Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 1 of 21
[6/24, 9:46 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers associationÂ
*MAFARI* .....
       ( _HARGITSIN RAYUWA_ )
*Umm'muaz*
   Â
Ø¨ÙØ³Ù’ــــــــــــــــم٠اللَّه٠الرَّØÙ’Ù…ÙŽ
الرَّØÙيْم.......
*In The Name Of Allah, The Beneficent, The Merciful.*
*Da Sunan Allah Mai rahama Mai Jinƙai* .
 Â
_MAFARI...komai yana da farko, komai yana da tushe, komai yana da asali, HARGITSIN RAYUWA kan faru cikin kankanin lokaci_ .
_Duniyar daka saba da ita zata iya birkicewa zuwa baquwa a gareka cikin kankanin lokaci._
_Tafiya mabanbanciya da sauri, a cikin kaddara da dai-daito._
       1
*SHIMFIÆŠA*
Ƙauyen Mairambiri , wani ƙauye ne , ko kuwa "ƙaramar Alƙarya" da yake tsakanin ƙananan hukumomin bama da konduga, wanda suke a karkashin jahar ( BORNO )
Mutanen garin mafi akasarin su barebari ne " kanurai", sai kuma shuwa, da fulani, tsilla-tsilla, babbar sana'ar mutanen garin shine noma, suna da makarantun primary da secondry na gomnati, sai kuma makarantun allo da mafiya yawan yaran garin shi suka fi zuwa ,tsiraru ne suke zuwa bokon da suke kira karatun "Malam nasara", kasancewar garin nasu yana tsakanin manyan-manyan hukumomi biyu ya sanya suke da kasuwar su a bakin babban titin da yake tsakanin garin bama da konduga" wacce take ci duk ranar Alhamis.
            **************
Cikin wani ƙwarababben gidan kasa , wasu yara ne su uku mata, suna cin wani zazzafan damalmalallen tuwon hatsi miyar kuka shar cikin wani tsohon kwanon da duk lamba da tsatsa suka gama munana shi , babbar baza ta wuce shekaru 16 ba ,sai ta tsakiyar me kimanin shekaru 14, sai kuma ƙaramar su me kimanin shekaru 8.
Cikin nutsuwa babbar ta ke kai lomar tuwon bakin ta bayan ta sanyawa ƙaramar su ita ma a bakin ta ,saboda zafin tuwon ta kasa sanya hannu taci ,"alama yanzu aka sauke dumamen tuwon daga wuta "duk da yanzun farar safiya ne ko 6:30am bai cika ba.
Wata doguwar mace siririya me ɗauke da wata irin farar fata sol-sol kamar ta so ta zama zabiya " Albinism" dan hasken ta yayi irin nasu, wacce da ganin ramar da take da shi na tsabar wahala da talauci ne ,tana zaune kofar wani taƙwarƙwasashiyar rumfa da alama madafi ne ganin yadda duhun wajen yafi na ko'ina a gidan, hannunta riƙe da wani jariri namiji kansa tanƙwal da aski , ta ciro yamushashen siririn maman ta tana kokarin cusawa yaron a baki shi kuma daga ya kama yayi tsotsa ɗaya-biyu yake sakewa ya cigaba da tsala kukan da yake da alamun yunwa ce ke addabar sa .
Wani baƙin dogon mutum ne, ya bullo daga bayan durkusassun ɗakunan nasu guda biyu ,hannun sa rike da babbar robar ruwa (table water ), wacce aka yanke daga wuyan ta zuwa sama gefen ta daga kasa yana ɗan ɗigar da ruwan ciki daidai inda ya ɓule aka toshe da bakar leda .
Duƙawa yayi tare da  wanke baƙaƙen kafafuwan sa da suke sanye cikin waɗansu ratattakakkun silifa (da guntun ruwan ) ,ya ɗago tare da kallon sashin da ƴaran nan suke zaune ya ɗan ɗauki wasu daƙiƙai yana kallon su cikin nazarin yadda babbar cikin take ta ciyar da kannan nata domin ya zuwa yanzu dai su duka biyun ita take sanya hannu tana zaƙulo tuwon da ya dilmiye cikin tsululun ruwan miyar da ta haura tuwon yawa har ta shaa kansa ,tana zaƙulo shi sannan ta hura iskar bakin ta ta gutsurawa ɗayar a hannu ta sanyawa karamar sauran abakin ta ,
kuma a take ta sake mayar da hannun ta cikin kwanon da hanzari tamkar dai ita bata jin zafin tuwon .
Yakaka " _nyidin biri bun" baa ? Duwan "bii lanyen wande kausuzuin_ (yakaka ke baza ki ci abincin bane ? Kiyi sauri ki ci mu tafi kar rana ta yi ) cewar wannan mutumin ga babbar É—iyar ta sa da ya kira da suna yakaka cikin yaren su na " _KANURI_ .
Amsa masa tayi da "toh" ,dai-dai lokacin da ta miƙe da hanzari ta zagaya ta bayan matar nan da hasken fatar su yake yanayi ɗaya da nata ,ta ɗauko wani bakikkirin ɗin tiren kwano da yayi fatsa-fatsa da lamba ta nufi fasashiyar randar su da take binne a kasa sai iya fasashen bakin ta ake gani a waje "wanda za'a iya zaton rami ne" ta sunkuya tayi goho ta kwarfi ruwa a chan kasa ta ɗauraye farantin ,
Ta sake kwarfo wani ruwan a cikin bulalliyar moɗar da ta sha liki da leda , cikin gudu gudu ta je ta juye tuwon a kan farantin tare da ajiye musu ruwan , har ta yunƙura ta tashi ,sai karamar ta riƙo hannun ta ,a hankali ta ɗago idanun ta ta dubi kanwar tata wacce idan aka dauke kamanni irin na jini , da kuma siraran zane ( _Shunkurai_ ) da yake kan fuskokin su guda tara-tara "wanda yake bayyanawa a sarari daga ƙabilar da suke na barebarin usul " bayan hakan kowaccen su kamannin ta daban ne ,
Babbar su tana ɗiban yanayi da uwar su "watau fara ce sol yanayin hasken mutanen da suka so zama Zabiya ( albino ) yayin da ta tsakiyar take da rangwamen hasken fata ,karamar kuwa baka ce sosai kamar mahaifin su , Da alamu dukkanin su dogaye ne samɓala-Samɓala duk da cewa suna kan shekarun kuruciya sosai "yara ne " .
Cikin yaren su karamar ta cewa babbar ta kawo mata gurji daga gona, shafa kan ta tayi cikin nuna kauna tace zata kawo mata daga haka ta juya ta nufi ɗakin su tare da sako wani ɗangalallen hijabi cukurkuɗaɗɗe yagagge bakikkirin da shi ta kuma zagaya bayan ɗakunan nasu ta ɗauko wani buhu da alama abubuwan bukata a gona ne a ciki.
Duk abun da ake mahaifiyar su tana zaune bata umm "bata a ah ,sai faman girgiza jaririn ta take da sigar lallashi "shima fari ne sol irin ta amma ita fuskar ta babu zane irin na ƴaƴan ta ga alamu ita ba babarbari bace , kamar yadda yaran da mahaifin su kana kallon fuskar su zaka shaida yaren su .
Sun zo zasu fita ita da mahaifin su mahaifiyar su ta miƙe ta rako su bakin zubabbiyar katangar da baza'a ce mutane na rayuwa cikin zagayen ta ba , a bakin labulen tsunman da aka kare wawakeken giɓin da ya kasance mashigar gidan ( ƙofa ) , ta tokare sannan ta ɗaga hannu cikin maganar kurame tana musu alamar a dawo lafiya ta hanyar jujjuya tafufukan hannun ta ( _bye-bye_ ) tare da yin gwalatu cikin maganar bebaye," wanda hakan shi yake bada tabbacin KURMA ce "kallo ta bisu da shi fuskar ta ɗauke da murmushin da sai ita kadai ta san dalilin yin sa a cikin wannan yanayin da su ke ciki" .
Sun dauki tsawon lokaci suna girbi cikin ƙatuwar gonar su da take wajen gari ,Suna hirar su da kana ji kasan akwai soyayya da shaƙuwa me karfi tsakanin uban da ƴar sa kafin lokacin da yakaka ta cewa mahaifin su zata je kama ruwa (Ban ɗaki ) , ta juya gami da shiga cikin dogayen shukokin masarar da suka fidda kai suna jiran girbi , tana tsugunne cikin duhun gonar ta fara jiyo kabbara tare da iface-ifacen mutane .
Ta miƙe da sauri tana sanya ɗan kanfai (wondon ta ) , lokacin da taji mahaifin ta yana kwala kiran neman ta da sauri ta nufo wurin da taji muryar sa , ita ma ta buɗe murya tana kiran sa tare da shaida masa ta dai-dai wurin take , wata razananniyar karar da taji tare da sake kusantowar kabbara da hayaniyar mutanen nan shi ya sake sa ta ruɗe .
Duk da bata san bindiga ba a zahiri amma tasan karar nan da take ji na abu me cutarwa ne , har zuwa lokacin da taji muryar mahaifin ta cikin ƙaraji yana cewa ta kwanta kar harbin bindiga ya same ta , ai sai ta sake ruɗewa ta nufo inda ta ji muryar sa cikin gunjin kuka da kiran sunan sa .
Shi kuma jin ta nufo shi ya sanya ya miƙe daga kwanciyar da yayi dan gujewa harsashi ,ya nufi inda yake jin kukan ta cikin tsoron kar harsashi ya same ta ko kuma ƴan tawayen su ganta su harbe ta ko su tafi da ita ( kamar yadda suka samu labarin hakan na faruwa a sauran garuruwa da ƙauyukan borno *ƳAN TAWAYEN BOKO HARAM* sun addabi mutanen ƴankin arewacin nigeria musamman jahar Borno da kewayenta wanda a nan mafarin abun ya ke. ) yana miƙewa yayi taku ɗaya biyu a na uku yaji kamar wani abu me karfi ya wuce ta jikin sa ya ɗauke shi yayi jifa da shi , yaji jikin sa kamar ba nashi ba .
Dai-dai lokacin da Yakaka ta ci tintiɓe da shi da sauri ta sunkuya gami da kamo shi ihun da ya ga ta sa tare da daura hannun ta akan kirjin sa yaga ta ɗago hannun na ta face-face da jini, shi ya tabbatar masa cewa harsashi ne ya same shi ,a take ya fara salati da karanto ɗukkanin addu'o'in da suka zo kan sa a lokacin .
Ita da kanta baza ta iya kiyasta tsawon lokacin da ta É—auka a zaune rungume da gawar mahaifin nata , wanda tun bayan da harsashin ya same shi bai sake ko minti goma ba ya rasu . ( *Yaa Allah ya jikan dukkanin Æ´an uwa musulmai da suka rasa rayukan su a sanadin annobar Boko haram Ameen* )
Tayi kuka har hawayen ta ya ƙafe har tunanin ta ya tsaya , ta gigice iyakar ɗimaucewa ,ta rasa hankalin ta a tsakiyar gonar rungume da gawar mahaifin ta wanda jinin sa ya bata mata jiki face face ,har wani wuri ya fara bushewa a hankali ta ɗaga kanta ta dubi yadda dare ya fara alamun shigowa rana ta tafi zata faɗi ga kuma hadarin da yake haɗowa, cikin shishiƙar kuka ,jiri da tsananin galabaita ta ɗaga kan mahaifin nata da tun kafin rai ya kammala fita daga jikin sa ta ɗora kan sa a kan cinyoyin ta a gaban idanun ta ya rasu ,ita ta ke bashi kalmar shahada duk da karancin shekarun ta , cikin wani irin kuka ta sake mayar da kan nashi ta ajiye bisa cinyoyin nata tare da sake rungume gawar shi ( da ta Riga ta fara ƙandarewa ) tana wani irin shishikar kuka , ta ɗau tsawon lokaci a haka sannan ta sake ɗagowa tare da zare hijabin kan ta ,ta shimfiɗa cikin karfin zuciya ta sauke kansa a hankali daga jikin ta ta ɗora akan hijabin nata, kuma ta ɗauki lokaci tana yi masa addu'a.
Sannan ta mike a zabure ta juya cikin hanzari ta nufi hanyar gidan su domin ta sanar tana tafe tana waiwayen duhun ciyawar da ta riga ta kare gawar mahaifin nata , har dai ta zura da gudu tana kuka tana sharar hawayen ta.
Birki ta jaa tare da rage takun tafiyar ta lokacin da ta bullo bakin hanya , hakan yana da nasaba da guje guje gami da iface-iface da ƙarar harbe-harben da take ji yana tashi daga ainahin cikin ƙauyen nasu , kowa ta nufa da gudu domin ta tsaida shi tayi tambayar me ke faruwa sai taga an bangaje ta an wuce da gudu wasu na kuka wasu na salati da addu'o'i wasu kuwa kana ganin su ma kasan gudun ceton rayukan su suke domin dai duk sun kukkuje sun ji munanan raunika ,amma ahaka suke gudu suna barin ainahin cikin ƙauyen nasu zuwa cikin gonaki da daji.
A hankali ta ɗaga kanta sama tana iya hango yadda sararin samaniyar ƙauyen nasu ya tuniƙe da hayaki har ma tana iya hango harshen wuta da yayi tsiri yake toroƙo a wasu sashi na cikin garin, nan take wani irin tsoro da tashin hankali ya mamaye zuciyar ta tunowa da mahaifiyar da kannen ta da tayi suna cikin ƙauyen nasu ,da yanzu take hango tarwatsewar sa da mummunan bala'in da ya fada musu .
Cikin karfin zuciya ta yunƙura da gudu ta nufi hanyar gidan su , tana ta cin gware da karo da mutanen da suke gudu daga cikin garin( amma ko kula bata yi ba) zuwa lokacin da ta ji carafa an kama hannun ta da karfi an fusgo ta, da sauri ta waiwaya tana fatan ko ɗaya daga cikin ƴan gidan su ne "mamar su ko ƙannen ta.
Amma sai taga modu ne saurayin da unguwar su ɗaya ɗan maƙotan su ne , cikin sauri ta dawo da baya tare da rike hannayen sa biyu tana haki ,fuskar ta ɗauke da matsanancin tashin hankali take tambayar sa ina mamar ta ina kannen ta ? Amma maimakon ya bata amsa sai taga yana jaan ta da gudu su koma hanyar da ta bullo , da karfi ta fisge hannun ta tare da yi ma sa tsawa tana sake maimaita tambayar ta "Modu nda mamanyi nda kiramiyanyi " ?
Yakaka yanzu ba lokacin tambaya bane domin rayukan mu suna cikin haɗari , ban san inda suke ba , ki zo mu gudu yagana, kashe mutane ƴan tawayen *BOKO HARAM* suke sun yanka babanmu ,da yaa bakura sun tafi da Fannah da yaakori "(kannen sa) " maman mu ban san inda take ba ita da sauran kannen mu ,sun ƙona gidan mu da gidan ku da ....
Tunda ya fara nisa cikin bayanin sa ta daina fahimtar me yake cewa , zuciyar ta ta tafi ga tunanin me yake faruwa da su ne ?, ta yaya zata rasa kowa da kome nata a yini ɗaya ? Baban ta ya mutu , bata san inda mahaifiyar ta da kannen ta suke ba a mace suke ko a raye ? Ina zata je ? Bata da kowa bata san kowa ba bata taba zuwa ko'ina ba babu inda ta sani bayan ƙauyen su , a hankali ta juya tana nufar cikin garin su hanyar unguwar su cikin ran ta tana aiyanawa gwara ita ma a kashe ta gwara ta mutu .
Bata da karfin jiki da na zuciyar tunkarar wannan sabuwar rayuwar da take tunkaro ta wacce bata hango kome a cikin ta ba sai tarin tashin hankali wuya da wahala ,maraici da rashin madafa .
Da karfi modu yake kwala mata kira yana so ta dawo su tafi domin shi yaga irin bala'in da bata gani ba da yake cikin garin wanda mutuwa ce murarar ta , mutuwar ma ta walakanci wanda aka harbe da bindiga ya mutu shi ya ji daÉ—i akan waÉ—an da aka kwantar aka yi wa yankan rago da waÉ—an da aka sanya wa wuta suka kone kurmus ,da waÉ—an da aka jefawa bom yayi kaca-kaca da su .
Dan haka ya kasa bin ta ya taro ta "duk da cewa akwai boyayyar soyayyar Yakaka cikin ransa wanda bai kai ga bayyana ta ba" amma baya jin matakin son da yake yi mata ya kai wanda yake yiwa ransa da rayuwar sa baya jin zai iya salwantar da ran sa domin taya ta neman iyayen ta, dan haka ya sake juyawa da gudun gaske yayi gaba ba tare da ya sake waiwayar ta ba ,
Cikin rashin sanin inda take sanya kafafun take tafiya kunnuwan ta sun toshe daga jin hayaniyar da ta cika duniya, tunanin ta ya bar gangar jikin ta ta yadda har bata jin turewa da bangajewar da mutane suke mata , wanda yawancin su daga unguwannin da suke ƙasa da tasu unguwar suke fitowa wanda a halin yanzu ƴan tawayen suke far musu ,.baza ta ce ta yaya aka yi ba kawai taga kanta ne a gaban rugujajjen ƙonannen gidan nasu da har yanzu ta wasu wuraren wutar bata gama mutuwa ba domin tana iya hango hayakin da ya ke turnuke da gidan .
Da gudu ta taka ta shiga gidan tana kwalla kiran "mama "yaana "falmata " shiru taji babu motsin kowa , cikin tashin hankali take kallon tsakar gidan nasu da yake a hargitse kamar sansanin yaƙi , kome baya muhallin sa duk da daman su basu da kome a cikin gidan nasu sai tsumokarai da ƴan tsofaffin kayan aikin su na gida wanda su ma a halin yanzu duk a ƙone suke idan ka dauke randar su da take binne cikin ƙasa da gudu ta nufi ɗakin su duk da hayakin da take hangowa cikin ɗakin ta saman sa wanda rufin zanar ya riga ya cinye ,ya zama saman a buɗe yake wayam, hakan bai hana ta cusa kanta cikin ɗakin ba babu kome cikin ɗaƙin sai burbuɗin tokar wutar da ta gama cinyewa , bakikkirin hayaƙin ma daga kan guntun kayan su ne da ya gama ƙonewa ba jimawa yake tashi .
Durƙushewa tayi ta saki wani irin kuka da yake fita daga karƙashin zuciyar ta ,kukan maraicin da ya same ta a rana daya , kukan rasa komen ta da tayi , kukan sabuwar Rayuwar da take fuskanta .
Ta ɗauki tsawon lokaci tana kukan nan har zuwa lokacin da ta fahimci hayaniyar da ta cika garin nasu ta fara raguwa sai tsilla tsilla take jiyo ihu da wucewar mutane a guje , har zuwa lokacin da ta tabbatar dare yayi , ganin duhun da ya mamaye sararin samaniya , da sauri ta miƙe tunowa da tayi bata yi sallar azahar, la'asar, da magarib ba ta kuma tabbatar lokacin isha'i ya yi tana son yin addu'a ta sani bata da kowa bata da kome a yanzu sai Allah dan haka gun shi zata kai kukan ta .
Tana fitowa tsakar gidan ta rasa abun da zata yi alwala da shi ,( sakamakon duhun da ya mamaye tsakar gidan, ) da taimakon hasken walƙiyar da take ta haske sararin samaniya, ta hango wani bakin kwanon da duk wuta ta kone sa wanda ada shine kwanon da suke ji da shi duk gidan kuma shine kwanon cin abincin baban su .
Da gudu ta karasa ta É—auki kwanon ta rungume tare da fashewa da kukan tuno mahaifin ta da gawar sa take can a cikin gona bai samu ko darajar suturtawa a kai sa makwancin sa ba .
Bayan ta share hawayen ta takarasa tare da buɗe randar su wacce ita ƙadai ce ba'a tarwatsa ba a gidan su ,"dalilin tana binne ne cikin ƙasa" ta sunkuya tare da buɗe randar , hawayen idanun ta da suka ƙi tsayawa suna ɗiga cikin randar , ta yi goho tare da sa kwanon cikin randar da nufin ɗibo ruwan ciki amma sai taji hannun ta ya tokare bai karasa ƙasan ba sannan kwanon ya bigi wani abu a cikin randa a firgice ! Ta mike jikin ta yana rawa tafara jaa da baya ,tana tunanin menene a cikin randar ?
Ji da tayi kamar wata karamar dushashiyar murya tayi magana Daga cikin randar da ya sanya ta sake shiga cikin fargaba !, kuma kamar wacce aka zabura ! Sai ta nufi randa da gudu gami da durƙusawa ta leƙa cikin randar zuciyar ta cike da zumuɗin Allah ya sa tunanin ta ya zama gaskiya .
Ai kuwa da sauri ta sa hannu gami da taya ƴar uwar ta ta fitowa daga cikin randar da tayi maboya a ciki wacce bakin ta ya riga ya guntule ya farfashe daga sama , tana gama taya ta fitowa ta rungume ta cikin kuka yakaka take tambayar Falmata ina mamar su ? ina sauran ƙannen su ?
Cikin kuka da dushewar muryar da bata fita sosai tsabar kuka take cewa lokacin da muka fara jin harbi sosai sai mama ta ɗauki bulama da yaana, ni kuma ta saka ni cikin randa "saboda tasan bazan iya gudu da sauri ba dan bana GANI " ta ce min zata kai su yaana gona ta boye su ta dawo nima ta ɗauke ni , shine har yanzu bata dawo ba, Yakaka ina baban mu ? Ki kaini gurin sa ya nemo mana mama da su yaana ,,, ina jin tsoro dazu naji mutane har gida suna neman mu inajin ihu a gidan su modu da gidan su yanziye naji suna ihu da cewa wuta wuta , ana ta kuka da salati ina ji ana harbin mutane , meye yake faruwa yau a garin mu ?
Jin shiru ya sa falmata ta fara lalube har ta kama hannun yakaka wacce tun da falmata ta fara bayanin take kuka , kukan mutuwar mahaifin su , da batan mahaifiyar su da ƙannen su , kukan tausayin falmata da take MAKAUNIYA , marar gata marar galihu , daman gatan su Allah sai kuma iyayen su to gashi sun rasa su a lokaci ɗaya , ba iyaye kawai suka rasa ba har da dangin su ƴan uwa , makota da abokan arziki , gidan su da garin su baki ɗaya , dan ko ba'a fada musu ba ta san garin su ya tarwatse , hakan yana nufin sun rasa kome nasu .
Wani irin kuka me karfi ne ya kwace mata ta sake rugume kanwar ta tsam-tsam tana jin bata da kowa bata da kome sai Allah sai *FALMATA KANWAR TA* ,
Kukan su ya tsannanta lokacin da yakaka ta gama sanar da falmata kome game da mutuwar baban su , kuka suke an rasa me rarrashin wani a tsakanin su , ga wani irin mugun tsoro da zukatan su ke ciki na rashin jin motsin kowa a unguwar su kusan ma garin nasu baki daya , ga baƙin hadarin da ya hado bakikkirin wanda ya kara wa sararin samaniyar garin da dare ya riga yayi duhu sai walkiya da cida ,alamun ruwan sama gaf yake da fara zuba .
A hankali yakaka ta É—ago falmata daga jikin ta tana share mata hawayen da suke zubowa daga gurbin idanun ta wanda idan ba an fada maka ba ko kuma ka lura kaga yadda suke tsaye kem alamun basa amfani uwa uba kagan ta tana lalube , baza ka taba cewa bata gani ba domin tar idanun ta biyu suke a buÉ—e ,ko meye sanadin makantar ta ? Ko haihuwar ta aka yi da shi ?
Ɗaga kai tayi ta sake kallon sama tana tunanin ina zasu samu mafaka daga dukan ruwan saman da yake daf da tsugewa , da sauri wata dabara ta faɗo mata cikin dusashiyar muryar tace falmata muyi sauri muyi sallah kin ga ruwa za'a fara ke kuma kin san kina rashin lafiya idan ruwan sama ya doke ki "zazzabi da mura" dan haka idan mun idar da sallah sai ki koma cikin randar ki bani hijabin ki na haɗa da zani na na rufa a bakin randar sai na daura murfin "wani ƙuzajjen farantin kwano ne" na rufe ki a ciki zuwa lokacin da ruwan zai tsaya sai musan in da zamu yi .
gƴada kai kawai falmata tayi , cikin sauri-sauri suka yi alwala suka duddungura sallolin su wanda kana gani kasan akwai ƙarancin ilmin addini a tare da su, ko kafin su gama an fara yayyafi da karfi da ya sanya yagana yanke doguwar addu'ar da ta fara ta kama hannun ƙanwar ta tare da kama mata ta koma cikin randar .
ko kafin ta gama toshe mata bakin randar ruwan ya riga ya tsinke, cikin hanzari ta gama rufewa ta tsugunna a bakin randar daga ita sai rigar ta da É—ankwali sai kuma siket É—in ciki, haka ta takure jikinta ruwan nan yana dukan ta , ta É—aura kanta akan gwaiwar ta hawaye yana sauka a idon ta tare da zubar ruwan saman da yake sauka a fuskar ta yana wanken hawayen da yake sauka, bakin ta É—auke da addu'o'i iri-iri da take yin su cikin yaren ta.
Ruwan saman sai yayi kamar zai tsaya sai kuma ya sake tsugewa , a hankali sai da tsakar gidan su ya cika taf da ruwa, " kamar yadda ya saba" cikin karamar muyar falmata ta ankarar da yakaka wacce ta yi nisa cikin tunani har bata jin yawan ruwan da ya haura idon kafar ta ,"ruwa ya fara shigowa cikin randar yakaka,' cikin tashin hankali da sauri ta zame dankwalin kan ta ta matsa ruwan jiki ta sa dankwalin ta toshe hudar jikin randar da ruwan ya ke tsiyaya ciki ta ɓulin,
Ta sake tsugunnawa gami da takure jikin ta cikin jin matsanancin sanyi da wani ciwon kai da suka dirar mata lokaci daya , hakoranta sai karo da junan su suke tsabar karkarwa,
a hankali ruwan ya fara tsagaitawa bayan kwashe kimanin awa daya da kusan rabi ana tsugawa , sai iska me karfi da matsannancin sanyi ne yake busawo tare da sauran feshin ruwan saman .
*************
  *MARAƊi Niger République*
Jihar maraÉ—i itace cibiyar kasuwanci a kasar Niger wacce Allah ya albarkace ta da masana'antu , masu kudi, da ma'aikata sanan kuma tana daya daga cikin garuruwa na kudancin Niger karkashin manyan garuruwan kasar hausa kuma ta kasance karkasin mulkin katsina shiyasa ma ake mata lakabi da katsinar maradi domin katsina ta mulke ta tun lokacin yakin kasar hausa kuma hasalima yanzu idan za a kira sarautar maraÉ—i sai ance sarkin katsinar maraÉ—i.
Kenan zamu iya cewa maraɗawa katsinawa , tun asali Maraɗi tayi yake yake sosai a kasar hausa inda taci nasarar wasu garuruwa wasu kuma su ka bata kashi amma dai tarihi ya nuna bamaraɗe jarumi ne kuma baya tsoro wanan shi yasa ta bunƙasa har zuwan turawan mulkin malaka a kasar hausa inda suka sha gwagwarmaya da turawa a wancan locakin ,a zamani sarkin katsinar maradi tsakanin shekara ta 1892 zuwa 1894 .
Bayan jihadin sheik usmanu fodio inda ya yaki sarakunan kasar hausa ya kuma jaddada addinin islama a wanan nahiyar ya kuma canza sarakuna da dama musaman wadanda suka bijirewa kaidodin sa maradi ta shiga cikin jerin kasashe da wanan abu ya ritsa da su
Kuma tasamu sarakuna 23 Tun daga kan Sarkin katsinar maradi Dan kassawa 1817, 1830
Har izuwa kan na yanzu .
Wannan kenan
Cikin Tafkeken falon wanda yake É—auke da kayan ado da alatu , irin wanda ake samun su kaÉ—ai gidan sarakai ,cikin masarautu irin namu na gargajiya ,
Mutane biyu ne cikin falon Mutumin da kallo daya za'a yi masa a hango girman cikar kamalar sa ,kasaitar sa da mulkin da ke gare shi yana zaune kan É—unÉ—umemiyar kujerar da take ware daga tsakiyar falon tana fuskantar duk me shigowa cikin falon .
Gefe da gefen kujerar ƴan kananun teɓurin gilas ne dayan teburin saman sa ɗauke yake da ƴaƴan itatuwa nunannu lafiyayyu tun daga kan inabi,ruman ,zaitun,tuffa,tanjari, da sauran manyan ƴaƴan itatuwa masu daraja , ɗayan teburin kuwa ɗauke yake da wata kyakkyawar butar shayi da take kan wani babban farantin da suka zo tare ruwan zaiba tare da kananun kofunan ta da chokulan da daga gani du tare suka zo ,
Daga kasa kuma tsakanin kewayen manya-manyan kujerun da suka yiwa tafkeken falon ado , wani dogon saurayi ne wanda bayan sa kawai za'a kalla a gane tsawo da cikar halittar sa ta ɗa namiji kansa a sunkuye ,kafafun sa a tanƙwashe yayi zaman raƙumma gaban wannan mutumin yana sauraran duk wasu kalamomi da suke fitowa daga bakin sa ɗaya bayan ɗaya , da yake cewa ,
YOUSSOUFA na samu sakon bukatar da Ka zo da shi ,sai dai ina bukatar jin ƙarin bayani daga gare ka ,? Cikin kwantar da murya wanda aka kira da youssoufa ya ce ranka ya dade kamar yadda na fada wa jakadiya , wani aiki ne ya taso daga gwamnatin kasar nan wanda ta zabi sojoji kimanin dubu ɗaya da ɗari biyar, ta kuma wakiltani a matsayin shugaban su da zan jagorance su zuwa kai tallafin gaggawa ga yankin makociyar mu kasar Nigeria akan ƴan tawayen nan na boko haram da suka addabi yankin arewacin kasar wadda idan muka yi wasarere mu ma annobar tana iya shafar kasar mu nan Niger saboda boda da makoftakar da muke da juna ta kurkusa ,ya ɗan tsagaita gami da ɗaga kai ya kai kallon sa ga fuskar mutumin da ya zuba masa ido yake saurarar sa da dukkan hankalin sa.
Sake sunkui da kai yayi gami da cigaba da cewa shine nake neman alfarma akan a ɗaga biki zuwa lokacin da zan dawo wanda nake tunanin ba zai gaza nan da shekara ɗaya ba , do Allah ayi mini alfarma mai Martaba ,"ya karasa furta hakan cikin marairaicewa da kwantar da murya " ?
Ɗan gyaran murya yayi kafin yace ,wagga lamari naka da ban mamaki ike kai youssoufa anya aikin taimakon ƙasa zai wucce raya sunnah ?  ɗan jim yayi ɗaga bisani yace tashi kaje du shawarar da muka yanke tana iso maka ta hannun jakadiya ,
Ras-ras yaji zuciyar sa ta tsinke tun da Mai Martaba yace sai yayi shawara yasan bai gamsu ba bai amince da alfarmar da ya nema ba hakan yana nufin bazai amince masa ya tai zuwa nigeria wanda kuma hakan yake dai-dai da rasa aikin sa da tun da yayi wayo a duniya ya san soja ya kasance bashi da wani burin da ya wuce ya zama SOJA , duk da kasancewar sa ɗan sarki kuma BIYAMARADI , haka ya dunga kawar da duk wasu kalubalen da zasu shiga tsakanin sa da cikar burin sa ya shaa gwagwarmayar da ta kawo sa kan matsayin da yake na yanzu me amsa cikakken sunan COLÓNEL YOUSSOUF ABDOUL AZIZOU BASKORE !!!!!!!....
[6/24, 9:49 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association
*MAFARI.......* ( _HARGITSIN RAYUWA_ )
       *Umm'muaz*
2
Cikin sanyin jiki tare da rashin kuzari yake takawa yana wuce zauruka da sashi sashi kamar yadda aka San tsarin ginin masarauta yake.
Jerun gwanon bayin sa su rai biyar suna biye da shi tun daga ƙofar fada inda ya amsa kiran Mai martaba , tafe yake cikin kasaitar da ta amshi tsarin zubin sa na ingarman namiji dogo da ya kere dukkanin mutanen da suke tare da shi tsawo a lokacin.
fuskarnan tasa a murtuke kitib ya fito a SOJAN sa sak kuma BIYAMARADI, baya ko amsa gaisuwar bayin da suke ta faman zubewa a ƙasa suna kai gaisuwar su tare da kirarin da suka saba yi masa.
Biyamaradi dan sarki mai jiran kujerar mulkin kassar mu
albarka, kayi gadon mai martaba. Biyamaradi jarumin jarumai, biyamaradi namijin, ayi yau ayi gobe sai gaskiya jibi rago ya kassa.
Dan sarki mai makaman yaki, Dan sarki mai ado.
Biyamaradi kai zaki ne mai watsar da taron maza Dan sarki mai tarin illimi to kayi ga arabi ga boko wallahi ka kure tunanin Masu tunani.
Allah.ya kare ka gwani na hattara biyamaradi. hattara biyamaradi. Hattara biyamaradi HATTARA BIYAMARADIÂ
Sai dai ga Biyamaradi yousoufa a yanzu sam basa burge shi basa sanya shi nishaɗi , babu abun da yake sanya shi nishaɗi a yanzu irin karar kafafuwan sojojin da suke jaan tunga su ƙame masa idan sun hango shi , babu muryoyin da suke burge shi irin na amsawar sojojin da ke karkashin ikon sa idan ya basu umarni ,
Dai-dai ya zo shiga sashin sa da yake bangare guda ko kuwa ɗaula guda a cikin gidan nasu ya ga wani hadimin sa ,wanda yana karasowa wajen ya zube ƙasa yana ƙirari tare da kai gaisuwar sa , bayin da suke tsaye a bayan sa su suka amsa da " Biyamaradi ya amsa gaisuwar ka meke tahe da kai ? " yana daga durkushe yake isar da sakon dalilin tsayuwar sa anan "jakadiya" ce tace ya zo ya jira shigowar yarima ya koma ya sanar da ita .
yana jin abin da bawan nan ya faÉ—i ya sanya kansa gaba gaÉ—i ya shiga gidan sa tare da yi wa bayin alama na kadda su biyo bayan sa , ( domin shi ya tsani taron bayun nan da suke zuwa du su zagaye shi su hana shi sakat ko wanne motsi yayi idanun su na kai suna yi masa surutun banza"kirari" a cewar sa)
babu wanda ya motsa daga inda yake cikin bayun nan domin idan da sabo yaci ace sun saba da tsarin halayyar BIYAMARADI"
Yousoufa shine É—a na biyar a wurin mai martaba É—a na huÉ—u a wurin mahaifiyar sa , kuma É—a namiji na farko a gidan baki É—aya , mahaifiyar sa É—iya ce ga sarkin birnin gaoure, ita ce Æ´a ta biyu cikin jerin Æ´aÆ´an mai martaba LamiÉ—o " Bafullatana ce gaba da baya kamar yadda kowa yasan birnin gaoure garin hullanin usul ne ,
Mahaifiyar yousoufa da mai martaba(sarkin maraɗi ) auren so da kauna suka yi , tun lokacin mai martaba bai kai ga hawa kujerar mulkin birnin maraɗi ba suka haɗu a wurin bikin yaye ɗalibai ƴan makarantar gaba da primary ta makarantar "École Bedir" da ke birnin Niamey a wancen zamanin da sai ƴaƴan wane-da-wane ke yin makarantar ,kanwar mai martaba " Zainab tana cikin ɗaliban da aka yaye a wannan shekarar ta alif dubu ɗaya da ɗari tara da saba'in da tara 1979, "wanda shi mai martaba Abdoul azizou ya wakilci mahaifin su wajen taron a lokacin shi ɗalibi ne a jami'ar Abdoul Moumouni Diof da ke nan cikin birnin Niamey"
Anan yaga safiyya , tana ɗaƴa daga cikin ƴan matan da aka zaɓa domin su gudanar da ƴar kwarya-kwaryar wasan koikoyo da akan yi lokacin bikin yaye ɗalibai , kallo ɗaya yayi wa ƴar fulanin yaji ta kwanta masa ya kuma ji cewar ya samu matar aure ,
Bai yi ƙasa a gwaiwa ba ya sanarwa zainab tare da gwada mata yarinyar daga nesa lokacin da aka kammala taron ana shirin watsewa nan take kuwa zainab ta shaida ta domin ta san safiyyah farin sani hasalima tamkar kanwar ta take domin koh lokacin da aka kawo safiyyah ajin farko a makarantar ita kuma tana aji na uku a lokacin ɗakin kwanan su guda su biyu ne rak a ɗakin kasancewar haka tsarin ɗakunan kwanan ɗalibai na makarantar yake, mutane bibbiyu ne a kowanne ɗaki , sun shekara guda tare cikin aminci har zuwa lokacin da ita zainab ta shiga ajin manyan ƴan secondry "aji huɗu" a lokacin ne aka sauya mata ɗaki ta koma saman bene a hawa na farko ,
Hakan ne yasa koh da yayan ta ya nuna ra'ayin sa akan safiyyah taji dadi sosai kuma ta wuce masa gaba ta gabatar da shi a wurin safiyyah duk da cewa dai ita a lokacin ne ma take aji na huÉ—u , Amma tayi na'am tare da maraba da bamarÉ—e Abdoul azezu .
Haka dai tafiya sannu-sannu suna tare cikin aminci da so da ƙaunar junan su har zuwa lokacin da safiyyah ta kammala karatun gaba da primary a shekarar mai martaba sarki Youssoufa Baskore mahaifin "Abdoul azizou ƴa tura da takardar neman aure da kayan nagani ina so ga masarautar sarki lamiɗo na barnin gaoure inda shima bai yi kasa a gwaiwa ba ya amsa cikin tsantsar farin ciki da lamarin "domin a garesu hakan babbar nasara ce kasantuwar kowa ya san sarautar maraɗi ita ce ta biyu a karfin mulki kaf kasar niger "
Aka tsaida ranar auren su sha biyar ga watan satumber na shekarar alif dubu É—aya da É—ari tara da tamanin da É—aya "15-sept-19981, rana ta zo aka sha biki amarya ta tare a gidan mijin ta sasahi guda a cikin gidan sarautar maraÉ—i .
Kwance tashi rayuwar su ta fara miƙawa cikin aminci fahimtar juna da tsantsar ƙaunar junan su , Allah ya Albarkace su da haihuwar ɗiya mace shekara ɗaya da auren su wacce ta ci sunan marigayiya mahaifiyar su Abdoul-azizou wacce ta jima da rasuwa tun su na yara ,"Halimatu'sa'adiyyah" ana kiran ta "Ammi"
Tsakani shekara biyu cif da safiyyah ta sake haihuwar É—iya mace aka sanya mata sunan mahaifiyar safiyyah "Suwaiba" ana kiran ta "dada "
Bayan watanni tara da haihuwar "dada "
safiyyah ta sake samun ciki ta haifo "zainab" wacce ta ci sunan kanwar Abdoul-azizou sai ake kiran ta "ubbo"
Tun daga nan fa sai mai martaba sarki Youssoufa ya ce Abdoul-azizou sai ya sake aure koh ya samu magaji tun da ga alama matar sa uwar Æ´an mata ce , babu yadda Abdoul-azizou bai yi ba akan ya fahimtar da mai martaba haihuwa kyautar Allah ce babu É—iya mace koh É—a namiji dukkaninnsu É—aya ne har kullum masu albarka ake nema .
Sai dai fir mai martaba yaki saurarar sa domin a gefe guda "hajiya uwa " da takasance matar sarki ta biyu "wacce take matsayin babbar matar sarki tun bayan rasuwar mahaifiyar su Abdoul-azizou " a lokacin ta samu wuri sai daÉ—a hura wutar kiyayyar É—iyoyi matan da ake haihuwa a gidan abdoul-azezu take " a cewar ta sarauta ta kama hanyar barin hannun Baskore tunda ga alamu Sarautar tana dakatawa ne akan Abdoul-azizou da yake a matsayin yarima a lokacin ,
Ba tare da neman shawarar Abdoul-azizou ba mai martaba ya nema masa Auren Æ´ar abokin sa kuma yayan matar sa "Hajiya uwa "Babban Limamin MaraÉ—i "Malam muhammadou" wacce ake kira "Saratu " .
Tare da sa hannun hajiya uwa wacce tayi ɗare-ɗare akan harkar bikin nan tayi uwa tayi makarɓiya , ranta ƙwal ! tana ƙitsimawa "idan sarauta ta kuskure masu ta wani wuri kasancewar ita bata taɓa haihuwa ba toh tabbas ga sarautar nan dawo masu ta wani hannu " tana da tabbacin daga saratu ta zo ta haifi ɗa namji shikenan sarauta ta zamto tasu.
Saratu ita ce ɗiya ta shiddah cikin jerin ƴaƴan Liman muhamdou , mahaifiyar ta tun tana ƴar shekaru biyu suka rabu da mahaifin ta "mahaifiyar ta ƴar Nigeria ce a can wani gari da ake kira zuru a ƙasar kebbi Nigeria , Saratu ta taso tsakanƙanin matan uba , babu irin izaya da wahalar da ba'a gana mata ba , shi ya sa ta tashi a kangare sannan me mummunar zuciyar da take cike da ƙudirin ɗaukar fansa,
Lokacin da ta shekara goma sha biyar ta kasance fanɗararriyar yarinya ce ta kin ƙarawa wacce tun da ta fara girma ta buwayi matan mahaifin nata da fitsara da raini uwa uba saratu ta kasance me matukar fasahar iya shirya zancen ƙarya da tuggu domin ta tada husuma a tsakanin matan mahaifin ta duk a cikin mummunan ƙudirin ta na ɗaukar fansa .
A take -take zata haɗa zantukan ƙarya ta ɗora mutum kome girman sa akai kuma ya hau ya zauna daram , saboda tsabar yadda ta iya shirin ƙarya , wasa-wasa sai da ta maida gidan mahaifin ta sansanin yaki a wurin matan gidan , kullum cikin faɗa ake kamar garken karnuka , ita kuwa ta koma gefe tana wake-waken ta ,bayan idanun su ta shiga ɗaki ta ci dariya son ran ta ta fito tsakar gida tana karya wuya tare da bai wa wacce ta zuga hakuri .(Saratu kenan , ƴar malam wacce taƙi halin malam )
A tsakanin matan mahaifinta su uku babu wacce ta kai ga fahimtar hallayar saratu na karya da munafurci "sakamakon rashin haÉ—in kan su tare da zazzafan kishin su tun asali " sai shi mahaifin nata ne da kan sa ya fahimci "saratu ita ce matsalar gidan sa " yana tunanin yadda zai iyi ya samu ya kawar da ita daga gidan sa "( ya aurar da ita ) .
Sai ga sakon kira daga mai martaba "Liman bai yi ƙasa a gwaiwa ba "ya amsa kiran da ya sanya shi kwanan farin ciki bibbiyu na farko dai farin cikin zai zama surikin yariman maraɗi a yanzu , kuma surikin sarkin maraɗi a gobe idan da rai , uwa uba zai rabu da annobar da ta ke sanya shi fargabar shigar sa gidan sa a kullum,
Dan haka cikin rawar jiki da murnar sa da ta kasa boyuwa ya amsawa mai martaba sarki youssoufa , ya bawa yarima Abdoul azizou auren Saratu koh gobe ake so a É—aura ya shirya ,
cikin farin ciki da karamci da aka nuna masa Sarki youssoufa ya tsayar da ranar É—aurin auren Abdoul azizou da saratu ranar ishirin da biyar ga watan sha biyu shekara ta alif dubu daya da É—ari tara da tamanin da biyar 25-Dec-1985 .
A daren ranar ya aika aka kira masa yarima abdoul azizou , in da ya sanar da shi hukuncin da ya yanke tare da bashi umarnin ya shirya gobe da Maraice ya je su ga juna shi da saratu É—iyar liman domin kwanaki ishirin da É—aya kachal suka rage a É—aura musu aure ,
Ba tare da yarima Abdoul azizou yana fahimtar sauran kalaman bakin mai martaba ba ya amsa masa gami da yi masa godiya da sallama ya fito daga turakar mai martaban zuciyar sa cike da zogi da raÉ—aÉ—in bacin ran tashin hankalin da yake iya hango samuwar sa tsakanin sa da abar son sa "safiyyah "
Tabbas shi yasan yadda safiyyah take tsananin kaunar sa da kishin sa , yasan duk lokacin da ya je mata da labarin auren da aka riga aka nema masa ya kuma zama dole a gareshi ya amsa hannu bibbiyu , kasantuwar bai taɓa musantawa mahaifin sa ba akan duk wani hukunci da ya yanke a rayuwar sa domin shi mutum ne me ilmin addini sosai , yayi karatu sosai arabi da boko ya san irin haƙoƙin da iyaye suke da shi akan ƴa ƴan su hakan ya sa ya kasance ɗa mai tsananin biyayyah ga iyayen sa .
Dan haka a yanzu ma yayi aniyar karban auren da za'a yi masa da hannun aminci duk da cewa shi ba son auren yake ba asalima bai taba kawowa ransa sake yin aure nan kurkusa ba kamar yadda tun da yake bai taɓa son wata ɗiya mace irin son da yake yi wa safiyar sa ba kuma baya jin zai sake son wata ƴa mace irin son da yake yi mata " ya ajiye auren da za'a yi masa a karo na biyu a mizanin kaddara "
Sai dai babbar matsalar sa a yanzu tunanin hanyar da zai bi ya tunkari saffiyah da batun karin auren sa ,"a daren yau din domin baya son ma lamarin ya kwana ba tare da ya fitar mata da hakkin ta ya sanar mata ba a matsayin ta na matar sa da suke zaman aminci , kaunar juna da fahimtar juna " sai dai ya san mata idan aka zo batun kishiya ba dama ne '
Haka dai ya shiga gidan nasa baya sun natsa ya fuskance ta da maganar auren , sai dai ga mamakin sa ,' bata tayar da hankalin ta irin yadda yake zato ba hakan kuwa yana da nasaba da zancen ya riga shi isowa zuwa kunnuwan ta "
Abun nufi ta ji zance a cikin gida " abun ka da gidan sarauta da kuma yadda ya kasance hajiya uwa tana ta yamiÉ—iÉ—i da zance tana yada magana tare da fiffikar ta ta zata shigo gidan " da farko bata fahimci zancen ba sai da ta tambayi jakadiyar sarki ta wancen zamanin ita ce ta warware mata zare da abawa ta kuma kwantar mata da hankali tare da bata shawarwarin alkhairi da za su taimaka mata.
Amma duk da haka bayan dawowar ta sashin ta yini tayi tana kuka tare da tunanin ƙalubalen da yake fuskanto ta "abu ɗaya ne ya rage mata jin zafi ji da tayi matar da za'a aurawa mijin nata ba ƴar wani babban sarki bace ko kuwa wani hamshaƙin attajirin da kasa ta san da shi ba "
Ƴar Limamin Maraɗi ce hakan sosai ya rage mata zafi kasancewar safiyyah irin ƴaƴan sarautan nan ce masu ji da kan su da nuna isa sosai jinin sarauta na ƙasaita , da iko suke yawo a jikin ta ta yadda take ganin duk wani wanda ba ɗan sarautar da ya kai ya kawo ba a matsayin kasasshe a wurin ta,
safiyyah tana son sarauta tana alfahari da sarauta tana kuma ƙaunar masu sarauta , bata daukar mutanen da basu da sarauta da wani muhimmanci a rayuwar ta .
Dan haka koh lokacin da ranar da aka yanke na ɗaurin auren Abdoul-azizou da saratu ya zo , aka kuma ɗaura auren cikin kwanciyar hankali tare da bakukuwa kamar yadda yake a al'adar su , sam safiyyah bata bayyana matsanancin tashin hankalin ta ba duk kuwa da cewar abun yana nuƙurkusar ta a karkashin rai !Saboda yadda take kaunar mijin ta sai ga shi a yanzu ya zama nasu ita da wacce take ganin bata kai matsayin ta haɗa kafaɗa da ita akan abun da take so ba .
Hakan ya sa bayan tarewar Saratu "a sashin ta da aka gina mata daura da sashin Safiyyah ta hannun hagu "Sam safiyyar bata shiga harkar Saratu "A ganin ta saratu bata isa tayi gogayya da ita ba " "iyakaci idan sun haÉ—u a cikin gida 'idan sun je gaishe da hajiya uwa da sauran matan mai martaba biyu "Hajiya mai karamin É—aki da umma Amarya " " su gaisa da juna sama-sama, sosai ita saratu take jin zafin yadda safiyyah ta tattara ta tare da shirgin ta ta watsar a gefe take nuna kamar bata san ma da zaman ta a cikin gidan ba , "
Hakan yana kona ran ta , domin ita ta shigo gidan ne da nufin ta dunga bi ta ƙasa-ƙasa irin yadda ta saba ( a gidan mahaifin ta) tana tunzura safiyyah tana tada bala'i a tsakanin ta da Abdoul-azizu har dai tayi nasarar dusashe karfin soyayyar da ta lura Abdoul-azizu na yi wa safiyyah ,ta yadda ya kasance idan suna tare koyaushe bakin sa cikin ambaton Alkhairin safiyyah da kyawawan halayenta tare da yabawa safiyyar yake ,"
Sai dai bata samu damar hakan ba domin duk wata kafar da zata bata damar aiwatar da mummunan nufin ta safiyyah ta toshe "ta hana ta fuska "
A cikin hakan ta fara laulayin ciki bayan watanni biyu da auren su "wanda kuma kusan tare suka É—au cikin da safiyyah " domin ita ma tana É—auke da É—an tayin cikin ta na wata É—aya " .
Nan fa Saratu ta samu abun yin lanɓo ,kitifiri da feleƙe , ita a dole ga mai juna biyu " cikin yana wata uku su ka fasa Sanarwar ai Malamar jinya a asibitin da take zuwa awo a wancen zamanin ta tabbatar mata da cewa "Ɗa" namiji zata haifa '
Sanarwar ta fito ne ta bakin "Ɗan Zagii" a karkashin jagorancin "Hajiya uwa "wacce ita ma saratu ce ta yi mata Albishir tare da tabbatar mata da abun da malamar jinyan ta faɗi gaskiya ne "cikin rashin sanin Hajiya uwa cewa zancen ƙarya ce tsagoronta wacce ita Saratu ita ta haɗa zancen ta sakamakon jin wata matar babban likita da suka haɗu da ita wurin awu tana bada labarin injin awun da yake bayyana jinsin jariri tun yana cikin mahaifiyar sa " ( Asalima a wancen zamanin injin yin awun da ke gano jinsin halitar da yake ciki bai riga ya bazu a kasashen africa ba )
Nan take zance ya kewaya fada har ya isa kunne mai martaba ta bakin jakadiya " sosai mai martaba yayi farin ciki tare da bada goron Albishir me yawan gaske"
A bangaren Yarima Abdoul azizu shima yayi matuƙar farin ciki da wannan albishir har ma ya gaza boyewa ya bayyana farin cikin sa a sarari gaban idanun safiyyah tare da nuna ɗokin sa akan samun ɗa namiji da zai yi nan ba da daɗewa ba "wanda hakan ya tashi hankalin safiyyah a karon farko tun bayan auren sa da saratu "Amma sai ta share ta taya shi murna a sarari "duk da cewa cikin ran ta taso a ce ita ta haifo magajin maraɗi saboda kaunar ta da sarauta ",
Sai dai kasancewar ta ƴar sarauta ta kasance me iya boye hakiƙanin cikin ta, ya sa ba wanda ya fahimci halin da zuciyar ta ke ciki , hatta Saratu wacce take yin duk wani kilbibin ta da biyu 'dan ta turawa safiyyah haushi " ta gaza ganin bacin ran safiyyar .
cikin watannin girman cikin kafin zuwan ranar haihuwar sa kaf an gama tanadin kayan jarirai na É—a namiji wanda wasu ma mai martaba da kan sa ya sayo su a tafiyar sa Umrah , tarairaya da kulawa kuwa babu irin wacce Saratu bata samu tun daga kan surukan ta hajiya uwa da sauran matan mai martaba "da kusan suke karkashin ikon hajiya uwa "har zuwa kan shi kan sa mai martaba, da uban gayya yarima Abdoul-azizu wanda shima zuwa lokacin zuciyar sa sosai ta rinjaya ga son haihuwar É—a namiji sakamakon "janye hankalin sa ta siyasa da hajiya uwa da saratu suke yi "
Wanda har hakan ya soma taɓa amintaccen zaman su na fahimtar juna da su ke shi da safiyyah.
Ranar biyu ga watan ɗaya na shekarar alif dubu ɗaya da dari tara da tamanin da bakwai ,2-jan-1987 Saratu ta wuni tana naƙuda taci wahala sosai , kafin zuwa maraice ta haifo Santaleliyar ɗiyar ta mai kama da ita sak "
An É—auki tsawon mintoci uku a É—akin haihuwar da yake cikin baban asibitin maraÉ—i bayan bayyanuwar kukan jaririyar da likitocin da suka karbi haihuwar suka tabbatar wa hajiya uwa wacce take tsaye a dai-dai kan saratu tana ta faman jera mata sannu , cewar Saratu É—iya mace ta haifa har ma suka É—ago Santaleliyar jaririyar da ba'a ce yanzu aka haife ta ba saboda girman ta suka nuna wa hajiya uwa da saratu, shiru ne ya ratsa tsakani kafin Muryar hajiya uwa ta bayyana Cikin cewa".
Saratu kika ce Malamin jinya ya tabbatar miki Ɗa namiji ne a cikin ki ? watau ashe zancen ba haka bane ? ashe dai zance Altine "yayar saratun da suke uba ɗaya " zancen ta gaskiya ne da take cewa ke Saratu ba ƙaramar maƙaryaciyar yarinya bace " ,
Amma ban yi zaton karyar taki da yauɗarar ki ta kai har haka ba , da har domin rashin hankali zaki yi irin wannan ƙasurgumar karyar da yaudarar a gidan sarauta, toh Maza sai ki tanadi ruwan wanke kan ki a idanun mai martaba da shi kan sa mijin naki , ki kuma tabbatar kin riga kin gama zubda ƙimar ki a idanun mutanen gidan nan ciki kuwa har da bayun da suke karkashin ki , haba saratu me ake da wannan irin karyar taki "
Saratu dai babu bakin magana sai sharar ƙwalla take "wanda hakan ya jaa hankalin malaman jinyar da suke gyara ta har ta kai su ga tambayar dalilin kukan ta "hajiya uwa" ta faɗe musu biri har wutsiya akan yaudarar da saratu tayi mata da kunyar da ta jefe ta " Malaman jinyar su da kan su sun ga rashin kyautawa, tare da mamaki irin karyar saratu sai dai sun bada tabbacin akwai irin na'urar a kasashen da suka cigaba ,"sai dai koh na'urar ma ba koyaushe take bada bayanin gaskiya ba"( Sanin gaibu sai Allah ) jin hakan ya sa "Hajiya uwa jin wani farin ciki ko ba kome sun samu hanyar da zasu fidda , kan su "
Haka aka gama gyara ta tare da jariryar aka tura su É—akin da zasu zauna "a lokacin ba'a sallamar mace daga haihuwar ta har sai ta zauna a asibiti kwanaki biyu zuwa uku domin tabbatar da karfin jikin ta "
Bayan isar su É—akin hutun kafin jama'ah su zo "Hajiya uwa ta sanar da Saratu shawarar da ta gama yankewa domin samun rufin asirin su ,nan take yanke "ba tare da jaa ba" Saratu ta amince .
Da zuwan yarima Abdoul-azizu "hajiya uwa ta sanar masa da É—iya mace aka haifa ba É—a namiji ba ta kuma É—ora da bayanin da malaman jinyan nan suka yi musu na cewa ana iya samun kuskuren inji wurin bayyanuwar jinsin abun da ke cikin mahaifiyar sa "
Ƙwarai yarima abdoul azizu yayi kokari wurin nuna rashin damuwar sa akan kuskuren na'urar da ya riga ya yadda akan cewa an samu " Amma cikin ran sa sam sam lamarin bai mar daɗi ba sun riga sun ƙwaɗaitar dashi son haihuwar ɗa namijin .
Bayan isar labarin haihuwar saratu "Fada " tare da sabon sauyin da aka samu daga haihuwar É—a namiji da ake sa ran haihuwar sa zuwa samun labarin haihuwar É—iya mace , Fada ta shiga Alhini da har hakan ya gaza boyuwa akan fuskar mai martaba ,
Haka aka yi bikin suna cikin rashin Armashi bayan dawowar su daga asibitin "inda yarinya taci sunan "hajiya uwa Asma'u " Sau É—aya mai martaba ya sa aka kai masa yarinyar turakar sa "a washegarin dawowar su daga asibiti" in da yayi mata huÉ—uba tare da bata suna " tun daga ranar bai sake waiwayar su ba.
Ga bangaren safiyyah har ila yau dai bata bayyana wani alama ba ta bangaren ta ,na farin ciki koh saɓanin sa akan sauyin jinsin abun da Saratu ta samu . Ita ma tana fama da nata cikin , da yayi wani irin mugun girma fiye da sauran cikin ta guda uku na baya , hakan ya sa da zainab ta zo bikin sunan ɗiyar Saratu "ta nemi da ta ɗauki Zainab "ubbo"(takwarar ta )
Kasancewar tun da aka mata aure a lokacin shekarun auren ta bakwai bata taɓa samun haihuwa ba "sai bari da take ta faman yi " ganin yadda cikin yayi wa safiyyah nawi ga kuma rigamar zainab wacce ba ta kai ga cika shekaru biyu ba a lokacin "sannan gata da jarabar ƙiuya bata yadda da tarin bayu da suke cike da bangaren nasu da ma gidan baki ɗaya "sai jikin uwar ta , ya sa ta nemi tafiya da ita nan take kuwa safiyyah da Abdoul azizu suka bata zainab ɗin ta tafi da ita "
Ranar goma ga watan biyu na shekarar alif dubu ɗaya da ɗari tara da tamanin da bakwai 10-feb-1987 ita ce Ranar da ta zamto ranar farin ciki ranar da baza'a manta da ita ba a tarihin masarautar maraɗi ranar da ta shiga jeru ranakun tarihi, Ranar da aka wayi gari gimbiyyah safiyyah tana nakuɗa , zuwa hantsi ta haihu lafiya " farin ciki ne ya wanzu akan fuskar gimbiya safiyyah a lokacin da malaman jinƴar da suka karbi haihuwar ta su ke tabbatar mata da ta samun Ɗan ta namiji 'Ƙato da shi jazir ya ɗauko hasken fatar ta irin ta fulanin usul yayin da tun kallon farko da tayi masa bayan da "malaman jinyan suka gama wanke mata shi tare da shirya shi cikin kayan jarirai" tana yi masa kallo guda ta hango tsantsar kamannin sa da kakan sa"mai martaba sarki youssoufa " kamar an tsaga kara , kakaf cikin ƴaƴan da ake haihuwa a gidan babu wanda yayi kama da Mai martaba irin wannan jaririn "Cikin nutsuwa ta dunga kwararo masa addu'ar kariya kamar yadda take jin matsananciyar kaunar sa tana kwarara cikin zuciyar ta da wani al'amari mai girma irin wada bata taɓa jin sa akan sauran ƴaƴan ta ba"cikin nutsuwa ta ɗaga shi dai-dai fuskar ta gami da sumbatar goshin sa , da kuncin sa dama da hagu,
Dai-Dai lokacin da yarima Abdoul azizu ya karaso ɗakin , farin cikin zuciyar sa ya kasa boyuwa daga zuci har zahiri bakin sa ya gaza daina furta kalmomin godiya ga ubangijin sa , ba tare da lura da wurin da suke ba ya haɗa su baki ɗaya ya rungume su , zuciyar sa tana buɗewa tare da sabuwar ƙaunar uwar da ɗan ta ,
Biki sosai aka dunga yi tare da yanke-yanke ana sadaka domin nuna farin cikin wannan haihuwar , har zuwa ranar da takasance ranar raÉ—in suna , É—aruruwan mutane suka hallarci wurin bikin raÉ—in sunan inda yaro yaci sunan "mai martaba "Youssoufa"
A nan wurin kuma mai martaba ya Sa aka yi shela akan bai amince ba a boyewa yaro sunan sa "laƙani " a kira yaro da sunan sa Yarima Youssoufa Abdoul-Azizou Baskore Sunan sa kenan .'''
Bayyana irin bacin rai da bakin cikin da hajiya uwa da saratu su ka shiga bai kwatantuwa "domin a ranar da labarin haihuwar ya iso musu kwana suka yi basu yi bacci ba suna jimami da taya junan su bakin ciki " Amma da yake dukkanin su sun ƙware a harkar kissa da kilbibi , sai suka shafe , hajiya uwa tayi ruwa tayi tsaki akan harkar mai jego da jaririn ta , tayi ƙabe ƙabe akan harkar kome , "ta nuna jika dai nasu ne "
Haka ita ma saratu take wuni a sashin safiyyah tana taya ta raino "a cewar ta " sosai ta sake a cikin jama'a ana ta hidima da ita "yayin da take nunawa mijin ta da ma ita safiyyar cewa youssoufa ita ma ɗan ta ne " (cikin rashin sanin su saratu da hajiya uwa suna nan ƙudurce da mummunan ƙudirin su da su kadai suka barwa kan su sanin sa , Sai kuma Allah wanda yake masanin kowa da kome )
kwance tashi youssoufa yana girma har zuwa lokacin da ya cika shekaru biyu a lokacin ne babban rashi ya samu birnin maraÉ—i , in da mai martaba sarkin youssoufa ya amsa kiran mahaliccin sa bayan Æ´ar gajeruwar jinya ,
haka aka gudanar da zaman makoki cikin alhinin rashin wannan adalin sarki nasu , bayan an share makoki akayi bikin naɗi inda "Yarima Abdoul azizou ya ɗare kujerar mulki "ya zama sarki " a kuma tsukin kwanakin Saratu ta sake haihuwa inda ta sake samun ɗiyar ta mace "wacce taci sunan mahaifiyar ta Maryam" bayan watanni biyu safiyyah ita ma ta ƙara haihuwar ɗan ta namiji ,"da aka sanya masa sunan lamiɗo "
Lokacin da Biyamaradi youssoufa ya cika shekaru biyar da watanni a lokacin ne wani babban rashin ya sake samuwa , Allah ya yiwa zainab kanwar mai martaba rasuwa a wurin haihuwa , ta mutu ta bar ƴar jaririyar ta da ta haifa wacce koh samun damar ganin fuskar ta bata yi ba mai rabawa ta raba " bayan share zaman makoki An samu saɓanin ra'ayi akan wacce zata yi rikon jaririyar zainab da ta ci sunan kakar ta ta wurin uba "siyama " A karshe an tsaida shawarar "safiyyah ita zata yi rikon siyama tare da jaririn ta da ta haifa kwanaki arba'in da suka wuce "Aminu " a dalilin sanin da kowa yayi cewar akwai aminci tare da ƙauna mai karfi a tsakanim marigayiya zainab da kuma safiyyah " domin tun ranar da akayi rasuwar ma jaririyar take karkashin kulawar safiyyah ita take kula da ita ,"take shayar da ita maɗarar da aka tanada domin jarirai sabuwar haihuwa "
Dan haka aka miƙa rikon siyama ga safiyyah tare da mayar mata da ƴar ta hannun ta zainab karama "ubbo" wacce a lokacin take da shekaru bakwai tana aji biyu na primary amma sosai ta shaƙu da uwar goyon ta , babar ta ,kuma takwarar ta marigayiya zainab a saboda rikon gaskiya soyayyah da amana da tayi mata " hakan ya sa ta ɗauki son duniya ta ɗora akan wannan jaririyar da take yi wa kallon ƙaramar kanwar ta take kuma son ta fiye da kannen ta da suka fito ciki guda "
Cike da ƙauna da tsaftataciyar soƴayyah safiyyah ta karbi riƙon siyama "gefe guda na zuciyar ta kuma ɗauke da wani babban burin da take fatan kasancewar sa , wanda ta riga ta ayyana shi akan jaririyar da aka bata amanar ta "
Bayan maryam ita ma saratu ta sake haihuwar É—iyar ta mace "da ta amsa sunan hauwa"u " , kuma ita ce aka yi goyon su tare da su siyama da aminu "
Zuwa lokacin saratu kakaf ta gama bin gidajen bokaye da Æ´an bori akan su taimaka mata ta samu haihuwar É—a namiji "wanda ita ma zata É—aga tace wannan É—an ta ne namiji amma shiru ake ji "wai malam ya ci shirwa " akan cikin 'hauwa'u babu irin tsubbace tsubbacen da basu yi ba ita da hajiya uwa wacce har zuwa lokacin bata saduda ba .
A gefe É—aya suna nan suna shirin kaddamar da mummunan aikinsu ,
kwanci tashi yara suna girma Arzikin iyayen su yana sake bunƙasa ,cigaba da wayewa yana sake yawaita , sauye-sauye suna samuwa , yanayi yana juyawa ,
*2005*
yanayin ya juya ta inda ya mayar da kananun yaran nan wasu matan aure wasu kuma samari " inda Æ´aÆ´an sarki Abdoul azezou Baskore suka cika su Goma sha biyar cif-cif , siyama da ita ma take amsa sunan É—iyar gidan ta cikace su suka zama su goma sha shiddah cif cif "safiyyah tana da takwas ,HuÉ—u maza huÉ—u mata "Saratu tana da bakwai shiddah mata É—aya namiji ' , An rufe haihuwar da É—iya mace kamar yadda aka buÉ—e ta da diya macen ,"
Biyamaradi yousoufa tun tasowar sa mutum ne miskilin gaske marar son hayaniya "yana da tsananin tausayi ko ma ace rauni akan mata da yara kanana " , baya shiga harkar kowa a gidan babu me ganin fara'ar sa idan aka ɗauke iyayen sa , sai kuma abokin sa , kuma Aminin sa Tafeedah da ya kasance ɗan uwan sa domin da mai martaba da mahaifin tafeedah da yakasance me riƙe da sarautar ɗan malikin maraɗi , ƴa ƴan wa da kani ne uwa ɗaya uba ɗaya .
Tun tashin su tare suka tashi tamkar ƴan tagwaye ance sai hali ya zo ɗaya ake abota toh abotar Biyamaradi yousoufa da tafeedah ta ƙaryarta hakan domin idan aka ɗauke ra'ayin su da yazo ɗaya akan karatu da aikin da suka yi haɗakar ra'ayi akan sa ,"watau aikin ɗamara " da ya kasance su dukkanin su sojoji ne sai dai shi tafeedah sojan sama ne , saɓanin yarima yousoufa da yake sojan ƙasa .
Bayan hakan kowannen su halayen sa saɓani da na ɗan uwan sa ne , inda Tafeedah ya kasance mutum me barkwanci , surutu da saukin kai, saɓanin yarima yousoufa , hakan ya sa suke yawan samun saɓani akan halayyar juna in da kowannen su yake ƙalubalantar ɗan uwan sa , a ganin yousoufa tafeedah ya cika sakarci da sakewa mutane , yayin da shi kuma tafeedah yake ganin yousoufa a matsayin bauɗaɗɗen mutum miskili marar dadin sha'ani ,
A tsakanin su ɗaya ya kasa sauyawa ɗaya halayyar sa kamar yadda saɓanin halayyar su sam-sam bata taɓa karfin aminci da abotar su ba ,tun suna yaran su har yanzu da suke kan shekarun girma ,basu da abokan da su ka wuce junan su , duk wasu shawarwarin su tare suke yi , sun san sirrin junan su daɗi da rashin daɗi basa rabuwa duk inda dare yayi idan har suna cikin gari ɗaya ,"aiki bai tura ɗayan su wata jahar koh wata ƙasar ba "toh dare yana yi ka gansu tare koh dai a sashin biyamaradi yousoufa koh kuwa a sashin tafeedah da shima yake bangare guda a gidan su da yake baya kaɗan daga shiyar gidan sarki " sosai abotar su me tsafta ce irin wacce take wuyar samu a wannan zamani "
Bayan Tafeedah babu wanda Biyamaradi yousoufa yake so da ƙaunar gani irin karamar kanwar su A'isha wacce ake kira "meram" kasancewar ta (meramar sarki) .
ƙwarai Biyamaradi yousoufa yake kaunar meram duk da cewa kanwar sa ce da suke uba ɗaya , domin meram ita ce ƙaramar ɗiya ga hajiya mama ( Saratu ) a cikin ƴaƴan gidan mata ita ce karama , A'isha"meram" yarinya ce ƴar kimanin shekaru sha uku a yanzu tana aji na uku a makarantar gaba da primary .
Aisha irin yaran nan ne da gatan da suke da shi bai sa sun lalace da rashin tarbiyyah ba , ta samu tarbiyya sosai a wurin uwar goyon ta "Safiyyah" uwa ga Biyamaradi yousoufa , hajiya umma "kamar yadda ƴaƴan ta suke kiran ta" ita ta ɗauki Aisha tun daga yaye wanda hakan yana da nasaba da ƙaunar da ta ga ɗan ta mafi soyuwa agare ta yana yi wa kanwar ta sa da tun daga lokacin da aka haife ta ya ƙyalla ido ya ganta ,Allah ya dasa masa kaunar ta ciki ran sa fiye da duk sauran ƴan uwan sa ciki har da waɗan da suke ciki ɗaya da shi da su .
Lokacin yana matakin farko a jami'ah ai kuwa ya mayar da sashin mama wurin yada zangon sa a duk lokacin da ya dawo daga ɗaukar darasi haka zai kwace aisha daga hannun masu rainon ta yayi ta faman hidima da ita, hakan sam baya yi wa hajiya umma daɗi ganin yadda ɗan ta ya tare a sashin da a da kafin haihuwar aisha sai yayi shekara ma bai taka kafar sa bakin sashin ba " hankalin ta ya tashi akan sanin da tayi cewa garin su baya jiƙuwa a ƙoƙo ɗaya tare da saratu"hajiya mama "
Baza ta iya hana yousoufa zuwa sashin hajiya mama kai tsaye ba kasancewar ta san shi kaifi ɗaya ne ,miskilin gaske da ba'a iya sauya masa ra'ayi ta daɗi , hakan ya sa ta bi hanyoyin da take ganin zasu taimaka mata ta dakatar da ɗan ta daga shiga sashin hajiya mama domin tana gudun ta janye mata ɗa tsaf "sanin halayyar saratu "(hajiya mama) " da tayi na tsantsar kissa da siyasa tare da hilatar mutum ya so ta a dole karshe kuma ta cuce sa "macijin sari ka noƙe ce " ( cikin rashin sanin hajiya umma aikin gama ya riga ya jima da gamawa )
Dan haka tayi mata shigar sauri ta bi duk hanyoyin da take da damar bi ya haɗu kuma da ita ke jaan ragamar gidan ta ɗauke Aisha can-cak daga wurin mahaifiyar ta a lokacin tana shekaru biyu a duniya ta dawo sashin ta baki ɗaya , ai kuwa murna gurin yousoufa ba'a cewa kome " yayin da hakan da tayi ya baƙan ta ran hajiya mama sosai amma sai ta boye bacin ran ta. (sanin da tayi ta riga ta gama rarake ƙasan hajiya mama )
Cigaban labari .
Yana shiga tamfatsetsen (palourde-parlour )falon nasa ko kafin ya karasa zama akan É—aya daga cikin kyawawan fararen kujerun da suka sake haskaka falon wayar sa da take cikin aljihun sa ta hau ruri .
Ciro wayar yayi daga cikin aljihunn sa tare da tsira mata ido tamkar me nazarin ta ,har sai da ta kusan tsinkewa tukun ya É—aga gami da yin sallama ya É—ora da faÉ—in "Comment vas-tu aujourd'hui princesse"?
Daga dayan bangaren aka amsa cikin wata narkakkiyar murya " je vais bien Mon amour comment va le travail"?
Ya amsa da Alhamdulillah daga haka suka ci gaba da hirar da ake yin ta cike taf da kasaita daga dukkanin bangarorin biyu da shi da wacce ga alamu budurwar sa ce .
Idan ɗaya ya furta kalma sai an biyo bayan wasu ƴan ƙananun daƙikai (seconde -seconds) kafin " ɗayan ya bada amsa , inda daga baya ma ya koma budurwar ita ke jaan ragamar hirar, shi daga yayi murmushi sai yace eh ko a ah.
Har dai zuwa lokacin da ya sako mata zancen tafiyar sa akan aikin sa har na tsawon lokacin da yake zaton zai iya kaiwa shekara .
Nan take ta katse shi tun ma kafin ya karasa yi mata bayani cikin tashin hankali take tambayar sa akan ina lamarin bikin auren su ya kwana ? Wanda ake sa ran zuwan ranar da aka yanke nan da Æ´an wasu watannin da suke gaza da uku "lokacin da zata kammala karatun ta" ?
Cikin jin haushin tarar numfashin sa da tayi wanda yake ganin kaf duniya yana iya kirga mutanen da suka isa yi masa haka ,yace ke dakata MAIMOUNA lamarin ayki matsayin shi ya wouce douk yadda kike tounani don haka ki ajiye komi a guefe har sai bayan na cimma matsaya bisa aykina.
Ko kafin ya gama bayani budurwar da aka kira da maimouna ta fara shishiƙar kuka gama bayanin sa yazo daidai da fashewa da kukan ta bata ko kuma saurarar sa ba ta kashe wayar ta ,
Ta barshi riƙe da kan waya a kunne , ɗan jim yayi yana son fahimtar abun da ya sanya ta kuka cikin kalmomin da ya furta ,?
Rashin gano dalilin ya sa shi ɗaga kafaɗun sa biyu cikin nuna alamar rashin damuwa ya miƙe tare da nufar daya daga cikin fankama-fankaman ɗakunan da suke cikin falon nasa yana shiga ɗaki ya nufi ƙaton window ɗakin gami da buɗe sa a take ƙamshi damina da wata sassayan iskar maraice da ta fi ta ac da yake ɗakin dadi ,ni'ima da sanya nishaɗi ta buso zuwa cikin dakin .
Rage kayan jikin sa yayi tare da nufar bayi da alamun wanka yake da niyyar yi ,sai dai wayar sa da ya ajiye gefen gado ta É—an jaa hankalin sa sakamakon hasken da tayi ,É—an guntun murmushi yayi ganin sunan princesse da alamar sako a fuskar wayar ,ba tare da ya É—au wayar ba ya faÉ—a bayi domin yin wanka.
Yana kammala shirin sa ya fito falo jikin sa sanye da uniforme riga da wondo me dabbare-dabbaren kore , ruwan kunkumadi, ruwan madara, da kuma jaa Wanda ko ba'a faÉ—i ba za'a san kakin soja ne .( Tenue Saharienne ).
Da sallama ɗauke akan harcen sa ya sanya kai cikin katafaren Palourdes (falon) mahaifiyar sa wanda yake kama da ɗakin taro "hall" dakatawa yayi daga gefe ya sunkuya tare da kwance igiyoyin jikin takalman sa da suke ɗaure gam-gam da kafar sa har kusan ƙwarin sa ,
Wucewa yayi niyyar yi (zuwa ciki wurin umma ) bayan ya amsa gaisuwar jakadiya wacce ya tarar tana zaune daga gefe a cikin palourn amma sai jakadiyar ta dakatar shi cikin cewa "Ranka ya dade biyamaradi " yanzu kuwa nake shirin zuwa sashin naka "ta furta hakan tana me satar kallon bayu uku da suke ta faman goge-goge da ƙwal-ƙwale cikin palourn daga can geufe ( umartar su tayi da su kauce su basu wuri ).
Gyara tsayuwar sa yayi bayan ya kammala sauraron bayanin bakin jakadiyar , sannan ba tare da ya nuna wata alama! Akan fuskar sa ba ya ce "madallah da ke jakadiyar sarki zan kuma yi taka tsan-tsan tare da sanya ido sosai domin gano gaskiyar wannan zancen da kika zo min da shi , "bayyanuwar wani abu wanda ya sha banban da wanda kika sanar da ni a yanzu " zai iƴa jawo hukunci me tsanani a gare ki dai-dai da yadda doka da shari'a ta tanadar ga masu yin ƙage da sharri , wanda kin riga kin san haka .
Daga haka ya juya ya fara tattaki domin nufar wurin mahaifiyar sa "cikin zuciyar sa kuwa cike taf da bakin ciki da baci rai ! Akan labarin da jakadiya ta zo masa da shi game da É—an uwan sa muhamadou .'mamman"
Muhamadou shine É—a na huÉ—u a É—akin hajiya mama "kuma shine É—an ta É—aya tal namiji .
******************
Dai-Dai ya sanya kan shi cikin ɗan madaidaicin wurin "da yafi kama da dakin hutawa " ita ma ta kawo kai kiris ya rage su ci gware cikin sauri ta ɗago kai da niyyar buɗe baki amma ganin wanda yake tsaye a gaban ta ya sanya a take ta diririce "tare da yin ƙasa da sauri ta kai gwiwowin ta ƙasa cikin ƴar siririyar murya tace "ina kwana hamma youssouf " , kallon ta yayi na daƙikan da suke gaza da biyar ya ɗauke kansa tare da sake yin kicin-kicin da fuska daga bisani ya wuce yana me amsawa ciki-ciki da lafiya lau " bayan sa ta bi da sassayan kallo daga bisani ta miƙe daga durƙusan da tayi tana me kakkabe gefe da gefen fara sol ɗin rigar da take ɗore bisa kan kayan ta , gyara zaman farin gilashin idanun ta tayi " da saboda firgitar da tayi kiris ya rage ya subuto daga kan siririn karan hancin ta ",
Cikin sassarfar yake taku fuskar sa ɗauke da yalwataccen murmushi da yake bayyana ƙatuwar wushiryar da take tsakanin fararen hakoran sa na sama" har ya ƙarasa gefen dardumar da farar dattijuwar take zaune hannun ta riƙe da wani ɗan ƙaramin littafin addini tana dubawa "zama yayi tare da miƙa hannun sa ya kamo nata hannayen da suke ciƙe da awarwarayen zinare da suke ta faman haske idanun me kallon su , ɗaga hannuwan nata yayi dai-dai fuskar sa ya sumbancin bayan hannuwan nata ɗaya-bayan-daya kafin ya sarƙafe dogayen ƴan ƴatsun sa cikin nata yatsun da suke ƙawace da adon jaan ɓakin lalle da yake ta faman sheƙi tare da tashin sassanyan kamshi "
Fuskar ta ɗauke da tattausan murmushi take bin duk wani motsin sa da ƙwarar idanun ta zuciyar ta fal! Cike da ƙaunar gudan jinin zuciyar ta
"ina kwana ummana kin tashi lafiya ? Yaya fama da jama" ? Allah ya ƙara miki nisan kwana da hakuri da mu umma " cikin murmushi take shafar baƙar kwantatciyar sumar kan sa tana me amsa addu'ar sa da Ameen kafin ta ɗora da tambayar lafiyar sa shima sannan ta ƙara da tambayar sa yayi karin kumallo ? Ƴar dariya yayi sannan "yace umma na makara sai naje officie zan sha café " tana shirin yin magana ta sake shigowa palourdes (falo ) " Bakin ta ɗauke da ƴar siririyar sallama "Budurwar da suka kusan yin karo da biyamaradi ce "
Tare da kulawa hajiya umma take kallon ta kafin ta ce yaya kuma kika dawo SIYAMA ? Ke da kike ta mitar kin yi latti , 'cikin inda-inda tare da satar kallon biyamaradi da ya ciro wayar sa yake dannawa "da alama kira yake shirin yi " tace "umm daman umma kamar nayi mantuwa ne , cikin sauri ta juya gami da nufar wata Æ´ar kofar da take tsakankanin kofofi huÉ—un da suke cikin wurin "bayan ta hajiya umma tabi da kallo cikin ran ta kuwa tausayi-kauna gami da soyayyar siyama ce taf take kai kawo"
Tana shiga ta tura kofar gami da dafe kirjin ta bayan ta jinginu da jikin ƙyauren kofar " a hankali ta juya tare da zamewa ta durƙusa gami da sanya fuskar ta a dai-dai saitin ramin ɗan mukullin kofar , nan take idon ta ya ƙƴallo mata fuskar sa yana hirar sa da mahaifiyar sa hankalin sa kwance in da yake sanar mata da zancen tafiyar sa a cikin kwanaki uku masu zuwa "idan mai martaba ya amince" ɗan jim hajiya umma tayi sannan ta ɗora da cewa wai kou yarona (bata kiran sunan sa saboda sunan surikin ta ne ) shi tahia bisa aykin ba'a iya yin sa ne tare da amre "abun nuhi bai yuwuwa mutun ya tai tare da iyalin sa " ? ...
[6/24, 9:49 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association
*MAFARI .........*
( _HARGITSIN RAYUWA_ )
*Umm'muaz*
3
Gyara zama Biyamaradi yayi kafin yace " A zahiri ummana ba wai ba'a tahia akan hidimar aiki tare da iyali bane sam-sam sai dai duba da irin wurin da zan tai ba kasa ta bace ba ,kuma zan tai ne domin kwantar da tarzoma sannan zan jagoranci mutane sama da dubu É—aya ne ,ni ne shugaba gare su ina bukatar tattara hankalina kachokam na É—ora bisa aykina tare da kula da mutanen da suke karkashi na "
Numfasawa yayi daga bisani ya ɗora da cewa kuma"ummana ki yi duba da irin ita Maimuna ɗiyan sarki ce wacce du inda zata ta zauna sai tare da bayun ta masu yi mata hidima , shin ya kamata daga amren mu na douke ta zuwa wata ƙasa a bakin ayki na wurin da babu tabbacin zata samu irin gatan da take samu a gidan su da kuma wanda zata iya samu da ace anan ta zauna da auren mu ? Ummana a duba lamarin nan da kyau ,?
Sauke numfashi "hajiya umma" tayi duk zance ɗan nata gaskiya ne aykin sa me tattare da hatsarin rasa rai ne , ayki ne na sadaukarwa ga ƙasar sa ,shi ya sanya tun farko bata so ba youssof ya zaɓi da ya zama soja , so tayi yayi ta karatu me zurfi har ya zama alkali ta yadda du ranar da ya zama shi ne bisa gadon sarauta mulki ba zai taɓa yi masa wahalar gudanarwa ba ,
Sai dai duba da yadda shi youssof ya ɗage ya tsaya kai da fata kan ra'ayin sa , ya sanya daga karshe ita da mai martaba suka tsaya masa wurin ganin cikar burin sa bayan kammala karatun jami'ar da ita ma da rarrashi da ban baki youssof yayi "domin da farko so yayi yana kammala karatun gaba da primary ya fada makarantar horar da sojoji " sai dai mai martaba yayi masa jaan ido sosai sannan ya yadda yayi karatun jami'a inda ya karanci fannin sociologue" yana fitowa kuwa ya miƙa takaddun sa ga neman shiga soja , nan take kuwa aka ɗauke sa "kasancewar sa ɗan manya"
cike da so da kaunar aikin sa gami da nuna tsantsar ƙwazo ya fara aykin wanda hakan ya jawo nan take ya fara taka matakan nasara hawa hawa , sau biyu ana sawa da shi a cikin zaɓaɓɓun sojijin da ake turawa kwantar da tarzoma a kasashen ƙetere "kasar Somalia da Libya " cikin ikon Allah kuwa duk tawagar da yake jagoranta lafiya suke dawowa cike kuma da tarin nasarori " hakan ya bashi ɗaukaka a cikin ƙanƙanin lokaci har ta kawo sa ga matsayin da yake kai a yanzu wanda a karo na uku sai ga shi an sake tura shi ƙasar Nigeria domin yaƙi da ƴan tawayen Boko haram "
Cikin yanayi marar daɗi yake kallon fuskar mahaifiyar sa wacce da alama tayi nisa cikin tunani "shi ya san daga mai martaba har umma basa son aikin sa "kuma da yana da iko tabbas da ya haƙura da aikin amma toh shi yaya zai yi ne shi ya tabbatar haka Allah ya halicci zuciyar sa da ƙaunar aikin soja "domin baya mantawa tun yana shekaru biyar yake ƙwalafaci tare da mararin ganin sa riƙe da bindiga sanye da kakin soja haka ya tashi ya tsinci kansa kullum wayewar gari da mafarkin ya zama soja "abun a jinin sa yake "
Muryar sa ce ta doki dodon kunnuwan ta tare da dawo da ita daga duniyar tunanin da ta lula "ummana a cigaba da yi mana addu'a kamar yadda aka saba da iznin Allah babu abun da zai faru da mu sai Alkhairi sannan shekara kamar kwana ce tamkar yau zaki ga É—an ki ya dawo , ya karashe zance yana dariyar tsokana ".
Ƴar dariya itama tayi kafin ta ce addu'a muna kan yin ta yarona kuma insha Allah zamu cigaba fatan mu Allah ya kiyaye tare da shiryar mana ku a duk inda kuke da sauran ƴaƴan musulmai baki ɗaya ,
to yaya ita É—iyar tawa da fatan ka sanar mata da batun tafiyar duk da cewa ma nasan idan har tafiyar takasance mai martaba da kansa zai tada É—an aike zuwa Birnin Agades É—in " ta É—ora da sake tambayar sa, yaya É—iyar tawa ta aminta dai kou batare da ta tayar da hankalin ta ba ?
Gimtse fuska biyamaradi youssof yayi kafin ya É—ora da mun gama magana kuma ta fahimta , cikin ransa ! Kuwa mamakin yadda wannan lamari zai tafi a haka karfi da yaji yana namiji umman sa ta dunga nunawa da lalle ne ya yi abun da maimouna take so ,
Sau tari hakan ya sha faruwa hatta akan tsarin ginin gidan sa da aka yi duniya guda daga can Babban filin da yake karshe a cikin masarautar maimouna ita ta zaɓi irin ginin da take so kuma irin sa sak aka yi , ya rasa gano dalilin haka ,
Shi shine namiji shine shugaba tayaya za'a dunga gwada masa sai abun da matar da zai aura ta zaɓa shi zai yi ?
Miƙewa yayi yana me duba agogon hannun sa cikin sauri yake yi wa umma sallama "Ummana ni zan wuce ina ga yau zan iya kaiwa cikin dare kafin dawowa ta sabadda yau zamu fara zuwa bakin bodar da ta haɗa mu da Nigeria domin duba irin tsaron da za'a fara ajiyewa ta wurin" ,
Bin sa da ido hajiya umma take "tana lure sarai da sauyin da aka samu akan fuskar sa tun da ta ambaci sunan maimouna "cike da so ta fara kwarara masa addu'a tare da sake jaddada masa ya kula da kan sa sosai , har zuwa lokacin da ya karasa ficewa daga wurin da take ",
Sauke ajiyar zuciya tayi a lokacin da ya bacewa ganin ta ,lokaci daya ta ɗauke fuskar ta daga jikin bulin makullin kofar tare da miƙewa tsaye ta juyo fuskar ta wacce take " ɗauke da wani tattausan murmushin da a zahiri yake nuna zuciyar ta na cikin annashuwa " dan tsalle tayi tare da juyi kafin a hankali ta motsa laɓɓan ta cikin cewa " za'a ɗaga bikin auren hamma youssouf har zuwa nan da wata shekarar me zuwa ,' taku ta fara yi a hankali da ya dangana ta da jikin katafaren gadon da yake rufe ruf da kyakyawan labulen da iskar da take busowa daga jikin tagar ɗakin yake ɗan kaɗa shi a hankali " janye labulen tayi tare da zama a bakin gadon " ɗan rangwaɗa kan ta tayi cikin cewa "ɗaga ranar bikin hamma youssouf yana nuni da nasarar da na kan iya samu ,hakan yana iya yiwuwar samun wata sabuwar dama a gareni ".,
Lokaci ɗaya ta gimtse fuska domin tunowa da tayi da nisan da hamma youssouf ɗin zai yi mata wanda ya sanya ba shiri ta ji hawaye ya cika gurbin idanun ta ","hamma youssof zai tafi Nigeria har na tsawon shekara , zan rabu da ganin sa na adadin kwanaki ɗari uku da sittin " bazan iya ba " zuciyata zata iya samun matsala kafin cikar adadin kwanakin nan ya zama dole na samowa kai na mafita " ., zabura tayi jin ana ƙwanƙwasa mata kofa ,'
Cike da jin haushi ta ce "waye a nan ? Cikin ladabi hadimar da take durkushe ta bakin kofar tace '"Allah ya huci zuciyar uwargijiya ta sako ne daga " Babbar uwa (hajiya umma ) tace a sanar da ke lokaci yana tafiya " ., É—an jim tayi kafin ta amsa kina iya tafiya gani nan fitowa ., ki fito lafiya ranki ya dade,'
Miƙewa tayi tana me jin duk fitar ta yau ta fice mata daga kai "tana da tabbacin yau bata iya tsinana wani abun kirki a wurin aykin ta "saboda chakuɗuwar farin ciki tare da bakin ciki ! A lokaci guda cikin ran ta ,'
Sake ɗurkusawa tayi har ƙasa tana me daɗa yin sallama da hajiya umma wacce ta kafe ta da ido tana me yin nazarin ta ", har ta miƙe da shirin tafiya ta ji hajiya umma ta sake kiran ta "yaki nan ɗiya ta ', dawowa tayi tare da sake durkusawa ", babu dai wani abun da yake damun ki koh ?
Da murmushi ɗauke akan fuskar ta ta ɗago tana me kallon fuskar mariƙiya gareta matar da a da take mata ganin mahaifiya tun tasowar ta domin bata taɓa cin karo da wani abu wanda zai sanya ta kokonto akan zaman hajiya umma mahaifiyar ta ba ,' har sai da lokacin da ta shekara goma sha bakwai(ta kammala makarantar gaba da primary ) a lokacin ne hajiya umma ta shaida mata hakiƙanin gaskiyar matsayin ta a wurin ta "hakan kuma ya samo asali ne dalilin ƙin amincewa ta bi mahaifin ta na ainahi da tayi ," da ya nemi son tafiya da ita wurin sa tayi hutun kammala karatun gaba da primary da tayi ", yazo da buƙatar tafiya da ita gidan sa domin ta ga sauran ƴan uwan ta da ya haifa tare da matar da ya aura bayan rasuwar zainab ",
Sosai a ranar tayi kuka ,kukan maraicin ta kafin a hankali ta hakura ," ta bi mahaifin ta , ta kuwa ji daÉ—i sosai da wannan hutun da tayi tare da kannen ta da matar mahaifin ta da ta kasance matar kirki ,'
Sai dai tun bayan dawowar ta daga gida (daga wurin mahaifin ta ) ta tarar da hamma youssof shima ya dawo daga jami'a inda ya kammala karatun sa ,' Rana ɗaya ta tsinci yanayin ƙaunar da take masa a zuciyar ta tana sauya muhalli ,daga so irin na ƴan uwan taka zuwa wata irin zazzafar soyayyah ,' ta aure wanda take jin idan har bata mallaki hamma youssof a matsayin mijin auren ta ba zuciyar ta kan iya samun babban raunin da zai iya dangana ta da kushewar ta ",
Gyaran murya hajiya umma tayi bayan ta gama nazarin ta sosai ta ce "siyama ki kasance me tsananta addu'a a koyaushe akan dukkanin lamuran ki kin ji koh ? Gƴaɗa kai siyama tayi ,' to maza tashi ki je ɗiyar Albarka Allah ya tsare min ke ya dawo da ke lafiya ," cike da jin daɗi da wata irin kakkarfar soyayyar mariƙiyar ta siyama take amsawa da Ameen "umman mu" Alherin Allah ya isar miki umman mu" ,
Tsaf hajiya umma ta gama gano abun da yake nuƙurƙusar zuciyar ɗiyar ta siyama ,'domin tun ba yau ba dai take lure da duk wani motsin Siyama akan youssof ɗin ," a kuma bangare guda na zuciyar ta lamarin sosai yayi mata daɗi ganin yadda yayi kicibus da tsohuwar niyyar da ke kulle a cikin zuciyar ta akan siyama da youssof ɗin tana da tabbacin baza ta samu matsala daga bangaren siyama ba".
Damuwar ta akan youssof ɗin ne wanda tun farko ta lura youssof ɗin bai wani cika kula lamarin siyama ba tun suna yara "kusan ma za ta ce jinin sa bai ɗauki siyama ba domin tun suna yara kullum faɗan sa da yayar sa 'ubbo' akan siyama ne ,' yana dukan siyaman kasancewar ta yarinya me tsinannen rawar kai a lokacin kuruciyar ta ,"shi kuwa youssof mutum ne marar son hayaniya hakan yasa garin sa bai jiƙuwa ƙoƙo guda da na siyama 'nan take zai bige ta ' wanda hakan yake haɗa sa faɗa da yar tasa domin duk duniya idan aka ɗauke hajiya umma da mahaifin siyama na ukun su a ƙaunar siyama ubbo ce ,sam bata ƙaunar abun da zai taɓa siyama ,' sosai take gwadawa siyama soyaƴyah da gata fiye da ƴan uwan ta da suke ciki guda ma, ' har dai zuwa lokacin da ubbo tayi aure a birnin Niamey gidan ta shine wurin hutun siyama a duk lokacin da ta samu hutun makaranta ,har kuma yanzu da siyama ta kammala karatun ta a shekaru biyu da suka gabata daga Université médecine- medical school ( makarantar horar da likitoci ) in da ta karanci fannin likitar haƙora ( Dentiste-Dentist ) ta kuma fara aiki a asibitin gwamnatin tarayya ta ƙasa reshen jahar maraɗi watanni sha tara da suka wuce , siyamar bata da zancen da ya wuce wurin da zata rubuta hutu musamman ta je da ya wuce gidan addar ta ta ubbo ,wacce mijin ta a yanzu ɗan majalisar tarayyah ne na ƙasa baki ɗaya ,"
A lokacin da youssof ya zo tare da batun ya samu matar aure a shekarar da ta gabata "dai-dai lokacin da ita kuma take gaf da fiddo manufar ta na son haɗa youssof da siyama aure ta shaida ga mai martaba "wanda ta san zai fi kowa farin ciki da wannan lamarin sanin da tayi lokacin marigayiya zainab tana raye suna da kyakyawar mu'amala ita da mai martaba duk kuwa da cewa shi mai martaba ya girmewa kanwar ta sa da tazara sosai domin mutane uku ke tsakanin sa da marigayiya zainab " , sai dai kuma youssof ɗin ya riga ta tada maganar auren in da yazo da murnar sa yake sanar mata da samar mata da suruka da yayi,' tun a lokacin ta so ta rusa maganar ta kuma fiddo masa da ainahin nata ƙudirin na son haɗa su aure shi da siyama,'
Sai dai jin wacce ɗan nata yake da zummar aurowa a matsayin surukar ta ya sanya ta yin laƙwas "ba wata bace wacce youssof ɗin zai auro illah maimouna ɗiya ga mai martaba sarkin AGAƊES , Maimouna ita ce ɗiyar sarkin agades mace ɗaya tal 'ƴar da ta samu gata da kulawa irin na bada kwatance .' Maimouna kyakyawar yarinya "ƴar buzaye" wacce ake kwatancen kyaun ta har ta kai sunan ta da kyaun ta ya shiga jerin abun kwatance a bakin al'umma " haka za'a ji budurwa idan ta ƙure wanka da gayu za'a ji masoyan ta na kururutata " wance kin kou ga kan ki sai kace gimbiya maimouna '? " ko kuwa idan budurwa ta cika feleƙe da yanga dan ita ɗiyar masu akwai ce nan za'a ji ƴan adawar ta suna faɗin" yo ai mu munga gimbiya maimouna ma karshen gata dai kenan" a taƙaice dai gimbiya maimouna ɗiyar gata ce gaba da baƴa ,
Sanin duk wani wanda ya kwan ya tashi ne cikin ƙasar Niger ", Sarautar birnin Agades shi ke da suna har karfin mulki fiye da dukkanin sauran manyan masarautun gargajiya da ke ƙasar Niger , sanin hakan da hajiya umma da mai martaba sarkin maraɗi suka yi ya sanya nan take zuciyoyin su suka cika da farin ciki ganin ɗan su zai auro ɗiya mafi soyuwa ga Sarkin agades ", wanda sun san hakan ba ƙaramin babban nasara tare da samun sabuwar ɗaukaka gare su da ma jahar maraɗi baki ɗaya ba ne ,"
Nan take hajiya umma ta ajiye zancen auren siyama da youssof a gefe wanda a da take jiran kammaluwar karatun ita siyama sai ta tado maganar kuma a wancen lokacin siyamar ta riga ta kammala karatun tun watanni biyar da sun ka wuce ", jinkirin da aka samu na son ta sake tsananta addu'ar neman zaɓi ne sai kuwa ga shi jinkirin ya zama Alkhairin da ya sa dole ta ture maganar siyama gefe ba kuma domin ta hakura ta janye zancen baki ɗaya bane "sawun giwa ne ya take na rakumi "sannan cikin ranta tana maimaita ai youssof mijin mace huɗu ne ", da wannan ta ajiye batun gefe , tare da bayyana tsantsar farin cikin ta da batun maimouna ,
Cikin satin mai martaba sarkin Maraɗi Abdoul-azizou Baskore ya tura da takardar neman aure ga sarki Usoumanu Ibrahim tounouss na birnin Agades , koh da sakon ya isa ga Mai martaba sarkin Agades shima ya bayyana farin cikin sa bayan da yaji ta bakin ɗiyan sa , in da ta tabbatar masa da amincewar ta tare da sake jaddada yawan ƙaunar ta ga biyamaradi youssofa, anan take mai martaba sarkin Agades ya bada tukuici mai yawa tare da takaddar jaddada amincewar sa ,"
Bayan dawowar ƴan aike daga birnin Agades a daren mai martaba sarkin Maraɗi ya gana da hajiya umma inda yake sanar da ita tayi magana ga ɗiyar ta siyama cewa a tare za'a haɗa bikin ta da na youssof dan haka ta tsaida guda cikin masoyan ta ," Anan hajiya umma bata yi ƙouron baki ba ta sanar da mai martaba haƙiƙanin shirin zuciyar ta tun daga farko ',
Ɗan jim mai martaba yayi bayan kammala jin dukkanin kalaman uwargidan sa ," sosai yaji daɗin kyakkyawar niyyar ta sai dai yadda ta ture Al'amarin bayan bayyanuwar maimouna ya sanya shi jin wani iri tamkar dai akwai sautin son kai cikin lamarin nata ," sai dai yayi saurin kauda zargin daga ransa akan sanin da yayi a duniya idan ana kirga masoyan siyama hajiya umma tana daga sahun farko ƙwarai yana alfahari da ita akan irin kyakyawan riƙon da tayi wa ƴar kanwar sa , " dan haka yace idan har ita siyama ta amince da shi youssof ɗin ya zama dole ga youssof ya auri siyama a matsayin matar sa ta biyu shekara guda bayan auren sa da maimouna idan Allah ya yadda ",
Nan take maɗaukakin farin ciki ya bayyana akan fuskar hajiya umma ,' tana mai sake jaddada masa da ƙaunar da ita siyama ta lura tana yi wa youssof ɗin tun shekarun baya ," nan dai mai martaba ya tsaida batun auren siyama da youssof sai dai ya nemi hajiya umma da ta bar batun nan a tsakanin su ,"saboda gujewa ƴan kai-kawo ', .
*Mairambiri Borno Nigeria*
Hasken ranan da ta ɗago ta fara ɗan zafi ita ta sanya ta fara motsi , kafin ta buɗe dogayen manyan idanun ta da suke farare tas tas , da sauri ta miƙe daga kwanciyar da take a cikin taɓon da ya cakuɗe da ruwan da ya kwanta a cikin ƙonanne ɗakin nasu wanda wuta ta riga ta ƙona azaran saman ɗakin ," da sauri ta fara lalube gefe-da-gefen ta , jin bata ji almun mutum a ɗakin ba ya sa ta miƙe tsaye ta fara laluben hanyar fita tare da kiran sunan ƴar uwar ta "yakaka "yakaka " santsi ne ya kwashe ta suuu ta tafi ta faɗi dabas a bakin kofar ," bayan ta ya bada ƙara ƙaƙas , " wani kuka ne ya taho mata a lokacin da wani mugun tsoro ya ɗarsu a ranta koh dai ƴan tawayen boko haram sun dawo ne jiya ? Sun tafi da yakaka ," tunanin hakan ya sa taji wani karfi ya zo mata ta yunƙura da karfin ta ," ta miƙe ta fara tafiya a cikin ruwan da ya cika tsakar gidan nasu da ƙasa bata kai ga shanye sa ba ',
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.