Complete Hausa Novels

Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 29 of 43

*Page 141 to 145*

K'arfe hudu a kauyensu Sulthana tayi musu, bayan layinsu Sulthana sukai Parking motarsu, yaro sula samu suka hadashi da sabuwar dari biyar ya musu k'iran Babban Almajirin Mallan. Sai washe baki yaron yak'e dagudu ya nufi runfar Almajiran, yakoyi Sa'a ya sameshi zaune shi kad'ai a dakinsu yana karatu. Tare suka k'araso wajan sannan yaran yabar gurin cikeda murna..

Musabaha suk'ai Sannan Sa'ood yace
"Sunana Sa'ood sai abokina Fareed, mu yan cikin garin kano neh. Munzo akan maganar wata yarinya Sulthana munasan musan labarinta dan gwamnati na buk'atar a taimaka ma yara masu irin shekarunta"

D'an jim yayi Sannan ya dago yace
"Ni sunana Sani kuma Almajiri neh ni, kuyi haquri bazan iya fadan wani abu dangane da cikin gidan Malamina nah"

Hannu Fareed yasa a Aljihu ya ciro bandir din y'an dari biyar ya mik'a mai yana cewa
"Kah taimaka, ka fada mana munaso neh mu taimaka mata"

Jim Sani yayi yana tunani Shi kanshi bayasan abinda akema Sulthana a gidan, yanke shawara yayi kawai ya fada musu dan haka yace

"Kuzo ga Bakin bishiyar chan akwai inuwa sai mu zauna"

Bah musu suka nishi suka zauna, nan Sani ya soma basu labari tiriyan tiriyan iya abinda ya sani. Kuka neh kawai Fareed beyi bah anma idanunshi sunyi jah, shi kanshi Sa'ood hankalinshi bah k'aramin tashi yayi bah. Sa'ood neh yayi k'arfin halin cewa

"Mallan Sani anya kuwa Mallan neh ya haifeta"

Dagowa yayi dasauri yana k'allanshi da Mamaki

"Shine mahaifinta mana"

Girgiza kai Fareed yayi fuskansh bah Annuri

"No bashi ya haifeta bah, dan mahaifi bazai taba muzgunama D'anshu haka bah"

Sani yayi murmushin takaici Yace

"Mallan jamilu shine ya haifi Sulthana, duk kuma wanda zaka tambaya a kauyen nan abinda zai fadama knan"

Fareed neh ya mik'e dasauri yana k'arkade rigan jikinshi, Sa'ood ma ya mik'e yana k'allan Sani

"Mungode sosai Sani, zamu tafi idan bukatar k'ara ganinka ta taso zamuzo mu sameka"

Shima mik'ewan yayi ya basu hannu sukai musabaha

"Bbu komai ai ina maraba da dawowanku matukar za'a san yanda za'ayi a taimaka ma Sulthana"

Kudin Fareed ya mik'a mai, ya nok'e yaki k'arba

"Kubar kudinku, Allah dai ya baku sa'an niyyan da kuka dauka"

Ameen sukace suk'a k'arami godiya. Kasa driving Fareed yayi Sa'ood ya amsa keyn motan suka bar wajan kowa da abinda yak'e sakawa a Ranshi..
Fareed yayi ajiyan zuciya yana k'allan Sa'ood

"No mattet how hard the situation will be, no matter how bad. Sai na fitarda Sulthana daga k'angin nan datake ciki, koda kuwa zanyi asarar dukiyana da matsayina matsawar zata kasance cikin farinciki da Annashiwa"

Girgixa kai kawai Sa'ood yayi baice komai bah har suka k'arasa gida..

Ala ala Mami tak'e Daddy ya dawo, bai dawo gidan bah sai wuraren k'arfe goma da rabi na dare. Saida yaci abinci ya huta sannan Mami ta sameshi a office dinshi dake cikin gidan, zama tai kusa dashi
"Sannu da hutawa"

Da Fara'a yadan juyo yana k'allanta

"Sannu uwargida sarautar mata"

Murmushi tayi Sannan tace

"Alhaji inaso neh muyi magana dakai kuma naga kamar kana busy"

Takardun hannunshi ya aje ya matsar da system din dake gabanshi

"Ina jinki"

Jim tai tana k'allanshi Sannan tace

"Akan Maganan Masroor neh, yana daki tun dazu yak'i cin abinci sai aikin kuka yake, saima danai ma Yasir.."

Saurin katseta Daddy yayi hankali tashe

"Meke damunshi? Meyasa yake kuka?"

Nan Mami ta kwashe duk abinda ya faru ta sanar dashi Sannan ta fadamai yanda sukai da Yasir .

Baice komai bah yadau waya ya soma neman layin Masroor, yana dauka yace

"Kah sameni a falona"

Bai jira mai zaice bah ya kashe wayan sannan ya mik'e yana k'allan Mami

"Muje falona"

Koda suk'a karasa falon sun sameshi zaune akan Carpet kanshi a k'asa. Daddy ya zauna kusada shi yana k'allanshi

"Son meke faruwa? Karka boyemin fadamin damuwanka"

Baice komai bah k'anshi na k'asa, k'ara magana Daddy yayi Sannan ya d'ago jajayen idanunshi yana k'allan Daddy

"Daddy inada wacce nakeso but.."

Shiru yayi ya kasa k'arasa maganan

Daddy yayi murmushi

"Go on ina jinka"

Masroor ya sunkuyar dakai sannan ya cigaba

"Sunanta Sulthana ina santa daddy kuma babanta yace zai aura mata almajiri"

Daddy ya k'alleshi da mamaki

"Almajiri"

Kai Masroor ya gyada, daddy ya nisa yace

"Wanene Mahaifinta a garin nan"

Gaban Masroor neh ya fadi jin abinda ya fada, Mami tai saurin amshewa

"Alhaji inace munyi wannan maganan tun achan"

Hannu Daddy ya d'aga mata alamar tai shiru yace

"Ina jinka"

K'ara sunkuyar dakai yayi

"Daddy babanta bah kowa baneh a kauye suke"

Har daddy ya bud'e baki zaiyi magana Mahnoor ta shigo falon dagudu, jikin Mami ta d'ane tana kallan Daddy tana dariya

"Daddy uh welcome"

Murmushi daddy ya mata
"Thank uh my baby, ya school?"

Ta amsa da lapia lau. Hade rai Mami tai

"Tashi min a jiki, bakiga muna magana baneh kin wani shigo bako Sallama"

Zumbure baki tayi ta mik'e zatabar wajan, daddy yace

"Kyalleta zo nan abinki babyna"

Da d'an murmushi ta k'arasa ta zauna kusada Daddy.

"Maminku ta fadamin duk yanda kukai da ita, da kuma yanda zukai da yasir. So zan fara sawa a bincika min Yarinyar da Asalinsu idan har babu matsala insha Allahu she will be ur wife"

Dago kai yayi da Fara'a yana k'allan Daddy

"Daddy dagaske?"

Murmushi Daddy yamai tareda kyada kai. Mahnoor ta k'alli Masroor

"Bro Sulthana?"

Kai ya gyada mata Cikeda farinciki

Tsalle sukaga Mahnoor tahauyi tana murna, Mami da mamaki tace

"Ina kika santa"

Tsagaitawa tai tana k'allan Masroor. Da rarrafe ya matso kusada Daddy ya zauna kusada k'afarshi yanatamai Godiya Sannan ya mik'e yana hararan Mahnoor yabar wajan. Tasan mai yake nufi, murguda baki tayi ta juya tahau bah su Mami labarin zuwanda sukeyi gurin Sulthana..

Mami ta tausaya mata sai taji tanasan yarinyan tun bata hadu da ita bah...

Kwana biyun nan da Masroor baizo bah kullum Sulthana batada aiki sai kuka. Hakan yasa takanje gidansu Sadiya idan tadau tallan dan ta debe mata kewa. Yau tana zaune bakin tasha tayi tagumi tana k'allan hanyar da Masroor ya saba biyowa. Kamar a mafarki taga motarshi ya doso wajan, dasauri ta mik'e ta karasa inda yayi parking. Fitowa yayi yana mata murmushi, zumbure baki tayi ta juya ta koma inda take zaune

Murmushi yayi yabi bayanta, kusa ita ya zauna yana k'allanta. Kauda kai tayi ya juyo da fuskanta. Hawaye ya gani na gangarowa daga idonta

"Omg! Haba Beauty meya faru? Meyasa kike kuka"

Ai kaman jira take ta fashe da kuka harda shesheka, kanshi ya dafa

"Pls stop crying banasan kukanki beauty"

Hankie ya dauko ya soma goge mata hawayen dake fuskanta yana murmushi

"Me aka miki kike kuka?"

Zumburo baki tai

"Bakai baneh ka daina zuwa bah kullum sai nazo nan ina jiranka"

Kallanta yayi da Mamaki

"Kinyi kewana neh?"

Hannu tasa ta rufe fuskanta tana murmushi, shima murmushin yake cikeda Farinciki

"Oh come on! Fadamin kinyi kewana?"

Kai ta gyada mai, murmushi yayi mai sauti

"Nima nayi kewanki beauty, idan natambayeki wani abu zaki fadamin?"

Eh tace tana kallanshi, saida yayi jim sannan yace

"Kina sona?"

Dasauri ta mik'e tabar wajan tana dariya. Shima dariyan yayi kasa kasa, dakyar ya lallabata ta dawo ta zauna yace

"I so much love uh my beauty ina sanki sosai"

Hannayenta biyu tasa ta rufe fuskanta tana murmushi...

Shakuwa mai k'arfi ya k'ara shiga tsakaninsu, har Mami da daddy sun saba da hiran Sulthana da Masroor ke musu kullum. Lokaci nata tafiya, har yanzu bah abinda ya chanza dangane da k'iyayar da Baffa kema Sulthana...

*Bayan wata d'aya*

Alhamdulillah anyi Election Allah yaba Daddy sa'a yanxu shine gwamnan Jahar Kano, Alhaji shuaibu mahaifin Fareed shine mataimakinshi. Bayan komawansu government house Masroor ya matsama Mami akan zuwa gidansu Sulthana saboda nan da sati d'aya zai koma school, Mami na samun Daddy da maganan yace

"Nima abin na raina mantawa nai ban fada miki bah, gobe in Allah ya kaimu za'aje nema mai aurenta"

*tho fah* anya kuwa?

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.