Complete Hausa Novels

Adon Dawa Complete Hausa Novel

Reading file: Adon_Dawa_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 4 of 10

BABI NA BIYAR.
Kaltum ta tsaya tunanin ta inda xata soma labarinta, domin du duniya bata taba ba kowa labarin rayuwarta ba.
Madina ta katseta t ace, “ina sauraron ki fada min meye damuwarki!”

LABARIN KALTUM
Ta ce “suna na kaltume, sunan mahaifina saleh mahaifiyata kuma safiya sunanta ana kiranta da sofi.
Mahaifiyata ‘yar asalin wani gari ce da ake kira da IBONKOMO a cikin kasar Cameroon, mahaifina kuwa dan asalin xangon daura ne. mahaifiyata ta tashi a marainiya ba uwa ba uba sai ita sai kanwarta daya mai suna joda iyayensu suka mutu suka barsu, kawunsu yayan mahaifiyarsu mai suna jalo shi ya rike su har suka girma a bisa amana, ya aurar das u ga wanda suke so ba tare da takura ba.
Mahaifina shima maraya ne tun bayan da aka yaye shi mahaifiyar sat a rasu ta bar shi a hannun matar babansa ita GOGGO FATTU.
Goggo fatu c eta rike baba na tun yana da shekara biyu har rana irin ta yau ko tsinke ta ajiye baya tsallakawa saboda tsananin biyayya da tsoronta da yake. Daman ita bata taba haihuwa ba a duniya, mahaifina shi kadai ne aka Haifa a gidan su don haka bas hi da abokin shawara sai goggo fattu ko mahaifinsa bai isa ba.
Hakika tarihi ya nuna mahaifina ya sha wahala, axaba da makircin goggo fattu tun yana yaro har yau bai huta ba. Mahaifina ma kenan bai isa ba balle matarsa balle kuma ni ‘yarsa karan kada miya don haka kacokan dinmu sai abinda t ace xamu yi, sai yadda tayi da mu.
Madina ta gyara xama ta dubi kaltum t ace “na ji asalinki. Amma ta yaya saleh da sofi suka hadu ita da take Cameroon shi yana xangon daura!”
Kaltum tayi murmushi t ace “mahaifina ne ya je garinsu sofi yawon fatauci, tun yana yaro yake bin mahaifinsa suke xuwa tare har yake xuwa shi kadai daya gane hanya, suna shiga da kayanmu na nan gida Nigeria can su sayar sannan su kawo na can su shigo das hi ta a haka suka hadu. Aure kamar xai yiwu kamar ba xai yi wu ba, Allah Yasa ya yiyu aka yin ammadukka bangarorin biyu ba’a son ransu ba a bangarensa da bangarenta.
A bangaren su sofi suna ganin hatsari ne su dauki ‘yarsu su bawa bako wanda ba’a san asalinsa ba, haka suma danginsa suke ganin duk ‘yan matan das u ke xangon dauura ya rasa wacce xai aura sai ya fita wata kasar sannan xai yi aure. Karfin addu’arsu su masoyan da tsananin rabon haihuwa daya rantse sai aka yarda aka daura auren. Amma fad a farko dangin sofi basu yarda ya taho da ita ba sai dai ya kama haya a can ya ajiye ta, yana xuwa yana dawowa said a ta shekara sannan suka yaba da hankalinsa na ladabi, amana da rikon gaskiya. sannan aka sami wadanda suka san asalinsa ‘yan xangon daura amma maxauna garin su sofi sun yi gidaje, sun yi aure, sun hayayyafa sannan aka bari ya taho da ita. ‘yan uwanta suka rako ta har xangon daura suka ga mahallinta da ‘yan uwansa sannan suka tafi suka bar ta a lokacin tana dauke da karamin cikina.”
Madina ta nisa t ace “to naji yadda iyayenki suka hadu har suka yi aure. Da babanki ki ka yi kama ko da mamarki!”
Tambayar madina ta bawa kaltum dariya, sai ta kyalkyale da dariya sannan t ace, “da mama na nayi kama sak babu inda na baro ta, idan kika ganta kika ganni idan baki lura ba sai ki kira tad a sunana ko ki kirani da sunanta saboda bat a da kiba kma ba tsufa ba. Kamar yadda na fada miki fulanin Cameroon ne danginta kyawawa ne masu tsananin farar fata sai ka dauka larabawa ne, gashinsu har baya. Banyi kama da mahaifi nab a kwata kwata saboda shi baki ne, amman kanne na biyu sun yi kama das hi sak”
Madina tayi murmushi t ace “yaya xaman sofi ya kasance a xangon daura!”
Kaltum tayi murmushi t ace “gidan kasa da katangar xana gadon mahaifi na ke nan anan aka kai sofi, tana xaune a daki daya, goggo fattu a daki daya don a shekarar da aka yi auren baba na mahaifinsa ya rasu. Don haka goggo fattu ta sami filin casa sofi da saleh, sai yadda take so xa’a yi, sai abinda t ace xa suyi. Babu wahalar da sofi bata sha ba, ga cikin fari a wajen yarinya ‘yar shekara goma sha hudu, har ciki ya tsufa kuma ta hana a kai ta garinsu ta haihu. Da watan haihuwarta ya kama kawu jalo ya aiko da matarsa Asta da ‘yarsa Ladi su xo su dauko safi ta haihu a gida amma goggo fattu tayi musu dadin baki luf luf wai sofi ‘yar t ace tamkar wacce ta Haifa a cikinta don haka su bar ta a wajenta xata kula da ita sosai. A haka suka hakura suka tafi suka bar ta suna ta yabon kirkin goggo fattu, ita kuwa sofi tsoro ya hana ta fada musu gaskiya.
A cikin dare nakuda ta tashi sofi daga barci sai ita sai saleh, tashin farko daman dakin goggo fattu saleh ya nufa da gudu ya buga mata kofa ya sanar mata cewar sofi tana nakuda. Ta xage shi tsaf wai bashi da kunya meye abin gigicewa har ya fada da bakinsa matarsa tana nakuda. Ya sunkuyar da kai kasa yana bata hakuri, ta umurce shi day a fice daga gidan kada ya dawo sai gobe da safe.
Yana fita ta rufe kofar gidan sannan ta leka dakin sofi ta isketa a tsugunne ita kadai tana murkususu, tana ganin goggo fattu sai ta fashe da kuka ta hau kiran sunanta, amma goggo fattu ta tabe baki t ace “ki bar kiran sunana ma don ba xan shigo inyi ta fama da ke har gari yaw aye ba, haihuwar da bata da tabbas xata fito ko ba xata fito yanxu ba.”
Ta juya ta koma dakin ta tayi kwanciyar tat a bar ta a wannan halin. Allah cikin ikon Sa ta haihu ita kadai, jaririya ta fito fuk akan tabarma gtana tsala kuka haka mabiya ma ta fito . sofi ta rasa yadda xata yi da ni sai ta sami leda ta kwashe mabiyar da jaririyar ta rufe a leda fuskata ce kadai a bud eta dora ni akan gado ta xauna a gefena tana ta kuka har gari yaw aye tangarai sannan goggo fattu ta shigo dakin ta iske halin da muke ciki. Jaririya a kunshe a leda ga cibiya nan ba’a yanke ba a jikin mahaifar sai jini jage jage. Duk idanuwana, hanci na da kunnuwana duk busashshen jini ne.
Ta dau dogon salati ta dinga dimawa sofi duka a baya tana kiranta munafuka so take ta ja mata xagi a gari a c eta kasheta ta kasha jaririyar. Wai me yasa da haihuwa ta xo bata kwalla mata kira ba ko ta xo ta kira tad a kanta ba, xata xo ta kunshe ‘ya a leda ba’a yanke mahaifa ba alhali mahaifa shanye jini take.
Tayi tax age xagenta tana borin kunya sannan ta yanke cibiya, tayi ma ‘yar wanka ta gyara mai jegon sannan ta bude gida mahaifina ya shigo ya iskemu tsaf.
Haka danginsu su kayi tayi mata sannu da kokari yadda ta karbi haihuwar sofi tamkar ‘yar cikinta don sun iske mai jego sumul da jaririyarta kalau.
Bayan an yi suna aka saka min Ummu Kaltum sunana da goggo fattu ta xabar musu kenan wai sunan mahaifiyarta ne, basu isa su saka sunan mahaifansu bad a suka rasu tuntini. Sai dangin sofi suka xo suka dage xasu tafi da ita da kyar goggo fattu ta bari suka tafi da ita, mahaifina ya fi son haka daman. Bata dawo ba said a nayi wata uku nayi kwari sannan muka dawo xangon daura tun daga lokacin na fara shiga halin da nake har yanxu yak e bibiyata a rayuwata.”

Tab ashe haka wasu suke da busashshen imani!!!
Allah Ka sanya mu pi karpin xukatan mu, sannan Ka dada kare mu daga sharrin miyagu.
Se a saurara nan gaba domin jin yadda ta kasance.

Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 7
.
.
“kamar yaya halinda kike ciki har yanxu yake bibiyarki!”madina ta tambaya cikin rudani kaltum ta xubo da hawayenn daya cika mata ido tace “goggo fattu ta hana mahaifina ya dauke ni balle yayi min wasa ko ya rungume ni mu shaku. Ko kallona yayi sai ta dauki dogon salati kai kace mutum ya kashe. Ta ce wannan ai rashin kunya ne don haka kwata kwata baya kusanta ta. Haka mahaifiyata bayan nono da xata bani babu sauran soyayyar uwa da ‘yarta, idan kuwa ta cika daukana da tattalina sai xagi da Allah wadai take yi mata kala kala. Komai aka yi da ni, sai goggo fattu tace rashin kunya ne.
Wata rana har kuka goggo fattu ta ke saka musu, ta ce dan bata da haihuwa,a haka iyayena suka kyaleni, sai yanda goggo fattu ta yi da ni.kar ki dauka kulawar take bani, sai ta ajiye ni a dakinta in ta kuka, sai taga dama sannan tace sofi ta dauke nita bani nono. Har aka yaye ni na bar dakin mahaifana xuwa dakin goggo fattu, ba komai kuma take min ba sai duka da rankwashi musamman idan nayi fitsarin kwance, aka ce komai sanyin asuba xata kore ni waje tsirara bayan ta xane ni.
A lokacin karayar arxikii ta far wa baba na bashi da cin yau bare na gobe sai ya nemi shawara xai sayar da kiwonsa da mahaifinsa ya bar masa gado, akuyoyi da yawa da gonaki xai yi jari, sai ta ki amincewa t ace bakin ciki yake yi don ta xuba nata kiwon a cikin nasa shine yake so ya tona mata asiri a garin ace daman duk tulin akuyoyin nan ba nata ba ne don tayi karya t ace duk nata ne. muka dade cikin rashi da fatara da yunwa har Allah Yasa kawu Isiya kanin mahaifin babana ne yayi masa hanya ya samu aikin gadi a kano,ya tafi kano amma ya bar iyalansa a xangon daura.”
Madina ta gyara xama ta gyada kai ta ce “lallai yanxu xa’a fara labari. Daga nan yaya aka yi? ”
Kaltun ta girgixa kai ta ci gaba da Magana cikin marainiya murya ta ce “duk karshen wata yake xuwa ya kawo mana kudi albashinsa don mu ci abinci amma yana tafiya xata juya akalar kudin tayi sha’anin gabanta dasu .kuli –kuli guda uku shine bincin mu na rana, tuwon dawa da miyar kuka lami ko wace babu shine abincin dare, dumamensa sine abincinmu na safe.Duk muka rame muka lalace ita kuwa har tsire da kaxa take ci acikin shinkafa muna kallonta.
Da mahaifina yaga alamar mun rame sai ya dinga tambayar mahaifiyata ko lafiya muke rame wa?
Ta boye masa don itama irin halinta kenan ba xa ta yi Magana ba ko abu xai kashe ta, sai a makwabta aka fada masa duk abunda yake faruwa damu. Ya samu goggo fattu yace yana so ya tafi kano da sofi itama ta samu aikin wanke-wanke da shara duk wata xasu dinga hado mata albashinsu duka suna kawo mana ni da ita. Tuni ta amince sofi tabi mijinta suka tafi kano suka barni cikin wahala Kaman ta kashe ni tsunma ma ya fi ni nauyi, ga ciwuka kala-kala kullum.
Mahaifina bai fasa xuwa ba, duk wata xai shiga mota ya xo xango daura ya kawo kudin albashinsa fiye da rabi. Ina ganinsa sai in hau murna ina kiran “ga baba, ga baba.” Amma sai ya ture ni gefe in fadi kasa, ya dauke kansa baya kallon in da nake saboda kada goggo fattu t ace yayi rashen kunya.
Ina shekara uku yunwa da ciwon kyanda suka sa ni a gaba na rame sai kashi da fata, ido yayi min xuru –xuru kamar mai ciwon kanjamau sai ka kirga kashushuwan dake kirjina. Sai in suma sau biyar a rana wanar ba xan rayu ba sai ta ji tsoro kar in mutu a hannunta don haka sai ta nemi kawu isiya ya kawo mu har gidan da mahaifina yake gadi, suka ci sa’a kuwa a boy’s kuarter gidan suke xaune da mahaifiyata.
Ta hau fada hard a kumfar baki tana cewa sun gudo kano sun xo sun kwanta sun bar ta da wahala tana fama da ‘yarsu ko barchi bata yi, don haka ga ‘yar sunan su rike kayansu. Ta jankwabar dani da kayana ta juya ta tafiyarta, suna binta suna rokonta ta xo ta huta ta ci abinci, tace ba xata dawo ba dole ta tilastawa kawu isiya dole ya taso suka hau mota suka koma xangon daura.”

Madina ta girgixa kai t ace “daman haka halin goggo fattu yake! Ni fa na yi mamakin ace kaka ce take tsangwamar jikarta haka yadda naga tana kyararki a mota.”
Kaltum ta surnano da hawaye ta cika mata ido ta ci gaba da cewa “mai gidan da muke gidansa sunanasa Alh Adnan Mahbub, shi da matarsa Salaha sai ‘dan su daya Mashkur. Mashkur sa’ana ne shima a lokacin shekarunsa uku kamar yadda shekaruna uku cur a duniya. Alh Adnan yana da arxiki mai yawa duk da matashi ne a lokacin, aurensa ne na fari kuma haihuwarsa c eta fari bai wuce shekaru talatin ba aduniya, matarsa kuwa baxata wuce shekaru ashirin da uku ba don da haka kusan sun girmi iyayena ma. Suna xaune a kataferen gidan, kerarre mai girman gaske yayin da mu kuma muke xaune a boys quarters in gidan.
Alh Adanan na ganin halinda nake ciki na rashin lafiya sai ya ji hankalinsa ya tashi ya umurci direban saya dauke mu ya kai mu asibiti ni da mahaifana. Ya ce ayi duk abinda ya kamata ayi xai biya ko nawa ne. asibitin nasarawa aka kai ni a lokacin shine asibitin da yake tashe sai dan wane da wane. Likita na ganin yanayin jikina sai ya bamu gado muka kwanta aka dinga kara min ruwa da allurai. Allah cikin ikon Sa kafin sati guda na murmure, shi yasa aka ce kowace cuta da maganinta. Na samu sauki har na fara tashi xaune ina surutu kuma komai aka bani ina ci. Kusan kullum Alh Adnan da matarsa salaha suna xuwa su gaishe ni a asibitin bayan kayan dadi na marmari da abinci iri-iri da suke yini suna aiko direba yana kawo mana asibiti.”
Madina tace “gaskiya wadannan iyayen gidan naku suna da kiriki.”
Kaltum tayi murmushi tace “suna da matukar kirki shi da matarsa dukka. Bayan an sallamo mu mun dawo gida sai muka ci gaba da rayuwarmu a gidan, ina matukar jin dadin gidan saboda na samu walwala ba’a dukana, babu yunwa, ba babu hantara.
Makaranta mai tsadar gaske aka sani.
Madina tace “Allah kenan, haka yake ikonSa.”
Kaltum tayi murmushi tace “na tsinci kaina mai farin ciki matuka sai dai matsala daya data addabe ni itace bana samun kulawar iyayena. Ba kulawar rashin wanka da wanki ba ne, kuma ba matsalar abinci ba ne, basa hira da ni, haka basa saurarona, ko na matso kusa dasu saisu matsa saboda wancen ra’ayin da goggo fattu ta cusa musu.”
Madina tace “ban fahimci basa sauraronki ba, kamar yaya? ”
Kaltum t ace “kunyata su ke ji saboda ni ‘yar farice don haka na xama tamkar mujiya a tsakiyarsu sai kallo da ido. Ina matsowa kusa dasu saisu ture ni ko su tashi daga wajen, idan na taho musu da hira saisu gwale ni ba xasu saurareni ba. Idan xan yini ina kuka babu wanda xai lallashe ni a cikin su. Har ‘yan gidan suka fara fuskantar hakan, Alh Adnan ya dinga yiwa mahaifana nasiha yana nuna masa wannan kunyar da yake yiwa ‘yar fari ba’abun burgewa ba ne illa jahilci da cutar kai.
Akwai wata ranar asabar ba xan taba mantawa ba da sassafe misalin karfe takwas, a lokacin ana tsananin sanyi. Ni da mushkur muka fito bakin get wajen da babana yake xaune yana jin dumi da itace, yayin daya rufa da burgujejen bargo. Yana ganinmu ya tabbatar sulalowa mukayi muka fito ba tare da sanin iyayenmu mata ba, saboda ko rigar sanyi babu a jikinmu, ba hula, ba takalmi daga ni sai yar yaloluwar singileti da pant, haka mushkur daga shi sai karamar jallabiya ba dogon wando. Ana tsananin hunturu, mai tafe da haxo, da iska mai kura don haka hanci da ido sai xuba suke yi, yayin da duk ilahirin tsikar jikinmu ta tattashi.
Babana na ganinmu sai ya kira mushkur ya dauke shi akan cinyar sa ya rungume, ya lullube shi da bargo, yayin daya juyar dashi saitin garwashi suka yi ta jin dumi, suka juya min baya. Ina xaune akan benci a bayansu ina ta makerketa ban isa in kutsa cikin bargon ba saboda nasan hantara ta xai yi ya kore ni.
A cikin wannan hali Alh Adanan ya fito ya iske mu, sai ya ji ransa ya baci yayi ta yiwa mahaifina fada yana cewa shi fa ba burge shi yake yi ba in har xai bar ‘yar sa ta cikin sa a wulakance ya tallafi dan wani. In har iyayena basu shaku da ni ba to ina xansa raina, ya kwatanta wannan abunda suke yi da suna ADON DAWA wato gida bai wadata ba an wadata waje ma’ana ya wulakanta ‘yarsa ya tallafi bare.
Alh Adnan ya dauke ni ya rungume ni ya shiga da ni cikin falonsa ya dauki bargonsa ya lullube ni yayin daya kunna min room heater jin dumi ta lantarki. Yana lallashi na, ya bani biskit da alewa, har said a ya tabbatar hantsi yayi, sanyin safiya ya lafa sannan y ace in je gida ayi min wanka a saka min kayan sanyi. Haka shima mushkur yake samun wannan gata daga wajen mahaifana har goyon sa mama na keyi amma ni ban isa matsowa kusa da ita ba.
Dan haka na kasance ako da yaushe ina hanyar bangaren daddyn mushkur. Ina tashi daga barci wani lokacin ko karyawa bana yi sai in yi wuf nagudu wajensa, sai dai idan ban ci sa’a ba nayi karo da maman mushkur sai ta kora ni gida, idan kuwa tana kicin ko ban daki tuni na isa gare shi a falonsa ko akan gadonsa, yana gani na sai ya rungume ni ko daga ni sama cimak, ya wujijjiga ni in yi ta dariya.
Musamman saboda ni yake ajiye katan katan din alewa da biskit da kananan kwalayen lemuna. Ko da yaushe ka ganni ina ciye ciye, baya ga karatun boko dana arabiya da yake koya min. ya na sona saboda ina son karatu, kuma ina son in koya.
Ko da yaushe ina tambayarsa abun da ban gane ba haka duk abun daya koya min duk daren dadewa ya tambaye ni sai na fada masa bana mantawa, in da ya kara sona kenan.
Sabanin dansa wanda ya tsani karatu don haka ma basa shiri da uban. Gashi ina da tsananin wayo kamar ba ‘yar fari ba, ga ladabi da biyayya, na iya hira tatsuniya kala-kala da labarum nake bashi yayi ta dariya ya na tuntsurewa da dariya tamkar yana hira a cikin abokansa.
Amma fa bana labarin da kowa saishi kadai, idan baya nan sai ka rantse ni doluwa ce don bana Magana, sai kallo da ido a gidanmu saboda bana hira da iyayena. Don haka duk sanda daddy yayi tafiya kwana biyu sai kowa ya gane bana jin dadin rayuwata. Jikina sai yayi sanyi, in kaura bakin get ina duban hanya musamman idan na ji karar mota sai in xankada da gudu in leka, idan naga bashi ba ne sai raina ya baci ko kuma in fashe da kuka. Idan kuwa na ci sa’a shi din ne sai in yi ta tsalle da ihu don murna yayin da nake fara xaxxago masa labaru iri-iri dana tattara ina jira ya xo in fada masa.”
Kaltum tayi shiru tana matse hawaye, yayin da madina ta tsura mata ido tana yi mata kallon tausayi.
Madina ta nisa tace “ikon Allah idan da ranka babu abunda baxa ka jiba. yaya kuka kasance? ”
Kaltum ta gigixa kai tayi dan murmushi ta ci gaba da cewa “daddy shine tamkar uwata, ubana, kuma abokina. Shi kadai yake goge min hawaye a idona saboda a kasance koda yaushe ina cikin kuka a sanadiyar kyarar da mahaifana da kuma mamar mushkur ke yi min, tatsane ni saboda taga mijinta yana tarairayarta fiye da dansu na cikinsu.”
Madina ta girgixa kanta t ace “Allah sarki duniya, abun al’ajabi baya karewa ban tabajin irin wannan kauyenci ba. Daga kanki ba’a kara haihuwa ba a gidan ku? Mushkur ma ba’a hqifa masa kanne ba? ”
Kaltum tace “an haifawa mushkur kanne biyu amma dukkansu ba’a haifesu da rai ba, saura kiris mamarsa ta rasa ranta a garin haihuwarsu. Saboda duk a juye ake fitar mata dasu ta hanyar tiyata ma’ana kan jaririn ne suke komawa kirjinta, kafafuwan a kasa sai anyi tiyata ake fitar mata kuma a mace don haka nema aka juyar da mahaifarta baxata sake haihuwa ba. Ni kuwa mahaifiyata ta haifi namiji mai bina ya rasu bayan an yi suna, sai ta dade bata haihu ba sai daga baya ne haihuwar ta bude, kusan duk shekara sai ta haihu, a yanxu haka kannena bakwai na baro mata da maxa.”
Madina t ace “suma kannen naki suna jin kunyarsu basa kula su kamar yadda suke yi miki!” kaltum ta girgixa kai tace “iyayena suna son su, suna wasa dasu, suna hira dasu ba kamar yadda suke yi min ba har tsayawa nake ina kallonsu ina mamakin ashe mama da baba sun iya yiwa da wasa da lallashi.

Duk wani abu da ake bukata na makaranta sai na jira daddy ya xo sannan in fada masa, ya bani in kai makaranta idan kuwa baya gari ko baya kasar sai dai idan kashe ni xa’a yi a makaranta don duka amma babu wanda nake iya tara in fadawa sai daddy.
Ina shekara takwas nagama nursery har na shiga primary, ina primary 3 a lokacin ne karshen karatuna ya xo.”
“kamar yaya karshen karatunki ya xo? ”
madina ta tambaya cike da damuwa.
Kaltum t ace “eh, a lokacin ne goggo fattu ta aiko tana son ganin mahaifina, yana rawar jiki ya tafi kiranta a can garin mu xangon daura. Ta sanar masa abun da take bukata daga gare shi, gashi baya iya yi mata musu. Nan danan ya amsa mata ba tare da yayi kokonto ba saboda tsoro.”
Madina ta gyara xama t ace “me take bukata a gare shi!”
Kaltum ta cije baki tayi murmushin karfin hali t ace “ce masa tayi ya amince ta sayar da gadonsa da mahaifinsa ya bar masa sannan da tabkekiyar gonarsa dake garin sandamu, wacce mahaifiyarsa ta mutu ta bar masa, sannan da dinbin awakinsa xata biya kudin jirgi ni da ita mu tafi makka neman kudi. Idan muka je xa mu samo dukiya mai yawa , sai ta biya shi linkin ba linkin in kudin gonarsa.”
Madina tace “ya yarda a cire ki daga makaranta ku tafi maka? ”
kaltum t ace “a take ya yarda, haka mahaifiyata ma bata hana ba a sanda ya sanar mata. Ko da wasa babu wanda ya fada min shirye-shiryensu, ni dai nasan ankai ni gidan daukar hoto an yi min kananan hotuna, goggo fattu ta xo ta kwana biyu a gidan mu, sai kuma ranar da naga mahaifiyata ta xuba min kayana a dan buhu, goggo fattu tace in taho mu tafi.”
Madina tace “daddy ya sani bai hana a tafi da ke ba? ”
Kaltum ta girgixa kai tace ‘sai da suka ga daddy baya na sannan suka tarki tafiyar, koda wasu basu shawarce shi ba, matarsa ma bata sani ba.
Na tsinci kai na a cikin jirgi, sannan na tsinci kai na a cikin birnin makka.
Madina t ace ‘ki ce kin taba xuwa makka ba wannan ne xuwanki na farko ba? ”
Kaltum t ace”na dade a makka a can na koyi larabci, yanxu haka lungu-lungu da sako-sako na sani a cikin garin makka, haka da ace na samu xuwa xaki yi mamakin irin mutanen da xa ki ga sun sanni duk da na girma nasan xasu shaida ni saboda kammanina basu canxa ba.”

Madina tace”yaya xamanku da goggo fattu ya kasance a maka?
Amma dai bata wahalar dake ba tunda kin girma ba kamar sanda ta yeye ki ba, ga ku kuma a kasa mai tsarki, gashi komai a wadace ba’a wahalar abinci”
Kaltum tayi jugum can ta nisa t ace “uhum wahala ma daya kenan, ai ba xai yiwu in iya xayyana ta gaba daya ba saboda axabar tayi yawa.
Wahalar da na saha ina ‘yar jaririya ai karama ce saboda tsana bansan komai ba, a wannan lokacin kuwa nasan “eh” nasan a’a, na san ace in yi abu in yi, ace in bari in bari.
Da farko dai mun ci sa’a mun sami gidan haya a unguwar ‘yan kasa wato a unguwar masfala, a gidan wata balarabiya mai suna hajiya isra, hajja isra ruwa biyu ce mahaifiyarta baka, mahaifinta balaraben makka ne dan haka gadimiya ce. Hajja isra tana da ‘ya daya mai suna ahlan. Ahlan sa’ata ce, mahaifin ahlan ya rasu ya bar musu gida sama da kasa. Suna xaune a sama, mu kuma muna haya a kasa mu kadai ne.
Hajja isra tana da kirki matuka,tana sona sosai musamman yadda taga mun shaku da ‘yarta Ahlan, har ana cewa muna kama kasancewar Ahlan tayi kama da mahaifiyarta ba suyi kama da larabawa ba sak nima kuma gani fara sol mai gashi sai nake kama dasu. Ta kan yiwa goggo fattu wasa t ace “yadda fuskar nan taki take baka kirin idan askarawa (yan sanda) suka ganki da kaltum ki ka ce jikarki ce sai sun kama ki, suce karya ki ke ‘yar larabawa kika sato. Saboda baku yi kama ba kwata-kwata, gara ki dinga saka nikaf da safar hannu da ta kafa idan xaku fita tare.
In da xaki tabbatar hajja isra na sona sai ta siyawa ‘yarta ruguna ko sarka da ‘yankunne na gwal, biyu take saya iri daya ni da Ahlan musamman a lokacin sallah. Haka abinci, komai ta dafa sai ta aiko min sai dai kash aiken baya xuwa gare ni saboda goggo fattu karbewa take yi bata bani. Da takardar Ahlan ta ‘yan kasa hajja isra ta saka ni a makarantarsu Ahlan, muke xuwa tare duk da ba’a koyar da boko larabci xalla ake yi sai karatun qur’ani ta tahfix ce. Na koyi larabci, na koyi karatun qur’ani sosai, nasan baki, hadisai da daman na haddace su kuma xan iya fassarawa, haka fikihu, tafsir, sira da sauransu. Muna xuwa makaranta da sassafe misalign karfe takwas xuwa karfe goma sha daya muke tasowa. Muna tashi daga makaranta idan na shiga gida na ajiye jakar makaranta sai in karbi kudi a wajen goggo fattu in tafi sarar kaya sannan in je in sayar.”
Madina tace “ban fahimce ki ba. Ke kadai din ne xaki iya xuwa ki sari kaya da kanki? ”
Kaltum tace “ni nake xuwa in saro kaya, kar k ice tafiyar ba nisa, ko a mota tafiya ce mai nisa daga masfala xuwa shara Mansur masallacin mai cixo. Sai na niki tafiya kamar raina xai fita in saro kaya masu yawa sannan in doro kayan a kaina in nufi harami in da xan baxa a bakin hanya ina sayarwa. Idan na sayar sai in koma shara Mansur masallacin mai cixo in sake saro kaya in koma harami in sayar, har sai dare yayi bayan sallar isha’I sannan nake komawa gida sai na tabbatar kudin ya lunku sau biyu. Ma’ana idan riyad dari biyar ta bani sai ya xama riyad dubu biyu, ranar da ban yi ciniki ba ne xan kai mata ruyad dubu daya da ‘yan kai.”....
.
Gida fa ya fara shiru, mai yasa aka rage comments?
Ko littafin ya fara isan mutane ne?

Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 8
.
Madina tace “amma tana farin ciki da cinikin da kika yi mata bata kyarar ki ko? ”
Kaltum ta tabe baki ta ce “ko a lokacin xahma ma’ana lokacin da baki suke nan an fi yin ciniki wato lokacin Umara da Hajji idan ta bani riyad dubu daya in yi sari, daga safe xuwa dare sai nayi mata riyad dubu biyar xuwa dubu shida amma bata godewa kuma se ta dake ni kullum.”
Madina tace “to cnikin nawa take so kiyi mata? ”
Kaltum t ace “duka na take yi kullum ba sai nayi laifi ba, ba kuma dan ban yi ciniki ba. Yadda na lura doka ce wacce ta wajaba a kaina kullum sai ta xane ni ko da laifi ko ba laifi. Daman ina dawowa take ce min in cire kayana a bakin kofar shigowa daga ni sai dan wando, sannan in karaso gaban ta in durkusa, in mika mata cinikin dana yi. Sai ta kirga ta soka a aljihunta sannan ta xaro wayar rediyo ta fara sharara min a duk ilahirin jikina, laifin da take cewa nayi shine ban dawo da wuri ba ko kuma sharar da nayi da wanke-wanken da nayi da asuba kafin in tafi makaranta bai fita ba. In yi ta kuka da ihu ina mata magiya tayi hakuri ba xan sake ba. Har sai hajja isra ta jiyo ta xo ta kwace ni sannan take kyaleni, amma tun sanda ta yiwa hajja isra targade a yatsa garin kwata ta hajja isra ta daina saukowa ta kwace ni ki san larabawa da tsoro. Sai dai ki ji tana cewa “fattu kiji tsoron Allah, ki kiyaye ranar da hakkin yarinyar nan xai tabaye ki.” Amma goggo fattu bata ji, gobe ma xatayi min wanda yafi na yau.”
Kaltum ta fashe da kuka, yayin da madina ma taji hawaye ba kakkautawa yana xubo mata suka dauki lokaci mai tsawo babu wanda yake Magana don takaici. Can kaltum ta ci gaba da Magana cikin kuka take cewa “bulalar roba irin ta jona rediyo nan sai ta farfashe a bayana, yayin da karfen cikin wayar ke shiga cikin naman jikina ya nutse, jinni yayi ta fita. Idan wayar ta fatattake ta kare sai ta bani kudi in je in siyo wata a kanti da kaina, in kawo mata. Idan itama ta kare sai ta sake aikena in siyo wata.”
Kaltum ta juyowa da madina bayanta, yayin data daga rigarta sai ga shatin bulala xabga-xabga reras a jere a bayanta da wuyanta.
Madina ta shashshafa bayan yayin data gyada kai tace “kwarai kuwa wannan tabon duka ne. Allah sai Ya kama matar nan da hakkin yarinyar karama wacce bata jiba bata gani ba. Ta rabo ki da iyayenki ta xo ta axabtar da ke.”
Kaltum t ace “idan bayana ya farfashe yana jinni sai ta kaini bandaki ta daure hannuna da wuyana da kafata a jikin famfo kamar yadda na gaya miki sani take in cire kayana daga ni sai dan wando, sai ta dauko farin omo ta gurxa min a baya na a wajen ciwon sai kaji ya dau xugi yana tafasa, yana kumfa sai ciwo ya kakkame, sai jinin ya tsaya.”
Madina tace “ta daure ki a bandaki fa kika ce, kamar wata dabba?
Ko dabbace xatayi mata haka? ”
Kaltum t ace “na sha kwana a bandaki ina rawar sanyi har gari ya waye sannan ta jibgo min abinci t ace sai na cinye. Shinkafa himilin guda da kaxa dankwaleliya tace sai na cinye tas, inyi ta turawa badon ina jin dadin abincin ba saboda bana cin abinci sosai na saba in yini ina talla baci basha don haka nama daina son cin abincin kwata kwata.
Idan nace mata ya isheni sai ta kwada min mari tace sai na cinye duka, in yi ta ci har wani lokacin in amayar da duk abunda na ci, sai ta sani in kwashe aman in gauraya da abincin tace in cinye abincin da aman dole nake cakudawa in ci gaba da ci.”
Madina ta tsartar da yawu gefe,

(NI KUMA DAN ANTY, HAR SE DA NA KOMA YIN AMAI , YANXU MA AKAN AMAN NAKE OOOOOOOOO…….)

Ta dau dogon salati. Ta ce “kaltum kin sha wuya, kai wannan abu da me yayi kama?
Ke kuwa me kika yiwa wannan tsohuwar take wahalar da ke haka da alama don bata taba haihuwa bane take miki haka, da ta san xafin haihuwa da ta rage wani abu duk muguntarta.”

(NI KUMA NA CE, “BA WANI DAMAN MUGUNTAR A JININTA YAKE, WASU BABU HAIHUWA KUMA SUNA DA TAUSAYAWA DAN UWA. ALLAH MA YA TSARE MU DA IRIN WANNAN RASHIN IMANI. AMEEN)

Kaltum ta matse hawayenta tace “duk unguwar sun san ina shan wahala duk da basu san wata axabar da nake sha a cikin gida ba, amma suna ganin irin wahalar da nake wajen daguwar tafiya in saro kaya sannan in je in sayar, in koma in sake sarowa duk da kafa, saboda tsabar daukar kaya a kaina sai da kaina yayi tolo gashin wajen ya kade ya gurguje saboda wahala.
Akwai wani yaro saurayi a makwabtanmu mai suna Anwar. Bakar fata ne amma haifaffan Saudi ne yana tausaya min matuka y ace duk sanda xan je sari in je in karbi kudin motar xuwa da na dawowa in daina tafiya da kafa. Haka kuwa aka yi duk sanda na fito daga gida xan je in kwankwasa kofar gidansu ya fito ya bani riyal biyu, riyal daya na xuwa daya na dawowa. Sai in je in shiga doguwar bus a kai ni har kofar kantin sari, in saro kaya himili guda in sake hawa mota in tafi harami in sayar. Abunka da yarinta idan na sayar xan sake komawa in saro wasu bana shiga mota sai in tafi a kafata tunda Anwar bai bqni wanda xan sake komawa ba tsoro kuma ya hana in dauka a kudinta, gani nake kamar xata gane.
Wata rana da axumi na fito daga gida karfe shida da rabi na safe, gari ma bai karasa wayewa ba saboda akwai baki a garin don haka ana cin xahma. Anwar ya bani kudin mota na tafi na hau doguwar mota mai beni hawa biyu, sama da kasa don haka sai na samu lungu na shige a can sama.kan ka ce kwabo barci ya dauke ni kasancewar axaune a bandaki na kwana, tsirara ga tsananin sanyi dan haka ban samu nayi barci ba har asuba sannan ta kwance ni ta turoni sari ko karyawa banyi ba, anyi mana hutu saboda axumi a lokacin.
Ina wannan barci har aka wuce dani inda xan sauka ban sani ba. Da barci yayi barci saina sulale na mike a karkashin kujera na kwanta sosai na lulluba da gyalena. Ban tashi farkawa ba said a wata mata ta tashe ni ta ce in tashi masu mota dasu kai motar wajen parkin, sun gama aikin ranar. Sannan nayi firgigit na biyo bayanta muka sakko tare da ita. Ina tafe ina laluba kudina a cikin jaka dana daure a tsantsata, hakika kudina yana nan riyad dubu daya.
Ina fitowa sai na ganni a wata unguwa da ake kira shara sittin, sai ban damu ba saboda tafiyar da xan yi xuwa sharu Mansur babu nisa sosai don haka na tabbatar barci kadan nayi don ba’a wuce dani da yawa ba. Na duba sararin samaniya hakika har yanxu rana bata futo ba yayin da na duba agogon dake daure a hannuna karfe bakwai daidai. Sai farin ciki ya kama ni tunda na san karfe shida da rabi na fito daga gida mintuna talatin kadai nayi a hanya. Na dinga tafiya ina sauri kamar xan ci daka sai dai wani abu daya daure min kai sai naga du kana rufe kantina kuma kowa na haramar tafiya masallaci ko’ina sai kiraye-kirayen sallah ake yi. Sai nake ganin jama’a da dama suna cin dabino, wasu na shan shayi a cikin kantina ko a cikin motocin su, gashi axumi ne kuma asuba ta wuce an gama sawur. Na tambayi xuciyata me yasa suke karya axumin su?
Tambayoyi kala-kala na dinga yiwa kaina har na isa kantin sari. Mutum daya na iske yana alwala a bakin kantin. Cikin harshen larabci ya amsa min y ace “ba’adis salat”ma’ana, sai an idar da sallah xasu bude kantin. Na dube shi duba na rashin fahimta n ace “ba kuyi sallar asuba da wuri ba ne? ”
ya yi dariya yace sallar magariba xa mu yi ba dai asuba ba. Ko dan bakya axumi shi yasa baki damu a sha ruwa da wuri ba ko?
Sai gabana ya yanke ya fadi, nan da nan na rikice. Na ga wata mata ta xo wucewa jikina yana karkarwa n ace mata “karfe nawa yanxu? ” ta duba agogon dake daure a hannunta t ace “karfe bakwai.” Na tambaye ta “bakwai na safe ko bakwai na dare? ” itama sai tayi dariya sannan t ace “bakwai na dare ne. ba ki ga ana shan ruwa ba? ”
Sai na sulale na tsuguna ina ta salati, ina kuka hakika yau na shiga uku ban san abunda xan je in gayawa goggo fattu ba, ga dare yayi gashi ban juya mata kudinta ba. Ta yaya xan iya mayar da riyad dubu daya ya xam riyad dubu biyar ko dubu shida, daga magaruba xuwa dayan dare? Sai da su kayi sallar isha’I aka yi asham sannan suka bude kantina nan da nan na shiga na saro safar kala kala, da doxin doxin din carbina. Na fito na shiga mota na nufi harami kuka kawai nake yi jikina yana rawa, duk Alhajin da na gani sai in bishi, bakake da farar fata hawaye na xuba ina cewa ku siya kaya na don Allah idan ban sayar ba duka na xa’ayi a gida. Da yawa saisu tausaya min su saya ko basu yi niyya ba, wasu kuma saisu bani kudi sadaka, wasu kuma su fisge rigarsu su wuce subar ni. Kan ka ce kwabo na siyar na ruga da gudu na je na kara saro waqsu, na sake dawowa harami na sayar.
Akwai wasu kawayena ‘yan indiya da muka saba dasu a wajen talla, suma dasu ka ga ina kuka sai suka tausaya min suka sarar min da kayansu dukka a yadda suka saro na dora riba na sayar. A lokacin dasha dayan dare yayi jama’a sun fara tafiya masaukinsu suna barin harami sai mu ma masu talla suka fara neman hanyar gida. Ina tafe ina kirga kudin cinikin da na yi, saura kadan ya cika riyal dubu uku, sai na dinga kuka ina addu’a yayin da hankalina ya kada yayi gida ina tunanin abunda xan tarar don cinikin yau ba yawa. A titi na tunkaro wata mota wacce ta karkato xa ta tsaya (parking) gwuiwata ce ta daki gaban mota. Kan kace kwabo kwabrina ya fahse jinni yakece, na fasa ihu na daka tsalle gefe na tsuguna.
Hankalin direban ya tashi ya fito da gudu a gigice saboda yasan hukuncin kade mutum a kasar, ko ba’a ji ciwo ba balle a ce har an ji ciwo har jinni yana xuba. Larabci yake yi min, tambaya yake yana cewa wai me yasa nake tafiya kaina a kasa, bana lura da motocin kan hanya duk da horn dinda yake yi amma ban jiba? gashi nan na ja ya buge ni xan janyo masa wahala. Sai yaga ina ta bashi hakuri burina in tafi in bar wajen ban damu da ciwon da na ji ba. ya kira ni na xo, sai ya dunkulo kudi masu yawa ya bani yace in tafi chemist in sayi magani.
Na karba kudin ina murna, na wuce ina godiya sai na hada da kudin cinikina ya xama riyad dubu biyar harda doriya. Nan fa na ji hankalina ya kwanta na tsaya a fanfo na wanke jinin sannan na shiga gida. Na isketa a kufule tana jirana da bulalarta a hannu, kallo daya tayi min na gane manufarta. Sai na fara cire abayata na xama tik daga ni sai wando. Ina karkarwa na xo na durkusa na mika mata ciniki, ta karba ta kirga. Sai ta Harare ni ta ce “ina kika je aka ganki a mota daxu da magariba bayan ni ban baki kudin mota ba? ”
Sai na ji xuciyata ta harba tabbas wani ko wata sun ganni har an fada mata. Sai na shiga dogon tunani ina neman hanyar da xan kare kaina. Ta daka min tsawa t ace “Halima kawata ta ganki kina saukowa daga mota ina ki ka je? ”
Sai wata fasaha ta fado min nace askarawa ne suka kamani, suka tafi dani da kyar suka sake ni suka sake ni. Ta fixgi kunnena ta murda da karfi t ace duk sanda na sake na bari askari ya kara kamani to Nigeria xa’a mayar dani, ina xuwa Nigeria kuma daga filin jirgi xa’a yanka ni saboda yankan kai ake yi a Nigeria. Sannan ta kunnawa risho wuta yayi ja sosai sannan t ace in dauki risho din yana ci da wuta in xo in wuce ta gabanta yayin da take shauda min bulala idan na bari risho din ya fadi ko yayi karkacewa to dukan ya xube. “sai kaltum ta fashe da kuka mai tsanani.
Madina ma kukan take, ta dafa kafadar kaltum tana lallashinta tana bata baki. Tsawon lokaci kaltum bata daina kuka ba, saida kyar ta ci gaba da Magana. Ta ci gaba da cewa “tun ina kukan idan tana dukana har na daina kuka, tun ina ihu har na daina ihu, wannan abu kuwa yana bata haushi matuka ta fi so ta dake ni in yi kuka da hawaye sannan ta ji dadi don haka take dukana kamar xata fitar min da rai ni kuwa bana iya kukan.
Da wahala ta yi wahala sai nake fita in da Askarawa suke kame don su kamani amma basa kamani, sai daga baya na gane ashe basa kama masu talla sai masu bara don haka ina ganinsu sai in wurgar da kayan tallar nayi wuf na fada cikin masu bara. Naci sa’a kuwa rannan aka kamani aka kaimu sijin wato kurkukun da ake ajiye wa'anda aka kama ma’ana wa’anda basu da takardar ixinin xama.”
Madina tace “yaya rayuwar kita kasance a sin?
Kuma yaya goggo fattu ta yi data ji an kama ki? ”

Kaltum t ace “ai babu wanda ya san an kamani sai dai idan ta ji shiru ban dawo ba ta shiga tunani, musamman idan ta ji labarin an yi kame a harami. Bata cika damuwa ba saboda tasan riga kafin da ta yi min, ta riga ta tsorata ni da xuwa Nigeria . tace idan na yarda aka kawo ni Nigeria yanka ni xa’a yi a filin girgi, ni kuwa na yarda na dauka da gaske take yankan ake yi din. Su kuma askarawa baxa su yarda su kai yaro kasarsu ba shi kadai sai an hada da iyayensa. Don haka saisu tambayemu muna da iyaye a nan Saudi ya? Sai mu ce a’a saboda idan muka ce eh, to xa’a aka mu gaba a kaimu wajen iyayen namu.
To a haka da suka gaji da tambayar iyayen mu muka ce babu suka fitar da mu suka kaimu harami, amman ranar jikina se da ya gaya min, domin irin abunda ta saba min na cin xali, shi ta min. sauran da muke siya da siyrwa da su ba’a dukansu ko basu sayar da kayan su duka ba, basa damuwa saisu mayar gida gobe su xo su sayar amma banda ni, yi nake kamar raina xe fita sai na siyar ninkin baninki du da haka kuma ban tsira ba. Kaltum ta rushe da kuka.
Madina ta girgixa kai yayin data kurawa kaltum ido tana duban ta xuciyarta cike da tausayi akan tausayin da take ke ji a da. Can kaltum ta dago da luhu luhun idanuwanta ta kalli madina idanuwansu yayi musu jajawur ta ci gaba da cewa “da wuya tayi wuya shekara ta xagayo na fara wayo ina tunanin mafita sai naga babu wata mafita wacce ta wuce in koma sijin in xauna shine kadai salamata. Saboda a sijin akwai bangaren yara xalla a inda ake bamu duk wani abun dadi da ko a gidanmu ba ma ci. Shinkafa da dakwaleliyar kaji ga taliya, macaroni, lemo iri iri, nono (laban), madara, xuma da gurasa, kankana, da sauransu.
Watarana na ji labarin ana kame a wata unguwa tuni na xubar da kayan talla na nufi wajen, na sami fili na xauna ina bara. Da nayi sa’a sai suka gano ni suka kuwa xo cafke ni suka yi, suka tafi da ni sijin. Na shafe wata biyu cif a sijin, ina walwalata tare da sauran yara har akayi karamar sallah muna can, suka bamu kayan sallah kala bibbiyu.”
Madina tace “atamfa ko leshi? ”
Kaltum ta yi dariya t ace “larabawa ai basa saka atamfa ko leshi, dogayen riguna ne da dankwalayen su sai riga da siket ko wandaduna jeans wanda xamu saka daga ciki sannan mu dora da abaya daga sama, muci, mu sha, mu yi wasa, babu duka, babu xagi, sai dai muna leka wata ‘yar huda muna ganin bangaren karuwai da aka kamo su ake duka.”
Madina t ace “kullum sai ayi ta xane su? ”
Kaltum t ace “a’a, duk sanda aka kama karuwa sai a sakata a wani daki wanda aka sakale bulala sako sako, bulalen an jona su da na’urar lantarki. Ana saka karuwa sai a fito a barta a ciki sannan a kunna na’urar, makunnar na waje. Kan ka ce kobo bulalen nan sun hau aikinsu na duka ciki da waje, duk tsallanta haka ko kwanciya tayi sai dukan ya sameta, abunka da na’ura mai kwakwalwa daga sanda bulala tamanin ta cika sai injin ya mutu da kansa ma’ana bulala tamanin hukuncin xina, ana kiran dakin XANXANA.”

(YA ALLAH KA TSARE MU DAGA AIKATA TA, DA MU DA EN UWAN MU MUSULMAI BAKI DAYA AMEEN.)

Madina ta yi tagumi t ace “ikon Allah, kaji kasar da ake shari’a ake hukunta masu xina ba kamar kasarmu ba Nigeria wanda a wani bangaren ma xina ta xama fassion. Yaya ake yi da karuwa, idan an gama dukan ta? Nasan mafi yawancin su ‘yan Nigeria ne ko? ”
Kaltum ta girgixa kai t ace “cikin ikon Allah kuwa ban taba ganin an kamo bakake ba, sai irin kananan mutanen nan wato ‘yan Asia kamar Indonesian, malesian ko indiyawa. Idan an gama dukan daya sai a fito da ita a shiga da wata kuma, suyi ta kuka suna ta ihu daga nan suma sai akwashe su kowacce a kai ta kasarta bayan an bata mata passport dinta.”
Madina t ace “to yaya aka yi dake a sijin, tun daba xaki taba yarda ki nuna gidanku ba? ”
Kaltum t ace “tsoro kala kala ya hana in nuna, na daya ina storon in kaisu wajen goggo fattu a kamo ta nasan na lahira sai ya fini jin dadi, haka ina tsoron dira a filin jirgin Nigeria t ace xa’a yanka ni don haka na ki fada ina da iyaye. Suka gaji da ajiyarmu suka kai mu bakin harami suka ajiye mu, saura yara suna ta murna sun xo gida ni ina bakin ciki an raba ni da sijin, in da ba’a dukana, ba’a daure ni, bana talla.
Hakika ta gana min axaba irir iri, bata xuba min kalanxir ta kona niba, amma ta kyarta min ashana ta daddana min hannayena da kafafuwa na bayan duka. Ta shaida min cewar ai ta ji labarin har wajen kame nake xuwa da kaina don tsan ba’a kama masu talla sai masu bara.
Haka ake tayi kullum sai wahala da axabtarwa har na cika shekara sha biyu a duniya wato shekarrunmu hudu da rabi a makka. Na gaji da duka sai na sake xuwa wajen masu kame suka kama ni karo na uku kenan. Wannan karon kuwa na hadu da wasu yara sa’annina wanda suma irin matsalata ke gare su. Muka yanke shawara mu nuna iyayenmu a kamo su akai mu kasarmu ko xamu huta da wahalar duka. Na sanar musu cewar kakata goggo fattu tace yanka mutane ake a filin jirgin Nigeria, suka ce karya ne tsorata ni kawai goggo fattu keyi. Don haka ana tambayarmu muna da iyaye mu uku muka ce “eh muna da iyaye.” Sauran da suka ce basu da iyaye aka dawo dasu bakin harami aka xube su. Mu kuwa da muka ce muna da iyaye kowacce aka hada ta da Askarawa bibbiyu da mota don ta nuna gidansu. Tiryan tiryan na kaisu gidanmu, ashe labari ya kai kunnen goggo fattu tun kafin mu karaso kofar gidan cewar an ganni da Askari. Tabbas waya aka doka mata, don haka ta shige cikin tankin ruwa anan suka xaliko ta aka kwaso mu da kayanmu kwacokam. Hajja isra da ‘yarta Ahlan na kuka muma muna kukan rabuwa dasu, aka tafi damu sijin ammam ba na da bane, wannan sijin din na masu tafiya ne don haka yara da manya a hade suke.
Tun a sijin goggo fattu ta fara dukana, xagi ba adadi ko abinci na karbo sai ta kwace tace ba xan ci ba. Kwananmu uku ban ci abincin kirki ba, lauma daya ko biyu sai ta faki idon ma’aikatan ta fusge abincin ko ta ci ko ta xubar. A rana ta hudu aka kwashe mu, aka kai mu jidda airport daga nan sai aka saka mu a jirgin da xai kawo mu Nigeria yayin da farin ciki ya lullube min xuciyata su goggo fattu kuwa suka dau kuka da kururuwa kai ka ce lahira xa’a kaisu da ransu. Bana farin ciki don xan je in ga iyayena ko kadan ban tuno su, farin cikina daya ne xanga daddy, xanga mashkur dansa abokin wasa na to daga nan sai kannena guda biyu a lokacin na baro Amani da Yasmin, saida na dawo naga mamana ta sake haihuwar ‘ya’ya biyu Mohammad da Ishak.”
Madina ta tambaya “ya kuka kasance da goggo fattu a Nigeria? ”
Kaltum ta sharce hawaye tayi murmushin karfin hali tace “goggo fattu ta shaidawa iyayena abunda na jawo mata, cewa da gangan nake xuwa wajen masu kame har suka kama ni, na nuna ta. Duk da irin himilin kudin dana nemo mata har tsawon shekara hudu da rabi amma sai ta boyeta ce bamu samo komai ba don haka kudin gonakin babana da dabbobinsa da ta siyar sun mula ba xata biya ba. Ta ce wai bana tsinana mata komai a can sai kwanciya, yara kanan suna neman kudi wadanda ma basu kai ni girma ba.
Babana yayi shiru yasan halinta amma sai ya biye mata yayi ta xagina kuma ya bata hakuri, sai dai duk wanda ya kalli jikina yasan shatin duka ne a ko ina. Wuyana, dantsen hannayena, tsintsiyar hannayena duk sun dashe, sun yi jawur saboda dauri abunka da fara don a lokacin na fi haka fari sosai.
Haka daddy yana ganina ya tambaya yace “kaltum meye ya faru da wuyanki da ma duk jikin ki?
amman wannan shacin duka ne. wa yaketa dukanki haka? ”
wannan amsa ta gagare ni, balle iyayena sai ita goggo fattu take bayani tace “ai bata jin Magana a garin tsalle tsallenta take karkarcewa.” Ai idan mafadin Magana wawa ne, majiyanta ba wawa ba ne. sai dai su kyaleta a haka amma basu yarda da bayananta ba kowa yasan shatin duka ne. duk ilahirin kayan da kika sani wadanda hajja isra take saya min da gwalagwale sarka da ‘yan kunne da xobuna du ta kwashe babu wanda ta bani. Hatta da wando (fant) idan na saka sai ta kira ni daki tasa na cire ta ce wai ba nawa ba ne nata ne. kaya kadan ta bar min ta hada da himilin dilolinta tasa a mota aka kaita xangon daura, bayan ta shafe wata guda cur a gidanmu. Banda ‘yan tsummakaron data hada iyayena da kannena wato gumama babu abunda ta basu shine tsarabar su.”
Madina t ace “amma wannan matar makira ce bata tsoron Allah. Yanxu ina xata kai hakkin dukiyar mahaifin ki data danne ta gado? Yaya rayuwarki ta kasance kuma a kano tare da iyayen ki? ”
Kaltum t ace “kamar yadda muka saba sai kunyar da iyaye na suke ji ta karu, rashin kulawar ta dadu, dakina daban na kannena daban.
Aikina kuma wanke wanke da shara da yiwa kanne na wanka, aikina yi na ke, ba se an saka niba saboda na saba da aiki har bana son xama. Mama kuma ita ke dafa abinci safe rana da dare.”
Madina t ace “ba a cikin gidan su mashkur take dafa abinci ba har kuma ku samu, ko an raba girki saboda kun yi yawa yanxu? ”
Kaltum t ace “ai a lokacin su mashkur sun tashi daga kano sun koma Abuja daddy yayi arxiki ya ninka na da, sun wuce xama a irin wannan gidan yanxu. Gidansu na Abuja tamkar aljannar duniya, ga motoci kala kala.”
Madina t ace sai suka bar muku babban gidan kuka bar boys quarters? ”

(Wash , hannuna, se na ji kawar da su karye sabida typing gaskiya na gaji, masu so ga littapi nan suma suyi.)
.
Lol... Sadin Maa ina xamu iya wannan aikin naki?
Inbanda addu'a da patan alkhairi ai babu abunda xamu iya biyan ki da shi.
Allah Ya saka miki da alkhairi Ya biya miki bukatun ki na alkhairi baki daya..
Aamiin Yaa Rabb 🙏.
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 9
.
TRUE LIFE STORY
.
Kaltum t ace “idan ta daddy ne ba damuwa xai iya barmu mu shiga mu xauna amma matarsa anty salaha bata da kirki baxa ta yarda ba. Sai wata ‘yar uwarta tsohuwa mai suna Iya Altine itace take xaune a cikin gidan, tana sharewa tana goge goge don kada a bar gidan ya lalace saboda suna dadewa basu xo hutu ba. Daddy dai yafi xuwa akai akai ba kamar mashkur da mamansa ba, sai sallah ko bikin ‘yan uwa da yake su dukkansu ‘yan kano ne. mu dai muna xaune a boys quarters sai ma rashin dadi daya karu, saboda a yanxu basa gidan bare mamana ta dafa musu abinci su ci har mu ma mu samu mu ci, mu ke cefanen mu, mu auno abinci, sannan mu dafa don haka daga masara sai gero, shinkafa jifa jifa muke iya saye. Ga uwa uba duk gonakin da ake nomawa mahaifina kakaf goggo fattu ta sayar, bama samun ko kwayar masara daya daga gona sai dai mu auna daga albashinsa, sai ‘yar kyautar da daddy yake yi masa akai akai idan yaxo. Tunda ta abunda xa’a ci ake, babu wanda yayi tunanin a saka ni a makaranta. Da kanwar mahaifiyata ta xo wato goggo joda daga garinsu Cameron sai na bi ta muka tafi can na xauna. Hakika na ji dadin xama a kasar kuma na sake, ina walwala acikin dangin mahaifiyata suna sona sosai. Duk da kauye ne, talakawa, Fulani ne amma komai ya wadata. Ga abinci iri iri, ga ruwan fanfo, ga wutar lantarki.
Duk wasu labaru da tarihin rayuwata, da ta iyaye na, da yadda suka hadu aka yi auran, da yadda xamana ya kasance a hannun goggo fattu ina yarinya duk goggo joda ta fada min, badan ita ba da ba xan san komai ba saboda da mahaifana basa hira da ni. Amma mahaifiyata tana hira da kanwarta tana fada mata komai. Naja baki na gum na rufe ban fada musu irin axabar da goggo fattu ta gana min a saudiya ba. Sai dai duk sanda na cire rigata xanyi wanka kowa ya kalli bayana sai ya tambaya ni “wannan shatin meye.” Kuma har rana irin ta yau ina kwaikwalo robar wayar da ta shige min jikin nama na.
Wata na uku cur a Cameron sai kwatsam naga babana da direban daddy a mota sun xo daukana wai daddy ne ya turo su, su xo su tafi da ni kano an samarmin makarantar sakandire, rabi boko rabi Arabic ce. Bada sona ba na baro Cameron na dawo kano don bana jin dadin gidan mu musamman dasu daddy suka kaura Abuja ga tsananin rashin abinci.
Na iske daddy a kano, ya kira ni, sannan ya kira babana, mama ta muka xauna a gabansa a kasa kan kafet.
Ya fara bayani yace “nayi matukar bakin ciki dana dawo daga tafiya aka ce an cire kaltum daga makaranta an tafi da ita saudiya neman kudi. Naji tamkar in fasa ihu saboda takaicin yadda kuka tauyewa yarinyar nan hakki, ku ka tauye mata rayuwa gashi dai yanxu ta dawo ba dammar a mayar da ita aji uku na primary saboda ta girma, in da Allah Ya rufa asiri ta shiga makaranta a can, tasan qur’ani, tasan baki xataa iya karanta larabci aduk inda ta gani haka duk abunda aka fada mata da larabci xata ji shine naga ya dace asamar mata sakandire wacce ta hada Arabic da boko sai kwakwalwarta ta tafi daidai saboda har yanxu ta iya karatu da rubutun boko don haka ta je ta gurgura ta tsinci abunda xata tsinta.”
Daga karshe ya roke su Allah da Annabi su barni inyi karatu kada su sake cire ni su ce xa’a kaini Makka ko xancen aure. Ni kuma yayi min fada da na mayar da hankali nayi karatu musamman a bangaren boko shine wanda ban iya ba sosai. Muka yi masa alkawarin xamu bi duk abunda ya fada mana.
Makarantu uku na shiga, makarantar boko da safe, ta Islamiyya da yamma sai kuma ta dare karatun hadisi ake da tauhidi. Nayi bakin jini a waje ‘yan makaranta saboda na fisu kokari, nice karama a ajin manya cikin xabga xabgan ‘yan mata, suma na fi su kokarin domin kullum ni nake karatu da larabci malami yana fassara musu. Duk in da aka bude daga cikin kowanne littafi sai kiga na iya saboda an dade da koya min a Makka. Hakan ya jawo min farin jinni a wajen malamai kacokan suna so na, wasu ma daga cikinsu so irin na soyayya suke nuna min. yayin da hakan ya jawo min tsananin bakin jinni a wajen dalibai kacokam sun tsane ni, ba ni da ta kamammiyar kawa guda daya saboda ana tsoran kada bakin jinina ya shafe su.
Kullum idan aka tashi daga makarantun nan da nake xuwa guda uku, sai dalibai sun tare ni sun ja min kunne akan kada in sake dagewa wajen yin karatu tiryen tiryen bayan su basu iya ba, malamai su dinga yi musu kallon dakikai. Wasu kuwa saisu tare ni su dake ni akan samarinsu da suke ji kishin-kishin yanxu ni suke so alhali ni ban san hawa ba ban san sauka ba. Ba na saurayi, ban taba yi ba saboda da wadannan dalilai duk sanda garin Allah yawaye sai na ji gabana yana faduwa ina fargabar tafiya makaranta saboda a makarantar boko ma nice monita a ajinmu saboda kokarina suma sai suyi ta xagina idan na rubuta sunan ‘yan surutu, a islamiyyar yamma har abun yafi haka ta dare ma haka. Abu ya hadu ya yi min yawa na rasa yadda xanyi da rayuwata gashi babu wanda xan iya tara in fadawa har iyayena tunda ba hira muke yi dasu ba.

Wata rana daddy ya gani da idonsa an tashi daga makarantar islamiyya da yake makarantar bata da nisa daga gidanmu da kafa nake xuwa. Shi kuma ya xo gari, ya xo wucewa xai tafi gida sai ya hango manyan ‘yan mata su hudu sun tarar min suna ta dukana suna yi min kwallo da jaka da dan kwali. Ya tsaya da mota yayin da ya fito a gigice ya xo ya raba yana daga ido sai yaga ashe nice. Ya fatattake su, yahau lallashina yayin daya dauko tissue ya bani na goge hawayena, ya karkade min hijabi na da dan kwali na ya bani na sa ke haka jaka ta da kan sa ya dauko ya saka min a mota yace in shiga gidan gaba in xauna. Bayan ya bani baki kuka ya tsaya sai ya shiga yi min tambayoyi a kan abunda ya hada ni da manyan ‘yan mata har guda hudu fada. Ya ce a iya sanin da ya min bani da jan fada amma yaya akayi na tsokane su.?

Da farko na boye masa nace ba komai saida naga ransa ya fara baci, ya fara Magana cikin tsawa da fushi sannan na xayyano masa duk abun da yake wakana a duk makarantun da nake xuwa cewar haka ake tare ni kullum ana dukana da xagi saboda na fi su kokari. Ya tausaya min matuka amma ransa yabaci saboda ban fada masa tuntuni ba ya dau mataki. Yasan ba xan fadawa iyayena ba don bana hira dasu meyasa shi ban fada masa ba da wuri ba tunda ya xo garin a ‘yan kwanakn?
Nayi shiru ban bashi amsa ba.

Sannan yayi min wata tambaya cikin wata tattausar murya y ace “kaltum ada bakya boye min damuwarki, ada bakya shakkar ki tare ni ki fada min abunda yake damunki ko abunda ki ke so amma a yanxu bakya yi. Kina so in yi fushi dake? ”

Na girgixa kai yayin dana sunkuyar da kaina nace “a’a”. y ace “to daga yau ki tare ni ki fada min duk wata damuwarki, xan yi miki maganinta in shaa Allahu. Gobe da safe xan je makarantarku ta boko in sanarwa malamanku da shugabannin makarantar duk abun da dalibansu ke yi, haka da yamma xan je islamiyya, ta dare ma xan je xan fada cikin babbar murya duk dalibar da ta sake dukanki sai nayi shari’a da iyayenta. A haka muka isa gida, bai bar niba saida y ace in rubuto masa duk abunda nake da bukata na makaranta da na gida na ci da na sakawa a jiki, sutura da man shafawa da sabulai. Haka kuwa aka yi na je gida na rubuto masa ba tare da na nemi shawarar kowa ba, na shiga har falonsa washe gari da sassafe na durkusa na gaishe shi sannan na bashi na wuce xuwa makarnta.

Kafin a fito breakfast sai ga daddy da shugaban makaranta (principal) a ajinmu. Principal ya tashe ni tsaye yace un nuna masu dukana, daya bayan daya na dinga xakulo su, sannan ya sa su wankin bandaki da sharar sati guda. Haka da yamma daddy ya xo ajinmu shi da shugaban makaranta, irin na safe aka yi musu, suma na nuna su . amakarantar dare ma haka aka yi, shike nan daga nan na sami salama da kwanciyar hankali, ganin daddy da aka yi yayi shiga ta alfarma, ga lumtsetsiyar mota shi ya kara min daraja a wajen malamai da dalibai suka dinga gulma suna cewa ashe ni ‘yar gidan masu kudi ce har ake cewa babana mai gadi ne. duk xancen ya dawo kunnena sai nayi dariya kawai. A gaskiya kuma na fi kama da daddy fiye da mahaifina saboda daddy fari ne dogo mai hanci sam dansa mashkur bai yi kamada shi ba, ya fi kama da anty salaha mamarsa, baka ce gajera amma dai fuskarta mai kyau ce tana da dogon hanci siriri.”

Madina ta nisa tace “cafdijam ana irin wannan kara da xumunci ashe? Amma daddy nan yana da kiriki, a xamanin nan waye xai tsaya ya damu da rayuwar ‘yar mai gadinsa? Irinsu basu da yawa a xamanin nan.”

Kaltum t ace, “sai lokacinda wani dan unguwar mu mai suna Hussain ya takura yana sona, ya hana ni sakat a unguwarmu. Gidansu ajikin katangar gidan mu yake. Har gidansu ya fi gidan mu girma da kyau . Ya ce shi fa a duniya babu macen da ta yi masa sai ni, ni kuma bana son sa dan ban isa xance ba dan haka duk sanda ya xo sai in gudu gida in ki fitowa. Haka idan xanje makaranta sai ya dauko lumtsetsiyar mota wacce babansa ne kadai yake hawa a gidan yace sai na shigo ya kai ni makaranta ni kuma in ki shiga. Ya yi ta bina a mota har bakin get din makarantar. Idan an tshi ma shi xan gani dam ma ma haka.
Da daddy ya xo gari na fada masa, ya dauki mataki kuwa ya jawa yaron kunne kuma ya shaidawa mahaifinsa aka yi masa fada cewar ya kyale ni in yi karatu, sannan na sami sa’ida ya rabu da ni. Duk wannan abunda ake yi iyaye na basu sani ba, ko da sun sani ma basu nuna min ba, nima kuma daman ba fada musu xan yi ba.
Ina aji hudu na sakandire wato S.S 1, domin an yi min tsallaken aji guda daga aji daya aka kai ni aji uku saboda kokarina a dukka bangarori biyu boko da na addini. Shekaruna goma sha biyar a duniya, tsautsayi ya rufto min har na tsinci kaina a cikin wannan hali.” Sai ta rushe da kuka.
Madina ta daga kan kaltum ta goge mata hawaye ta tambaya cike da mamaki “ban fahimce ki ba? ”
Kaltum ta goge hawaye da gefen siket inta, t ace, “wata rana da maraice muna xaune ni da iyayena a tsakar gida. Ina wanke wanke a gefe, babana da kannena suna xaune a kan tabarma suna cin gyada, mamana tana xaune a bakin murhu tana tuka tuwo, yayin da iya Altine tsohuwar da nace miki a baya ‘yar uwar mummy salaha ce wacce take xaune a gidan tana kular musu dashi.”
Madina t ace, “eh na gane ta, me ya faru? ”
Kaltum ta nisa t ace “itace ummul aba’isin da ta hada min tuggun daya kawo ni nan.”
Madina ta gyara xama ta yi tagumi tace “ina sauraronki kaltum.”
Kaltum ta yi shiru yayin da hawaye ya fara diga da alamar maganar da take shirin fitowa daga bakin xaxxafa ce, tana yi mata kuna a rai.
Ta ce “iya Altine ta dube ni ta yi murmushin munafurci t ace “oh kaltuma gidanku shiru-shiru da ke tun daxu ana ta hira da kannenki ko uffan baki ce ba kamar bakuwa. Wannan da rikon ki ake yi a gidan nan ba iyayen ki ba ne ai sai ace wahalar dake ake yi, kowa yana cin gyadar nan amma ke kin ce bakya ci yanxu idan wani ya shigo ai sai yace hana ki aka yi. Idan ana so a ji hirarki sai idan daddy ya xo, sai in jiyo muryarki ras tana bashi labari shi kuma yana ta dariya.!
Mamana ta yi murmushi t ace “haka suke yi tun tana yarinya daga ya ji kukanta xai shigo har nan gidan ya dauke ta. Ya ce min “Safi, me kika yiwa gimbiya ta? ”
Babana y ace “ai abu da dama sai dai in ji a bakin direba, ko in gani tace daddy ne ya saya mata na makaranta ko sayayyar amfanin gida. Sai addu’a tsakanina da mutumin nan yana da matukar kirki.”
Sai ni kuma na yi Magana saboda babu yadda xa’ayi xancen daddy ban ji xuciyata ta yi fari ba. Na ce daddy abokin hirata ne, daddy ne mai share min hawaye idan ina kuka, shine mai sona a duniya wanda baya sona in shiga damuwa.”
Sai altine ta tabe baki tace “ko er gida xa’a yi a ci amanar mommy salaha? ”
Wannan Magana ta iya altine tasa gaba daya mun girgixa, muka dago kai muka kale ta. Babana y ace “haba iya altine me yasa kike irin wannan maganar?
Ai hanyar jirgi daban ta mota daban, yadda uba ba xai iya auren yarsa ba haka daddy yake da wannan yarinya.” Haushi ya sa baba ya tashi ya saka takalmin sa ya tafi bakin get. Mamana ta girgixa kai tace “ai ko da wasa ma bai kamata a furta wannan maganar ba.” Iya altine sai ta wayance ta share maganar data ga dukkanmu ranmu yabaci. Bayan ta yi sallar magaruba ta cika tunbinta da tuwo sai ta yi mana sallama ta shiga bangarenta ni da kannena muka ta fi makarantar dare.
Washe gari da safe lahadi ce ina gida ban je makarantar boko ba sai ga mummy salaha ta diro a kofar dakina, ta biyo jirgin safe daga Abuja xuwa kano.
Sai muka ji tana fada da xage-xage wai ni da iyayena munafukai ne daga yau xamanmu yakare a gidanta. A gigice muka firfito ba tare da mun fahimci abunda take fadi ba. Duk da haka ni da iyayena da kanena muka durkusa a gabanta muna bata hakuri. Ta kwalawa iya altine kira ta xo, t ace ta fada mana laifin da muka yi mata don mun raina mata hankali muna nunawa ba mu san abunda muka yi ba. Iya altine ba kunya, ba tsoron Allah ta maimaita sharrin da ta shirya mana a waya. Ta ce da bakinta da nata na fada a gaban iyaye na nace daddy yace yana sona nima ina son sa kuma yana saya min duk abunda nake so, wai har iyayena suma sun amince ayi aure. Mu dukka muka dau salati muka hau rantse rantse ba ‘ayi haka ba. Mummy salaha t ace ko ba haka ba ne ita daman xuciyarta bata kwanta mata da ci gaba da xamana a gidanta ba saboda na xama budurwa, kyau ya taso, tana fargaba ko ni ban ce ina son sa ba, shi xai iya cewa yana sona. Ga tsananin shakuwar da ya yi da ni tun ina yarinya, don haka mu kwashe kayanmu mu fice mata daga gida ta bamu kwana uku kafin daddy ya dawo daga London, kada ya dawo ya hana mu tafiya. Ta shiga gidanta ta xauna tace ba xata koma Abuja ba har sai ta tabbatar mun bar gidan.
Hankalinmu ya tashi muka rasa in da xamu saka ranmu. Ta ina xamu fara, kuma ina xamu nuna?
Gidan kasarmu na xangon daura ya rushe babu ko daki daya a ciki. Tun dawowar goggo fattu daga Makka ta yi aure a daura, mijinta ya kwashe dukiyar ya sake ta yanxu haka a daura take xaune a gidan ‘yar uwarta babu cin yau ballena gobe kasancewar gidan ba kowa duk ya rurrushe.
Babana ya dora hannu a ka yana rusa kuka, mamana har ta fishi tawakkali ita take bashi baki ita ke cewa mu je mu sayi kara ayi bukka mu xauna gidan haka. Bayan an yi haka da kwana biyu, saura kwana daya wa’adin kwanakin data bamu ya cika mahaifana suka yi shawararsu, bansan me suke nufi ba suka ce in hado kayana kocokan in shirya in fito. Jikina na rawa na hada kayana a jaka. Babana ya saka ni a gaba muka fito daga gidan, bansan inda xamu je ba. Muka tsayar da acaba biyu muka hau har kofar ruwa tashar kuka sai naga mun hau motar daura. Ni dai ina ta lissafi a hanya ina tunanin wajen wa xa’a kai ni?
Sai gamu a gaban goggo fattu itama da alama tayi mamakin ganinmu. Koda suka kebe da babana, ya fada mata cewar ya kawo ni, ni da ita xa mu koma Makka sai ta fara washe baki tana farin ciki amma fa da yasa hannunsa a aljihunsa bai fito da kudin kirki ba sai dai ya bata ixini ta sayar da gidansa na xangon daura mu yi kudin jirgi. Da aka yi lissafi kudin gidan ba xai isa kudin jirgin ko mutum daya ba, sai tace masa ya kwantar da hankalinsa xamu tafi ta mota mu shiga sudan sannan mu haura Makka ta ruwa kudin xai isa. To a haka mahaifina ya tafi ya bar ni ko sallama bai yi min ba, yana kallon hawaye da yake xuba daga idanuwana saboda na tuno axabar da na sha a wajenta a wancen karon.
Na shafe wata guda a daura sannan gida ya sayu muka biya kudin tafiya da sauran shirye-shiryenmu muka taho. To shine wannan ganin namu da kika yi a cikin mota. Da idonki kinga yadda take kyarata, take duka a cikin jama’a, kin ga horon yunwar da take yi min , kin ga horar da take min, duk da haka se da ta hada da jakar kayana kacokam ta tafi dasu da gangan ta bar ni da kayan jikina kadai. Domin kawarta iya mairo ta fada min cewar tun a can daura agent ya sanar mata cewar tunda bata cika kudin bisa ba idan aka samu matsala ban wuce ba babu ruwansa tace eh ta yarda.” Sai kaltum ta rushe da kuka.
Madina ta surnano da hawaye ta girgixa kai t ace “kaltum ki bar kuka ki sa axuciyar ki duk abubuwan nan da suke faruwa mukaddari ne daga Allah , haka madina tayi ta bata Magana a karshe ta ce “xamu haye mu shiga makka idan shiga makkan kike so da ixinin Ubangiji.”
Kaltum ta girgixa kai yayin data dago da jajyen idanuwanta ta dubi madina ta fada cikin takaici t ace “bana so in shiga makka don a kowanne lokaci xan iya haduwa da goggo fattu ni kuma bana so in kara sakata a ido na har abada
. bana so in sake komawa Nigeria.
Alhaji adnan ne kadai nake tunawa nayi kuka, naji ciwon rabuwa dashi saboda na san shi kadai ne xai yi kunar xuci idan ya xo ya tara bana nan.na fada xan maimaita ko a gaban matarsa shine kadai yake sona nima nake sonsa a rayuwata. Ba xan banbance wane irin so na ke yi masa ba, shi ne kadai a duniya wanda yake mayar min da hawayena da yake shirin digowa kasa dariya. A ko ina ina ji dashi sosai a gida ko a makarnta tsakanina da jama’a sai kyara amma shi yana lallashina, Allah Ya dasa min sonsa a raina tun ina karama da son da ya kamata nayiwa uwata da ubana shi nake yiwa haka ban taba tunanin wani ba a cikin dinbun samarina da sunan wanda xan aura, sannan ban taba tunanin xan auri daddy ba sai dai ban san me yasa na damu dashi ba, idan ban gan shi ba bana jin dadi. Ina girma ina sake ganewa cewar shine mutum kwara daya me yi min wahala.
Kyarar dasu rukayya suke min da kakarta da saura ma, du na saba domin haka kakata goggo fattu ta ke min. a makaranta, kyara, da muka je hutu Abuja wajen mommy salaha hutu ma be kare ba ta koro ni.. se ta fashe da kuka..
Madina ta girgixa kai ita ma kukan take t ace “daina kuka kaltum, ki nemi son Allah bana mutum ba. Duk inda akwai alamar nasara to ba xa’a rasa mahassada ba. Kema da kanki kin ce maxa suna sonki matan ne suka tsane ki, don haka mace ba xata iya aurenki ba duk in da kika kai ga kyau sai dai ma ta yi kishi kin fita kyau, ilimi, hakuri , fara’a da dai sauransu. Saurayinta ko mijinta xai aure ki ya daina sonta shi kuwa burin namiji ya sami irinki ya aura don haka maxa xasu so ki, amma baki da bakin jinni, iyayenki ma suna sonki kunya ce da rashin wayewa kawai saboda basu da ilimi duka.
Wallahi da sun san haka xe faru ba xa su turo ki ba sun gwammace ku koma xangon daura ku xauna ku duka a bukka. Kaltum waye Mambela? ”
Wannan tambayar madina ta fadarwa da kaltum gaba. Nan da nan ta dago ta dubi madina har tsawon wani lokaci, tana tunanin mai xurfi inda madina ta ji sunan mambela. Ta ina xata fara bayar da labarin mambela yadda xata fahimce ta. Hakika ba don dole da ba xata bada wannan labari ba, saboda yana daya daga cikin abunda ta tsana wanda bata so ta dinga tuno shi a ranta balle ace tana furtawa da bakinta. Kaltum ta cije baki yayin da hawaye mai radadi yake xubo mata.
Ta ce “Mambela! Mambela!! Mambela!!!
Wani dan ADON DAWA ne, wanda na hadu dashi a jim arab kasuwarsu, ranar wata asabar da yamma. Mambela da abokansa sun kaisu goma sun yi niyyar cutar rayuwata, yasa abokansa su dauko ni aka suna shirin turmusatsa ni a cikin wani shago xasu yi min fyade wani tsoho ya xo ya ceto ni ya hana su, ya rako ni har gida.”
.
Typing : Sadin Maa.
Posting : Dan Aunty.ADON DAWA 10
.
TRUE LIFE STORY
.
Madina ta dafe kirji ta ce “subhanallahi, daman mambela mutum ne! ai mu mun dauka aljani ne gamo kika yi saboda mun ga kina xabura cikin dare kina ihu kina kiran sunansa kina fita da gudu, kullum kina kokarin bude kofa ki fice kina cewa gasu mambela nan xasu kama ni.”
Kaltum ta xabura ta dafe kirji ta tambaya cikin rudani hade da matsananciyar damuwa t ace, “au har kiran sunansa nake cikin dare, ina fita da gudu!” sai hawaye ya kece mata.
Madina ta dafa kan kaltum ta girgixa t ace “kwantar da hankalin ki, ba wani abu ba ne daman haka ne idan mutum ya tsorata da abu. Babu abunda xai same ki in shaa Allah. Shine ya ji miki ciwo a hannu!”
Kaltum ta soka hannu a cikin rigarta sai ga wani karfe mai kyalkyali kamar axurfa. Yayin da madina ta bude baki tana dubanta cike da mamaki. Kaltum na danna gefen karfen sai ga kan wuka ya fito mai tsananin kaifi da sheik ko ba’a fada maka ba kasan wukar nan fit xata dauke kan kaxa. Madina tad aka tsalle ta ja da baya ta tambaya cikin gigita. Ta ce “kaltum ina kika sami wuka! Me xa kiyi da ita!”
Kaltum ta tauna lebe, yayin da ta runtse idanuwanta tana rike da wukar tana jujjuyawa.
Ta ce, “na sami wukar nan daga hannun wata mata a lokacin das u mambela suka tare ni, na shiga gidanta da gudu sauran matan gidan suka koro ni waje. Na dai yi mata bayanin duk yanda muka yi da mambela.”
Madina t ace “wa iyyaxu billah, Allah Yayi mana tsari da mambela. Shi ya kwace wukar a hannunki ya yanke ki!”
Kaltum ta sunkuyar da kai kasa tace “n ice na yanka a gabansu na shaida musu na yanka kaina ma balle wani, xan yanka duk wanda nake kuma xan iya yanka su tunda na yanka hannuna sai suka ja da baya suka fasa taba ni.”
Madina ta girgixakai t ace “lallai kaltum kina ganin jarabawa kala-kala daga Ubangijiki kina yarinyarki karama. Ki daure ki ci jarabawar nan kiga yadda Allah xai miki sakayya nan gaba. Shawarar da xan baki anan shine sai kinyi taka tsan-tsan, kid age da addu’a wajen tarkon maxan banxa.
Hakika kyawun da tsarin dirin jikinki tabbas xai ja hankali maxa da yawa.kina ganin a cikin gidan nan ma kaxaman samarinsu da tsofaffinsu suna xuwa ,ta bayan gida suna laka ki ta hudar bandakisunaganinki idan kina wanka. Suna leka kowacce mace amma sun fi leka ki saboda suna sha awar kyawunki.
Kaltum ta dafe kai don takaici, bakin ciki ya hana ta Magana.
Madina taci gaba da cewa “yadda aka yi na gane shine duk sanda kika shiga wanka saisu xo suyi kamar xasu shiga wanka sai a ce da mutum kaltum tana wanka,sai kiga daya bayan daya suna fita ashe waje suke fita suna leka cikin bandaki da naga haka nima sai na bisu baya sai gasu a jikin katako suna kyallara idanuwansu, nayi musu tas na xaxxagesu na kuma ja musu Allah ya isa amma yanxu na lura sun daina.
Kaltum nayi miki alkawarin tsaya miki tsayin daka wajen kare mutuncinki kamar ‘yar cikina. Idan ina raye a gidan nan ba xan bari wani da namiji ya nemi ya lalata miki rayuwarki ba sai dai idan ke kika kai kanki. Wanda nayi imanin ba halinki ba ne, ki kama kanki, dai –dai da rana daya kada ki bari wani da namiji ya taba miki jiki. Ko taba jikinki namiji yayi ciki xaki dauka kuma mutuwa xaki yi a wajen haihuwa tunda ke karama ce. Kiyi taka tsan-tsan da su membela kada ki sake bin hanyar da kika san suna bi balle ku hadu. Ban hanaki adana wukarki ba don ki kwaci kanki, haka ban baki goyon baya ki kara yanka kanki ba a banxa, sai dai ki tsorata su da wukar in har yin hakan xai raxana su su kyale ki. Idan kuwa tsautsayi yasa kika yanki waninsu da wuka ya ji ciwo akwai matsala saboda tabbas shi da ‘yan uwansa xasu kash ki. Ba sai sun kai ki kara hukuma ba, dan haka nake jin tsoran rike wukar nan a gare ki. Da akwai yadda xan yi kaltum da sai in hana ki fita bara kwata-kwata ma in dinga xuwa ina samo mana abuda xamu ci, to nima wata rana dakyar nake samu sai na yini ina yawo ban samu ba. Shawarata ta karshe a gare ki it ace ki sawa ranki kece uban kanki da kaki anan, ki sawa ranki idan kina bukatar wani abu anan ke xa ki fita ki nemo babu wanda ya ajiye ki don haka bana so ki xama wawuya a cikin mutane. Kin xama juji kowacce bola ke ake xubawa dole ki kwaci kanki.
”kaltum ta tsurawa madina ido tana kallonta da alama bata fahimci abunda take nufi ba.
Madina ta ce “ina Magana akan ‘yan dakinmu su rakiya da suke takura miki,koda yaushe suna xagin ki kina kuka. idan sunyi miki kiyi musu sai ki sami sauki wata matsala daga cikin matalolin da suka addabe ki. Xan iya faduwa na mutu a yanxu haka, ni mai rama miki sai kiyi yaya kenan! Don haka kiyi maganin wannan matsalar dakanki sai ki ji da matsalolin su mambela, su kuma Allah Ya fi su shi xe yi miki maganinsu babu wanda ya gagari Ubangiji. Babu yadda xa’ayi a waje a takura miki a gida ma a hana ki sukuni ina xa ki saka ranki kenan. Ka da kiyi tsokana idan ba’a taba ki ba, kada ki taba kowa ki girmama duk wanda ya fi ki idan ya kamata, nasan kina sallah akan lokacinta duk tsananin ciwo ko yunwa nayi miki wannan shaidar bakya kin yin sallah sai dai kina da karancin yin addu’a. ki yawaita addu’oin neman tsari daga sharin mutum da aljan, yaro ko babba, dare da rana. Ki yawaita addu’a samun sauki a lokacin kunci, sannan ki ji tsoron Ubangijin ki a duk inda kike ki san Allah Yana ganinki. Ki guji xina, ki guji xina kikiyaye kusantar xina ko talauci xai kasha ki balle Allah ba Ya hana duk wanda ya fita nema. Yin haka Allah xai xamanto jagoranki.”
Madina na rufe bakinta sai kaltum ta rushed a kuka ta rungume ta. Su dukka kukan suke yi ba kakkautawa aka rasa mai lallashin wani, har xuwa lokaci mai tsawo sannan kaltum ta janye jikinta daga jikin madina ta koma ta xauna. Ta sharce hawaye ta dubi madina.
Ta ce “kina fada min gaskiya anty, kina sona, nayi alkawarin xan bi duk shawarar da kika ba ni kin xama uwata, ke ce ubana, ke ce kika gaji daddy wanda yake share min hawaye. Anty madina, xan so in ji labarinki kema, in ji asalinki, da dalilin fitowar ki daga kasarku xuwa wannan kasar.”
Madina tayi murmushi t ace “so kike kiji labarina nima! Me yasa ki ke so ki ji labarina! Hakika labarina ya hada da abun mamaki mai firgitarwa. Xa ki ji abubuwan ban tausayi da yawa, abubuwan da baki taba jib a balle ki gani a rayuwar ki”.
Kaltum ta gyara xama t ace “ki bani labara anty madina.”

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.