Best / Popular Hausa Novels

Maradams Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt

Chapter 13 of 18

Page 14

"Shiru aunty tayi tana jin fad'uwar gaba mai tsanani tafi mintuna ashirin bata ce qala ba habib ya kai hannu ya d'ago ha'barta yana kallon cikin kwayar idanunta dake kwance da ruwan hawaye "male kece karfin gwiwar dake tafiyar da rayuwarmu Kinyi mana komai arayuwar mu ,kin nuna mana tsantsar soyayya ,kin nuna mana daidai da ba daidai ba kin bamu gatan da ba kowa yake samun irinsa ba wato ilimin addini dana boko , kin inganta rayuwarmu mun yaba miki kuma mun jinjinawa qoqarinki garemu da taimakon Allah da taimakon heartbeat gashi har heartbeat ta kammala karatunta kalamai soyayya iri iri dana sanyaya zuciya yake furtawa gareta wanda yake sake tsuma zuciyarta da soyayyarsu "wannan alfarma ce ki fad'a mana ."

Duk   yadda   habib  ya  d'auki lokaci   yana magana sai dai har zuwa wannan lokacin aunty  ta Kasa furta komai garesu   illa numfashin da take  janyowa ahankali tana fitarwa da kyar
sun sake d'aukar tsawon awa d'aya a wannan yanayin batare da ta fitar da abinda ke cikin zuciyarta ba ."sosai idanunta suka canza kala kallonta suka cigaba da yi suna jiran ta fara basu labarinta, yadda suke kallonta haka itama take kallonsu zuciyarta cike da wasi wasi tana son magana amman hakan ya faskara tana tsananin son yaranta ba zataso suji abinda zai d'aga masu hankali har da zai yi silar shigarsu damuwa ba haka zalika bazataso suji irin rayuwar da sukai da mahaifinsu kafin aure ba da irin tozarcin da mahaifinsu ya sha a wajen yan'uwanta ba ,ganinta fad'a masu wannan labarin babban kuskure ne zata aikata ko bama haka ba bata tunanin zuciyarsu zata iya d'auka , zuciyarsu ma bazata iya dauka ba , bazasu iya wannan juriyar ba."

Ahankali ta lumshe idanunta adaidai lokacin da habib ya d'auke hannunsa daga ha'barta har yau tana jin soyayyar mahaifinsu acikin ranta duk da bai duniya amman kullum ta kalli ya'yan da Allah albarkacesu da samu soyayyarsa na qara hauhawa acikin zuciyarta kuma bata jin Kuskure tayi dan ta auresa ".tana kallonsu suka mike atare suka nufi kofar fita kowannensu da abinda zuciyarsa ke tunani akanta dan daman sun san da matukar wahala mahaifiyarsu ta fad'a masu labarinta kasancewarta mace mai tsananin zurfin ciki da rashin son magana ."

bayansu tabi da kallo har suka 'bacewa ganinta bata iya d'auke kwayar idanunta akansu ba byan fitarsu ta gyara zamanta sosai tare da rafka tagumi gabad'aya kuma sai taji babu dadi aranta ji tayi kamar bata kyauta masu ba hakan yasa taji zuciyarta kmr zata kama da wuta ahankali ta mike tsaye cikin sanyin jiki ta isa bakin window falonta ta kai hannunta ta zuge labule tana kallon haraban gidan yaranta ta hango suna tafiya a natse kafad'a da kafad'a wanda kusan kansu d'aya basu tsaya akoina ba sai bakin part din umma "heartbeat  ban san  me yasa haka ke faruwa damu ba  ? bana son ganin kanmu  haka  ina  jin Kmr na kashe  kaina  na  huta  da  wannan rayuwa ".
ya fad'a yana dafe  goshinsa   cikin  tsananin damuwa .

"Subhanallah  after  dad  ka  daina  fadar  haka  karka sake  fad'ar  wannan  kalmar  Allah bazai sa naga  wannan  ranar  ba ,"ka  dinga  addua a duk lokacin  daka  tsinci kanka  cikin tashin hankali ambaton  sunan  allah  zakayi  karka  bari  zuciyarka tafi  karfinka  muryarsa  cike da tashin hankali
"amman  me  yasa anayi  mana  abubuwa  rashin  mutunci  aunty  ta hanani d'aukar   mataki ? "daidai kenan  habib  ,abinda aunty  tayi shine daidai shine abinda kowace uwa ta gari ya dace tayi  idan suna yi muma muna  yi to meye bambamci a tsakanin mai ilimi da  wanda bai dashi ? kowani irin  abu zaka  gani a gidan  nan  ka   d'aure ka  cije ni yanzu damuwata  ba matsalar Aunty hassana bace sanin  inda dangin  mahaifiyarmu  suke  shine babban damuwata ."

       Ya riko hannunta  cikin  nashi   yana  dubanta "ki ciresu  aranki  abinda muka fi  bukata sune  dangin mahaifi , ace yau bamu da dangin mahaifi ko  ba acikinsu muke rayuwa ba shine  babban tashin hankalinmu  "suma  dangin  mahaifiya suna da mahimanci  domin  zuciyarsu  tafi ta  dangin uba tausayi  ,  jikina  na bani akwai abinda yasa suka nisanci  juna  dole  ina  bukatar  nasan haka  har lokacin  aunty tana kallonsu har sanda maryama
ta nufi kofar shiga bangaren umma shi kuma habib ya nufi get din gidan da alamun fita zai yi ta saki labulen tana sauke naunayen ajiyar zuciya ta koma ta zauna cikin zullumi tana tuno rayuwarta ta baya "

Maryama bata iske umma a falo ba dan haka ta samu waje ta zauna akan d'aya daga cikin kujerun falon ta runtse idanunta tana tunani "anya ba wani mummunar abu mahaifiyata ta shuka ba wanda yasa yan'uwanta suka gujeta ita kuma take jin tsoron komawa garesu ba ?"anya ma yan'uwanta su suka d'aura aurenta da mahaifinmu ? anya ma akwai gasky a zamanta da mahaifinmu ? "wad'an nan tambayoyin tayita jerowa kanta wanda bata da mai bata amsa sai mahaifiyarta ko umma ."

shiru ta sake yi tana qoqarin kawar da zarginta akan iyayenta bata san shigowar umma ba sai dai taji an girgizata sannan tayi sauri ta juyo cikin tsoro taga tana kallonta tace "maryama mai kike tunani haka ?na shiga uku ni aseeya kar dai abinda ya faru Kika zauna kina tunani ?" nan da nan ta soma girgiza mata kai alamun "a'a! tana in in nah  "amm uhm Allah umma bashi bane ."umma ta girgiza ka fadanta cikin sanyin murya "kin kuwa san lokacin dana dauka ina miki magana baki sani ba ?na jima anan ina kallonki maryama kina tunanin abinda ya faru d'azu still maryama kai ta girgiza mata alamun" a'a!

Cike da nuna kulawa umma ta juya ta qarasa kitchen inda fridge yake ta isa ta bud'e ta dauko kwalin hollandia ta rufe fridge ta matsa kad'an inda d'an qaramin tray da glass cup's Ke kansa ta d'auki d'aya ta dawo inda take zaune ta janyo kujera gaban maryama ta zauna tana kallonta ta zuba mata hollandia ta mika mata tare da cewa "gashi ki sha dan nasan har yanzu baki sakawa cikinki komai ba ta kai cup bakinta tana kallon umma kad'an ta sha ta kawar da bakinta alamun ya isheta."

"karki sake tunanin abinda ya faru d'azu abinda ya rigada ya faru ya faru karki sakashi aranki yazo ya dameki wani ciwo yaje ya kamaki mu shiga uku dan sai nafi kowa shiga damuwa "Allah umma bashi bane wannan ai idan da sabo na rígada na saba "
"Wani kallo umma tabita dashi tare da sanyaya muryarta tace "idan bashi bane maryama sanar dani matsalarki dan bayan mahaifiyarki baki da wanda ya fini ina jinki tmkr ni na haifeki bancin ke kadai uwarki ta haifa da tuni na kwaceki gbdy daga hannunta , wannan soyayyar da nake miki yasa na janyoki jikina sosai karki ji komai sanar dani damuwarki ta fad'a tana kallonta ."

sunkuyar da kanta kasa tayi tana wasa da yatsun hannunta kusan second goma sannan ta motsa labbanta "daman ba komai bane kawai ina son nasan inda dangin aunty suke, ko sanin labarinta "me yasa bata zuwa wajen yan'uwanta suma kuma me yasa basa zuwa wajenta?" laifin me tayi masu? " me ya faru daita tunda na taso nake ganinta cikin damuwa da raunin zuciya wanda har yasa nima nake jin haka atare dani ."?

Wani dogon ajiyar zuciya umma ta sauke cikin fargaba ta tashi zata wuce har ta juya maryama tayi saurin riko hannunta cikin nata "umma ! ta kira sunanta muryarta na rawa cak umma ta tsaya tare da juyowa fuskarta da tausayawa itama maryama mikewa tayi cikin tsananin tashi hanakali ta rusuna kasa ta daura hannuwanta a saman kafafun umma cikin raunin murya ta fara mgn Kmr zatayi kuka "umma nasan Kinsan komai daya faru da iyayena dan allah karki boye min gskyr dana sanki daita "
umma ta zare hannuta ta sake juyawa "umma Kodai mu din bata hanyar sunah aka haifemu bane ?"

Umma ta juyo da sauri tana dubanta qirjinta na dokawa da karfin gaske "maryama ta gyada mata kai kana ta cigaba da mgn "duk yadda muke da aunty duk shakuwarmu da soyyyar da take nuna mana ta kasa fad'a mana haka kema gashi umma zaki wuce ki barni byn kece kika bukaci kisan damuwata .
"Nasan kinsan komai daya faru ki fada min mu san matsayinmu wata killa ma shine dalilin da yasa muke ganin tasko acikin gidan nan dan girman allah umma karki boye min abinda yafi komai mahimmanci arayuwarmu ki fad'a min na rabu da nauyin dake daskare da qirjina ta qarasa mgnr cike da sheshekar kuka ."

Girgiza kai umma ta shiga yi ta dawo inda take tsaye ta kamota ta zaunar daita akan kujera tana kallonta cike da tausayawa kusan mintuna ashirin sannna ta numfasa tana cewa "ku din ba shegu bane ku din yan halak ne" naunayen ajiyar zuciya maryama ta sauke tana kamo hannu umma cikin nata "kinsan kowani d'an adam da yadda yake kar'bar gaddararsa . wasu mutane basa gane rayuwa duk yadda allah ya rubutawa bawa babu wanda ya isa ya canza maka ita,ita qaddara kuma tana fadawa bawa daidai da yadda allah ya hukunto masa qaddara bata san talaka ba bata san mai kudi ba ,qaddara ce da rabonku ta nisanta mahaifiyarku da yan'uwanta yan'uwanta sun kasa kar'ban qaddarar data fad'a mata amatsayin su na muslimai amman mgn ta gsky ku din yan halak ne sai dai akwai yan'uwanki da'aka samesu bata hanyar aure ba .."

nan take jikin maryama ya kama rawa tmkr mazari ta tsaya tana kallonta tana assessing maganarta umma ta damke mata hannu gam cikin nata tana kallonta tana jin yadda jikinta Ke rawa tamkr mazari , maryama tayi imani bancin a zaune take da ta tabbatarwa kanta kafafuwanta bazasu iya d'aukar ba, da zuwa yanzu ta zube kasa."cikin kyarrrma wasu hawaye masu zafi suka shiga turereniyar zubo mata tana jin wani zafi a qirjinta mara misaltuwa cikin ikon allah allah ya bata ikon furta kalmar "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun shi tayita furtawa tana maimaitawa still jikinta da zuciyarta na rawa ."

Umma ta kalleta cikin sarewa ta cigaba da magana "wannan qaddara ce maryama km kowani bawa da tashi irin kalar qaddarar bata wuce Kan kowa ba , ki godewa  allah  da yasa  ta hanyar aure aka sameku bilkisu na bani tausayi matuka kullum idan na kalleta sai na zubar mata da hawaye , da gatanta da komai tana rayuwa tmkr bata da kowa ,tana rayuwa cikin kaskanci alhalin bata cancanci haka ba tunda taji an samu wasu babu aure taji komai ya tsaya mata cak hatta shi karan kanshi labarin taji ya fita kanta ."

Mahaifiyarki haifaffiyar wannan gari ce anan aka haifeta aka haifi iyayenta ke hatta kakaninta ana aka haifesu sune asalin yan kasa "Idan mutun ya shigo jahar lagos din nan ya tmbyi family's din alhj rafi'u giwa to babu wanda bai san mahaifinta ba ."mahaifinta ko nace dangin mahaifiyarki gbdy masu arziki ne ."mahaifinta alhj rafi'u giwa yana da mata hud'u kinga kenan suna da yan uba a qalla guda talatin sai dai  bazan iya kawo miki sunansu ba ina dai jin Aisha , hauwa wacce suke kira da jiddah abakinta gbdy a gidansu bilkisu ce auta a mata sai kannenta biyu maza dake binta daga kanta mahaifiyarta bata sake haihuwar mace ba haka ma sauran bangaren matan sun daina haihuwa wanda hakan yayi sanadiyar da soyayya mai karfi ya shiga tsakaninta da mahaifinta da yan'uwanta gbdy kowa yana sonta kasancewarta auta a mata "

gabadaya yan'uwan bilkisu masu kudi suka aura daga wanda yake london sai wanda yake Canadá ko American ,mafi yawa daga cikin yan'uwanta suna wata kasa daga maza har mata idan kuma anan ne zaki iske su cikin VI ita kadai ce ta auri talaka marashi ,dan gbdy asalin mahaifinki talakawa ne idan aka cire abban sadam wanda yake da d'an rufin asiri  dan  yana  da  gidan bread da kowa ya dogara dashi amman basu da komai ."

"bilkisu ta taso cikin gata da soyayya da kulawar iyaye tun daga tasowarta har zuwa girmanta duk abinda take so shi takeyi ta taso cikin soyayyar iyaye dana yan'uwa kowa yana sonta sannan ta taso da farinjin samari acikin family's dinsu kasancewarta kyakkyawa hasalima  kyawun  jikinta kika d'auko fuskarki  ce ta mahaifinki  amman km shi din ma baki dauko farinsa  ba dan shi fari ne sol tmkr bature   kmr  yadda  kike  ganinsa a hoto  ." kowa na sonta da nuna mata soyayya ,acikin masoyanta akwai mubarak dake mutuwar sonta, mubarak cousing dinta ne da ubansa da uwarta uwa daya uba daya kuma shima  mahaifinsa  mai  kudin  gaske ne  km shi  kadai   suka  haifa ,bilkisu  na da shekara shabiyar a duniya alokacin tana ss 1 a secondary school  alokacin mahaifiyarta da mahaifin mubarak sukai alkwarin aure a tsakanin  yaransu dan mubarak din zai yi tafiya zuwa american qaro karatu , sun bar mgnr atsakaninsu idan ta gama karatunta na secondary sai ayi musu aure ."

  mahaifinki ussein adam  shima asalin haifaffen garin nan ne haka iyayensa sun kasance su takwas ne a wajen iyayensu mata hud'u maza hud'u umar ,fatima ,gali saadatu ,nazifi fadeela Kmr yadda kikasani , hassana da ussein ne auta ."
yana da shekara ashirin da takwas  a duniya ya fara aiki a gidansu bilkisu  ta sanadiyyar abokin   abban sadam  abdulwahab wanda shi gadi yake a makotansu ." mahaifinki ussein ya kasance direban ne gidansu bilkisu wanda Ke kaita school , idan lokacin tashi yayi ya koma ya d'aukota duk inda zata shike kaita hussein ya kasance mutun ne mai tsananin kirki gashi kyakkyawa aji farko illarsa dai shi din ya kasance talaka ne mai son  jin dadi  arayuwarsa km yana harka da yammata da shaye shaye  sai dai bai ta'ba barin gidansu bilkisu sun san da zaman wannan halin nashi ba a boye yake yi saboda tsira da   aikinsa ."

Maryama  ta  runtse  idanunta tana jin wani tuttukin bakinciki   a zuciyarta. ta d'aura kanta  akan cinyar  umma  ko  zata  samu  sausaucin zugin da zuciyarta take  ,dan tun  baaje  koina ba   ta   fara datasanin  jin  labarin   iyayenta  , mahaifinta manemin mata ne ga shaye shaye a iyan nan  ma kad'ai  ta raina kanta ta sake yarda su   din  marasa gata ne ."

" tun farkon ganin bilkisu da ussein taji  ya  burgeta     daman   shi  Allah   yayi masa  farinjin  mata  dan  atarihinsa  bai  ta'ba  cewa yana  son  mace  ba   dan  har  prouding  yake , wannan yasa ya qara samun kusanci daita sosai , duk abinda taci sai ta rage masa idan zai kaita school ta bashi tun abun yana bashi mamaki har yazo ya daina bashi mamaki ya ajiye  abun amatsayin ita din mai alkhairi ce , shima kma yana kulawa daita sosai dan hatta murfin mota kafin ta fito ya fito ya bude mata sannan  idan   sun  iske an gama assembly  zai tabbatar  da ta  shiga  class  akan  idanunshi  sannan zai  juya ya koma  gida ,ga iya  bada  labari,  ussein ya iya bada  labarin da zai saka mutun nishadi  amman fa ga wanda  yake da mahimanci  a wajensa duk wannan yana cikin abinda yasa bilkisu ta sake sakewa dashi , shiyasa kullum bata da magana sai na fadar kirkinsa a wajen iyayenta wanda har hakan yasa iyayenta suke son batunsa tana sa ayi masa alkhairi na mussaman kullum da irin kyautar da take sa  ayi masa ."

haka rayuwa tai ta tafiya mubarak na kiranta a waya amman sam  bata  bashi  lokacinta  yayinda wata irin shakuwa mai karfin gaske ta shiga tsakanin ussein da bilkisu lokacin da ta kai shekaru sha bakwai ta fahimci ba shakuwa bace kawai a tsakaninsu soyayya ce mai karfi wanda shima zuwa lokacin ya kamu da matsanancin soyayyarta ta yadda ya kasa hakuri sai daya zaunar dani ya fad'a min ciwon dake zuciyarsa yace zai yi qoqarin ya boye nashi domin itama bilkisu ya fahimci irin son da take masa bazai ta'ba barin wannan soyayya ya tabbata a tsananinsu ba domin dai yasan tafi karfinsa tafi  karfin aurensa ita din ba sa'ar
aurensa bace babu ta yadda zai sameta arayuwarsa ."

"Nima na karfafa masa gwiwa ya  danne abinda yake  ji akan  bilkisu na nuna masa bambamci dake tsakaninsu  daita  samun auren irinsu akwai wahala duk  da babu yadda allah baya al'amarinsa shi yayi talaka kum shi yay mai kudi nace yayi addua sai allah ya kawo masa sauki da mafuta , amman alokacin ya sheida min zai ajiye aiki ya nemi wani still dai nice na hana na bashi kwarin gwiwa ya cigaba da aikinsa ya dai rage sakar mata fuska da kusanci daita ."

yana cikin wannan halin kwatsam bilkisu ta bayyana masa soyayyata da fari yaki amincewa hakan yasa ta shiga damuwa mai tsanani har rashin lfy ta kwanta batare da iyayena sun san akanshi take ciwon ba wanda ta kai har dakin daaka bashi a gidan take biyosa tana kukan ya amshi soyayyarta "ya zaunar daita ya fad'a mata gsky soyayya atsakaninsu ba abu ne mai yuwu wa ba duba da matsayinta da nashi , kuka take tana nuna masa babu wani bambamci a tsakaninsu dashi duk abu daya ne a wajen Allah da kalamai masu sanyaya zuciya da soyayya tasa ussein ya amince tunda daman shima yana sonta ranar daya amince aranar yan gidansu suka ga ikon allah domin dai bilkisu ta warke daga rashin lfy da take suka fara gudanar da soyayya ."

" tun tana boyewa har tazo ta fara bayyanawa zuwa lokacin a family's duk wanda yasan bilkisu yasan ussein idan har kana son kaga kyautar bilkisu ko yalwataccen fararta to kayi mata mgnr ussein family's dinta babu wanda bai san ussein direba ba idan ya dauko ta daga school zasu samu waje su parka su sha soyayyarsu ussein yana da yammata masu son shi amman soyayyar bilkisu tayi karfin da bazai iya cigaba da soyayya dasu ba ,wata irin soyayyar ussein Ke nuna mata mai karfi wanda har ta kai yana iya ta 'bata batare data hanashi ba nasan wannan ne saboda ussein na kawota gidan nan wajen mahaifiyarsa akwai lokacin dana shiga bangaren hajiya bata nan na iske su a dakin tana kwance ajikinsa sanye da kayan makaranta ajikinta suna romance ."hajiya mahaifiyar ussein ba ƙaramin jin daɗin haɗuwar bilkisu da ussein tayi ba ganin yadda yaron nata ya fara natsuwa ba kamar daba ba yanzu duk wani harkar mata ya jinginar da ita, haka zalika shaye shayensa yayi sauki sai wanda ba'a rasa ba."

Bayan bilkisu ta kammala karatunta na secondary akace ta fito da miji saboda masoya sunyi mata yawa kowa na sonta da aure km mafi yawansu cikin yanuwa ne sai kawai ta gabatar da ussein amatsayin mijin da zata aura hajiya rahma na gama jin abinda bilkisu ta fad'a ta mike tsaye tana dubanta abun ya mugun girgizata a matukar firgice tace "bilkisu banji abinda kika fad'a da kyau ba ina son ki sake maimaita min ,fad'a min naji da kyau tayi magana a tsawace batare da wata fargaba ba ta sake maimaita abinda ke ranta ai nan take mahaifiyarta da yan'uwanta da suka fito ciki d'aya suka nuna rashin amincewarsu mamakinta ne ya kamasu daman shakuwarsu ba iya nan ta tsaya ba ,har ta kai matakin soyayya juyin duniya akayi daita tace ussein take so har da ikirarin muddin zatayi aure to shi zata aura ,nan fa suka fara raba jaha da mahaifiyarta yan'uwanta kowa zaginta ya shiga yi me zatayi dashi ta rasa wanda zatayi soyayya sai direba common direba zata aura ? ita dai jinsu kawai take amman ita aranta ta kudurta komai zai faru sai dai ya faru amman ita ussein take so km har lokacin mahaifinki na shaye shayensa sai dai ba kowa ke iya fahimtar hk ba km nasan yawon tsaftansa da amfani da turaruka masu kamshi yasa baa ganewa amman mu dake rayuwa a gidan nan mun sani tunda idan yana gida yana shan kayansa a bayan dakin salma lokacin baa gina ba ."

Tashin farko mahaifiyarta tasa akayi kiransa cike
da matsanancin fargaba da tashin hankali ya nufi part dinta bakinsa dauke da sallama ya shiga falon tana zaune akan kujera na alfarma bata amsa sallamar da yayi ba haka zalika bata dubeshi ba tun kafin ayi masa gurin zama yayiwa kanshi yana mai yi sunkuyar da kanshi a kasa agabanta tmkr mai neman gafara ahankali ya furta" hjy barka da dare ta dago kai daga Kan tv ta maida kanshi tana qare masa kallon tsab tana nazarinsa ko kayan kirki ma babu ajikinsa kana kallonsa kasan mataiyaci ne mai yaci bare ya bawa bilkisu shi kuwa kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewar ba cikin natsuwa da kwanciyar hankali yake ba tunda ya samu kiran gaugauwa daga hajiya rahma bai sake samun kwanciyar hankali ba har zuwa yanzu da yake durkushe agabanta sai data gama qare masa kallo sannan ta numfasa ta fara magana a kausashe "meke tsakaninka da bilkisu ?da sauri ya girgiza mata kanshi alamun babu komai ."

Shiru tayi tana cigaba da kallonsa kafin daga bisani ta cigaba da magana cikin bacin rai "kace babu komai ?da sauri ya girgiza mata kai alamun Eh !
"ni nasan akwai komai amman tunda kai da kanka kace babu komai to ya tsaya a babu komai din domin idan ya zamo akwai komai zaka hadu da mummunar bacin raina zan maka abinda har ka matu bazaka manta dani ba sannan daga wannan lokacin aikinka ya qare acikin gidan nan ya dago da sauri yana kallonta a tsorace "haka nake nufi ko kana bin mu bashi ne da ka wani tsareni da ido .?"

ya sake girgiza mata kai alamun a'a ! "to maza ka tashi yanzu yanzu ka tattara komai naka ka bar mana gidan matsiyaci banza kawai ,kaga yarinya qarama shine kake son kayi mata wayo,  guda nawa bilkisun take da zata auri me shekarunka ? Idan km kwadayin  kudin  ubanta  kake  kayi  kad'an kaci . matsayinka  bai kai nan ba, ka  bari ya'yan manya ya'yan  masu  arziki  irinta  su more ba kai matsiyaci ba , matsiyacin  ma wanda ko rigar kirki baka dashi tana zuba ruwan bala'i ya zabura ya mike da sauri zai wuce tace " ba estate din nan ba ko a bakin get din estate din nan aka gaya min anganka wallahi wallahi sai nasa an daure min kai ko nasa a 'batar min da kai idan ma ba son abun duniya da son zuciya irin naka ba ina kai ina bilkisu? kai yanzu kaga dacewarku daita ?da sauri ya girgiza kai "a she kasan gsky maza tashi ka bani guri matsiyaci banza kawai ko maza sun qare a duniya mai bilkisu zatayi da kai da sauri ya qarasa barin  falon bai tsaya jin sauran karashen zancen ba yana fita daga falon bilkisu ta fito daga d'akinta  daman km hayaniyar mahaifiyarta ce ta fito da daita ta tmbyeta ita da wa ye ."

"Nida wannan matsiyacin ne dake neman cutar da rayuwarki "ta bata amsa atakaice tana dauke kanta bilkisu tayi shiru tana nazarinta idan har ta fahimceta da ussein take ? da sauri ta nufi kofar fita ta dakatar daita "idan kika sake kika bar falon nan sai na tsine miki albarka cak ta tsaya tana kallon mahaifiyarta " shasha shar banza da bata san ciwon kanta ba duk cikin yanuwanki wani dan iskan kika ga ya kawo miji Kmr wannan tsukakken da ko kayan kirki babu ajikinsa kullum yana yawo cikin kodaddun kaya ,kisani ko zaki mutu bazaki auresa ba na haramta miki aurensa ke intakaice miki baki da miji sai mubarak dan albarka in sha allahu
a ranar useein ya tattara ya bar gidan ya dawo dakinsa dake nan byn makaranta faidiyya ."

Tun daga ranar lamari ya sake lalacewa domin tunda bilkisu tasan ya bar gidan hankalinta ya tashi ta shiga damuwa sosai ta kauracewa kowa numfashi kawai take acikin gidansu amman rayuwarta da komai nata yana wajen ussein  ta kirasa yafi sau babu adadi bai daukar kiranta da kyar da ban hakuri da turo sakonin ya sauko sannan ta dawo daidai, acikin satin tasan yadda tayi  suka  hadu da ussein maganar gsky ussein na sonta shima bazai iya rayuwa babu ita ba ,sai  dai wulakancin da mahaifiyar  bilkisu tayi masa  da kiransa matsiyaci da tayi  shi  yafi  komai  tunzurashi   ,domin  duk gargadinta a banza ya daukesu babu abinda yasa aransa  kamar cima burin  sake kwace mata yarinya ta kowani hali   sannan bai boye ma mahaifiyarsa komai da irin wulakanci daakayi masa itama kwarin gwiwa ta bashi tunda yarinyar tana son shi a matsiyaninsa talaka  kar ya kuskura ya rabu  daita ai su suke da mace sune a wahala ,  ina son nayi mgn  alokacin  amman  babu halin yi a gabanta domin ussein shine auta km soyayyarsa dabam ce  acikin yayanta  amman dana fad'a masa gsky ya janye kudinrinsa ya rabunmusu da  yarinya "

"nasan duk wannan ne sbd ni abokiyar hirarsa ce
dan duk  gidan nan da yan'uwansa mata bai yarda
da kowa ba sai ni domin yace ina da sirri  wasu abubuwan ma a gabana suka faru ,ussein ya sha kawo min bilkisu bangarena ta yini anan bilkisu na da matukar kirki da son mutane sannan bata da rowa idan zata zo wajena tana kawo min abubuwan amfani ga aiki da take min sam bazakice diyar mai kudi bace bata da son jikinta tana son aiki sosai da son mutane sadam kam ya sha gata a wajenta dan komai ta gani na yara zata siyo ta kawo masa wanda hakan yasa naji ina matukar qaunarta har cikin raina nake jin tausayinta domin tana sakewa ta fada min damuwarta da duk halin da take ciki a gidansu da yawon mgnr aurenta da mubarak da mahaifiyarta ke mata tana nuna mata mubarak yafi ussein sam bata dace da ussein ba ."

"ni kaina nazo na gano bata dace da ussein ba a wani zuwa datai na zaunar daita nace ina son nayi magana daita a matsayinta na kanwata da muka fito ciki daya baa matsayin matar da kanin mijina keso ba ta bani hankalinta ni kuma na fara magana bilkisu ko kinsan ussein yana shaye shaye ? ."tace min "eh !tasani km tayi masa mgn yace da zarar ya auret zai daina ,na numfasa nace "ke kin yarda zai daina ?tace min "eh ! Ko kinsan yana da yammata byn ke ?ta sake ce min eh ai ya rabu dasu Ina son na bata shawara ta auri mubarak ta bar ussein amman ina jin tsoro kar taje ta kwashe ta fada masa tunda idanunta sun rufe shi kuma ya fadawa mahaifiyarsa na samu matsala na kama bakina amman duk wanda ya kalli bilkisu km yasan family's dinta gsky yasan basu dace da juna ba ."

Soyayya ta sake yin karfi a tsakanin ussein da bilkisu dan babu abinda barinsa gidansu bilkisu ya janyo sai tabarbarewar rayuwar bilkisu dan a tunanina ussein ya fara saduwa da bilkisu batare da aure ba ni kaina alokacin naso ace iyayenta sun barta ta aureshi tunda ita taji kuma tagani amman mutanen nan suka ki saboda kyamar talaka , dan da irin rayuwar da suke gara ace aure sukayi, bazan ta'ba mantawa ba wata rana bilkisu ta sameni tana kuka na tmbyeta bata boye min ba ta fada min ciki gareta nan take na shiga damuwa mai tsanani nace "haba bilkisu me yasa zaki sakewa nmj jiki haka ?bakya jin tausayin iyayenki da yan'uwanki bakya gudun ranar da ussein zai juya miki baya ?ina ta mata fad'a Kmr kanwata ta jini ita km tana kuka tace ."na taimaketa acire mata cikin nace babu ruwana bazan saka hannu a kashe rai ba ,muna cikin wannan halin hjy ta shigo ashe taji duk mgnr mu itama cewa tayi abarshi kar acire taje gida zata samu iyayenta sai ayi mgnr aure kawai abu ya bani mamaki kamar wasu yoroba tunda sune ake irin wannan rayuwar dasu sai kayi ciki zaa yi aure km su yin ciki ba wani aibu bane a wajensu murna ma zaayi da samunsa tun daga nan na fahimci duk abinda ussein yake da saka hannun hjy ciki ."

Tô tun daga ranar ban sake saka bilkisu acikin idanuna ba a she byn ta bar wajena ussein ya bata maganin zubar da ciki ta sha koda ta koma gida sai ciwon ciki kwana tayi tana murkususu ciwo har garin allah ya waye ,cikin yaki fita ga ciki yaki daina ciwo iyayenta dai suka gaji suka kira doctor ya dubata byn ya gama dubata ya rubuta mata scan tô a wajen scan ne likita yaga ciki a mahaifarta tunda likita ya soma bayani mahaifiyarta ta rikice ta dimauce ta kasa gane takamaiman abinda yake fada ganin ta rude yace mata wani abu ya gani me kama da gas a mahaifarta amman ta kira wani daga gida yazo nan ta kira Aisha yayar bilkisu hankalinta a tashe  tazo ta samu hjy rahma a reception zaune tayi  tagumi bilkisu zaune a gefenta cikin tsoro da fargaba scan taso cikin ya fita cikin sauki batare da kowa yasani ba hjy rahma  tace Aisha tashiga taji me doctor yake nufi da gas din da ya gani a mahaifar bilkisu ta shiga nan likita ya fad'a mata komai itama tashin hankali tashiga mai tsanani amman sai ta boye ta fito tana cewa uwar ulcer ke damunta nan hankalin mahaifiyarsu ya dan kwanta suka koma gida ."

Aisha ta kira bilkisu zuwa gidanta tana qarasowa bata tsaya wata wata ba ta rufeta da duka sai datayi mata mai isarta kamar zata kasheta sannan ta barta byn ta gama dukanta ta kira kaf yan dakinsu ta sheida  masu sannan  tasa akayi mata wankin ciki aka cire cikin lokacin da hjytr ussein taji babu cikin Kmr ta mutu dan bakinciki har da kuka tayi an cire mata jikanta dan karfin halin irin nata har da tmbyr bilkisu tayi  wa ya cire  mata jikanta  ita km kuruciya  ta fad'a mata tun daga lokacin hjy ta tsani Aisha da yan gidansu bilkisu amman km tana son bilkisu ace warta bazata tsaneta ba dan tana son danta."

Hajiya rahma ta lura tun da bilkisu ta dawo daga gidan Aisha ta  warke sumul babu kwana ciwon ciki ta cigaba  da abubuwanta sai dai Aisha ta kira hjy rahma tace  kar a sake barin bilkisu fito koina  har sanda mubarak zai dawo a daura masu aure abinda bilkisu ta tsani ji kenan dan ta tsani mubarak tsana mai girma bata ma son ana yi mata maganarsa karki ce shima mubarak din mummuna ne dogo ne sosai Kmr ussein sai dai shi baki ne kyakkyawan gaske dan sai dana sa ta nuna min hotonsa a istagram
an kafa wa  bilkisu  takunkunmi rashin fita koina hatta islamiyya ta daina zuwa alokacin sai datayi wata uku babu shiga babu fita kawai tana gida zaune km babu  waya a hannunta an kwace da  wayar hjy rahma take mgn da mubarak ."

Ganin Kmr ta kwantar da kai suna soyayya da mubarak  Kmr gske yasa mahaifiyarta ta dauka ta cire komai aranta  kuma taji dadin hk kulawa da soyayyarta ya qaru ta  zaunar daita tayita nuna mata illar ussein tana qawata mata mubarak zataji dadin rayuwa agidan mubarak alokacin ta tmbayeta ta yarda zata auri mubarak tace eh ta amince wanda ba haka bane acikin ranta  wata rana yan'uwanta gbdy suka zo gidan suna zaune a falon mahaifiyarsu  yayanta abubakar wanda ya kasance first born  a dakinsu yace a barta ta cigaba da rayuwata ta koma islamiyya Kmr kowa dan lokacin saukar alqurninsu ya kusa duk da bata   zuwa baa cire sunanta acikin yan walima ba ba dan me ma zaa hanata rayuwa sbd wani matsiyacin banza  Aisha da sauran yanuwata mata sukace  a'a basu  yarda da fitarta  koina ba shi  km yace abashi dalili gbdy suka kasa sheida masa dalili su dan haka yace dole ta koma islamiyya nasan kuna tunani ko zata hadu da wannan yaron ne yace su barta dashi   idan ta isa tayi Kuskuren haduwa da ussein nan  take uwar  tace "ai bilkisunta ta canza bama zata kunyatata ba yanzu mubarak ne agabanta ."

Cikin satin aka dinka mata sabon uniform ta fara zuwa  islamiyya  Kmr  abun  arziki  sai dai aranar ta samu waya ta kirasa bai shiga ba sai ta kirani nan na tmbyeta kwana biyu da halin da take ciki ,bata boye min komai ba a karshe tace na fadawa ussein ya kunna wayarsa nace mata  "to! na qara da yi mata fad'a kar ta sake yarda dashi  tace taji nan fa suka sake din kewa da ussein soyayya  ta  sake karfi   har tafi nada da zara ta fito daga gida  suke haduwa dashi  km ni na tabbatarwa kaina  bazasu ga junansu su bar junansu  hk ba  tunda sun dandani juna dole sai sunyi wani abu duk da  shiedar zina tana da wahala  "to ! bazan manta ba ranar wata asabar da safe ta fito daga gidansu da nufin zuwa islamiyya kai tsaye dakin ussein ta zarto ashe ana biye daita abaya batasani ba har ta shiga dakinsa  tana shiga suka fara abinda suka saba suna cikin wannan halin sai shigowar mutanen gidansu  sukaji  tana rungume ajikinsa  aiko ranar munga tashin hankalin da bamu ta'ba gani ba ."

Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number  din 1438775094 Aishat abdullahi access idan  an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

      
               Page 18

"wato  afa  akan dai  yarinyar nan ce  da  nazo  akanta  yar  kanin mijina  daya  mutu ya barmana amatsayin  riko  to malam  kamar yadda kasani  banason  yarinyar nan na  tsani  na  ganta  dan  ina ji ajikina  akwai  nasarori  da  anan  gaba  zata  iya  samu  domin soyayyar  da  mutane  suke  nuna mata  kamar  ma aikinka  na  farko bai  ci  ba, yanzu  haka samari  sunfi  biyar  da  suka  nuna suna sonta  sai  dai  dadin  abun  da zarar  sun  zo  lokaci  kad'an   sai su  gudu ."

    "to  ga  aikin  nan  yaci  zaki  ce kamar  aiki  bai ci ba , ai  haka  zasu dinga  zuwa  suna  'bata  mata lokaci  suna  wucewa  batare  da tasamu  wanda  zai  aureta  ba babu  fa  wanda  zai  like  mata acikinsu  sai  matsiyaci da  zarar masu  arziki  sunzo  zasu  gudu ."

"Ai  ni  ba  abinda nake só kenan ba ,ai  bana  son  ko  matsiyaci  ma yazo  wajenta   nafi  son  ta  qare  rayuwarta  a kaskance  a bauta  da  wahala , sai  tawa  yar  saurayin da  yake  sonta  mutun d'aya  ne kuma  ba  wani mai abun  kirki bane  gashi  kace  yarinyata  zata  samu   farinjin  samari  masu  kyau  da kudi sai gashi  sa'banin  haka  nake  gani  madadin  maryama  tayi  bakin jini  acikin  mutane  da samari  duk  banga haka ba ."

"kullum  farinjinta  sake  qaruwa yake  jamaa  suna  matukar  qaunarta  basa  son  kula ya'yana koina  akaje  sai  dai  ace a  gaishe da  maryama  amman  banda ya'yana , wani  abun  bakinciki afa  har  yaran  nawa  suma kullum maryama , suna  matukar  sonta  sunki  su  gane ita din  matsalarsu ce,  ko  wani  abu  nayi  mata  sai dai  kaji  suna  min  fad'a  suna nuna  min  rashin  daidai  nan  ta tsaya  ta  sauke  numfashi da ajiyar zuciya  ,afa  yace  "to  yanzu ki takaita  matsalarki  me  kike son ayi ?

Aunty  salma  ta  gyara  zama  tace "ina  son  a fara  rabata  da ya'yana ina  son  naji  sun  tsaneta  fiyye  da  yadda  nake  jin  tsanarta  acikin  raina  wannan  shine  kawai muradina  kafin  nazo  neman wani bukatar  ."afa  yayi  murmushi yace "ai  wannan  shi  yafi  komai  sauki ki  tafi  gida  kawai  zaki  ga aiki da cikawa  cikin  sati  biyu  masu zuwa , amman  ina  son  ki  dawo kafin  kwanakin su cika  akwai abinda  zan  baki  indai  har  na baki  ki  kai   amfani  dashi  magana  ta  qare  amman  yanzu zan  fara  jaraba  'yan  abinda bazaa  rasa ba ."

aunty  salma  tayi  godiya  ta  ajiye masa  kudi  ta  fice  tana  faman zuba  godiya  tana  cigaba da zagi da  maseefar  kiyayyarta  da maryama  har  ta  fice  daga  gidan afa  ta  dawo  gida  tana saka da warwara  dan ita ko kashe maryama afa  zai  yi  tana só saboda  tsanar  datai  mata  yarinya sai kace lu'u lu'u ai muddin tana  cikin  gidan  sai  ya'yanta  sun  rigata  samun  gidan  aure kafin  tayi  ,idan  kuma  har  zata yi auren  zata sa afa  yayi  mata aikin  da zata  auri  matsiyacin  daya fi ubanta  talauci ."

*****
Bayan  kwana  biyu  da  faruwar wannan  alamarin  maryama  tana tafiya  cikin  kayan  islamiyya ta Ardus-salam   yayinda  hannunta ke rungume  alqurani , yammaci ne duk  mazan  unguwarsu  sun  dawo  daga   aiki  duk  inda  ta  wulga  sai an  kalleta da  shaawar  tafiyarta   tmkr  bata  son  taka qasa tana   cikin  tafiya  taji  tafiya  abayanta  bata  juya ba dan  hakan  baya  daga  cikin d'abiarta ,  sai  ma   qara  saurin da tayi  ta cigaba da  tafiyarta saboda tasan  kowaye  ita yake  bi  zarginta  ma  cikin  samarin  unguwarsu  ne   dan  akwai  masu  nuna  suna  sonta  acikinsu ."

"maryama  wannan  uban sauri haka  da  kike  zabgawa ko dan gudun  kar  na  biyoki ne ?ta  tsaya cak  lokacin  data  fahimci  muryar malamin  islamiyyarsu ne  na Ardus-salam  mlm  yahuza  ta juyo a natse  ta  dubeshi  cikin nikaf dinta  tare  da  girmamawa ta gaishesa  ."ya  gyara  tsayuwarsa  yana kallonta , kunyarta  ita  tafi  komai tsoratashi  ,duk  iya  takun  saurayi  in  har  ya  had'u  da  mace  mai kunya  yana  samun  karaya matuka  a zuciyarsa ."

yayi  dan  murmushi  irin nasu  na ustaz "maryama  har  kullum zuciyata  bata  da  sukuni  jiddan wala  khairan  ,na  kasa mantawa dake  ,bani  da wani  sukuni  face na  samu  amsarki  game  da bukatata  dana  kawo  miki  ."yayi  shiru  tare  da tsayawa  yana sauraron  yaji  me  zatace  nan take  tayi  kicin  kicin  tamkar wacce  aka  tsare  da wuka  zaa yankata sai da ta  dauki  second  goma  sannan  tace "uhm  !sai   kuma  tayi  shiru  ta  qasa  qarasa  abinda zata fad'a  maganar ta makale acikin zuciyarta  shi  kanshi ganin motsa  lip's  dinta  bai  sawa ranshi cewar zatace  uffan ba  bayan  abinda ta furta  ba ."
ba  yau  bane farko haka  zalika  yasan  ba  yau  bane zai  zama   karshe ya  saba tareta a hanya  ta kasa ko  ambaton  sunan shi  bama shi  kadai  ba  kusan  mutane  suna  yawon  fad'ar  haka akanta   bata  da  yawon  surutu  da  saurin  sabo  da  mutun  duk wanda  ka  ganta dashi  tana d'ar d'ar  alamun  tsoro  shima dan matsayin  da  yake  dashi  na malaminta ne  yasa  har  ta tsaya akan  hanya  babu wanda ya kai ta tsaya  dashi  akan  hanya ".

"Maryama  idan  na lura  da yanayin  fuskarki  ba soyayyata bace  baki  amsa ba  amman kuma bazan  tabbatar akan cewar kin amsa  ba  ,tunda a kwayar idanunki kawai  nake  iya  karantawa shine kunya  ce ta  hanaki  ki  fad'ar   abinda  Ke  cikin  zuciyarki maryama  ki  daure  ki sanar dani menenê  acikin  zuciyarki  akaina  ko  zuciyata  zata  samu  sukuni da natsuwa  ?".

shirun  dai  da  baya  só  shi  tayi dan  bata  da  abinda  zatace  masa  ,bazata  iya  wata  soyayya ba  da'ace  ta d'aurawa  kanta  soyayyar  samari  da  lokacin da suke  guduwa  suna  barinta da ba qaramin  tashin  hankali  zata  shiga ba  gara  ta qarasa rayuwarta  haka  tunda  soyayya  ba  dole bane  arayuwar   mutun  haka  ma  aure   sunah ne matukar  mutun  zai  iya  rike   kanshi   domin  acikin
Sahbbai  ma  akwai  wad'an da  suka mutu basuyi aure  ba  dan  haka  mutun  zai  iya zamansa  haka   kuma   aure   da  haihuwa  bashi  bane   karshen   duniya  a ganinta  ko  babu  shi  mutun zai iya  rayuwarsa ."

"hakika   maryama   duk   cikin  unguwar  nan  kai  garin  nan  ma  gbdy  har  cikin  islamiyyarmu banga  diya  macen  da  take  burgeni   kuma   zuciyata  take dawainiya   da tarin  soyayyata  kamar ki ba ki samar  da  amsar  soyayyata a cikin  zuciyarki   ko zan samu farinciki da  sukuni  koda  ta  wata  sigace  da  zan fahimta ."sosai  hankalinta  ya  kai  kololuwar tashi  tama  qasa  tsayuwa  bisa kafafunta , kafafunta suka   shiga karkarwa  ,yana  son  ya  bata dama  ta  wuce  gida  saboda  halin  daya  karanta  atattare  daita amman  kuma  bai  gaji  da  kallonta  ba  kuma shi yasani ko zai kwana  tsaye  atare  daita  bazai gaji  ba , sakina  da kanwata ne suka  zo  zasu  giftasu malam yahuza  yayi  sauri yace "sakina ku tsaya  ga  maryama  tsaye  ku wuce  gida  tare ."

Shukura  ta  kallesa  tana  jin  wani  irin  tuttukin  bakinciki   acikin   zuciyarta   abun  yayi matukar  bata  mamaki  maryama  tare da mlm yahuza malamin da  take  matukar  só  amman  tsoro da  shakkansa   ya   hanata   fito  da  soyayyarsa
"malam ! kawai  tace  tayi  gaba  tana  jan  tsaki  acikin  ranta  dan tasan muddin  tayi a fili ta kad'e  har  ganyenta  dan  mlm  yahuza  babu wasa  wajen  disfila  d'alibai  da  iya  karatu  da  d'aukar  wanka  ga  tsantsar  kyau  shiyasa  kowani  d'alibi  ke  matukar  jin   tsoronsa  a kaf  ardus-salam  babu  malamin  da'ake   shakka  da só kamarsa  da yawa yammata  na   qaunarsa ."sakina  kam   jikinta  a matukar sanyaye  ta  wuce  batare  datayi  mgn  ba  maryama  ta  bita da  idanuwanta  wani  abu ya soki zuciyarta  domin tun safiyar yau ta lura  sakina  ta  canza  mata abun ya  matukar d'aure  mata  kai amman  tayi  mata  uzuri  da cewa yanayin  rayuwa  ne ."

Mlm  yahuza  bai  sake  magana ba sai  tunanin  kunyar  shi da sakina taji  dan  ganinsa  da maryama  yasa  ta  kasa  tsayawa dan haka  yace "maryama  sai  gobe  idan  mun  had'u  a makaranta amman  fa  kisani  bazan  ta'ba  daina  tsaidake  anan  ba har sai ranar  dana  samu  na  cire  kunyar nan  kika  amince min  "Kanta  kawai  ta  gyada  masa muryata  a  matukar sanyaye tace "sai  da  safe  ta  juya  ta  cigaba da  tafiya  a natse  bai  bar wajen ba  sai  da  tayi  nisa  sosai  ta 'bacewa  ganinsa  ."

yana  juyawa  sukai   ido   biyu   da  mlm  umar mai hausa  atare   sukai  murmushi "wato  kai  har  kullum bazaka daina  wahalar da kanka akan maryama ba  ko ?"Mlm yahuza ya qarasa  inda mlm umar yake ya tsaya  yana cewa "ya  zanyi  umar  allah  ya  jarabeni  da  soyayyar  maryama  bazan  iya hakura  daita  ba "kai   kuma  allah  ya  jarabi mata dayawa  da  sonka  ba ?"wannan kuma  damuwarsu  ce ,ai  dama  haka  zaka  fad'a  duk  kuna  son  maso  wani  ,kai  ma ka tausayawa masu  sonka  sai  allah  ya duba lamarinka  ".

"Allah  ma  ya sani  babu  wacce nasan  tana  sona  bare na tausayawa  ya fad'a yana wani  sham kamshi  "Uhm uhm  mutumina  banda  fad'ar son  rai   duk  wanda  ka  fadawa  haka  zai  d'auka  bakasan  abinda kakeyi  ba ,"kaga  umar rabani da wannan  zance  mu  barta  matsawar  bata  sarauniyar  mata zaka  min  ba "karka  duba yanayin  gidansu  maryama  amman  dai  kai  kanka  kasan  tafi  karfin  aurenka , maryama  macece  daya  kamata wani  hamshakin mai kudi  yayi wuf daita ."

dan  murmushi  mlm  yahuza  yayi yace "haka  ne  amman  ai  duk  mace   bata  fi  karfin  auren  nmj ba kuma  kowani   mutun  yana da nashi  matsayin  da  zai  iya  burge mace , kuma  ina  dashi  ina da quality da  mace  zata  soni  koda kuwa   bani   da  kosisi  bugu  da  qari  ita  mace  ba  kudi  take  bukata a soyayya  da  kulawa  take so ni  nan  kuma  zan  kula da maryama   ."

"da  me  zaka  kula  daita ?karka  manta  ita  din  cikakkiyar 'yar boko ce , yarinyar  da  idan  ta  fara aiki  yanzu  sai  ta  d'auki  nauyin ciyar da  mutanen  gidanku  gbdy  dan haka  banga abinda zai sa ka dinga wahalar  da  kanka  kana 'batawa kanka  lokaci  akanta  ba , kayi hakuri ka rabu daita  domin dai babban goro sai  magogin karfe ."

Mlm yahuza  ya  dan ji  zafin maganar  malam  umar dan haka ya  rage  farar  fuskashi "wai me kake  nufi ? kana nufin dan  ita din yar boko ce  tana da  kyau na bugawa a jarida  kana tunanin zata samu aiki  nan  gaba  zai sa ta  iya fin karfin  halittar  ubangiji "? yahuza  abinda  nake  son ka fahimta duk  wad'an nan  abubuwa da  kake  gani  fifiko ne a tsakaninka  da maryama  kawai  abinda  nake so  kaji  aranka  tafi  karfinka tafi  karfin  aurenka  ."

"kaga  dan  allah  mlm ka  barni ka zuba  min  ido ba wahalar banza nake  yi  ba ina cikin zuciyarta kunyar da take yawon nunawa akaina ta wadatar dani cewar nayi mata , nan  gaba kad'an zata fahimtar  dani  ."Ka  dai  bi a sannu kar  wata  rana  kana zaune wani hamshakin  mai  kudi ya shigo har cikin  unguwar  nan  ya  aureta .".

"bari  kaji  babu  wani  mai  kudin da  zai  aureta  domin  suma  masu kudin  sunfi  son ya'yan masu kudi yanuwansu , ita  maryamar da ba  galihu ne  daita  ba ,ai  ba uban da  zai  shigo  cikin  wannan  rubabbiyar  unguwar   ya   kwashta ai  duk wannan  kyawun  nata akan  irinmu  zai  qare "yana  gama fadar haka ya  juya  dan  baya  son  ya  sake 'bata  masa  rai ."

Tafiya  kawai  maryama  take zuciyarta  cike  da  kunci  da  tunani  barkatai  ba  kuma  akan mlm  yahuza  ba   sai  sabon  sauyin  data  gani  akan  fuskar  sakina  dan  na  shukura   mai  sauki ne idan  da  sabo  ta  saba  ita  da yaran  aunty  hassana  haka  suke mata  amman  sakina  fa  basu saba  haka  ba  suna  matukar  qaunar  junansu  tun  suna  yara su din  masoya  ne  na  hakika ."

da  wannan   tunani  ta  qarasa  cikin   gidansu   kai   tsaye   ta  nufi  bangaren su  sakina   domin  tambayarta  dalilin  sauyawarta  ashe  wahala ce  ta  shigo  daita  tana sallama  aunty  salma  tace " Yauwa maryama  d'auki   tsintsiyar  ki   share  min  d'akuna  tas   shine  amsar  sallamar  da aunty salma tayi  mata  kamar  tace  bazatai ba amman  ta  kasa  ta  ajiye alquranin  dake  hannunta  ta  d'auko  tsintsiya  ta  fara  shara  batare  da wata  damuwa  ba ."

tana  shara  aunty  salma  na  zaginta  ita  da  shukura   amman  sakina  na  zaune  batace  komai  ba  sa'banin da da bata  yarda a  zageta  ko  sakata aiki  akan  idanunta  ,tana  shara wani  gurin  da  simiti  wani gurin babu  ga  kuma  sakina  na   zaune ta  d'ago  idanunta  a  natse ta  kalleta  taga  kurar sharar  na zuwa inda  take  muryata a sanyaye tace "sakinata   ina  ganin  sai  kin  d'an  tashi  kinga  kurar  tana  zuwa  inda  kike  ta  wani  watso  mata harara  "ai  gudun  ruwanki  nake  kallo  naga zaki shareni  ko  kuwa   ."?

maryama  tayi  shiru  tsaye  tana karantarta  akwai  wulakanci  acikin   maganarta  "ke  kika  kyaleta  aunty  sakina  amman  banda  jakanta  irin  nata tana   kallon  mutane  suna  zaune zatace  su  matsa , banza  shasha  kawai   mai  siffar  mayu ." inji  cewar  shukara  dake  zaune  kusa  da  aunty  salma  abun  bai  yiwa  aunty salma  dadi  sosai  ba  domin  kuwa  sakina taso ta furta ma  maryama  haka  ba shukura ba  ,sakina  kam  tun maganar  farko  datai  bata  qara ba  ta  tashi  cikin  bacin  rai  ta  shige  daki tana jin  wani  zazzafan  kiyayyar  maryama  ."

Maryama  tayi  shiru  kawai  tana bin    shukura  da  kallo "me  kuma  hakan  yake  nufi  dani ? me na yiwa  sakina  ni  kuwa  daga  jiya zuwa  yau  take  fushi  daita  hk ."tayi wa  kanta  tambayar  da  bata  da mai  bata  amsa  sai  sakina  ita  zagin  shukura  bai  dameta  ba kamar  sauyawar  sakina  ta gyada kanta  ta  cigaba  da  shara  tana tunanin  laifin  da taiwa  sakina  har ta  qarasa  ta  wanke  hannunta  da kafafunta  ta d'auki  quraninta ta shiga  d'aki  inda  sakina  take  zaune  akan  gado  tana  cika  tana batsewa  tana  ganin  maryama ta  sake  had'e rai Kmr  taga  mugun  abu  maryama bata damu ba ta zauna  kusa  daita  ta  soma  janta  da mgn taso  tmbyrta  laifin  da  tayi  mata  amman  ganin  yadda  take barsarwa  yasa  tayi  shiru  daga  karshe ta wuce  zuciyarta  cike  da  matsanancin damuwa ."

*******

Da  misalin   karfe  d'aya   na  ranar  laraba  wanda  yayi  daidai  da sauran  kwana uku  jirgin  mr ata  ya tashi   zuwa   france   amman  har  lokacin  jikinsa   sai  a hankali  daga  matsanancin  ciwon  kai  ya dawo  masa  ciwon  gabobin  jiki  dan  ko  miyo  baya iya  had'eyewa  sosai  mami  ta  sauko  daga  saman   d'akin    mr  ata  tare da  likitansa  byn  mami  ta sallame  doctor  rafeeq  ta  dubi  maryam  da  nana  hauwa'u tace   "yayanku  fa  yau   tsawon  kwana   biyu bashi  da  lafiya  ku  shiga  ku  gaishesa  keda maryama  ,jiki  sanyaye  suka  ce" to!  suka  mike atare  suka   hau sama ."

A natse   sukai  knocking  wanda  nana   hauwa'u  ce  tayi   mryam  na  bayanta  ara'be  kusan  second  goma   suka  d'auka  tsaye sannan  ya  basu   damar  shigowa  d,akin  ,da  sallama  suka  shiga  parlour  suka   gansa  kwance   akan  doguwar  kujerar kushin ya   runtse  idanuwanshi  yana   sanye  da  riga  fari  sol  da  gajeren   wondo  iya  gwiwarsa  yayinda   hannunsa  d'aya  Ke  daidai  saitin  zuciyarsa  ya  d'an  bud'e  idanuwanshi  kad'an  ganinsu  yasa  ya    maida  idanuwanshi  ya  runtse  gam."

nana  hauwa'u  tace "sannu  yayanmu  ya jikin  naka kayi  hakuri  walllahi  bamu  san  baka  da  lafiya ba sai  yanzu  da  mami ta sauko  take  fad'a  mana  " shiru  yayi   bai  amsa  mata ba  nan  da nan  maryam ta  shiga  hankalinta  dan tasan  ita  kam  sai ya  had'a   mata  da  tsaki  muddin  tayi  masa  sannu   suna  zaune  shiru  nana  hauwa'u  ta d'an ta'ba maryam  tana  mai  mata  alamar  ta  gaishesa wani abu mai  d'aci  daya  tsaya  mata a  wuya ta had'iye  ta  bud'e  baki  muryarta na  rawa "yaya  sannu "ta fad'a  atakaice  ilai  kuwa  tunaninta ya tabbata  dan kuwa  bai  amsa  ba  sai  ma  tsakin  daya  ja yana  cewa "auta  ya  bani   abun  na  sha a fridge da  saurinta  ta mike ta isa  inda  qaramin  fridge  dinsa   yake  ta  bud'e  donsimo ta  d'auko  masa ta had'a masa  da  ruwa  ta ajiye  masa  akan  table din  dake  gabansa  ."

"gashi  yaya Allah ya  baka  lafiya  ya  d'an  motsa lip's  dinsa  alamun ya amsa ya mike  zaune  da  kyar  batare  daya  kalli  inda  mrym  take  ba  itama bata sake  kallon  inda  yake  ba sai ma fuskarta  dake  kallon  wani   katon hotonsa  dake manne  da bangon falon   sanye  cikin  kananan  kaya  riga  da  wondo  milk  colour  touch  of  black  ya  zura  hannuwansa  duka  cikin  aljihun  wondonsa idanuwanshi manne da  farin  glass  fuskar  nan  tashi  a had'e  Kmr koda  yaushe  "auta  !
Ya  kira  sunan  nana  hauwa'u  ta amsa da "na'am yaya! "shiga  bedroom  ki d'auko  min wayoyina da sauri  ta shiga wayoyin na kan katifarsa ta  d'auko tana  danna  gefen  wayar  inda  nan take wayar ta kawo  haske  screen ta  duba  fusakar  wayar wata kyakkyawar  fuska ta  gani  kanta  babu  d'ankwali gashin  kanta  ya  zubo kad'an ya rufe mata gefen  idanunta ."

ta tsurawa hoton ido sosai nan ta gane zane ne ba asalin  hoto ba ahankali take tafiya tana  kallon  fuskar  wayar  duk  da  zane  ne  ,amman  yarinyar  tayi  matukar  yi  mata  kyau ta kai  masa  tana cewa "yaya  zanen dake  kan screen din wayarka yayi min kyau  sosai wacece ?"tayi  masa tmbyr  tana duban mrym  da  hankalinta baya kansu yana can kallon mr ata , tana kallon kyaun da allah yayi masa ba abinda yafi  burgeta dashi kamar sheidar sallarsa daya fito masa a saman goshinsa yayi baki tmkr tawadar Allah ."

ahankali zuciyar mr ata  ta soma bugawa da karfin gaske  yana jin tmkr ta kunno masa emotion's din da yake ta qoqarin dannewa acikin zuciyarsa nan da nan idanunshi suka canza kala cikin tunanin da maryam take taji yana  cewa "yarinyar mafarkina ce dana  zanata da hannuna, itace  cikar  burina  ce farincikina ina matukar sonta itace mace ta farko da zuciyata take so  .." jin haka yasa gaban maryam  yayi wani mummunar  faduwa sakamakon jin abinda  ya fad'a ta juyo ahankali ta tsura masa idanunta duk da ba karon farko  kenan ya ta'ba fadar haka agabanta ba amman na yau din yasa taji wani iri a gbdy  ilahirin  jikinta  ta lura baya iya boye fellings dinsa  akan  zanen  ."

ina ma zata ga fuskar yarinyar taga dame tafita da har zuciyarsa ta zabeta alhalin ita din ba gsky bace ?tuna zane ce   yasa ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya mai  had'e da  zallar  kishi "ina  matukar  sonta  auta amamn na rasata a yanzu haka ina son raba rayuwata da tunaninta da duk abinda ya shafeta yana  magana yana  kallon  screen din  wayarsa wanda  Ke  dauke   fuskarta "mun dace da juna ko ?ya tambayi  nana  hauwa'u  yana  lumshe tsumammun  idanuwanshi   dake  cike  da  azaban ciwo ."

Nana  hauwa'u  bata  bashi  amsa  tmyr  da   yayi mata  ba  ta kalli  maryam  dake  tsaye  tana  dubansu   idanuwanta  cike  da  kishi  ajiyar  zuciya ta  sauke  tace "yaya  zamu ce allah ya  baka lafiya "na  tambayeki  baki  bani  amsa  ba ya fad'a a mutukar fusace  yana  watsa  mata  harara "me kace ?" shiru  kawai  yayi  tare  da  tsura  mata idanuwanshi   itama  kallonsa  take  tasan   abinda  ya  tsana  kenan  dan  hk  muryarta na rawa tace "kun..." kun  dace  sosai  kawai  dai  matsalar ita din ba   genuine  bace  wani  dogon  tsaki  yaja  yana  cewa "nonsense !"you  and   this  stupid  girl  should  leave  this  room  right  now "ya fad'a  yana furzar da iska mai   zafi  daga  bakinsa  da sauri ta kamo hannun maryama suka  fice  daga  d'akin ."

Bayan  fitarsu  kwanciya  yayi  yana cigaba da kallon hoton screen  din  wayarsa  dayawa daga cikin hotunta ya  konasu  hatta  tsarka  zanenta dake wuyansa always  yayi  flushing  dinsa  ,kadan ne daga cikin zanenta  suke cikin  d'akinsa   sai  na kan screen  din  wayarsa  suma nan kusa yana sa rai zai rabu  dasu  ya  huta  da  tunaninta  sosai  yake kallonta "muguwa "ya  furta a wahalacce   "kin addabi  rayuwata  kin  hanani  zaman  lafiya  ke  wace  irin  muguwa ce  da  zaki  damun  rayuwata ?ya  tambayi  kanshi  yana  mai  kawar da kansa daga kallonta  yana   tunani "anya  bazan  dinga  zagawa cikin  anguwane  anguwani  ba ko allah zai sa na ganta "? wannan ai hauka ne mr ata  kake  shirin yi ,me  yasa  bazaka  yarda  cewar  yarinyar nan ba  gsky  bace  Kmr  yadda  aka  Ke  fad'a  maka ?
shiru yayi  yana  jin  wani  irin  buguwa  da  zuciyarsa ke  yi  akanta  sosai  yake son raba kanshi da tunaninta  ."

Bangaren  maryam  kuwa   suna  taka  step  tana  maseefa "nifa  shiyasa  bana  son  zuwa  inda yake bashi  da  aiki  sai  maseefa  da  disga  mutun sannan wulakancinsa  baya  qarewa akan kowa sai akaina ko ban shiga  tsabgarsa ba sai ya hada dani ni wallahi bana  son  auren  zan dai  yi  ne kawai dan kun dameni , dan  allah  ku raba ni da aurensa na huta tunda ba'ayin  aure  mutun daya  ." murmushi nana hauwa'u tayi  "na lura kishi kike da zane fa  "babu wani  kishi  sister  amman ka auri mutun zuciyarsa na mafarkin wata aljana can wannan ai sai su shafi  mutun  azo arasa meke damuna "hhhhhhh nana hauwa tayi dariya "yarinya kina da aiki kam dan fasa wannan auren sai dai idan daya daga cikinku ne ya mutu  maryam  taja  tsaki ta  d'auki  hanyar  da  zata kai  ta  d'aki  ta  shige  tayi kwanciyarta dan kar mami  tayi amfani da zamanta  a parlour tayita aikenta  d'akinsa  shi  kuma ya samun damar ci mata  mutunci ."

Mr ata  na kwance akai  knocking kofar falon yana daga kwance ya bawa mai yi knocking din izinin shigowa hisam ne ya shigo cike da kulawa ya qaraso ya zauan yana cewa "a she bakaji dadi ba ? ya amsa da  kai kawai "oh my god  amman dai ba matsalar nan  bace ? "no ! wannan muguwar yarinyar ce "
maganar ta daki kunnuwan hisham ya dan tsaya yana kallonsa  yana nazarin maganarsa "yes  muguwa ce  taki  barin na ganta a zahiri  taki barin zuciyata  ta  zauna  yanzu  ko mafarkinta nayi bata min  magana , bata min murmushi this love is so hurt  wallahi  muguwa ce amman har yanzu ina jin sonta hisham na qasa  cireta  araina  ."

ya sake kallonsa ya girgiza kai cike da tausaya masa ya mike da kyar ya shiga bayin dake ciki ya zubar da yawu ya dawo ya zauna ya sake kallon hisham yaga shi yake kallo fuskarsa da mamaki ya sake  girgiza kai dan gbdy ya fahimci wa yake nufi "gsky wannan yarinyar tana baka wahala " ya langwabar da kanshi gbdy  ya koma kalar tausayi "wallahi yau shekara nawa ina faman da soyayyarta amman sam sam yarinyar nan bata tausayina yayi mgnr duk jikinsa ya sake kana kallonsa kasan bashi da lafiya ."

"da  ba dan baka da lafiya  ba  ai da mun dan dinga zagawaya  cikin unguwani ko zamu ganta ko wanda yasanya  nima  nayi  wannan  tunanina  hisham   amman  bazan  iya  ba  ya  fad'a  yana  lumshe  ido yana  jin  wani  d'aci  a bakinsa wanda ya rasa na meye ,"karka ce haka ata  ka bari  idan  ka samu sauki  kaje  france  ka  dawo  lafiya  sai  mu  fara nemanta " nace bazan  iya  ba  wannan  muguwar yarinyar  kona  ganta  damuwa  zata zame min
a  zuciyata ."

Zuciyarsa  na zafi yace tashi muje ka  d'a zaga gari ko jikinta  zai  rage  nauyin  da  yake "ya fad'a yana jin tsantsar soayyarta na  ratsashi  koina  ajikinsa ya mike da kyar "ata  kayi  zauna  gida  wallahi  jikinka babu  kwari   "karka  damu  muje  kawai tunda kana tare  dani  bani  da  wata  matsala ahankali suka sauko falon  qasa   babu kowa a  falonta   farko da alamun mami  tana  falonta  na  uku yaso sheidawa mami  amman  yasan  zata  hanashi  fita  koina  dan  haka   ta  kofar  baya  suka  fice  dan baya son escourt dinsa su  bishi  ya zauna shiru a gefen hisham dake  tuki  yana ciza lip's  dinsa "ina muka dosa "?cewar hisham ".

muje    gra   dan   ina  ji  ajikina a irin  wuraren  nan zamu  samu muguwar yarinyar nan   "hisham  ya kwashe da  dariya  har da  dukan stearing mota shi  kuwa gogan ya hade rai a she a fili   yayi mgn ba "wai muguwar yarinyar nan wallahi ata baka  da dama
,yanzu  dai  wani gra ne  a kusa damu  ?mr ata yayi  masa  banza  ya maida kallonsa  gefen  titi yana kallon mutane da motocin dake kai  kawo "duk  da kaki kayi mgn bari muje ikeja gra nan ma shiru  yayi  yaki  cewa  komai  "gskiy ata ka iya  bada suna pricess ta tashi da  sarauniya  ta  dawo  muguwa"dan  allah  malam  ban son isknaci ka maida hankalinka ga tuki " ya fad'a  yana nuna masa gaban mota da hannunsa  "naji  amman  yanzu ace taki sa'a   ka ganta  a  zahiri zaka ganeta "wallahi  zan  ganeta ". daga haka bai sake yin magana ba  shiru motar tayi babu wanda ya sake cewa komai  har suka d'auki titin  ikeja ."

Ahankali   Ummah  da  aunty  da maryama  suke  tafiya a hanyar   fitowarsu  titin unguwarsu domin su dauki  hanya zuwa marcaz  duba jikin hafsat diyar aunty  fati , maryamah  ta  hango mlm yahuza ya nufo  hnayar  da  suke  da littafi a hannunsa  da alamar islamiyya zashi  tun daga nesa ya fara raragefen  alamun Kamala ya durkusa har kasa ya gaishe da aunty da Ummah tare da cewa "unguwa zaku né ? maryama ta d'an kallesa ta  d'an  basar dan kar aunty da umma su  fahimci akwai wani  abu atsakaninsu tace" rakiya zanyiwa aunty  tare da umma  zuwa bakin titi ."

" allah sarki ya sake durkusawa har kasa ya  gaidai  umma da aunty duk da yasan tahirin rayuwarta amamn  bai  ta'ba  sanya mahaifiyarta  acikin  kwayar idanunshi  ba  amman ya gane aunty ce mahaifiyarta  dan  ko dan yanayin tsawonsu iri  daya ne , mlm yahuza yayi murmushi yace "dan allah ku dan jirani  minti uku kafin ku isa titi ma na dawo amman dan allah karku tafi a kafa  Ummah  ta d'an yi murmushi tace "kada ka damu dan allah , kada ka wahalar da kanka ba  wani  nisa da inda zamu ba mu gode Kwarai da gaske ."

" a dai min Afuwa ina zuwa  yanzu  Ummah  tace tô shikenan mlm yahuza yayi murmushi ita dai maryama ta bisa da kallon mamaki dan bata san me yake nufi da kafin suje titi ya qaraso ba ummah ta dubeta cikin mamaki "wannan kuma wanene ? wallahi malamin mu né na makaranta islamiyya ummah  tayi shiru domin ta danyi zargin son maryama din yake itama dai marayam taso ta fada mata kasancewar bata boye mata komai amman ganin fadar bashi da wani amfani tunda da zarar ta amincewa mutun ya fara zuwa kwana biyu sai ya gudu batare da laifin komai ba ."

suna tafiya suna hira  har suka karaso bakin titin gwagulori wanda ya dawo sabon titi  a yanzu sakamakon gyaran daaka masa suna tsaye kawai sai ga mota ta nufo inda suke maryama tasha jinin jikinta domin dai tasan bashi da mota amman babu mamaki ko ta abokinsa ce yayi burki agabansu ya fito daga cikin motar "umma  ku shigo na kaiku har inda zaku "maryama shiru tayi mamaki ne ya damu zuciyarta tunda take bata ta'ba jin mlm yahuza ya dan burgeta ba sai yau sosai tayi farinciki da abinda yayiwa mahaifiyarta da ummanta ido kawai ta tsura masa ta cikin nikaf dinta tana kallonsa cikin farinciki shi kanshi ya fuskanci  hakan ."

ya zagaya ya bude masu  mota suka  shiga kafin ya zagaya bangaren direba ya jefa mata wani kallo mai nuna tsantsar so kawai itama ta tsinci kanta da mayar masa da murmushi suka wuce ita kuma ta koma gida duk da  abinda yayi mahaifiyata da ummah  a yanzu bata ji ta  fara jin mlm yahuza acikin zuciyarta ba amman  ta kudirce zata danne zuciyarta ta fara sauraronsa ."

Hud'u  daidai  ta shirya zuwa islamiyya bata tsaya jiran sakina ba  ta  kama  gabanta acikin aji sune na farkon zuwa ita da kawarta subai'a wacce suka qare karatu tare ahankali suke hira fitowar result dinsu kafin malamin da zai daukesu darasin qurani ya shigo sosai taso tayi mata hirar mlm yahuza amman ta kasa har aka cika a ajin mlm abbas ne ya shigo nan da nan suka fara karatu ita dai karatun yau dai tazo makaranta tayisa amman zuciyarta fal da walwala da irin farantawar da mlm yahuza yayi mata dan tana matukar qaunar mahaifiyarta da umma duk wanda yaga girmansu kuma ya mutunta matasu tô lallai zai samu wani babban matsayi acikin zuciyarta most especially mahaifiyarta tana tausayin halin data tsinci kanta ciki yana daya daga cikin abinda yasa ta d'auki komai nata da mahimmanci ."

"ta godewa allah ta kuma ta godewa mahaifiyarta da umman tare da  abban sadam domin sun tsaya akan ganin sun ingata rayuwarta da karatun boko da Arabic tun alokacin da take secondary babu wanda yasa rai zata cigaba da karatunta zuwa jamia sai gashi kwatsam allah ya taimakesu ita da subai'a sun samu scholarship daf da zaa tashi ta shigowar mlm yahuza makaranta  ,taso Kwarai ta gansa tayi masa  Godiya ta fito tana duddubawa ko zata gansa amman bata ganshi ba zuciyarta taso ta gansa farincikin da yasa  iyayenta  take son tayi masa godiya dan tasan dole zai ji dadi acikin ranshi ."

Bayan an tashi daga makaranta bai biyota ba kamar yadda ya saba sai dai kafin ta isa gida kanwarsa nafisa tayi saurin isa inda take daman kuma tasanta sai dai ba aji daya suke ba tana gaba daita sosai suka gaisa tare daita suka cikin gidansu inda suka iske aunty salma a tsakar gida  tana zaune tana waya ganinta tare da nafisa yasa aunty salma kashe wayar suka gaisheta suka wuceta suka shiga bangarensu maryama." suna shiga ta nuna mata wajen zama "nafisa ki zauna ga waje tayi murmushi ta zauna akan kujera ita kuma ta shiga dakin aunty ta duba inda aunty tasaba ajiyar kudi taci saa ta samu naira dari ta dauka ta fito tana cewa nafisa "ina zuwa ."

"nafisa ta mike ta biyota ina zaki bari muje tare maryama tayi dan Jim dan taso ta zauna taje ta siyo mata lamurje ta kawo mata amman bata da choice dole ta barta suka sake fitowa tare kai tsaye bangaren aunty hassana suka shiga tayi sallama ta isketa zaune tare da yaranta babu wanda ya amsa sallamarta bare ya kalli inda take bata damu ba dan ta saba "aunty hassana ina yini akwai lamurje?
"Akwai na nawa zaki tsiya "?amm.. na naira dari ne wani dogon tsaki taja "ai nasan bazaki canza zani ba daga na naira darin babu qari kullum ana waje daya baa cigaba ni  bani kudin ki shiga ki dauka ki bace min da gani ."

Zuciyar  nafisa ta cika da mamakin aunty hassana maryama ta mika mata kudin ta shiga ciki ta dauka suka fito ta mikawa nafisa gashi nafisa babu yawa "kai  haba ai babu komai ai danasan ma kashe kudinki zakiyi da tun farko na hanaki " karki damu ai ba wani abu bane maryama ta fada tare suka shiga bangaren Ummah duk inda maryama tasa kafarta nan nafisa take ajiyewa ta share wa umma gida ta gyara mata koina tare da nafisa suka fito zasu wuce aunty salma ta kirata cike da isa ta isa inda take "kije kiyi min shara "

"Shara !"
Maryama ta furta a hankali?eh ko bazakiyi bane kika tsaya kina maimata min abinda na fada ?zanyi ta fada a taikaice tare suka shiga bangaren aunty salma ta fara shara "aunty maryama kawo na share miki da sauri dan akwai abinda ya kawoni "? itama tashi jinin jikinta dan tunda suke da nafisa  bata taba zuwa inda take ba sai yau "no ki barni na share nima yanzu zan gama ta zauna akan kujera sakina da shukura suka shigo shukura  na ganinta ta washe mata hakora "nafisa yau kece agidanmu ?ta tambayeta murmushi ya sake bayyana akan fuskarta "eh nazo wajen aunty maryama ne "aunty kuma ?ta fada a rude "eh mana aunty ce ai maryama tunda zuciyar babban yayanmu ta kamu da matsanancin sonta dan har wani kirki ya kirkirawa kanshi dan kawai ya aikoni wajenta ta fada batare da wani shakka ba ."

shukura  batace komai ba ta zauna kusa da nafisa " inata son nazo gidanku amman ban samu damar zuwa ba saboda makaranta nafisa tayi murmushi "ai kuwa sai ki arawa kanki lokacin ki dinga zuwa gidanmu tunda yayana ya kamu da soyayyar maryama nasan naki  matsayin sai yafi nawa zance bai yiwa shukura  dadi ba dan haka kawai taji bata son wata halaka a tsakanin maryama da mlm yahuza haka kawai take jin rashin jin dadi aranta ."

Maryama tana gama shara ta fara kokarin wucewa yayinda nafisa take qoqarin mikewa shukura  kuma tana janta  da hira "kinga bari na isar da sakon da aka aikoni gobe ma hadu a islamiyya ta tashi tabi bayansa maryama suka jera har cikin falonsu atare suka zauna akan kujera nafisa na cewa "aunty nah "maryama tayi murmushi "kai nafisa da ki daina ce min aunty kullum fa da sunana kike kirana "ai yanzu komai ya canza baki ji yan karin magana ba sunce idan kidi Ya canza dole ma rawa ta canza nafisa ta fada tana dariya "ya karatu yanzu uzukin nawa ?maryama ta sauya magana dan bata son wata maganar soyayya mlm yahuza yayi mata mutunci Kwarai kuma ta yaba masa amman batu na soyayya bata jin zata iya

yayana ne yace na fad'a miki zai zo zuwa anjima maryama tayi murmushi amman shine tun dazu baki fad'a ba  kika zaunar da kanki "ai ina sane na zauna ina qarewa zabin yayana kallo naga shin haukan da yake akanta ya dace abun mamakin sai naga tafi gaban tunanina ashe da kawai kallonki nake ta fad'a tana dariya "kai nafisa a she haka kike kema?maryama ta fad'a tana murmushi santi nake yi yayana ya iya zabe wallahi maryama nayi matukar farinciki da yaya ya sanar dani Ke yake so kuma har kin amince nan fa yanayin maryama ya sauya daga murmushi da take zuwa mamaki "ita a ina ta amince masa da zai qarar .?

"kun dace da yayana sosai ni daman ina tunani wa yahuza zai dauko mana acikin yammatan dake mutuwar sonshi saboda tsananin kyawunsa da kyawun halinsa uwa uba ilimi kema kuma munyi saa a komai kina dashi taso kwarai ta tsaida nafisa akan yayanta amman kuma sai ta kasa har zuwa lokacin data ciro wata karamar takarda ta bata tace gashi inji yaya in baki hanuna da naki ta fad'a tana shirin tashi daga kan kujerar da take zaune  itama maryama ta tashi ganin tana alamar fita domin rakiyarta da hannunta ta dakatar da maryama "zauna abunki ba sai na wahalar dake ba ki zauna ki karanta sakon yayana cikin tsigar wasa maryama tace "ban son iskanci nafisa naga alamun raini ya fara shiga tsakaninmu ta bude baki "ni kuma  asuwa na raina aunty  amman dai Kiyi zamanki wallahi na gode ?"

Ta koma ta zauna ganin idan ta biye mata sai su kai dare bata gama iskancin ba ta fice ita kuma ta samu waje ta zauna ta bude takarda da nafisa ta bata ."
_Ina son ki takaita kanki  da abinda kikasan zai war gaza farinciki dana gani akan fuskarki ina bukatar ganinki cikin farincikin dana ganinki dashi yau my maryama ina son jin muryarki cikin kunnuwana ina son jin hirarki zanzo yau byn sallah ishai_

Ta sake karantawa ta sauke naunayen ajiyar zuciya ita sam bata jin wata soyayyarsa wata killa da a shekaru biyu da suka gabata yazo lokacin tana shekara shatakwas kuma alokacin maza basu zama abun tsoro a wajenta ba da babu mamaki taji tana sonshi har ma ta iya aurensa amman zatayi kokari ko yaya ta fahimtar dashi illa soyayya gareta ."

ahankali ta jingina jikinta akan kujera tana jin bakinciki abubuwan da suke faruwa daita allah ya bata kyau ya bata ilimi tana da nagarta amman bata san dalilin da maza suke gutunta bayan sun kawo kansu wajenta ba , tana zaune tana tunanin taji sautin muryar aunty salma"maryama !maryama!!ke dan uwarki wannan wani irin rashin mutunci né kalmarta ta katse mata tunaninta ta dawo haiyacinta tana magana cikin bacin rai "au zama ma kikayi dan iskanci ni nawa mijin bai kwanta ya huta ba yana can neman abinda zaku ci shine ke zaki zauna saboda sakarci banza da tunanin banza daga yarinya tazo tana sakarci da munafurci sai ki nemi waje ki zauna kina tunanin iska dana banza da wofi allah dai yasa komai zai faru abanza né tunda bashi da wani amfani ana da kyau amman ya zama na banza ."
"tô ai dole ya zama na banza  tunda mugun hali yayi yawa "

tarasa me ta tsarewa aunty salma  acikin gidan nan zuwa yanzu bata tunanin iya kiyayya ce kawai ta fara tunani har da hassada take mata akan halittar da allah ya bata idan ba haka ba tana mata komai iya bakin gwargwado tayi mata shara tayi mata wanki idan ta kama wanke wanke duk tana yi dan dai a zauna lafiya da kuma kar ayi masu gorin ciyar dasu daake acikin gidan shiyasa sau tari bata son fita tsakar gidansu tafi son tayi zamanta a daki dan da zarar ta fita ko ita ko aunty hassana sai an samu wanda yasata aiki ko ya zageta ko mata gori ."
muryarta a sanyaye tace "yanzu ni aunty salma me nayi miki ?akwai abinda kike bukata da banyi miki ba ?ta rike baki au tambayata ma kike yi  saboda yanzu kin kawo karfi an balaga an balallage an zama iyayen mata ? "

"allah yasa ba ita kadai ta balaga ta zama iyayen mata ba wadan da suka balaga suka zama iyayen mata suna da yawa " suka tsinkayi muryar habib abayansu  yana harararta ta juya tana kallonsa
"zo ki fitar mana daga daki kafin na miki dukan mutuwa "uwarka da ubanka basu isa ba bare kai qaramin dan iska  bazan fita ba idan kana iyawa zo ka fitar dani tattaccen d'an  iska ."

Jin haka yasa cikin fusata ya nufota gadan gadan maryama ta mike da sauri  ta shiga tsakani tana cewa "Uhm uhm after dad babu ruwanka daita "tô wallahi kice mata ta fita ta bar mana dakinmu "au har wani takama kake da dakin aro? "dakin aro ne a aka bawa uwarka  byn kai a kusa da dakin kashi aka haifeka idan bakasani ba kasani ga dakin daaka yi cikinka ga masai Shege ma shegen girman tsiya anyi mugun gado a wajen uwa ".

Ya daga hannu zai kai mata mari maryama ta rike hannunsa a rikice cikin muryar kuka tace "haba habib ka barta mana ta fadi duk abinda take son fad'a ai bakinta ne tunda mu din ba shegu bane meye abinda zai dameka arziki kuma  na allah né "kinga makira banason iskanci da munafurci ki barshi yayi min abinda ya ga dama amman gamawarsa ke da wuya zanci uwarsa da shi kansa dan wallahi duk iskanci da yayi akan uwarsa zan rama dan ita ce daidai ni ba shi qaramin dan tasha  ba ,yana yawo suki suki duk yunwa ta gama cinyesa tayi maganar cikin daga murya ".

"Dan allah   kiyi  hakuri  karki saka aunty cikin fadan nan habib yayi Kuskure amman kiyi hakuri bazai sake ba habib ka bata hakuri ".
"What!"
"Allah ya tsareni na bawa wannan matar hakuri kar allah yasa tayi hakuri ko ki fitar mana da wannan mahaukaciyar matar koni yanzu najata na fitar daita sha shar mata mara sallah mai dotti kawai hannu aunty salma ta daga zata wanke masa mari taji ya rike mata hannu sannan ya tsura mata idanunshi cikin sarkewar murya yace "kin gama ta'ba lafiyar kowa acikin gidan nan yanzu ke har yanzu a tunaninki kin kai matsayin da zaki cigaba da marena na kyaleki ? tô  idan kina wannan tunanin ki daina yanzu dan zaki ya girma ya wuce wannan tozarcin dan bake ba hatta wanda ya ajiyeki acikin gidan nan  kanin mahaifina kenan ba bai isa ba bare ke banza jaka dabba mai hali irin na dabbobi mara hankali ."

a fusace ta fixge hannunta tare da cewa "da uwarka kakeyi itace jaka dabba  ai ,dan marasa mutunci irin tsiya irin jaraba tana fada yana maida mata ita kuwa maryama sai faman kuka take tana bawa aunty salma hakuri data gaji ma sai tayi shiru kawai tana kuka tana kallon fuskar habib dake tsine mata yana hadawa da yaranta da kaf dangin mahaifinsu da yasan basa qaunarsu  a maganganunsa ta fahimci babu wanda ya tsana kamarsu aunty salma ta fice cikin fushi ta bar dakin cike da tsananin damuwa ."

Maryama ta zauna jagwaba akan kujera tana mai runtse idanunta habib ya lumshe idanunshi "shiyasa kullum suke takura miki wannan sanyin naki yayi yawa ki zama mutun ki nuna masu zamani ki nuna ma kema yar zamani ce sai ku dawo daidai dasu ba kullum ki zauna kina asarar hawayenki a banza ba .""haba after dad mutunci aunty zamu duba yanzu kasan halin matar nan sai taje tayi mana wata kullaliyar a wajen baba gali ".

"taje dan kutumar ubanta shima dan kutumar ubansa yazo daidai nake  da kowa allah ya taimakesa yazo  idan ban raba masa kanshi gida hudu ba kice Shege ne , anan zan jira zuwansa ya fad'a yana huci tmkr zaki ta mike ta kamo hannunsa ta zaunar dashi ta zauna kusa dashi tana shafa masa baya dan ta fahimci ya dauki zafi dayawa "kayi hakuri komai me wucewa ne wata rana sai labari abinda ya baka dariya wata shi zai saka kuka ka bar aunty salma da duk wanda zai fad'a son rashi acikin gidan nan akanmu."

ita fa aunty salma bata da laifi gani tayi yanuwan mahaifinmu suna yi mana yau da sun  ga kima da darajanmu wallahi bata isa ba amman nasan wata rana idan ance tayi bazatayi ba kayi hakuri kaji danuwana rarrashinsa tayita har ya sauko tace "kaje kayi sallah nima zanje nayi kafin aunty su dawo ni na godewa allah ma da bata nan bare taga abun bakinciki  kuma allah yasa kar aunty salma ta fad'a wa baba gali "ta fad'a masa mana Ke kike tsoronsa yazo ni yau a gida ma zanyi sallah ina jiran duk abinda zasu dashi bari ma naje na nemo atakobina wacce zan fellewa mutun kai dashi ."

"Dan girma Allah kayi hakuri meye hadinka da takobi kai ba dan daba ba "na zama yau "allah ya tsareni allah kiyaye bazaka zama haka ba Kiyi adduar karsu zo da hauka ya fad'a tare da shigewa dakin aunty kofar  tabi da kallo kafin daga baya ta mike taje tayi alwala ta fita ta tada sallah tana cikin sallah tajiyo sallamar   aunty tana kiran sunanta  tana jin habib ya fita yana cewa "sallah take aunty sannu da zuwa "
"Yauwa habib a she kana gida ?nima ban jima da shigowa ba ina kika je ne ?kai habib zaka fara tambayoyinka kenan babu  damar kaga na fita murmushi  yay yana sake cewa "aunty ina kike je ?munje duba jikin  hafsat ne ta haihu amman cs aka mata ".bai sake cewa komai ba saboda ya fahimci  kowace hafsa take nufi diyar aunty fatima yayar mahaifinsu aunty ta mike ta shige dakinta domin yin sallah ."

Byn mintuna goma maryama ta fito daga dakinta  zuwan dakin aunty  duk jikinta a sanyaye lokacin aunty tana kan dadduma ta idar da sallah tana dai zaune  "aunty sannu da zuwa "yauwa my princess ya zaman gida ?ta gyada mata kai alamun Lfy!"ya na ganki wani iri ko akwai abinda me damunki ne ?tayi shiru kawai tana jin faduwar gaba "kin dan daura mana wani abu kuwa ?ta bude bakinta ahankali tana shirin bawa aunty amsa suka jiyo hayaniya shiru tayi tare da kasa kunne muryar baba gali ne ta mike da sauri jikinta har rawa yake ta nufi kofar fita itama aunty ta biyo bayanta a tsakiyar falon suka gansa tsaye tare da aunty salma da aunty  hassana sai hargagi suke tamkar wasu karnuka yayinda habib ya shiga kitchen ya dauko zabgegiyar takobinsa mai tsine ya koma bakin dakalin kofar fita  ya zauna  yana wasa  takobinsa ,aunty hasana ta nufo inda yake shi kuwa habib kanshi na kasa yana cigaba da wasa takobinsa  jira kawai yake suyi masa wata maganar banza ."

Aunty ta kalli maryama ta kalli habib tana bukatar qarin bayani cikin fusata aunty salma tace babu irin qare maku zagin da wannan tantirin yaron bai yi ba ta uwa ta uba har da ce mana dabbobi jakuna aunty hasana tace "da ubansa yake Shege dan Shegiya "da sauri ya mike yana zagayesu da takobi  kiiiii kake jin tsinin bakin takobi asimintin falon basu ba hatta aunty da maryama sun tsorata "kai ko ka fara shaye shaye ne ko meye ?"da sauri ya juyo kan baba gali da yayi mgn fuskarsa a tsuke alamun bai son ya kawo masa raini "dan ubanka da kake zare masa idanu ka dauka zamu ji tsoronka ne ?"

"a'a nasan bakwa jin tsorona kamar yadda nima yanzu babu wannan tsoron duk wanda ya nemi zaman lafiya ayi wanda yace sabanin haka yake bukata bismillah ni bazan bata bakina ba sassara mutun kawai zanyi na aika sa lahira ."ya fad'a yana tsoka takobi daidai kafar baba gali ."

Da wani saurin gabadayansu suka ja baya suna kallonsa da mamaki kamar yadda aunty Ke kallonsa "tunda ku kun zama ahlin sheidan bakwa jin wani yare sai na dabbobi bismillah  nima zan nuna muku akwai digon wannan dabbar ajikina  ,tunaninku me zakuyi da kuka wani kwaso jiki gbdynku kuka zo ?
"To wallahi  yau koni ko ku duk wanda ya zagi uwata da yaruwata sai na yanke masa harshe byn na raba kanshi gida hudu ."

zaro idanuwa sukayi suna sake ja  baya dan ya daga takobin hannunsa daga aunty hassana har aunty salma suka koma bayan baba gali suka boye cikin  karfin halin yace " bamu bane dabbobi da uwarka kake aiko jin haka Ke da wuya habib yayi kansa gadan gadan  zai sara mata takobi  aunty ta rike masa hannu tana zabga masa mari cikin muryar kuka tace "meke damunka habib ta fad'a tana kwace takobin tayi jifa dashi  "zaka kasheni ne  ?

"Ai da zai kashe dabba irinki da mun samu kwanciyar hankali "inji cewar aunty salma .
aunty kina jinsu ko bani takobina na sassara
shegu yan kutumar uba .."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun allahumma ajirni fi musibatihi   Waklifli khairan minha tana gama fadar haka ta durkushe kasa tana cewa "yanzu habib irin tarbiyar dana baka kenan ?maryama ta durkusa kusa daita tana mai rike hannunta tana ma habib wani irin kallo mai cike da tashin hankali ".

"Me  yasa bazaka koyi danne fushinka ba ?me yasa zaka min haka habib ? me nayi maka dana cancanci haka habib ? "Kuji makira ina allonki allonki yana jahannama ,makira  mata kin gama koya masa yadda zai ci mutunci mutune shine  yanzu kizo kina kukan munafurci yau zamanku ya qare acikin gidan nan ku hada ina ku ina ku ku bar mana gidan nan mun gaji da ganinku daga Ke har wadan nan mataiyatan yayan naki bama bukatarku."inji cewar baba gali ."

nan da nan habib yayi kan baba gali duk da yaso ya rabu dashi ganin mahaifiyarsa tana kuka dan a duniya babu abinda ya tsana sama yaga ana cin mutunci mahaifiyarsa da yar uwarsa baya son ana zagar masa su bare a zagi qaddararta da binta da muyagun kalamai ko zubar hawayenta  ,wuyan baba gali yake shirin damka ya

jiyo sautin muryar aunty cikin kuka tana cewa "wallahi habib idan ka ta'ba shi sai na tsine maka albarka "cak ya tsaya yana kallon baba gali ido cikin ido jikinsa na wani irin rawa tamkar mazari ."

Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access  idan an tura sai a turawa wannan  09136918331  alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

             Page 16

Ahankali   maryama   ta  mike  daga  cinyar  umma   hawaye  ne  sha'be sha'be  akan   kuncinta
ta tsurawa umma  manyan    idanunta  wad'an da   suka   canza   kala  tana kallonta   batare  da   tace  uffan  ba  ,duk  yadda  taso  ta daure  ta  tsaida  hawayenta  kasawa   tayi  hawaye  take   zubarwa  sosai  cikin  tashin  hankali  mai  tsanani ita  kad'ai  tasan  halin  bakinciki  data  tsinci   kanta   ciki   adalilin   jin  labarin   iyayenta ."labarinsu  yayi  matukar  d'aga  mata  hankali "a  she  wahaalarsu  da  tsanar  da'aka yi  musu   acikin  family's  ta  samo  asali  ne  daga  soyayyar  iyayensu ?  haka nan  taji   tausayin  kansu  na   sake  shigarta   . "

     Koina   ajikinta   yayi  sanyi  yayinda   falon  ya  d'auki  shiru  ,yadda  maryama  tayi  shiru tana zubar da  ruwan hawaye  tana sake tariyo  halin  da  iyayenta  suka tsinci  kansu  adalilin  soyayya haka ma  umma  bata  sake  cewa  komai  ba  " ahankali  wani  irin  so  da  qaunar   mahaifiyarta da qaninta  habib   ya  qara  shigarta"  allah  sarki  aunty  "hakika  kinga   rayuwa,  hakika   ahlinki  sun  d'auki  zafi  dayawa  akanki  ."

"hukuncinsu  yayi tsanani  dayawa  domin  allah Ke had'a  soyayya  alokacin  daya so ba  dabarar  mutun  ba  ,ba  son ran mutun  bane  ,domin  kuwa  idan da  dabarar  mutun  ne  ko  son ran mutu da  mutanen  duniya  dayawa  basu  tsinci  kansu  cikn
ta ba ."

a qalla  sun  d'auki  minti  goma a haka  suna  kallon  juna   sannan  maryama ta  lumshe  idanunta da sukai   jajur  alamun  tarin  quna da bakinciki ahankali  umma  ta  numfasa  "maryama !  ta  kira sunanta  a  natse , ahankali  ta motsa  lip's  dinta  alamun ta amsa dan  zafin  da  zuciyarta  keyi  ya danne  fitowar  muryarta "ki  godewa  allah  ba  kuka ya  kamata kiyi   ba  maryama."

    "ki  godewa  allah  daya  qaddara  aure  a tsakanin  iyayenki  da  har  aka sameku  ta  hanyar  sunanh "  "Alhmd!ta  furta  a can kasan   makoshinta   tana  dafe  kanta  dake  sara da mugun karfi "ya  kai  ki godewa  allah  ki  sake  gode  masa  ko  bai  kai ba ? kanta  ta  gyada  mata  alamun "eh!.

"To  ki  manta  da  duk  abinda na  fad'a  miki  muje  Kiyi  sallah  kici  abinci  ki kwanta ki huta "  da  karfi  maryama  ta  fizgo  magana  "bazan  iya manta komai  ba ,a halin  yanzu  ma   ganin  komai   nake kamar   a yanzu  ya  faru  har  nayi  danasani  umma nayi  danasani   jin  wannan  mummunar   labarin  rayuwa  irin  rayuwar   da  iyayena  sukayi  rayuwar kaskanci  ne a wajena."

    "why  umma? "me  yasa  komai yake  faruwa  damu haka ?ahankali  ummah  ta  shafa  kanta
zuwa gadon bayanta  tare da cewa "kiyi  hakuri  maryama kowa da  kalar  irin  tasa  qaddara a yanzu  jajurcewa  zaki qara  akan  wanda  kikayi  har kika samu  cikar  burinki  na  zamowa  cikakkiyar  mai  ilimin  lissafi  ,kiyi  qoqari  ki tsaya  bisa  kafafunki  domin  tallafawa  rayuwar   mahaifiyarki   daya  qaninka   domin  ina  hango  tarin nasara  da  kwanciyar  hankali  atattare  dake , bilkisu  na  bukatar  farinciki  ,maryama  nasan  da sannu  zaki  zamewa  bilkisu  sanyin  idaniya  amman  fa  sai kin manta  komai  maryama  kin rungumi  qaddarar  rayuwarku ."

"Na  yarda  da  qaddara  ummah  domin  yana  daga  cikin cikar  imani  mutun , na yarda da qaddara  amman  umma  aunty  tayi  kuskure  arayuwarta  bance  laifi   bane  dan  taso mahaifina  amatsayin  da  yake amamn  iyaye  fa  umma ? "manzon   sallahu  alaihi  wa salam  yace "ridal  lahi  fi ridal walidaini , wa sakad'ul  lahi fi sakad'il  walidai ."yarda  allah  yana  tare  da  yarda  iyaye, haka zalika fushin  allah yana  tare  da  fushin  iyaye  allah  ya  fifita  iyaye  akan  komai most  especially  uwa ummah ,babu  uwar da  taza ji  dadin irin rayuwar da  aunty  tayi ."

umma  tayi  shiru  kawai  tana sauraronta "misali  na kwatantawa  aunty  irin  abinda  tayiwa iyayenta ya  zataji ? na  kawo  mata  in responsible  man  nace  naji  nagani  sai  shi  duk  tarbiyar da tayi  tsawon  shekaru  tana  bani nasa  kafa na  rugujeta ya zataji ?" magana  ta   gaskiya   iyeyenta  da yan' uwanta   sun d'auki  zafi  dayawa  amman  aunty  ta fisu  laifi  kuma  lallai  ya  kamata  taje  ga  iyayenta  ta  roki  gafararsu sannan  ta  koma  cikin  danginta zuciyarta ta  samu  salama ."

   "wallahi  yadda  nake  jin  habib araina  bazan  iya  barinsa  saboda  wani  ba  bare  iyayena  da suka kawoni duniya ba ,abun  da ciwo  ummah  ba  kamar  yadda  kuka  d'auka  bane  kema  uwa ce ummah , aunty  ta  kona  zuciyar mahaifiyarta   dayawa,  yanzu na gano duk  aunty  ce  silar  shigarmu   cikin   matsala , iyayenta  na  can  suna  fushi daita  har  yau  ta  yaya   kike tunanin zataji  dadi ?"ta  yaya  kike  tunani  zan  iya  bata  farinciki  byn  ga  inda  zata samu  fiyye  da  nawa  ."?

maryama  ta  kalli  umma  cikin  sarewa  ta cigaba  da  magana " umma  abun na  da matukar  ciwo  irin  ciwon  dake  cin  zuciya da  bargo  ,ciwo  ne da  bashi da  magani  da   mafuta  har  sai  ka  had'u  da  mahad'inka , shiyasa a kullum  idan  na  kalli  aunty  sai naji  tamkar  tana  boye  mana  wani  abu  mai  mahimanci  ga  rayuwarta , ashe  gsky  né  hakika bakinta  bazai  iya  furta  mana komai  akan  rayuwarta  ba  matsawar  ita  din  uwa  ta  gari 
ce , dan   allah  umma  Kiyi   min  rai ki  raba  zuciyarta  da  wannnan rayuwar  idan  kuma  baki  yi  ba ni  zanyi  ,zan  rabata da  nauyin  dake   daskare  a  qirjinta ."

Tana  gama  fadar  haka ta  mike  a hankali  tana  share hawayen idanunta  da  suka  gagara tsayawa  tana  jin  wani  zafi a qirjinta , bazata  cigaba da d'aukar  wannna  nauyin  ba , koda  aunty bata  amince  ta  koma  ga yan'uwanta  ba ,lallai  ita   zata nemosu  a duk  inda  suke  acikin garin  nan  ."muryarta  a sanyaye  tace "umma ni   zan  wuce  sai   da  safe  " kai  kawai  ummah   ta   gyada  mata  sannan   maryama   ta  fara  tafiya  umma   tayi   shiru   tabi   bayanta da  kallo  tana  kallon  yadda  take d'aga  zara  zaran yatsun kafafunta da  kyar  tamkar  wacce  bata  da laka ."

  " A inda  ta  bar  mahaifiyarta anan  ta  sameta  tare  da  habib suna  hira  da  alamun shi  baya cikin  damuwa   kamar  ita." bata   tsaya  ba  byn  tayi  sallama tace  "aunty  sai  da  safe  tana gama  fadar  haka  ta  wuce  ta  nufi   d'akin   baccinta  bayanta suka   bita  da  kallo , yanayinta  kad'ai  ya  fahimtar  da  aunty  akwai  tarin  damuwa  atattare daita  shiru  kawai  tayi  tana  tunani "har  yaushe  maryama zata yi  farinciki  arayuwarta  ?".
A natse  aunty  ta  mike tabi  bayan maryama  tana  jin  tsinkewar zuciya  haka  shima  habib  akan kujerar  da  take  zama  idan  zatai zane  suka  isketa  ta  dafe  kanta  tana  sheshekar  kuka  atare  suka qaraso  suka  zauna  abakin  gado  suna   fuskantarta  shigowarsu  yasa  ta   tsaida  kukanta   wanda taso tayisa  sosai  har  taji natsuwar zuciyar."

    dogon  numfashi  aunty  taja tare  da  cewa "na  shiga  uku ni bilkisu   " ta furta cikin tsananin tashin hankali dan  bata  qaunar  abinda  zai d'agawa  yaranta  hankali  shi  kuwa  habib  hannun  maryama  ya  kamo  cikin  nashi  ya  damke da  karfi  cikin   tsananin  tashin hankali " heartbeat  meke damunki ?." muryarta  a  raunane tace  "babu  komai after dad "ya  babu  komai  zaki  shigo cikin damuwa  , yanzu  mun shigo mun ganiki  kina  kuka  amman  kice  babu  komai  ki fad'a min idan akwai  abinda  ke  damunki  ."

shiru  tayi  tana  cigaba  da  shesheka "ki  sani  bamu saba  boyewa  juna  komai  ba  idan kika  min  haka  baki  min  adalci  ba  ,ko  km damuwar  dazu ce  ? still  dai  shiru tayi  ,sosai  suka  d'aga  hankalinsu  ita  kuma  taki  cewa  komai  sai faman  ajiyar  zuciya  ta  saukewa ." damke  hannunta  ya sake  yi  sosai  yana  rokonta "dan allah   heartbeat  karki  daga  mana hankali  ki fad'a min kukan me  kike yi  ?kallonsa  kawai  tayi  tana lumshe idanuwanta ganin yadda  hankalinsa yay matukar  tashi da yadda ya  d'aga  hankalinsa  ya matukar bata  tausayi  daman kuma haka ne idan daya yana cikin damuwa dole ne daya shima ya tsinci kanshi cikin damuwa."

  "Yanzu princess bazaki koyi dauriya akan kowacce irin damuwa bace domin ki tsira da rayuwarki da rayuwarmu gabadaya ,Ke kenan kullum cikin zubar da hawaye akan damuwa me yasa zaki dinga asarar hawayenki  tare da qoqarin kashe kanki abanza ."?
"Gara dai ki fada mata gsky aunty domin ita rayuwar nan da take ganinta wani lokacin idan abubuwa suka wa mutun tsanani dole mutu ya rage wasu abubuwa domin tsira da rayuwarsa da lafiyarsa."
hawayen da take qoqarin maidawa ne suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri tashiga gogewa wasu na sake gangarowa duk  yadda  suka dinga kwantar da kai da murya dan  suji  damuwarta amman   taki  fad'a masu komai domin da zarar ta bude baki hawaye da sheshekan kuka Ke hanata magana dole tasa suka daga mata kafa suka  fice  d'aya  bayan  d'aya daga dakin  da zumar  zasu  lalla'bata  gobe ta fad'a  masu dalilin kukan  ."

tafi  mintuna  goma  byn fitar aunty  da  habib   zaune  sannan  ta  yunkura  ta  tashi  tana  sauke naunayen  ajiyar  zuciya ta shiga bayi  ta d'auro  alwala ta  fito ta gabatar  da  sallahr magariba da isha'i  tare  da  shafa'i  da  wutiri byn  ta  idar  ta  koma  kan  katifa ta  zauna  tare  da  jingina bayanta da  pillow  ta  rungume hannuwanta  duka  a qirjinta ."

ahankali  ta  runtse  idanunta  tana tariyo  komai  daya  faru  dasu tun suna  yara  "Kenan  adalili  rasa  mahaifi  da  kaka  yasa  rikonsu  ya dawo  hannun  abban  sadam  ."tun  tana   qarama yar shekara hud'u a  duniya ta  taso cikin so daga  bangaren  abban sadam da umma  da  mahaifiyarta   amman  daga   bangaren  aunty  hassana  da  sauran  'yan'uwan  mahaifinta   kuwa  saboda  haushin  da kiyayyar  mahaifiyata  yasa  suka dinga   nuna  masu  tsana  da tsamgwama ,  sun ci wuyarsu  sosai  most  especially  Ita   ganin kiyayyar  dangin  mahaifinsu  da irin  tsanar  da  baba  gali  yayi masu  ya  bawa  aunty  salma  damar  cin kashi  akansu  da mahaifiyarta ."

tun  daga  lokacin  kuruciya har zuwa  girmanta  abinda  yake  rage mata  zafin  gidan  shine soyayyar umma  bancin  ita  kowa a gidan baya   sonsu amman kuma  wani lokaci   shi   kanshi  baba gali  ya kan  tausaya masu  in dai ba fad'a sukai  da  sakina  ba ko  yarshi qarama  ba , idan  tayi  mata  laifi ta  d'an  daketa  shine   zai  fito da 'bacin  ransa  har  ya  fito  da  zallar  kiyayyarsa  ,kuma  tun da ta lura  son ya'ya ne  dashi domin ba ita ba  ko uwar  data  tsugunna ta haifesu  baya  raga  mata  akan ya'yansa  ."

"yayan  baba  gali  uku  ne aliyu sakina  wacce sa'artace  sai mai bi mata  salamatu  wacce  taci  sunan hajiya  kakarsu  ana  kiranta da shukura  bata  fi  shekara sha bakwai  ba a yanzu ,itama babu yabo  babu  fallasa  suna  d'an  shiri  daita  sai  dai  idan  taga uwarta  na  fushi  da  zagina bata hanata  sai  ma  dai  ta zugata domin  itama  tana  nuna kishinta akainta  idan  taga  umma tana tarairayata ko wani ."
Baba  gali  dinki  yake  ada  rasuwar abban  sadam  yasa   gidan  buredi da  rikonsu  ya  koma  hannunsa  alhamdulillah  babu  laifi  ita  din mai  qokari  ce  ta  kowani fanni boko da arabic ga baiwar zane da Allah  ya  bata ."

Alokacin  baya  kullum  ta  allah  sai  aunty  tayi  masu  special  lesson  ita  da  habib  kusan kokarinta ta samu ne a wajen mahaifiyarta  ,duk  unguwar da makarantarsu  ana  maganarsu akan  ilimi  bokon  da suke dashi haka  duk  gidan  ba masu  jin   turanci  kamar  ita  da  habib ko wani  abu  za'a  tambaya  ita ko habib  ake  tambaya mahaifiyarsu ta  tsaya  masu  akan  karatunsu shiyasa  ma  education  dinsu  yayi  very  fast  kuma à sanadiyar qoqarinta ita da kawarta subai'a yasa gwanati ta dauki nauyin karatunsu zuwa lagos state university ".

   bangaren sakina da  sauran  yaran  gidan  matsalar  iyayensu ne dan  basa  maida hankali  akan karatun  yaransu  gashi  sam  basu da  isashen  ilimin  boko ko Arabic barin  ma  aunty  salma  karta ji labari  ba  arabi ba boko sai  uban girman  kai  ,sau  tari  idan shukura tazo   koyon  wani  abu a wajenta bata  só  sai  ta  nuna  ai  itama tasani  dan  me  zatazo  wajenta akarshe  idan  tayi  mata  zero take samu  a makaranta shiyasa da  yarinyar  ta gane ta daina  bata  idan tace ta kawo kai  tsaye  take ce  mata  bataso   zero  zataci ."

hatta  alwala  ba  daidai aunty salma  take yi ba  kuma sallah ma bata  dameta  ba  ,tun  suna yara baba  gali Ke  mata   fad'a  akan tarukun  sallah din  da take yi amman  taki  ta  daina  shi  kansa daya  gaji  sai ya  rabu  daita ya dinga  Kwa'bar  yaransa da yin sallah  sanin  in  har  dan uwarsu ne sai  dai kar su yi  babu abinda ya  dameta dan  idan ma  koyi zasu yi  daita  sai  dai su  koyi taruku sallah."

Su  kuwa  aunty  bata yarda tana gama  dauro  alwala  zata  tura habib  zuwa  masalaci  ita km ta umarceta taje  tayi  alwala sannan  a  kullum  dare auty  ta kan fito  tsakar  gidan  tare dasu  har  sakina  kasancewar  tana  qaunarta  ta  koya  masu  darasin lissafi , tana  daukar  lokaci akansu  har sai  taga sun gane sannan ta bukaci  wanda yake da damuwa a bangaren  karatunshi ko baka da matsala  zatai  'yan  tambayoyi  ana  bata amsa  idan bata gamsu da  amsar  ba ta qara yi masu  bayani , bangaren  karatun alqurni kafin  suyi  bacci  sai  aunty tasa sun  karanta izawaka  da tabaraka kafin  su  kwanta  da  safe kuma sai  sunyi murajaa  alqurni sannan su shirya su wuce  school  ko islamiyya ."

A ranar batayi  isashen  bacci ba  ga tsananin  tunani  ga  kwadayin son  ganin  yan'uwan  mahaifiyarta  gargadin  kanta  ta shigayi   akan fad'awa  soyayya  da ma ko waye idan  kuma  soyayyar ta zama dole sai  dai  tayi a gidan aurenta  ga duk wanda ta aura har  asuba  tayi maryama batai   wani  yi  baccin  kirki  ba shiyasa  kiran  sallahr  farko  acikin kunnenta  akayi   ta  gyara kwanciyar  ta koma  ta  kwanta bacci   kad'an  tayi ta  lalubo wayarta  ta  duba  taga biyar da  rabi   saura  lokacin  sallah yayi dan har an  tada sallah a matsalacin unguwarsu ."

a hankali ta  mike  zuciyarta cike da damuwa bakinta dauke da  adduar   tashi  daga  bacci ta kai tafukan hannunta tana shafa fuskarta sannan a natse ta zuro kafafunta ta sauko ta  shiga  bayi ta dauro alwala ta fito cike da sanyin jiki ta  gabatar da sallah asuba  byn ta idar  ta d'auko  alqurni ta soma karatu  cikin suratul  baqara anatse ta  kai idanunta  ga  window d'akin taga gari ya  fara sha tayi azkar  din safe tana nan zaune tana lazimi har shida  saura sannan ta koma ta kwanta akan sallaya nan da nan  bacci mai nauyi ya dauketa ba ita ta tashi ba sai goma saura ."

Ta  mike da  kyar  bakinta  dauke da  salati  sakamakon qirjinta dake wani irin bugawa ta 
gyara gadonta ta fita ta dauko tsintsiyar  shara
ta  share d'akin  ta fito har falo ta shiga d'akin  mahaifiyarta  bata  ganta ba   tasan may be ko tana byn gida wajen yin wanki ,dan wannan kaida ne  kullum safiya sai  tayi  wanki  kayanta wani   lokacin  da nasu  ta  share d'akin  tasss ta fito da  sharan zuwa falo ta  shiga  kitchen ta hada kayan wanke wanke ta wanke atake  ta goge koina ta sharo sannan ta hada da share falo tayi mopping ta koma daki ta cire kayan jikinta ta shiga wanka bata wani jima ba tayi alwala ta fito kai tsaye ta shimfida daddumar sallah ta sallacci salatul duhu byn ta idar ta shirya kanta ta kwanta lamo cikin zullumi ta kamkame jikinta waje daya wani iri take ji a duk gbdy ilahirin jikinta soyayya irin wacce iyayenta sukayi bazata ta'ba yarda ta jefa kanta cikinta ba".

Ta godewa allah  daya bata kyakkyawar zuciyar da bata da lokacin maza ,bata jin soyayyar ko wani  nmj ta ratsa koina ajikinta ,duk wanda yazo da sunan sonta ya dawo ya gudu bata taba  jin haushi ko kewarsa bare ta damu kanta akansa ita fa gsky tafi ganin laifin mahaifiyarta akan abinda iyayenta sukai  mata kuma taji dadin mutuwar mahaifinta akan rayuwarsa domin daa kalleta ace ita din diyar dan shaye shaye da neman mata ne wallahi gara mutuwarsa akan rayuwarsa, data dangwama tana masa adduar shiruya allah gara ta qare rayuwarta wajen yi masa addua samun rahmar Allah ."

Da misalin karfe goma sha d'aya da rabi daidai na safe aunty duk ta damu tun jiya rabon tasa maryama a cikin kwayar idanunta ga dai alamun ta tashi dan har tayi ayyukanta na yau da kullum data saba  dan ga parlour nan a gyare tsab sai zuba kamshi yake koina tsab daga ita har habib sun kasa samun kwanciyar hankali bare su karya ,sai ma wata faduwar gaban data ziyarci zuciyarsu ."

mikewa aunty tai ta  nufi dakinta shima habib ya biyota kusan atare suka shiga dakin  har suka shigo maryama batasani ba tana can duniyar tunani tare da rafka uban  tagumi  da sauke numfashi a hankali ahankali, da sauri suka qarasa gareta dan yadda suka ganta ya matsifar daga masu hankali  fiyye da jiya dan har wani doguwar rama tayi atare suka kira sunanta suna tmbyrta "wai  maryama menene  damuwarki ne ?"

  "heartbeat   banason  ganinki cikin damuwa  saboda duk duniya babu wanda  nake  so  byn  Allah  da aunty  sai  ke  karki   bari  tunani yasa  mu   rasaki  ya fad'a idanuwanshi na kanta "bansan me yasa kike son kashe kanki akan damuwa ba wanda ni a tunani kowace irin damuwa ce zaki iya hadiyeta". aunty ta qarasa maganar tana furzar da iska me zafi daga bakinta  a hankali ta mike ta koma kan kujerar aikinta ta dauko farar takardar daya  ta ajiye akan table domin samun damar cigaba da aikinta ta zaro pencil har kala uku ta fara zane sai dai zuciyarta rawa take nan da nan idanunta suka cika da ruwan hawaye tarasa dalili daga jiya zuwa yau ta sake rasa sukuni da farincikinta, bata jin shaawar komai babu abinda take so da bukata kamar ta kadaice kanta ."

Aunty ta dakatar daita daga abinda take tana dubanta zuciyarta na mata wani irin suya a game da halin da take ganin maryama din ciki wanda bata san silar faruwar haka ba maryama bata dago ta kalleta ba ta cigaba da abinda take gbdy kamaninta ya canza ,ahankali habib ya shiga  rarrashinta da nasiha mai kashe jiki  gbdy fuskarsa ta canza Kmr zai yi kuka , Ita  kam  aunty  kasa  furta  komai tayi  ta  zuba  masu  idanunta tana jin tarin damuwa ganin  hk yasa maryama ta soma magana kamar bata son yi "abinda muka bukaci Auny ta fada mana taki jiya umma  ta fada min babu abinda ta boye min sai wanda batasani ba." ta karasa mgnr tana dago kanta Tare da sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta sakin wani sabon kuka lokaci daya shima kwayar idanunshi suka kada suka canza nan take yaji tsanar dangin aunty ya shigesa kasamcewarsa nmj kuma duk nmj dole yayi kishin mahaifinsa nan take ya yanke cewar a zuciyarsa bazai furtawa aunty komai akan yanuwanta ba  koda kuwa ita kanta uwar gayya ta amince zata koma garesu amman shi babu shi babu su har abada ."

"Tô  princes kinji kadan daga cikin tarihin rayuwata kuma ina fatan kin gamsu ?shiru kawai maryama tayi tana kallonta tare gyada mata kai "good my princess kinga rana ya fara ki tashi  kici abinci ki kwanta ki dan huta kafin lokacin sallah yayi ta fada tare da mikewa tsaye "yanzu aunty haka rayuwa zata cigaba da tafiya ?tayi maganr cikin raunin murya aunty taja ta tsaya tana dubanta tare da nazarin maganarta "ina nufin haka zamu cigaba da rayuwa batare da kin san  matsayinki a wajen iyayenki ba ?

"karki damu dan ni har yanzu bana bukatarsu arayuwata ina ganin kuma ku ciresu acikin zuciyarku "ni daman a yanzu dana gama jin komai na ciresu araina dan basu da wani amfani a wajenmu gara mu qarasa rayuwarmu haka batare dasu ba "haba habib me yasa zaka fadi haka shikenan ita aunty haka zata qare rayuwarta ? kai yanzu zaka iya rayuwa babu ita da kake goya mata baya ?"tayi maganr cikin tsananin fushi "kai daya kamata mu taru mu shawo kanta shine zaka ce haka .?"

guntun numfashi ya sauke yana cewa "lallai heartbeat kina da aiki mutanen da suka wulaqanta mana mahaifi dan kawai talaka ne shine zamu tashi muje wajensu alhalin bamu da komai muna nan dai a yadda suka san mahaifinmu babu wani cigaba da muka samu gsky ni bazanje inda suke ba kuma har abada "gsky habib ya  kamata ka tsaya kayi tunani da kyau abinda ubanka yayi bai kyauta ma iyayen aunty ba, ni nan naji dadin dana girma baya raye wallahi da cigaba da ganin rayuwarsa gara mutuwarsa a wajena ."kallonta habib yayi yadda ta zuba masa idanunta cikin bacin rai tana fidda numfashi da kyar "ni babu wani tunani da zanyi akan wannan matsalar ke ma kuma ki bar magana a iya nan dan banga abinda zai sa naje gurin makiyanmu ba kuma ni banga abinda mahaifinmu yayi ba daya cancanci tozarci irin wanda akayi masa ba tun kafin ya qarasa maganar qirjin aunty yayi wani irin bugawa da karfi duk da bata bukatar iyayenta arayuwarta amman bataji dadin kalmar habib din ba ."

"wallahi wallahi habib idan ka sake furta wannna kalmar zan balain baka mamaki "kinga ni tafiyata ya nufi kofar fita yana cewa "allah dai ya baki hakuri amman babu abinda zai kai mu gurin makiyanmu ya qarasa fita ,jikin aunty yayi sanyi ta bude baki zata yi magana sai kuma ta kasa cewa komai  "aunty !.
maryama ta kira suannata ,a hankali aunty ta motsa lip's dinta "naam !"karki dauki maganar habib da mahimmanci domin shi yaro ne ke uwa ce da muke kallo muke koyi daita kuma kece malamammu dake nuna mana daidai da ba daidai ba ,ki natsu aunty da kyau ke mai ilimi ce allah subuhanahu wata ala yace acikin suratul ahkhaf aya ta arabin da biyar وَوَصَّيْنَا الْإِنْسَانَ بِوَالِدَيْهِ إِحْسَانًا ۖ حَمَلَتْهُ أُمُّهُ كُرْهًا وَوَضَعَتْهُ كُرْهًا ۖ وَحَمْلُهُ وَفِصَالُهُ ثَلَاثُونَ شَهْرًا ۚ حَتَّىٰ إِذَا بَلَغَ أَشُدَّهُ وَبَلَغَ أَرْبَعِينَ سَنَةً قَالَ رَبِّ أَوْزِعْنِي أَنْ أَشْكُرَ نِعْمَتَكَ الَّتِي أَنْعَمْتَ عَلَيَّ وَعَلَىٰ وَالِدَيَّ وَأَنْ أَعْمَلَ صَالِحًا تَرْضَاهُ وَأَصْلِحْ لِي فِي ذُرِّيَّتِي ۖ إِنِّي تُبْتُ إِلَيْكَ وَإِنِّي مِنَ الْمُسْلِمِينَ
Allah yana yiwa mutane wasiha ne akan su kyautatawa iyayensu ,  mahaifiya ta d'auki cikin mutun ,tana mai shan wahala ,kuma ta sauke  shi   cikin  wahala ,da daukar cikin  da  yaye  d'a  na  tsawon wata talatin  har  lokacin da karfin mutun  zai  kai  girma yasan ciwon kansa har zuwa karshen ayar  ,cikin girmamawa ta cigaba da magana "kiyi min wannnan alfarmar aunty , wallahi dan kinje garesu a halin yanzu ba kasawa bane bugu da qari iyayenki  suna da hakki akanki babu ruwan allah da abinda sukai miki ".

"maryama mu bar maganar nan ta wuce  dan allah sannan ki fito ki karya kar abincinki yayi sanyi tana gama fad'ar hk ta juya ta fice daga dakin shiru tayi  kawai tare da bin kofar dakin da kallo idanunta na  kawo ruwan hawayen tana tausayin mahaifiyarta  bata san meke damun mahaifiyarta ba akan iyayenta sam sam bata son ana mata maganarsu tamkar wanda akayiwa farra'u amman tasan abinda zatai zata janye jikinta tare da tsananta addua akan lamarin allah ya daidaita da iyayenta  da yanuwanta ,yinin ranar a daki ta yini taki fitowa taci komai ."

*****

Tun karfe takwas na safe maryam da mami da masu aikinta ke faman kai kawo a kitchen suna qoqarin had'awa mr ATA breakfast sosai mami take lura da yadda maryam take gudanar da aikinta , babu laifi tafi da kokari sosai sannan ta rage son jikin da take dashi wajen girki suna girki suna hira mami ta cigaba da nuna mata wasu abubuwa suna cikin aiki sai ga sallamar hindu ta shigo maryam ta amsa tare da lekawa tace "hindu ce ki  shigo muna kitchen muna aiki ne."

wani irin kallon tayi mata wanda yasa maryam taji wani iri ajikinta ,hindu ta tsaya bata shiga kitchen din ba kamar yadda maryam tace ta samu waje ta kame akan daya daga cikin kujerun falon ,mami ta dawo inda maryam take tsaye tana kallonta "sannuki maryam gsky kinyi kokari sosai yau kin aikatu da kyau haka ake so, maryam tayi murmushi kawai tana jin dadin yabon da mami tayi mata "na gode sosai ai nan gaba zan kware na zama professional ta bangaren girki bazan ta'ba baki kunya ba ."

mami tayi murmushi tace "da alama zaki wanke zuciyar mamnki ta gyada mata kai alamun "eh !"
"To ni zan hau sama na dubo adamcy Idan kin kammala komai ki shirya dinnig kije kiyi sauri Kiyi wanka ki shirya ki dawo Kiyi saving din sarkin zuciyar Kiyi komai a natse  kin dai san halinsa dan oya oya ne yafi son komai cikin sauri sauri bare yau  din nan sai ahankali ."mami dan allah ki zuba masa da kanki mana"idan kunyi aure nice zan dinga zuwa gidanku ina zuba masa ?"dakewa zakiyi  maryam ai ya kamata ace kin saba da halinsa "wallahi mani babu mai iya sabawa da halinsa sai ke nifa mugun tsoro yake bani idan na gansa hatta kayan cikina karkarwa suke mami tayi murmushi tana cewa ni na wuce "To mami sai kin fito ta fad'a cikin murmushi mami ta fito zuwa parlour'n."

hindu na ganinta ta saki fuskarta sosai tare da gaishe da mami cike da sakin fuska mami ta masa tana tmbyrta mutanen gidansu ta amsa da lafiya lau kowa yake "mami ina ya adam ne ko har yanzu bai tashi ba ?"eh!hindatu ina tunanin bai tashi ba amman yanzu haka ma samansa zani na taso shi dan yace idan ya wuce tara bai tashi ba na tashesa rausayar da kwayar idanunta tayi tana jin wani zazzafan sonshi ."

Mami ta nufi saman dakinsa tana mamakin hindu su dai yaran zamani basu da ta ido akan nmj so na mugun rufe masu ido shiyasa har kullum take ganin girma da kimar maryam, a dai barta da son social media dinta amman rawan kai akan maza sam bata dashi dan tasan bancin itace ta hadata da adam to har abada bazata iya bude baki tace tana son shi ba ."

Maryam ta kammala komai a natse ta fito a yatsine hindu ke binta da kallo tana shirya dining ,ita kuma tana tunanin yadda zasu buga kishi daita idan tai nasara shigar gidan ya adam dinta dan dole ta fita ta bar mata gidan ta zauan ita kadai ,dan idan bata kaita lahira ba lallai zata raunatata dan irin son da takewa ya adam ba na wasa ba so ne wanda bazata iya sharing dinsa da kowa ba ."

Marayam ta sha jinin jikinta da irin kallon wulakancin da hindu Ke mata dan duk lokacin data kallo bangarenta sai taga kamar hararata take wanda ta rasa dalilin faruwar hakan ,sai da maryam ta tabbatar da komai yayi neat babu abinda mr ATA zai gani yayi complain sannan ta wuce ta nufi dakinsu cikin sauri still tana mamakin hindu ."

tana shiga dakin bathroom ta shiga ta fara wanka sai dai matsalarta bata iya wanka cikin sauri ba idan ta shiga wanka a qalla tana daukar awa daya a bayi amman kasamcewar zatayi saving din mr ATA yasa ta tsakaita tayi wanka ta fito ta dauki man shafa warta wanda shima shafa man kanshi aiki ne domin tana daukar a qalla mintuna talati bare aje ga make up ta shirya cikin doguwar rigar shadda bazin har kasa bata gama kammala shiri ba taji sautin muryar mami na kiranta da d'an sauri ta fito zuciyarta na rawa kuma har lokacin hindu na zaune a parlour'n tayi shiru tana yi masa kallon tsab komai nashi yayi mata irin wanda take so nmj ne sai kallonsa take yayinda mami ke qoqarin jawa mr ATA kujera baya"

Wani abu mai mugun daci ya hadiye tare da zama yana mai runtse idanunshi ganin mami na son bawa maryam umarnin saving din mr ATA hindu tayi sauri ta mike tsaye tana cewa "mami bari nayi saving din yayana ta fad'a tana mai sunkuyar da kanta alamun kunya "amm...! "Sweetheart bari tayi kawai ya fad'a atakaice mami ta kallesa na second biyu dan sam bataji dadin hukuncinsa ba dan tasan da wata manufa hindu ta fadi hk shi kuma gudun karyaci daga hannun maryam ya fadi haka dan tasan shi tasan halinsa baayi masa gwaninta ranta ya baci sai dai danne damuwarta ."

Madadin mami ta zauna kusa dashi kamar yadda ta saba sai ta koma kan kujera ta hankince ta nunawa maryam kusa daita"maryam zauna anan kinji  yar albarka ta maida hankalinta kan tv mr ATA yaji babu dadin yadda mami taja jikinta amman sanin dan maryam tayi haka yasa ya share ya dauki wayarsa yana duba sakonin dake shigowa yayinda hindu ke zuba masa abinci acikin wani haddaden plet ta matso daf dashi Sannan ta ajiye plet din a gabansa."

cike da girmamawa ta kira sunansa"ya adamccccyy...!yadda ta kira sunan cikin slow voice yasa daga maryam har mami suka waigo suna dubanta murmushi ta sakar masu wanda ke nuna tana cikin farinciki sannan ta dauke kanta ta maida kanshi wanda shi gogan har lokacin bai daina abinda yake ba bare ya dago ya kalleta sai faman ciza lips din yake yana kallon screen din waya ."

kira ne ya shigo wayarsa ya dauka a natse "ok but I think kasan nan da 1week zan wuce france ya aikin gunka ina fatan akwai nasara ya hade rai sosai haba hisham you should know me by now ka ta'ba ganin inda akayi haka ?kawai dan na tattara hankalina zuwa wani waje kawai su kamawa yiwa mutane barna ,ka kuwa san adadin kudaden da mukayi asara kuwa ?kowa acikinsu kanshi kawai yasani ba cigaba AGC bane agabansu well sai na shigo dai hindu ta marairaice murya sosai tace "ya adamcy ga abincin ka dan ajiye waya kaci abinci ".

Banza yayi mata ya cigaba da wayarsa "a lokacin zuwa office muke gashi naji ya sultan yace yau kuna da zama na mussaman "bai kalli inda take ba bare ma ta samu matsayin ya bata amsa hakan kuwa yayi wa maryam dadi sosai ,sauran kadan ta fashe da dariya amman ta danne ,ta kalli mami wacce itama ita take kallo suka sakarwa juna murmushin jin dadi sai daya gama wayarsa ya ajiye sannan ya fara cin abinci babu irin kwarkwasan da batayi masa ba da jansa da magana amman bai ce uhmm ba bare uhmm uhm ba illa ma mikewa da yayi tsaye yana gyara yar saman suit dinsa ya dan qarasa kusa da mami muryarsa a dake yace "ni zan wuce kuma kai tsaye daga nan AGC zani "to Allah ya tsaye sai ka dawo yace" Ameen!
"har ya juya ta kirasa "adamcy ! ya dan tsaya yana saurareta "kabi komai a hankali dan Allah karka dauki zafi dayawa ahankali ake bin komai ka tsaya ku fahimci juna da yanunwaka".

Kai kawai ya gyada mata ba dan zai yi abinda tace din ba dan yau kusan sai ya tashi rabin mutanen kamfanin kuma daga aiki wanda dayawa yanuwa ne a natse ya juya ya fice yana fita hindu tabi bayansa har tayi taku biyu mami tace "amm...hindu yau yayanku baya cikin moon mai kyau ba kin kuma san halinsa bare idan yana jin miskilancinsa idan kika nemi ki tsaida shi komai zai iya faruwa ko kina son wani abu ya faru ne ?"

Hindu ta girgiza mata kai alamun a'a daman ba tsaida shi zanyi ba gida zan wuce "to shikenan sai anjima sai data fice mami ta dawo da kallonta kan maryam "mami me kika karanta akan hindu ni yau gani nayi tana wasu abubuwa kamar son ya adam take mami ta tabe baki "wai son shi take amman shi har yanzu bai sani ba dan dayasani bazai bari tayi saving dinsa ba" maryam ta dan ware kananun idanunta sanna tasa dariya tana cikin dariya sai ga nana hauwa'u "sister yi sauri kizo kije wani sabon rigima da sauri ta qaraso tana cewa "bani na sha matar yayana "wai hindu Ke son ya adam wace hindu kuma ?"

Wacce hindu mike dashi a gidan nan data wuce ta gidan baba qarami wallahi har na tausaya mata dan idan ya kirani guntuwa ita km fa me zai kirata ?"
gabdaya suka sa dariya har mami "wanna kam gsky ne ina zai kaita ? ga wani cream na organic tasha duk ya canza skin dinta ta dawo farar karfi da yaji ,shi daaka bashi farar mace sol yace bai so ina ga mai shafa cream? ni wallahi da zai karbeta ma ya barni da naji dadi anan ne mami tasa baki "kar na qara jin kin fadi haka ai babu wacce zaki barwa shi da sannu zai koyi sonki dan nasan you are so different daga sauran mata ai shiyasa nace a saka sati uku ayita ta qare burina ki rage media ki janyo hankalinsa cikin kankanin lokaci ku zo juna ."

"mami kina ganin komai zanyi ya adam zai soni ?"
Mai zai hana maryam zai soki mana aure nawa akayi irin naku km a karshe ya zama soyayya mai karfi ,ni dai ina ji ajikina aurensa zai sa ku rasani da wuri tun lokacina bai yi ba." maryam ta fad'a idanuwanta na kan Mami "ki daina irin wannan tunani babu abinda zai faru sai alkhairi zai soki ki so shi babu abinda zai rabaku sai mutuwa shiru maryam tayi tana jin mami ."

Motocinsa na tsayawa a haraban AGC escout dinsa suka firfito daga cikin motocinsu mutun biyu na qoqarin bude masa murfin mota ya bud'e ya fito fuskar nan tashi sam babu annuri yana miqawa na hannun hangunsa wayoyinsa ya nufi cikin kamfanin kallo daya zaka yi masa zaka qara jin tsoronsa fiyye da yadda kake ji ."

tunda ya samu information barnar daake yi a kamfanin walwalarsa ta ragu sosai babu inda zaka kalla a fuskarsa kaga rahma ganinsa yasa kowa ya shiga hankalinsa domin a irin wannan ziyarar da yake kawowa yake korar mutun daga aiki yana tafiya ana gaishesa cike da girmamawa yayinda sectary dinsa some na biye dashi abaya hannunta rike da files wanda ake bukatar saka hannunsa duk cikin wad'an da suke gaishesa babu wanda ya masawa daya daga cikin escout dinsa yayi saurin bude masa kofar office dinsa ya shiga a natse yana duba agogon rolex din dake daure a tsintsiyar hannunsa ."

ya qarasa mazauninsa ya zauan ransa a matukar bace, cike da girmamawa some tace "good morning sir ?kanshi kawai ya gyada mata batare daya amsa ba "sir ana bukatar saka hnnunka acikin wadan nan file's din ta fad'a muryarta na rawa dan ta tsorata da yanayinsa na yau gabansa ya nuna mata alamun ta ajiye cike da girmamawa ta ajiye tana rusuna masa "ya tsurawa file's din ido kawai yana kallo kafin a hankali ya dauki daya ya rabashi gida biyu a matukar tsorace ta dinga binsa da kallo har ya gama yagasu gabdaya ya watsasu sama suka tarwatse yana hura hanci sannan yace "are you crazy some ?

Mmm sudais
💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.