Maradams Book 2 Complete Hausa Novel
Reading file: MARADAMS book 2 by Aysha A Bagudo.txt
Chapter 6 of 14
Page 11
Jiki a sanyaye maryama take taku gabad’aya kuzarin jikinta yayi kasa ,”aiki zatayi kenan nifa bana ra’ayi ? maganarsa ta shiga yawo acikin kwakwaluwa da zuciyarta , tana tafiya tana tunanin maganarsa , a qalla yaya sadam ya kusan minti shabiyar zaune acikin motarsa yana jiranta , ya dubi agogo a karo kusan na shabiyar yaja qaramin tsaki a lokacin da wayarsa ta soma ringing ya kai hannu ya d’auka ya duba yaga sunan ummanshi ke yawo akan screen din wayar. numfashi ya sauke sannan ya d’auka cike da girmamawa “sadam !”ta kira sunansa ya amsa da “na’am “ina son kaso maryama tun daga qasan zuciyarka ,sannan zaka iya zama madadi ko ka cike gurbin abubuwan da maryama ta rasa a rayuwarta na shekaru baya.”
“ina jin ciwon da qunci abubuwan da sukai ta faruwa daita amman ina fatan kai ne zaka wanke min wannan quncin ya dawo farinciki na har abada “naji ummah in sha Allahu zan yi iyakar qoqarin na kawo miki wannan farinciki “dan allah sadam ka son maryama “ yayi murmushi kawai yana sosai keyarsa yayinda idanunshi ke kallon hanyar da maryama zata bullo .”ahankali yaga tahowarta a natse take yin komai nata kamar bata son taka kasa koma yace tausayin kasar take “nayi magana ba kace komai ba ? “duk abinda ummanah take so ya zama dole naso “ya fad’a yana sake tsaida idanunshi akanta “
“na gode maka allah yayiwa rayuwarka albarka yadda kayi min biyayya kai ma allah ya baka ya’yan da zasu maka biyayya “Ameen ya hayyu ya qayyum “
qirjin maryama na tsananin fad’uwa ta qaraso bakin titin unguwarsu har ta tsaya jikin motarsa bai iya d’auke kwayar idanunshi akanta ba ,jikinta a matukar sanyaye ta bud’e gaban motar yaya sadam ta shiga yayinda zuciyarta Ke bugawa da karfin gaske ta zauna tare da rafka tagumi cikin rashin sanin madafa madadin taji yaja motar sun wuce sai taji yayi sallama ya ajiye wayar hannunsa ya kunna music yana bin wakar ahankali .”
Kanta taji ya sara mata ganin bashi da niyyar tafiya ga lokaci na wucewa ya sata kallonsa kamar mai shirin yin kuka tace “yaya sadam !”tamkar ba magana take yi masa ba haka ya cigaba da bin wakarsa babu alamun damuwa ko nadama a fuskarsa hannu ta mika hakan yasa sukayi daf da juna wanda da zata qara matsar da hannunta zata iya yin masauki a jikinsa, a natse ta kashe wakar ta sake kallonsa tace “i am talking to you yaya sadam “.“me kike son na yi ?ya fad’a a sanyaye “kayi hakuri dan allah idan wani laifi nayi maka lokacin na tafiya gashi naga baka da niyyar tafiya wannan aikin shine rayuwata bana son rasashi .”
ya d’an matsota yana cewa “ni dana zauna jiranki tsawon mintuna shabiyar bani da aikin yi ne ?”ko bani da wajen zuwa ne?” ko kuma aikina bashi da mahimanci ne ?”yayi mata tambayar ajere yana sake kunna wakarsa .”sake kashe wakar tayi ta kallesa a marairaice sannan tace “am sorry duk maganarka ce ta rikitani har yasa kuzarina yayi kasa wallahi da kyar na kawo kaina bakin titin nan shiru yayi yana kallonta fuskarsa a d’aure tmkr wanda bai ta’ba dariya ba “ka d’an saki fuska nan dan fushi baya maka kyau “ ta furta cikin wani irin salo da sautin murya mai sanyi huci bakinta da numfashinta duka na dukan wuyansa wanda sanadiyyar hakan ya haddasawa tsigar jikinsa mikewa ya kuma qara bugawar da zuciyarsa take .”
ajiyar zuciya ya sauke yana jin wani iri a ilahirin jikinsa “saboda nace bana ra’ayin aiki ?”wallahi duk shi ya sanyayyar min da jiki da dai zaka amince zanyi farinciki da hakan “bai sake cewa uffan ba ya kunna motar ya soma tafiya kamar wasu kurame haka suka cigaba da tafiya .”qarfe tara saura wasu mintuna suka isa bakin tafkeken get din Z&A yaja ya tsaya batare daya kashe motar ba cikin siririyar muryarta tace “yaya sadam na gode sosai allah ya kai lafiya “ ta fad’a tana qoqarin fitowa daga cikin motar adaidai lokacin da hancin motar ammar ta sanyo kai “Ameen ki kula da kanki “I will !ta fad’a tana sakar masa murmushi duk da bawani sonshi take ji ba amman taji dadi sosai kuma zata iya rayuwa dashi muddin rai .ammar yana kallo sukayi bankwana “
da sanyi jiki ta shige cikin sadam ya cigaba da tsayuwa yana kallon bayanta har ta ,bace masa sannan ya lumshe idanunshi lokaci d’aya kuma ya bud’e “oh my goodness god “ya furta a can qasan zuciyarsa ta yadda idan ba bakinsa ka kalla da kyau ba bazaka fahimci abinda yace ba .”murmushi ya kwace masa a saman fuska wa zai same kamar maryam yace bai so ?”sai dai wani dalili na dabam ya haifar da hakan ,sam ya manta a inda yake sai da yaji mutane ana masa hon a she fa motoci ya tare duk suna tsaye suna jiransa murmushi yayi sannan ya kama gabansa yayinda maryama tuni ta shige cikin ma’aikata bata ma san lokacin da yaya sadam ya wuce ba .”
tana shiga sauran abokan aikinta suka qaraso suna mata magana suna shirin shiga inda zaa wa masu neman aiki interview amman ita maryama hankalinta bai garesu yana kan neman inda subia ta shige ,tunda tasan a tun lokacin da sukai waya daita ya cancanci ace tana wajen koma anyi mata interview an gama .”taja ta tsaya tana cewa” kuje zanzo na sameku daga baya “.ta bud’e jakarta ta ciro qaramar wayarta ta shiga neman layin subai’a ,ganin an bud’ewa ammar mota ya fito yana nufota yasa ta sauke wayar daga kunnenta tare da kashewa gabad’aya “ya iso har inda take tsaye yana gama qarasowa wayar hannunta ya amsa ya rike ta kallesa tana murmushi sannan tace “barka da safiya ?
“Barka !
“me ya tsayar dake da sai yanzu kika qaraso ?ya tmbyeta yana duba screen din wayarta sunan wacce ya gani ne yasa ya mika mata wayar “wallahi wanda zan aura ne ya ‘bata min lokaci “ tayi maganar cikin salon jan hankalin duk wanda yake tare daita, ammar kasa magana yayi kafin daga baya da kyar cikin fad’a yace “wato har zaki iya fad’a min wanda zaki aura ne ya ‘bata miki lokaci ? tayi shiru tana wasa da yatsun hannunta dan batayi tsamanin zai ji haushi maganarta ba ganin babu komai a tsakaninsu sai mutunci da girmamawa “amman ki sani wannan ba mutuncinki bane ko nace zaki zubda mutuncin family d’inku ne .”
“Ai shima family dinmu ne da mahaifinsa da mahaifina the same mother the same father wani irin kallo yayi mata mai cike da tunhuma,itama kallonsa tayi numfashi ya fesar yace “shi kuma mijin da nayi miki fa ya zanyi dashi ?tayi murmushi tana cewa “allah sir ka daina min haka wallahi kana d’aga min hankali ,kai kanka kasan kafi karfina bare wanda kake fad’a wannan sai dai na qara dagewa da aikin ibada wata killa na samu irinsa a aljanna yayi murmushi yace muje “.
Ahankali suke takawa yayinda mutane suke gaishesa wasu ya amsa wasu kuma ya d’aga masu hannu “kefa ko anyi miki interview ko ba’ayi miki ba dole zaki yi aiki damu “sure tunda inda kai ba ,ai sunanki na can tuntuni kinga office dinki can ta kalli inda ya nuna mata “woow gsky naji dadi sosai “kinga ga office dinki ga na mijinki in sha allahu “tayi murmushi kawai tana cewa “subai’a fa ?nifa nafi son naji kana magana kana had’awa daita zai yi magana kenan, wayarsa ta d’auki qara sauti ,ya soma qoqarin d’auka bata tsaya jiransa ba ta cigaba da tafiya dan daman da kyar take iya jirawa dashi da sauri ta qarasa tana shiga aka kira sunanta .”
Sai da tayi addu’a sannan ta shiga office din ta gaishe da mutumin data gani zaune mai suna wale yana duba wasu fararen takardu,ya d’ago ya kalleta a natse sannan ya sake kiran sunanta “maryama hussein !”tace yes sir ! sai daya bata izinin zama sannan ta zauna a natse tana wasa da yatsun hannunta wanda ya zame mata jiki ,ya d’an saci kallonta yana mamakin matsayin da aka bata ,domin kujera ne da suka dade suna neman wanda zai maye gurbinsa , sai dai lokacin daya fara auno mata tambayoyi akan kasuwanci da kuma matsayin da zata taka ya ajiye mamakinsa a gefe domin kuwa ta cancanci ta hau matsayin kuma irinta mai kamfanin ya dade yana nema .”
bata wani jima ba ta fito har da award aka bata sakamakon aikin da tayi dasu daman kuma sun ajiye ne domin rana irin ta yau “congratulations sauran abokan aikinta suka shiga yi mata tana amsa masu da “thank you tare da rungumar mata daga cikinsu duk wannan farinciki da take ciki bai kawo mata natsuwa ba saboda rashin ganin subai’a da batayi ba ta ciro wayarta ta soma nemanta tana tafiya ahankali har ta fito haraban ma’aikatan subai’a ta d’auka tana kuka hankalin maryama ya sake tashi sosai ciki tsanani tashin hankali tace “subai’a kina ne na shigo har an d’aukeni aiki banganki ba ? tana shirin sake yin magana ta hangota a bayan wata bishi tana qoqarin fitowa .”
Da sauri maryama ta qaraso ta tsaya tana qare mata kallo tsab hawayenta yasa zuciyar maryama tsananin bugawa “me Ke faru dake subai’a ?kukan me kike yi ?muryata cike da kuka tace “na rasa aikin nan ,da yawa wad’an da suka d’auka alfarma ne yanzu bansan ta yaya zamu cigaba da rayuwa ba daman da allah da aikin nan na dogara gashi ban samu ba muddin sai da wata alfarma zan samu aikin nasan har abada bazan samu ba .”ta riko hannunta maryama tana cigaba da kuka ta soma rokonta “dan girman allah maryama karki barni haka ki taimakeni ki bar min aikin nan nasan zaki samu wanda yafishi gabad’aya idanun subai’a sun rufe har sai da maryama ta kira sunanta sannan ta tsaigaita kukanta “ki kwantar da hankalinki ki bar kuka nan haka” amman ta yaya babu sunanki bayan ..”sai kuma tayi shiru ta janyo hannuta zuwa ciki “zo muje .”
maryama na gaba subai’a na bayanta har suka qarasa bakin office din james ta nemi izinin ganinsa aka bata damar shiga ,wanda ta samu wannan damar ne saboda ammar domin yadda yake mata yasa mutane dayawa d’aukar sonta yake maryama ta shiga tare da subai’a dake kuka har lokacin .”bayan ta gaishesa cike da ladabi tace “dan allah ina neman wata alfarma agareka ya kalleta dan shima ta burgesa yadda ma’akatan suka dinga yaba kwazonta tun kafin tazo kuma zuwanta wale ya sake tabbatar masa iri irinsu basu dayawa a duniya dan tunda ya sheida masa ya kira mai gidansa seun ya sheida masa muryarta a matukar sanyaye ta soma magana kamar zatayi kuka “dan allah sir wannan yaruwa tawa nake son ta maye gurbina ma’ana acire sunana a saka nata .”ya kalleta a tsanake domin yasan yadda ake shan wahalar neman aiki yanzu da kudinka ma baka samu “.
“Saboda allah zakayi karka tsaya tunanin komai ni inda aikin da zanyi domin tallafa rayuwata for now ,ita kuma bata dashi da wannan aiki Kawai ta dogara ga mahaifinta ya rasu ko da yake nima marainiya ce amman dai tafini bukatan aikin nan saboda tana da kanne dayawa da mahaifiya mara lafiya dake karkashin kulawarta itace komai nasu “da wannan maganar ta karyar da zuciyar James ya kalli subai’a cike da tausayawa yace “sorry oo !”zan iya miki wannan alfarma sai dai bazata maye gurbin kujerarki ba “tayi shiru tana tunani abinda zata ce kafin tayi magana ya cigaba” kujerarki ke kad’ai ake bukata sakamakon oga ammar sunanki ya bayar gashi yanzu kinzo da wata magana “karka ji komai a saka a duk inda zaa sakata nidai burina ta samu aikin ni zuwa gaba in sha allahu zanyi aiki daku amman a yanzu burina subai’a ta samu aiki .”
Mr James ya saka sunan Subai’a ya cire sunan maryama “ suka fito zuwa gindin wata bishiya maryama na cewa subai’a “congratulations na tayaki murna kawata yanzu kin zama cikakkiyar maaikaciya ta fad’a tana murmushi subai’a ta rungumeta cike da farinciki “na gode na gode maryama allah ya saka miki da mafifincinsa nayi imani zaki samu aikin da yafi wannan da kika bar min tana kuka tana gode mata” haba subai ki daina kuka kawai dan na sadaukar miki da aikina kike wannan godiya da kuka haka ?” ta goge mata hawaye tana cewa ni na zan bar ki na wuce gida nasan akwai abubuwan da zaku yi kafin ku wuce ina miki fatan alkhairi allah yasa ki fara aiki a saa ta juya a hankali ta soma taku subai’a tabi bayanta da kallo hakika bazata ta’ba manta alkhairinta gareta ba .”
Da wuri maryama ta dawo gida koda ta shigo kai tsaye bangaren ummah ta shiga ta sheida mata amman ta isketa a dakinta tana bacci dan haka ta fito ta shiga bangarensu ta zauna a parlour’n tana sauke numfashi tare da dafe goshinta ko cikakken minti biyar batayi ba ,Aunty ta fito da mamaki take kallonta “lafiya naga har kin dawo ?lafiya aunty nan ta zayyane mata komai sosai ran aunty ya baci kamar ta rufeta da duka musaman data lura ko ajikin maryama dan babu alamun damuwa atare daita “me yasa zaki bada aikinki bayan Kinsan muma muna fama da kanmu ? “aunty kiyi hakuri kin sani ni zan iya cigaba da aikin zanena kafin na samun wani aikin ita fa ?bata da wani sanar hannu da zatayi kuma rokona tayita tana kuka saboda bata da hanyar da zata kula da kannenta da mahaifiyarta fatana allah yasa ya zame min alkhairi ta qarasa mgnr muryarta na rawa alamun kuka “.
Aunty ta samu waje ta zauna kusa da ita tana cewa “shikenan allah yasa ki samu wani wanda yafi shi muryarta a raunane tace “Ameen ko da ummah da habib suka ji suma abun bai masu dadi ba amman babu yadda suka iya tunda ta bayar sai hakuri da fatan alkhairi .”washegari tana zaune a parlour’n su tare da aunty kiran ammar ya shigo ta tashi ta koma dakinta sannan ta d’auka tana dauka ya rufeta da fad’a “kin kyauta saboda shakuwa da qaunar da nake miki yasa na tsaya lallai Ke zaa bawa wannan matsayin saboda ina son shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninki da Adam amman kika zuba min qasa a ido ,ina ganin idan shakuwa ta shiga tsakaninki dashi zai taimaka kwarai wajen janyo hankalin gareki shine kika bar wata .”
sanyayyen murmushi tayi kamar tana gabansa “to amman ai na fad’a maka akwai wanda zan aura .”“wanda zaki aura din banza ,wallahi ko ba dan Adam ba nan gaba kadan zaki fara gano illar abinda kika aikatawa kanki ,kuma duk abinda ya faru babu ruwana ke kar ma ki sake nemana ko da yake ma tafiya zan yi gobe kuma zan dauki lokaci ban dawo kasar ba “allah ya kaika lafiya “Ameen amman babu ruwana dake wallahi ko a hanya kika gani kika min magana sai bata miki rai “a ina ma zan ganka dole sai ma’aikata kuma babu abinda zai kaini tunda bana aiki a karkashinku tayi mgnr aranta alokacin ya katse kiran .”
ranar yau din jinsa maryama tayi dabam wani irin damuwa ta tsinci kanta ciki ita kanta tana jin mai yasa tayi abinda tayi kowa ya kalli fuskarta zai ga canji laifin kanta ta gani me yasa ma ta bar wayarta a kunne bata kashe ba da wata killa bai qara mata damuwa akan wanda take ciki ba tayi shiru yayinda a cikin zuciyarta takewa kanta fatan alkhairi .”awanni sukai ta zuwa suna wucewa amman maryama bata daina jin damuwa dan haka fito ta nufi bangaren ummah tana shiga ta isketa tana tsinke ewedu “sannu da aiki ummah!Yauwa maryama ya zaman gida ?gamu dai yanzu zamu fara ummah tayi murmushi “zaki samu wani aiki nan kusa ta zauna kusa daita ta d’auki gayen ewedu ta fara tsinkewa “gobe nan ma zan fara nema ssi ku tayani da addua,in sha allahu alkhairi zamu ji .”
Ahankali sukai ta hirarsu daga nan umma ta sako mata maganar sadam “maryama kin dai san komai daga Ke har sadam baku kawowa zuciyarku zaku zama abu d’aya ba sai gashi allah yayi ikonsa dan haka ki saki jikinki dashi karki tsaya sai yajaki ajiki ai kin fahimceni ina ganin nan da wata biyu masu zuwa zaa daura maku aure” maryama tayi shiru ba dan bazata aikata abinda take butaka ba bata da option dole zata jashi ajiki tuni ma ta sadaukar da rayuwarta garesa ko ba dan shi umma ta wuce komai gareta nan ta garasa yininta tare sukai komai a kitchen har karfe shida da rabi ta buga ta fito parlour’n inda ta iske yaya sadam zaune shiru a falon da alamun yayi zurfi cikin tunani maryama ta qaraso idanunta akanshi kallon minti goma tayi masa sannan tace “meke damunka yaya sadam kayi shiru haka ? “
Ya sauke numfashi tare da sauke kwayar idanunshi akanta a natse ta samu waje ta zauna kusa dashi tana cewa “ya wurin aikin naka ? babu komai aiki kuma alhamd wasu abubuwa né suka sha min kai amman in sha allahu zan shawo kan komai na gode sosai da kulawarki “no karka damu yaya sadam , sukai shiru na kusan minti goma sannan ya kira sunanta “.marayam! ta tsura masa ido kawai tana kallonsa “ya batun aikin da kika fita nema ?”naje na samu amman na bawar qawata subai’a aikin “why ?!ya tamvayeta yana dubanta. “saboda tafini bukata aikin itace komai na gidansu gashi mamanta bata da lafiya ga rashin mahaifi da sukai yaya sadam wallahi ina tausaya mata “gsky abar tausayi ce kin kyauta sosai da kika bar mata .”
taso yayi mata fatan samun wani aikin amman taji yayi mata shiru “yaya sadam a fahimtata naga baka son auren mace mai aiki ya kalleta kawai “nasan kana da dalilinka kin haka amman ka yarda dani zan kare maka mutuncin aurenka wallahi bazan maka wasa da aurenka ba ,nima fa nasan ciwon kaina bayan hakinka dake kaina akwai hakin allah dan allah ka bari nayi ayyukana “zan duba !ya fad’a atakaice tare da mikewa tsaye “na gode sosai “.
******
Cikin sauri ata ya shigo office dinsa mataimakinsa na biye dashi ya zauna a mazauninsa yana kallonsa batare da yace komai ba “good morning sir “morning! Ya amsa atakaice yana maida hankalinsa Kan system “uhm amma sir ko zan iya magana yanzu “uhm ! Ya fad’a a takaice daman
akan yarinyar nan dana baka labari tana da kwarewa sosai akan lissafi duk wani lissafi na kamfanina nan tasan kansa ta hada komai daake bukata takardunta sunyi kyau sosai kuma anyi mata interview komai nata daidai ,amman abun mamaki tace bata bukatar aiki damu wai a dauki wata amadadinta .”ATA ya dago kyawawan idanunshi a natse yana furta “ what ? She rejected our job duk yadda aiki yake wahala a kasar nan? .”
Ya kankantar da idanunshi tare da yin shiru yana tunanin abinda zai sa wani mutun biladam mai jini ajiki yayi rejecting din aiki a maakatarshi ya hade rai sosai cike da takaici a fuskarsa sannan Ya koma ya zauna sosai akan kujera yana jujjuyawa a hankali yana cigaba da tunanin Ya furzar da iska mai zafi yana tsotsa keyarsa “ina ganin wannnan yarinyar tana da damuwa a brain dinta ,kai kwata kwata ma dakikiya ,for god sake ni me ye damuwata yanzu ? me yasa zaka kawo min wannan banzar maganr ?meye damuwata daita dan taki amsar aiki inda ga mutane can bila adadin suna nema ?ya qarasa mgnr cike da jin haushi yana ja tsaki “ noncess !Ya furta yana dungule hannunsa .
“Am very sorry sir daman dan ka bukaci mai ilimin lissafi ne shiyasa har muka bukaceta amman dai tace zuwa nan gaba zata iya kasancewa damu “I don’t care kawai make sure bata samu aiki a koina ba a duk fadin garin nan, kai har karshen rayuwarta duk inda kuma aka dauketa aiki let me know .”
“an gama sir …ring din wayarsa yasa seun yayi shiru tare da daukar wayar ya mika masa cike da girmamawa Ya amsa ya manna a kunnensa tare da mikewa Ya qarasa jikin window office dinsa yana kallon haraban ma’aikatan yana amsa wayar ransa duk abace “daga can bangaren nana hauwa’u ta gaishesa “ ina kwana yaya ?”lafiya ya kike auta? “lafiya ! daman na kira na fad’a maka zan biya na d’auki maryam muje gaishe da mami “okay ! ya fad’a tare da katse kiran .”ya cigaba tsayuwa yana jin zafi aransa .”
Nana hauwa’u tayi shiru kafin daga baya ta mike tsaye ta kammala shirinta ta fito ta shiga mota kai tsaye hanyar gidansa ta dauka daman sunyi waya da maryam din itace ma tace ta kirasa ta fad’a masa a bakin kofar gidan ta tsaya ta kirata bayan ta fito ta shiga gaban mota suka dauki hanya suna tafiya suna hira maryam tace “sister ya zamanku da yaya hisham kuwa naji kwana biyu bakya magana akanshi “na gaji sister na kawo ido na zuba masu duk wanda yayi da kyau zai gani ina sauke duk abinda ya rataya a wuyansa na zamantakewa aure hakinsa ne ban tauye masa ba idan ya nema zan bashi ,idan bai nema ba huta roro zama haka maryam ta sauke numfashi tace “duk da haka dai ai naki da sauki tunda yana cin abincinki “eh to da sauki gsky Kinsan daman shi ba mai daukar abu da zafi bane kamar yaya bane .
“Ni dai gsky babu wani sauki a zamanmu dashi muddin yana gida bani da kwanciyar hankali sausaucin da nake samu dukkaninmu kuna kokari dani ,kuma na gode sosai da kulawarku ‘yanuwa allah ya bar zumunci amman ina jin tsoron ranar da zai hadu da wacce yake so yace zai qara aure ina rokon allah kafin zuwan ranar allah ya kasheni dan nasan bakincikin da zan qunsa yafi wanda nake qunsa yanzu “ babu wannna ranar for now mami fa tace muddin yana son qara aure sai ya kwantar miki da hankali shi kuma Kinsan halinsa da wahala ya kwantar da kai “kina ganin har yarinyar mafarkinsa in da zasu had’u mami bazata yarda ya aureta ba ?”yadda idan mutun ya mutu baya dawowa haka labarin wannan mafarkin nasa yake.”
Maryam tayi shiru tana tunani nana hauwa’u ta dafata tana cewa “don’t worry siater komai zai daidaita kinji “ naji amman rayuwarta abar tausayi ce baya son ganina baya son ko jin muryata idan ya ganni ko yaji muryata Kmr ya matu mgn kadan nayi yace na cika surutu ni yanzu dan allah ina da magana ?tai mata tmby tana dubanta girgiza mata kai nana hauwa’u tayi “wallahi bancin na bar gidansa mami zata shiga damuwa wallahi dana gudu,” ki gudu kije ina? kar ma ki soma muna tare babu inda zaki maryam ta girgiza kai tana jin zafi aranta sister wallahi baki san abinda nake hadiya bane .”idan kika tafi babu ni babu ke har abada zumunci mayi a lahira maryam tayi saurin goge hawyenn daya soma bin gefen idonta tare da cewa “ nima wasa nake babu inda zani muna tare mutu ka raba tafiyar mintuna ta kawosu bakin get din estate dinsu sukai hon masu tsaron get suka bud’e masu suka shigo sukai parking .”
atare suka nufi gidan mami suka kunna kai ciki tare da sallama a parlour’n suka iske Aunty shahida ,da Aunty khadija ,har ma da Aunty zabiba zaune sai mami da mamaki maryam ta bude baki cikin tsananin farinciki da gudunta ta kwaso bata zube gaban kowa ba sai a gaban aunty shahida ta ruqunqumeta tsam ajikinta tana cewa “wayyo allah babbar yaya naji dadinku daman sister kinsan suna nan ne ?ko daya yadda kika gansu yanzu nima haka nagansu ta zame jikinta ta durkusa gabanta “ina yini babbar yaya aunty shahida ta shafa fuskarta “ya kike maryam “lafiya lau .” ta isa gaban mami ta durkusa ta gaisheta cike da farinciki da girmamawa cike da kulawa mami ta amsa tana kallonta a tsanake “ dan tun washegarin tarewarta sai yau ta sake daura kwayar idanuna akanta “wallahi Allah mami jiya kasa bacci nayi saboda zan zo na ganki sai kuma gashi naga yan’uwana gabad’aya .”allah sarki maryam nima nayi kewarku sosai .”
Tayi murmushi mami ta cigaba da kallonta “tunda sister ta fad’a min zamu zo tare nake murna sai naga gari kaman da gangan yaqi wayewa don kada inxo na ganki” to gaki ga maminki kinganta cikin koshin lafiya “wallahi gashi na ganki kuma naji dadi sosai ai ni ina ganin ma na dawo kenan bazan koma wannan gidan mai kama da makabarta ba sai na kwana biyu “.nana hauwa’u ta zungurinta kan tayi shiru amma ina maryam bata fuskantarta ba mami ta miqe tsam ta basu waje dan tasan dole zasu tautauna a tsakaninsu .” mami na fita nana hauwa’u ta zubawa maryam duka a cinya wallahi ki rufa min asiri baki isa ki kwana a gidan nan ba yadda na dauko ki haka zan maidake gidanki “.
wajen da nana hauwa’u ta daketa take sosawa tana dariya tace “wallahi babu inda zani “kamar zaki iya bayan kina tsananin sonshi ? “kai nana hauwa’u ban da sharri wa ya fad’a miki son 'ya'yan take?inji zabiba ta fad’a tana murmushi nana hauwa’u tace “ai ni tuni na san da wannan ga tanan kuma idan ta isa ta karyata ,sister ban da sharri fa auren daaka samu na amince da kyar zaki zo kice ina son shi nana hauwa’u ta sake qara mata wani dukan maryam tace “babu komai wallahi koda da zafi ni banji zafin ba, dan bakya laifi ko kin kashe dan masu gida wani dan masu gida ?”yayanki ! dariya suka bushe da ita gabad’aya su Aunty zabiba tace "Kefa sabon iskancin mai lasisi kikaje kika koyo a gidan yaya “barta dole tayi iskanci da alamun taga gadon baccinsa shima yaya naga ya canza kwana biyu da alamun ya angwance inji cewar zabiba “.
wallahi ku daina fad’ar haka kar sautsayi ya shigo dashi mu shiga uku “ku dai shiga uku amman mu ai yayensa ne dole ya daga mana kafa dariya maryam ta saki har da tafa hannu “wannan kanin naku ai mami kawai yake d’agawa kafa hira suke sosai yayinda maakatan gidan suka cika gabansu da kayan marmarin da abinci da abun sha aunty khadija ta dubi auta “da alamun kin samu lafiya “alhamdulillah Aunty khadija rayuwar aure is not easy amman haka zamuyita hakuri har allah ya kawo mana sauki Ameen “ kefa maryam yaya zaman naku da uban shegu ?uhm ta numfashi “to da sauki zance amman ni matsalata mai girma ce kuma ban san ranar da zan fita ciki ba” ta qarasa maganar kamar zatayi kuka .”
Gabad’aya suka zuba mata ido cike da tausayawa “ita fa siater matsalarta mai sauki ce ba kamar ni ba da ko muryata baya son ji baya cin abincina kona girka sai dai masu gadin gida suci bani da kwanciyar hankali matukar yana gida , sister kuwa nuzla ce matsalarta amman ni zanyi maganinta “ki rabu daita huce haushi take akan hisham shi kuma rashin ganewa ne idan ba haka ba ko sauraranta ma yayi “inji cewar aunty khadija “allah ya kyauta daga nan Suka cigaba da hirar matsalolin rayuwa wani suyi dariya wani suyi jimami cikin haka aunty abida ta shigo daman ita tana yawon shigowa ko dan taji halin da ata yake ciki a wajen mami diyana da rukkaya suka shigo su kuma nana hauwa’u ce ta kirasu kusan duk yammatan gidan suka shigo aka sake bud’e habin hira banda nuzla har karfe shida ta buga suna tare ana hira .”
Ahankali motocin ata suka shigo haraban estate dinsu sakamakon kiransa da mami tayi suna gama daidaita tsayuwar motocin ya fito kamar ance ya kalli kofar gidan baba babba hisham ya gani tsaye tare da nuzla ya zuba mata ido kamar zai mata numfashi .”shiru yayi yana mamakin karfin halinsa ko bai ji kunyar kowa ba ai ya duba mami bare tsakaninsa dashi” ahankali nuzla ta kalli inda yake kallo d’aya tayi masa ta d’auke idanunta tana jin farinciki dan yanzu bata jinsa aranta haka ne ma yasa take son dandanawa jininsa wahala kuma har ga allah tana son ta auri hisham yanzu dan hishsm miji ne bancin yana kawo mata uzurinsa akan mahaifiyarsa da yanzu ta dade da kasamcewa a gidansa .”
daya daga cikin masu tsaron bakin get din ya dagawa hannu ya taho da sauri ya tsaya a gabansa cike da girmamawa “daman hisham na zuwa wajen nuzla ne ?Eh !ranka ya dade kusan kullum yana zuwa shiru yayi kafin daga bisani yace “okay zaka iya tafiya “ya juya ya koma bakin aikinsa shi kuma ya nufi kofar gidan mami yana kiran mb ,yayan mami suna shirin mikewa su kama gabansu har nana hauwa’u dan ita maryam mami tace ta zauna ATA zai zo sai su wuce tare suka ga mutun ya shigo kamar wanda aka jehoshi yana huci “gabad’aya suka mike tsaye suna kallonsa .”bai ce masu komai ba ya samu waje ya zauna akan kujera yayinda kannensa suka gaishesa amman yaki magana ya soma waya da yaya Ibrahim .”
Hankalin mami ya tashi ta qaraso garesa ta dafa shi tana tambayarsa “lafiya adamcy naga ka shigo wani iri ?still shiru yayi yaki magana ganin haka aunty shahida ,aunty khadija da zabiba har da nana hauwa’u sukai ma mami sallama zasu wuce muryarsa a kausashe ya soma magana cikin tsananin fushi “auta kar naga kin fita daga gidan nan kin dawo gida kenan .”gabad’aya suka dawo cikin tsananin tashin hankali suna dubansa “akan wani dalili kenan adamcy ?aunty shahida ta tambayesa “yayi shiru yana huci tamkar zaki “ka barta ta koma gidanta tayi zaman aure tunda suna zaune lafiya da mijinta “inji wa yace miki haka ?ya fad’a a zafafe yana fesar da hucin numfashi “zaku iya wucewa amman ita babu inda zata mami kam shiru tayi ta kasa magana “mami kice wani abu mana kinyi shiru kina kallonsa “aunty khadija ta fad’a tana dubanta “zaku iya wucewa zanyi magana dashi “
Suna shirin fita mb ya shigo dole tasa suka tsaya kallo d’aya yayiwa abokinsa ya fahimci akwai damuwa ya qaraso kusa dashi ya zauna yana cewa “yaakayi friend ! kace nazo yanzu yana qoqarin bud’e bakinsa yaya Ibrahim ya shigo “ya fesar da numfashi sannan ya soma mgn “mb daka shigo yanzu kaga hisham tare da nuzla ko baka gani ba ?“na gansu amman.” dakata mb “an tabbatar min kullum yake zuwa wajenta kuma nasan yana yin hakan ne saboda ne “.juya can ka kalli auta da kyau “haka aka kai masa ita ?yau zaa yita ta qare gidan nan laifin mai tayi masu ?idan laifi ne ,ni ne nan nayi saboda naki amincewa da soyayyar nuzla kuma nasan shine sila da dalilin son a kuntatawa auta tunda ni babu abinda zaa iya min ,dan haka yau zan kashe wannan aure .”mami ta sauke numfashi sannan ta mike ta bar wajen.”dan tasan halin d’anta wani irin murdaden mutun ne mai wuyar shaani ”
Yan’uwansa ma numfasawa sukayi domin wannan karon fad’an gasky yake da son kwatarwa kanwarsa ‘yanci amman sunyi mamaki wannan shine karo na biyu da ya nuna kulawarsa akan nana hauwa’u amman duk da haka bazasu bari ya kashe mata aure ba .”maryam ta kallesa taga yadda hankalinsa ya tashi akan yaruwarsa ya manta irin azabar da yake gana mata ,ya manta cewar itama diyar wani ce yake quntata mata hawaye ya cika idanunta tausayin kanta ya kamata ta kalli nana hauwa’u taga itama hawaye take ta kalli ata cikin sa’a idanunsu ya tsarke cikin juna tayi kamar zata girgiza masa kai amman wata katuwar hararar daya zabga mata mai had’e da kallon banza yasa ta d’auke idanunta akanshi ,tana mai share hawayenta da hannu ta qaraso kusa daita nana hauwa’u ta riko hannunta zuwa gefe “sister kinji hukunci yayanki dan allah karki yarda ya kashe miki aure saboda ya hisham mutumin kirki ne nuzla ce matsalarki .”
“bani da zabi sister bazan iya ce masa a’a ba duk abinda yake son ya zarta akaina na amince ni mai biyayya ce a garesa ,maryam ta rungumeta ajikinta “bakya son yaya hisham ne ?”to bazan ce bana jinsa araina ba , amman idan yayana yace na koma gidansa zanyi idan yace a’a babu inda zani “wallahi sister kina son mijinki “ta fad’a tana zare jikinta a nata ta tsura mata ido tana kallonta hawaye ne kawai yake fita daga cikin idanunta qirjinta har wani sama da kasa yake “ta riko hannunta tana cewa “ shi bai rike nashi auren ba zai kashe auren wasu muje ki fad’awa mami kina son mijinki nana hauwa’u taki binta ta zare hannunta ta rakube gefe tana share hawayenta dole tasa maryam ta dawo ta tsaya kusa daita tana share mata hawaye .”
mb ya kira layin hisham cikin kankanin lokaci sai gashi ya shigo yayi mamakin ganin mutane cike ya tsaya yana kallonsu d’aya bayan d’aya sai dai bai ga matarsa acikinsu ba , wani mugun kallo ata yayi masa sannan ya qaraso gabansa ya tsaya tare da jin kai ya zuba hannuwansa duka cikin aljihunsa “baka son auta shiyasa ka zabi ka dinga quntata mata ta wannan hanyar ko ?hisham yayi shiru yana mai sunkuyar da kanshi kasa dan jin kunya “kasani nasani kowa yasani ban bada goyon bayan auren nan ba dan har yanzu bana son aurenku daita “cool down ata mb ya fad’a yana dafashi ya buge masa hannu yana qoqarin cukumar wuyan hisham yaya ibrahim ya shiga tsakaninsu “dan girman allah ka matsa “ babu inda zani ka samu waje ka zauna ayi magana ta natsuwa “idan har kaga na zauna to ya miko min takardar sakinta dan bazata qara zaman aure daahi ba har abada ya saketa yaje ya auri wacce yake so .”
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 12
Jin abinda ATA ya fad'a yasa maryam duk ta rud'e sai zufa take fitarwa hankalinta yayi matukar tashi gbdy ta nemi natsuwarta ta rasa domin tasan halinsa tunda ya furta zai raba auren lallai zai aikata hakan "ta fashe da wani irin kuka mai karfi , haka ma nana hauwa'u kuka take sosai , yadda maryam ta rud'e haka matan dake tsaye a wajen suka rud'e gashi babu damar yin magana .mazan kuwa sai faman bashi hakuri suke yana fixgewa mb ya fuskancesa sosai yana cewa "haba ATA ka kwantar da hankalinka abi komai ahankali "kasan allah muddin ina raye sai na kashe wannnan banzar auren ."
qanqame maryam nana hauwa'u tayi ajikinta suna mai fashewa da wani kuka cike da tashin hankali maryam ta soma magana muryarta na rawa "sister ke kad'ai ce zaki kawo karshen wannan matsalar "nana hauwa'u ta zare jikinta ta tsura mata ido ,idanunta na sake cika da ruwan hawaye . saboda babu mai fad'a ma yaya adam yaji sai ke a yanzu idan kika nuna masa kina matukar son mijinki shikenan magana ta qare dan dole zai hakura ya barku "nana hauwa'u ta girgiza mata kai "dan allah sister karki bari ya rabaku yaya hisham mutumin kirki ne ki tashi kiyi wani abu ta karashe mgnr tana kuka numfashi nana hauwa'u ta sauke tana share hawaye "bazan iya ba sister duk abinda yayana ya zaba min shine daidai ."haba sister haba sister !! karkice haka mana kiyi hakuri kiyi wani abu mana ta qarashe maganar tare da qoqarin mikar daita tsaye "
da kyar nana hauwa'u ta mike tsaye bisa kafafunta ta soma tafiya jikinta na rawa rawa taku biyar tayi ta tsaya cak ta kasa cigaba da tafiya hawaye na sake wanke fuskarta yayinda ata da hisham suka tsurawa juna ido kowannensu zuciyarsa na zafi cike da tashin ahankali ." hisham ya janye kwayar idanunshi cikin nashi ya tsurawa nana hauwa'u yana mai shafa kanshi abu d'aya zuwa biyu ne suka tsarga masa a tsayen da yake a gabansa ,abu na farko farinciki yadda Adam yaji zafi da ciwo acikin zuciyarsa ,abu na biyu kuma mahaukaciyar soyayyar nana hauwa'u da yaji yana bin jinin jikinsa tare da huda duk wani tsoka dake sansar jikinsa ,cikin wani irin sauri zuciyarsa ta dinga tsalle tana bugawa da matsanancin karfi kamar zata fito daga cikin qirjinsa hannuwansa duka ya miko mata alamun tazo garesa dan bazai iya rabuwa daita ba ."
ta kalli yayanta dake tsaye rike da kugunsa, ta waiga ta kalli yan'uwanta sannan ta kalli hisham da har lokacin yake miko mata hannunwansa gabad'aya nana hauwa'u ta nemi natsuwarta ta rasa ji take kamar zuciyarta zata buga sakamakon fad'uwar gaban data risketa ,haka ne ma yasa jikinta ya cigaba da rawa gashi yaya hisham yaki d'auke kwayar idanunshi akanta wanda yayi sanadiyyar da suka fad'a kogin tunani hankalinsu ya bar duniyar da suke ciki ya lula dasu can wata duniyar . "friend kayi hakuri ka kwantar da hankalinka hisham bazai ta'ba cutar da auta ba ,sannan hukuncin da d'auka akanshi daidai ne ko yanzu ka taka rawa aciki rayuwar aurensu wannan zai zama kashedi ne mai karfi kayiwa hisham".
"shi kansa bai san yana son matarsa ba sai yau haka zalika itama auta tana son mijinta ka duba ka gani yanayin da suke ciki na damuwa a yanzu "ATA ya sauke hannunsa dake rike da kungunsa ya juyo yana kallon mb a kallon da yake masa ya fahimci ransa ya kai kololuwar tashi da maganar da yayi masa ahankali ya kalli inda hisham yake tsaye yana mikowa nana hauwa'u hannu ranshi ya qara 'baci cikin tsananin fushi yace "wallahi wallahi idan kika kuskura kika isa garesa sai na balballa ki "Jin sautinn muryarsa yasa nana hauwa'u tai saurin dawowa haiyacinta tana mai sunkuyar da kanta kasa ."
A rud'e maryam tace "me yasa yaya adam "! ta matso gabansa ta tsaya tana dubansa hawaye na sauka daga idanunta "me yasa zaka kashe mata aure alhalin tana son mijinta ?ya kamata kayi masa uzuri saboda kai kanka kasan yaya hisham mutumin kirki ne wallahi bazai ta'ba cutar da sister ba duk duniya a halin yanzu sister bata da kamarsa idan ka tsaya domin kwatar mata 'yancinta nifa ?"nida kake min fiyye da abinda yake mata fa"? sai da gaban kowa dake wajen ya bada wani sauti bugu mai karfi
Wani mugun kallo yayi mata da tsumammun idanunshi yana nuna da yatsan hannunsa "wacece ke da ina magana zaki saka min baki ?ya fad'a tare da d'auketa da wani gigitaccen mari yana sake nuna ta how dare you ?".
" duk nan babu wanda ya isa bare ke din banza da ko kwatan matsayi kowa anan baki kai ba ." abinda nake miki ina yi ne dan bana sonki ,suma kuma da kika ga zan rabasu dan nasan basa son juna sukai aure, bana goyon bayan auren da ba'a so, dan bana son a aura min matar da bana só kamar yadda adabaibayeni dake "yayi maganar da karfi jikin maryam yana rawa ta fad'a jikin aunty shahida tana wani irin kuka mai ta'ba zuciya ."gabad'aya parlour'n yayi shiru tamkar babu wasu halittu acikinsa, babu wanda bai tausayawa maryam ba illa aunty abida wacce taji dadi aranta kuma hankalinta ya kwanta ta qara tabbatarwa kanta sultana ce macen da zatai wining din heart dinsa dan haka ta washe baki cikin jin dadi tace tana ".
"kema maryam da karanbani kike keda kika san matar cushe bata daraja ,me ya kaiki saka masa baki a maganarsa ?."you're very stupid kema nace ki saka min baki a maganata ne ?"ko ina ruwanki ? kai tsayuwar me ma kikewa mutane anan ?da mijinki nake da issue ba dake ba oya leave "ya nuna mata kofar fita cikin kuka tace "ah ah ni ai yar'uwarka ce dole ina da ikon da zanyi magana kuma ma ai anan ka sameni ba daga sama na shigo ba ,magana kuma dole nayi wallahi wannan kam ba irin matarka bace sam baku dace ba ka jira matarka na nan zuwa amman kam sam ba mata bace " abida i saiid out of this hall kuma ko da wasa karki sake shiga hurumina idan ba haka ba zan baki mamaki .yaya ibrahim ya kama hannun matarsa yayi hanyar waje daita amman aunty abida ta turje tana cewa "ka sakar min hannu babu inda zani da kyar ya samu ya fitar daita ya dawo ."
"Me ye laifinta adamcy ai gsky maryam ta fad'a maka "wato laifi tudu ka take naka ka hango na wani ya kalli Aunty shahida da kyau yace "ina mata abinda nake mata ne saboda bana sonta kuma da ina da dama zan iya rabuwa daita har abada ,haka zalika shine dalilin da yasa zan kashe auren auta domin zukatan kowa ya huta, yaje ya auri wacce yake so itama ta samu wanda take so yake sonta ya qarasa mgnr gumi na karyo masa sannan ya kalli nana hauwa'u "Ke maza ki koma d'aki "da mugun sauri ta juya tayi hanyar d'akin tana jin wani irin fad'uwar gaba mai tsanani hisham ya kallesa kawai batare da yayi magana ba duk da maganar yake son yi amman idan yace zai yi komai zai qara rikicewa ne shurunsa ne yafi zama alkhairi ."
A rikice mami ta fito alamun tashin hankali aunty khadija na biye daita ."ta tsaida nana hauwa'u aunty khadija ce taje ta fad'a mata abinda yayiwa maryam tana gama qarasowa ta dakawa ata tsawa tace "me maryam tayi maka ka mareta "?yayi shiru yana sake tamke fuska sosai "adamcy kaji tsoron allah, kaji tsoron ranar da hakin maryam zai kamaka idan baka sota ba'ace ka qaunaceta ba amman me yasa zaka dinga tozarta min ita agaban mutane wallahi duk namiji mai wulakanta matarsa agaban mutane yayi asarar rayuwa dan haka ka bata hakuri yanzu yanzu ."
"What !?
ya furta a razane zai sake bud'e bakinsa yaji mami ta d'aukesa da mari "you're very stupid too hakurin ne bazaka bata ba "sweetheart marina kikayi akan wannna yarinyar ?na mareka kai ma baka duba darajata ba bare hisham ya duba darajata har ya ragawa diyar cikina "hisham ya sunkuyar da kanshi kasa yana mai tsananin jin kunyarta "yanzu sweetheart akan na mari wannan duwaf din yasa kika mareni?"eh akanta na mareka idan ka sake ce mata duwaf zan maka double dinsa idan bakaji kunyata ba bazan ji kunyarka ba bare na raga maka maryam ta rike hannu mami dan ta fahimci qara masa wani marin zatayi "dan allah mami ki rufa min asiri kiyi hakuri karki masa komai ."
a fusace yake kallon maryam fuskarsa a tsuke itama din shi take kallo nan da nan jikinta ya dauki rawa ."ido cikin ido suke kallon juna a karo na farko kenan a rayuwarsu duk da suna kallon juna amman ba kamar haka ba kallon nadama take masa yayinda shi kuma yake mata kallon zaki gane kurenki da sauri ta janye kwayar idanunta saboda wani irin mugun kallon da taga yanayi mata yana fesar da iska mai zafi daga bakinsa."hisham !"mami ta kira sunansa ya d'ago a natse yana dubanta cike da girmamawa "ban hanaka qara auren duk wacce kake so ba amman bazan d'auki tozarci da wulakanci ba karka wulakanta min yarinya idan kasan wulakanta min yarinya zakayi na had'aka da allah ka sauwake mata kamar yadda d'anuwanta ya bukata ".
"kiyi hakuri Mami "ba maganar hakuri bane hisham bazan yarda yarinyata tayi zaman rashin yanci a gidan aurenta ba" hisham ya sauke boyayyen ajiyar zuciya domin gani yayi kamar son kai garesu menene ata baya yiwa maryam? irin cin kashin da yake mata shi ko kwatansa ba yayiwa nana hauwa'u amman shine dan son kai irin nasu zasuji haushi har su buqaci raba auresu "idan kasan baka bukatarta arayuwarka kaje ka aiko min da takardarta "muryarsa a sanyaye sannan cike da girmamawa yace "mami Kiyi hakuri ina son aurena ! "to kayi magana da yayanta tana gama fad'ar haka ta juya ta zata koma d'akinta." taji qara fashewar glas tass !
Ta tsaya cak tare da juyowa ata ta gani tsaye jini na bin hannunsa ,ya rasa meke masa dadi bakinciki goma da ashirin ga marin da mami tayi masa ga damar da ta bawa hisham yasa zuciya ta dibesa ya bugi show glass din dake gefensa shine nan take jini ya soma bin hannunsa aiko maryam ta rikice "na shiga uku mami yajiwa kanshi ciwo ita kanta mami cikin tashin hankali da kidema take kallonsa ranta ya baci matuka da abinda yayiwa kanshi amman ta danne zuciyarta daga taimaka masa ta maida idanunta ga maryam dake kyarma cikin alamun rashin damuwa tace "meye damuwarki dashi ?cikin yin qasa da murya maryam ta kalleta "jini ne fa mami ."ina ruwanki oya wuce muje d'aki taja hannunta suna tafiya maryam na kallon bayanta ."
Shi kuwa ATA zuciyarsa banda tuttukin bakinciki babu abinda take Mb ,yaya ibrahim yan'uwasa har ma da hisham hakuri suke bashi ganin yadda jinin ke tsiyayya a sakamakon jininsa dake gudu fiyye da kaida amman ko motsi bai yi ba ,da kyar suka kamoshi suka zaunar dashi akan kujerar dinnig d'aya byn d'aya mutanen dake tsaye suka fita a parlour'n ya saura iyasu kawai nana hauwa'u ta yage bakin mayafinta ta durkusa gabansa idanunta cike da kwalla bai d'ago ya kalleta ba ,tana qoqarin kamo hannunsa cikin zarewar ido da maseefa ya janye hannunsa ." cikin tsarkewar murya tace "please yaya karka ce a'a wallahi zan iya had'iyar zuciya na mutu idan wani abu ya sameka bazamu iya jurar rashinka ba muna sonka fiyye da tunaninka ,bazamu so mu rasa d'an'uwa kamarka ba ."
runtse idanu shi yayi kawai jikinta na rawa ta sake riko hannunsa dake tsiyayar jini wannan karon bai dakatar daita ba ta daure tana cewa "bari a kira doctor" still bai ce uhm bare uhm ba sai dai wata irin zufa ke tsatsafo masa akan goshinsa da ilahirin jikinsa ya kamo lip's dinsa na qasa yana cizawa da karfi ya bud'e tsumammun idanunshi da suka gama canza kala tsabar zuciya ,hanunsa dake daure ya tsurawa ido suka dan ja baya kad'an dan ya samu dasataccen iska ." yana zaune yana cikin tsananin damuwa maryam ta fito da sanyi jiki ta kallesa zaune shiru har tsawon minti uku kafin ahankali ta dinga takowa har ta qaraso garesa ta tsaya taga alamun an daure masa hannu ."
ajiyar zuciya ta sauke kana ta daura tafin hannunta akan goshinsa tare da goge masa zufar dake tsatsafo masa duk da sanyin ac dake ratsa parlour'n idanunshi ya sake runtse wa yana jin qarin ciwo akan wanda yake ji cikin kulawa tace "sannu yaya bai amsa ba sai ji da yayi kamar ya tashi ya rufeta da matseyacin duka, ganin bai ce komai ba ta juya da sauri ta nufi dining area ta zuba ruwa a glass cup ta nufo inda yake zaune yana huci tamkar zaki da sauri aunty shahida ta rikota tana girgiza mata kai alamun ta barshi hakan sai dai itama kanta ta girgiza mata tana kokarin fixgewa daga rikon datai mata ta qaraso inda yake jikinta na kyarma ta mika masa cup din ruwa cikin tsanani tashin hankali ta furta" ruwa ..! "
ya dago fuskarsa a hade cike da fushi da zafin zuciya ya amshi glass cup din hannunta ya buga akan tayis yana huci tare da cewa "Congratulations maryam kinyi nasarar kinyi nasarar !! sace min zuciyar mahaifiyata ba? Cike da tsoro ta qame a gabansa hawaye na turereniyar zuba daga idanunta tana girgiza masa kai ya mike tsaye yana nuna ta "wannan kad'ai Ya sake ninka wutar kiyayyarki acikin zuciyata , bana sonki kuma bazan ta'ba sonki a matsayin mata acikin gidan nan ,bazaki ta'ba zama suruka acikin gidan ba dan ban amince dake a matsayin matata ba "yana gama fadar haka ya ciro waya daga cikin aljihun wandonsa ya soma kira wata number yana tafiya yana waya "kuna da daki a girls house dinku okay ka duba min ina bukatar d'aki ganin nan zuwa ".
Yana tafiya suna biye dashi babu irin kiran da Aunty shahida batayi masa da yaya Ibrhim mb har da hisham ba amman ina ATA bai waigo ba ya ma dade da yin nisa dan tuni ya shiga motarsa atare gbdynsu suka sauke ajiyar zuciya suna sauke numfashi su aunty shahida suka riko hannun maryam suka shigo parlour'n suka bar su yaya ibrahim tsaye a waje suna tautaunawa ."suka zaunar da maryam wacce ta gama rikicewa tare da zuba masa ido "dan girman allah waye ya fadawa mami ya mareni ?sukai shiru "wallahi ko waye bai kyauta min ba saboda kunga abinda aka jawo min, kunga bala'i da aka had'a min allah ne kadai zai kwace a hannunsa ta qarashe mgnr tana zubar da hawaye."
"kiyi hakuri maryam na d'auka hakan da mami tayi zai kawo miki mafuta né arayuwarki " maryam ta matso ruwan hawaye tace "dan allah karku bari mami tasan ya tafi guest house dan damuwar zata sake mata yawa mu bar shi a tsakanin mu ta qarasa mgnr tana sheshekar kuka dan tasan yau allah ne kawai zai kiyayesa daga koma wa shan giya sigari kam ma baa magana tasan dole sai ya sha aiyar zuciya suka sauke gabad'ayasu babu wanda zai fad'a basu sani ba bayan shigar mami ta dawo parlour'n kuma taji duk abinda ya faru sam batayi nadamar abinda abinda ta aika masa ba duk da tasan a yanzu adamcy yayi girma da ya kama ta ace ya wuce ta kai hannunta jikinsa amman bazata iya d'aga masa kafa akan maryam ba "su aunty shahida suka qasa komawa gidajensu kuma basa jin zasu koma din har sai sun san halin da danuwansu yake ciki suna zaune jugun jugun ."
bayan awa d'aya suka soma neman layinsa sai dai babu abinda computer Ke fad'a masu sai swichoff .maryam ta zamo daga Kan kujerar kushin din da take zaune zuwa kasa ta dafe kanta tana ganin itace silar faruwar komai da bata tsoma bakinta ba da duk hakan bata faru ba "me yasa na saka bakina ta furta a fili tana fashewa da wani sabon kuka cike da kulawa aunty khadija tace "lahaula wala kuwata illa billa babu tsumi babu dabara maryam dole hakan zata faru "ahankali ta kalleta da idanunta da suka yi jazir alamun tarin tashin hankalin tace "bazaku tafi gida ba ?"bazamu iya tafiya ba dole mami tana bukatar mu "."zaku iya wucewa suka tsinkayi muryar mami cikin rashin nuna damuwarta ."
ahankali ta cigaba da motsa lip's dinta "kuci abinci ku wuce gbdy na sallameku suka girgiza mata kai "ni ba uwar banza bace yadda bazan dauki haka daga matar dana ba haka bazan barku ku kwana batare da kun sanarwa mazajenku ba da kwarin gwaiwar mami suka wuce gida ya saura daga maryam sai nana hauwa'u da mami .mami tasa aka kawo masu abinci ita kuma ta maida hankalinta ga tv kamar abun bai dameta ba , kasa ci sukayi ta waigo ta kallesu a natse "ku ci abinci mana!" suka girgiza mata kai alamun basa ci' ko akawo maku abinci mara nauyi ?da kyar nana hauwa'u ta fixgo magana "ni dai bazan iya ci komai ba amman ban san ko sister ba mami kam tasan maryam bazata ci ba dan haka ta mike ahankali tana cewa "sai da safenku "yanzu mami bacci zakiyi ?to me zanyi maryam ?Zan kashe kaina akan adamcy ne ."kuma kuje ku kwanta ku hutar da ranku dan shi bai ma san kun damu da halin da yake ci ba ta juya ta fara tafiya ."
daren ranar daga maryam har nana hauwa'u babu wanda runtsa damuwar nana hauwa'u ta hade mata biyu na halin da danuwanta yake ciki da kuma kewar mijinta dan tasan da yanzu suna can makale da junansu duk yadda yake nuna mata bai sonta amman basu ta'ba raba wajen bacci ba kuma kwana yake yana wasa da jikinta ganin baccin yaki zuwan mata sai juyi take ta juya gefenta inda maryam take kwance yadda ta barta haka take ta mike ta shiga bayi ta dauro alwala ta soma gabatar da sallam ganin haka yasa maryam ma ta yunkura da kyar ta tashi itama taje ta fara jera nafilfili ."
washegari tun karfe takwas yayan mami suka wa gidan diran makiya dan kwana suka yi kiran layukansa amman baya shiga ita dai mami bata ce masu komai ba ta cigaba da tsabgar gabata ."kwana biyu ATA bai dawo gidan ba kuma gbdy sun sa an bincika gidajensa bai je can ba hatta office bai zuwa gashi babu wanda yasan girls house din da yaje gbdy yanuwana sun shiga damuwa maryam kam kallo daya zaka mata ka fahimci yadda ta fita haiyacinta Har mamakinta suka dinga yi gabad'ayasu sun gane tana mutuwar sondanuwansu "zabiba ta matso kusa daita "ki rage son nan maryam zai miki illa ta kalleta kawai tana sauke numfashi "ki yawaita addua sai komai yazo miki da sauki babu wanda bai kira layinsa ba amman yaki daga wayar har da wasu layuka da dabam sun kirasa da zarar yaji muryarsu zai katse kira tun suna boyewa har dai sai da mutanen gidan fahimtar sun nemesa an rasa ne dan duk sunfita haiyacinsu ."
Ganin da mami tayi ya'yanta sun fita haiyacinsu yasa ta dauki wayarta ta soma neman layinsa kira daya tai masa ya dauka alokacin ana bude masa bayan mota zai shiga "barka da... "bana bukatar gaisuwarka
"Kana ina? ta katseshi da fad'arhaka ?ina wani wuri !"tô ka dawo gida yanzu yanzu muddin baka son ka hadu da mummunar tashin hankali arayuwarka ".tana gama fadar hk ta katse kiran dole ya bada umarni a dauki hanyar zuwa gida dashi yana shigowa gbdy yan'uwansa sukayo kansa banda mrym dake rakube cikin farinciki dawowarsa "big sister aunty shahida ta zauna kusa dashi tana shafa gefen fuskasa tana kamo hannunsa me ciwo "hope kana Lfy ?yayi mata banza hannun suka tsurawa ido nad'e da bandages "dan allah adamcy ka dinga hakuri wannan maganar bai kai ace ka bar gida ka tare a guest house ba, "dan rani wayo kawai wallahi wannan ba mutuncinka bane tô ita mrym meye nata laifin "?
"Oh My god ! taya yarinya na had'ani da mahaifiyata zakice meye laifinta wallahi tana damun rayuwata sweetheart kuma na damuna akanta, kuma kullum mgn d'aya ya zanyi ne? dame zanji ne? bana sonta amman kun matsa sai dana aureta dole , kuna son na mutu ne ?duk yayi masu tmbyr a matukar rud'e gbdy suka girgiza masa kai alamun a'a ita kam mrym hawaye ne ke zuba a idanunta tana jin ciwon yadda yake iya furta kalmar bai sonta a gaban kowa "ka dubi allah ka duba lamarin maryam " what ! ni kun duba lamarina da zan duba nata ?ihu nake kamar mahaukaci amman bani da mai fahimtata acikinku bare ku taimaka min ."
"Samu natsuwa adamcy ,yanzu me kake so?" mafarkina nake so !"muddin ana son wata taji dadina sai dai a nemo min ita, idan ba haka ba wallahi wallahi kowa bazai ji dadina ba acikin gidan nan , yadda zuciya take quna a kullum haka take son kowa yaji radadin da take ji, kun kasa samo min ita ,kun kasa yi min komai akai ,kun kasa fahimtata kun kasa min uzuri kullum maganar mrym marym !! ku dai burinku yarinyar taji dadin rayuwar aure ni kuma ko oho Inpossible wallahi bazai yuwu ba sai dai mu taru muyi rayuwar qunci gbdy ."
suka zuba masa ido kawai suna kallonsa cike da tausayawa "matuqar kuna son farincikina ku nemomin mafarkina ya qarashe mgnr yana huci sannan ya mike."
" ina kuma zaka "ina bukatar na kasance ni kadai daga haka bai qara cewa komai ba kai tsaye step ya haye mrym ta juya tana kallon bayansa zuciyarta na bugawa da sauri sauri gbdy suka qaraso suka zagayeta "karfa ki yarda ki saka damuwa aranki muna sonki mahaifiyarmu tana tare dake me ye abun damuwa ?kai ta girgiza "yan'uwana bazaku gane yadda nake ji araina ba ,aunty zuciyata kamar ta fashe idan naji yana magana akan mafarkinsa da furta bai sona, idan ya zama dole ne sai ya furta ni ya dinga fad'a min ni kad'ai ciwo bazai dame ni haka ba wai har a gaban aunty abida ,rukkaya ,diyana ."
In fact ya nunawa duniya ni din bakowa bace garesa hatta zumuncin dake tsakaninmu yayi watsi dashi ."
"Kiyi hakuri komai zai zama labari wata rana "babu komai allah ya nuna min wannan ranar bari naje na kai masa wani abu yaci ta barsu tsaye ta nufi kitchen bayanta suka bi da kallo suna jinina girman hakurinta dan ko su bazasu iya daukar wulakancin nmj haka ba ,amman tunda ita haka allah yayita da hakuri sai su tayata da addaur allah ya qara mata hakuri ."tana qoqarin had'a masa abinci wayarta ta soma ringing ta duba taga mahaifiyarta ce dan haka tasa wayar a handsfree muryarta a sanyaye ta gaisheta "umma ina yini ?lafiya kalau maryam ya kike da wannan mugun mijin naki ?yana nan yana halin nasa ko ?"duk lafiya muke dagani har shi amman dan allah ummah kiyi hakuri ki daina kiransa da mugu yaya adam nada kirki fa kawai dan bai sona ne ."
"Wannan shine dalilin da yasa bana son shi yanzu bai son jinina me zanyi dashi "tô ai shi só halitta ne umma amman ina sa rai wata rana zai duba lamarina da izinin allah ki tayani da addua,addua kam muna yi dan tun daakayi auren naku ban zauna ba wajen neman miki taimakon samun 'yanci a gidan miji ,yanzu haka ma ga wani taimakon nasa an amso miki daga zuru zan turo miki ta jirgi kije ki karbo da kanki acikin abinsa zaki zuba masa idan allah ya taimaka yaci wallahi sai dai wani ba wannan adamun ba sai yadda kikayi dashi maryam tayi sauri ta cire wayar a speaker tana waiga bayanta dan datasan mgnr da zai cigaba da fitowa bakin mahaifiyarta kenan bazata saka wayar a speaker ba."
Ta sauke numfashi sannan ta maida wayar kunnenta ta rage murya sosai ta cigaba da magana "gsky ummah bana son nayiwa yaya adam wani abu tukun ya soni nafi son ya soni dan kanshi "tô shikenan zanyi amfani dashi tayi discounting kira tare da soke wayar acikinta ta kawo karshen maganar né da fad'ar haka dan ita bazatayi masa amfani da komai ba , taji ma da tarin zunubin dake kanta ta hada masa abinci akan qarami tray ta fito ta nufi hanyar d'akinsa bynta suka sake bi da kallo cike da tausayawa a hankali ta tura kofar d'akin ta shiga yana zaune a kasan d'akin ya tokare hannunsa yana kallon sama . yana jin motsin shigowa d'akin ya kalli kofar ganinta yasashi jan tsaki yana kwar da idanunshi gefe ta karaso ta tsugunna kusa dashi jikinta da murya na rawa ta d'an saci kallon hannunsa mai ciwo sannan tace "ga ...ga abinci!
" bai ce komai ba ya kamo lip's dinsa na kasa yana cizawa da karfi "kayi hakuri da abinda ya faru wallahi bani da masaniyar faruwar komai da kuma nasan hkn zata faru wallahi bazan bari ba bazan ma sa bakina ba daman nayi haka né dan "ya waigo a fusace ya kalleta a kaskance hakan yasa ta kasa cigaba da magana zuciyarta na bugawa ganin bai yi magana ba yasa ta sake bude baki zatai mgn ya d'aga mata hannun tare da tsareta da idanunshi wanda hkn ya haddasawa zuciyarta shiga rudani da bugawa da sauri "kin kamu da sona ko ?tai shiru tana duban cikin kwayar idanunshi karo na biyu kenan daya furta mata haka sai dai ta kasa bashi amsa tmbyrsa ."
"kina sona kuma shine dalilin da yasa kika dawo abar tausayi haka ba ? nan ma shiru tai masa dan batasan me zata fad'a masa ba "nonsense girl kawai wallahi kin cuci zuciyarki ke yanzu kinga dacewar mu da zaki kamu da sona ?tai saurin girgiza masa kai "ba.." bana só.."you are very stupid shut up iam talking you talking sai na kasheki da mugun duka taja bakinta tayi shiru tana sauke numfashi."
Ya mike tsaye yana dubanta kamar zai had'eyeta da idanunshi "itama da sauri ta mike jikinta na kyar "ni zaki kalla kice baki so ?ta sake girgiza masa kai ."
"better kin taimaki kanki da kanki ,kingan ni nan har abada bazan ta'ba ganganci barin ki zauna acikin nan ba "ya nuna daidai saitin zuciyarsa da d'an yatsansa ."
" zan baki shawara kiyi gaugauwan cire sona aranki kamar yadda na ta'ba fad'a miki adam mallakin mafarkinsa ne idan ban sameta ba mallakin wata ce dabam amman bake ba "tunda ya soma magana tske jin tashin hankali mara misaltuwa" me yasa zakace haka yaya adam? daga ranar da ka zama miji agareni daga ranar na sanyaka acikin abinda yafi zuciyata da gangar jikina ,zuciyata ta haukace akan sonka ina jin ciwon kiyayyar ka gareni amman na kan kawar dashi domin na samu damar dasa soyayyata acikin zuciyarka ta hanyar maka biyayya "enough...! bana son jin maganar soyayya daga bakinki ai tunda kina iya shiga tsakanina da mahaifiyata kin kad'e a wajena domin wannan son wa ni kadai ya dace ban dake amman gashi an kasashi gida biyu "ya fad'a ya fusace ."
"ban kwace maka soyayyarka ba mami tana sonka fiyye da komai kuma matsayinka na nan acikin zuciyarta ,bazata ta'ba canzaka da wata ba, watan ma ni ai ban isa na taka matsayinka a zuciyarta ba kuma duk wannan kulawar da kake ganin tayi karfi yanzu saboda kai ne saboda ..."please let me be alone ya fad'a yana juya mata baya cike da jarumta ya zuba hannuwansa duka cikin aljihunsa "out of this room now ya nuna mata hanyar fita ."shiru tai ta kasa motsa jikinta ."ganin hk yayi tunanin bar mata d'akin ya nufi hanyar fita ta biyosa da sauri tana cewa "d'an allah kayi hakuri kaci wani abu sai daya bari ta fita daga d'akin gbdy ya dawo da baya ya rufe kofar.
cike da muryar kuka tace" ka yafe min banyi maka laifin komai ba wallahi ban had'aka da mahaifiyarka ba ni kaina bansan hakan zata faru ba wallahi dana san wanda zai fad'a mata alokacin dana hana bai ce uhmm ba bare uhmm ya bar jikin kofar yana jan tsaki tare da furta "nonsense!wani sabon kuka ta rushe dashi"maza masu sanyin halima baka barinsu haka ,bare miji irin naki dole sai kin tashi tsaye wajen mallakesa sannan zaki samu 'yanci agidan aurenki "maganar mahaifiyarta na karshe kenan a wayar da sukai yi d'azu nan take taji ta yarda kuma zuciyarta ta amince zatayi amfani da maganin da mahaifiyarta zata aiko mata domin samarwa kanta kwanciyar hankali a gidan mijinta "ahankali taji an dafata ta waigo idanunta cike da ruwan hawaye "Mami ce !
"Mami dan allah ki fad'a masa cewar bani na hadashi dake ba, dan allah mami ki bari ya fahimce hakan " naunayen ajiyar zuciya ta sauke " na rasa me yasa adamcy yake son caza miki kwakwaluwa mami ta fada hk a fili "ita kuwa mrym kuka kawai take tana rokon mami ta fahimtar dashi "kukan ya isa haka zan fahimtar dashi duk da ba rarrashi ya kawo wajensa ba amman zan kwantar da kai saboda ke "yauwa mami na gode sosai dan allah ki lalla'bashi kar kiyi masa fad'a ta fad'a tare da share hawayenta "mrym ki daina yawon kuka ki dinga dauriya mijinki ba mutun bane mai damuwa da kukan mutun ko sanin mahamancin hk, jajurcewarki ita zatasa kiyi nasara akansa ta runtse idanunta wasu hawaye masu zafi zuka zubo mata ".
"nace kukan ya isa haka "tô mami kice ya bude kofar yaci abincin nasan tunda ya bar gidan bai ci komai ba amman sam sam yaki saurarata"kije for now nasan halin d'ana kema kuma idan da sabo ya kamata ace kin saba da halinsa bazai ce miki komai ba sannan bazai ci komai ba, ki bari zan fada masa komai zan fahimtar dashi baki da laifi kuma zan lalla'ba miki bazan masa fad'a ba ki kwantar da hankalinki naunayen ajiyar zuciya ta sauke sannan ta fara janjikinta ta bar wurin mami tai knocking tana kiran sunansa da kyar ya bud'e mata kofa.
Ahankali ta tura kofar ta shiga ta tsaya abayansa bai juyo ba tasan yayi haka saboda fushin da yake daita ."
Numfashi ta sauke tare da d'aura hannunta ta dafa kafad'ansa tana kiran sunansa "adamcy nah !kmr jira yake ya juyo ya zuba mata tsumammun idanunshi yanayinsa kmr zai yi kuka itama mami ganinsa haka ya karyar da zuciyarta domin ya zube ya fita haiyacinsa acikin kwanki hud'u kawai idanunshi duk sun rikid'e sun canza kala alamun shan sigari hannunsa mai ciwo ta kamo tana kallo nan take yanayinta ya sauya idanunta suka fara kawo ruwa .ganin haka ya rungumeta ajikinsa qirjinsa na bugawa da wani irin karfi sai da mami taji tsoron yanayin bugun zuciyarsa . ta zaresa ajikinta tana kallonsa hawaye ta gani a fuskarsa hankalin mami ya qara tashi wannan shine karo na biyu da taga d'anta na kuka a tun tasowarsa lallai adamcy baya son mrym ".
"kiyi hakuri sweetheart ina 'bata miki rai hakika ban rike amanar da dad ya bani ba ki yafe min zuciyata ta kasa son mrym ki bani damar na auro wata please." nasani nasan baka sonta amman ina sa rai zaka sota wata rana ,ni ban hanaka qara aure ba ko kawo zabinka ba amman sai naga irin adalcinka ina son kasan mutunci maryam kasan daraja maryam ka bata kimarta da darajarta ta matarka ,ka bata matsayin mata acikin zuciyarka, ka yarda daita wannan shine burina kafin ka shigo da wata matar gidanka."adamcy maryam na da kirki tana da biyayya da hakuri ban maka zaben tumun dare ba na zaba maka abinda zaka yi alfahari ne ko bayan raina zaka yi alfahari daita fatana ka rike matarka amana na yafe maka na yafe maka na kuma janye fushina akanka allah yayi maka albarka allah ya azurtaku da samu zuria masu albarka ".
Shiru yayi yaki amsawa da ameen "ina son maryam sosai Adamcy kai ma kuma ina son ka koyi sonta .."ya qara tsura mata idanunsa da sukai jazur "zaka min wannan alfarmar?zaka koyi sonta ?shiru yayi ya kasa furta komai "kayi shiru Adamcy ya kamata kace min wani abu ko zuciyata zata samu salama ta fad'a tana d'aura hannunta akan sumar kanshi yayinda hawaye ya cika idanunta ta rasa wani irin baqar zuciya garesa tun yana yaro take fama dashi idan ya tsani abu ya tsana kenan idan yace yana son abu shima haka ne, tasan da wahala ya so maryam kamar yadda take bukata. ta cire hannunta dake Kan sumar kansa ta tsurawa yatsun hannunsa ido hawayenta ne suka dinga diga akan nashi tafin hannun da sauri ya dago kansa ya sanya kwayar idanunshi cikin nata yana furta "why sweetheart me yasa zaki min haka ."?
Hawaye ta cigaba da zuba aiko ya rude "wayyo allah na shiga uku ,mami ki taimakeni karki cigaba da zubar da hawayen nan idan dai ba so kike wani mummunar bala'i ya sameni ba "ya qarasa maganar cikin rawar jiki numfashi ta sauke ta janyo hannunsa mara ciwo ta zaunar dashi sannan ta zauna gefensa tana cewa "babu abinda zai sameka zakayi albarka da izinin allah domin kai ne komai arayuwata babu abinda zai sameka zan daina kuka amman kai ma kayiwa maryam adalci ka duba irin kulawar da take bani irin kulawar da take bawa yanuwanka da kowa naka ni mahaifiyarka ce na fi kowa sanin abinda ya dace da rayuwarka ka sake da maryam zata kula da rayuwarka dan dukkanin alamunta sun nuna tana sonka yanzu ,ganewa bakwa yi amman kun fi samun kwanciyar hankali a wajen matar dake sonku ,matan da kuke so kuma wahala suke baku ."shiru ATA yayi yana nazarin maganarta ."
" kasan me yasa na had'a aurenka da maryam ?ya girgiza mata kai yana daura kansa a saman cinyarta ya natsu sosai ya bata dukkanin natsuwarsa "na had'a aurenku ne saboda ko byn raina maryam zata maye maka gurbina zata baka kulawar da uwa ce kawai zata baka, zata jurewa duk wani shagwa'ba da jin kanka,uwa uba hakuri gareta ,zatayi hakuri da duk wani iskancinka dan haka ina mai umartarka ka dauketa a matsayin mata zakaji dadin rayuwar aure daita". ta qarasa maganar tana shafa sumar kansa ya dago a hankali ya sake zuba mata idanunshi kamar zatai kuka "please sweetheart karki min haka karki bani umarni ,zanyi kokari na koyawa zuciyata sonta ta yadda zata bata matsayin mata amman ki bani lokaci ."
ta numfasa taso ya fadi abinda yafi haka amman a hakan ma ta gode "na gode allah yayi maka albarka ta mike tsaye bari na turo maka maryam ta zuba maka abinci kasa ma cikinka ,kanshi kawai ya gyada mata tana barin d'akin ya sauke wani wahalallen numfashi yana tunanin maganganunta "ta ina zai fara bawa maryam matsayi mata ?"
"matsayin mata da take nufi fa tana nufin wani abu ya shiga tsakaninsu kenan ?ya mike tsaye cike da sanyi jiki "tabbas abinda take nufi kenan idan dai haka ne ta ina zai fara ?a hankali ya shiga zariya acikin dakin yana ciza lip's dinsa at the same time yana hura hancinsa ."
byn kmr minti biyar mami ta dawo d'akin hannunta rike da mrym tana bata umarni "maryam zuba masa abinci" ta fad'a tare da samun wuri ta zauna kusa dashi tana dubansu adamcy nah bari mrym ta zuba maka abinci kaci ka d'an kwanta ka huta kafin zuwa anjima ka d'auki matarka ku wuce gida kaji masoyina ."kallonta kawai yayi yana mai tausaya mata " maryam ta zuba masa abinci ta janyo qaramin table gabansa ta ajiye masa tana satar kallonsa aranta tace "rigimamme kawai da baya son zaman lafiya ."
yayi shiru kawai yana kallon abincin kafin ahankali ya fara tsakura babu laifi ya d'an ci kad'an ya ajiye spoon alamun ya koshi mami ta tsiyaya masa ruwa a glass cup ta bashi ya sha sannan ta mike idan ka tashi ka d'auki matarka ku wuce gida kanshi ya gyada mata batare da yace uffan ba , ta juya har tayi taku biyu taja ta tsaya "batun hisham kayi hakuri kabar auta ta koma d'akinta zai yi magana tace "alfamar na nemar masa a bashi dama ta biyu stil bai yi magana ba ta fito ta bar maryam tana tattara wajen ."da yamma mami ta kira hisham yazo ya d'auki matarsa bayan tayi masu nasiha mai ratsa jiki ." haka ma maryam tabi mijinta suka wuce. gidan ya saura daga mami sai yayanta wad'an da suke shirin tafiya ."
Akan hanyar su nana hauwa'u ta koma gida tafiya ce sukai tamkar kurame hassalima bata kalli inda yaya hisham yake ba ta juyar da kanta gefe tana kallon tsirarrun motoci dake wucewa akan titi saukar hannunsa taji akan nata wani irin yarrrr taji a gbdy ilahirin jikinta, sai dai bata juyo ta kallesa ba ta cigaba da kallon titi "auta !" ya kira sunanta yaushe rabon da ya kirata da wannan sunan ?sai daya sake kiranta sannan ta juyo da kyar ta zuba masa idanunta ya kwantar da murya sosai "kiyi hakuri da abubuwan da suka faru a tsakaninmu shiru tayi Kmr bazata yi magana ba sannan ta motsa labbanta tace "babu komai ,komai ya wuce ,"Kinsan ko wanene ba haka halina yake ba ."
"Nasani shiyasa nayita mamaki wai yaya hisham mai tausayi da kulawa ne nake rayuwa dashi cikin fargaba da nadamar da tsoron kasancewata dashi yadda baka son auren nan haka nana hauwa'u bata só ,alfarma tayi ta sadaukar da farincikinta, na dauka yadda nayi zai sa na kasance masoyiyarka tare da tunanin zaka fi kowa jin dadi da sona amman sai naga sa'banin haka wallahi nayi mamaki yaya hisham ban ta'ba tunanin haka daga gareka ba". ta qarasa mgnr cikin rawar murya ya kamo hannunta ya tsarke cikin nashi" yana murzawa ahankali yana jin canjin yanayi a sansar jikinsa ,yayinda soyayyarta ke sake huda zuciyarsa "kiyi hakuri hisham zai dawo miki fiyye da yadda kika san shi a baya ,bazan sake yunkurin cutar dake ba ."wani sanyi dadi taji yana bin jinin jikinta ahankali ta dinga jin gurbin daya fara samu a zuciyarta yana qaruwa ."
Washegari ATA na barin gida aka kira maryam sakonta ya iso take ta shirya ta fita batare da neman izininsa ba ta karbo magani cike da farinciki ta dawo gida ta kira mahaifiyarta ta sheida mata ta kar'bi sakon ,yini ranar cikin farinciki da murna maryam tayisa da yamma ATA ya dawo gida cike da kulawa ta tarbesa da abinci ,bai kalli inda ita da abincinta yake ba ya haye samansa wanka yayi ya sauya kaya ya bar gidan gbdy .hankalinta a tashe ta kira mahaifiyarta tayi mata bayani "umma ki tambaya ko zan iya zuba masa cikin abun shansa dan baya cin abinci sai coffe da ruwan gidan kawai yake sha?to shikenan sai najiki ."
*****
Bangaren maryama kuwa zaman gida ya soma damunta yayinda subai'a tuni ta fara aiki da kamfanin Z&A dan haka ta fara neman aiki sai dai duk inda taje ba'a daukarta aiki tun abun baya damunta yazo ya fara damunta tayi tunanin tayi chart din ammar ko zai taimaka mata dan haka ta shiga what's app dinta tayi masa sallama ya bude amman bai bata amsa ba. ta sake aika masa still ya bude amman babu amsa dan haka tayi tunanin kiransa WhatsApp call bai dauka ba sai ma sakonsa ta gani "lafiya !?kiran me kike min ?"Jikina na rawa ta soma typing "dan allah oga ammar kayi hakuri akan abinda nayi, yanzu nasan nayi kuskure mai girma "ta tura masa."
jin kad'an sai ga amsarsa ta shigo " bakiyi kuskure ba tukun sai anan gaba karki manta don't ever call me again or chart me "inna lillahi wa innna ilahi rajiun allah ka gani taimako nayi allah karka barni da iyawata kabi bayana akan dukkanin lamurana ."
tun daga wannan rana maryam bata kuma wani sukuni ko walwala ba ,har mamakin kanta takeyi dan bata d'auka abun zai dawo ya dameta ba kullum cikin damuwa take da neman aiki bata wani cin abincin kirki gashi kowa ya gane halin da take ciki a gida sai dai kowa ya tambayeta sai tace bata da lfy ne aunty salma kam kirikiri take mata dariya tare da cewa "an gama boko anyi bautar qasa babu riba dole a zaman gida tare damu ."
azumi da nafilflii kullum cikinsu take domin allah ya kawo mata mafuta da samu aikin, abun duniya ya ishi Aunty dan yar magana da take ma yanzu ta rage Ta sake dawowa shiru shiru ga rashin aiki ga aurenta da yaya sadam na matsowa ranar monday ta shirya zata neman aiki aunty tace kar taje koina "me yasa Aunty ?"bazan iya kije ki dawo baki samu ba ki kwanta rashin lafiya nafi bukatar lafiyarki akan aiki ida ma zaki iya muje Asibiti a duba min lafiyarki dan wannna ramar ta isheni" muryarta a sanyaye tace "nifa lfy ta kalau "ina wani lafiya ana ?Kiyi hakuri aunty ki barni naje ."
"Ni baki min laifin komai ba "to amman ai fushi kike dani Kiyi min addua ko zan samu aiki "kullum ina miki addaua amman dai yanzu kinsan kiyi wasa da damarki ta barwa subai'a aikinki ?nasani Kiyi min addua allah ya sake aramin wata damar "allah yasa a dace sai kin dawo allah ya tsare" jiki a sanyaye tace "ameen!"sannan ta fita yau din ma dai kamar ko yaushe bata samu tayi kukanta har idanunta suka kunbura damuwarta ta qaru wunin ranar cikin tsananin damuwa tayisa . yadda take cikin damuwa haka zuciyar ATA ta kasa samun sukuni duk inda ya motsa sai yaji zuciyarsa na luguden bugu da tunaninta duk inda ya motsa yana jinta a jikinsa da zuciyarsa ,wunin yau din wutar soyayyarta sai qaru yake a cikin zuciyarsa ya sauke naunayen ajiyar zuciya ya yunkura ya mike tsaye daga zaunen da yake yana gyara zaman yar saman suit dinsa ."
Dakin dake manne acikin office dinsa ya shiga ya tsaya hannunsa d'aya rike da kugunsa yana qarewa makeken zanenta kallo "to ban zata daidai bane ko ya ?ya tambayi kansa yana zurfafa tunaninsa "amman kuma wannan fuskar nake gani acikin mafarkina "me zai hana kasa a nemo maka kwararrun masu zane su zana maka ita kaga nasu kwarewar ko akwai abinda zai bambamta da naka ?nan take ya amince da shawarar zuciyarsa ya fito yana kiran yaronsa seun cikin kankani lokaci ya shigo cike da girmamawa "yayi masa bayanin abinda yake bukata "amman sir me zai hana ka gwada masu zanen kamfaninka AGC mana "nasan dasu na buqaci wasu dabam ,kaje kayi abinda nasaka "okay sir ya juya da sauri ."yadda yake cikin damuwar rashinta haka itama ta kasance cikin damuwar maseefar rashin aikinta dake bibiyar rayuwata kukan data yini yi ne yasa kafin shida na yamman ranar jikinta yayi zafi tamkar garwashin wuta aunty ce tsaye akanta tana shafe jikinta da jikakke
towel byn ta bata magani tasha ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.