Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 19 of 43
*Page 86 to 90*
"Yarinyan nan tana cikin damuwa"
Kamar zai bita ya fasa ya shiga mota ya nufi Cikin garin kano. Zama tai Bakin Bishiyan Data saba Zama, Gyadan ta soma saidawa kamar yanda ta Saba. Atika dake kusa da ita tana saida Rogo ta yafici Ladi tana nuna mata wata hadaddiyar mota datazo wucewa
"Kai Ladi ji Wachan motan, Tafdi! Ni tunda nake ban taba ganin mota mai sama a bude bah"
Kyalkyacewa da dariya ladi tai tana tafawa
"Kai Wallah Motan nan Akwai Kyau, Allah ka bamu irin wanna motan"
Jin Yanda suke zuzuta motan yasa Sulthana ta dago ta K'alli motan, Lallai kuwa motan yanada Kyau, Murmushi ta soma tanabin Motar da K'allo. Duk mutanen dake K'asuwan kowa bin motar yake da K'allo cikeda Sha'awa, Wanda ta gani Cikin motan neh yasa Fara'ar dake Fuskanta yakau, Hijabin Fuskanta ta Turo Gaba ta Rufe Fuskanta dashi..
Zagaye yake yana yatsine Fuska, Waje ya samu yayi Parking Sannan ta fito. Mata sa binshi da K'allo suke harda Mazan, Dan D'an gayu neh na K'arshe. duk gungun Yara masu talla daya gani sai ya tambaya tareda Fadin sunanta anma duk suce basu santa bah, Ganin Yana Kokarin nufosu yasa Sulthana ta mik'e tana K'okarin daukan trayn Gyadan tah k'araf suka hada ido, Dauke kai tai Ta dauki Trayn Gyadan ta Fara tafiya. Binta Yayi tateda Kiran sunanta, Juyowa tai ta Murguda mai Baki
"Kah daina kiran sunana kuma ka daina bina"
Murmushi Yayi yanda ta murguda bakin Saita k'ara mai kyau
"Meyasa zakice na daina binki"
Batareda ta juyoba tace
"Nidai Dan Allah ka daina bina kada Yaya hafsatu ta ganmu taje ta fadama Baffa, Idan ta fadama Baffa dukana zeyi, Jiyama saida ya dakeni"
Tausayi ta bashi Ya sha gabanta yana K'allanta
"Kiyi Hakuri nasan mu muka ja miki dukah koh"
Batace mai komai bah tana k'okarin tafiya, hannu ya daga mata Yana cewa
"Tsaya mana, kudinki na jiya nakeso na Baki"
Kauda kai tai gefe
"Kah barshi, nidai dan Allah ka bani Hanya na Wuce"
Matsa mata Yayi ta soma Tafiya Yana K'allanta, meya tuna ya bita da Sauri tareda shan gabanta
"Tsaya tho kiji"
Tsayawa tai hannunta d'aya a kugu
"Inaso gobe mu hadu a Inda kike saida Gyada kamar wannan lokacin kinji"
Batacemai Komai bah ta cigaba da tafiya abinta. Binta yayi da K'allan tausayi, A Ranshi Yana raya
"She's Cute n Young, She need help. No matter how Zaki Kasance Cikin Farinciki nan daba"
Motarshi ya nufa dan komawa gida, Yara ya gani Yayyabe da Motan Sunata Shafawa, K'arasawa yayi dasauri ya koresu. Ganin Sunki Tafiya yasa ya Dauko bandir din yan Hamshin ya soma Raba Musu, ai a nan yaga wawaso harda manya. Tausayama Halinda yan K'auyen suke ciki yayi. Motan ya shiga ya tada Yabar kauyen Cikeda Tausayin Sulthana...
Gida Ya nufa Kai Tsaye, Horn yayi masu Gadi Suk'a budemai kofa, Saida yayi Parking Sannan ya Fito. Bodyguards din dadd ya gani a tsakar gidan, Murmushi Yayi
"Wel daddy is back"
Main palour ya nufa tareda Danna Bell, wata mai Aiki ce ta bude Tareda Zubewata gaidashi, Bai amsa bah ya Shiga falon Yana Fara'a Baiga kowa A falon bah. Wani Corridor ya nufa wanda zai sadashi dah Dinning area, a nan ya gansu zazzaune suna Lunch. Sallama yayi ya k'arasa ya rungume Daddy Yana dariya,
"I Missed uh Daddy"
Murmushi Daddy yayi Yana Shafa Kanshi cikeda Zolaya Yace
"Sai Kace nayi shekara kwana biyu fah nai"
Turo baki Mahnoor tai tareda Rungume Hannayenta
"Daddy kacema Bro Masroor ya daina Rungumeka shi babba neh"
Zama Masroor yayi akan Kujera suka fashe da Dariya duka, Hararanta yayi
"Lallai baki isah bah, Ai daddy nane"
Idonta ne ya ciko da K'walla ta kara hade rai tace
"Daddy na dai"
K'ara Fashewa da dariya sukai duka. Ganin Sunata mata dariya yasa ta fashe da kuka ta mik'e Tabar wajan tana kuka..
Hararan Masroor Daddy yayi
"Kaga kah koranmin Baby koh, Tho Maza ka tashi ka Lallasheta ta dawo taci abinci"
Turo baki Masroor Yayi yana Kai Loman Abinci
"Daddy kah kyaleta cikin wah Bah nata bah, Karta Cin"
Lekowa Mahnoor tai Tana Share kwalla
"Baza'a kyaleni din bah."
Guntse Dariya Mami da Daddy sukai dan Yanzu sunayi zasu takalo Rigima..
Rungume Mami tai ta Baya ta shagwabe Fuska
"Mami yanzu bro Masroor baya sona, Bro Yasir ne kawai ke Sona"
Cup din Juice Masroor ya dauka ya kora Sannan ya aje Yana cewa
"Kedai kika sani"
"Ahan ina Kaje dazo baka fadama Yasir bah, yazo nemanka neh kuma nasan din inda zaka tare kuke zuwa"
D'an jim yayi sannan yace
"Eh wannan fitan ni kadai neh, Banda Shi"
Murmushi Daddy yayi cikeda Nishadi
"Koh anje Wajan Sirikan nawa neh"
Suman Kanshi Ya Shafa Yana Y'ar Dariya.
"Aa Daddy"
Mami Itama Dariyan tai
"Ai dama bazaka fada bah, tho bari kaji gwara fa kama fada tun yanzu coz ana gama Hayaniyar siyasan nan Zamuje neman aure"
Turo Baki Masroor Yayi ya mik'e yabar Dinning din...
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.