Best / Popular Hausa Novels

Maradams Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt

Chapter 10 of 18

Page 10

"ai Kuma shine babban matsalar abokina domin yarinyar  itama ta kafe akan bata sonka amman nasan da zaka mata magana  da kanka zata iya amincewa kayi k'okarin  ka shawo kanta da kanka dan Allah ,ka kwantar da kai  ka shawo kanta  yarinya nan yar'uwarka ce jininka ce  sannan ita din mace  ce ,mace Kuma 'yar rarra..."
"ban son iskanci MB  ya katseshi a matukar  tsawace yana furzar da huci mai zafi daga bakinsa " sbd me zaka  fad'a min hk ?" how dare you talk to me like that   ? “

shiru mb yayi  yana mamakin yadda abokin  nashi  ke saurin  daukar   zafi  akan abinda bai kai ya kawo ba "to me ma ya fad'a da zai dauki zafi haka ?mr ATA ya mike zumbur  daga Kan kujerar da yake  zaune tare da tura  kujerar baya tamkar ita tayi masa laifi ya soke hannunsa daya cikin aljihun wondonsa "Ita din  makiyata ce ita din ba jini bace karka sake fad'a min cewar yaruwata ce ko jinina ce Ka dinga sanin irin maganar da zaka fad'a min taya da girmana da mutuncina zakace na tunkareta common mace daita yarinyar da umarni kawai zan  bata  kuma dan dolenta tabi ,ta Inda yake shiga bata nan yake fita ba  "

Shikenan kayi  hakuri abun ne yazo  hk amman  dai  ka  k'okarta ka....."dan Allah malam ka maida   hankalinka  jikinka sai  wani  qoqarin son saka min magana abaki kake wannan ai  mgnr banza  ce   "ka tsaya ka saueareni mana nifa hankalina  yana  jikina kai dai.... "dan Allah malam  kayi min shiru  babu wani saurararka da zanyi a yanzu  ".yana gama  fad'ar hk  yay disconnecting din   Kiran yana huci  ..."

    "Nonsense girl kawai ai bata Isa ba ,bata ma kai wannan matsayin ba shi da mata ke bi suna kuka suna rokonsa  ko gaisawa su dingayi bai kaskantar da kanshi ya amince  ba bare har ya ajiye girmansa matsayinsa komai nashi yace yana son mace macen ma irinta  ko cikakken minti biyar bai yi da katse kiran    ba kiran hjy zulaiheart ya  shigo  sai   da gabansa yayi wani irin mummu nar fad'uwa kusan yanzu duk sanda zai ga kiranta sai hankalinsa ya tashi saboda yasan Kiran baya wuce akan  wannan banzar yarinyar  bane ."

ilai  kuwa yana d'auka  da  maganar ta fara "Adamcy  kana  son ganin 'bacin raina  yayi saurin girgiza mata Kai kmr yana gabanta  "wallahi zan cire hannuna acikin lamarinka idan haka kake so "kiyi hakuri sweetheart inshallahu zanyi yadda kike so "kullum abinda kake fad'a kenan ka kasa aiwatarwa dan hk ka  shirya shigowa nigeria dan  cikin satin nan  maryam  zata dawo Kuma tana dawowa zaayi mgnr aurenku  da baba babba  har ta gama maganarta  bai sake  cewa qala ba ganin tayi shiru shima yayi shiru yaki cewa komai duk da yaso komai yaya ya bata hakuri  amman zafin da zuciyarsa keyi ta hanashi aiwatar da hakan har kusan minti goma tana jin yadda numfashinsa Ke sauka  da karfi kamar wanda yayi gudun tsare da kyar ya iya fezgo magana "sweetheart akwai abubuwan da nake son na kammala bazan samu damar dawowa nan kusa ba zaku iya yin  .."

  "No babu  wani uzuri  da zanyi maka kayi duk abinda zakayi ka gama ka shigo cikin satin nan shiru ya sake yi yana sauraronta  tana gama fad'ar haka ta katse  Kiran bayan wayar ta katse ya bita da kallo zuciyarsa na rawa ."ajiye wayar yayi  akan makeken table din dake office din ya buga wani uban tagumi wanda dagani na takaici ne."

   ya sake had'e fuskar nan  tashi  sosai wani irin bakinciki yake  ji acikin zuciyarsa, ji yayi kamar zuciyarsa  zata kama da wuta yana matukar  jin  bakinciki  abinda mahaifiyarsa  take  bukatar yayi ,shi da yake adduar komai ya watse a manta komai  amman ita kullum burinta  bai wuce taga faruwar wannan auren ba .

banda 'bacin rai mai Kona zuciya babu abinda yake ji mikewa yayi ya shiga zariya a office din  yana zagaya koina  yana zurfafa tunaninsa kafin ya soma magana shi kadai  "ya zanyi ?me zanyi ?taya zan soma  rayuwa da yarinyar  da kake qoqarin amincewa aurenta ? sosai kwakwaluwarsa ta shiga tunani neman mafuta  dan dole yasan abun yi kafin mahaifiyarsa tayi masa  wannan auren  mr ATA ranar  kwana yayi  yana tunani  ."

******
Bayan  kwana  biyu  maryam  ta dawo  daga  Abuja murna gurin  nana hauwa'u hjy zulaiheart  da sauran 'yammatan   gidan babu  magana  dan  sunyi  matukar  kewarta sosai  hira  ce  ta yaushe gamo ta barke a tsakaninsu sai yamma suka bar gidan haka ma washegari  suka cika gidan har da rukkaya makociyarsu anan grã gidansu yake asalinsu nufawa né suna cikin hira rukkaya ta Kalli  maryam sannan ta Kalli  diyana  da nuzla tace   "nafi  kowa  Jin dadin dawowar  marsi  bari na  baku labari    nayi wa marsi    saurayi  kyakkyawa   ajin   farko ."

     maryam   ta  kalleta   tana  kwa'be  fuska cike
da takaicin Jin  maganarta   yayinda  itama rukkaya
ta kalleta tana  sakar mata murmushin  jin dadi  .
Sai dai a matukar  wulakance  maryam ta
cigaba da  kallonta  kamar ta rufeta da dukan
mutuwa   sannan ta  fara  magana cikin fushi da 'bacin rai  "bangane  kinyi min  saurayi ba ance Miki  bani  da  saurayi ne  ko ya    ? ke da duk fuskarki ta dame da   bille  kota  Ina an watsa  miki shi ba'a ce anyi miki saurayi  ba  sai ni  da fuskata take  lafiya lau  babu zane ko daya    ,Kalli  bakinki duk a warwatse  kamar  lefen sakarya shine zakice  kinyi  min saurayi , karki qara min  irin  haka wallahi  banaso ai kinfini bukatar saurayi ."

Gabad'aya  suka kwashe da dariya rukayya kuwa tsayawa tayi tana kallon maryam da mamaki nana hauwa'u kam har da zubewa kasa  tare da rike ciki dan dry  ."Ina ganin dai  baki san    aljanu sun  shigi     marsi  ba ko ?  ai  babu damar  ayi mata  maganar maza sai hankalinta   ya tashi ." nifa  ba  haka bane  Ina da zabi  acikin  zuciyata  Ina da ra'ayin irin mijin da nake son aure ba kowani shasha ba  amman dai  na  barwa zuciya  irin mijin da nake so Ke mai bille sai ki rike saurayin dan kinfini bukata ."

rukayya  ta Kalli nuzla nuzla ta kalleta  sannan a matukar fusace rukayya tace  "karki qara cewa fuskata anyi  min bille "to karya ne ba'a yi miki ba ? "idan bakya so nace miki hk  nima ki barni da batun wani saurayi can   tun da bance miki  nayi ina son ba wadan da nake dasu ma sun Isheni bana neman qari sun  dade  a d'akin  suna hira  akarshe duk suka watse  suka kama gabansu."

******
Karfe   shabiyu   daidai jirgin   Mr ATA ya sauka  a lagos  a haraban  gidansu tun   kafin   jirgin ya k'arasa sauka  security's  dinsa  ke zagaye da gurin har sanda ya sauka , a hankali   ya  mike yana  gyara zaman rigarsa Sannan   ya fara  takowa  daga matattakalar bene yana taku da  kyar cikin  tafiyarsa nan nashi na Koda yaushe wato tafiya cike da alfarma da izza  yana d'aga  kafafunsa yana shakar iska  da kyar  tare  da hura hanci  escort  dinsa already sun fito suna  nan tsaye  suna  jiransa duk Inda ka duba acikin haraban  gida masu aiki ne ke Kai kawo suna aiwatar da aikinsu."

yana qarasa saukowa escort dinsa da security's  sukayi masa caaaa har zuwa Inda yake tsaye Inda ya fara taku suna biye dashi har zuwa bakin kofar  shiga cikin   parlour'n mahaifiyarsa  na d'aya ,  yana isowa gurin yaja ya tsaya  d'aya daga cikinsu mai suna muzammil  ya  bud'e masa kofar  ya shiga yabi bayansa shi kad'ai rike da bakar jaka  ATA   bai tsaya akoina ba  sai  a babban falon  mahaifiyarsa   ya  shiga ya zauna ya kame akan  d'aya  daga cikin kujerun falon  ya d'aura hannunsa d'aya  akan gwiwarsa  yana d'an  jijigawa yaronsa  muzammil  ya rankwafo  ya ajiye  masa  jakarsa  ya  bashi  izinin tafiya ya  juya da sauri  ..." 

A hankali  mami  tayi sallama cikin  had'ad'd'en falon a zaune ta samesa akan kujera ya lumshe lumtsatsun idanuwanshi ,da kyar  ya bude baki ya amsa sallamarta  batare daya bud'e idanunshi ko matsowa ba har sanda ta zauna akan kujerar dake kallonsa tana jin sanyi da farinciki mara misaltuwa  da ganin kamilallen  danta mai nagarta da haiba illarsa dai rashin ajiye  iyali da miskilanci da zafin rai duk wannan farinciki daga ciki take jinsa dan bata bayyana shi ba .

a hankali ya bud'e lumtsatsun idanunshi ya mike ya k'araso gabanta ya rusuna  har  kasa  "mun sameku lafiya  sweetheart? Wani sanyin dadi Ya ratsata  ta kai hannunta kanshi "alhamdulillah ka sauka  lafiya   ya aiki Ya  fama da jama'a ? ta fad'a fuskarta  babu yabo babu fallasa "alhamdulillah sweetheart  yayi magana yana matukar tausayin Kansa dan yasan tunda ya zo ya  dinga cin karo da matsaloli kenan dole sai yayi hakuri dan magana daya ce za'a yita ana mai maitawa ,."

A natse  ya mike ya koma mazauninsa ya zauna 
yana neman layin M.B  da sauran friend's dinsa   kafin kace me hjy zulaiheart tasa an  cika masa gabansa da kayan itatuwa dabam dabam sai dai babu wanda ya d'auka yaci illa amsa waya da yake ta bangare damba dabam , nana hauwa'u ta shigo ta gaishesa cike da ladabi  "yayanmu Ina yini ka dawo lafiya .?"
"Lafiya auta  ykk ya fad'a  atakaice"  lfiya ta bashi amsa da haka sannan  ta  mike ta koma ciki dan yadda fuskarsa take a  murtuke  nan   komai  zai iya faruwa , haka  rashida   da muna   yaran baba qarami   sun shigo  gaishesa a mutunce ,  babu yabo  babu  fallasa ya amsa  haka akayita shigowa yi masa sannu da zuwa sai dai ya amsa atakaice ba tare daya bi ta kansu ba maryam ce kawai bata shigo kawo gaisuwa ba har  sanda MB ya k'araso sai daya yi sallama a bakin kofar falon aka bashi izini  shigowa sannan  ya shiga .

ATA  bai motsa daga Inda yake ba har MB ya shigo ya zauna cike da tausayin abokinsa dan kallo d'aya zaka masa kasan baya tare da walwala da farinciki  har wata siririyar rama yayi "ATA..!" ya kira sunansa  anatse ATA  bai amsa ba illa zuba masa kwayar idanunshi   da yayi yana sauraronsa "yana  ga duk ka rame ? shiru yayi bai ce uhm ba bare uhm uhm sai dai ga dukkanin alamun hankalinsa na kanshi "dan Allah ka kwantar da hankalinka komai na duniya mai wucewa ne idan kabi komai a sannu da sannu komai zai zama normal ."

wani huci numfashi ya saki yana sake tsaida idanunshi da gbdy  suke cikin damuwa akan mb
sai da yayiwa MB kallon wasu mintuna sannan ya furzar da abinda ya tsaya masa a makoshi mai mugun daci cikin son danne duk wata damuwarsa yace "na rasa yadda zan cire wannan damuwar MB "kallonsa MB yayi yayinda ATA ya Maida idanunshi ya lumshe "Ina zanganta ?ya furta a saman labbansa cikin tsananin damuwa  "wa kenan ..?Idanunsa dake lumshe ya d'an bud'esu  da   kamar  bazai yi magana ba sai Kuma ya furta ", princess.."

  murmushi MB yayi "ka iya fad'ar sunan nan tamkar kai ka fara tsarashi a duniya "zaka ganta inshallahu Ina maka adduar ta zamo mutun ce ba aljana ba , sai abu na gaba  ka fara da abinda mami   take so "bana jin zan iya MB zan dai ta bin sweetheart  a hankali  har  sanda zan samo yarinyar ko  kuma na samo wata dabam  amman wannan guntuwar yarinyar  bazata zamo mata a gareni ba  sun dade suna tautaunawa kafin daga baya sukayi sallama duk Kuma maganar da suke akunne mami   sukayita ,
dan  haka ta shaka sosai  tun a lokacin ta fara  shirya abinda zata masa ."

Tunda  masu aikin gidan suka  san  ATA  ya sauka kowan nensu ya shiga hankalinsa hatta shigowarsu part din hjy zulaiheart ya taikaita sannan komai cikin sauri suke yi kasancewar sun san  shi dan Oya  oya ne duk da ba  abincinsu yake ci ba sai na mahaifiyarsa  kuma  bata zauna ba har washegari  tana kan  yi masa hidimar abincin da zai ci tare da abokansa Amar, shawul, shamsu MB  sun baje  a falonsa sai kwasar abinci suke Amar yace "friend duk fa matar da ka aura muddin bata iya girki irin na mami  ba zaku samu matsala daita  ",Sosai kuwa dan ni dai Ina ganin zan kawo fedy gurin mami  a sake  bata class na mussaman dan wanan girki yayi inji cewar  MB " suka sa dariya banda ATA  dake rike da waya yana duba mahimmam bayanai masu shigowa  .

Sai  daya  rage  mahimmam abubuwansa  sannan 
ahankali ya motsa  lip's dinsa "gaskiya ne Ina son macen da ta iya girki kuma qala dabam dabam  shiyasa kuka ga Ina dojewa auren yarinyar  nan dan nasan  babu abinda ta iya sai salo da  rike waya da shiga social  media ,ni Kuma ta Inda za'a samu matsala dani  kenan  dan  bazan yarda da rashin kamun Kai ba.

   gbdy suka  gyda  Kai  batare  da  sunce komai  ba  sai can  shawul yace  "ai idan princess dinka  ka aura ko bata iya  girki ba zaka  zauna daita haka  har karshen rayuwarka ATA ya sauke numfashi kawai   batare da yace uffan ba "kayi  shiru ko ba haka bane ? Inji cewar MB "ka'ajiye wannan magana bama zata  zo a haka ba  am very sure ta iya komai  ." Shawul yayi sigili yace " mai kmr mrym me zaiyi da wannan princess din taka ya watsa masa wani mugun kallo  "ra'ayina kenan princess  bana son mace  irin wannan yarinyar da ake kokarin lika min  yayi mgnr yana furzar da iska mai  zafi  daga bakinsa.

"Wai  Kai wayace  maka ana auren mace mara kiba a yanzu Kai gaka ba jiki ba , Kai    Kashi  ita kashi kuzo Kuna haihuwar kasusuwa Kai da zaka samu mai nama irin Marym chubi daita komai zamzam inji cewar Amar  gbdynsu babu Wanda bai dara ba MB kam har da fadowa yayi kasa  daga kan kujera dan dariya "ko jini  zamu dinga   haifa   ba kasusuwa ba. nafi  sonta  akan wannan  mai  siffar aljanu guntuwa  gata nan  dai  fari ne kawai ya taimaki rayuwarta.

  nana  hauwa'u  da  mryam  dake tsaye a bakin kofar falon hannu nana hauwa'u rike da tiren silver mai d'auke da gasashen kifi anyi raping dinsa  ita kuma mryam na rike da tire na harish   suka  Kalli  juna dan sunji abinda suke tautaunawa daga ciki , naunayen ajiyar zuciya nana  ta sauke tace "mu shiga sister ta fad'a tana  rike tiren hannun maryam  dake  k'okarin  subucewa qirjinta na dokawa tace  "a'a sister  ke dai ki shiga ke kad'ai  bari na tsaya anan  har  ki fito banason na shiga Ina jin tsoron kar ya disgani agaban abokansa ta k'arasa maganar tare da  d'aura  tire  dake hannunata akan tiren hannun nana hauwa .

suna  tsaka da hira suka jiyo sallama a bakin kofar falon MB ya bada izinin shigowa tare da komawa mazauninsa    ta shiga a natse ta  gaishesu  cike da ladabi  sai dai kallo d'aya zaka mata kasan ranta a 'bace  yake ta tsani taji yayanta yace bai son mrym ko aibantata  bare yau a gaban abokansa ."

Amar ya washe baki yana dubanta kana ya  soma  mata wasa kasance warsu abokan wasa   "a'a gasu cubi   hauwa  fa  ,farar mace alkyalbar  mata Ina ganin nida  madam  zamu  lalla'bo muzo  ki sammana man da kike shafawa kullum ke da maryam kmr bakwa fita rana,  gaku na nan  dau  kmr yanzu kuka sauko daga sama."

  tayi masa banza   tana jan tsaki a ranta "Ina kika baro mrym dan nasan ke daita 5&6 ne?  ta sake sharesa   tana kokarin   ajiye  tiren hannunta wayarta dake rike a hannunta tayi kasa zata fadi madadin ta bar wayar sai tayi k'okarin rikota  Aiko tiren  gbdy suka  sullube a hannunta sukayi kasa tiren  kifi ya kife nan take mai  ya fara malala  gabanta ya buga da karfi  nan take jikinta ya kama rawa   ta d'ago da sauri ta Kalli Inda ATA yake zaune gabanta na cigaba da fad'uwa ."

wani dogon tsaki ATA  yaja kana ya soma magana cikin fushi da zafin rai   "  kunga irin haukan nasu ba koina zaaje da waya kamar wasu  yan kauye "haba ATA  me yasa zaka dangantata da  Kalmar hauka tsautsayi ne ko babu waya a hannunta hakan zata  kasance "shawul karka goyi  bayan wad'an yaran sam babu abinda suka iya sai hauka komai na mata basu iya ba basu iya girki ba basu iya gyaran daki ba sam basu iya komai na mata ba yan iskan banza kawai  sai aikin rike waya  da surutun banza da wofi da  maza  kije ki dauko abinda zaki  gyara min guri kafin na soma kwallo dake, sai naci ubanku daya byn daya kafin na koma idan Kuma baki dawo kin gyara ba kika turo min masu aiki  sai na canza miki kamanni stupid kawai ."

fuuuuu ta fita tana zunburo baki   a bakin kofar  nana hauwa'u ta samu  mrym  tsaye duk ilahirin jikinta rawa yake gbdy  duk ta Kara firgicewa
Ta kalleta tana hawaye bata tsaya yi mata bayani ba ta wuce dan tasan taji komai  daya faru."
Kai tsaye   kitchen Inda hjy zulaiheart take  ta shiga  ita Kuma maryam ta gudu tayi dakinsu , nana hauwa'u  na gama shiga kitchen ta   soma zuba balai "wai mami  dole ne sai ya Adam   ya  auri mrym ne ."

"Dan girman allah me zai hana abar maganar kowa yaje ya auri wanda yayi masa  ? mami ta dubeta a natse  "me yasa kika fadi hk  hauwa wani abu ne ya faru  ?"to  gashi can sai faman fad'awa su ya amar yake wai bai sonta guntuwa ce  fari ne kawai ya  ceceta  mene mene  ko ance masa itama tana son shi ne ? gsky kiyi masa mgn ya daina  nima yanzu kafin na fito sai daya tozartani a gaban abokansa shiyasa wallahi ban so zuwa ba ,wallahi duk matar data auresa ta shiga uku da matsalolinsa  wallahi ni dai a fasa had'in nan da marsi  tana gama fad'ar haka ta juya fuuuu  ta fita  mami  tayi murmushin  takaici  kawai tana girgiza Kai ,nana  bata so komawa bangarensa ba amman babu yadda ta iya haka ta d'auki abun gyara ta koma kafin yaci ubanta  ".

******
Washegari  da misalin Karfe biyu   daidai  Kiran aunty shahida  ya shigo wayar mrym  tana    d'auka tace ki samemu a parlour'n mami  na biyu bata tsaya ji abinda  zatace ba ta katse Kiran ,shiru tayi tana sauke wayar daga kunnenta jiki a sanyaye ta mike ta d'auki mayafin abayar dake sanye ajikinta tayi rolling din kanta ta fito ta nufi parlour'n gabanta na dukan uku uku.

     zaune ta iskesu gbdy ya'yan  hjy zulaiheart 
banda  nana hauwa'u ATA zaune yana rike da waya yana daddanawa  sau dari zaka gansa to  da waya ne ko system yana operate "samu guri ki zauna aunty zabiba ta fad'a tana nuna mata kan kujera  kasa zama tayi a Inda ta nuna mata .
a hankali ta samu guri ta zauna nesa kadan dasu a qasa dan gudun balain ATA  ta kasan idanunta take qare masa kallo  sanye yake da dogon wando da riga mai gajeren hannu blue   da ratsin fari kayan sun yi masa kyau sosai ga gashin Kan nan nasa sai sheki yake wanda da alama yana shafa man gashi ne yasa yake fitar da sheki  ko yaushe ."

"Adam ga mryam  nan "inji cewar aunty shahida "naga  tantiriya mara kunya mara mutunci , uhm
Ina jinki ki  maimaita abinda kika fad'awa aunty  a gabana ".  sai da gabanta yayi wani irin  mugun fad'uwa taji wani abu ya tsarga mata tun daga qirjinta har zuwa kasan mararta  take taji  marata ta soma murd'awa  taji wani abu mai d'umi ya zubo mata wanda bata raba d'ayan biyu na tsananin tsoronsa ne."

  ta d'ago kanta a hankali taga har lokacin kanshi na sunkuye yana danna wayar hannunsa  "ke har kin Isa kice wai bazaki aureni  ba ?tayi saurin   sunkuyar da kanta kasa tana sake jin digar wani abu mai zafi na diga a pent dinta wanda babu tantana jini ne yazo mata a dalilin tashin hankalin daya risketa ne
ya cigaba da magana fuskarsa a d'aure tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa  "daraja kika ci bancin haka har duniya ta nade baki Isa ba , km baki Kai matsayin da zaki zamo mata agareni ba ."

ta  d'an dago kad'an  ta saci kallonsa adaidai lokacin daya dago idanunshi suka tsarke cikin nata wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki wanda babu tantama na tsoro ne  wani irin mugun kallo yake mata mai firgitarwa "Ina  jinki  fad'a  min abinda kika fad'a masu ?"kaga AD  ba dan ka tutsiye yarinyar mutane muka taro anan ba mufi bukatar amincewarta akan komai "no aunty shahida bari ta fad'a  taga yadda zanci ubanta  ".

"nace abar wannan mgn  ta wuce ke  mrym kin amince zaki  auresa ko kuwa  har yanzu baki so dan yau shine final decision domin zamu sanar da mami  komai ? "muryarta na rawa tace "na ...na amince .."
"kin amince da me ya fad'a a tsawace yana zaro mata Idanunshi  "na amince zan..zan  aureka " you are very  stupid ,useless kawai tashi ki 'bace min da ganin  kafin na miki dukan mutuwa ,bana sonki kuma bazan aureki ba daman nasan baki Isa  ki kalleni ki fad'a min abinda kika fada musu ba ,  maza tashi ki bar nan bana son  kallon wannan banzar  fuskartaki ya k'arasa maganar  yana jan tsaki tare  da runtse idanunshi ."

har ta mike zata  tashi  aunty shahida tace  "koma ki zauna tayi saurin  girgiza mata Kai tana duban Inda yake zaune tare da jujjuya hannuwanta cike da tsoro  "nace  ki koma ki zauna a d'ard'ar  ta zauna tana kallon kasa a ranta tace "masefaffe banza kar Allah yasa ka aureni nima ai banasonka .

muryarsa  a kasalance yace "muddin kuna  bukatar na cigaba da zama na saurareku sai wannan yarinyar ta bar falon nan  " shiru falon yayi babu wanda yace uffan gashi babu wanda ya Isa yayi mgn sai aunty shahida ko khadija da yake bi bata isa ba bare zabiba da  kanwa ce ,aunty shahida  ta Kalli maryam tace  "mrym  kin  amince zaki auresa ?tayi saurin gyada mata Kai alamun "eh .!

"Okay tashi ki wuce abunki ta mike da sauri  kmr iska ta bar parlour'n "a gsky Adamcy ban ji dadin abinda kayi ba ,a hankali ake bin komai Kai komai zuciya da zafin rai Allah ya sausauta mk zuciyar nan karta sa wata rana kayi nadama  iska ya furzar "yanzu tunda ta amince shikenan sai mu sanar da mami  aunty shahida ta fad'a tana kallon kannenta mata "eh hk ne suka hada baki gbdy .

"Da izinin wa kenan zaku sanarwa sweetheart .?

"Da fari na amince maku  zan aureta  amman wannan iskancin da tayi yasa na fasa aurenta har abada km  komai zai faru sai dai ya faru amman na fasa "haba yayanmu dan Allah kayi hakuri karkayi haka  tunda ta amince ka aureta kawai a wuce wajen   tsoronka take ji shiyasa kaji ta fadi hk, cewar zabiba "ka taimakemu karka fasa auren nan  kodan mami  kabi komai a sannu please "ai bai ma Isa ba tunda ta yarda dole ya  aureta  ka godewa Allah da kasamu salahar mace mai kamewa kmrta  ."

"bafa zan aureta ba I repeat it I can't marry her ,na aureta na kaita Ina da wannan rashin tarbiyar nata ?"yanzu ku baku ga rashin dacewarmu ba ?A tare suka girgiza masa Kai "mu bamu gani ba sai sam barka .Ya girgiza Kai " matar data Kalli tsabar idanunku tace bata son jininku har abar so ce agurinku  ?yayi musu tmbyr a matukar fusace"

   dukkaninsu kallonsa sukayi yadda jikinsa ke rawa kmr anjonasa masa shocking ."Ku bar ganinta shiru shiru irin wadan nan  mutanen abun tsoro ne wallahi gara a  bani masefaffiya daita  juyin duniya sukayi dashi yace bai sonta km bazai aureta ba  "na yarda ku nemo wasu mata  ku aura min ko guda hudu ne  km a rana daya na amince amman ban da wannan jakar yarinyar mara tarbiya  yana gama fad'ar hk  ya mike ya kama gabansa kallon junansu sukayi na second  goma sannan suka numfasa "yanzu me kuka ga  zamuyi ?inji cewar aunty khadeja "mu fad'awa mami  kawai tasan komai dan boye boye bashi da wani amfani zan fada amnan mu bari zuwa jibi zan san yadda zan fad'a mata  .

atare suka mike suka nufi d'akin hjy zulaiheart tana zaune akan kujera tana duba abubuwan da suka kawo mata  suka shigo jikinsu a sanyaye tana ganinsu ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi  duk suka yiwa kansu mazauni ta kallesu daya byn daya "Allah  dai  ya taimakeku gbdy  yayi muku albarka yadda kuke tsaye akaina da abinda kuke min dukkaninku Kuna min k'okarin gurin yin abubuwa ."

"da wanda ya bani million daya da wanda ya bani dubu dari da wanda ya bani  dubu hamsim dukkaninku abu d'aya ne agurina Kuma inshallahu ladanku daya ne saboda dukkaninku abu d'aya ne
ni dai fatana Allah yayi muku albarka ,kowa yayi abinda zai iya ban da takura kai , Allah ya raya muku zuriarku yadda kuke hidima dani Allah yasa yayanku suyi muku fiyye da haka "Ameen suka had'a baki gurin fad'ar hk.

shiru sukayi babu wanda  ya sake  kokarin fad'a  mata halin da'ake ciki ta d'ago daga duban kayan da suka  kawo mata, shiru tayi tare da tsura musu Ido"ya na ga  kmar bakwa  cikin farinciki alhalin ba haka fuskokinku yake ba a d'azu da kuka zo  ? naunayen ajiyar zuciya suka sauke "ku fad'a  min  idan wani abu ne  ? shiru sukayi kowannensu najin tsoron mgnr ta fito daga bakinsa "Kun min shiru ku fad'a min mana Kun tasani gaba Kuna kallona da kyar  aunty khadeja ta soma bayani "kiyi hakuri aunty shahida zata fada miki komai amman ba yanzu ba ."

"akan Adamcy ne ko ?ta tmby tana dubansu a tare suka girgiza mata Kai  alamun "eh  suka tsinci kansu da bata amsa da haka "yanzu har akwai matsalar da zaku boye min bayan bani da kowa daga Allah sai ku duk abinda ya kunno Kai cikin rayuwarmu tare muke had'uwa muke magance matsalar shine yau zaku barni cikin duhu, shikenan na gode karku fad'a dan ko Kun fada min daga baya bazan gode ba Kuna iya tashi ku kama gabanku ."

zubewa sukayi a gabanta kamar zasuyi kuka "kiyi hakuri mami  zamu fad'a miki a natse aunty shahida ta zayyane mata  komai tun daga ranar da suka fara magana da mrym har zuwa yau din nan "shiru hjy zulaiheart tayi tana sauraron  aunty  shahida  da sauran  yaranta mata  byn ta gama Jin komai ta numfasa  kafin daga  bisani tace "shikenan ku barni dashi zan nuna masa ni na haifesa bashi ya haifeni ba  daman na dade da sanin  baya son farincikina."

nan  suka cigaba da tautaunawa  "Allah  mami   ki bud'e  masa wuta idan yaga kin haukace masa zai yi abinda kike so "ku  barni  dashi a yau din nan zai amince ko kuma ya canza uwa  aunty shahida tace "duk abun bai kai haka ba ki dai bisa a hankali kar komai ya jagule  "babu wani binsa da zanyi ahankali ai shi zuma ne sai ancisa da wuta ake samun kansa daman Ina lallabasa ne na d'auka abun nasa na girma da arziki ne  a she wulakanci ne  tana gama fad'ar  haka ta mike ta nufi d'akinta   .." tana shiga  aunty khadeja ta mike  ta d'auki jakarta ta rataya "ni zan wuce baza'a yi wannan dramar Ina gidan nan ba ,itama zabiba  ta mike jirani mu wuce tare gbdy suka mike suka fito tare  ."
*******
A bangare  mrym kuwa tana shiga d'akinsu  ta fashe da matsanacin kuka nana hauwa'u dake zaune ta zabura ta k'araso Inda take ta rungumeta tsam tana tambayarta sai dai taki bata amsa kuka take sosai zuciyarta na zafi da qunci "me yasa ya Adam bai sona ?me yasa nana hauwa'u fada min aibuna  da yasa baya Sona  ? tayi mgnr hawaye na tsiyayowa daga cikin idanunta ,nan nana hauwa'u ta fahimci dalilin kukanta "Kiyi hakuri marsi baki da wani aibu illa rashin sa'a irin nasa domin sai ya aureki zai san yayi Sa'ar samu mata  mai kyakkyawar zuciya."

       qaruwa kukan marsi yayi ",yadda bai sona
nima bana son shi amman nayiwa kaina alkwarin zan auresa zan rayu dashi muddin rai "  wani murmushin farinciki nana hauwa'u ta saki tare da sake rungumeta ajikinta tana Shirin magana qarar  wayar   yasa tayi shiru sannan  suka saki juna a hankali ta k'arasa ta d'auka tana kokarin fita daga d'akin  mrym ta shige bayi ta kulle ta jingina bayanta da kofar ta sulale  zuwa kasa tare da sakin wani  kuka tana toshe bakinta da sauri nana hauwa'u ta fito zuwa haraban gidan Inda ta iske yayyunta mata da mamaki take kallonsu ",ya haka har zaku wuce ?tafiyar dole ce auta  dan yau bom zai tashi a gidan nan Kuma tashin babba ne gara mu san Inda dare yayi mana "daman na kiraki ne dan kisan yadda zaki kwantarwa mrym hankali tare da bata kwarin gwaiwa ."

"Ga ta can kuwa sai kuka take amman ai ta amince zata auri yaya ? " eh ta amince amnan ai shi uban gayyar yace bai yi inji cewar zabiba "Kai!
ta fad'a tare da dafe goshinta "kiyi kokari ta dawo normal inshallahu zuwa jibi zamu shigo idan munji yarda suka kare da mami   juya sukayi a tare kowace ta nufi motarta tana tsaye direbobinsu suka jasu sannan ta juya da sauri ta koma ciki. koda ta koma d'akin bata ga mrym ba tana toilet ta kunnawa kanta ruwa tana kokarin daidaita natsuwarta da rarrashin zuciyarta, dole tana bukatar ta  rarrashi kanta sannan ta sanyawa zuciyarta hakurin zama dashi ta kowani hali , guri nana hauwa'u ta samu ta zauna abakin gado tana jiran fitowarta ."

Rai  a matukar bace hjy zulaiheart ta shiga bangaren  ATA   tana gama shiga ta fara zuba masa fad'a " tur da haihuwarka Adam  " ya  waigo a matukar firgice yana zaro Idanu lokaci guda yay fillinging da wayar dake rike a hannunsa ya zube kan gwiwowinsa kasan  a gabanta cikin tsananin tashin hankali muryarsa a shake yace "sweetheart  me nayi ?"dan Allah ki yafe min ,kiyi min afuwa bazan sake ba."

hjy zulaiheart ta nuna sa da yatsa "Kai Adamcy ban ta'ba  sanin baka da hankali da tunani ba sai yau , yau  tsawon shekaru Ina binka akan magana daya amman babu komai na rantse da girman Allah bazan sake maka magana akan batun aurenka ba ka cigaba da rayuwarka  haka har mutuwa ta riskeka  tunda baka san mutuncin kanka ba, ga yarinya yar mutunci yar'uwarka amman dai..."sai tayi shiru tana huci ta kasa cigaba da mgn  sai lokacin ya fahimci laifinsa ."

        ya sunkuyar da kansa kasa yayinda mami  ta cigaba da magana cikin zafin rai "idan baka so maryam ba   wa yakamata kaso?" ba dan maryam na diyar dan'uwana ba tana da nagarta da kamun kan da  kowani nmj zai sota Kuma mahaifinta nada nagarta da zai zama surukinka  "ai ka nuna min ban Isa da Kai ba ko ? to  na gode Allah ya saka da alkhairi Allah ya biya ."

"a'a sweetheart wallahi kin Isa dani sai dai zuciyata ta kasa  ..."mami  tayi saurin  tareshi da cewa ",aikin banza daga yau in nice na haifeka to ka fara shirin aurenka da maryam Koda yin hakan yana nufin rasa komai naka  ATA  ya kalleta da sauri sannan yace "to sweetheart zanyi duk yadda kike so sai dai naso ki dan saueareni kiji ita kanta yarinyar bata ..."

Mami  ta juya a matukar fusace tana cewa  "bazan saurari komai daga bakinka ba ni dai na fad'a maka muddin nice uwarka ka shirya rayuwar aure da mrym idan baka zo ka sameni da maganar aurenta a daren yau ba   na rantse maka da girman Allah sai dai ka nemi wata uwar bani zulaiheart ba kayi abinda nake so shine zaman lafiyarka dani  ta karasa fita tana magana  cikin tsananin fushi da bata ta'ba yin irinsa ba ."

ATA ya rike kanshi tare da furta "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun"shikenan zuciyarsa ta sake shiga rud'ani   kasa ya zame ya zauna  akan capet tare da zabga tagumi tunani yake yi yanxu ya zai yi kenan?"shin ya cigaba da kafewa akan ra'ayinsa ne ko Kuma ya hakura ya aureta  a wuce gurin ?cike da sanyin jikin ya mike ya nufi bangarenta   Yana kokarin shiga part dinta sukayi karo da maryam  itama d'akin hjy zulaiheart zata sakmakon kiranta datayi ."

wani irin gigitacen mari ya ɗauketa dashi Sanna ya rufeta da duka "kina hauka ne da zaki hada jikinki danawa ? kasa tayi dafe da kuncinta tana kallon zara zaran yatsun ka'fafunsa dake jere kowannensu dauke   da kwantaccen gashi ,koina ajikinta rawa yake "mahaukaciya kawai ko ni sa'anki ne ?ta d'ago tana dubansa sai faman huci yake "Maza ki d'auke wad'an nan banzayen idanun naki akaina wallahi ban taba jin na tsani wani halitta ba kamarki har kece zaki bude baki ki fuskanci 'yan'uwana da Kalmar baki sona saboda ke din dakikya ce da bata san hallici ba yasa kafarsa d'aya ya take mata kafa yana watsa mata kallon banza ."

   "ki sani bana sonki kuma har abada bazan soki ba wani abu taji ya caki zuciyarta tare da kafeshi da idanunta da suka canza kala zuwa na bacin rai  yayinda wani bakinciki ya tokare mata kahon zuciya wanda yasa hawayen ya cika  idanunta amman ta danne taki barin su zuba  tunda  take baa ta'ba mata wulakanci irin na yau ba wannan shine karo na biyu da ya daura hannunsa ajikinta ranta yayi matukar baci  tana son ta bar wajen amman bazata iya ba bazata iya ba dan batasan me zai sake biyowa baya ba ,dan haka ta kife kanta akasa kuka take son tayi amman bata son tayi akan wani banza da bai san darajarta ba ..."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
   MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS
AYSHABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.