Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Sulthana Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 27 of 43
*Page 136 to 140*
*DA BAZARMU WRITERS ASSOCIATION*
Wannan Shafin Sadaukarwa ce gareku All *Da Bazarmu Writers Association* Members.. Allah ya bar K'auna.
Shekewa da dariya Hafsatu tayi harda tafawa
"Gaskiya neh Baffa haka yayi"
K'ara rushewa da kuka Sulthana tai jin Abinda Baffa yace, Saida tai mai isarta Sannan ta shigo cikin Gidan idanunta a kukumbure. Gyadan daya saba aje mata a kofar dakinshi ta dauka ta daura a wuta ta koma gefe tana cigaba da hawaye...
Yana dahuwa ta sauke ta zuba a tray, batayi mah Mama sallama bah ta tafi, inda suka saba zama ta hango Motar Masroor, ta k'arasa jiki asanyaye ta samu guri ta zauna batareda tamai magana bah. Sam bai lura da tazo wajan bah saida ya leko tah glass din motarshi sannan ya hangota zaune tayi tagumi, fitowa yayi dasauri ya k'araso inda take ya zauna
"Sulthana meke damunki"
Shiru tai k'anta a kasa
Ya marairaice Fuska yana cigaba da K'allanta
"Banasan ina ganinki cikin damuwa kinsan fah ina..."
Kasa k'arasa Maganan yayi ta dago jajayen idanunta tana kallanshi. Ajiyan zuciya ya sauke
"Meyasa yau kike so boyemin damuwarki? Nifah Abokinki neh kuma yayanki"
Hawaye ne ya gangaro mata, ta dago tana k'okarin Fashewa da kuka
"Baffa neh zaimin Aure"
"What?"
Fashewa da kukan tai ta duk'ar dakai K'asa
Rudu Masroor ya shiga ya mik'e ya dawo gabanta ya tsugunna
"Sulthana kin Tabbatar da abinda kike gayamin"
Batace komai bah sai kukan data cigaba
Suman kanshi yaja ranshi b'ace
"Pls Banasan kukan nan, ina jinshi har cikin raina. Just answer my question"
Ganin tak'iyin shirun yasa ya mike tsaye, k'ugunshi ya rik'e da hannu daya, dayan kuma yana cigaba da jan suman kanshi. Nan da nan idanunshi suka kad'a sukai ja
Tsugunawa yayi guiwa biyu a k'asa
"Pls stop crying, fadamin meya faru"
Cikin sheshekan kuka ta bashi labarin duk abinda ya faru
"No!!!" ya fada da k'arfi hakan jaya hankalin mutanen dake wajan suna k'allansu, bai damu da yanda ake kallansu bah saima cigaba da magana dayayi cikin D'aga murya
"No 1 can snach uh from me, u're mine."
Duk abinda yake fada bah wanda Sulthana tasan ma'anarshi idan bah no din bah, duk'ar dakai kawai tai saboda yanda mutane ke K'allansu
Gani tai ya mik'e ya shiga motarshi yaja yabar wajan da gudu. Bin motan tai da k'allo ta k'ara fashewa da matsanancin kuka, cikin muryan kuka take magana a hankali
"Shiknan yaya yayi fushi ya barni na shiga uku, meyasa Baffa baka sona? Menai maka??"
Hannu ta daura akai tana kuka wiwi
"Mama meyasa kika tafi kika barni? Kowa baya sona ki dawo dan Allah"
Mutanen dake wajan sun tausaya mata matuk'a jin kalaman datake fada..
Wasu ko basa sha'awar gyadan suna siya dan su rage mata radaddin datake ciki, haka taita bah mutane tana cigaba da kuka harta siyar. Hanyan da Masroor yasaba bi taketa k'allo tana hawaye, ganin bai dawo bah yasa ta mik'e jiki a sanyaye ta kama hanyar gida...
Gudu Masroor ke shararawa kamar zai tashi sama, Ikon Allah ne kawai ya kaishi gida, baiyi wani k'wakwaran parking bah ya fito ya nufi side din Mami idanunshi jawur. Bell ya danna aka bude mai ya shiga, masu aiki sai gaidashi suke anma baiko kallesu bah ya nufi falon Mami. Ganin bata falon sai bak'inta dake zaune suna jiranta yasa ya k'arasa dakinta, knocking yayi a kofar dakin ta amsa tareda tambayan waye
"Masroor" yace atakaice
Bashi umarni tai daya shigo
Yana shiga suka hada ido ta mik'e dasauri ganin yanda idanushi suka rune
"Son whats wrong"
K'asan dakin ya zauna yana cigaba da ajiyan zuciya
Mami ta k'araso kusadashi tareda dafashi
"Son tell me whats wrong pls, meke damunka? Why are you like dis"
Kama hannunta yayi ya ya dago ya k'alleta idaunshi Cikeda kwalla
"Mami som1 wnts 2 snach her from me, I love her, I so much love her. Shes my happiness, I cnt do without ha"
Fashe mata da kuka yayi ya duk'ar da kanshi kasa
Rungumoshi jikinta tai itama hankalinta tashe
"Its ok son, stop crying. Cool down and tel me meya faru"
Kasa magana yayi sai kukan daya cigaba dayi, dak'yar ta ja hannunshi suka mik'e tsaye, hannunshi ta rik'e ta kaishi side dinshi. Bedroom dinshi ta shiga dashi tareda zaunar dashi kan gado, tsugunawa tai ta ciremai cover'n dake kafanshi sannan ta mik'e tana shafa suman kanshi
"Its ok son have some rest, idan kah huta sai muyi maganan kaji"
Kai kawai ya gyada mata, ta fita daga dakin cikeda damuwa...
Masu aiki tasa suka kaimai abinci, anma koh kallan abincin beyi bah..waya Mami ta d'auka ta kira Yasir bai d'au lokaci bah ya k'araso gidan a rud'e. Falon Mami ya fara zuwa saboda tace ya sameta.
Da sallama ya shiga ya sameta zaune tana y'an rubuce rubuce. Zama yayi ya gaidata, ta amsa fuska bah walwala..
Duk abinda ya faru ta zaiyanama Yasir sannan tace
"Yasir nasan kai zakafi kowa sanin wanda Masroor yakeso, baya cikin hayyacinshi dats why ban tambayeshi bah"
Yasir yayi murmushi ya gyara zama yaba Mami labarin tun sanda suka soma ganin Sulthana har zuwa daukota da Masroor yayi da labarin data basu nata. Mami ta share k'walla tace
"Yasir meyasa tuntuni baku fadamin bah? Yarinyan nan bah kalar Masroor bace anma kodan yanda yak'e santa zan hakura kuma nasan Alhaji zai yarda"
Shiru yayi baice komai bah kanshi a k'asa, Mami ta cigaba da cewa
"Ya zamuyi yanzu Yasir? Masroor na dak'i yana kuka"
Jin haka yasa Yasir mik'ewa dasauri ya nufi side din Masroor hankalinshi tashe..
Zaune ya sameshi yanda Mami ta barshi, saidai yanzu bah kukan yake bah. Ya k'arasa ya zauna kusa dashi
"Friend why all this?, uh have to be strong. Komae zai zama normal"
Masroor baice komai bah sai girgiza kanshi dayayi. Dak'yar yasir yasamu yaci abincin ya hada mai ruwan wanka yayi sannan yajashi suka tafi yawo ko hakan zaisa ya rage tunanin dayake...
Washe gari kamar yanda Fareed da Sa'ood sukayi hakan neh ya faru, karfe hudu a kauyensu Sulthana tai musu, bayan layinsu Sulthana sukai parking motarsu, yaro suka samu suka hadashi da sabuwar dari biyar ya musu k'iran Babban Almajirin mallan.
Ummy Abduol✍🏻
[28/08, 01:12] Friend Hussaini: 💐💐💐💐💐💐💐💐
💐💐💐💐
*SULTHANA*
💐💐💐💐
💐💐💐💐💐💐💐💐
By *Ummy Abduol*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.