Complete Hausa Novels

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 2 of 21

Cigaba tayi da ƙwalla kiran sunan yakaka ' yakaka ' yakaka , ruwan hawaye yana me cigaba da ambaliya akan fuskar ta da karfi take jefa kafar ta ba tare da tana laluben gaban ta ba burin ta kawai ta tafi neman ƴar uwar ta ɗaya da ta rage mata," ji tayi ta kaiwa bango karo tayi taga-taga ta tafi da baya ta sake faɗuwa," da gudu take jin takun tahowar mutum kafin taji sautin muryar ta itama cikin firgici tana ƙwalla kiran sunan ta 'falmata 'falmata falmata'

Da gudu ta shigo gidan ,"wurgi tayi da ledar da take hannun ta tare da ƙarasawa gurinta zuwa lokacin ita ma kokarin tashi take tana mai sake kiran sunan "yakaka ', ɗago ta tayi tare da rumgume ta cikin jikin ta ,' itama kamkame ta tayi ," kafin su dukkanin su biyu su saki juna suna masu haɗa baki gurin tambayar junan su,'
"Falmata baki ji ciwo ba koh ?
Yakaka ina kika je babu abun da ya same ki koh ?
Banji ciwo ba yakaka ina kika tafi kika barni kin sa hankalina ya tashi kar ki sake tafiya ki barni yakaka ,"falmata ta furta hakan tana me laluben fuskar yakaka ,"

Hannun ta kai gami da share mata hawayen da suke gudu har yanzu akan ƙuncin ta ,"kafin cikin ƙarfin zuciya tace kiyi hakuri kanwata lokacin da gari ya waye naji wucewar mutane ɗai ɗaya hakan ya sa na lallaɓa na leƙa anan naga wani mutum shi ɗaya da gudu zai wuce shine na bishi nima ina tambayar sa koh ya ake ciki a gari ," shine yake gaya min shi hanya ce ta biyo da shi ta nan ƙauyen mu ,'daga ƙaramar hukumar Bama yake ," a yau suka wayi gari da afkawar ƴan tawayen boko haram a yanzu haka sun farma ƙaramar hukumar Bama suna ta kisa ,"irin dai yadda suka yi anan jiya ", mutumin ya tabbatar min da gwara na gudu domin ƴan tawayen boko haram zasu iya dawowa su mamaye dukkanin ƙauyukan da suke tsakanin Bama da Konduga tun da sun riga sun mamaye garin bama ", na tambaye shi to ina zamu ? Shine ya ce min ance wai a cikin Birnin Maiduguri gwamnati ta tanadi wurin da mutane irin mu ƴan gudun hijira zamu zauna a kula da mu kafin a yaki ƴan tawayen boko haram ,"

Tashi mu tafi falmata kar mutumin nan ya yi mana nisa kin ga mu ba mu san hanyar Maiduguri ba bamu taɓa zuwa birni ba ," zame hannun ta da yakaka ta kama tayi kafin cikin muryar kuka ta fara cewa "yakaka ni babu in da zan tafi , yakaka ba mu san inda su mama suke ba , idan muka tafi kuma su mama suka dawo neman mu fa ? Mu zauna yakaka mama zata dawo neman mu zata dawo ta tafi da mu inda ta ɓuya ,"

Share ƙwallar idon ta tayi kafin ta ce falmata su mama fa su ma sun tafi Maiduguri suna jiran mu a can ," da zasu dawo ai da tun jiya zasu dawo idan muka zauna anan koh ƴan tawayen boko haram basu kashe mu ba wuya da yunwa da kishirwa zasu kashe mu ," miƙa hannu tayi ta kamo baƙar ledar da ta shigo da ita wacce take yawo akan ruwan da yake tsakar gidan ," kin ga wannan ma tsintowa nayi a hanya wata kaza tana ta so ta fasa ledar ta kasa shine na bita na ƙwace" biredi ne a ciki ki ƙarba ki ci mu tafi falmata," ta karasa zancen da sigar rarrashi ,"

********************

Hannun su sarƙafe da na juna suke tafiya ," bayan sun fito daga gidan nasu kowaccen su tayi shiru da abun da take saƙawa a cikin ran ta .

A hankali yakaka ta waiwaya tana me kallon kofar gidan su ," sosai ta tsirawa gidan ido tamkar me son kirga adadin yawan bulon da akayi amfani da shi wurin ginin gidan ," gizo idanun ta ya fara yi inda ta hango mahaifin ta ya fito kamar yadda ya saba hannun sa riƙe da hular sa , gefe guda ita ce a tsaye hannun ta riƙe da buhun su na zuwa gona daga bakin kofar kuwa mahaifiyar su ce tana ɗaga musu hannu kamar dai yadda ta saba ," hawayen idanun ta ne suka gangaro gami da ɗiga akan kafar falmata ɗan jijjiga hannun ta da yake cikin na yakaka falmata tayi kafin ta ce mu tafi mana yakaka,"

Mu tafi falmata cewar yakaka wacce ta ke bin dukkanin ginin unguwar su da kallo hotunan al'amuran da suka gudana tun daga tasowar ta a cikin unguwar suna ta wucewa ta cikin tunanin ta ," wata irin kewar mahaifarta tana mamaÆ´ar ta tana jin tamkar ta tafi kenan ," tana jin tamkar karshen ganin ta da gidan su da garin su kenan ," gefen zuciyar ta tana jin wani sabon karfi tare da karban sabon sauyin da rayuwa ta zo mata da shi ,"yayin da take jin nawin girman da ya hau kan ta na rike kan ta da kanwar ta falmata yana kama ta,' sai dai tana jin kome runtsi da Wahala zata kula da falmata ko da ita zata rasa rayuwar ta," miskin falmata ,"

Taku Falmata ta fara yi tana me jin yadda duhu yake mamaye zuciyar ta kamar dai yadda duhun yake a zahiri a idon ta ," tana jin duk wani farin cikin da ta san ta samu daga lokacin da tayi wayo zuwa yau yana barin jikin ta ,' wani irin ƙunci yana mamaye cikin ran ta ," tana jin kuncin yana ƙaruwa da dukkanin wani takun ta guda ɗaya da take yi da niyyar barin garin su mahaifar ta , zuciyar ta tana cike da tsoron sabuwar rayuwar da zata fuskan ta alhalin tana makauniya a garin da bata da kowa bata san kowa ba sai ƴar uwar ta ," tsoro sosai ya ɗarsu a ranta " , sai dai wani sashi na ranta yana faɗa mata zata dawo watarana , wataran zata dawo garin su mahaifar ta , zata sadu da mama da sauran kannen ta ," bata san lokacin da wani matsanacin kukan da yake cike da tsoro da kuncin zuciya ya kufce mata ba ,' kuka take bilhaƙ ,"

Matsa hannun ta yakaka take yi alamun rarrashi domin a zuwa yanzu ita ma bata da karfin zuciyar rarrashin falmata domin tana da tabbacin tana buÉ—e baki kukan zuciyar da take yi zai bayyana a zahiri ," ita ma bukatar rarrashi take tana bukatar matallafin da ko da ba zai taimaka mata da kome ba ," zai furta mata kalmar ZAKI IYA YAKAKA,

Hanyar da mutumin nan ya gwada mata ita su yakaka suka kama," suna tafe basa jin motsin kowa sai kukan tsuntsaye ," É—an turus yakaka tayi ganin hanyar bakin jeji sosai ta kawo su ," jin sun tsaya ne ya sanya falmata wacce ta fara gajiya tace yakaka har mun kawo Maiduguri ne ? Cikin sanyin murya yakaka tace falmata gani nayi hanyar da muke tafiya a kan ta ta kawo mu bakin jeji ," jin batun jeji ya sanya falmata sake cukumo rigar yakaka tare da cewa mu koma kawai yakaka ," na faÉ—a miki daman kar mu taho ,"

Jin takun tafiya tare da hayaniya kamar har da kukan yara da suka ji shi ya sa su saurin juyawa " wasu gungun mata (sun fi su goma ) tare da yara da namiji guda É—aya suka hango ," bisa ga dukkan alamu su ma a jigkace suke daga su sai kayan jikin su ," wucewa suka yi ta gaban su ba tare da sun ko kula da su ba ," cikin sauri yakaka ta saki hannun Falmata tare da cewa ", bari na tambayo su koh su ma maiduguri suka nufa ," da É—an gudu ta cimma su saboda saurin da suke zabgawa cikin harshen su take tambayar su ," ko maiduguri za su ?" Ba tare da sun waiwaye ta ba É—aya daga cikin su ta bata amsa da ",Eh ",

Da gudu ta koma baya gami da kamo hannun ƴar uwar ta tana jaan ta tare da cewa zo mu tafi falmata mun samu abokan tafiya waɗan nan mutanen su ma maiduguri suka nufa ,' ita dai falmata bata ce ƙala ba ta bi yakaka suka faɗa jeji tare da bin bayan mutanen nan da har sun fara yi musu nisa cikin duhun ciyawa ,"

Doguwar tafiya suka yi sosai cikin ƙungurmin dajin nan da yake cike da itatuwa da ciyayi gami da ƙayoyin da suke ta faman huda musu takalman su suna sukar kafafun su, ba sa cewa ƙala a tsakanin su ," har zuwa lokacin da rana ta ɗan gota tsakiya alamun azahar ta yi ", namijin ciki shine ya basu umarnin tsayawa a dai-dai wani wurin da ruwan sama ya ƙwanta yayi kamar ƙaramin kududdufi " , cewa yayi a huta a sha ruwa sannan ayi sallah a cigaba da tafiya ,"

Yaraf ,'duk suka zazzauna wasu ma kwanciya suka yi warwas a ƙasa ,kallo ɗaya za'a yi musu a fahimci tsabar gajiya da yunwa a tare da su ," yaran ciki kuwa daman tuntuni suke kukan yunwa da kishirwa dan haka ko da su ka ga ruwan nan , nan take suka nufi wurin wasu suka sa tafukan hannayen su biyu suna ɗebo ruwan suna sha wasu kuwa bakin su suka sa a kan ruwan suna sha ",

Yakaka da falmata suna cikin waÉ—anda su ke shan ruwan da hannayen su ,É—auro Alwala su ka yi bayan sun sha ruwan ," su ka kuma jira sauran matan su ma su ka zo sha ruwan tare da É—aura alwala ," namijin ya jaa su jam'i haka a cikin dajin ,"

Ƙarar wucewar wani abu me tsananin karfi da matsanancin ƙara da yake barazanar kashe musu dodon kunnuwa shi ya sanya a firgice ! Su dukkanin su, su ka ɗaga kai sama ba tare da sun sallame sallar da su ke ba ," yaran ciki kuwa nan take su ka fasa kuka tare da ƙanƙame iyayen su

Shawagi wannan abun da wasu daga cikin su , su ka ce "jirgi ne " ya cigaba da yi ," yayin da su kuma su ke tsaye carko carko , kawukan su a ɗage suna hango jirgin da yayi ƙasa ƙasa da har su ke iya ganin launin sa da yake koren kala , ruwan madara da kuma ruwan hanta "(coffee),"

Falmata lalubo hannun yakaka tayi tare da riƙe ta gamgam cikin karkarwar murya tace yakaka menene shi jirgin ?

Basu yi aune ba kawai su ka ji an saki wani abu kamar bom ," wanda ya faÉ—o kurkusa da mutumin nan da yake jagorar tafiyar su tare da wasu mata biyu da suke tsaye ,' nan take su ka tarwatse jinin su ya watsu a jikin sauran su ,"

wani irin kururuwa su ka yi a tare da yake nuna tsantsar firgicin su ," karo suka fara yi da juna cikin gigicewa suna masu neman hanyar gudu jin yadda jirgin nan ya sake sakin wanna abun da basu kai ga fahimtar harsashi ne ko kuwa bom ?,"

Fisgar hannun Falmata, yakaka tayi wacce take ta faman waige-waige tare da ihun tambayar yakaka me yake faruwa ? Ba tare da yakaka ta bata amsa ba ta fisge ta cikin ihun kukan da ƙarar jirgin nan ya dusashe ƙarfin sautin take cewa mu gudu Falmata idan ba haka ba zamu mutu ,"

Takawa su ke da matsanancin gudu suna jefa ƙafafun su wanda ko takalma babu "domin basu samu damar sanya takalman su ba " wurin da duk suka tsinci kan su nan suke jefa kafa basa duba gaban su bare su waiwaya baya ,"wasun su kuka da ihu suke yayin da tsiraru daga cikin su suke addu'a ," gudun ceton rai suke cike da tsananin tsoro tare da tashin hankalin jin kamar ƙarar jirgin nan na bin su  ,"

Cikin tsananin gudun da su ke ne yakaka taji hannun falmata da take riƙe da shi gam-gam suna gudun tare ," hannun ta ya fisge daga cikin nata lokaci guda kuma taga falmata tayi ƙundubala ta tafi gaba ɗaya ta faɗi ta gaba fuskar ta ta bugu da ya sa ba shiri ta saki wani irin ihun azaba tare da ƙwalla kiran sunan Allah ,"

Cikin kaɗuwa yakaka wacce har ta yi gaba saboda matsanancin gudun da suke ," ta dawo da baya da gudu gami da durƙusawa ta tallafo falmata wacce hancin ta da bakin ta ke fidda jini ," sai dai wata ƙarar da falmata ta sake saki a lokacin da yakaka take koƙarin ɗago ta ya sanya babu shiri ita ma yakaka ta fashe da matsanancin kuka ,"
Falmata sannu Dan Allah ki tashi
" ta furta hakan tana me gogewa falmata jinin da ya bata mata fuska da É—ankwalin kan ta da ta zame lokaci guda kuma tana me É—aga kanta sama tare da yawata idanun ta a sararin samaniya cikin tsammanin ganin jirgin sojojin nan ,"
Ƙafata yakaka ƙafata ta maƙale a rami wayyo Allah na yakaka zan mutu ,"
Falmata ta furta hakan a lokacin da ta ruƙo ɗayar ƙafar ta, take ƙokarin zaro ƙafar daga wani ɗan ramin da yafi kama da na "ƙurege" ko kuwa dai kananun dabbobi dangogin sa ",

Cikin tashin hankali yakaka ta sake fuskar falmata gami da miƙewa ta koma ta wurin ƙafafun ta ,"kokarin zaro ƙafar ta fara yi ,"idanun ta suna zubar hawayen tausayin kanwar ta da ya sa ta kusan mance halin tsaka mai wuyar da suke ciki ,"

A gigice ta É—ago kan ta ganin wani hannun da tayi ya kama kafar falmata "cikin taya ta kokarin zaro kafar ,"

ÆŠaya daga cikin abokan tafiyar su ce ," ita ma yarinya ce wacce zata iya girmewa yakaka da kadan ",

Da karfi su ka samu nasarar fusgo kafar falmata wanda hakan ya sa yakaka tayi faɗuwar ƴan bori akan ciyawar farar ƙayar da ta soki bayan ta ya sa ba shiri ta sake zabura ta miƙe gami da rugowa ta ɗaga kafar falmata wacce tayi futu-futu da ƙasa," ta ɗora akan cinyar ta ,"lokaci guda tana tambayar falmata kafar bata ji ciwo ba koh ," ?

Yakaka kamani na tashi mu gudu," Falmata ke furta hakan a lokacin da take laluben hannun yakaka fuskar ta tana bayyana tashin hankalin da take ciki ," da sauri yakaka ta miƙe bayan ta sauke kafar falmata daga jikin ta ,"yunkurawa tayi tare da ɗago ta ," ganin haka ya sa yarinyar da take tsaye a gefe tana kallon duk abun da suke ta matso gami da kai hannu ta kamo ɗayan hannun falmata da nufin taya yakaka ɗaga ta ,"

Wani irin zamiya falmata tayi tare da warce hannun ta daga jikin yarinyar wanda hakan yayi sanadiyar komawar su ƙasa da ita da yakaka ,a lokaci ɗaya ta kanƙame jikin ta wuri guda tare da cewa ,"
Yakaka waye a wurin nan tare da mu ? Aljanu ne koh ?

Falmata wacce ta taya ni muka zaro kafar ki daga rami ce É—aya daga cikin abokan tafiyar mu ........,"

******************

Kika ce kin san hanyar Birnin Maiduguri Yagana ? Tambayar da yakaka ta jefawa Yagana (abokiyar tafiyar su ) kenan lokacin da suke cigaba da tafiya ," sai dai saɓanin ɗazu yanzu a nutsen su suke tafiya ,"samun nutsuwar su ya samo asali ne daga fahimtar da suka yi jirgin nan ya tafi ya daina bin su ,"

Sai dai fa a yanzu zuciyoyin su cike take taf da tsoron ganin su uku ne rak a ayarin tafiyar su sauran duk sun watse kuma basu sake cin karo da ko guda daga cikin mata takwas da kananun yara biyar É—in da suka rage a ayarin nasu a bayan mutuwar namijin cikin su tare da mata biyun ba ",

Eh nasan maiduguri yakaka mun taɓa zuwa tare da yaakura na ( yayar mahaifiyar ta )

Sau goma kuka taɓa zuwa koh sau ashirin ," da a yanzu kika ce zaki mana jagora ? cewar falmata wacce take ɗingisa kafar ta gefe-da-gefen rigunan su ita da yakaka a ƙulle da na juna ,.

Sau ɗaya dai na taɓa zuwa tun lokacin ina shekaru biyar na taɓa yin rashin lafiya wai wasu kuraje suka fito min shine aka ce sai a Babban asibitin cikin Maiduguri za'a ban magani ," ta karasa zancen tana me ɗaga zanin ta zuwa gwaiwa ," kin ga taɓon kurajen nan yakaka wannan tabon da kike gani tun ina shekaru biyar a duniya,"

Waiwayawa su ka yi jin Falmata ta jaa ta tsaya lokaci guda suka dawo gefe da gefen ta suka tsaya ," yagana tana cewa kin gaji ne falmata ?
Falmata wani wurin yana miki ciwo ne cewar yakaka ?

Fashewa da kuka tayi cikin shishiƙar kuka ta fara cewa yakaka sai da na faɗa miki kar mu taho kar mu taho kika ce sam sai mun taho ," kika nace ," gashi nan yanzu zamu mutu a cikin daji kura ta samu na kalaci ," ta karashe zance tana jaan majina .

Shiru yakaka da yagana suka yi domin a hakiƙanin gaskiya su dukkanin su biyun karfin hali kawai suke domin kuwa ƙarƙashin rayukan su cike yake taf da tsoron duhun daren da ya riga ya fara shigowa ne,"alhalin suna cikin ƙungurmin dajin da basu san gabas ba bare yamma ,"

Kiyi hakuri Falmata ni bana son yawan kukan nan da kike kin san dai baki da lafiyar idanu ," muyi ta addu'a kawai Allah yana tare da mu ," cewar yakaka

Eh Falmata addu'a ita ce mafita kuma ina jin kamar ma mun kusa isa maidugurin dan ina tunanin lokacin da aka kaini asibitin kamar ance wai bamu kwana a hanya ba wai awanni bi......

Ke ni dallah ki mana shiru ,"ke idan ana zancen waɗan da suka taɓa zuwa birnin maiduguri ma har kya sako baki ?

Wucewa gaba Falmata tayi a fusace tana lalube a ranta kuwa tana ayyanawa kome ta fanjama .
[6/24, 9:58 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association

*MAFARI.......*
( _HARGITSIN RAYUWA_ )

*umm'muaz*

4

Ƙanƙame da juna suke kwance a ƙarƙashin duhuwar bishiyar kukar da duhun ta ya haɗu da duhun dare tare da na damina ya bada matsanancin duhun da ba'a ko iya ganin tafin hannu .

Falmata ce a tsakiyar su yakaka da yagana suna gefe-da-gefen ta ,ko ƙokkwaran motsi basa iya yi saboda tsabar zullumi da tsoron da ya cika musu rai ! Numfashi ma a sace suke yin sa yayin da kunnuwan su suke tarwai a buɗe daga jin motsin abun da yake nesa da su da kusan rabin kilomita .

Babu motsin kome a dajin da ya wuce kukan jemagu da kuma wasu ƙananun ƙwarin da ba'a iya tantance kukan su ," haɗi da wani kuka da suke ji daga nesa ƙadan da su wanda tsananin tsoron da suke ji ya sa suka kasa tantance kukan koh na menene ,"ya dai fi musa kama da kukan bijiman sa (shanu) sai kuma jifa-jifa kukan manyan namun dawa waɗanda suke nesa sosai daga wurin da suke .

Ƙasa-ƙasa muryoyin su suka fara tashi ,"
Umm Yakaka zan yi fitsari ,"
Fitsari kuma falmata dan Allah kiyi hakuri mu jira safe.
Falmata kawai kiyi fitsarin nan anan kwance a jikin mu ," cewar yagana

Motsin da suka fara ji mai ɗan karfi yana doso inda suke ne ya sanya su sake damuƙar junan su kafin jikin su ya ɗau karkarwa kar-kar-kar .
Shikenan muryoyin su sun jawo mu su .

Wani ɗumi yakaka da yagana suka ji a jikin su wanda yake tabbatar musu yawaitar motsin da suke ji tare da ƙarin gabato su da motsin ke yi shi ya sanya falmata sakin fitsarin da tace tana ji saboda tsabar tsoro

Haske suka fara hangowa wanda basa raba ɗaya biyu hasken tocila ne ," kafin su fara jin taƙun kafafun mutum ," tare da tashin muryoyin mutanen da baza su wuce biyu ba sai dai magana suke a cikin yaren da su yakaka basa fahimtar sa ,"

Gani suka yi an ɗan kau da hasken tocilan kafin su ji an taho har kurkusa da su ," karar zubar wani abu kamar ruwa ne ya fara sauka kunnuwan su kafin su ji ruwan mai ɗumi ya fara fallatsuwa akan fiskokin su a zaɓure suka miƙe zaune wanda a tunanin su koh ruwan zafi ake watsa musu ,"

Miƙewar da suka yi shi ya mutumin da yake tsaye shima ya zabura tare da yin eho a take kuma ya buɗe murya gami da yin magana da maɗaukakiyar murya cikin yaren sa nan take sai ga hasken tocila ya dallare fuskokin su yakaka ,"

*****

A tsugunne suke bisa gwaiwowin su tamkar mai laifi a gaban hukuma ," maza ne kimanin goma a zagaye da su dukkanin su hannun su rike da makamai kama tun daga kan ,sanduna , gatari ,takobi,kwari da baka , wuƙake , da ma bindigar harbi ka buya ,

Fahimta da suka yi su yakaka basa jin yaren su na hullanci ya sanya É—aya daga cikin su ya juya harce cikin yaren hausa
Yaro ku su waye ? Kuma daga ina kuke cikin daren nan ?

Nan take yagana wacce da alamu ta fi su yakaka fahimtar hausa ta ce mu Æ´an gudun hijira ne daga garin Bama nake waÉ—anan kuma "tana nuna su yakaka " abokan tafiya ta ne daga nan kauyen mairambiri suke ," Æ´an tawayen boko haram ne suka tarwatsa mana garuruwan mu ,"

Duk bayanin nan da suke yi yakaka da yagana basu samu damar ganin fuskokin su waye a tsaye zagaye da su ba su dai sun san mutane ne , kuma a ƙalla sun ji saukin tashin hankalin da suke ciki akan sanin da suka yi ashe akwai mutane dayawa haka kurkusa da su ,".

Juya harshe wannan mutumin da ya tambayi su yakaka yayi ,"tare da yi wa abokan tafiyar sa fassarar bayanin da yagana tayi cikin yaren su na hullanci ," nan take hayaniyar su ta ƙaure a wurin da alama Tausayawa yaran suke tare da Allah wadai da ƴan tawayen boko haram wanda sun riga sun san da zaman su ," kuma tsakanin su da su babu kare bin damo "abun nufi ko da sun haɗu cikin daji basa shiga harkar juna ," ( Makiyaya da ƴan tawayen boko haram )

Bayan doguwar muhawarar da suka yi a tsakanin su nan mutumin ya juya ga su yakaka yace ":
Yaro yanzu ku ina kuka nufa ?

Maiduguri zamu ," ance gwamnati ta tanada mana wurin zama ', za'a kula da mu cin mu da shan mu sutura da wurin kwana har ma ance za'a samu a makarantun gwamnati ," abincin cin mu ma na....

Katse ta mutumin yayi :
Yaro kun san hanyar Maidugurin ne ?

Nan falmata wacce take fahimtar mafi yawan kalmomin nasu ," mayar da magana cikin hausar ne ke yi mata wahala ,

Tayi tsagal tace Baba wallahi bamu san hanya ba", dan Allah ku taimaka ku kai mu Maiduguri dan Allah ta karashe zancen tana matsar ƙwallar wahalar da ta ciko mata ido,"

Yaro zamu taimaka muku amma mu ba Maiduguri muka nufa ba ," mu daga nan ikko muka nufa ,"amma zamu raka ku har inda muke ganin kun wuce hatsari sai mu gwada muku sauran hanyar ," nan wurin da kuke akwai hatsari sosai ,

Juyawa ya sake yi suka yi magana da Æ´an uwan sa ," sannan ya juyo tare da cewa ku biyo mu ,"

Lumshe matsakaitan idanun ta tayi lokacin da ɗumin madarar saniyar sabuwar tatsa ya sauka a cikin ta ," dago kan ta tayi daga cikin ƙoƙon da yake cike taf da madarar ta maida kallon ta ga fuskar kanwar ta wacce tayi kasaƙe hannun ta rike da nata ƙoƙon da bata tunanin ma ta kai bakin ta ," idanun ta suna sheƙin ruwan da ya taru a cikin su a tsaye idanun na ta suke ƙem wuri guda ," da alamar tayi zurfi cikin tunani ," a hankali taga ƙwallar da ta taru a gurbin idanun nata sun silalo da gudu sun sauko bisa ƙuncin ta ," da sauri ta ajiye ƙoƙon madarar ta gami da ƙarasawa inda falmata take zaune akan wani ɗan dutse ," dire gwaiwowin ta tayi a ƙasa lokaci ɗaya kuma ta sanya hannu gami da goge mata ƙwallar da suke cigaba da fitowa

Yakaka yau kwanaki biyu kenan muna wayar gari ba tare da iyayen mu da sauran Æ´an uwan mu ba ," Allah ya jikan Baba ya gafarta masa ,"insha Allah shi mutuwa hutu ce a gareshi ,"

To amma yakaka mama fa da sauran kannen mu a wane hali suke ciki ? Wataƙila suma ƴan tawayen boko haram sun kashe su irin yadda suka yi wa Baba ," idan kuwa har suna raye tabbas mama tana cikin mawuyacin halin da ya fi wanda muke ciki a yanzu ,"

Yakaka muna shiga birnin Maiduguri abu na farko da zamu fara yi shine neman maman mu ,"

Ƙai hannunta tayi ta lalubo fuskar yakaka jin tayi shiru bata cewa kome duk bayanin da take yi , nan taji ruwan hawayen da suka faca-faca akan fuskar ta ," share mata hawayen tayi kafin a hankali ta kai kanta ta ɗora akan kafaɗun ƴar uwar ta , idan ke kika yi kuka a halin yanzu ni me kike so nayi yakaka ? ,kiyi haƙuri ki daina kuka insha Allah zamu haɗu da maman mu ,"

Nemo yatsun hannun falmatan tayi ta sarƙe su cikin nata hannun "falmata ba ina kuka bane a domin wahala koh raunin zuciya akan halin da muke ciki ba," ina kuka ne akan tunanin halin da mama da ƙannena suke ciki ina kuka akan wahalar rayuwar da kike ciki a halin yanzu alhalin bani da karfin taimakon ki ,"dubi kafar ki falmata ta ɗago kafar falmatan da take ɗaure da ɗankwalin ita yakaka,"

Duk ƙafar ta soke da kayoyi daga idon sawun ƙafar kuma a kumbure yake in da ta faɗa rami a jiya ," Falmata tun tasowar mu ban taɓa ganin ciwo irin wannan a jikin ki ba ,"duk da cewa muna rayuwa cikin talauci amma iyayen mu suna tattalin mu ,da lafiyar mu" amma ki duba daga shekaranjiya zuwa yau da rikon ki ya dawo kaina na gaza wurin baki kulawa gashi duk kin ji rauni ," sai nake ganin laifin kaina da zan iya falmata da goyon ki zan yi nasan da mama ce da ta sauke Bulama ta goye ki amm dubi ni ...

ÆŠago kan ta tayi tare da toshe mata bakin ta da hannun ta ," fuskar ta babu walwala tace yakaka daga yanzu ki daina ganin laifin kan ki akan duk wani abun da kaddara zata É—oramin ,"
Sannan ki daina ganin kamar ni a dalilin bani da ido bazan iya yi wa kaina kome ba ," wasu abubuwan zan iya yakaka ,"a yanzu rayuwa ta sauya min ta inda nake ganin dukkanin wasu abubuwan da a baya bazan iya su ba a cikin sabuwar rayuwar da zamu fuskanta zan iya su ," abun da nake so kawai kar ki taɓa ɗauke matsayin ki na wacce take gaba da ni a koyaushe kika ga zan faɗa rami ki taro ni kin ji yakaka ?

Naji Falmata sai dai nima ina son ki bar min matsayina na yayar ki a duk lokacin da na nuna cewa nice gaba da ke wurin baki kulawa ,"kin ji koh ?

ÆŠan siririn murmushi tayi
" naji yaa yakaka ,"

A hankali yagana ta sanya babban ɗan yatsan ta, ta ɗauke ƙwallar da ta gangaro mata daga cikin ido ," tana tausayin kan ta sosai da sosai tun tasowar ta kasancewar ta tashi ne ba tare da mahaifan ta ba mahaifiyar ta rasu tun tana yarinya yayin da mahaifin ta ya tafi ci rani ,"tun tana shekaru goma har yau bai dawo ba "dan haka a hannun kakar ta mahaifiyar Baban ta ta girma" sai dai daga jiya zuwa yau ta sake tausayawa kan ta a sanadin ganin tsaftatatciyar soyayyar ƴan uwan taka da take gudana tsakanin yakaka da falmata , wanda ya sa ta fahimci ba ƙaramin gibi take da shi a cikin rayuwar ta a sakamakon rashin dan uwa koh ƴar uwa da take da shi ba ," sosai soyayyar da ta lura tana gudana a tsakanin ƴan uwan biyu ta birge ta tare da bata sha'awa .

Ajiye ƙoƙon ta"wanda ta riga ta shanye madarar ciki tas " tayi a gefe tare da miƙewa ta nufi wurin da har yanzu yakaka da falmata suke zaune ,"sai dai saɓanin ɗazu yanzu a jere suke a zaune inda falmata ta matsawa yakaka ta zauna a gefen ta suna fuskantar mahuɗar rana da ta fara ɗagowa tana keto tsakankanin ciyayin , ranar ta bada wani haske mai kyau ,"

Dafa kafaɗun su tayi da hanun ta ɗai ɗaya ," idan an gama tattaunawar sirrin tsakanin ƴan uwa a tashi mu tafi mu mayar musu da ƙoran nasu kafi su gama shiri su fara jiran mu kuma ,"kun san dai sun ce da wuri zamu kama hanya saboda miƙaƙƙiyar tafiyar da ke gaban mu ," murmushi yakaka tayi ," yagana baki da dama ,"
Satar kallon falmata yagana tayi wacce ko alama bata nuna ma taji abun da yaganan ta ce ba ,"

Kamo hannun falmata ," yakaka tayi da sauri yagana ta zagayo tare da kama mata É—ayan hannun ,"amma ga mamakin su sai ji suka yi tace
"zan iya tashi da kaina ,!
Yunƙurawa tayi amma sai suka ga ta kai hannun ta gami da lalubar hannun yakaka ta rike gam gami da miƙewa a hankali ,"hakan da yagana ta gani ya sa ta fahimci falmata bata so ta ita ta taimaka mata sai ƴar uwar ta "ɗan tabe baki tayi cikin nuna ko oho ",

*****

To kun ga nan shine karshen dajin konduga daga nan ai gashi kuna iya hango gidajen da suke ta cikin yankin unguwannin Birnin Maiduguri ,"wadancen gidajen da kuke iya hangowa daga nan suna cikin unguwar da ake kira dalori ne , kuna ƙarasawa can kun riga kun shiga birnin Maiduguri ," mu daga nan muke sake komawa mu ɗauki hanyar in da muka nufa ," wannan dogon bayanin yana fitowa ne daga bakin bafullatanin mutumin nan ,"bayan sun kawo su yakaka iyakar dajin yankin konduga da cikin garin maiduguri ,"

Nan take su yakaka suka durkusa akan guiwowin su suna masu jero godiya da tarin addu'o'i ", zuciyoyin su kuwa ƙwal kamar an musu bishara da wani babban abun Alkairi,"

Da murmushi É—auke akan fuskokin fulanin nan su biyar "da alama sun baro sauran a daji tare da dukiyoyin su (shanun su ) suke amsa jerun gwanon addu'o'in su yakaka ," kafin mutumin ya É—ora da cewa toh yaro sai ku kula da kan ku sosai ,maiduguri babban gari ne sosai domin haka sai kun yi taka tsantsan da kome , da mu Æ´an gari ne da zamu sanya ku a hannun wasu da muka sani to mu ma bamu san kowa ba cikin maiduguri,"

Sanya hannun sa yayi a aljihu ya zaro wata tsohuwar naira ɗari biyu ya damƙa a hannun falmata wacce ya lura bata gani ," daga haka suka yi musu sallama tare da juyawa suka ɗau hanya abun su ba tare da sun sake waiwayawa ba ,"

Shirun dakikai biyu zuwa uku ne ya gitta tsakanin ƴan matan uku bayan juyawar fulanin zuwa inda suka fito ,"ga su dai ga birnin maiduguri bayan doguwar tafiyar da suka yi na kimanin kilomita 74-76, akan kafafun su daga ainahin garuruwan su , da kuma tarin ƙalubale da hatsarin da suka shiga a yayin tafiyar ," wanda ya kamata ace a yanzu da maɗaukakin farin ciki za su durfafi birnin na maiduguri , to sai dai a halin yanzu da fulanin nan suka juya tare da tafiya suka bar su a faffaɗan fili sararin Allah da ya tafi ɗoɗar daga nesa suna hango gidajen jama'a da fulanin nan suka tabbatar musu gidajen cikin birnin maiduguri suke ," sai duk suka ji zuciyoyin su sun raurawa ,'akan tunanin ina kuma suka dosa ? Ina zasu nufa ?

Falmata ce ta katse shirun nasu a yayin da ta tattaro gutun yawun bakin ta da ya gama bushewa a sakamakon ranar damina da aka bude a yau ", Yakaka tsayuwar me muke yi ne kuma ? Kamata yayi mu ƙarasa cikin garin mu fara da neman maman mu a yau ɗin nan kin ga idan Allah ya sa muka ganta kafin dare ,"yau baza ta shiga cikin lissafin ranakun da zamu ƙara kwana ba tare da ita ba ko kuwa ?

Mukut ! Yakaka ta haɗiye guntun yawun da ya saura mata a baki ," Falmata a yadda fa nake hango girma da yawan gidajen da suke cikin Birnin Maiduguri ya sha banbam da irin na garin mu" amma dai bari mu ƙarasa mu gani ,"

Yunkurawa suka yi tare da kama hanyar suna tafe babu me cewa ƙala ," sun yi tafiya me ɗan tsawo zuwa lokacin da suka fara cin karo da gidajen da suke farko-farkon unguwar dalori Qaurters .

Ware ido sosai yakaka tayi tana kallon tsarin gidajen tare da yawan mutanen da ta gani suna ta kai kawon su ," nan take taji zuciyar ta buga da tunanin ina zasu fara bi su nemo mahaifiyar su a cikin wannan faffaÉ—an birnin ?

Ta bangaren yagana kuwa yawan jama'a da tsarin gine-ginen , bai wani zama baƙon abu ba a saboda babu laifi garin su "Bama" shima babbar Alkarya ce wacce take cike da Al'umma da kuma cigaba dai-dai da zamani ," tunanin ta ya fi karkata ga inda zasu je su samu mafaka kamar yadda kafin su fito daga gida a lokacin da labarin shigowar ƴan tawayen boko haram ya baza garin su aka fara guje guje da ƙokarin barin garin ɗaya daga cikin ƙannen mahaifin ta shi ya basu tabbacin idan suka tafi birnin maiduguri akwai mafaka agaresu da musamman gwamnati ta tanada ,"

Dan haka take taku zuciyar ta cike da son ganin sun isa mafakar ta su ,"

Ga bangaren Falmata kuwa ita ba ganin garin take yi ba amma hayaniyar muryoyin jama'a tare da ƙarar wucewar ababen hawa da suka cika mata kunnuwa sun isa sanar mata cewa ta shigo wani wuri da ya sha bamban da mahaifar ta me rangwamen hayaniyar jama'ah , ƙarar ababen hawa kuwa sai ranar cin kasuwar garin su take iya jiyo su daga nesa-nesa ," nan take taji tsoro ya kamata sakamakon tunowa da tayi da fannah ƴar makotar su wacce mota ta taɓa bigewa ta karya mata kafafu " , nan take ta lalubo jikin rigar yakaka ta haɗa da jikin tata rigar ta sake ƙullewa ," sannan ta sake jefa hannun ta cikin na yakakar wacce ita ma ta rike hannun falmatan gam-gam .

Cikin mutuwar jiki suke tafiya a lokaci guda yunwar da take ƙwaƙular cikin su tana tuno musu da rabon su da sanya wani abu a cikin su tun madarar da suka sha da safe ga shi dai yanzu azahar ta yi domin suna iya jin kiran sallah daga massalatan da suke cikin unguwar,"Yakaka idan muka samu wurin da ake sayar da abinci mu tsaya mu saya kafin mu isa ga masaukin mu ,"

Uhm yagana wane masauki kike zance a yanzu bayan duk alamu sun bayyana a garemu bamu da hanyar da zamu bi ta sada mu da gidan gwamnatin ,"idan kuma kina da hanyar sai ki faÉ—a ," cewar falmata ,

Yagana Jaan bakin ta tayi ta tsuƙe domin ta lura ba wani birge falmata take yi ba a kome ," a gefe guda kuma na zuciyar ta ,tana me gaskata zancen falmatan tabbas , ganin kitse take yi wa rogo a duk zaton ta suna tako kafafun su cikin garin maiduguri zasu tadda jami'an da aka ce suna bada tsaro ga mutanen maiduguri zasu chafe su ,tare da sada su da masaukin su cikin farin ciki da walwala ,"

Sai dai tabbas a yanzu tana iya hango yiwuwar sauyawar tunanin ta "wanda ya sanya ta hango kanta a matsayin wacce tayi masauki a kan bola " da hakan ya sanya ba shiri ta fara zare idanu tana kallon mutanen da ta lura su ma a halin yanzu kallo suke bin su da shi a duk inda suka gifta .

Duk ba wannan ba yanzu abun da yakamata mu fara yi shine mu samu wuri muyi sallah daga nan sai mu fara tambayar mutane hanyar masaukin da kika ce an tanada ga irin mu ,"koh me kuka ce ,"Yakaka ke furta hakan bayan Æ´ar gajeruwar muhawar da taji falmata da yagana suna yi ,

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.