurin mom da nadiya susha firar su duk da rashin kulatan dayake yana damunta kuma bata taba furta kowaba don bawanda yasan irin zaman dasukeyi a gidan ko magana baya mata se in a gaban mom ne.

BAYAN SATI BIYU

Komai yanzu ya lafa na hidimar biki kowa hutunsa yake abinsa,
Gidan muhammad
Yana zaune a parlour meenal tana kan cinyar sa a kwance sunata fira yana wasa da suman kanta suna kallo a TV, abinda tagani ne yasata yin dariya tace." Ya muhammad abin mamaki duk girman mutum fah sekaga yana yiwa matar sa kuka,
Murmushi muhammad yay don yasan inda zancen nata ya dosa shi takeson tsokana,yace." Eh hakane amma kuma suma matan fah abinda sukeyi fah ai yama wuce misali nidin nan shedane don anyimin basau daya bah ma kuwa, wata zata fara Ahhhhhh! washhhhhhh! ya muhammad ka kashe ni wlh wayyo daddy zan..... Baki meenal ta tsoshe masa tana dariya sosai yadda yake kwatan tawa abin dariya ga kunyar data isheta, tura baki gaba tayi tace." To ni daga nafadi gaskiya ay dai naga bani kadai nakeyi bah"
muhammad yana dariya yace. "Bawani nan kada ayimin sharri"
Kada idanu tayi itama zata soma kwatan ta abinda yakeyi to amma yadda ya kafeta da idanu ne yasa ta kasawa tanajin kunya tamike tashige bedroom da gudu tana dariya,Shima kuma hakan yana dariyar ya kashe kayan kallon yaname cewa." Yarinya kinjawa kanki tunda kika tsokane ni zakiyi bayani yau" seda yagama kashe kayan kallon yabita dakin.

BAUCHI

Mimi yanzu tasaki jikinta da mujaheed sosai suke cakal kalar amarcin su tawani murje tasoba kiba kamar ba itaba don kulawa sosai mujaheed kebawa amaryar tasa haka mom take kulawa da ita basada wata matsala suna zaune lpy abinsu gwannin ban sha'awa.
Gidan daddy mah yanzu yakara kwantarwa da safiyya hankali life suke cike da farin ciki su muhammad kullum da daddare se sunshiga gidan ansha fira hakan kuwa bakaramin faranta mata yakebah, sedai karkashin zuciyanta imam kullum take tunani shin koyana wani hali yanzu.
auntie kuwa har yanzu tana asibiti suna zuwa akai akai suna dubata nana kuwa duk randa taje gun mahaifiyar tata tana kuka take komawa gida don lamarin ta se du ah ei kam, gidan tama daddy gaba daya ya sallami 'yan aikin cikinsa se gate man kawai yanzu ke kula da gidan,( Allah sarki rayuwa )

To Nana rayuwa take da dadi ba dadi gidan auren ta haryanzu babu abinda yasauya zani tsakanin su kuma babu wanda yataba sani har kawo iyau sau daya muhammad yabar meenal taje gurin nana shima don yaji labarin baya nan ne yousep din,
Kimanin wata uku kenan da tafiyar yousep din training na Army shima ze gaji mahaifin sa, yau takama friday kuma ze dawo, tunda suka tashi ake shirya masa abin cin cika kala kala, kullum cikin mom cikin tsuma sirikar tata take da magun guna dagyarata hakan kuwa yasoma yima nana aiki sosai, tarasa yadda zatayi ta fadawa mom irin zaman dasukeyi da dan nata, ga magun gunan datake dirka mata suna sakata feeling sosai, seda suka gama aiki ne zataje tayi wanka mom takirata dakin ta kamar kullum tabata wani abu a bowl tace tashanye shi kafin ta tafi,
Kallon bowl din nana tafara kamar tayi kuka saboda tagaji kam gaskiya, da mamaki mom tace." Wai nana meyasa ke bakisan gyara kanki ne kamar ba wayay ya, sekace bakisan yadda mazan nan na zamani suke bah mussam man nawa dan ma a gurinki kullum burina shine na kankaro miki mutumci amma ke gani kike kamar ina takura miki " jikin nana a sanyaye tasoma magana don dole yau tasanar mata abinda yake faruwa bazata yadda ta cuci kanta aita dirka mata abinda ze ringa hanata bacci tana fama da ciwon mara." Mom kiyi hakuri bahaka bane wlh baki fahimce ni bane inasone mugama daidaita tsakanin mu dashi tukunna komeye mah senayi"

Mikewa mom tayi cikin wani yanayi tace "nana mekike nufi?" shiru tayi mata kawai ta sukuyar dakanta kasa, cikin tsareta da idanu mom tace nana gaya min tsakaninki da Allah yousep yataba kwanciya dake ko a ah Kada yimin karya ki gayamin gaskiya,
Jikin nana a sanyaye ta girgiza mata kai, cikin kaduwa kuwa mom tasaki bowl din hannun nata tana salati, idonta taf da kwallah tace." Lallai yousep yau ka tabbatar min da kai ba yaron arziki bane aikuwa wlh kataro wa kanka yau zaka hadu dani sena bala in bata maka rai mara mutumcin yaro, kiyi hakuri nana tunfar ko dakin yimin nayani daban ringa baki abubuwa bah haka"
Jikin nana a sanyaye tace." Bakomai mom pls kada kiyi masa maganar ranshi ya baci insha Allah zamu daidaita kanmu" sakin baki mom tayi tana kallonta cikin zuciyanta kuwa tana jara gidewa Allah daya bawa dan nata mata me kaunarshi da gaskiya,
Cikin shan mur mom tace." Kina nufin nakyaleshi muzuba muku ido yana daukar alhakin ki,sam naze yiwubah" idon nana tafda kwallah tace "Na rokeki mom ki kyaleshi karkice mishi komai zamu daidai ta ni baya daukar alhaki nah ina yimasa uzuri" ganin nana dagaske take ta dage ne yasata kyaleta tashiga wanka....

TAKU A KULLUM NANA BMB

08147110349

TSOKACI!!

Daga sabon book dina mesuna.

JARABTAR MU

Love story

Hannu yasa yakama kuma tunta gami da sakar mata murmushin dayake tafiya da zuciyan ta aduk sanda yayi shi,cikin sanya yay yar muryar sa yace." my beautiful wife ya kike?" kasa jurema kallon sa tayi ta lumshe idanun ta, seda yakare mata kallo tukunna ya hura mata iska a face din tata bashiri tabude idonta, murmushin kawai yayi yakoma kan kujera yazauna gami da gyaran murya yace." mufeeda ina mummy? kafin tayi magana sukaji saukowan ta daga sama yakuwa zuba mata idanu harta zauna shikuma yasauka kasa yazauna yana me gaisheta, sedai ko inda yake bata kalla bah don dama tuni annurin fuskarta yadauke na ganin shi datayi, ita da mufeeda TV kawai suka zubawa ido duk da ita rabin hankalin ta nakanshi tana satar kallon shi, seda ya sauke ajiyan zuciya yace." mummy kinga JARAFTAR MU! mu kuma" muryanshi sosai ta canza kamar zeyi kuka yacigaba dacewa" Heedaya ta haifamin 'yan uku yau"
Suduka cikin firgici suke kallon sa, tsam mufeeda ta mike tazo ta tsugunna gefensa tace." Ya adnan kasan abinda kake cewa kuwa? kuka mummy tafara tana cewa." Allah ya isanmu Adnan shikenan ka gurbata mana zuri armu ka lalata mana suna, 'ya'yan zina a cikin family din mu! INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI UN! shikawai take nana tawa, " Kacuci rayuwarka Adnan da tuni matarka mufeeda keda wan nan yaran! tahanyar zina zaka fara tara naka iyalin wan nan waca irin kaddarar rayuwace?.....

LITTAFIN JARABTAR MU! NA KUDINE ZEZO MUKU A FARASHI ME SAUKI👌

ALLAH KASA MU DACE DUNIYA DA LAHIRA!

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.