Complete Hausa Novels

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 9 of 21

Cigaba yayi da hirar sa cikin nishaɗi yana jin yadda albishirin da tayi masa yake ƙara masa kuzari , lalle maimartaba yayi masa attaque par surprise
 
    Fiye da mintoci ishirin suna hirar su sannan suka yi sallama ya aje wayar sa ,
   
   Bankwana yayi da hajja wacce har lokacin tana kitchen goye da mama tana girka musu ɗan abinda zasu ci kafin kwanciyar bacci ,
   
    Har ƙofa ta raka shi tana masa addu'a da godiya

    Inda yake sanar da ita gobe zai wuce garin su zai iya kaiwa sati biyu zuwa kwanaki ishirin idan ya tafi saboda haka zuwa goben su masa lissafin abubuwan da zasu iya buƙata baki ɗaya ,

    Bayan fitar sa ta kulle ƙofar ta dawo ciki zuciyar ta cike da wasi-wasi akan hirar da ta ji youssouf ɗin na yi da wata wacce bata kai ga sanin wacece ba , sai dai cikin hirar su da mafi yawa da faransanci shi youssouf ɗin yake bada amsa , ta fahimci mafi yawan maganganun nasa na soyayya ne saboda zaman da tayi a ƙasar kamaru , kurtun ɗan sanda ne mijin nata a bariki suka yi rayuwar su dan haka sosai take tsintar wasu kalmomin faransanci duk da dai shekaru ya sa ta manta yaren sosai !

A fahimtar ta youssouf yana da wata mace wacce yake tsanananin so da a kowanne lokaci zata iya cuso kan ta cikin rayuwar sa ta mallake shi wanda hakan yake babbar barazana ga rayuwar auren sa da yarinya falmata miskiniya ,

   Hodijan !

Kai tsaye É—akin da falmata ta shiga nan ta tasamma ,

  A zaune ta tarar da falmatan daga ƙasa a bakin ƙofar ɗakin ta takure ,

Kallon ta tayi ta ji tausayin ta ya tsirga mata , hakkun ta fara hango ƙalubale a rayuwar auren yarinyar da ko fahimtar kalmar auren ma ba ta kai ga yi ba ,

  mutuniyar kina zaune anan ne ??

da sauri falmata ta É—ago kan ta ,
  Hajja ya tafi ??  Mama tana hannun ki ?
   Eh ya tafi ga kuma mama a baya na , taso nan muyi wata magana kin ji ƙawalliye roman jaɓa !

******
Abuja Nigeria

Yakaka ta dage da neman ilmi tun ana koya mata haruffa ,A ,B,C,D , da kuma ا ب ،ت ،ث، sannu sannu ta haddace su tare da iya rubutun su , aka fara haɗa mata jimla , tana koyan rubutun su tare da sanin ma'anar su ,

ba ƙaramin daɗin koyar da yakaka malama maryam take ji ba saboda wankakkiyar ƙwaƙwalwa me saurin ɗauke abu da yakaka take da ita ,

A hankali ta fara lura da ƙarancin wayon da yake ga yakaka tare da gidadanci , sai tayi ƙoƙari tana gyara mata duk lokacin da ta ga tayi wani abunda bai kamata ba , tare da yawaita yi mata ƴan nasihu akan duk wasu manya da ƙananun zunubai .

Gefe guda lubna na ƙara zage damtse ita a dole sai yakaka ta iya English da arabic ta iya magana da yarukan kamar yadda ta iya , dan haka sai ta tsiri yiwa yakaka magana da English ko Arabic ta daina yawan yi mata magana da hausa koyaushe ,

ga bangaren yakaka ita ma ƙwarai ƙwarai take jin daɗin haɗuwar ta da malama maryam da ƴaƴan ta , domin sun ja ta a jiki suna kuma gwada mata ƙauna hatta mahaifin su da ba sosai ma suke haɗuwa ba , amma duk lokacin da suka haɗu yana amsa gaisuwar ta faram-faram babu nuna tsangwama ,

Dan haka gidan su nan ne wajen yinin ta idan babu makaranta , ranakun makarantar ma daga ta baro makarantar gida zata tayi sallah ta ci abinci ta sauya uniform ɗin ta , ta dawo gidan ta kama musu ƴan aikace aikace kafin malama maryam tayi sallah ta ɗan huta , zaman ta da samy baby sai ya ƙaranta ,

Ranar wata litinin an tashi da hazo sosai tare da sanyi mai tsanani tun safe , zuwa yamma sai hazon ya ƙaru sararin samaniya yayi jawur iska me ƙura tare da tsananin sanyi yana kaɗa jikin al'umma , kusan kowa sauri-sauri yake ya gama abunda yake a titi ya koma gida

Bayan tashin su yakaka a makaranta tare suka dawo da malama maryam ita ta wuce gida da zummar yin sallar la'asar ta ci abinci ta sauya kaya ta koma gidan malama maryam wacce ta sake jaddada mata kan lalle fa ta zo su yi darasi kar ganin yanayin garin ya sa ta ƙi zuwa , cikin ladabi ta amsa da
   To zan zo Anty !

Da sallama ta tura ƙofar falon samy baby tare da danna kan ta kai tsaye , abunda ta gani ya sa jakar hannun ta saɓulewa zuwa ƙasa ,
   Ɗaya daga cikin ƙawayen samy baby ne tare da saurayin ta suke yin masha'ar su nan kan kujerar falon babu kunyar ubangiji ko shakkar za'a iya shigowa agan su haka ,

Da sauri yakaka ta kawar da ganin ta daga kan su , tare da sunkuyawa ta É—au jakar ta da sauri ta wuce É—aki ba tare da ta sake kallon su ba tana jin yadda jikin ta baki É—aya ya É—au rawa da tasowar sabon yanayin da take ji cikin illahirin wata jijiyar jikin ta ,"

A kasalance ta gama kome hatta cin abincin ta da samy baby take ajiye mata shi a É—akin ta,

ta shiryo ta fito falon da fatan son sake ganin su , saboda ganin su na ɗazu da ya tayar mata da wani yanayi cikin jikin ta tare da bijiro mata da guguwar begen yarima da ta ɗan kwanta sakamakon mayar da hankalin ta da tayi kan karatu ,

sai dai ganin da ta yiwa waɗanan fasiƙan ya sa ta fara tuno da wasu abubuwa masu kamanceceniya da wanda ta ga suna aikatawa , da abunda ya shiga tsakanin ta da bature kam silum ,

ba ta tarar da su a falon ba , dan haka ta sanya ƙafafu ta bar gidan , tana tafe tana jin ƙewar bature kam silum na sake lulluɓar ta , ko yana ina yanzu ? Wataƙila ma ya manta da ita ! , ruwan hawaye ta ji suna taruwa a idanun ta ,daidai lokacin da take tura babbar ƙofar gidan su malama maryam ta shiga ,

   karaf suka ci karo da lubna wacce take ƙoƙarin fitowa daga gidan hannun ta riƙe da wata leda ,

Yauwa ƙawata Dan Allah zo ki raka ni wancan gidan ummi ta aike ni ,
   Tana mata nuni da wani babban gidan da yake chan kusa da ƙarshen layin su ,
   Ba musu ta bi bayan ta , lokacin da lubnan take jan hannun ta ,

   Saƙo lubna ta kaiwa matar gidan tana bata saƙon suka mata sallama suka yi fitowar su ,

Sun zo dai-dai tsakiyar harabar babban gidan , yakaka ta ga wani É—an dogon saurayi É—an gayu ya sha gaban lubna fuskar sa a marairaice idanun sa fes akan ta ,

   Lubna Haba dan Allah ki saurareni , yau wajen watanni bakwai kenan ina bin ki da soyayya ta amma kina min walakanci , dan Allah ki TAIMAKA MIN ki yadda da soyayya ta wallahi ina tsananin son ki ,

   Ba tare da lubna ta ɗaga ido ta dube shi ba ta kewaye shi ta wuce tana sake jan hannun yakaka ,

Charaf ! Ya riƙo hannun ta Lubna Dan Allah ki taimak....

  Wani irin ƙara lubna ta sa kamar ya jona mata wuta , ta warce hannun ta da matuƙar ƙarfi cikin abinda bai wuci daƙiƙai ba ta cire hannun ta ta wanke shi da mari , kafin cikin muryar ta da take karkarwar kuka ta tace
    Kar ka kuskura ka sake taɓa ni , ni ba ƴar iska karuwa ba ce ,

   Kukan da ya zo mata ya sa ta kasa ƙarass zancen ta da gudun gaske ta juya tana barin gidan ,
   Yakaka wacce take sakakai a tsaye ta bi shi da kallon tausayi a hankali ta furta kalmar
    Kayi hakuri
  Gƴaɗa mata kai yayi
Cikin sanyin jiki ta juya ta bar shi a wajen ta nufi gida ,

Tana shiga cikin gidan ta tarar da lubna rungume jikin mamar ta banda kuka babu abunda take , malama maryam sai tambayar ta take me ya same ta ? Me aka mata ? Ta gaza bata amsa ,

  Kallo mai bayyana haushi yakaka tayi mata lokacin da take zama a gefen malama maryam ,

Anty wai fa dan kawai wani mutum ya kama hannun ta yace ta taimaka masa yana son ta shine ta mare shi ta gudo gida tana wannan kukan ,
   Ta ƙarasa zancen muryar ta na nuna jin haushin abunda lubna tayi ,

    Waye ya kama hannun ta ? Wanne mutum ne , ke lubna ɗago ki dube ni waye ne ya riƙe miki hannu meye tsakanin ku da shi ? Ki faɗa min gaskiya ,
   cikin shisshiƙar kuka lubna tace ummi , Mukhtar ne ɗan gidan Alhaji Umar , shine tun watannin baya yake tare ni yana cewa wai yana so na , shine yau ya tare ni a gidan su har ya riƙe min hannu wai na taimake shi yana so na ,

    Nan take fushi mai tsanani ya bayyana a fuskar malama maryam , ta shiga yin faɗa meyasa tun ranar farko lubna bata sanar mata ba ? Ita kuma ta faɗawa baban su lubnar ya sami mahaifin yaron anyi musu tsakani ba ,
    Faɗa take yiwa lubna tamkar zata doke ta , a karshe ta gargaɗe kan ko kusa ta da shi bata yadda ta sake tsayawa ba kuma zata faɗawa baban su ya sanar da mahaifin yaron su ja kunnen ɗan su , ya fitar harkar ƴar su ,

  Sororo ! Yakaka tayi cikin jin mamakin malama maryam menene abun tashin hankali haka ?
  Da son kwantar mata da hankali tace ,

   Anty ai hannun ta fa kawai ya riƙe , kuma fa cewa yayi ta taimaka masa ,

wani irin kallo malama maryam tayi mata ,

   Yakaka ,

Namiji baligi ya kama hannun mace baliga haramun ne a musulunci , muddin ba muharamman juna suke ba domin tafarki ne na samar da ZINA a tsakanin mace da namiji  ,

Zina kuma haramun ce a musulunci, kuma tana daga cikin manyan laifuka wanda ake kira Kaba'ir.
Allah ya fada cikin Qur'ani
و لا تقرب الزنى
Wato kada a kusanci zina.
Hikimar fadin hakan shine ba aikata zina kadai ba, aikata abunda zai janyo zinar irinsu rungumar juna , taɓe-taɓen juna da shafe-shafen jikin juna tsakanin namiji da mace dukkansu Allah yayi hani domin hanya ce ta kusanta kai ga zina ,

cikin sanyin murya yakaka tace

Anty menene ZINA  ??

Zina ita ce Saduwa a tsakanin namiji da mace ,( ina nufin mace da namiji su kasance cikin abun rufuwa É—aya jikin su na cikin na juna , azzakarin namiji yana cikin farjin mace ) ba tare da hukuncin aure ya shiga tsakanin su ba , duk mace da namijin da suka yi tarayya irin haka ba tare da an É—aura musu aure kamar yadda addinin musulunci ya koyar ba to babu shakka sun aikata zina ,

kamar yadda na faÉ—a miki ita zina tana cikin manyan laifukan da Allah yayi hani da su sannan kuma ya tanadi hukunci ga duk waÉ—anda suka aikata ta ,

Hukuncin Zina a shari'ance ,  ita zina ba'a tabbatar wa da mutum ita dole sai da hujjoji, hujjoji guda biyu ne ko dai mutum ya yarda da kanshi ya aikata , ko kuma mutane huɗu su ganshi turmi da taɓarya a wannan hali ne ake tabbatar da zina,

Amma ko mutune uku ne suka ce sun ganshi turmi da taɓarya sai ɗaya yace shi dai ya gansu a tube suna shafe shafe to baza a karbi shaidun su ba, za'ai musu bulalar ƙazafi tamanin tamanin ,

Amma idan shaidu sun kammala ko mutum ya amsa da bakin sa yayi zina Hukuncin sa a shari'ance shine bulala É—ari ga waÉ—anda basu taba aure ba. Kamar Yadda Allah ya faÉ—a"

الزانية والزانى فاجلدا كل واحد منهما مأة جلدة، ولا تأخذكم بهما رأفة فى دين الله إن كنتم تؤمنون بالله واليوم الآخر.
Wato mazinaci da mazinaciya ayi wa kowanne su bulala É—ari, kada tausayi ya kama masu dukan idan har sun kasance masu imani da Allah da ranar lahira.

Sai wanda yayi aure akwai hadisin da yace duk mai aure ko wanda ya taɓa aure idan ya taɓa zina za'a jefe shi, amma sai idan shine da kanshi yazo yace yayi zina yana so a jefe shi, amma idan bai yadda a jefe shi ba ba za'ayi mishi dole ba za'a barshi ne.

Wani irin tsoro da tashin hankali me tsanani ne ya dirar mata , cikin wata irin muryar da ke bayyana tsantsar firgicin da ruhin ta ke ciki , tace

   Anty ko da mutum taimako yayi ,

Malama maryam cikin tsanaki tace ban fahimce ki ba yakaka wanne irin taimako ne yake zuwa ta hanyar aikata zina ??

Anty ina nufin ko shi namijin cewa yayi mace ta taimaka masa , sai ita ma ta taimaka masa , suka yi , shikenan tayi zina ??

Su dukan su sun aikata zina , saboda babu biyayya ko temakekeniya tsakanin bayin Allah wajen saɓa masa , su dukkanin su basu da hujjar kare kan su , suyi gaggawar tuba ga ubangiji domin zina babbar musiba ce ,

Sannan kuma yakaka ai duk namijin da zai cewa mace ta taimaka masa ta bashi kan ta suyi zina , ai wannan babban maƙiyi ne a gare ta , bata da maƙiyi sama da shi , mugu ne kuma macuci domin na farko zai ɓata tsakanin ta da ubangiji , yasa ta aikata abunda Allah zai yi fushi da ita , da zai hana ta samun ganin Alkhairi da dacewa cikin rayuwar ta duniya da lahira har sai idan ta tuba ,

Na biyu duk ranar da mutane suka san me suke aikatawa, mutanen kirki zasu guje ta , za'a dunga mata kallon fasiƙa, mazinaciya ƴar iska , karuwa .

Na uku idan ta hanyar zina da suka aikata ta samu ciki ta haihu , abun da ta haifa idan ya girma shi ma da kan sa zai tsane ta , ƙimar ta zata zube a idanun abunda ta haifa , saboda ta zamto sanadin da mutane zasu dunga ƙyamatar sa da ganin sa wani mutum da aka samar da shi ta haramtatciyar hanya ,

Bayan haka illolin zina suna da yawa , daga ciki akwai É—aukar munanan cututtuka da zasu iya kai me su ga mutuwa ,

A ƙarshe namijin da duk zai yi zina da mace abu ne me wuya ya aure ta , ko da ya aure ta kuma bazai taɓa ganin ƙimar ta da mutuncin ta ba , sannan ƙanƙanin kuskure zai iya haifar da zargi a tsakanin su da zai lalata musu aure ,

Kuma duk macen da tayi zina kafin tayi aure bata da wata martaba a idanun duk wani namijin da zai zo ya aure daga baya saboda ta rasa ƙima da mutuncin ta na ƴa mace tunda tayi zina .

Ki gujewa abunda duk zai kai ki ga aikata ZINA yakaka cikin ta akwai tarin masifu kin ji ko ??

Bata amsa ba illa miƙewar da tayi bata tsaya ba ta taka da gudun gaske tana barin gidan ba ta ko tsaya ta sanya takalman ta ba bare ta saurari ƙiran da malama maryam take mata ,

gudu take bata ko dub Inda take jefa ƙafar ta ,
   Da ƙarfi ta tura ƙofar ɗakin tana shiga ta zuɓe a tsakiyar ɗakin tana sakin wani irin kuka marar sauti da yake tuƙowa daga ƙasan ruhin ta ,

   Cikin wata irin murya ta fisgo kalmar ,

   ALLAH NA TUBA , NA TUBA ALLAH , BAZAN SAKE BA ,ALLAH NA TUBA KA YAFE MIN ,

  Kuka take tana maimaita kalmomin nan jikin ta har tsuma yake ,

Ashe haka ne girman laifin da ta aikata batare da ta sani ba ? Ashe ita É—in me tarin zunubi ce ? Ashe baza ta samu wani alkhairi ba arayuwar ta tunda tayi zina ,

Ta jima a zaune a wajen tana kuka har duhun dare ya shigo , zuciyar ta ta tsorata iyaka , neman yadda zata yi Allah ya yafe mata take yi , sai dai bata san yadda zata yi Allah ya karbi tuban ta ba , ji take kamar zata mutu ,

Tashi ta sake yi tana gama hanya saboda kukan da ta É—auki lokaci tana yi yasa kan ta sarawa tare da fara jin jiri ,

tana gama hanya ta fito , bata ko dubi ɗakin samy baɓy da kiɗa ke tasowa ta cikin sa alamun da ke nuna ta dawo gidan ba , ta sake fita ,

hanyar gidan malama maryam ta sake  ɗauka ,

  tana so ta san yadda zata yi Allah ya yafe mata , tana so ta san yadda zata yi ta gyara kuskuren ta ,

a falo ta tarar da malama maryam tare da iyalan ta suna cin abincin su na dare ,
   Babu sallama ta rakaɓe daga bakin ƙofar gami da sakin kuka me ciwo ,

hankali tashe malama maryam ta tsame hannun ta daga abincin da suke ci ta miƙe , ta zo ta kama yakaka ,
    Tambayar ta take lafiya ?meye ya same ta ? Ko wani abu ya samu antyn ta ? Daman yanzu take so idan ta gama cin abinci lubna ta raka ta gidan nasu ta duba ta domin ɗazu ta fita bata cikin nutsuwar ta yanzu kuma ta dawo tana kuka , shin menene yake damun ta ??  

   Cikin muryar ta da kuka ya fara disarwa , tace nayi ZINA malama maryam , ki taimake ni ki faɗa min yadda zan yi Allah ya yafe min , ban sani ba malama maryam wallahi ban sani ba ,

  Ta shi , ta shi mu shiga ɗaki ki nutsu ki min bayani yadda zan fahimce ki ,
   Ta kama hannun ta zuwa ɗaki ta zaunar ta bakin gado , ina sauraran ki me kike son faɗa min yakaka ?

Tiryan tiryan , yakaka ta fara bada labarin tun daga farkon haɗuwar ta da yarima har yanayin yadda abubuwa suka kasance har zuwa yadda alaƙar ta da samy baby da yadda ta yaudare ta ta zo da ita garin  abuja ta baro ɗanyar jaririyar ta tare da makauniyar ƙanwar ta,  bata idasa ba malama maryam ta katse ta ,

Kin yi kuskure yakaka , kin yi kuskure , kin yi kuskure ,! Kaicho  
    wani irin tausayi chakuɗe da bacin rai take ji cikin ran ta , tamkar wata makusanciya a gareta ce ta aikata abubuwan da yakaka ta aikata ,

tun farkon fara koyar da yarinyar ta fahimcin tana da raunin sani sosai da sosai game da addini , kusan ma bata san kome ba , shiyasa ta É—aura aniyar ganin ta kawo sauyi ta fidda ta daga duhun jahilci , cikin rashin sanin ta ashe jahilci tare da rashin wayon yarinyar har ya kai haka ( Bata san menene zina ba ) ? Ta yadda aka yi amfani da jihilcin aka cutar da ita cuta mai tsanani irin haka ?

Kukan da yakaka take ya tsansnta ganin shirun malama falmata ya É—au lokaci tare da bayyanuwar matsanancin tashin hankali bisa fuskar ta ,

  ALLAH zai yafe miki yakaka , muddin kika nemi yafiyar sa tare da niyyar baza ki sake komawa ga aikata saɓo irin wannan ba , ALLAH me yawan gafara ne ga bayin sa ,

Duk da cewa akwai bayanai daga malamai game da mutumin da ya aikata saɓon Allah alhalin bai san cewa sabon nan me girma bane da zai iya kai me shi ga shiga wuta ,ko kuwa bai ma san saɓo bane baki ɗaya, akwai hukunce hukunce , hukunci na farko shine , Shi JAHILCI ba'a uzuri da shi, sai dai cikin wannan hukuncin akwai bayanai da suke nuna akan karbi uzurin JAHILI , idan ya kasance gurin da ka tashi babu addini , babu malamai masu koyarwa ,ko kuwa an hana ka damar fita neman ilmin kuma ba'a koyar da kai ba a gida ,  to za'a iya yi maka uzuri da wannan , amma idan gurin da kake akwai addini akwai malumma , sai kaƙi fita ka nemi ilmi kasan hukunce hukuncen addini kayi zaman ka cikin jahilci to wannan baka da uzuri a addini , jahilcin ka ba uzuri bane ,

to amma idan ka rasa damar samun ilmi ne , akwai hadisin manzon Allah sallalahu alaihi wa sallam da yake cewa :
     Allah ya ƙetarar da Al'umma ta abu uku , ma'ana ya yi musu afuwa akan abu uku , na farko shine mutum yayi abu cikin rashin sani , na biyu mutumin da ya aikata wani kuskure akan mantuwa , sai na uku wanda aka tilasta ma sa aikata saɓo, !

To idan aka yi duba ga wannan hadisin za'a yiwa mutumin da duk ya aikata wani saɓo cikin rashin sani , uziri a sassauta masa , sannan shi kuma yayi tuba zuwa ga Allah , tsarkakaken tuba ,

Manzon Allah yana cewa : duk wanda yayi tuba na gaskiya to zai kasance kamar bai taɓa aikata wannan Zunubin ba , amma wanda yake tuba alhali yana komawa ga aikata zunubin sa to tamkar yana yiwa Allah izgili ne .

kiyi Tuba na gaskiya yakaka tare da niyyar baza ki sake kusanta kan ki ga aikata ZINA ba a rayuwar ki , Allah zai yafe miki ya wanke ki a idanun Al'umma domin Laifin shi kika yiwa ,

Sannan , ki tashi ki nemi ilmi ki kuma yi aiki da shi idan dama ta samu gare ki kome ƙanƙantar sa ki koyar da ilmin da yake gare ki domin sauran Al'umma su amfana ,

shiriya ta zo miki hasken ilmi ya zo miki ki sa hannu biyu ki karɓe su ƙwarai akwai falala tare da samun dacewa a cikin su , ki manta da rayuwar baya ki himmantu wajen neman gafarar ubangiji akan saɓon da kika wanzu kina aikatawa , da fatan kin fahimce ni ??

bata amsa ba illa hannu da ta kai ta rungume malama maryam , idanun ta na zubar ƙwallar da ita kaɗai ta san dalilin sauƙar su a daidai wannan lokacin

Godiya ta dunga jerowa malama maryam har lokacin da ta sanya ƙafar ta tana barin gidan lokacin dare ya fara shiga karfe goma saura ,

kan titi babu kowa garin ya sake ɗaukar sanyi , a hankali take tafe iska yana ɗaga hijabin ta , tayi zurfi cikin tunani , daki-daki take tuno kome da ya dunga faruwa a rayuwar su ita da ƙanwar ta ,

tana so ta zargi iyayen su akan killace su a gida da suka yi suka hana su neman ilmi , sai dai so irin na tsakanin ɗa da iyayen sa ya mata dabaibaiyi yaƙi bata dama , ji take suna da wata hujjar su , babu shakka akwai dalili ,

tunanin falmata da baby mama yayi mata dirar mikiya , wata irin kunyar falmata ta ji tana nuƙurƙusar ta , yaya zata Ji ranar da duk ta san irin kuskuren da tayi har ta samar da baby mama ta gudu ta bar mata ita ? Wataƙila daga ranar zata fara tsanar ta ,

tsoro take ji tsoron girma ya zowa baby mama ta samu sani akan irin ta hanyar da aka samar da ita , ? Me zata cewa waÉ—annan bayin Allah biyu ??

Lalle wajibi ne a gare ta ta nemi ilmin addini ko domin ta samun ƙarfin guiwar da zata iya fuskantar su tare da tarin hujjoji da bayanan da addinin ya tanadar domin ta gamsar da su ta kuma wanke kan ta a idanun su su san cewa ta aikata kome ne cikin DUHUN JAHILCI ,!

Ko zasu fahimce ta ? Ko falmata zata yadda ta cigaba da riƙe ta a matsayin ƴar uwa masoyiya ? Ko baby mama zata yadda da ita a matsayin uwa ?? Yaushe wannan ranar zata zo ? Zata zo nan kurkusa , ko sai bayan shuɗewar tsawon wani lokaci ? Abun da ta riga ta sani muddin su na raye wannan ranar zata zo ,

YARIMAN MARAÆŠI ,

Zuciyar ta ta auno mata da sunan sa da kome da ya wakana cikin rayuwar ta a wannan gaɓar shine sanadi ,

bata gan shi ko kusa tare da duhun jahilci makamancin nata ba , kome da shi yayi mata yayi ne cikin ilmin sa ,da sanin sa ya aikata Zina da ita ,

zuciyar ta take ji tana wani irin buÉ—awa da sabon yanayin da yake shigar ta akan sa da sabon matsayin da ya kamata ta ajiye shi tun farko a ran ta ,

Tunowa ta fara yi filla filla da farkon haɗuwar su har zuwa ranar ƙarshe da ya kore ta daga motar sa a tsakiyar titi  tana kuka , yayi tafiyar sa ya bar ta har yau bai sake waiwaiyar ta ba ,

tabbas shi macuci ne azzalumi agare ta bai chanchanta da samun soyayyar ta ba ko kaÉ—an ,

bai taɓa son ta ba , kawai amfani yayi da jahilcin ta ya ribaci gangar jikin ta ya yasar da ita tare da cikin da yayi mata , wani irin yanayi mai ƙarfi da kaifi ta ji yana keta zuciyar ta a game da shi , hannun ta ta kai ta tattaro bakin hijabin ta ta riƙe tare da cije gefen leɓen ta na ƙasa da ya zo daidai da zubowar hawayen ta da yake nuni da mummunan ƘULLACIN da tayi masa .... !!!!!!
[9/3, 10:13 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association

MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )

umm'muaz

31

Ba ƙaramin kaɗuwa Youssouf ya yi ba lokacin da Maimartaba yake shaida masa zancen auren sa da Siyama , da har an riga an miƙa dukiyar auren ta ga mahaifin ta dake niamey , za'a yi ɗaurin auren sa da ƴan matan duk biyu a rana guda kamar yadda ya buƙata ,

Ya jima a zaune gaban Maimartaba yana jin yadda zuciyar sa take cunkushewa da tarin takaici ,

Ba tun yau ba ya gama lura da take-taken yarinyar , shi yasa sam baya sakar mata fuska ashe bai sani ba har tayi girman da zata iya yin tsaurin ido irin haka a matsayin ta na mace ta doshi iyayen sa da buƙatar son a haɗa su aure ? Babu shakka zata ɗanɗani kuɗar ta a hannun sa , sai tayi danasanin wannan mummunan shisshigi da tayi ta kutso kan ta cikin rayuwar sa da take a hargitse a halin yanzu ,

Ganin shirun sa ya tsawaita ba tare da ya amsa da amincewar auren ba , ya sa me maimartaba yin gyaran murya

  Da fatan ba zaka bijirewa oumarnin mu ba ? Bisa ga wannan haɗi da munka yi na amre tsakanin ka da ƴar ouwar ka , saboda ba muyi haka ba face sai da munka hango tarin alkhaire tare da dacewa sannan munka so ƙulla igiyar amre a tsakankanin ku , wannan ɗiya ɗiyar ƴar uwa ta ce , kai ma kuma ƴar ouwa take gare ka , ina yi maka oumarni ka karɓi amren nan da hannu biyu da ikon Allah gaba kai zaka yi farin ciki .

Kalmar 'Umarni, ta daƙile dukkanin wani yunƙuri da zai iya yi , domin shi ɗin me yawan biyayya ne ga iyayen sa , haɗi da sanin da yayi a yanzu shi me tarin laifuka ne , wanda yake neman wata kafa ko yaya ne da zai iya faranta ran iyayen sa ta dalilin ta, ko domin su iya masa uzuri a duk ranar da laifukan sa suka bayyana a gare su , su duba irin faranta mu su da yayi su sassauta masa hukunci ,

Cikin harhaɗa kalmomin da suke suɓcewa daga harshen sa saboda kaifin su da yake iya ji ya furta ,

Na Amince , Allah shi ƙara girma da ɗaukaka .

Da murmushi bisa fuskar sa yace

Madallah da kai , Allah shi maka Albarka , Ya Albarkaci zuri'ar ka , Allah shi yi katanga tsakanin ka da miƙiya , kana iya tafiya ka fara shiri doumin nan da sati biyu da ranar tayi dai-dai da gomma ga watan gobe ake ɗaurin amre .

Godiya yayi ya miƙe yana barin shigifar sarki , kai tsaye gidan da zai tarar da Tafeeda ya nufa ,

Cikin sa'a ya same shi dawowar sa kenan daga aiki da sanyin la'asar ,

Babu walwala a fuskar sa ya samu wajen zama bisa kujerun shan iska ,

  Ɗan ouwa ka kuwa san me ke shirin farouwa gare ni ?

Maida ganin sa yayi kan sa , bayan ya miƙa masa sassanyan lemun da ya tsiyayo masa a kofin gilashi ,

Sanar da ni É—an ouwa

Wai amren mataye biyu a rana gouda , kuma amre tare da yarinyar nan siyama da ko ƙamnar duban ta bana yi , shin baka yi tounanin akwai wani dalili da ya sa maimartaba haɗa min amren mataye biyu a rana gouda ba ?

    Ɗan guntun murmushi tafeeda yayi

Banda abun ka Yarima shin amren mataye biyu a rana gouda ba gata bane ?
   Ita siyama ai duk inda ake neman macen amre ta zarta ,

  Maimartaba bashi da sani kan kome wataƙila hasashe ne yayi irin nasu na manya ya sanya shi yi maka gatan amra maka mataye biyu a rana gouda ,

Juyar da kan sa gefe yayi yana jin yadda ran sa ke sake ɓaci , kan batun auren , ga kuma ya lura Tafeeda ba shi da niyyar taya shi jimami , shi ina zai kai mata har uku a shekarun nan nasa ??
   
Kurɓar lemun sa tafeeda yake yi yana satar kallon youssouf da yayi tagumi hannu biyu ya nisa cikin tunani ,
   So yake ya masa tambaya game da al'amuran sa na ƙasar nigeria , ɗiyar sa da take can , ƙaƙa ya ƙarƙare da barin ta a chan ? Hannun wa ya baro ta ? Sai dai rashin son tuno masa da ita ya sanya shi haɗiye tambayoyin sa , ga zaton sa Biyamuradi yayi amfani da shawarwarin sa , ya baro duk wasu kuskuren da ya aikata a inda ya aikata su !

Farin cikin da Siyama ta tsinci kan ta cikin sa bai misaltuwa , domin duk wani da ke mu'amala ta kusa ko ta nesa da ita zai iya shaida farin cikin tare da walwalar da ke tare da ita , da ɗai bata taɓa farin ciki me yawan haka ba cikin rayuwar ta ,

   Ƙulluwar aure a tsakanin ta da Youssouf wani abu ne da tayi shekaru tana mafarkin sa a bacci ko a farke , bata taɓa zaton zata samu damar mallaƙar sa a matsayin miji a sauƙaƙe haka ba , a kuma daidai lokacin da take zaton ya sulluɓe mata zai zama malakin wata ba ita ba , duk tunanin ta na bata sai wani nisan shekaru wataƙila idan da rabo suyi aure , ga haɓakar farin cikin ta ashe tabbatuwar mafarkin ta zuwa gaske yana kurkusa , ashe tare zasu mallake shi ita da wacce take tunanin ta fita sa'a , ashe sa'ar na gare ne su biyu ,?

Bata ji ko É—ar ba akan sanin da tayi auren su auren haÉ—in iyaye ne , tare da sanin da take da shi akan irin tsanar da shi yake gwada mata , ta ji ta gani ta amince ta kuma shirya yin zaman aure da shi da gasken gaske , cikin kowanne irin hali , tana jin son da ita take masa zai ishe su rayuwa ita da shi ,
   Soyayyar sa ga gimbiya maimouna bata razana ta , illa kishi da ke nuƙurƙusa ran ta , dan haka ta sha alwashin ko da ƙaƙa , sai sun raba soyayyar youssouf biyu ita da maimouna kamar yadda zasu mallake shi a matsayin miji su biyu a lokaci guda , idan ya so ita na ta kason soyayyar idan ya so ya zubda a rariya , bata da damuwa son da take yi masa ya ishe su , .

Shiri take ka'in da na'in ubbo tana taya ta haiƙan , gefe guda hajiya umma na bada ta ta gudummawar a matsayin siyama na ɗiya a gare ta , ɗiyar da ta goya tayi rainon ta tun tana tsumman goyo ,

Lokacin da gnala take sanar da gimbiya maimuna dangantakar dake tsakanin youssouf da siyama har ma da zantukan da ta ji siyama na tattaunawa da  ubbo , bata wani ɗau batun da muhimmanci ba , saboda wasu dalilai nata da take ganin ko da ace zai aure su su biyun ita bata jin hakan zai dame ta , burin ta ɗaya tal , shine ta samu nasarar aiwatar da ƙudurin da zai sa ta aure shi .

Dan haka ko da yake kame-kamen sanar da ita batun auren sa da siyamar yana bin ta da kalaman rarrashi , kwantar da murya tayi ta dunga zuba masa sassanyan rikicin da ya sake ɗaga darajar ta a idanun sa tare da sake dilmiyar da shi cikin ƙaunar ta ,
     Ya dunga jin yayi sa'ar samun nutsattsiyar mace kuma me haƙuri, wacce mace ce a zamanin yanzu da za'a yiwa kishiya gab da lokacin auren ta , a kuma haɗa su aure rana guda , ba'a yi danbarwa da ita ba ? Ƙwarai ƙwarai maimouna ta ƙara ƙima a idanun sa ,

Samun haɗin kan ta farad ɗaya ya lafa guguwar ƙin auren a cikin ran sa , sai ya samu nutsuwar fuskantar shirye-shiryen auren tare da cigaba da zarya wajen sabon gurin aikin sa da aka tura shi Dosso , inda zai zama shugaban soji na baki ɗayan yankin na jahar Dosso ,

Tafkeken gida aka mallaka masa tare da motocin hawa biyu , ƙari da tarin hadimai sojoji tun daga kan masu gadi , direba , har zuwa kan me girki .

Tsakanin jahar Maraɗi da jahar Dosso babu tazara me yawa , dan haka lokacin da yake da samun tabbacin wajen zama a dosso , sai yayi niyyar bayan bikin su , zai dawo da gimbiya maimouna nan gidan sa na dosso , kusa da shi , ita kuwa siyama ta cigaba da zama can a maraɗi , tunda ita ta zaɓi auren cikin gida sai ta samu matabbata a cikin gidan , !

Sai dai yana sanar da hajiya umma niyyar sa , a take ya ga sauyin fuskar ta ,
     Abu guda ta ce da shi .

Kome tsanani kayi ƙoƙarin kwatanta adalci tsakankanin matayen da Allah ya baka amanar riƙon amren su , kar ka kuskura ka karkata ga ɗaya daga cikin su , saboda gujewa fushin Allah da azabar sa ka kiyaye , siyama da maimouna duk su biyun matan amren ka ne .

*****

Tun farkon satin aka fara gudanar da shagulgula da wasannin daga bangaren masarautar maraÉ—i har da ta Agades wanda suke da tarin wasannani da al'adun gargajiya fiye da na maraÉ—i , haÉ—i da shiri sosai da suka yi na bikin kasantuwar kowa ya san gimbiya maimouna É—iyar gata ce ta sosai ,

Har zuwa yau da take ranar sakun lalle ga amare , gobe juma'a za'a É—aura auren

Kamar yadda al'adar masarautar maraÉ—i take , duk lokacin da za'a yi sakun lalle ba'a yi a cikin masarauta ,

can tsibirin maraɗi ake tafiya da amayar ,"wani ƙaramin gari ne da yake ƙarƙashin jahar maraɗi da ake ƙiran sa tsibiri bashi da nisa sosai da ainahin cikin garin maraɗi ,

Gidan sarkin tsibirin nan ake sakun lallen a cikin gidan akwai wata mace da ake ƙira ,inna , wacce sunan sarautar ta ce ,inna ɗin ," ita take sakun lalle ga amaren da duk za'a shigar ko za'a fitar daga masarautar maraɗi,

Karfe ɗaya na rana gimbiya maimouna tare da ƙanwar mahaifiyar ta da ƙanwar mahaifin ta da matar maimartaba sarkin agades ta biyu tare da wasu daga cikin matan ƴan uwa na ƙurƙusa tare da rakiyar amintattun hadiman ta mata biyu da bayu maza uku  sai kuma ƙaramar jakaɗiyar agades,  jirgin su ya iso tashar jirgin sama na maraɗi daga agades ,inda nan take motocin da suke jiran su domin kai su tsibiri suka ɗauke su kai tsaye zuwa tsibirin maradi ,

Tarɓa me cike da girmamawa aka yi musu , inda suka tarar da gidan cike da manyan mata masu sarauta na kurkusa da fada cikin su har da manyan yayun biyamuradi ,"Ammi da Dada da Asma'u da ake ƙira ma'u ƴar wajen hajiya mama ta farko . ," da kuma ƙaramar jakadiya .

Tsakanin su bai cika awanni biyu ba siyama ta iso ƙarƙashin rakiyar ƙannen maimartaba sarkin maraɗi su biyu tare da hajiya mama da ubbo sai kuma ƙannen baban ta su biyu ,

Ta ko'ina buɗa da ƙirari ne yake tashi saboda makaɗa da maroƙa da suka cika faɗar sarkin tsibiri duk da cewa an dakatar da su daga shiga cikin gidan inda aka fara shirin sakun lallen amaren
   
  Shimfiɗa ce aka yi da manyan jajayen dardumai , a tsakiyar babban ɗakin , inda aka ajiye babban tum-tum na zama a tsakiyar shimfiɗar ,

Inna tayi umarni da a shigo da siyama za'a sanya ta a lalle ,

Ko kafin bangaren gimbiya maimouna su ce kome , hajiya mama ta yunƙuro ,

  Wacce siyama kouwa ? Ai ita maimouna ita ce matar farko dan haka ita za'a fara sanyawa ga lalle ko kouwa ?

  Hakka zance yake ranki ya dade uwagijiya ta ,

  cewar ƙaramar jakadiyar Maraɗi

Aiyuriyuriyyyy ayuririyyyyyy ayyuririyyyy !!

Wata zazzaƙar guɗa ta fito daga hancin jakaɗiyar agades , saboda jin babban matsayin da uwargiyar su ta samu ,

  Taka a sannou-sannou ƴar sarki jikar sarki , matar yarima ɗan sarki surikar sarki , gaban ki salama bayan ki lafiya  farar macce fitila gida , tauraruowar ki me ƙarfi ce wacce hasken ta ya tarwatsa ya zagaya nahiya tun dagga birnin agades har yankin maraɗi , wouce gabba kin yiwa sauran mata zarra , kin yi gado ba haye kika yi ba mahaifiyar ki ai ita shugaba ta matayen agades ,
 
  A hankali ta sanya kan ta cikin ɗakin tana jin yadda ginshiri irin na sarauta yake sanya ta ƙasaita da jin faɗi.

Bayan shigar ta guda daga bangaren mahaifin ta tare da guda daga bangaren mahaifiyar ta suka rufa mata baya , ubbo ta yunƙura zata shiga hajiya mama ta dakatar da ita tare da yiwa ma'u umarni da ta bisu kamar yadda al'adar take mutum ɗaya daga bangaren dangin miji ke shiga ɗakin sakun lallen .

Bayan zaman gimbiya maimouna inna ta janye hular alkƴabbar dake bisa kan ta , baƙin gashin ta da ya sha gyara ya bayyana , inna ta sanya wata ƴar kyakkyawar kibiyar kitso ta raba gashin biyu hagu da dama ,

Matar da take waziriyar inna ta miƙo mata wani ƙoƙo cike fal da madara sanuwa/nono , ta karkata ƙoƙon a sannu sannu ta fara zuba madarar a daidai tsakiyar tsagun ,

A hankali kakkauran nonon ya fara kwaranya , bisa tsagun kafin ya saki layi ya tarwatse a gaba ɗayan cikin gashin maimakon ya bi kan hanyar da aka masa ƙaɗai ,

Nan take inna da waziriyar ta suka haɗa ido suna masu gƴaɗa kai a hankali , yayin da fuskar ma'u ta sauya tana bayyana ɓacin rai a sarari , har aka gama zuba nono nan haka yayi faca-faca akan fuska da jikin kayan gimbiya maimouna ,

A fusace ma'u ta juya ta fita daga É—akin gefen mahaifiyar ta ta je ta tsugunna ta mata raÉ—a , nan take fuskar hajiya mama ya bayyana wani sirrantatcen murmushi , kafin tayi gyran murya tayi wa jakadiya alama da ido ,

Nan take jeka ta karkace kai ta rangaɗa ƙaƙƙarfar guɗa da ta sanya , mutanen agades samun kwanciyar hankali musamman innonin gimbiya maimouna da duk suka sha jinin jikin su , kan shirun da suka ji daga ɗakin ko dai ƴar ta su tayi kuskure ne cikin rayuwar ta ?

Amma jin buɗa daga bakin jekadiyar maraɗi ya sa hankalun su ya kwanta yayin da tasu jakadiyar ma ta karkace kai ta dunga sakin zaƙaƙan buɗoɗi ,

  Bayu mata biyu suka jawo wata ɗirkekiyar tunkiya fara sol suka ɗanka ta ga hannun matar sarkin agades ,
   Tunkiyar gimbiya maimouna ce ta sakun lalle , nan take bayun agades suka kama igiyar tunkiyar suka riƙe gam .

Ma'u ta koma ɗakin ƙarƙashin umarnin hajiya mama ta sanya farin kyalen ta share fuskar gimbiya maimouna gami da jan hular alkyabbar ta ta rufa mata akan ta ,

Suka fito daga É—akin ,

Bayan an sauya shinfiÉ—a da wajen zama aka yi umarni a shiga da siyama ,

Ƙanwar mahaifin ta ɗaya tare da hajiya mama sai kuma ubbo su ne suka shiga da ita ta zauna akan tum-tum

Inna ta tsaga gashin ta , ta karbi ƙoƙon madarar ta shiga tsiyayo mata shi daga tsakiyar kan ta sannu sannu ya shiga bin layin yana gangarawa har zuwa kan siririn karan hancin ta yana ɗiga a gaban rigar ta , har nono ya ƙare bai karkace hanya ba ,

Wata ƙarƙarfa guɗa ce ta taso daga hancin inna da tayi amsa kuwwa har fada da nan take makaɗa suka ƙara ƙarfin kiɗan su da ƙirari ,

Daga waje ma bayun masarautar maraɗi suka dunga sakin buɗa ba ƙaƙƙautawa ,

Zuciyar hajiya mama tayi bakikkirin lokacin da ubbo ta sunkuya ta ɗau farin kƴallen tana gogewa siyamar madarar fuskar ta idanun su suka gauraye cikin na juna sassanyar ƙaunar da take tsakanin su tayi tasiri idanun siyama suka ciko da ƙwallar murnar ganin wannan ranar me cike da ɗinbin tarihi a wajen ta , a hankali ubbo ta kai hannun ta duk biyu ta rungumo siyamar zuwa jikin ta , a hankali ta raɗa mata a kunne

   Madallah da ke ƙauna ta ɗiyar kirki , me daraja ,Madallah da ke mace tagari abar alfaharin iyayen ta da mijin auren ta !

Ko kusa ran hajiya mama bai yi daɗi ba da cikar budurci da alamu suka bayyana ga siyamar kamar yadda al'adar daman take nuni ne da macen da take cikakkiyar budurwa ita ce wacce nonon ke bin dai-dai tsagun layin ba tare da ya karkace ba , ta so ƙwarai ace an samu matsala irin wacce aka samu ga gimbiya maimouna ,

domin tayi amfani da damar wajen hana yiwuwar auren siyama da youssouf wanda ta ji zancen sama ta ka babu zaton ta babu tsammani , kuma a zahiri bata ƙaunar duk wani abu na alkhairi ya raɓi youssouf ,

Sannan irin tashin hankalin da mommoudu ya shiga da jin zancen haɗin amre tsakanin youssouf da siyama , alhalin shi zuciyar sa ta rayu tsawon lokaci ɗauke da dakon soyayyar siyamar , meyasa kome na cigaba da samun nasarar rayuwa yana ga youssouf ba shi ba ? Meyasa maimartaba ya tattara duk wasu gata da kulawa ya bada ga youssouf alhalin ga shi , shine kuma ƙarami ?

*******

Biki aka yi na bajinta da gata , irin wanda ba'a taɓa yin makamamcin sa ba a tsakanin jahohin biyu , aka yi biki aka gama lafiya lau amare sun ka tare a gidajen su da suke cikin da'ira guda sai dai kowaccen su tana sashin ta yayin da sashin biyamuradi yake tsakiyar nasu , gini ne guda uku a tsaye ,

Daren ranar lahaɗi da aka yi wuni aka watse shine daren da farkon sa yake zaƙi ga youssouf kafin zuwan tsakiyar sa da kome ya rikiɗe ya kuma sauya ya birkice ya hautsine masa , ya sanya shi shiga ruɗani , nadama bakin ciki tare da tarin tsoro ,

Maimouna ita ce macen da ya ɗau aniyar kwada mata ƙauna da soyayya irin wacce yake da burin nunawa ga matar auren sa , hakan kuma ya fara gwada mata a tun farkon daren da yake jin tamkar ya haɗiye ta dan so ko kuwa ya buɗe cikin ƙirjin sa ya cusa ta , sai juyi da ita yake yi yana lallaɓa ta daki-daki tamkar ƙwai , kafin kome ya kankama , zuwa lokacin da zai fahimci bara gurbin ƙwan da ya ɗaukowa kan sa ya kuma ta'alaka soyayyar sa akan ta , har ma ya sallama mata duk wani so gami da yadda da ya mallaka ,

Ashe yayi kuskure ne , shin ashe ta riga ta so wanin sa kafin shi ? Har ma ta mallaka masa abu mafi daraja agare ta wato gangar jikin ta ? Ashe ita ɗin ta ha'ince shi ne ? Shin ko dai shine ya ha'inci kan sa ? Shin ko dai ayar Ubangiji ce ke tabbata akan sa ? Idan kayi zina da matar wani ? Idan kayi zina da ƴar wani ?  Idan kayi zina da ƙanwar wani ?? Uwar wani ??

Tunanin hakan ya tsorata shi tsoro me tsanani , da ya hana tasirin fushin sa bayyana har ya nuna shi ga gimbiya maimouna da ta cigaba da yi masa lamɓo da nuna masa salo salo na gogaggun mata har da ƴan ƙananun koke koken ta , ita ciwo take ji ,

Sai yayi wani zugum kamar soko ya sanya mata ido , ah to shi zata yi wa bariki ?? Ai ya san me ake nufi da budurci , " amma tunaninikan da suke bijiro masa da shuÉ—aÉ—É—en laifin sa suke barazana ga nutsuwar sa saboda zuwan dodo-dodo da suke masa suna sake maimaita kan su tare da bada fassara akan halin da ya riski matar sa a ciki ,

Hannun sa ya kai da ƙarfi ya jawo ta ya jefa kan ta kan ƙirjin sa yana jin yadda iskancin kukan da take yana sake dagula masa lissafi ,

ÆŠan Allah ki min shiru
  Yace da ita , a tsawace

Da yake daman kukan gulma ne sai tayi luf kafin gajiyar biki tare da gajiyar farkon daren su danne ta bacci me matuƙar ƙarfi da daɗi ya silalo ya chafke ta ,

A hankali ya zame ta daga jikin sa ya miƙe daga kan gadon , rigar baccin sa ya ɗauka ya saka , ya fara taku yana barin ɗakin ,

Yayi zurfi a cikin tunanin abun da ka iya je ya dawo cikin rayuwar sa , mama ita take ta kai kawo cikin ran sa , rayuwar É—iyar sa yake hangowa , yana jin wani irin al'amari me girma wanda yake tafe da tsoro akan ta , yana son tsare ta , so yake ya boye ta kar laifin da ya aikata ya shafe ta , tsoro yake kar tarihi ya maimaita kan sa ,

Bakin cikin da yake shaƙa kaɗai a wannan daren yayi masa yawa ma , me yafi ka san cewa matar ka tayi tarayya da wani ta hanyar zina sanya bakin ciki da ruɗani a cikin rai ??

Wani irin kishi me tsanani yake ji , wani irin yanayi yake ji akan ta , ji yake ƙimar ta na zubewa tana zagwanyewa daga ran sa tamkar narkakkiyar roba a cikin wuta , ji yake tamkar yana ƙyamar ta ,

," yaya maimounatu zata min haka,"??
    Yake tambayar kan sa , yana sake maimaitawa ,

  Meyasa ? Meyasa ? Wai meyasa ?

Bai san cewa ya fito har harabar gidan ba sai da ya ji ƙaƙƙarfar iskar dake wajen tana ɗaga rigar sa da bai ɗaure maɗaurin ba , a hankali ya kai hannu ya ja igiyar yana ɗaurewa ,

Tun da ya fito idanun ta suka sauƙa a kan sa saboda daman ta gagara bacci ban da juyi babu abunda take , ita mace ce me zafin kishin abunda take so , dan haka sanin cewa da tayi yau ɗin biyamurdi zai kasance da gimbiya maimouna ya ta'azzara soyuwar ran ta , ya sa bacci gagara ɗaukar ta duk kuwa da iya satar sa ,

   Dan haka ta fito ta barandar ɗakin ta dake sama tana iya hango gaba ɗayan harabar gidan ta kurkusa daga inda take , duk kuwa da sanin da tayi dare ya raba ƙarfe 1:30am , to amma zafin kishi haɗi da bagen so ai rufe idanun me su suke yi .

  Me ya fito da shi a wannan daren ??
   Ta tambayi kan ta

Ta san shi farin sani kamar yadda duk wani motsi nasa yake kusa da zuciyar ta , take kuma iya fassara kowanne motsi nasa

Kada dai inda ya saba fita ya tafi a dai-dai wannan lokacin ya nufa ?? Wani irin tashin hankali ta ji ya taso mata ,
   Zato take ya daina ? Tunda tun bayan dawowar sa daga nigeria bata ji alamun fitar sa ba , bata kuma gan shi ya fita ba ,

Tunanin ta ya katse lokacin da ta ga ya É—aga kan sa sama tare da waiwayowa sashin da take ,

   Da sauri ta tsugunna tana ɓuya a bayan ginin gaban barandar ,

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.