Maradams Book 1 Complete Hausa Novel
Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt
Chapter 10 of 18
Page 10
"ai Kuma shine babban matsalar abokina domin yarinyar itama ta kafe akan bata sonka amman nasan da zaka mata magana da kanka zata iya amincewa kayi k'okarin ka shawo kanta da kanka dan Allah ,ka kwantar da kai ka shawo kanta yarinya nan yar'uwarka ce jininka ce sannan ita din mace ce ,mace Kuma 'yar rarra..."
"ban son iskanci MB ya katseshi a matukar tsawace yana furzar da huci mai zafi daga bakinsa " sbd me zaka fad'a min hk ?" how dare you talk to me like that ? “
shiru mb yayi yana mamakin yadda abokin nashi ke saurin daukar zafi akan abinda bai kai ya kawo ba "to me ma ya fad'a da zai dauki zafi haka ?mr ATA ya mike zumbur daga Kan kujerar da yake zaune tare da tura kujerar baya tamkar ita tayi masa laifi ya soke hannunsa daya cikin aljihun wondonsa "Ita din makiyata ce ita din ba jini bace karka sake fad'a min cewar yaruwata ce ko jinina ce Ka dinga sanin irin maganar da zaka fad'a min taya da girmana da mutuncina zakace na tunkareta common mace daita yarinyar da umarni kawai zan bata kuma dan dolenta tabi ,ta Inda yake shiga bata nan yake fita ba "
Shikenan kayi hakuri abun ne yazo hk amman dai ka k'okarta ka....."dan Allah malam ka maida hankalinka jikinka sai wani qoqarin son saka min magana abaki kake wannan ai mgnr banza ce "ka tsaya ka saueareni mana nifa hankalina yana jikina kai dai.... "dan Allah malam kayi min shiru babu wani saurararka da zanyi a yanzu ".yana gama fad'ar hk yay disconnecting din Kiran yana huci ..."
"Nonsense girl kawai ai bata Isa ba ,bata ma kai wannan matsayin ba shi da mata ke bi suna kuka suna rokonsa ko gaisawa su dingayi bai kaskantar da kanshi ya amince ba bare har ya ajiye girmansa matsayinsa komai nashi yace yana son mace macen ma irinta ko cikakken minti biyar bai yi da katse kiran ba kiran hjy zulaiheart ya shigo sai da gabansa yayi wani irin mummu nar fad'uwa kusan yanzu duk sanda zai ga kiranta sai hankalinsa ya tashi saboda yasan Kiran baya wuce akan wannan banzar yarinyar bane ."
ilai kuwa yana d'auka da maganar ta fara "Adamcy kana son ganin 'bacin raina yayi saurin girgiza mata Kai kmr yana gabanta "wallahi zan cire hannuna acikin lamarinka idan haka kake so "kiyi hakuri sweetheart inshallahu zanyi yadda kike so "kullum abinda kake fad'a kenan ka kasa aiwatarwa dan hk ka shirya shigowa nigeria dan cikin satin nan maryam zata dawo Kuma tana dawowa zaayi mgnr aurenku da baba babba har ta gama maganarta bai sake cewa qala ba ganin tayi shiru shima yayi shiru yaki cewa komai duk da yaso komai yaya ya bata hakuri amman zafin da zuciyarsa keyi ta hanashi aiwatar da hakan har kusan minti goma tana jin yadda numfashinsa Ke sauka da karfi kamar wanda yayi gudun tsare da kyar ya iya fezgo magana "sweetheart akwai abubuwan da nake son na kammala bazan samu damar dawowa nan kusa ba zaku iya yin .."
"No babu wani uzuri da zanyi maka kayi duk abinda zakayi ka gama ka shigo cikin satin nan shiru ya sake yi yana sauraronta tana gama fad'ar haka ta katse Kiran bayan wayar ta katse ya bita da kallo zuciyarsa na rawa ."ajiye wayar yayi akan makeken table din dake office din ya buga wani uban tagumi wanda dagani na takaici ne."
ya sake had'e fuskar nan tashi sosai wani irin bakinciki yake ji acikin zuciyarsa, ji yayi kamar zuciyarsa zata kama da wuta yana matukar jin bakinciki abinda mahaifiyarsa take bukatar yayi ,shi da yake adduar komai ya watse a manta komai amman ita kullum burinta bai wuce taga faruwar wannan auren ba .
banda 'bacin rai mai Kona zuciya babu abinda yake ji mikewa yayi ya shiga zariya a office din yana zagaya koina yana zurfafa tunaninsa kafin ya soma magana shi kadai "ya zanyi ?me zanyi ?taya zan soma rayuwa da yarinyar da kake qoqarin amincewa aurenta ? sosai kwakwaluwarsa ta shiga tunani neman mafuta dan dole yasan abun yi kafin mahaifiyarsa tayi masa wannan auren mr ATA ranar kwana yayi yana tunani ."
******
Bayan kwana biyu maryam ta dawo daga Abuja murna gurin nana hauwa'u hjy zulaiheart da sauran 'yammatan gidan babu magana dan sunyi matukar kewarta sosai hira ce ta yaushe gamo ta barke a tsakaninsu sai yamma suka bar gidan haka ma washegari suka cika gidan har da rukkaya makociyarsu anan grã gidansu yake asalinsu nufawa né suna cikin hira rukkaya ta Kalli maryam sannan ta Kalli diyana da nuzla tace "nafi kowa Jin dadin dawowar marsi bari na baku labari nayi wa marsi saurayi kyakkyawa ajin farko ."
maryam ta kalleta tana kwa'be fuska cike
da takaicin Jin maganarta yayinda itama rukkaya
ta kalleta tana sakar mata murmushin jin dadi .
Sai dai a matukar wulakance maryam ta
cigaba da kallonta kamar ta rufeta da dukan
mutuwa sannan ta fara magana cikin fushi da 'bacin rai "bangane kinyi min saurayi ba ance Miki bani da saurayi ne ko ya ? ke da duk fuskarki ta dame da bille kota Ina an watsa miki shi ba'a ce anyi miki saurayi ba sai ni da fuskata take lafiya lau babu zane ko daya ,Kalli bakinki duk a warwatse kamar lefen sakarya shine zakice kinyi min saurayi , karki qara min irin haka wallahi banaso ai kinfini bukatar saurayi ."
Gabad'aya suka kwashe da dariya rukayya kuwa tsayawa tayi tana kallon maryam da mamaki nana hauwa'u kam har da zubewa kasa tare da rike ciki dan dry ."Ina ganin dai baki san aljanu sun shigi marsi ba ko ? ai babu damar ayi mata maganar maza sai hankalinta ya tashi ." nifa ba haka bane Ina da zabi acikin zuciyata Ina da ra'ayin irin mijin da nake son aure ba kowani shasha ba amman dai na barwa zuciya irin mijin da nake so Ke mai bille sai ki rike saurayin dan kinfini bukata ."
rukayya ta Kalli nuzla nuzla ta kalleta sannan a matukar fusace rukayya tace "karki qara cewa fuskata anyi min bille "to karya ne ba'a yi miki ba ? "idan bakya so nace miki hk nima ki barni da batun wani saurayi can tun da bance miki nayi ina son ba wadan da nake dasu ma sun Isheni bana neman qari sun dade a d'akin suna hira akarshe duk suka watse suka kama gabansu."
******
Karfe shabiyu daidai jirgin Mr ATA ya sauka a lagos a haraban gidansu tun kafin jirgin ya k'arasa sauka security's dinsa ke zagaye da gurin har sanda ya sauka , a hankali ya mike yana gyara zaman rigarsa Sannan ya fara takowa daga matattakalar bene yana taku da kyar cikin tafiyarsa nan nashi na Koda yaushe wato tafiya cike da alfarma da izza yana d'aga kafafunsa yana shakar iska da kyar tare da hura hanci escort dinsa already sun fito suna nan tsaye suna jiransa duk Inda ka duba acikin haraban gida masu aiki ne ke Kai kawo suna aiwatar da aikinsu."
yana qarasa saukowa escort dinsa da security's sukayi masa caaaa har zuwa Inda yake tsaye Inda ya fara taku suna biye dashi har zuwa bakin kofar shiga cikin parlour'n mahaifiyarsa na d'aya , yana isowa gurin yaja ya tsaya d'aya daga cikinsu mai suna muzammil ya bud'e masa kofar ya shiga yabi bayansa shi kad'ai rike da bakar jaka ATA bai tsaya akoina ba sai a babban falon mahaifiyarsa ya shiga ya zauna ya kame akan d'aya daga cikin kujerun falon ya d'aura hannunsa d'aya akan gwiwarsa yana d'an jijigawa yaronsa muzammil ya rankwafo ya ajiye masa jakarsa ya bashi izinin tafiya ya juya da sauri ..."
A hankali mami tayi sallama cikin had'ad'd'en falon a zaune ta samesa akan kujera ya lumshe lumtsatsun idanuwanshi ,da kyar ya bude baki ya amsa sallamarta batare daya bud'e idanunshi ko matsowa ba har sanda ta zauna akan kujerar dake kallonsa tana jin sanyi da farinciki mara misaltuwa da ganin kamilallen danta mai nagarta da haiba illarsa dai rashin ajiye iyali da miskilanci da zafin rai duk wannan farinciki daga ciki take jinsa dan bata bayyana shi ba .
a hankali ya bud'e lumtsatsun idanunshi ya mike ya k'araso gabanta ya rusuna har kasa "mun sameku lafiya sweetheart? Wani sanyin dadi Ya ratsata ta kai hannunta kanshi "alhamdulillah ka sauka lafiya ya aiki Ya fama da jama'a ? ta fad'a fuskarta babu yabo babu fallasa "alhamdulillah sweetheart yayi magana yana matukar tausayin Kansa dan yasan tunda ya zo ya dinga cin karo da matsaloli kenan dole sai yayi hakuri dan magana daya ce za'a yita ana mai maitawa ,."
A natse ya mike ya koma mazauninsa ya zauna
yana neman layin M.B da sauran friend's dinsa kafin kace me hjy zulaiheart tasa an cika masa gabansa da kayan itatuwa dabam dabam sai dai babu wanda ya d'auka yaci illa amsa waya da yake ta bangare damba dabam , nana hauwa'u ta shigo ta gaishesa cike da ladabi "yayanmu Ina yini ka dawo lafiya .?"
"Lafiya auta ykk ya fad'a atakaice" lfiya ta bashi amsa da haka sannan ta mike ta koma ciki dan yadda fuskarsa take a murtuke nan komai zai iya faruwa , haka rashida da muna yaran baba qarami sun shigo gaishesa a mutunce , babu yabo babu fallasa ya amsa haka akayita shigowa yi masa sannu da zuwa sai dai ya amsa atakaice ba tare daya bi ta kansu ba maryam ce kawai bata shigo kawo gaisuwa ba har sanda MB ya k'araso sai daya yi sallama a bakin kofar falon aka bashi izini shigowa sannan ya shiga .
ATA bai motsa daga Inda yake ba har MB ya shigo ya zauna cike da tausayin abokinsa dan kallo d'aya zaka masa kasan baya tare da walwala da farinciki har wata siririyar rama yayi "ATA..!" ya kira sunansa anatse ATA bai amsa ba illa zuba masa kwayar idanunshi da yayi yana sauraronsa "yana ga duk ka rame ? shiru yayi bai ce uhm ba bare uhm uhm sai dai ga dukkanin alamun hankalinsa na kanshi "dan Allah ka kwantar da hankalinka komai na duniya mai wucewa ne idan kabi komai a sannu da sannu komai zai zama normal ."
wani huci numfashi ya saki yana sake tsaida idanunshi da gbdy suke cikin damuwa akan mb
sai da yayiwa MB kallon wasu mintuna sannan ya furzar da abinda ya tsaya masa a makoshi mai mugun daci cikin son danne duk wata damuwarsa yace "na rasa yadda zan cire wannan damuwar MB "kallonsa MB yayi yayinda ATA ya Maida idanunshi ya lumshe "Ina zanganta ?ya furta a saman labbansa cikin tsananin damuwa "wa kenan ..?Idanunsa dake lumshe ya d'an bud'esu da kamar bazai yi magana ba sai Kuma ya furta ", princess.."
murmushi MB yayi "ka iya fad'ar sunan nan tamkar kai ka fara tsarashi a duniya "zaka ganta inshallahu Ina maka adduar ta zamo mutun ce ba aljana ba , sai abu na gaba ka fara da abinda mami take so "bana jin zan iya MB zan dai ta bin sweetheart a hankali har sanda zan samo yarinyar ko kuma na samo wata dabam amman wannan guntuwar yarinyar bazata zamo mata a gareni ba sun dade suna tautaunawa kafin daga baya sukayi sallama duk Kuma maganar da suke akunne mami sukayita ,
dan haka ta shaka sosai tun a lokacin ta fara shirya abinda zata masa ."
Tunda masu aikin gidan suka san ATA ya sauka kowan nensu ya shiga hankalinsa hatta shigowarsu part din hjy zulaiheart ya taikaita sannan komai cikin sauri suke yi kasancewar sun san shi dan Oya oya ne duk da ba abincinsu yake ci ba sai na mahaifiyarsa kuma bata zauna ba har washegari tana kan yi masa hidimar abincin da zai ci tare da abokansa Amar, shawul, shamsu MB sun baje a falonsa sai kwasar abinci suke Amar yace "friend duk fa matar da ka aura muddin bata iya girki irin na mami ba zaku samu matsala daita ",Sosai kuwa dan ni dai Ina ganin zan kawo fedy gurin mami a sake bata class na mussaman dan wanan girki yayi inji cewar MB " suka sa dariya banda ATA dake rike da waya yana duba mahimmam bayanai masu shigowa .
Sai daya rage mahimmam abubuwansa sannan
ahankali ya motsa lip's dinsa "gaskiya ne Ina son macen da ta iya girki kuma qala dabam dabam shiyasa kuka ga Ina dojewa auren yarinyar nan dan nasan babu abinda ta iya sai salo da rike waya da shiga social media ,ni Kuma ta Inda za'a samu matsala dani kenan dan bazan yarda da rashin kamun Kai ba.
gbdy suka gyda Kai batare da sunce komai ba sai can shawul yace "ai idan princess dinka ka aura ko bata iya girki ba zaka zauna daita haka har karshen rayuwarka ATA ya sauke numfashi kawai batare da yace uffan ba "kayi shiru ko ba haka bane ? Inji cewar MB "ka'ajiye wannan magana bama zata zo a haka ba am very sure ta iya komai ." Shawul yayi sigili yace " mai kmr mrym me zaiyi da wannan princess din taka ya watsa masa wani mugun kallo "ra'ayina kenan princess bana son mace irin wannan yarinyar da ake kokarin lika min yayi mgnr yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa.
"Wai Kai wayace maka ana auren mace mara kiba a yanzu Kai gaka ba jiki ba , Kai Kashi ita kashi kuzo Kuna haihuwar kasusuwa Kai da zaka samu mai nama irin Marym chubi daita komai zamzam inji cewar Amar gbdynsu babu Wanda bai dara ba MB kam har da fadowa yayi kasa daga kan kujera dan dariya "ko jini zamu dinga haifa ba kasusuwa ba. nafi sonta akan wannan mai siffar aljanu guntuwa gata nan dai fari ne kawai ya taimaki rayuwarta.
nana hauwa'u da mryam dake tsaye a bakin kofar falon hannu nana hauwa'u rike da tiren silver mai d'auke da gasashen kifi anyi raping dinsa ita kuma mryam na rike da tire na harish suka Kalli juna dan sunji abinda suke tautaunawa daga ciki , naunayen ajiyar zuciya nana ta sauke tace "mu shiga sister ta fad'a tana rike tiren hannun maryam dake k'okarin subucewa qirjinta na dokawa tace "a'a sister ke dai ki shiga ke kad'ai bari na tsaya anan har ki fito banason na shiga Ina jin tsoron kar ya disgani agaban abokansa ta k'arasa maganar tare da d'aura tire dake hannunata akan tiren hannun nana hauwa .
suna tsaka da hira suka jiyo sallama a bakin kofar falon MB ya bada izinin shigowa tare da komawa mazauninsa ta shiga a natse ta gaishesu cike da ladabi sai dai kallo d'aya zaka mata kasan ranta a 'bace yake ta tsani taji yayanta yace bai son mrym ko aibantata bare yau a gaban abokansa ."
Amar ya washe baki yana dubanta kana ya soma mata wasa kasance warsu abokan wasa "a'a gasu cubi hauwa fa ,farar mace alkyalbar mata Ina ganin nida madam zamu lalla'bo muzo ki sammana man da kike shafawa kullum ke da maryam kmr bakwa fita rana, gaku na nan dau kmr yanzu kuka sauko daga sama."
tayi masa banza tana jan tsaki a ranta "Ina kika baro mrym dan nasan ke daita 5&6 ne? ta sake sharesa tana kokarin ajiye tiren hannunta wayarta dake rike a hannunta tayi kasa zata fadi madadin ta bar wayar sai tayi k'okarin rikota Aiko tiren gbdy suka sullube a hannunta sukayi kasa tiren kifi ya kife nan take mai ya fara malala gabanta ya buga da karfi nan take jikinta ya kama rawa ta d'ago da sauri ta Kalli Inda ATA yake zaune gabanta na cigaba da fad'uwa ."
wani dogon tsaki ATA yaja kana ya soma magana cikin fushi da zafin rai " kunga irin haukan nasu ba koina zaaje da waya kamar wasu yan kauye "haba ATA me yasa zaka dangantata da Kalmar hauka tsautsayi ne ko babu waya a hannunta hakan zata kasance "shawul karka goyi bayan wad'an yaran sam babu abinda suka iya sai hauka komai na mata basu iya ba basu iya girki ba basu iya gyaran daki ba sam basu iya komai na mata ba yan iskan banza kawai sai aikin rike waya da surutun banza da wofi da maza kije ki dauko abinda zaki gyara min guri kafin na soma kwallo dake, sai naci ubanku daya byn daya kafin na koma idan Kuma baki dawo kin gyara ba kika turo min masu aiki sai na canza miki kamanni stupid kawai ."
fuuuuu ta fita tana zunburo baki a bakin kofar nana hauwa'u ta samu mrym tsaye duk ilahirin jikinta rawa yake gbdy duk ta Kara firgicewa
Ta kalleta tana hawaye bata tsaya yi mata bayani ba ta wuce dan tasan taji komai daya faru."
Kai tsaye kitchen Inda hjy zulaiheart take ta shiga ita Kuma maryam ta gudu tayi dakinsu , nana hauwa'u na gama shiga kitchen ta soma zuba balai "wai mami dole ne sai ya Adam ya auri mrym ne ."
"Dan girman allah me zai hana abar maganar kowa yaje ya auri wanda yayi masa ? mami ta dubeta a natse "me yasa kika fadi hk hauwa wani abu ne ya faru ?"to gashi can sai faman fad'awa su ya amar yake wai bai sonta guntuwa ce fari ne kawai ya ceceta mene mene ko ance masa itama tana son shi ne ? gsky kiyi masa mgn ya daina nima yanzu kafin na fito sai daya tozartani a gaban abokansa shiyasa wallahi ban so zuwa ba ,wallahi duk matar data auresa ta shiga uku da matsalolinsa wallahi ni dai a fasa had'in nan da marsi tana gama fad'ar haka ta juya fuuuu ta fita mami tayi murmushin takaici kawai tana girgiza Kai ,nana bata so komawa bangarensa ba amman babu yadda ta iya haka ta d'auki abun gyara ta koma kafin yaci ubanta ".
******
Washegari da misalin Karfe biyu daidai Kiran aunty shahida ya shigo wayar mrym tana d'auka tace ki samemu a parlour'n mami na biyu bata tsaya ji abinda zatace ba ta katse Kiran ,shiru tayi tana sauke wayar daga kunnenta jiki a sanyaye ta mike ta d'auki mayafin abayar dake sanye ajikinta tayi rolling din kanta ta fito ta nufi parlour'n gabanta na dukan uku uku.
zaune ta iskesu gbdy ya'yan hjy zulaiheart
banda nana hauwa'u ATA zaune yana rike da waya yana daddanawa sau dari zaka gansa to da waya ne ko system yana operate "samu guri ki zauna aunty zabiba ta fad'a tana nuna mata kan kujera kasa zama tayi a Inda ta nuna mata .
a hankali ta samu guri ta zauna nesa kadan dasu a qasa dan gudun balain ATA ta kasan idanunta take qare masa kallo sanye yake da dogon wando da riga mai gajeren hannu blue da ratsin fari kayan sun yi masa kyau sosai ga gashin Kan nan nasa sai sheki yake wanda da alama yana shafa man gashi ne yasa yake fitar da sheki ko yaushe ."
"Adam ga mryam nan "inji cewar aunty shahida "naga tantiriya mara kunya mara mutunci , uhm
Ina jinki ki maimaita abinda kika fad'awa aunty a gabana ". sai da gabanta yayi wani irin mugun fad'uwa taji wani abu ya tsarga mata tun daga qirjinta har zuwa kasan mararta take taji marata ta soma murd'awa taji wani abu mai d'umi ya zubo mata wanda bata raba d'ayan biyu na tsananin tsoronsa ne."
ta d'ago kanta a hankali taga har lokacin kanshi na sunkuye yana danna wayar hannunsa "ke har kin Isa kice wai bazaki aureni ba ?tayi saurin sunkuyar da kanta kasa tana sake jin digar wani abu mai zafi na diga a pent dinta wanda babu tantana jini ne yazo mata a dalilin tashin hankalin daya risketa ne
ya cigaba da magana fuskarsa a d'aure tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa "daraja kika ci bancin haka har duniya ta nade baki Isa ba , km baki Kai matsayin da zaki zamo mata agareni ba ."
ta d'an dago kad'an ta saci kallonsa adaidai lokacin daya dago idanunshi suka tsarke cikin nata wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki wanda babu tantama na tsoro ne wani irin mugun kallo yake mata mai firgitarwa "Ina jinki fad'a min abinda kika fad'a masu ?"kaga AD ba dan ka tutsiye yarinyar mutane muka taro anan ba mufi bukatar amincewarta akan komai "no aunty shahida bari ta fad'a taga yadda zanci ubanta ".
"nace abar wannan mgn ta wuce ke mrym kin amince zaki auresa ko kuwa har yanzu baki so dan yau shine final decision domin zamu sanar da mami komai ? "muryarta na rawa tace "na ...na amince .."
"kin amince da me ya fad'a a tsawace yana zaro mata Idanunshi "na amince zan..zan aureka " you are very stupid ,useless kawai tashi ki 'bace min da ganin kafin na miki dukan mutuwa ,bana sonki kuma bazan aureki ba daman nasan baki Isa ki kalleni ki fad'a min abinda kika fada musu ba , maza tashi ki bar nan bana son kallon wannan banzar fuskartaki ya k'arasa maganar yana jan tsaki tare da runtse idanunshi ."
har ta mike zata tashi aunty shahida tace "koma ki zauna tayi saurin girgiza mata Kai tana duban Inda yake zaune tare da jujjuya hannuwanta cike da tsoro "nace ki koma ki zauna a d'ard'ar ta zauna tana kallon kasa a ranta tace "masefaffe banza kar Allah yasa ka aureni nima ai banasonka .
muryarsa a kasalance yace "muddin kuna bukatar na cigaba da zama na saurareku sai wannan yarinyar ta bar falon nan " shiru falon yayi babu wanda yace uffan gashi babu wanda ya Isa yayi mgn sai aunty shahida ko khadija da yake bi bata isa ba bare zabiba da kanwa ce ,aunty shahida ta Kalli maryam tace "mrym kin amince zaki auresa ?tayi saurin gyada mata Kai alamun "eh .!
"Okay tashi ki wuce abunki ta mike da sauri kmr iska ta bar parlour'n "a gsky Adamcy ban ji dadin abinda kayi ba ,a hankali ake bin komai Kai komai zuciya da zafin rai Allah ya sausauta mk zuciyar nan karta sa wata rana kayi nadama iska ya furzar "yanzu tunda ta amince shikenan sai mu sanar da mami aunty shahida ta fad'a tana kallon kannenta mata "eh hk ne suka hada baki gbdy .
"Da izinin wa kenan zaku sanarwa sweetheart .?
"Da fari na amince maku zan aureta amman wannan iskancin da tayi yasa na fasa aurenta har abada km komai zai faru sai dai ya faru amman na fasa "haba yayanmu dan Allah kayi hakuri karkayi haka tunda ta amince ka aureta kawai a wuce wajen tsoronka take ji shiyasa kaji ta fadi hk, cewar zabiba "ka taimakemu karka fasa auren nan kodan mami kabi komai a sannu please "ai bai ma Isa ba tunda ta yarda dole ya aureta ka godewa Allah da kasamu salahar mace mai kamewa kmrta ."
"bafa zan aureta ba I repeat it I can't marry her ,na aureta na kaita Ina da wannan rashin tarbiyar nata ?"yanzu ku baku ga rashin dacewarmu ba ?A tare suka girgiza masa Kai "mu bamu gani ba sai sam barka .Ya girgiza Kai " matar data Kalli tsabar idanunku tace bata son jininku har abar so ce agurinku ?yayi musu tmbyr a matukar fusace"
dukkaninsu kallonsa sukayi yadda jikinsa ke rawa kmr anjonasa masa shocking ."Ku bar ganinta shiru shiru irin wadan nan mutanen abun tsoro ne wallahi gara a bani masefaffiya daita juyin duniya sukayi dashi yace bai sonta km bazai aureta ba "na yarda ku nemo wasu mata ku aura min ko guda hudu ne km a rana daya na amince amman ban da wannan jakar yarinyar mara tarbiya yana gama fad'ar hk ya mike ya kama gabansa kallon junansu sukayi na second goma sannan suka numfasa "yanzu me kuka ga zamuyi ?inji cewar aunty khadeja "mu fad'awa mami kawai tasan komai dan boye boye bashi da wani amfani zan fada amnan mu bari zuwa jibi zan san yadda zan fad'a mata .
atare suka mike suka nufi d'akin hjy zulaiheart tana zaune akan kujera tana duba abubuwan da suka kawo mata suka shigo jikinsu a sanyaye tana ganinsu ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi duk suka yiwa kansu mazauni ta kallesu daya byn daya "Allah dai ya taimakeku gbdy yayi muku albarka yadda kuke tsaye akaina da abinda kuke min dukkaninku Kuna min k'okarin gurin yin abubuwa ."
"da wanda ya bani million daya da wanda ya bani dubu dari da wanda ya bani dubu hamsim dukkaninku abu d'aya ne agurina Kuma inshallahu ladanku daya ne saboda dukkaninku abu d'aya ne
ni dai fatana Allah yayi muku albarka ,kowa yayi abinda zai iya ban da takura kai , Allah ya raya muku zuriarku yadda kuke hidima dani Allah yasa yayanku suyi muku fiyye da haka "Ameen suka had'a baki gurin fad'ar hk.
shiru sukayi babu wanda ya sake kokarin fad'a mata halin da'ake ciki ta d'ago daga duban kayan da suka kawo mata, shiru tayi tare da tsura musu Ido"ya na ga kmar bakwa cikin farinciki alhalin ba haka fuskokinku yake ba a d'azu da kuka zo ? naunayen ajiyar zuciya suka sauke "ku fad'a min idan wani abu ne ? shiru sukayi kowannensu najin tsoron mgnr ta fito daga bakinsa "Kun min shiru ku fad'a min mana Kun tasani gaba Kuna kallona da kyar aunty khadeja ta soma bayani "kiyi hakuri aunty shahida zata fada miki komai amman ba yanzu ba ."
"akan Adamcy ne ko ?ta tmby tana dubansu a tare suka girgiza mata Kai alamun "eh suka tsinci kansu da bata amsa da haka "yanzu har akwai matsalar da zaku boye min bayan bani da kowa daga Allah sai ku duk abinda ya kunno Kai cikin rayuwarmu tare muke had'uwa muke magance matsalar shine yau zaku barni cikin duhu, shikenan na gode karku fad'a dan ko Kun fada min daga baya bazan gode ba Kuna iya tashi ku kama gabanku ."
zubewa sukayi a gabanta kamar zasuyi kuka "kiyi hakuri mami zamu fad'a miki a natse aunty shahida ta zayyane mata komai tun daga ranar da suka fara magana da mrym har zuwa yau din nan "shiru hjy zulaiheart tayi tana sauraron aunty shahida da sauran yaranta mata byn ta gama Jin komai ta numfasa kafin daga bisani tace "shikenan ku barni dashi zan nuna masa ni na haifesa bashi ya haifeni ba daman na dade da sanin baya son farincikina."
nan suka cigaba da tautaunawa "Allah mami ki bud'e masa wuta idan yaga kin haukace masa zai yi abinda kike so "ku barni dashi a yau din nan zai amince ko kuma ya canza uwa aunty shahida tace "duk abun bai kai haka ba ki dai bisa a hankali kar komai ya jagule "babu wani binsa da zanyi ahankali ai shi zuma ne sai ancisa da wuta ake samun kansa daman Ina lallabasa ne na d'auka abun nasa na girma da arziki ne a she wulakanci ne tana gama fad'ar haka ta mike ta nufi d'akinta .." tana shiga aunty khadeja ta mike ta d'auki jakarta ta rataya "ni zan wuce baza'a yi wannan dramar Ina gidan nan ba ,itama zabiba ta mike jirani mu wuce tare gbdy suka mike suka fito tare ."
*******
A bangare mrym kuwa tana shiga d'akinsu ta fashe da matsanacin kuka nana hauwa'u dake zaune ta zabura ta k'araso Inda take ta rungumeta tsam tana tambayarta sai dai taki bata amsa kuka take sosai zuciyarta na zafi da qunci "me yasa ya Adam bai sona ?me yasa nana hauwa'u fada min aibuna da yasa baya Sona ? tayi mgnr hawaye na tsiyayowa daga cikin idanunta ,nan nana hauwa'u ta fahimci dalilin kukanta "Kiyi hakuri marsi baki da wani aibu illa rashin sa'a irin nasa domin sai ya aureki zai san yayi Sa'ar samu mata mai kyakkyawar zuciya."
qaruwa kukan marsi yayi ",yadda bai sona
nima bana son shi amman nayiwa kaina alkwarin zan auresa zan rayu dashi muddin rai " wani murmushin farinciki nana hauwa'u ta saki tare da sake rungumeta ajikinta tana Shirin magana qarar wayar yasa tayi shiru sannan suka saki juna a hankali ta k'arasa ta d'auka tana kokarin fita daga d'akin mrym ta shige bayi ta kulle ta jingina bayanta da kofar ta sulale zuwa kasa tare da sakin wani kuka tana toshe bakinta da sauri nana hauwa'u ta fito zuwa haraban gidan Inda ta iske yayyunta mata da mamaki take kallonsu ",ya haka har zaku wuce ?tafiyar dole ce auta dan yau bom zai tashi a gidan nan Kuma tashin babba ne gara mu san Inda dare yayi mana "daman na kiraki ne dan kisan yadda zaki kwantarwa mrym hankali tare da bata kwarin gwaiwa ."
"Ga ta can kuwa sai kuka take amman ai ta amince zata auri yaya ? " eh ta amince amnan ai shi uban gayyar yace bai yi inji cewar zabiba "Kai!
ta fad'a tare da dafe goshinta "kiyi kokari ta dawo normal inshallahu zuwa jibi zamu shigo idan munji yarda suka kare da mami juya sukayi a tare kowace ta nufi motarta tana tsaye direbobinsu suka jasu sannan ta juya da sauri ta koma ciki. koda ta koma d'akin bata ga mrym ba tana toilet ta kunnawa kanta ruwa tana kokarin daidaita natsuwarta da rarrashin zuciyarta, dole tana bukatar ta rarrashi kanta sannan ta sanyawa zuciyarta hakurin zama dashi ta kowani hali , guri nana hauwa'u ta samu ta zauna abakin gado tana jiran fitowarta ."
Rai a matukar bace hjy zulaiheart ta shiga bangaren ATA tana gama shiga ta fara zuba masa fad'a " tur da haihuwarka Adam " ya waigo a matukar firgice yana zaro Idanu lokaci guda yay fillinging da wayar dake rike a hannunsa ya zube kan gwiwowinsa kasan a gabanta cikin tsananin tashin hankali muryarsa a shake yace "sweetheart me nayi ?"dan Allah ki yafe min ,kiyi min afuwa bazan sake ba."
hjy zulaiheart ta nuna sa da yatsa "Kai Adamcy ban ta'ba sanin baka da hankali da tunani ba sai yau , yau tsawon shekaru Ina binka akan magana daya amman babu komai na rantse da girman Allah bazan sake maka magana akan batun aurenka ba ka cigaba da rayuwarka haka har mutuwa ta riskeka tunda baka san mutuncin kanka ba, ga yarinya yar mutunci yar'uwarka amman dai..."sai tayi shiru tana huci ta kasa cigaba da mgn sai lokacin ya fahimci laifinsa ."
ya sunkuyar da kansa kasa yayinda mami ta cigaba da magana cikin zafin rai "idan baka so maryam ba wa yakamata kaso?" ba dan maryam na diyar dan'uwana ba tana da nagarta da kamun kan da kowani nmj zai sota Kuma mahaifinta nada nagarta da zai zama surukinka "ai ka nuna min ban Isa da Kai ba ko ? to na gode Allah ya saka da alkhairi Allah ya biya ."
"a'a sweetheart wallahi kin Isa dani sai dai zuciyata ta kasa ..."mami tayi saurin tareshi da cewa ",aikin banza daga yau in nice na haifeka to ka fara shirin aurenka da maryam Koda yin hakan yana nufin rasa komai naka ATA ya kalleta da sauri sannan yace "to sweetheart zanyi duk yadda kike so sai dai naso ki dan saueareni kiji ita kanta yarinyar bata ..."
Mami ta juya a matukar fusace tana cewa "bazan saurari komai daga bakinka ba ni dai na fad'a maka muddin nice uwarka ka shirya rayuwar aure da mrym idan baka zo ka sameni da maganar aurenta a daren yau ba na rantse maka da girman Allah sai dai ka nemi wata uwar bani zulaiheart ba kayi abinda nake so shine zaman lafiyarka dani ta karasa fita tana magana cikin tsananin fushi da bata ta'ba yin irinsa ba ."
ATA ya rike kanshi tare da furta "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun"shikenan zuciyarsa ta sake shiga rud'ani kasa ya zame ya zauna akan capet tare da zabga tagumi tunani yake yi yanxu ya zai yi kenan?"shin ya cigaba da kafewa akan ra'ayinsa ne ko Kuma ya hakura ya aureta a wuce gurin ?cike da sanyin jikin ya mike ya nufi bangarenta Yana kokarin shiga part dinta sukayi karo da maryam itama d'akin hjy zulaiheart zata sakmakon kiranta datayi ."
wani irin gigitacen mari ya ɗauketa dashi Sanna ya rufeta da duka "kina hauka ne da zaki hada jikinki danawa ? kasa tayi dafe da kuncinta tana kallon zara zaran yatsun ka'fafunsa dake jere kowannensu dauke da kwantaccen gashi ,koina ajikinta rawa yake "mahaukaciya kawai ko ni sa'anki ne ?ta d'ago tana dubansa sai faman huci yake "Maza ki d'auke wad'an nan banzayen idanun naki akaina wallahi ban taba jin na tsani wani halitta ba kamarki har kece zaki bude baki ki fuskanci 'yan'uwana da Kalmar baki sona saboda ke din dakikya ce da bata san hallici ba yasa kafarsa d'aya ya take mata kafa yana watsa mata kallon banza ."
"ki sani bana sonki kuma har abada bazan soki ba wani abu taji ya caki zuciyarta tare da kafeshi da idanunta da suka canza kala zuwa na bacin rai yayinda wani bakinciki ya tokare mata kahon zuciya wanda yasa hawayen ya cika idanunta amman ta danne taki barin su zuba tunda take baa ta'ba mata wulakanci irin na yau ba wannan shine karo na biyu da ya daura hannunsa ajikinta ranta yayi matukar baci tana son ta bar wajen amman bazata iya ba bazata iya ba dan batasan me zai sake biyowa baya ba ,dan haka ta kife kanta akasa kuka take son tayi amman bata son tayi akan wani banza da bai san darajarta ba ..."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS
AYSHABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.