Ciki Da Gaskiya Littafi Na Daya Complete Hausa Novels
Reading file: Ciki Da Gaskiya Part 2.txt
Chapter 50 of 52
*_part 2_*
_(littafi Na biyu📙)_
*_yanda kike tadaban haka gaisuwarki tadabance my dear pinky pinky😜, Anty Zuwairiyya, k'awarki anty zuwairah ta gaisheki🤭. Alkairin ALLAH yakai miki har Kano auntyna ta mutunci._*
💋💋💋💋❤👍🏻
5⃣0⃣
Azaba ta ishi Aysha, duk addu'ar datazo bakinta yitake, tana kiran mama da khaleel suzo su taimaketa zata mutu.
"Wayyo Ammah zan mutu, Dan ALLAH ki ciremin jaririnnan, zai kasheni wayyo Anty Mamie."
"Daure Aysha kiyi nishi da k'arfi kinji, kinga kan yaro gashinan, insha ALLAH kinayin nishi zai fito ki huta, runga addu'a, bazaki mutuba insha ALLAH".
" to Ammah, inayin addu'ar aii, hazbinallahu wani'imal wakil, ya khaleel kana ina?, shikenan kabarni da wahala? bama zakazo ka taimakenib......? kai ya salam, I love you mamana.....wayyo ALLAH Na.
Duk surutannan da Aysha keyi dakiran sunansa khaleel najikin k'ofa yanaji, tausayinta yakuma kamashi, jiyake inama zai iya maido ciwon jikinsa, yanzu nan haka Anty Mamie tasha azabarnan, Amma momy bataji tausayintaba ta d'aukeni batareda ko ganina tayiba, momy kin cutar da Anty Mamie gaskiya, wannan alhakin kad'ai ya isa hanaki zaman lf..........
Tunaninsa yakatse lokacinda yaji kukan babie yacika d'akin, Ammah kuma tana fad'in kai Alhmdllh sannu da k'ok'ari Aysha, masha ALLAH barka dazuwa duniya.......
Waigawa yayi yaga Anty Mamie bata wajen, tana kichin d'ora ruwan zafi, ai baiyi wata-wataba yatura k'ofar yashige.
Ganinsa kawai Ammah tayi yafad'o.
Shikam ko kallo batama isheshiba yanufi inda Aysha take kwance tana maida numfashin wahala da k'yar.
Kanta yad'auka yad'ora bisa cinyarsa, yasaka gefen rigarsa yana share mata gumin fuskarta, sai jero mata sannu yakeyi .
Sannu Humairah na, ALLAH yayi miki albarka, yasaka farinciki arayuwarki, kin faranta min, kema ALLAH ya faranta miki fiye da haka, ya ubangijina bazan daina godemakaba da wannan k'yauta dakamin".
yaduk'o yasumbaci goshin Aysha, datake guntun murmushi idonta arufe.
Ammah dai batama kulasuba, tana gama yanke cibi tamaida hankalinta wajen gogema jariri jiki saboda d'a na fad'owa uwa tabiyo baya.
Muryar Aysha can k'asan mak'oshi tace, ''Sadauki zansha ruwa".
"Ruwa?, tom inazuwa bara Na d'akko miki".
Da sauri yafita, batareda Ammah ta kallesaba ta tuntsure dadariyar tsokana, baimasan tanayiba, Dan tuni yafice abinsa ma.
" a'a babana lfy? Mizaka d'auka? Yama naga jini ajikinka?".
"Anty Mamie ta haihufa, ruwa tace zatasha shine zan d'auka mata."
"Alhmdllh Anty Mamie tafad'a cikin d'aga hannu sama, amma khaleel yabata dariya yanda yarikice, badai tayiba ta danne".
" kaga baruwan sanyi zata shaba, kar6i wannan kakai mata".
Tamik'o masa ruwa maid'an d'umi.
Yana zuwa ya iske Ammah ta kulle d'akin, bugun duniya amma tak'i bud'e masa, haushi ya isheshi, hardai Anty Mamie tafito daga kichin tana tambayarsa lafiya?".
Da hannu ya nuna mata d'akin.
Murmushi tayi, dantasan shida Ammah ne, tunda sunsaba, "kaga kyale Ammah kaji babana, tashima kacire wannan kayan kayi wanka, kaga duk jini ya6ataka ko?".
Kallon jikinsa yayi, shi saima yanzu yalura jinin ya6atashi. mik'ewa yayi yashiga d'akinsa, sai jero tsakin haushin Ammah yakeyi, batama barsa yaga koda jaririnba mtsoow, ALLAH tsohuwarnan tagama rainashi.😂
********
Cikin mintunan dabasufi 30 ba Ammah tagyara maijego da jariri tsaf, d'akinma aka gyarashi, kaikace ba'a haihuba.
6angarenta taje ta d'akko turaren wuta data tanada domin wannan ranar, matan su Sultan ma duk haka tamusu, harda kayan sanyi Na jarirai masu azabar k'yau.
Tazo ta kunna, Dan danan 6angaren Aysha yad'auki k'amshi, aka sakama jariri fararen kayannan Na sanyi, sunmasa k'yau, sai barcinsa yake zubawa hankali kwance, bashida wata damuwar data wuce hakan to🤷🏽♀.
Sai a lokacin Anty Mamie takai labari cikin gida.
Aifa kowa yarud'e da murna, Dan danan suka cika d'akin, jariri d'an dangi, harfad'an wazai d'auka akeyi.
Suna tsaka da murnarsu ya khaleel yashigo, babuma Wanda yalura dashi, sai Aysha dake kwance akan gado tana kallonsu cikeda jin dad'i.
Yunk'urawa tayi zata tashi zaune Dan ganin ya khaleel, amma saiya dakatar da ita, tareda zama kusada ita abakin gadon ya kamo hannunta yahad'e danasa.
"Sholyna sannu da k'ok'ari kinji? babudai inda kemiki ciwo ko?".
Akunyace ta jinjina masa kan, dansu ummi Amarya suna d'akin, ga matansu ya mujahedeen mamadai batazoba, Anty Mamie ma batadawoba duk sunama ummi amarya kara.
Yasan sarai mitake jima kunya, amma yak'i sakin hannun.
Ammah data shigo d'aukeda kofin tea ta balla masa harara, shima hararar tata yayi yana kauda kai.
" yo iro, iyakarkadai hararar tawa, amma babu yanda ka iya dani, ka harareni son ranka, nasan yanda zanyi maganinka agidannan".
Shiru yamata, yacigaba dama Aysha magana.
"Yo karka tankamin d'in, dama masana sunce dogo da hankali dacene, mtsoow".
Shi dariyama takoma bashi, amma saiya k'iyi, ya shareta.
Kowa ad'akinkam fad'an nasu dariya yake bashi, kowa kuwa yana darawa k'asa-k'asa, Anty Mamie da ummi amarya ne kawai tasu tafito fili.
Ummi amarya tamik'o masa jaririn tana fad'in kaga bar Ammah kaji babana, sotake kawai tabaka haushi. Ga maigida kamasa addu'a.
Sai yanzune zai d'auki yaron, bakinsa d'aukeda addu'a yad'aukeshi, wani farinciki yaratsashi, wai wannan nasane, kai 'ya'ya k'yautar ALLAH, ya mannashi da k'irjinsa tareda lumshe manyan idanunsa.
Ummi amarya dukta kad'a Kansu suka koma falo, akabar Ammah dasu ayshan kawai ad'akin.
Cikin mamaki Ammah da Aysha suke kallon khaleel dake rungume da yaro yana hawaye, bakinsa yana d'an motsawa ahankali, dagani kasan ALLAH yakema kirari da godiya, yakai tsawon lokaci ahaka sannan yabud'e idanunsa akan yaron, yashiga sumbatarsa kuma.
Ammah dai da Aysha sunzama 'yan kallo, Dan sun sakin baki sukayi suna kallonsa.
🤔kai masu karatu, lallai khaleel yanason yara, nifa harma narasa yanda zan musalta muku farincikin dayake aciki.
Bayan Aysha tad'an huta khaleel yakaisu asibiti itada Ammah Dan a duba lafiyarsu data jariri maikama da babansa sak👍🏻.
Ya khaleel an.......🤭koda yake bara nayi shiru kawai.😎
Alhmdllh, maijego da jariri lafiyarsu lau sai wasu magunguna da doctor Faisal yabasu susaya Aysha tasha, shima jaririn saboda 'Yar mura dayazo da ita anbasu Wanda zasuna bashi.
Daganan suka dawo gida.
Kasancewar haihuwar yammace, dare yafarayi makwaftane kawai suka shishshigo sukayi barka daganin jariri.
__________________
Bayan sallar isha'i Baffah yashigo shima ganin jinjiri, daduk samarin gidan, yanata barcinsa aka kawoshi.
Cikin tsokana baffah yace, "iye, kaga d'an gayu, barcima kakeyi? Idon maza biyu kaikuma naka arufe?".
Dariya aka sanya gaba d'aya, zunnurain yace, " a'a baffah karfa kace haka, yarona jarumine, ba barci yakeba likimo yayi dai".
Suka kuma tuntsurewa da dariya, baffah nata tsokanarsa sukuma suna kare masa, ya khaleel dai baicewa komai sai dariya.
Addu'a baffa yamasa, sannan yad'ago yana kallon khaleel, "mu'azzam kamasa hud'uba ko?".
" a'a baffah, kaidama ake jira".
Baffah yay murmushi, yasan dama za'a rina, Dan ya khaleel tun yana yaro idan yasamu Abu, kafin wani yagani, koyayi amfani dashi saiya kaima baffah.
Baffah yace, "wane suna kakeso?".
K'asa khaleel yay dakansa yana murmushi, " baffa duk Wanda kaza6a masa shine dai-dai".
Nanma baffa murmushin yayi, sannan yafarama yaron hud'uba.
Yana gamawa yamik'ama Ramadan dake kusadashi yaron yana fad'in "ALLAH ya raya Takwarana Abdallah".
Masha ALLAH Sukaita fad'a, kowa ya yaba da wannan suna.
Haka sukaita d'aukarsa d'ai-d'ai suna masa addu'a amatsayinsu Na iyaye.
Khaleel da farinci ya isheshi, dama sunan dayake burin sakama yaron kenan, gashi tunaninsa yazo d'aya dana baffah, dad'i yaji sosai, mik'ewa yayi yashiga d'aki yakira Aysha.
Cikin ladabi ta durk'usa gaban baffah tana gaidashi, ya amsa da kulawa, yana tambayarta jikinta.
Kasa amsawa tayi saboda kunya, takumayin k'asa da kanta tana d'an murmushi, baffa yanata zubamata addu'oi da albarka, ahankali take amsawa da ameen, su Muslim natayata.
Muslim azuciyarsa yana tuna dayanzufa shi aka haifama yaronnan, wayyo ALLAH ya khaleel yamasa kwace😂😜.
Bayan tafiyarsu baffah ma Anty Mamie da mama suka shigo sukaga jariri, suma sunmasa addu'oi.
Nace, "kaga yaro d'an gatan dangi😃👍🏻.
_________________________
Washe gari aiba'a magana, gida yacika da 'yan uwa da abokan arzik'i, su Amal amare, kowacce danata cikin, matansu Joseph suma da 'yan yaransu abin sha'awa, Anty zuwairah ma saigata tabiyo jirgi, danta kasa hak'uri, su Anty Shukurah ma anzo, 'yan Kano dai sai nanda kwanaki uku, ammafa tuni sunga hotunan baby da'aka tura musu, Anty Amatullah ma pictures d'in baby tuni suncika wayarta, kowa yagani dole yayaba.
Fans ma pictures duksun zomuku nasani😉😃🤚🏻.
🤣🤣
Ammah tayi karnene ad'aki tahana khaleel sakewa, Bai isa yak'e6e dagashi sai ayshaba, daya shigo zatazo ta zauna itama, idan zaicika d'akinnan da harara bazata kulashiba.
Takuma hana Aysha shiga d'akinsa.
Haushinta sosai khaleel yakeji, yarasa kuma yanda zaiyi da'ita, duk wani motsinsu akan idon Ammah ne😂.
Kai Ammah jidalice fans🤣🤣.
********
Masha ALLAH Abdallah yayi yayi goshi, kayan barka ba'a magana, baffa yayi nasa, Anty Mamie danata, mama danata, ummi amarya danata, to ballantana kuma iyaye su ya Sultan, duk basu manta rawar gani da d'an uwansu yataka anasu haihuwar 'ya'yanba, harma da bikin nasu, kowa saida yaymasa hidima ta bajinta, hakama Anty Zuwairah wannan karon tayi hidima kodan tawanke laifinta nabiki dabatama ya khaleel komaiba, kayan baby 'yan ubansu haka tahad'o, banda Na Aysha dashi khaleel d'in kansa, Anty shukurah, Anty Amatullah ma duk ba'a barsu abayaba.
Abin tamkar fariyya, ya khaleel maiyine, shiyyasa shima ba'aji k'yashin masaba, koya kukace fans🤷🏽♀.
Kumafa nasan kunan kuna shirya gifts😉😂.
_____________________
Kwanaki hud'u da haihuwa saiga Anty Fadeelah da Anty Hafsat, sunyo gaba daga Kano.
Zokaga murna wajensu dasukaga jariri.
Aysha taji dad'in ganin 'yan uwanta, sunzo dakayan arzik'i suma, daga kawu bilyamin, Na Ummah ma daban, haka su ya Qaseem.
Aikam ranar ansha hira.
Ana gobe suna kuma su ummah suka iso suma, harda matar kawu Ahmad da Ummulkhairi autarsu Aysha dake hannunsa, yarinya tayi girma sosai, zasu iya zama sa'anni da ummunoor, bana zata jss 1 secondary, gwaggo Asma'u ma tazo daga katsina, da Matan su ya Qaseem, matan kawu bilyamin ma da 'ya'yansa, su Rufaidama ba a barsu abayaba, sunzo da 'ya'yansu masha ALLAH dunsunyi wayo.
To saikuma ga 'yan jigawa, harda inna tsohuwa mairan k'arfe, dukda tasan duk abinda yafaru hakan bai hanata shan sabon kukaba ta rungume khaleel tana fadin "dama tanaji ajikinta khaleel jinintane, ba'a banzaba take k'aunarsa kamar tsoka d'aya amiya😂, shikansa saida kwalla ta tarumasa agefen idonsa.
Matan uncle ma'aruff ma duk sunzo, da gayyar dangi Na 6angaren Ammah da Anty Mamie, gidafa yacika kaikace biki akeyi. Kowa burinsa ya kwatanta alkairi ga ya khaleel koda baikai Quarter d'in Wanda shi yake musubama.
Saikuma ga 'yan Canada kamar wasa su Anty meerah, Aysha batayi zaton zuwan nasuba, aikam kamar ta had'iyesu saboda murna, babyn Anty meerah Raudat tagirma ko INA yawonta takeyi.
Gidakam ba'a cewa komai, ranar kwanan hira akayi, musamman 6angaren Aysha dayazama dabar yaran mata, duk can suka kwana.
Washe gari aka saka suna a massalacin anguwar bayan anyi sallar asuba.
Akaita sakama yaro albarka.
Muma munce ALLAH yaraya Abdallah Ibraheem Abdallah💋.
Dagananfa shagali yadawo Na mata acikin gida.
Aharabar gidan aka shirya walima iya mata zallah.
Suma su khaleel sunyi tasu daga 10am zuwa 1:0pm, saboda abokan aikinsa da abokansa, aikam nasha mamaki, dannaba k'aramin cika akayi awajenba, shi harma mamaki abin yayta bashi..
And'auki Abdallah anje dashi, ALLAH ya taimakesu kuma baiyi kukaba, yanatama barcinsa, kunsan jariri da barci.
Ansha hotuna kam sosai, lamarin harba'a cewa komai.
4:0pm Na yamma mukuma mukayi namu shagalin acikin gida, babu k'arya munfa cashe, lamarin harba'a cewa komai.
Kai fans kunsha casu wlhy, babufa Wanda banganiba, munci rangam munsha zo6o, kowa saida yaciko jakka dakayan alatu, su o e ina kallonta harda guziri tayi a leda bakko😜, bandai fad'i sunaba ehe😏.
Alhmdllh suna yayi suna, Aysha da Abdallah sunsha gayunsu, nimadai nasaka leshina Na k'aramar sallah nayi k'yau😎, ba'a d'aukar rahoto kawai natsayaba ehe😏.
😂😂😂🤣
Su Taheer sun taka rawar gani wlhy, abin arzik'i harba'a cewa komai, lallai Abdallah yayi goshi fans, ALLAH yabamu farar haihuwa irin tasa🤷🏽♀👍🏻.
___________________________
Kowa jikinsa yafad'a masa saboda gajiya, Aysha kanta agajiye take, saboda gidan yakuma cika dole tashiga d'akin ya khaleel dantad'an gasa jikinta susamu su kwanta, toilet d'in d'akinta bak'i nata layin shiga.
Batayima zaton yana gidanba.
Aikam babu kowa ad'akin, ta sauke Abdallahd dake goye abayanta yanata barci, Ammah tace dolene taringa goyashi yanajin d'umin bayanta, yanzuma ana kiran sallar magriba tace tad'aukesa tagoyashi, karkuma ta saukeshi sai anyi sallar isha'i, babu yanda Aysha zatayi dole tagoya gudun jarabar Ammah.
Saman gadon ya khaleel ta kwantar dashi, barci yakeyi har yanzu, ta lullu6eshi sannan tashiga bayin. tana shiga kamar jira yaro yafara kuka yana wuntsila 'yan k'afafu sama.
Ya khaleel ne yashigo d'akin danufin d'aukar Abu yafita, dan 6angaren baffa yakwanama jiya.
Da sauri yak'araso gaban gadon yana fad'in ''ya salam, jenior miyafaru kaikad'ai ad'aki? Ina A'eeshan?".
😂ni dariyama yabani, kaikace yaron zai amsa masa tambayoyinsane🤣.
Ya d'aukesa yasaka akafad'a yana jijjigashi, saikiran sorry yakeyi, sorry my Darling, bar kuka kaji".
Aysha Na toilet tana jiyosu, aikam taita dariya, kusan mintuna 20 saigata tafito, bud'e k'ofarne yasaka khaleel juyowa yana kallonta.
"Yanzu dama kina cikin d'akinnan Amma kika barsa yake zunduma kuka haka".
" kai Sadauki, wannanne zunduma kuka? kumafa wanka nayi, ajiyesa kenan nashiga wanka yafara kukan, ALLAH yaronnan yacika wayon tsiya, shikenan dayaji babu motsin mutum kusadashi sayaytama mutane kuka? ALLAH akwai takura, shikenan banida aikinyi saina gadi, yanzuma damutane kenan, inaga kowa yatafi kuma?".
"To minene aikin naki idan ba rainonmuba?". 'Yay maganar yana sakkoda junior daga kafad'arsa'.
Aikam idonsa k'yar abud'e.
Dariya ya khaleel yayi, yasumbaci kumatunsa, ''sholy zokiga abin dariya, waifa idon yaronnan k'yar abud'e".
Dariya itama tayi, tamatso kusadasu.
" to kallafa dan ALLAH, anya bakai jenior yabiyo wayoba".
"Hhhhh, aikema d'in gwanace afagen wayon, kuma aii dama k'yan d'a yagaji babnsa ko".
"Hakane kam".
'Aysha tayi maganar da dariya'.
Kwanciya khaleel yayi akan gadon yad'ora jenior a saman cikinsa, ya kalli Aysha dake saka kayan barci " shi baza'a masa wankanba ne?".
Juyowa tayi tad'an kallosu, sannan tamaida kanta ga madubi tana tufk'e gashinta, tace, "aii Ammah tamasa tun d'azun bayan anyi sallar magriba".
" OK, Ammah ko fitina, yanzu dai datasan kina d'akinnan dayanzu tashigo, bansan miyasa takemin hakaba?".
Zama Aysha tayi a bakin gadon kusada kan ya khaleel tana 'Yar dariya.
"Kabar Ammah kaji, aii yanzu hira da innah ne ke d'auke mata hankali".
" hakane, amma miyasa taketa wani kaffa-kaffa dake".
"🙈catayi idanfa ina shige maka saika kuma min wani cikin, waikuma ga jenior k'aramine".
Bashiri khaleel yatashi zaune yana 'Yar dariya, ''kai amma dai tsohuwarnan ta rainani, to bansan kina jego bane komi? Tama maidani wani bunsuru alkuran".
Dariya Aysha taita masa harda tuntsurawa.
Tuni dariyar ta Aysha tafara narkar da ya khaleel, dama gata acikin kayan barci, jegon kuma yasakata yin shar, takuma murjewa da 'yar k'iba, kasa hak'uri yayi, ya ajiye jenior agefe yamatso kusada Aysha.
Tashagala cikin masa dariya taji ya kwantota jikinsa, kafin tayi yink'urin kwacewa kam bawan ALLAH ya had'e bakinsu waje guda.
Tunfa Aysha nad'an tittirjewa sai jikin mutuniyar taku yasaki🤣, tafara badakai😎.
Sun lula wata duniya kukan Abdallah yadawo dasu hayyacinsu, yaro kamar yasan mi'akeyi ya daddage ya callah kuka😂🤣.
Dole suka saki juna suka dawo gareshi, kunya dukta ishi Aysha, khaleel yad'akkosa yad'ora mata acinya yana murmushi.
''Inagafa yunwa jenior yakeji".
Kan Aysha ak'asa takar6esa tafara shayar dashi, cikeda sha'a khaleel yake kallonsu, jiyake tamkar ya had'iyesu donsi, waya yad'auka yamusu pic, sannan yamatsa tareda rungumo Aysha jikinsa ya manna mata kiss akumatu yad'aukesu ahaka.
Nida nake ala6e nace "lamarin zaaaaam fans😂🤙🏻".
Ranardai haka ya khaleel ya yaudare Aysha takwana d'akin, dukda baimata komaiba tasha jagwalgwala.
Nace, "Ashe dai gaskiyar Ammah😱".
_______________
Washe gari kuma bak'i sukaita tafiya d'ai-d'ai.
Cikin kwana biyu kowa yakama gabansa, kaikace gidan baitara kiwaba, daganan kuma sai bikinsu musleem.
Ammah tace sai Aysha takoma 6angarenta kokuma d'akin ummi amarya.
Khaleel yay tsalle yadire akan bai aminceba, Ammah kuma tace bai isaba.
Ankai ruwa rana kam kafin ya yarda dan dole Aysha takoma 6angaren Ammah, saida baffah yasaka bakima sannan.
Aikam yayta fushi dakowa agidan, harma ita ayshan kanta.
Daga k'arshema wani aiki yataso masa yashirya yatafi France, headquarter d'insu dake birnin Lyon.
Bayan sati uku da haihuwar Abdallah (jenior).............✍🏻
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu._*😭🙏🏻
[10/26, 4:30 PM] Aysha Galadima: *_📲Typing_*
🤰🏻
*_CIKI DA GASKIYA!!......_*
_{🔪wuk'a bata hudashi🗡}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_HASKE WRITERS ASS......._*
_(Home of expert and perfect writers)_
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.