Complete Hausa Novels

Adon Dawa Complete Hausa Novel

Reading file: Adon_Dawa_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 3 of 10

BABI NA UKU
A lokacin dasu kaltum suka cika sati uku a bur sudan dole tasa suka fito neman abunda xa su kai bakinsu, mata da maxa, yara da manya kowa ya ja xugarsu suka shiga gari.
Tawagar ‘yan mata su biyar kaltum, rakiya, huwaila, jidda’u da amina suka fankama garin ADON DAWA don yin bara. Suka kuwa ci sa’a suka samo kudi da yawa wanda xai ishesu su ci abincin yinin yau. Kalmar da suke ambata itace “karama fisabilillahi” sai kaga an miko musu kudi. Su kan basu wahid jine wato kamar naira daya kenan, wasu se su basu hamsin jine ficika kenan idan kuwa suka ci sa’a sai a rana daya saisu hada maitan jine daga nan saisu wuce cikin gari maka makan wajen sayar da abinci (restaurant)su sayo abunda suke so, kamar su kisra wato sinasir ko su sayi esha wato gurasa, wani lokaci saisu hada da ful. Ful wake ne manya manya sai a dafa shi ba gishiri ana ci da gurasa. Idan suka samo kudin bara da yawa saisu sayi baitil mandi shima dafaffiyar shinkafa ce fara sai a kwarara madara akai, a yanka tumatiri da albasa, a yanka karas da kabeji, sannan a dora gasashshiyar kaxa a barbada dan gishiri sannan a ci.
Daga dukkan alamu yunwar da ke addabar su ta fara sauki har sun sami karfin da suke iya debo bokitai da manyan darukan ruwa akansu, su niki tafiya mai nisa sannan su samo ruwan da xa suyi amfani dashi wajen wamka, wanki da wanke-wanke. Ta cikin makabarta suke bi sannan su isa gabar kogin da suke debo ruwan.
Ruwan baya shawuwa saboda jajawur ne mai dandanon gishiri.
Jikin kaltum yakan yi sanyi har takan fashe da kuka idan taga yadda ake binne mutane a makabarta. Saboda sahara ce don haka suke yin dogon rami mai xurfi sosai, wanda mai hakawar sai ya shige ciki sosai yayi xurfi.sai an daina hango shi sannan ya miko hannunsa a kamo shi waje dan ba xai iya fitowa ba. Sannan saisu taru su saka gawa, sannan su jera bululluka a maimakon itace saboda yashi ne itatuwa ba xa su tsaya ba. Allahu Akbar!
Allah Ya sa mu cika da imani, Y a jikan musulman da suka riga mu gidan gaskiya.
Ameen.
A yau kaltum bata bisu bara ba saboda tana son ta wanke kayan jikinta kwaya daya kacal, yayi dakun dakun har gefen xanin ya yage don haka ta yanke shawarar sai kowa ya tafi bara sannan ta rufe gida ta cire kayan ta wanke ta xauna ta jira ya bushe sai ta yi wanka ta saka. Da ta tabbatar mata da maxa sun fita daman tun da sassafe ta debo ruwan wankinta, sai ta tsinci guntayen sabulai ta harhade ta ajiye. Suna ficewa sai ta rufe kofar ta fara wanke riga da dankwali da mayafin ta shanya ta koma gefe ta takure tana jiran su bushe.
Ta duba gabas da yamma, kudu da arewa na gidan sai tace a ranta “yanxu fa a makabarta muke rayuwa alhalin muna raye.”
Ta sake duban katon tudun kabarin da yake gefenta ta mika hannu a hankali ta shafa tace, “ko mace ce ko na miji ne a cikin kabarinnan Allah Shi ya barwa KanSa sani. Allah Ya jkansu da gafara.”
Ta ji hawaye yana sirnanowa daga idanuwanta don tausayin kanta da irin matsananciyar rayuwar da take ciki. Ta tuno gwaggo fattu wacce ta kawo ta nan ta ajiye ta ita kuma ta haye ta yi tafiyarta makka tana can tana jin dadin rayuwarta.
Babban tashin hankalin shi ne iyayenta basu san halin da take ciki ba don su a tunanisu tana saudiya kuma tasan mugun halin gwaggo fattu ba xata yi waya ba ko ta aika wasika ta fada musu gaskiya ba sai dai ta bar su a haka, suma kuma iyayen nata ba waya gare su ba balle su san lambarta ta makka su buga mata su tambayi halin da take ciki. Kaltum ta fi jin haushin iyayenta su da suka yarda suka yarda suka bayar da ita aka taho da ita don basa tausayinta. Ta ji ta tsani kowa a duniya kamar yadda kowa baya sonta, sai ta fashe da kuka mai tsananin ta kifa kai a jikin katakon dakin su. Kuka take yi haikan amma tana fada cikin daga muryar ta “inna lillahi wa inna ilaihi raji’un”
Tsananin bugun da ake yiwa kofar gidan ne ya sata tsagaita da kukan da take yi, ta kasa kunne tana sauraro sannan ta gaskata wani ne yake buga kofa. Sai ta mike tsaye ta yi wuri wuri tana tunanin yadda xata yi. Shawara take yi shin ta je a haka da daurin kirji ta bude kofar, sai dai ai bata sani ba mace ce ko na miji! Idan namiji ne ba xata iya tsayawa da daurin kirji a gabansa ba musamman yadda maxan suke ‘yan iska ko wanka ka ke yi idan baka kula ba saisu yi ta liken ki. Haka idan ki ka yi sake a daki kina barci baki killace jikinki ba sai dai ki ga suna ta xirga xirga ta kofar dakinku suna kallonki a dole wucewa bandaki su ke yi, ko suyi ta leke ta hudar katakon musamman dakin su kaltum da yake kunshe da ‘yan mata.
Ta ji sautin bugun kofar ya kara tsamari don haka ta yayimi jikakkiyar rigarta ta saka ta jawo jikakken mayafinta ta sharba a kanta ta goge idonta saboda hawayen da yayi mata kawanya. Ta isa da sauri bakin kofar ba tare da ta tambaya ba ko waye ta ja sakata ta bude game da wangale kofar. Jikinta na rawa ta dubi wacce ke bakin kofar sai taga madina ce tayi sauri ta duka a tsorace.
Ta ce “sannu da xuwa, yi hakuri ban xo na bude miki kofa da wuri ba ina kokarin saka rigata ne.” madina tayi murmushi t ace”lah ai ba komai kaltum.”
Kaltum ta mika hannu xata kar bi himilin daurin kayan dake kanta sannan ga leda a hannunta. Madina tace “bar shi kaltum, ba komai ba sai kin taya ni ba ai na xo gida mu shiga ciki.”
Kaltum ta dawo tsakar gida inda ta cire jikakkiyar rigarta da mayafinta ta mayar kan igiya ta shanya. Madina kuwa ta wuce cikin dakinsu kai tsaye ta xarce kan kwalin shinfidar ta da jakar kayanta a gefe ta ajiye himilin tsummakaron da ta samo. Ta fito tsakar gida inda kaltum ta daga ido da sauri ta dubeta sai suka yiwa juna murmushi a lokacin guda. Kaltum ta mayar da kai kasa don kunya da girmamawa. Madina tace “kaltum me yasa yau baki fita bara ba!”
Kaltum ta dan yi murmushi tace “kayana ne suka yi datti nake so na wanke sai sun bushe sannan in fita.”
Madina tace “ me yasa sai sun bushe xaki tafi, ki wanke ki shanya sai ki saka wasu kayan ki tafi ki nemo abunda xaki ci, yaushe xa’a ce tun safe baki karya ba har rana tayi yanxu kina jira sai kaya sun bushe!”
Kaltum ta langwabar da kai gefe tace, “ai bani da wasu kayan, kayan jikina ne kadai nake da su, kakata ta tafi da kayana hade da nata ta haye tana cikin wadanda suka tafi makka.” Hawaye ya sarnano daga idanuwan kaltum.
Madina ta tambayeta cike da mamaki tace “au iya mairo ba kakarki bace daman!”
Kaltum tace “kawar kakata ce, garinsu daya tare muka taho dasu, rakiya ce jikarta.”
Tsawon mintina biyar madina tayi tana kallon kaltum saboda tsananin tausayin ta da ya lullube mata xuciya, ta rasa kalma guda daya da xata iya furta mata. Tana tausayin kanta da kanta, amma ta fi tausayin kaltum yarinya karama ba uwa ba uba, ba dangin iya balle na abba a kasar da bata taso ba.
Kaltum ma ta yi shiru kanta a sunkuye a kasa sai kwalla data cika mata ido ta rasa abunda yake damunta saboda kuncin rayuwa.
Madina ta yi ajiyar xuciya ta share hawayen daya cika mata ido, sai ta shiga cikin daki inda ta kwance daurin tsummakaron data shigo dasu ta fara daddagawa tana warewa. Kala biyu riga da siket ta debo ta fito ta mikawa kaltum, kamar an xare mata laka haka ta mika hannu ta karba. Ta kurawa madina ido tana sauraron abunda xata fada, madina ta juya xata shiga daki sai kaltum tace,” wanke miki xanyi!” sai dai babu sabulu, nima guntayen sabulai na tsintsinto a bandaki na yi nawa wankin.”
Madina ta waiwayo ta dubeta sai tayi murmushi t ace “a wanke suke, baki nayi kyauta ki saka nima yanxu nan aka bani su sadaka a garin ‘yan Adon dawa.”
Farin ciki ne bayyane hade da mamaki suka halacci fuskar kaltum ta yi murmushin da har saida wushiryarta ta bayyana yayin da gafen kumatunta ya loba wato (dimple) ta dago da fararen idanuwanta dara dara ta dubi madina ta fada cike da annashuwa.
“anty kin bani kyauta in saka!”
Madina ta yi dariya tace “na baki kyauta kaltum, me ye sa kike mamaki!”
Kaltum, ta sunkuyar da kai kasa ta yi godiya sannan ta fara warwarewa tana duddubawa farin ciki fal a xuciyar ta. Kafin madina ta fito daga daki kaltum ta saka riga da siket cas da ita kuwa kamar dan ita aka saya daidai jikinta sun yi matukar yi mata kyau. Madina ta fito daga daki dauke da wata bakar leda a hannunta tana duban kaltum sai suka yiwa juna murmushi a lokacin guda. Madina ta yaba da yadda kayan ya karbe ta, sannan ta samu inuwa ta xauna a kasa ba tare da ta nemi wani abu ta shinfida ba. Kaltum ta jefa xanin da ta kunce a cikin bokitin data adana sauran kunfar data wanke riga da mayafinta ta fara sabawa . madina ta kwance leda sai ga kisra da ful.
Madina ta dubi kaltum tace “xo mu ci abinci yarinya”
Wannan kalma ta bawa kaltum matukar mamaki wanda har yasa ta dago da sauri ta dubeta har na tsawon ‘yan dakiku masu yawa ta kasa Magana, can ta yi murmushi.
Ta ce “na koshi, nagode.| madina tace, “me kika ci da xaki ce kin koshi.! Ki saki jikinki da ni ki xo mu ci ai xai ishe mu daman dayawa na siyo in ci yanxu sauran inci daddare ba komai, Allah de bani wanda dan ci daddaren.” Tsananin yunwa ce daman ta addabi cikin kaltum banda kugi babu abinda cikinta yake yi saboda ya fafake babu komai tun a bincin jiya da rana bata sake samun abunda xata sakawa hanjinta ba. Ta ajiye wankin ta goge hannayenta ajikin siket din dake jikinta ta karaso a hankali inda madina ke xaune, cikin kunya da nutsuwa ta xauna yayinda hannunta ya dau rawa a lokacin da take kokarin gutsurar gurasar madina ta dubeta, sannan ta tambayeta cike da mamaki.
Ta ce “kaltum lafiya, meke damunki, ya naga kina karkarwa kuma duk kin tsangwami kanki! Haba kaltum ki saki jikinki ai ba wani abu bane duk wanda ya taimaki wani shima Allah xai taimake shi.” Kaltum ta sunkuyar da kai kasa ta fada cikin sanyin jiki.
Ta ce, “ina mamaki ne saboda tun a mota kowa ta kansa yake babu mai taimakon wani ko dai dai da mukurwar ruwa ne sai naga kin bani sutura kyauta sannan kin siyo abinci kince in xo in ci shine na keta mamaki.”
Madina ta yi murmushin karfin hali ta dafa kafadar kaltum tace “yarinya ba haka bane duk masu yin haka jahilai ne, babu yadda xa'ayi musulmai su hadu a waje daya su ce babu wanda xai taimaki dan uwansa musulmi. Babu mai imani ga duk musulmin daba xai so wadan uwansa abunda ya sowa kansa ba.
Ko a lahira aikinmu ba xai kaimu shiga aljanna ba sai dai alfarma albarkacin masu albarka. Kaltum, ki cire wannan mugun tunani a ranki, ki dauka a xuciyarki duk runtsi duk talaucin da kike ciki komai kankartar abu xaki taimakawa wanda ki ka fi ko da babu mai taimaka miki domin Annabi Muhammad (S.A.W) y ace “hannun da yake mikawa shine a sama, ya fi hannun da yake karba shine a kasa.”
Babu wanda kaltum take yi sai gyada kai hakika tana gamsuwa da abunda madina take fada mata. Suka ci, suka koshi suka kora da ruwa sannan kaltum ta yi godiya ta tashi ta je ta ci gaba da wankinta, ta dauraye ta shanya. Dai dai lokacin iya mairo da tawagarta suka shigo, a jigace suke saboda tsananin yawon bara da suka yini suna yi da alama kuwa kwalliya ta biya kudin sabulu saboda kowaccensu hannunta dumu dumu da ledoji. Cikin fara’a kaltum ta tare su gani da yi musu sannu da xuwa. A tunaninsu kwadayin abunda suka samo take don haka kowa ya tsuke fuska babu wanda ya amsa gaisuwarta sai ma dai kauce mata suke yi suna kewaye ta suka nufi daki.
Iya mairo ce ta tsaya tace mata “sannu isashshiya ‘yar gata wacce bata iya wahala ba, kowa ya fita nema ke kina kwance a gida wa xai nemo ya baki a wannan marrar da nafsi nafsi babu mai taimakon wani, keta wanki ma kike yi. Waye ya baki aron Kaya ko kin fara tsayawa sai kinga ba kowa ki bude jakunkunan mutane ki daukar musu kaya! To kada ki sace kayan wani a kama ki kice kin sanni ko kice ni kakarki ce.
Rakiya ma ta leko daga daki ta tsoma baki tace “tun shigowata nake kallonta daga gani kayan nan na wani ta sato saboda bai yi kama dana bola ba kuma bata fita bara yau ba. Tun da safe ta debo ruwan wanki bata kara fita ba.” Sai sauran ma suka tsoma baki babu wacce bata yi mata cari ba a cikinsu.
Kaltum tadago da sauri ta dubi madina yayin da madina ta yi mata nuni da hannu alamar ta yi shiru kada tace komai. Kaltum ta sunkuyar da kanta kasa sai wani kuka na takaici ya kece mata marar kakkautawa. Ta koma gefe ta tsugunna tamkar almajirarsu yayin da kowaccensu ta shiga daki ta baje ledar abincita suka ci. Wasu shinkafa ce da miya, wasu baital mandi, wasu taliya, wata macaroni. Abun mamaki sai suka dinga yiwa madina tayi wai ta xo su ci. ta ce ta gode a koshe take amma babu wacce ta tuntubi kaltum.
Wani kululun takaici ya tsayawa kaltum a wuya ta fara tuhumar kanta tana tambayar xuciyarta wane irin mugun hali nake yiwa mutane haka suka tsane ni! Me nake yi wanda kowa baya sona aka tsane ni!”
Sai tayi xunbur ta mike ta shiga daki wajen shinfidar kwalinta ta dauko robar cin abincinta, yayin da kowacce ta dinga kare abincinta wasu ma suka fara daure ledar abincinsu a tunaninsu rokarsu xata ta yi, ta dube su duba irin na takaici ta langwabar da kai ta matse hawaye sai ta fice, ta yayimi gyalenta ba tare da ta yiwa kowa Magana ba har madina da take xaune a tsakar gida a wajen da suka ci abinci har yanxu bata tashi ba.
Fitarta kofar gida keda wuya sai ta tsaya cak ta dubi gabas da yamma, kudu da arewa babu abinda take gani sai tulun bola da kabarurruka yayin da gabanta kuwa katon kogi take hangowa yana ambaliya. Ta ji a ranta tamkar ta fada kogin nan ruwa ya hadiyeta ta mutu ta huta da bakin cikin rayuwa sai kuma ta tuna da wa’axin da aka yi musu a makarantar islamiyya cewar duk wanda ya kashe kansa ya mutu a kafuri. Ta juya ta dubi kabarurrukan da ke gabanta sai tayi sha’awar dama ace ita ce a ciki a mace ta mutu an binne ta. Ta ji a ranta rayuwar wadannan bayin Allah da suka mutu ta fi mata irin rayuwar da take yi a duniya jin dadi da kwanciyar hankali.
Kamar daga sama ta ji Magana a bayanta, ta waiga da sauri saida suka hada ido da madina.
Ta ce “kaltum ina xaki je!”
Kaltum ta saki fuskarta ta yi murmushin karfin hali. Ta ce “xan je bara.”
Madina tace ki kula da kanki, shawarar da xan baki itace kada ki je garin jange saboda kin ga ke yarinya ce akasarinsu kuma ‘yan iska ne gara ki je garin Adon dawa tunda su na da musulmai xa su fi tausaya miki. Hadari ne ma ki dinga tafiya ke kadai ba’a tawaga ba saboda irinku suke so ‘yan mata ba kamar mu ba manya ba damuwa.
Kaltum ta gyada kai tace “to anty bari in je garin Adon dawan.” Ta juya ta tafi yayin da madina ta dade a tsaye tana kallonta har saida ta kure ta daina hango ta sannan ta girgixa kai don tsananin tausayin kaltum ta shiga gida.
Kaltum tafiya take amma fa har yanxu bata fasa kuka ba harta iske gidajen Adon dawa. Ta fara shiga gida daya bayan daya, Kalmar da take ambata itace “karama fi sabilillahi”
Da alama yau bata fito da sa’a ba daga inda ake kyaleta ta yi ta bara ta gaji ta tafi da kanta sai inda ake yi mata korar kare. Ta yanke shawarar tunda yamma tayi yanxu duk maxan suna kasuwa bari ta je can ko Allah xai sa ta dace. Kaltum ta kama hanyar jim arab, nan ta iske dandaxon maxa kungiya kungiya suna sha’aninsu wasu suna caca, wasu kuwa suna hira suna shan jabna, yayinda wasu suke saye da sayarwasu. Kaltum na fara bara sai ta ci sa’a duk rumfar da tayi bara sai a miko mata sadakar wahid jine wato kamar kandala, farin ciki ya lullube xuciyar kaltum don ada ta shiga wani mawuyancin hali tana tunanin yadda xata yi in har bata samu ko kwabo ba idan ta je gida xasu kusa cinyeta da baki bayan wulakancin kala kala.
Ta ci gaba da bara harta karkashin wata inuwa inda dandaxon samari ne xalla, sun shinfida katuwar tabarma suna ta shan jabna suna caca. Sun kaisu goma sha biyu dukkanninsu shekarunsu basu wuce ashirin da biyar xuwa ashirin da bakwai ba. Shewa da ihu kawai suke yi da alama basu da matsala a rayuwa. gasu a kauye, a cikin gidajen katako da katangar kaya yayin da suturar jikinsu bakin yadi ne mai layi layin fari wacce suke dinka ‘yar shara da wando iyaka guiwa amma koda yaushe sai kaga suna farin ciki ko me yasa. Kaltum take xayyanowa aranta sannan ta bawa kanta amsa “tabbas dole suyi farin ciki a rayuwarsu saboda suna tare da iyayen su, a garinsu, kuma ga dukiyoyinsu” ta katse tunanin da take yi da ta ji suna tambayarta “lafiya, me kike nema a wajenmu!”
Tayi firgigit t ace “karama fi sabilillahi.” Kalma daya ta ji wani daga cikinsu ya fada a cikin yarensu sai taga dukkaninsu sun waiwayo sun kalleta a lokaci guda. Ta yi sauri ta sunkuyar da kanta kasa, da tadago taga har yanxu suna kallonta, sai ta sa gefen gyalenta ta rufe da fuskarta. Daga karshe ta yanke shawarar gaggauta barin wajen tun kafin su iskance ta.
Cikin harshen larabci daya daga cikinsu yace ta xo, kasancewar tana jin larabci sosai tun tana karama sai ta juyo ta dawo wajensu a nutse cikin ladabi amma fa duba daya xaka yi mata ka tabbatar a tsorace take. Ya dubeta sama da kasa duba irin na kurulla yayi dariya ya shafa baki don haka kaltum ta fara fuskantar manufar kiranta da yayi, sai ta fara ja da baya.

To pa, ko ya data kasance tsakanin kaltum da en samarinnan!
Sai ku biyo mu dan jin yadda xata kaya..
.
Typing : Sadin Maa.
Post : Dan Aunty. 👫️‍ADON DAWA 4

Ya fada cikin shagobe “ke me kyau, yaya sunanki!”
Ta na mkyarkyata tace “kaltum”
Su dukka suka maimaita sunan “kaltum” a lokaci guda suka ci gaba da dubanta suna kwada kyawunta, suna mamakin kyawunta don basu xata akwai masu kyau a cikin bakin almajiran nan ba saboda sun dauke su wulakanttatun bayi.
Daya daga cikin su ya dubi shugaban tawagar mai suna Mambela wanda har yanxu bai ce komi ba sai duban kaltum yake yi kasa kasa.
Cikin yarensu yake Magana yace “ranka ya dade shugabana mambela kai ka dace da kyakkawar halittar nan, du da de ba niman mata kake ba, lallai tana da kyau kuma ta hadu. Ya kamata a mika maka ita cikin shagon nan kawai in ka gama sai ka bata alif jine (dubu daya) ka ga sai tayi sati tana cin abinci, gobe xa ka ga ta dawo da kanta.”
Duk da cewar a cikin yarensu ya yi Magana bata ji duk abubuwanda yake fada ba amma ta fuskanci abunda yake fada, don haka sai ta juya da sauri ta fara tafiya. Mambela yace “tabbas yarinyar na ta dace da ni don haka ku dauko min ita, ku shigar min da ita cikin shagon nan.” Ba tare da bata lokaci ba kartai hudu suka bi ta da gudu suka damkota cak suka daga ta kamar kaxa suka nufo inda mambela ke xaune. Tuni robar bararta da yan kudaden data samu suka waste a kasa, ta kurma ihu kai kace rai ake xare mata.
Cikin kuka tace “inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un. Laa ilaha illa anta subhana inni kuntu minaxxawalimin.”
Mambela yace su ajiyeta kasa a gabansa yayin da ta xabura da gudu sai ya damki hannunta ya fada cike da damuwa cikin harshen larabci.
Ya ce”kaltum bkya son kudi ne! bakya son mambela dan sarki, mai kudi da dukiya!”
Ta fada cikin firgicewa da kuka mai tsanani .
“eh, bana so.”
Ya yi murmushi cikin mulki da kasaita y ace “amma ni na ji ina sonki, so mai dinbin yawa kuwa. Yaya xa’a yi ken an!”
Abokansa suka fada cikin fusata “ka bamu ixini mu shigar maka da ita ciki kawai, ka gama da ita mu ma idan ka gama ka bamu sauran, tunda bata da gata a kasar nan waye xai tsaya mata.”
Mambela ya mike tsaye cak yana duban kaltum dake tsugunne a gabansa har yanxu kuka take, gardawan kacokan sun xagayeta babu hudar da xata samu ta arce . mambela ya dade a tsaye yana dubanta daga shi sai mahaliccinsa ya san abunda yake aiyanawa a ransa. Can ya dago ya dubi yaransa daya bayan daya sai yayi murmushi da kyakkyawar fuskar nan tasa, sannan ya yi musu nuni da hannu ko bai furta ba su sun fahimci abunda yake nufi nan da nan suka fara aiwatar da abunda ya umurcesu dasu yi domin ba’a yiwa mambela musu a garin.
Kartai uku ne suka damko ta suna kokarin shiga da ita shago. Ta kurma ihu ta ci gaba da kiran “inna lillahi wa’inna ilaihi raji’un.”
Muryar wani tsoho ne suka ji a bayansu ya fada cikin yarensu, daga dukkan alamu ransa a bace yake, y ace “haba mambela ko sauran ba musulmai ba ne ai kai musulmi ne, ko kunyi niyyar cutar da yarinyar nan albarkacin sunan Allah da take ambata ya kamata ku kyaleta.”
Suka ajiye ta yayin da ta balla da gudu ta je bayan tsohon ta labe, karkarwa kawai take yi. Gyalenta ya dawo wiyanta, kanta babu dankawali sai burtintin kitson da ya tuttuje wanda ya cika da yashi a sanadiyar rashin siminti balle katifa a dakinsu. Tsohon ya juya ya dubi kaltum yayi mata yarensa, sai ta girgixa kai ta yi masa larabci. Ta ce, “bana jin yarenka, larabci nake ji kadai” ya fada cikin harshen larabci “yi hakuri yarinya, daura dankwalinki, goge hawayenki ki tafi gidanku. Ki daina shigowa kasuwa bara wajen maxa ki dinga bararki a cikin gidajen mata ya fi miki alkhairi a matsayinki na yarinya mace budurwa kuma kyakkyawa.”
Ta gyada kai t ace “ nagode, ba xan sake xuwa ba. Baba karaka ni gidanmu tsoro nake ji kada su bini su sake tare ni a hanya.”

Ya ce to muje in raka ki.
Jikinta na karkarwa, hawaye yana kwaranya ta shige gaba tsohon na biye da ita a baya har suka yi nisa.
Mambela ya cije baki ya gyada kai ya dubi abokinsa.
Ya ce “xan jinyata tsohonna idan be daina shiga shirgata ba. Yanxu haka shima idan suka raba daji yaga ba kowa xai iya yi mata lalata, shine mu ya hana mu. Xamu hadu da kaltum wata rana wallahi ba xan hakura da ita ba duk ihunta.”
Abokansa suka ci gaba da xuga shi suna bashi kwarin guiwar gami da daukar masa alkawarin idonsu idon kaltum xa su kamo masa ita.
Har kofar gidansu kaltum tshon nan ya raka ta da gudu ta fada cikin gida ba tare da tayi msa godiya ba saboda a firgice take don tsananin tsoron da ta ke ciki.
Kaltum ta dawo gida da magaruba, kallo daya xaka yi mata ka tabbatar hankalinta a tshe yake ko Magana aka yi mata sai ka ga ta xabura. Babu irin tambayar da ba’a yi mata ba amma amsa daya ta gagara sai hawaye da take xubarwa. Daga ita sai Ubangijinta suka san abunda ya faru amma bata fadawa kowa ba.
Madina ceta ja hannunta tsakargida, suka shafe tsawon sa’a guda tana lallashinta tana bata baki da dubaru iri iri akan ta fadi abunda yake damunta amma kaltum ta ki cewa uffan, sai girgixa kai kawai take yi alamar babu komai. Karshen maganar madina t ace “babu yadda xa’ayi kice babu komi amma kuma kina kuka.”
Ta bata ruwa a buta tace ta yi alwala, ta yi sallah, ta yi addu’a ko me nene ma Allah Ya sawake mata.
Karkarwa hannu kaltum yake yi data dauki buta ta xagaya ban daki, ta fito tana alwala jkinta na rawa, kukan dai bata fasa ba har yanxu. Tana sallah tana sheshekar kuka a bayyane, hankalin madina ya tashi amma sai ta ji haushin kaltum ya kama ta saboda ta ki fada mata matsalarta. Su kuwa su huwaila banda xagi da dungure mata kai babu abunda suke yi suna cewa watakila satar kayan jikinta tayi masu kayan suka doke ta.
Rakiya tace “watakila gidan wasu ta shiga ta satar musu abinci tunda da yunwa ta fita tun jiya bata ci abinci ba.”
Amina t ace, “ko kuma xagin wasu ta yi suka kikkifa mata mari don bata da kunya.”
Iya mairo t ace, “ku kyale ta mana karta fadi abunda yake faruwa tunda bakin hali ne da ita babu mai jin cikinta.”
Kaltum na kudundune a kan kwalinta cikin mayafinta sai kuka take yayin da jikinta yak eta karkarwa. Har kowa y agama cuku cukun kwanciya, aka hure acibal bal wato fitilar da ake cika kwalba da kanaxir ayi lagwani da tsumma.
Duhu ya bayyana a cikin dakin, yayin da gari yayi shiru alamar dare ya tsala, kowane bawa ya kwanta hakarkarinsa kamar yadda masu iya Magana suke cewa dare mahutar bawa. Wannan dare kuwa ya xamarwa kaltum daren jan aiki babba maimakon ta huta sai ma ta tashi tsaye.
Misalign karfe daya na dare kaltum tayi firgigit ta mike tsaye a firgice gami da kwalla ihu mai tsanani tana fadin “wayyo Allah na, ku taimakeni gasu mambela nan xasu kamani.”
Ta tattaka sauran matan dake kwance a tsakiyar dakin burinta kawai ta fice waje da gudu. Gaba daya ‘yan dakin suka tashi a gigice suna riketa, tana bankarewa tana xubar das u sai da ta fita tsakar gida da gudu tana ihu tana fadin.
“su mambela ne xasu kamani, gasu nan xasu kashe ni.”
Madina da jidda’u ne suka bita da gudu suka damko ta suka shigo da ita daki sannan ta dan lafa ko minti biyar ba’ayi bat a sake kwalla ihu ta fice ta gudu. Wannan karon harda iya mairo a masu bin ta da gudu suka cafko ta. Ba ‘yan dakin su kadai ba gaba daya ‘yan sauran dakunan gidan babu wanda ihun kaltum da dawainiyar masu rike ta bai tasa daga barci ba. Kowa ya fito ido luhu luhu saboda barci suna tambayar “me ke damunta!”
“ba mu sani ba.” Amsar da su madina ke bayarwa ken an. Su duka suka kewaye kaltum suna tambaya,
“waye mambela, mutum ko aljan!”
Babu amsa, makyarkyata kawai take yi tana kuka, madina ce mai ilimn kur’ani ita ke tofa mata addu’o’I sannan kaltum tadan lafa harta fara gyangyadi, sannan ta sake firgita ta mike tsaye tana kokarin rugawa da gudu suka damko ta, suka xaunar da ita har yanxu fada take.
“ga mambela nan da abokansa xasu kamani.”
Su dukka sun tausaya mata, kowannensu mata da maxa sai addu’o’I suke tofa mata har saida ta lafa sannan suka koma dakunansu. Wsau suka kwanta amma wasu suna tsaye akanta har saida gari yawaye tangarai sannan kaltum ta sami barci. Sai kowa ya shiga neman ruwan alwala da sauransu.
Kaltum barci take yi haikan mai nauyi wanda bata iya jin duk wani motsi da surutan da ake yi akanta, bata bude ido ba sai karfe biyu na rana. Ta tashi xaune firgigit ta dubi sama da kasa, gefen hagu da damanta sai taga babu kowa sai ita. Ta dinga kokarin tuno komai. Kanta ne yake tsananin ciwo dan haka ta shafe awa guda a xaune ta rasa abunda yake mata dadi. Can ta daure ta yunkura xata tashi sai ta koma jabar ta xauna, ta sake cije baki ta rike katakon ginin dakin ta yunkura da karfi sannan ta mike tsaye. Ta fara tafiya a hankali yayin da kafarta ke xugi a sanadiyar bubbugewar da ta dinga yi jiya. Hakika duk ilahirin jikinta ciwo yake yi musamman kafadar ta saboda ciccibar da abokan mambela da ‘yan dakinsu suka dinga yi wajen jawo ta.
Ta fito tsakar gida ta tsaya ta dubi kowacce kusurwa babu kowa sai ita kadai, ta sake ci gaba da tafiya har saida ta fito kofar gida sannan ta sulale ta xauna a gefen wani kabari ta xura masa ido tana kallo. Sai hawaye ya fara sirnanowa daga idanuwanta, ta fashe da kuka mai tsanani ta fara Magana ita kadai tamkar tababbiya.
Ta ce “a ina nake! Ni wacece! Wa nake da shi a duniya! Me na ke yi a duniya!”
Sai kwakwalwarta ta tuno mata mambela da abokansa a lokacin da suke kokarin ciccibarta xasu shiga da ita wannan shagon, sai ta rushe da kuka. Ta ce “inna lillahi wa’inna ilahi raji’un. Yaya xan yi da rayuwata! Kowa ya tsane ni, kowa baya sona, kowa yana hantara ta, ga kishirwa ga yunwa. Allah Ka dau raina a saka ni a cikin kabari in kwanta in huta in daina ganin kowa, kowa ya daina ganina balle wani ya ji haushina.”
Ta sa hannu ta shafa kabarin ta fada cikin kuka ta tambaya tace “waye a cikin kabarin nan, mace ko namiji! Ina so in xama kamar ku, in mutu kamar yadda kuka mutu. In daina motsi kamar yadda kuka daina, in daina tafiya kamar yadda ku ka daina, in daina bara balle su mambela su kamani.” Yayin da kuka ya ci karfinta ta kasa ci gaba da Magana.
Muryar mai sayar da ruwa ne ya katse ta, ta dago idanuwanta da sauri ta dube shi, sai a lokacin ta tuno tsananin kishirwar da take matukar addabarta. Ta fada cikin wata marainiyar murya “saga dagiga moya hilwa wala murra!” ma’ana mai ruwa tsaya ruwan dadi ne ko na xartsine!
Mai sayar da ruwa ya tsayar da jakunansa ya dubeta yayi murmushi y ace “muya hilwa” ma’ana ruwan dadi ne.”
Ta ci gaba da Magana cikin harshen larabci tace “ka sauke min jarka daya.”
Ya sauko daga kan keken jakinsa da farin ciki yana godiya ya na fadin”Allah Ya yi miki albarka yarinya, kin taimakeni da xaki sayi ruwana yau ko digon ruwa ban siyar ba ban samu ko kwabon da xan yi cefane ba.
Maganar da yayi ya ambaci kudi shi yasa ta tuno dan silillikan data samu jiya da yamma. Sai ta yi sauri ta laluba jikin siket dinta, ta ji ba komai, sai ta tuno ashe sun xube a lokacin da ake ciccibar ta a kasuwa daga kudin har robar bara sun xube. Sai ta ji hankalinta ya tashi ta shiga tunanin abunda xata fada masa. Ya katse tunanin da ta ke yi ya tambaya, “a ina xan juye miki ruwan!”
Sai ta yi firgigit ta dube shi sannan ta sunkuyar da kai kasa, ta sosa keya, ta fada cikin gargadar murya “baba ka yi hakuri ba ni da kudi, ashe kudin ya xube jiya a jim arab. Ko xaka bani kofi daya in sha sadaka saboda Allah kishirwa nake ji.”
Tsoho ya tsuke fuska ya ciccibi jakar ruwansa ya mayar kan jakunansa yah aye, ya kada su suka tafi. Kaltum ta bishi da kallo har yayi nisa ta daina hango shi sai ta sulale ta kwanta a kasa domin a halin yanxu ta kasa kukan ma karfinta yakare. Can ta ji wata mryar kamar daga sama ana Magana cikin harshen larabci yace.
“yarinya, tashi ki karbi ruwa ki sha Allah Ya taimake ni yadda na taimake ki jikata.”
Ta daga ido da sauri sai taga mai sayar da ruwa ne ya dawo . ta tashi xaune da sauri yayin da farin ciki ya lulube mata xuciya, ya sauko daga kan keken jakunansa y ace.
“a ina xan juye miki jarka daya!”
Ta tashi da sauri ta shiga gida ta dauko bokiti ta kawo masa, ya tuttule mata jarka guda har saida bokitin ya cika taf da ruwan dadi. Ruwan da mutu daya baya iya siya a cikinsu sai daisu hada kudi su saya su uku ko su hudu su yini suna sha, ko alwala basa iya yi dashi sai dai su je kogi su dauko ruwan xartsi su yi alwala, wanka da wanki.
Kaltum ta dube shi ta fada cikin lallausar murya “baba, Allah Y dube ka kamar yadda ka dube ni, Allah Ya kawo maka ciniki ka samu na cefane kamar yadda ka taimake ni.”
“amen jikata” Kalmar da yake fada mata ke nan har ya hau keken jakunansa ya tafi yana daga mata hannu itama tana daga masa.
Ta tsugunna ta kafa kai a cikin bokitin ta sha ruwan nan tamkar rakumar da ta bude tankin cikinta. Ta dago ta yiwa Allah hamdala, ta sake kafa kai ta sha, ta sha, harta gaji sannan ta mike ta samu karfin ciccibar bokitin ta shiga dashi cikin gida, bayan ta kama ruwa sai ta shiga yin alwala ta shiga daki tayi sallolin axahar da la’asar domin har la’asar tayi. Tana idarwa amai ya kece mata a wajen da take xaune saida ta amayar da gaba daya ruwan da ta sha. Idonta ya yi jawur ya dinga xubar da hawaye saboda wahala sai a nan ta tabbatar yunwa ceke damunta ta fara tunanin ta inda xata samu abinci ta ci. Motsin shigowar mutanen gidan ne ta xaburar da ita ta yi sauri ta tula kasa akan aman ta rufe sannan ta fito tsakar gida da sauri sai taga ba ‘yan dakinsu ba ne.
Su na ganinta suka fara tambayarta yaya jikinta ta amsa da sauki. Duk da ta shiga rudani bata fahimci sannun da suke yi mata ba . tana tambayar kanta da kanta.’daman ba ni da lafiya! To ciwon me nayi da har ‘yan wasu dakin suke yi min sannu!”
Ta tambayi xaibu ko taga su iya mairo! Xaibu t ace ta bar su a gari ‘yan jange suna wankau, wasu daga cikin ‘yan matan kuma suna wajen sayen abinci suna saya. Kaltum ta yi shiru tana tunanin a ranta tana tababtarwa kanta kanta cewar ko yunwa xai kashe ta ba xasu bata loma daya ba, gara ma madina xata iya bata abinci ta ci amma da kunya jiya ta bata yau ma ta jira sai ta bata.
Xaibu ta katse tunaninta t ace “baki fita bara ba ne yau!”
Kaltum ta gyada kai tace “ban je bara ba saidaI yanxu xan tafi. Ko xaki bani aron robarki in tafi bara tawa ta bata jiya.”
Xaibu ta shiga ta dauko mata roba, a cikin robar da gutsurin gursa. Farin cikin ya lullube xuciyar kaltum, ta karba ta duka ta yi godiya ta yagi gayan gurasa ba tare da tagama taunawa bata hadiye tamkar mayunwancin xakin da yasa mu danyen nama. Fitowar ta keda wuya sai ta sake cin karo da tsohon nan mai sayar da ruwa akan jakunnan sa, ya dubeta yayi murmushi.
Ya ce “jikata, ki godewa Allah, ki yiwa Allah gadiya domin ke ‘yar baiwa ce, ki yi min addu’a ko Allah xai amsa min bukatuna.”
Kaltum ta yi kasake tana dubansa duba irin na rashin fahimta, ya lura da hakan sai ya ci gaba da cewa “na taimake ki daxu, ki kayi min addu’a kuma Allah Ya amsa miki. Ina barin wajenki na samu mai siyan ruwana ya saye dukka ya bani kudina, a yanxu haka jira na yake in je in debo masa wani ruwan in kawo musu xasu juye suba ni kudina. Na manta rabon da in sayar da jarkokin ruwa na duka har sau biyu lokaci guda. Yaya sunan ki!”
Ta yi murmushi ta amsa masa da “kaltum” ya dau waka yana cewa “kaltum ‘yar baiwa, kaltum ‘yar albarka.”
Ya wuce yana rera waka yayin da ta bishi da kallo fuskarta cike da murmushi. Ta fara xaiyano mutanen da suka fara sonta a rayuwa. madina, mai ruwa sai kuma xaibu wacce ta bata gurasa yanxu.
Muryar ‘yan dakinsu ta jiyo haya haya suna tafe suna tayar da kura tamkar dokunan da suke sukuwa. Kallo daya ta yi musu ta sunkuyar da kai kasa don tasan xaginta xasu yi, ta yi mamakin da ta ji su dukka suna yi mata sannu, yaya jiki! Ta amsa musu “da sauki.”
Iya mairo t ace “xaki iya xuwa bara, Amma ki yi sauri ki dawo kar ki kai magaruba don kar kiyi gamo irin na jiya.”

To pa, anya kaltum tana sane da halin da ta shiga jiya kuwa!
Meye dalilinta na shiga wannan halin!
Domin jin amsa, se ku biyu mu…
.
Typing : Sadin Maa.
Post : Dan Aunty 👫👨ADON DAWA 5
.
Kaltum ta tambaya a bayyane “gamo, wane irin gamo!”
Rakiya t ace “kin fi kowa sani ki ke tambayar mutane.”
Suka wuce suka shige cikin gida suka bar ta a nan tsaye tana tambayar kanta abunda suke nufi.
“shin me ya faru da ni jiya har ake ta min sannu!”
Ta nufi garin jange sai ta juya ta kama hanya garin Adon dawa, can ta ja burki ta tsaya cak data tuno abunda su mambela suka yi mata a kasuwa jiya ta yarda robar barar a kasa ta toshe kunne ta tsugunna ta kudundune jikinta kamar wacce xata nutse a cikin kasa. Wani hannu ta ji ya dafa bayanta, sannan ta ji wata murya mai laushi ta ambaci sunanta, kaltum ta dago a firgice sai taga madina ce.
Ta tashe ta tsaye, ta tambaye ta lafiya! Me take yi a tsugunne a nan! Amsa ta gagari bakin kaltum, madina ta yi shiru ta fara tunanin “anya kuwa kaltum bata yi gamo da aljannu ba a garin nan!”
Kaltum tace “bara xanje.” Ta tsugunna ta dauki robarta ta juya tana tafiya madina ta kwalla mata kira, kaltum ta waiwayo ta kalleta. Madina t ace “kin tabbata xaki iya xuwa bara yau! Domin baki da lafiya.”
Kaltum ta gyada kai t ace “xan iya xuwa” madina ta bita da kallo har said a ta yi nisa sannan ta juya ta shiga gida.
Garin jange kaltum ta je, daga dukkan alamu sun fara gajiya da barar nan ta su. Tun da safe su iya mairo suke abu daya, bayan wanki da wanke wanke da suka yi musu don haka basu da sauran wani aiki da xa’a yi musu kuma. Sai dai ta hadu da wani tsohon banxa wanda ya nemi ya kaimata cafka ta daka tsalle ta fito daga gidansa, har kofar gida ya biyota wai in ta yarda dashi xai bata kudin abinci. Don haka tunda ta juya ta fara sauri bata tsaya a ko’ina ba sai garin Adon dawa. Ta yi bara a gida daya bata samu ba, a gida na biyu sai ta ci sa’a ta samu shinkafa gaya ko gishiri babu aka cika mata robarta. Farin ciki tamkar anyi mata albishir da gidan aljanna, a kofar gidan ta durkushe ta dinga ci tamkar ta hada da yatsunta saboda yunwa, dadin gayar shinkafar da ta ke ci take yi kai ka ce da miyar kaji take hadawa. Shakewa take yi saboda rashin maiko ga babu ruwa a kusa.
Ta kusa cinyewa sai taga wata kwababbiyar kafa a gabanta wacce ta yi kama da kafar samudawan da. Ta dago ido da sauri sai taga wani sarkacecen saurayi dogo baki faffada a tsaye akanta da bakaken kaya. Saboda firgici sai shinkafar dake cike a bakinta ta fara xubowa yayin da laumar da ta debo a hannunta ta waste kasa saboda makyarkyata tana tunanin a inda ta taba ganin wannan halittar.
Bata jin yaren da yake yi mata sai dai ta yi kara mai tsanani ta tambaye shi da larabci me yake so a wajenta! Me tayi masa! Ya girgixa kai cikin harshen larabci y ace “ba ki yi min komai ba sai dai uban gidana yake neman amincewar ki.”
Ta tambaya a gigice “waye uban gidan naka!”
Yayi murmushi yace “mambela.”
Sannan yayi mata nuni da hannunsa, ta juya a hankali ta dubi inda ya nuna mata mambela da tawagarsa ta hango a tsaye suna dubanta. A inda taji wani mummunar faduwar gaba wacce ta fi wacce ta hadu da ita da farko. Kalmar “inna lillahi wa’inna ilaihi ra ji’un” ta ambata yayin da ta xura cikin gidan da aka bata sadaka da gudu. Cikin harshen larabci ta ke cewa “ku taimakeni mambela ne xai kama ni.”
Daga dukkan alamu ta tsorata matan gidan kasancewar duk saida suka xabura suka mike wasu kuwa har sun runtuma cikin daki da gudu. Da suka fahimci abunda take fadi sai wasu suka hau xaginta suna tankadar keyarta waje, wasu kuma daga cikinsu suka tausaya mata suka jawo ta cikin gidan.
Karkarwa take tana fadin “ni musulma ce, ku taimake ni ku biye ni xasu kashe ni.”
Hayaniya ta tashi tsakanin matan gidan su biyar uku suka ce kaltum sai ta fice ta bar musu gida saboda kada fushin mambela ya shafe su dan tsoransa ake yi agarin. Mabela yaro ne dan gata gaba da baya iyayensa masu arxiki ne, kakanninsa masu sarauta ne, yaro ne kwalli daya tak a wajen uwa da uba kuma shine kadai jika a wajen kakanninsa don haka ba’a saka shi, ba’a hana shi.
Daya daga cikin matan biyu da suke so su taimaki kaltum tayi fushi ta shige daki da taga hayaniyar ta yi yawa, fushi ta shige daki da taga hayaniyar ta yi yawa, yayin da dayar tace xata fita ta roki mambela ya kyale kaltum kada ya taba ta, amma in har mambela bai yarda ba sai ya taba kaltum to tabbas ba xata bar yarinyar nan ta fita ba sai dai in a cikin dare mambela ya sakawa gidan wuta.
Daga karshe dai aka fi karfin ta matayen nan uku suka turo kaltum kofar gida suka datse kofar gidansu, ta yi ta buga kokarin bankare kofar da karfi ta shiga tana ihu ba a bude mata ba, ta juya baya ta dubi inda su mambella suke tsaye, hakika har yanxu suna kallon gudun ruwanta se rada suke yiwa junansu, suna shawarta yadda xasu bullo mata. Ta kwalla ihu ta fashe da kuka ta sake kama katangar gidan ta kaya ta wujijjiga yayin da dukka hannayenta suka huhhuje jinni ya dinga xuba, can se taga matar da take son taimakon ta wacce aka hana ta boyeta ta a jikin Katanga ta dubi kaltum tana hawaye itama, cikin harshen larabci.
Ta ce “yarinya ki yi shiru ki kwantar da hankalinki xan taimake ki, amma sai kema kin taimaki kanki.”
Kaltum ta tsagaita da kukan ta dubi matar daga duk alamu bata fahimci abunda matar take nufi ba. Matar ta mika mata wani dan karfe karami dogo mai kama da axurfa. Kaltum ta karba ta jujjuya da alama bata san abun ba.
Matar ta sharce hawaye t ace “ki danna gefe ki gani.”
Kaltum ta danna, tana dannawa sai ga wata wuka kakkaifa ta fito fit. Hannun kaltum ya hau karkarwa ta fada a gigice “wuka ce.”
Matar t ace “sake dannan gefen.”
Kaltum ta sake dannawa sai tsinin kan wukar ya sake komawa ciki ta dawo ‘yar karama kamar da. Bakin kaltum na karkarwa ta tambiyi matar t ace “me xan yi da ita!”
Matar t ace “ki kwaci kanki da ita, duk wanda xai cuce ki ki kare kanki da ita, ki kashe duk wanda yake kokarin ya kashe ki, ki yanka duk wanda yake son ya yanka ki kafin ya yanka ki.”
Kaltum ta damke wukarta a hannu ta runtuma da gudu ta nufi hanyar garinsu, babban tashin hankali sai taga gardawan nan a guje suna biye da ita. Ba tare da bata lokaci ba suka damko ta tamkar kaxa haka ta ji sun cilla ta gefe, sai gata a kasa wanwar ta fadi ta yi ruf da ciki yayin da gardawa shida suka xagaye ta. Ta daka tsalle ta tashi tsaye da sauri ta kudindine jikinta da gyalenta tana kuka. Ta na cewa “me na muku, me ku ke so da ni!”
Se yanxu mambella ya karaso gareta, yana tafe yana takama tafiya ta kasaita ya tsaya a gabanta. Ya yi murmushi y ace “ke mai kyau, ya ki ke wahalar da ni ne don ina son ki! Ba kida labarin mambela a garin nan, baki da labarin ina da kudin da xan iyan siyanki keda iyayenki idan ma kina dasu! kar ki manta kasarmu ce nan, arxiki ku ka xo ci. Wuce mu je wancan gidan kafin na illata ki.” Ya nuna mata wani gida da hannu. Kaltum ta girgixa kai ta fada cikin kakkausar murya t ace “ba xan je ba, babu inda xan je sai dai ku kashe ni.”
Sauran suka kufula suka nufo ta a fusace xasu cafke ta sai ta daka tsalle gefe da sauri ta matsa gefen wukar dake hannunta kan kace kwabo wata kakkaifar wuka mai kyalli ta fito. Sai su dukka suka tsaya cak suna kallonta. Ta daga hannunta dai dai sangalin hannunta ta sa wukar nan ta keta da karfi, nan da nan wani sharbabben yanka ya bayyana mai tafe da jinni jawur ya fara gudana a kasa. Mambela ya raxana ya runtse ido saboda jinin day a gani yana xuba, sauran kuwa suka dakka tsalle gefe.
Ta ce duk wanda ya matso kusa da ni sai na yanka shi kamar yadda na yanka hannuna. Kun gani da idonku yadda na yanka hannuna jinni yana tsartuwa to ku tabbata xan iya yanka ku har lahira. Ku rabu da ni, ba ruwana da ku.”
Mambela ya kira sunayensu daya bayan daya, y ace ku xo mu tafi ku rabu da ita xamu hadu da ita wata rana.”
Sai suka juya suka tafi suka bar ta a wajen a tsaye, suna tafe mambela na waiwayanta har saida suka daina hangota. Tasa wukar ta yanki gefen gyalenta ta daure hannunta wajen yankan duk da haka hannun bai daina xubo da jinni ba, sai xuba yake ba kakkautawa. Ta danna gefen wukar tsinin ya koma ciki ta bude rigar ta, ta saka wukar a ciki ta juya ta tafi gida, kuka take yi a hanya tamkar ranta xai fita.
Tun daga kofar gida maxa suka fahimci jinni ke xuba daga hannunta, tambayata suke yi amma bata amsa ba ta shige cikin gida kai tsaye. Jama’ar da ke cikin gida suka taru akan kaltum suna tambayarta “lafuya, a ina ta yanke jinni yake xuba haka! Ta wuce daki da gudu ta fada kan kwalinta ta rike hannu jinni ne ke gudana, kuka take yi tun karfi saboda tsanani xugi radadin da yake yi mata babu wanda bai shigo ya tambayi kaltum ba amma bata amsa ba har bakinsu ya gaji da tambaya yawun bakinsu tamkar xai kare.
Jidda’u ta dubi iya mairo t ace “wai ni wannan kaltum din mutum ce, ko dai ba mutum b ace aljana ce! Ni fa na rasa kanta tsakanin jiya dayau.” Rakiya t ace “iskanci ne take ji das hi kala kala gara mu koreta daga dakinmu, idan aka bibiya ma sata take yi ake dukanta.”
Huwaila t ace tabbas biri yayi kama da mutum saboda kayan da yake jikinta ma na sata ne ai bata da Kaya ko daya.”
Aibu t ace “ba wannan ba ma, ina roba ta da kika karba xaki je bara daxu ba dai kin batar min ba nima kamar yadda kika batar da taki!”
Malam lawan y ace “ku yi mata a hankali mana jiri ne fa yake daukarta ku kalli idanuwanta bibbiyu take ganin mu, gashi asibiti sai an kasha kudi da sai a goyata a kaita.”
Madina ta tashi da sauri ta je ta bude jakar kayan aikinta sai ta dauko wata ‘yar karamar jakar hannu ta umurci jama’ar da suka baibaye kaltum das u marmatsa sannan ta umurci huwaila ta rike mata acibalbal ta haska mata. Koya yayi cirko cirko yana kallon madina suna son suga abunda take shirin yi. Ta bude jakar sai ga kayan asibiti burjik kamar su spirit, panadol, gestid, iodine da shan-shan bali. Ta yi mata allura a gefen ciwon don tsayar da jinin da yake xuba kan kace kwabo jinni ya tsaya, sanna ta fara xarga xare da allura tana daurewa. Ta dinke hannun nan tsaf, xafi ya addabi kaltum babu abunda take yi sai runtse ido hawaye na ta kwaranya, madina ta saka mata plasta ta like, sanna ta bata panadol ta sha ta kwantar da ita ta lullubeta da xani. Jama’a suka dinga mamaki suna tambayar madina ashe dama ita likita ce! Ta yi murmushi kawai domin babu amsar da xata iya basu, kowa ya waste ya shiga dakinsa. Ba’a hana mutane Magana da bakinsu musamman mata, sharrace sharrace iri iri da kage-kage akan kaltum suna fassara sanadiyar jin ciwonta sun fi dangatawa da watakila sata ta yi aka yanka mata hannu amma jama’a da yawa musamman madina sun musanta hakan don sun yaba da hankalin kaltum cewar ba xa ta yi haka ba. Allah Shi Ya barwa kanSa sani daga karshe suka gaji da Magana sannan kowa ya kwanta.
Tsakar dare misalin karfe biyu kaltum ta runtuma da gudu tana ihu fadi take “wayyo Allah na ga sunan xa su kamani mambela da abokanan sa ne”
Dole kowa ya tashi a firgice aka riketa, yau ma kamar jiya a tsaye aka kwana ana yi mata addu’a, kowa ya dinda tofa mata duk addu’ar day a iya wanda ma bai iya ba yana tofa mata yawun bakinsa.

(irin su o’o ken an, ni kuma na yi dariya……. Na ce dai ayi hankali, kar a topa min yawu ……..)

Da gari yaw aye tangarai kaltum ta sami barci yayin da hannunta wajen yankan ya kumbura sumtum saboda bibbigewar data dinga yi wajen ficewa da gudu. Kaltum abun tausayi har hawaye madina take yi don tausayinta.
Har axahar bata farka ba bata ma san har kowa ya fita ya barta ba har said a suka daddawo daga bara sannan ta bude ido. Madina ta gani ta riko hannunta ta tashe ta xaune ta girgixa ta, t ace “kaltum dube idonki tashi ki ci abinci kiyi sallah.”
Sai ta ji tamkar a mafarki ta manta rabon da ace mata ta tashi ta ci abinci kyauta ba tare da ta je nemo wa ba. Ta mike a hankali ta shiga bandaki ta rage faitsarin day a cika mata mara, tana fitowa tadaura alwala, a daddafe ta yi sallar da ake binta. Tana idarwa madina ta miko mata leda a cike da taliya dafaffiya da miya don haka kaltum bata yi wata-wata ba ta dinga xabga lauma.
Harara irir iri hade da tabe baki kawai sauran ‘yan dakin suke yi mata, wani abunda ya sake basu haushi ma shine hatta ruwan da xata sha saida madina ta kawo mata gabanta. Haushi ya sake karuwa a xukatansu sai suka shiga habaice habaice da jan dogon tsaki harda tsartar da yawu. Madina ta yiwa kaltum nuni da hannu ta yi shiru kada ta daga ido ta kallesu. Daga dukkan alamu kiyayyar da ake nunawa kaltum ta fara shafar madina saboda ita bata biye musu a dinga kyarar kaltum.
Iya mairo ta dubi madina ta tabe baki t ace “madina yarinyar nan kaltum fa ba’a wajenki kakarta ta dankata ba, haka baki san tsakaninmu ba har ki ke kokarin raba mu da ita. Kina son ki sangartar da ita alhali ba gata kike yi mata ba, cutar ta ki ke yi saboda yau idan aka ce kin gaji kin daina nemo mata abunda xata ci ita kuma bata iya nema ba yaya ki ke tunanin xata yi! Sai dai ta fara daukar na wasu.”
Madina ta yi murmushin karfin hali t ace, “iya mairo a ganina kaltum yar uwata ce a musulunce tunda dukkan mu musulmai ne kuma ban hana kaltum fita bara ba idan tana da lafiya yanxu ma dan bata da lafiya ne yasa na nemo mata abinci ko da ace haka kawai na nemo na bata taimako ne saboda kaltum yarinya ce xan iya kiranta marainiya tunda bata da uwa da uba a nan.”
Maimuna ta hasala ta katse madina t ace “in xancen yarinta xaki yi ai rakiya it ace karama a dakin nan, ita da take tare da kakarta ma wannan gatan bai sa ta nade kafa t ace aljannu sun taba tab a.” sais u dukka suka hau kunfar baki ana tsuye madina da kaltum. Amsa daya madina bata sake mayar musu bat a yi musu shiru ma’ana shiru ma Magana ce inji masu iya Magana.
Cikin dare kaltum ta sake firgicewa tana ihu da guje guje ana riko ta, madina addu’a kawai take ta tofa mata sannan can ta lafa. Duk da ‘yan dakin basa so su katse barcinsu akan kaltum dole kowacce ta tashi, idan kaltum ta fara ihu da guje guje ba xasu iya kwanta hakarkarinsu ba har sai sanda kaltum ta samu barci sannan kowacce xata rintsa.
Yau ma madina ta hana kaltum fita bara t ace ta xauna xata je ta samo mata abunda xata ci. Kaltum ta nuna xata iya xuwa bara saboda gudun xagin da ‘yan dakin ke yi mata, madina t ace ta yi xamanta ita xata nemo mata.
Kafin axahar madina ta dawo dauke da abinci mai yawa, ta yi sa’a aka ciko mata kwanonta da abinci mai xafi sadaka, suka hadu suka ci suka koshi su biyu. Kaltum ta yiwa Allah godiya ta yiwa madina godiya.
Kwanci tashi said a kaltum ta shafe sati guda cur a gida bata fita bara ba sai dai madina ta nemo mata har said a ciwon hannunta ya kame ya fara warkewa. A ranar da kaltum xata fara fita bara madina t ace da ita “kaltum ki bi kawayenki ku tafi bara tare kada su ce na raba ku tunda ada tare ku ke xuwa. Kin ga ni ban cika yawon bara ba ina da gidaje biyu da nake aiki a garin jange, ina yi musu wanki ko dahuwar abinci, in yiwa yaransu wanka sannan su bani ladan kudi ko abinci dafaffe ba xasu yarda mu je tare ba suna biyan mutane biyu ba.”
Kaltum ta ji gaban ta ya yanke ya fadi tana fargabar yadda xata kasance a cikin su huwaila. Hakika xa su yi mata korar kare don suna jin haushinta matuka. Kaltum tana tsaye a kofar gida tana jiran fitowar su iya mairo don madina harta yi gaba. Suna fitowa suka kalleta suka bar ta anan a tsaye, said a ta bari sun yi nisa sannan ta fara bin su a baya idan sun waiwayo sun kalleta sai ta tsaya cak har suka tabbatar su take bi amma fa tsoransu take ji matuka.
Hankalinta ya tashi da taga sun nufi jim arab kasuwar adon dawa sai ta fara jan burki tana kokarin tsayawa. Tana tsaye daga nesa ta ki karasowa cikin kasuwar tana hangen su suna bin rumfa suna bara da lama suna samu don taga ana ta miko musu kudi ko dabino. Sai ta fara tahowa a hankali amma tana ta addu’a kada Allah Ya hada tad a su mambela.
Ta iske wani tsoho mai sayar da namijin goro a runfarsa, sai ta yi bara, ya tsakuro namijin goro guda hudu ya miko mata, ta sa hannu a sanyaye ta karba yayinda suka hada ido da tsohon sai suka shaida juna. Wannan tsohon ne day a kwace ta daga hannunsu mambela. Sai yayi mata duba irin na tausayawa y ace “yarinya baki daina shigowa kasuwar nan ba ko kamr yadda na shawarce ki, sai yan iskan yaran nan sun sake far miki ko!”
Ta xubo hawaye ta fada cikin wata siririyar murya “baba, yunwa nake ji dole ta sani nake fitowa.” Sai yayi shiru da alama yana tausaya mata, sannan ya dauko kamsa jine ya bata hakika kudin nan ya isheta ta sayi abinci ta ci ta koshi a yau don haka sai ta yi murmushin jin dadi, ta durkusa ta yi godiya ta karba. Ta juya xata tafi kamar daga sama ta ji muryar rakiya ta kwalla kiran sunanta, ta waiga da sauri sai ta hango su a kofar wata rumfa suna tsaye carko carko dukkansu. Sai ta nufi inda suke tsaye xuciyarta cike da mamaki da kuma fargabar ko me nene dalilin kiran da suke yi mata. Jikin ta na rawa ta isa gare su.
Rakiya t ace xo ki yiwa wannan mutumin larabci tundaxu yake so ya bamu kudi sai larabci yake yi mana mu kuwa bama ji.
Kaltum ta cusa kai cikin rumfar dan ta jiyo musu abunda yak e cewa sai ta hada ido da mambela. Yayi murmushi ya fada cikin harshen larabci yace, “sannu da xuwa yake abar kaunata a ko da yaushe, ce musu nayi su kawo min ke xan basu metan jine (dari biyu) ke kuma idan kin amince da nixan baki alif jine(dubu daya) ya ishe ki ki ci abincin wata guda idan yak are in kara miki.
Kaltum ta tuntsura ta fadi kasa saboda fargaba ta mike a guje ta falfala da gudu kai ka ce gudun fanfalake take yi saboda tamkar kafarta xata tabo keyarta. Mamaki ya kama su iya mairo suka rasa abinda ya fada mata su dai sun gay a mayar da kudinsa aljihu sannan yayi musu korar kare.

.
Subhan Allah.
Allah Ya raba mu da kunci na rayuwa ko wacce iri ce..
Aamiin...
.
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 6
BABI NA HUDU

Gari yaw aye hantsi ya keto, yayin da fataken gidan nan suka dinga baxama neman abunda xasu kai bakin salati. Kaltum a xaune take a tsakar gida cikin hantsiba sunkuye a kasa da alama rashin lafiya a jikinta. Mutanen gidan mata da maxa suka yi ta tsayawa a kanta suna tambayarta shin lafiyarta kalau ko jikin ne! sai ta girgixa kai t ace das u lafiyarta kalau, ba tare da tad ago ido ta kallesu ba. Hajara c eta fito daga cikin dakinsu ta tsaya akan kaltum ta dade a tsaye tana harar ta. Kaltum tad ago ido a hankali ta dubi wacce ke tsaye a kanta, kallon da hajara tayi mata na wulakanci shi yasa ta gane bada alkhairi take nemanta ba don haka sai ta mayar da kanta kasa ta sunkuyar.
Hajara ta girgixa kugu t ace “kaltum, na rasa robata da gurasa aciki wacce na ajiye jiya da daddare a wajen shinfidarki.”
Kaltum ta girgixa kai t ace “ba ni na dauka ba.” Hajara ta fusata t ace, “wane shegen ne xai dauka idan ba ke ba! Ko kin dauka bamu da labarin sace sacen da ki ke yi a gari!”
Kaltum tad ago da sauri ta dubi hajara hakika ko ba’a fada ba kaltum taji haushin maganar amma sai ta maida kanta kasa ta sunkuyar. Iya mairo da jikarta rakiya suka fito suka dubi kaltum suka ce “yauma ba xa ki je bara ba, sai kowa ya tafi bara an bar miki gidan sannan ki lalube mana ‘yan abubuwanda mka ajiye ko!”
Huwaila t ace ai ba lefin kowa bane laifin madina ce da ta shagwabata, sai ta je tayi aikatau hard a jido ruwa a biya ta amma ta je ta siyo musu abinci ta kawo su ci tare shiyasa ma bata fita bara sai taga dama. Taci ta koshi dare yayi ta dinga ihun karya tana hana mu barci.” Amina ta fito daga daki t ace “idan gari yaw aye saita kwanta tayi ta barci har yamma mu kuma mu fita nema mu yini muna yawo lokacinda ya kamata mu kwanta sai ta hana mu barci, gaskiya a raba man daki dan yanxu ma ciwon kai na ke yi saboda rashin barci.”
Hawaye ya dinga xuba shaf shaf shaf daga idanuwan kaltum. Madina c eta fito daga wanka sanye take da hijabi sa daurin kirji ta karasoi da sauri inda suke t ace “haba ku kuwa bayin Allah me kaltum tayi muku a rayuwa da kuka takura mata haka! Xagin safe daban na rana daban dan kun ga bata magan, ku kira ta barauniya, ku kira ta ‘yar iska, ku ce mata munafuka. Da me xa ta ji, ciwon dake addabarta! Baku ganin da xaxxabi take kwana kullum saboda raunin da ke jikinta! Ku tuna fa ku musulmai na Allah Yan a son kaltum tunda Shine Ya halicce ta. Baku ganin hakkinta da ku ke dauka xai iya kaiku wuta, shirun nan da take yi tsananin hakuri ne, hakurin da take yi bata rmawa xai iya sawa Allah Ya yi mata sakayya da KanSa.”
Maimuna ta katse ta , tace “madina dan Allah kiyi mana shiru ke ba kya ganin laifin kaltum, ke c ma mai xuga ta har wata rukiyya kike mata wai ita mai aljannu, mu dai gaskiya tana hana mu barci mun gaji.”
Madina ta ji hawaye yan surnano mata daga idanuwanta dan takaici, ta share hawaye ta dubi maimuna t ace “haba maimuna ban taba xata ba wannan maganar xata fito daga bakinki a matsayinki na babba. Shekarunki talatin da biyar kin haifi kaltum hard a ma wadanda suka girmi kaltum. Kinsan ciwon haihuwa, kin san dadin ‘ya’ya dan kusan kullum kina kuka idan kika tuna ‘ya’yanki da kika baro, ban dauka xaki ki tausayawa ‘ya’yan wasu baa she xaki biyewa rakiya, huwaila, amina ‘yan matan da basu taba haihuwa ba!
Ke ma hajara ba yarinya bace tunda kin kusa haihuwar kaltum shekarunki ashirin dad a biyar ‘yayanki uku. Ba kwa tunanin abunda ka yiwa ‘yar wani sai an yiwa naku! Iya mairo kin ci amana tunda yarinyar nan ke aka dankawa amanarta da tun kakarta bata tafi ba sai ki fada mata baki karba ba, amma kika karba ki ka xo kina banbanta tad a jikarki. Ko ba komai kece wacce kuka fito gari daya ko albarkacin sanin asalinta da ki kayi bai kamata kiji ana kiranta barauniya ba kiyi shiru.”
Kan kace kwabo hayaniya ya hargitse tsakanin madina das u dukansu. Harda masu dammara xa’ayi dambe. ‘yan sauran dakunan suka fito maxa da mata suna bada hakuri, da yake duk fita xasu yi daman sun shirya dan haka aka tura su maimuna waje ita kuma madina aka tura ta cikin daki, sannan kunnuwansu suka huta da hayaniya. Kaltum tana xaune har yanxu kantga a sunkuye yake a kasa.
Madina ta dade a daki bata fito ba sai shehshshekar kukanta ka ke jiyowa daga cikin dakin da alama kuka ta ke yi. Sai da ta tabbatar ba kowa a gidan sais u biyu sannan ta fito tsakar gida a fusace ta dubi kaltum. Ta kira sunan kaltum, sai tad ago a gigice hankalinta a tashe ta dubi madina ta amsa kiran da tayi mata.
Madina t ace “ki kula da abunda xan fada miki, ki fahimci a inda kike da kuma abunda kike ciki. Ki sani xaman nan da mukeyi xama ne na kowa yayi ta kansa.” Kaltum ta ci gaba da kallonta sokoko da alama bata fahimci abinda take fada mata ba.
Madina ta ci gaba da cewa “ban hana ki yin hakuri bad an Allah Yana tare da mai hakuri, yana dad a kyau yin hakuri, amma ina baki shawara ki tashi haikan ki kwatarwa kanki hakkinki na ‘ya dank e ba baiwa b ace. Saboda me xaki xama sakarya a cikin al’umma, ki xama juji wacce ake xuba mata shara da aka yayimo daga ko ina! Yara da manya kowa kaltum yake tsangwama bakya katabus sai kuka, to ina mai baki shawara ki nutsu kisan abunda kike yi.”
Hawayen kaltum k eta ambaliyar xubarwa shiyasa madina ta kasa ci gaba da magan sai itama ta fara hawayen.
Madina ta share hawaye da gefen hijabinta t ace “kaltum Allah Yayi miki xurfin ciki wanda duk irin tambayar da xa’ayi miki baxa ki fadi halin da kike ciki ba,
Abubuwa da dama sun faffaru wanda ya kamata ace kin samu mutum daya kin fada masa amma kin ki. To ki sani wannan kunshe kunshen da kike yi a xuciyar ki ba komai xai jawo miki ba sai ciwon xuciya ko hawan jinni. Kina yarinya karama xa’aji tuf kin fadi xuciyar kit a fashe.
Gara ki dinga amayar da abunda yake damunki, wacce kika san xata rufa miki asiri ki shawarce ta tunda kin rabu da iyayenki da ‘yan uwanki dole ki samu wasu su xamar miki abokan rayuwa da aminci.”
Har yanxu kalma daya bata fita daga bakin kaltum ba, hawaye kawai take yi kanta a sunkuye a kasa.
Madina ta rike kugu ta fada cikin fushi da kunar xuciya t ace “kaltum, waye mambela!”
Wannan karon a gigice kaltum tad ago ta dubi madina duba mai tafe da tsantsar mamaki gami da faduwar gaba. Madina ta sake maimaita tambayarta, nhar yanxu ba amsa daga bakin kaltum tambaya ta uku da madina xa tayi bada baki ta yi mata ba, wani wani xabgaggen mari ta kifa mata mari wanda said a kaltum ta kwanta kasa ta rike kunci yayin data fahse da kuka mai tsanani.
Madina ta fisgo hannunta ta xaunar da ita ta rike kunnenta na hagu da karfi har said a kaltum tayi kara. Madina t ace “waye mambela! Ko kuma wacece mambela idan mace ce! A ina take! Me yake faruwa a tsakaninku!”
Kaltum tana mai matukar mamaki inda madina ta ji sunan mambela, sai ta shiga tunanin waye yake labewa har ya san abubuwan da suka faru tsakaninta da mambela, domin ita bta san abubuwanda take yi a cikin dare ba, bata san tana fita da gudu ana rike tab a har take ambatar gasu mambela nan xasu kasha ni har kowa ya ji.
Madina ta tunkude ta gami da rankwashin goshinta t ace “to yau rabuwarmu ta xo ni da ke, yau ne rana ta karshe dana nuna na sanki, nasan sunanki a rayuwata, kema kuma koda wasa kada ki sake nuna wa kin taba ganina a rayuwarki. Hanyarki daban, tawa daban bari ma sauran ‘yan dakin su xo su kore ki daga dakinmu baxan hana sub a saboda na fahimci xama da irinku hatsari ne, xaki iya kasha mutum ba’a sani ba saboda xurfin cikinki yayi yawa, bana xama da masu hali irin naki. Ashe su iya mairo sun fin gaskiya har nake dukan kirji nake fada a kanki, babu ruwana dake har abada haka ko xaki fice waje da gudu da tsakar dare ba xan kamo ki ban a daina sai dai in kin tafi a rasa ki, ki koma can wajen mambela ko mutum ne ko aljani ne, ko matattune oho. Na daina damun kaina a kanki, na daina tausayinki, na daina shigar miki fada, duk abunda mutane xa suyi miki ido ne nawa.”
Madina ta shige daki a fusace ta ratayo Jakarta kamar mai shirin fita unguwa ta fito ta iske kaltum a durkushe a bakin kofar dakin tana kuka mai tafe da ruri idanuwanta sun yi jawur kallo daya madina tayi mata ta Harare ta, ta dauke kai tana kokarin kewayeta ta fice sai kaltum ta rike kafarta.
Ta ce “aunty madina, kiyi hakuri ki yafe min abinda nayi miki.”
Madina ta tsaya cak t ace “ai ni baki min laifi ba, shawara na baki baki dauka ba. Tambaya nayi miki baki amsa bad an haka xama dake ba xai yiwu ba, bana xama da masu bakin hali da xurfin ciki. Na kasa gane ko ke wa cece, ko ina kika dosa, ko wane hali kike ciki! Dan haka na rabu da ke kaltum kamar yadda na rabu da ‘ya’yan ciki na a Nigeria. Kinsan kuwa tunda na rabu da ‘yayan ciki nab a xai yi wahala in rabu da ke ba wacce na hadu dake a hanya a kwanan nan. Ni haka nake al’amurana xaman yarda na ke yi da mutum, da xarar babu yarda to bana kara yin ko second daya xan matsa daga wajensa. Kaltum, ko baki bar dakin nan ba hakika nix an bar miki dakin a tunanina ada na dauka ke mutuniyar arxiki ce, ashe bah aka ki ke bad an haka na daina tausayinki ki je ki karata.”
Madina na rufe bakinta sai ta fisge kafarta daga hannun kaltum ta juya a fusace xata fice, cikin kuka mai tsanani kaltum ta sake wawuro xanin madina ta riketa kam tana cewa ki taimakeni anty madina karki rabu dani ba ni da kowa sai ke a kasar nan, na yi alkawari xan fada miki komai.”
Madina ta ji sanyi a ranta sai ta juyo, ta daga kaltum tsaye ta karkade mata yashinda yayi mata bududu a jiki. Ta dawo da ita inuwa ta xauna yayin da itama ta samu waje ta xauna. Madina ta san har ga Allah tana kaunar kaltum a ranta tamkar jinin jikinta, tana tausayin rayuwarta dan haka ta kudiri niyyar taimaka mata ba xata iya rabuwa da ita ba. Ta yi furucin rabuwa da ita dan ta tsorota ta, tana tsananin son ta ji tarihin rayuwar kaltum da asalinta da abubuwan da suke faruwa da ita suke damunta. Tana so taji ta ina kaltum ta samo kyakkyawar halittar ta wacce kyawunta ya xama abun kwatantawa da sha’awa, sannan a ina ta samo sunanda take kira idan ta firgita wato, mambela! A ina kaltum ta samo ilimin addini dana xamani haka! Don ta iya larabci tamkar jakar makka. Haka ta iya turanci tamkar karamar jakar London, shin ‘yar gidan masu hali ce ko ‘yar gidan yak u bay ice! Tana da iyaye ko kuwa marainiya ce! Meye ya raba tad a kasarsu ta taho sudan! Shin ita kuwa a matsayinta na yarinya karama meye damuwartada hart a yadda xa ta yi hijira dan ta samu salama! Anya goggo fatu kuwa kakarta c eta jinni, amma take axabtar da ita hart a iya tafiyar tat a bar ta bata damu ba duk da yadda aka san soyayya da shakuwar dake tsakaninta da kakarta!
Amsoshin tambayoyinta suna nan tafe a bakin kaltum, kamar yadda ta ji kaltum ta soma bata labarinta kamar haka, wanda ke kunshe da duk amsoshin tambayarta kakaf.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.