Complete Hausa Novels

Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 26 of 43

*Page 126 to 130*

Bata jira mai zaice bah ta fara tafiya tana waigenshi tareda daga mai hannu. Binta yayi da k'allo harta bace ma ganinshi, Ajiyan zuciya ya sauke sannan ya shiga motarsa yaja yabar wajan...

Saida ya shiga cikin gari sosai Sannan yadau waya ya soma kira, ana dauka yace
"Am on my way na kusa gida"
D'an murmushi yayi Sannan yace
"Ok sai kah karaso"
Ya kashe wayan ya tura a aljihun shi. Bai zame koh ina bah sai gida, a haraban gidan yaci k'aro da Mahnoor ita da wasu masu aiki tana tayasu shara, girgiza kai kawai yayi ya nufi side dinshi. Tana ganin ya wuce ta aje tsintsiyan ta bishi, wanka ya farayi sannan ya fito Cikin Threequaters dah T shirt fari kal, zaune ya samu Mahnoor a falonshi tana K'allo, jin Karan bude kofa ta shagwabe fuska ta dago tana kallanshi
"Bro Masroor shine ka tafi bakaje dani bah koh"

Zama yayi kusa da ita ya kamo hannunta
"Am sorry sis, kinga fah bakwa nan and I cnt wait har sai kun dawo, dnt uh worry wata rana nan zata dawo ku zauna tare"
Zaro ido tai ta saki murmushi
"Allah dagaske bro Masroor"
Kai ya gyada mata shima yana murmushin _kujimin wannan masroor din fah taya zata dawo gidansu_

Phone dinshi yadau ringing ya dauka Sannan yace
"Ok ganinan zuwa"
Ya kalli Mahnoor wacce itama shi take kallo
"Barinje nayi bako"
Tare suka fito ita ta nufi side dinsu shi kuma ya fita wajan gate, a kofar gidan ya ganshi zaune Cikin mota, karasawa yayi yana y'ar murmushi
"Uh welcome old friend"
Dariya yayi Sukai musabaha, Masroor yace
"Wai gidan bakonka neh dah bazaka shiga bah"
K'asumbarshi ya shafa yana y'ar murmushi
"Banasan Mami ta ganni neh dan nasan sai nasha surutu"
Dariya Masroor yayi mai sauti
"Surutu koh sai kasha shi indai mami ce, saidai kah rufe ido kah toshe kunnuwan kah"

Yasir neh yayi parking ya fito yana murmushi
"Kai wah nake gani haka?"
Hannu yabashi suka gaisa "Dama ana ganinka"
Dariya yayi
"Yasir knan dama kana nan?"
A tare suka shiga cikin gidan zuwa side din Masroor, maids din gidan suka shiga hidima dasu. Jin surutu na tashi daga side din Masroor yasa Mahnoor ta shiga side din tana rarraba ido, dagowa bakonsu yayi yadan zare ido
"Wah nake gani nan kamar Mahnoor, lallai kin zama big girl"
Murmushi tai ta k'arasa kusada shi ta zauna
"Bro Sannu da zuwa"
"Yauwa" yace yana shafa kanta yana murnushi. Zamewa tai daga jikinshi ta fita daga daga side din... batafi minti biyar da fita bah wayan Masroor ya soma ruri..

Dauka yayi yasa a kunni sannan yayi murnushi yace
"Ok gamu nan zuwa"
Dariya ya saki mai sauti yana shafa sumar kanshi, binshi da kallo sukai da mamaki, sai dayayi mai isarshi Sannan yace
"Numbernka ya fito Mami na kiranka, kuma nasan Mahnoor ce ta fada mata"

Dariya Yasir shima yayi
"Kace mai lefi neh?"
Kai masroor ya gyada yana cigaba da dariya a hankali. Murmushi yayi ya mik'e
"Tho ku tashi muje"
Bah musu suka tashi suka nufi side din Mami, A falonta suka sameta zaune da bakuwa, kan carpet suka ya zauna su kuma Masroor da Yasir sukai d'are d'are akan kujera, sunkuyar dakai yayi sannan yace
"Ina yini Mami"

Kallanshi Mami ta tsaya yo jin shiru yasa ya dago suka hada ido ya maida kai dasauri
Murmushi tai
"Likita bokan turai Kama daga kai kawai, wato kasan bakada gaskiya shine harda zama a kasa"
Dagowa yayi yana y'ar dariya
"Mami knan kiyi hakuri, bana zama neh shiyasa"

Masroor da Yasir sai dariya suke mai yanata susunne kai, Mahnoor ce ta shigo falon ta zauna kusadashi a Kasa
"Bro fareed zakaje dani wajan Umma"
_niko Ummy Abduol zaro ido nai jin sunan da mahnoor ta fada_ wah knan take nufi?

*manage dis banida chargi*

Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐

By *Ummy Abduol*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.