Complete Hausa Novels

Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 12 of 43

*Page 56 to 60*

Dakin Mama ta shiga tana nuna mata kudin, Chak ta tsaya ganin Mama zaune tana kuka gaban Sulthana dake kwancd Warwas Bata numfashi, A Hankali ta Sulale ta Zauna a Wajan Tana K'allan Mama
"Mama Meyasa kike kuka"
Cigaba da Kukan Mama tai Dak'yar ta Iya Cewa
"Sulthana Bata Numfashi, Allah dai Yasa bah rai baneh Yayi Halinsa"
Mik'ewa Zumbur Ameenatu tai ta Fita Ta nufi Dak'in Baffa, A Rufe ta Sameshi Alamar Ya Kulle daga Ciki. Dukan Kofan ta fara tana magana cikin daga murya saboda ya jiyota
"Dan Allah Baffa ka bude kofan, Sulthana bata numfashi ka tashi dan Allah mu Kaita Chemist"
Kuka Take sosai a wajan tana cigaba da buga kofan anma a banza, Hafsatu da tunda ta fara bugawa ta leko daga dakinsu tace
"Yaya Ameenatu ku daina damuwa da Lamarin Yarinyan nan, Wanda ma ya haifeta bai damu da Itaba Balle Ku"

Mari mai rai da Lapia Amenatu ta Wankama Hafsatu tana huci
"Hafsatu na lura Iskancinki k'ara Gaba yake, Tho Wallahi ki sani idan baki sauke gigin dake Kanki bah Sai nayi maganinki a gidan nan"
Kuncinta tah Rik'e baki bude
"Dan Nafada muku gaskiya shine zaki Mareni"
Tsaki Ameenatu taja ta Shiga Dak'in Mama a Fusace.
"Mama tashi Muje Chemist, Insha Allahu bah abinda zai Sameta"
Mik'ewa Mama tai tadau Hijabinta Tasa, Ameenatu ta Mik'e Sulthana Tsaye
"Mama Samin Ita a baya na Goyata"
Taimaka mata tai tah Goyata Suka Fito Suka Fita Daga Gidan, Dare Ya soma yi dan Sahu har sun Fara daukewa. Tafiya Suke dasauri sauri Mama na Haska musu Hanya da Torch light, Akwai Tazara sosai Tsakaninsu Da Chemist din Saboda Shi Kadai Garesu duk Kauyen..

Saida Sukai Tafiya Mai Tsayi Sannan Suka K'arasawa Wajan, Koda Sukaje sun Tadda Mutane Sosai a Wajan, Sauke Sulthanan Ameenatu Tai Mama Ta Rungumeta a jikinta ita Kuma ta k'utsa Cikin Mutanen
"Dan Allah Ku Taimaka, Yarinya ce Bata Numfashi ina Likitan"
Mutanen da Suk'a bi Layi Kowa Ya Tsaya Suka Shiga da Ita Cikin Dakin Maganin, Kwantar da ita akai a irin Gadon Marasa Lapaia dake Dakin, mutumin Ya dauko Sthethoscope Yasa a K'irjinta Cikeda Fargaba, jin Zuciyarta Na Harbawa Yasa Ya Sauk'e ajiyan Zuciya. Ameenatu daketa K'allanshi Hankali Tashe Tace
"Likita ta mutu koh?"
Kai Ya Girgixa mata Sannan Yace
"Bata Mutu bah tanada rai, Anma maiya Sameta"
Itama Ajiyan Zuciyan tai Tana K'allan Sulthanan
"Ruwa neh ya mata duka dazu shine ta dawo gida tana numfashi Sama Sama"

Baice Komai bah Sai Gani datai ya Hado wasu Allurai Guda Biyu Ya mata Sannan Ya Dauko wani ya mata a Hannu. Ganin Abubuwan Dayake Yasa Ameenatu Tai Saurin Cewa
"Likita Wallahi Bamuda kudi Dari biyar ce a Hannun mu ka taba magani K'awai"
Juyowa yayi ya K'alleta tareda Murmushi
"Karki damu, ni Likita ne nazo Kauyen nan dan Taimaka ma Alumma kuma Kyauta nakeyi"
Murmushi ne Ya subuce mata har saida Fararen Haqoranta Suka Baiyana. Cigaba Yayi da Abinda Yakeyi Har drip yasa mata Sannan Ya maida dubanshi da Mama Dak'e Tsaye
"Mama Samu Guri ki Zauna Dan Bah Yanzu Zaku tafi bah Har sai Ruwan dana Sah mata ya K'are Sannan kuma ta Farfado"

Wuri yaba Mama Ta zauna tana mai Godiya, Baice komai bah Sai Murmushin dayakeyi. Ameenatu ta matso inda Mama take Zaune Ta sadda kai Kasa tana cewa
"Mama ki koma gida, Banasan Abinda zaije ya dawo, karki Damu Insha Allahu komai zai daidaita. Kada Baffa ya fito bakya nan"
Tho Mama tace Tareda Mik'ewa tai Musu Sallama Ta Wuce Gida. Har Likitan ya Gama Bah duban Mutanen Dake waje Magani Anma Sulthana Bata Farka bah, Dak'in ya Shigo Tareda Cire Lapcoat din dake Jikinshi. K'allanshi Ameenatu tai
"Likita Har yanzu bata Farka bah"
Juyowa yayi ya K'alleta Yana Y'ar Murmushi
"Karki damu Zata Farko koda xuwa Safe neh"

Ameenatu Batace Komai bah ta Maida Dubanta ga Sulthana Dak'e Kwance.
Wayoyinshi Dake kan Table ya dauka Tareda Briefcase dinshi Sannan Yace
"Yan Mata Zan Tafi Masaukina"
Key din Chemist din ya Mik'a Mata Yana cewa
"Nasan Sai nah dawo ruwan zai k'are dan Haka Ga Key ki rufe Kofan Karki bude har sai idan nine nace miki nazo"
Hannu bibiyu ta Amsa tamai Godiya, Torchlight ya Mik'a mata Sannan ya Fita Ita kuma ta Tashi ta Rufe Kofan Ta dawo ta zauna...

Bacci ne Ya kwasheta a Wajan bata farka bah Saida Dataji Ana Kiran Sallan Asubah, Mik'ewa tai dasauri Sai a Sannan ta tuna Bah Gida tak'e bah, Sulthana ta k'alla taga ta juya Kwanciya. Murmushi tai ta tabata
"Alhamdulillahi, Allah Ya baki lapia"
Dube dube ta soma yi koh zata samu ruwan Alwala, Anma bata samu bah. Haka ta zauna har Gari yayi Haske Tangaran har ta soma jin hayaniyar mutane Bakin Shagon Alamar Magani sukazo Amsa, Jin Ana dukar kofan Yasa Tace
"Waye"
Muryan Likitan Ta jiyo yana cewa
"Bude Nine"
Bah Musu ta Bude kofan Ya Shigo Yana K'allan Sulthana. Gaidashi Ameenatu tai Ya Amsa Da Y'ar Murmushi a Fuskarshi
"Ya Jikinta"
Dasauki Ameenatu Tace K'anta a K'asa, Karasawa yayi inda Sulthanan keh Kwance Ya soma Dubata, A Hankali ta bude ido ta daura su akan Kyakyawan Saurayin Dake Tsaye a Kanta
Mik'ewa Tai dasauri tana K'allanshi Shima ita Yak'e Kallo. Kauda kai tai tareda Bin dakin da K'allo, Ameenatu ta Gani zaune tana K'allanta ta mik'e Tana kokarin Sauka daga Gadon, Saurin Rikota Ameenatu tai tana cewa
"Ina zaki bayan Bakida Lapia"
Sai a sannan Taji zafi a Hannunta, Duba Takai Wajan tana Hannunta da Allura Ruwa na Bi. Tabe Baki tai Ta zauna Tana Yatsine Fuska. Tunda Ta bude ido bah Abinda Likitan nan keyi sai K'allanta Kamar zai Cinyeta. Ganin Irin Kallan Da yak'ema Sulthana Yasa Ran Ameenatu ya baci Zuciyarta Tahau Mata zafi...

*Tho! Kunjimin Wannan Ameenatun, Tho me Take Nufi*

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.