Maradams Book 1 Complete Hausa Novel
Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt
Chapter 13 of 18
Page 14
"Shiru aunty tayi tana jin fad'uwar gaba mai tsanani tafi mintuna ashirin bata ce qala ba habib ya kai hannu ya d'ago ha'barta yana kallon cikin kwayar idanunta dake kwance da ruwan hawaye "male kece karfin gwiwar dake tafiyar da rayuwarmu Kinyi mana komai arayuwar mu ,kin nuna mana tsantsar soyayya ,kin nuna mana daidai da ba daidai ba kin bamu gatan da ba kowa yake samun irinsa ba wato ilimin addini dana boko , kin inganta rayuwarmu mun yaba miki kuma mun jinjinawa qoqarinki garemu da taimakon Allah da taimakon heartbeat gashi har heartbeat ta kammala karatunta kalamai soyayya iri iri dana sanyaya zuciya yake furtawa gareta wanda yake sake tsuma zuciyarta da soyayyarsu "wannan alfarma ce ki fad'a mana ."
Duk yadda habib ya d'auki lokaci yana magana sai dai har zuwa wannan lokacin aunty ta Kasa furta komai garesu illa numfashin da take janyowa ahankali tana fitarwa da kyar
sun sake d'aukar tsawon awa d'aya a wannan yanayin batare da ta fitar da abinda ke cikin zuciyarta ba ."sosai idanunta suka canza kala kallonta suka cigaba da yi suna jiran ta fara basu labarinta, yadda suke kallonta haka itama take kallonsu zuciyarta cike da wasi wasi tana son magana amman hakan ya faskara tana tsananin son yaranta ba zataso suji abinda zai d'aga masu hankali har da zai yi silar shigarsu damuwa ba haka zalika bazataso suji irin rayuwar da sukai da mahaifinsu kafin aure ba da irin tozarcin da mahaifinsu ya sha a wajen yan'uwanta ba ,ganinta fad'a masu wannan labarin babban kuskure ne zata aikata ko bama haka ba bata tunanin zuciyarsu zata iya d'auka , zuciyarsu ma bazata iya dauka ba , bazasu iya wannan juriyar ba."
Ahankali ta lumshe idanunta adaidai lokacin da habib ya d'auke hannunsa daga ha'barta har yau tana jin soyayyar mahaifinsu acikin ranta duk da bai duniya amman kullum ta kalli ya'yan da Allah albarkacesu da samu soyayyarsa na qara hauhawa acikin zuciyarta kuma bata jin Kuskure tayi dan ta auresa ".tana kallonsu suka mike atare suka nufi kofar fita kowannensu da abinda zuciyarsa ke tunani akanta dan daman sun san da matukar wahala mahaifiyarsu ta fad'a masu labarinta kasancewarta mace mai tsananin zurfin ciki da rashin son magana ."
bayansu tabi da kallo har suka 'bacewa ganinta bata iya d'auke kwayar idanunta akansu ba byan fitarsu ta gyara zamanta sosai tare da rafka tagumi gabad'aya kuma sai taji babu dadi aranta ji tayi kamar bata kyauta masu ba hakan yasa taji zuciyarta kmr zata kama da wuta ahankali ta mike tsaye cikin sanyin jiki ta isa bakin window falonta ta kai hannunta ta zuge labule tana kallon haraban gidan yaranta ta hango suna tafiya a natse kafad'a da kafad'a wanda kusan kansu d'aya basu tsaya akoina ba sai bakin part din umma "heartbeat ban san me yasa haka ke faruwa damu ba ? bana son ganin kanmu haka ina jin Kmr na kashe kaina na huta da wannan rayuwa ".
ya fad'a yana dafe goshinsa cikin tsananin damuwa .
"Subhanallah after dad ka daina fadar haka karka sake fad'ar wannan kalmar Allah bazai sa naga wannan ranar ba ,"ka dinga addua a duk lokacin daka tsinci kanka cikin tashin hankali ambaton sunan allah zakayi karka bari zuciyarka tafi karfinka muryarsa cike da tashin hankali
"amman me yasa anayi mana abubuwa rashin mutunci aunty ta hanani d'aukar mataki ? "daidai kenan habib ,abinda aunty tayi shine daidai shine abinda kowace uwa ta gari ya dace tayi idan suna yi muma muna yi to meye bambamci a tsakanin mai ilimi da wanda bai dashi ? kowani irin abu zaka gani a gidan nan ka d'aure ka cije ni yanzu damuwata ba matsalar Aunty hassana bace sanin inda dangin mahaifiyarmu suke shine babban damuwata ."
Ya riko hannunta cikin nashi yana dubanta "ki ciresu aranki abinda muka fi bukata sune dangin mahaifi , ace yau bamu da dangin mahaifi ko ba acikinsu muke rayuwa ba shine babban tashin hankalinmu "suma dangin mahaifiya suna da mahimanci domin zuciyarsu tafi ta dangin uba tausayi , jikina na bani akwai abinda yasa suka nisanci juna dole ina bukatar nasan haka har lokacin aunty tana kallonsu har sanda maryama
ta nufi kofar shiga bangaren umma shi kuma habib ya nufi get din gidan da alamun fita zai yi ta saki labulen tana sauke naunayen ajiyar zuciya ta koma ta zauna cikin zullumi tana tuno rayuwarta ta baya "
Maryama bata iske umma a falo ba dan haka ta samu waje ta zauna akan d'aya daga cikin kujerun falon ta runtse idanunta tana tunani "anya ba wani mummunar abu mahaifiyata ta shuka ba wanda yasa yan'uwanta suka gujeta ita kuma take jin tsoron komawa garesu ba ?"anya ma yan'uwanta su suka d'aura aurenta da mahaifinmu ? anya ma akwai gasky a zamanta da mahaifinmu ? "wad'an nan tambayoyin tayita jerowa kanta wanda bata da mai bata amsa sai mahaifiyarta ko umma ."
shiru ta sake yi tana qoqarin kawar da zarginta akan iyayenta bata san shigowar umma ba sai dai taji an girgizata sannan tayi sauri ta juyo cikin tsoro taga tana kallonta tace "maryama mai kike tunani haka ?na shiga uku ni aseeya kar dai abinda ya faru Kika zauna kina tunani ?" nan da nan ta soma girgiza mata kai alamun "a'a! tana in in nah "amm uhm Allah umma bashi bane ."umma ta girgiza ka fadanta cikin sanyin murya "kin kuwa san lokacin dana dauka ina miki magana baki sani ba ?na jima anan ina kallonki maryama kina tunanin abinda ya faru d'azu still maryama kai ta girgiza mata alamun" a'a!
Cike da nuna kulawa umma ta juya ta qarasa kitchen inda fridge yake ta isa ta bud'e ta dauko kwalin hollandia ta rufe fridge ta matsa kad'an inda d'an qaramin tray da glass cup's Ke kansa ta d'auki d'aya ta dawo inda take zaune ta janyo kujera gaban maryama ta zauna tana kallonta ta zuba mata hollandia ta mika mata tare da cewa "gashi ki sha dan nasan har yanzu baki sakawa cikinki komai ba ta kai cup bakinta tana kallon umma kad'an ta sha ta kawar da bakinta alamun ya isheta."
"karki sake tunanin abinda ya faru d'azu abinda ya rigada ya faru ya faru karki sakashi aranki yazo ya dameki wani ciwo yaje ya kamaki mu shiga uku dan sai nafi kowa shiga damuwa "Allah umma bashi bane wannan ai idan da sabo na rígada na saba "
"Wani kallo umma tabita dashi tare da sanyaya muryarta tace "idan bashi bane maryama sanar dani matsalarki dan bayan mahaifiyarki baki da wanda ya fini ina jinki tmkr ni na haifeki bancin ke kadai uwarki ta haifa da tuni na kwaceki gbdy daga hannunta , wannan soyayyar da nake miki yasa na janyoki jikina sosai karki ji komai sanar dani damuwarki ta fad'a tana kallonta ."
sunkuyar da kanta kasa tayi tana wasa da yatsun hannunta kusan second goma sannan ta motsa labbanta "daman ba komai bane kawai ina son nasan inda dangin aunty suke, ko sanin labarinta "me yasa bata zuwa wajen yan'uwanta suma kuma me yasa basa zuwa wajenta?" laifin me tayi masu? " me ya faru daita tunda na taso nake ganinta cikin damuwa da raunin zuciya wanda har yasa nima nake jin haka atare dani ."?
Wani dogon ajiyar zuciya umma ta sauke cikin fargaba ta tashi zata wuce har ta juya maryama tayi saurin riko hannunta cikin nata "umma ! ta kira sunanta muryarta na rawa cak umma ta tsaya tare da juyowa fuskarta da tausayawa itama maryama mikewa tayi cikin tsananin tashi hanakali ta rusuna kasa ta daura hannuwanta a saman kafafun umma cikin raunin murya ta fara mgn Kmr zatayi kuka "umma nasan Kinsan komai daya faru da iyayena dan allah karki boye min gskyr dana sanki daita "
umma ta zare hannuta ta sake juyawa "umma Kodai mu din bata hanyar sunah aka haifemu bane ?"
Umma ta juyo da sauri tana dubanta qirjinta na dokawa da karfin gaske "maryama ta gyada mata kai kana ta cigaba da mgn "duk yadda muke da aunty duk shakuwarmu da soyyyar da take nuna mana ta kasa fad'a mana haka kema gashi umma zaki wuce ki barni byn kece kika bukaci kisan damuwata .
"Nasan kinsan komai daya faru ki fada min mu san matsayinmu wata killa ma shine dalilin da yasa muke ganin tasko acikin gidan nan dan girman allah umma karki boye min abinda yafi komai mahimmanci arayuwarmu ki fad'a min na rabu da nauyin dake daskare da qirjina ta qarasa mgnr cike da sheshekar kuka ."
Girgiza kai umma ta shiga yi ta dawo inda take tsaye ta kamota ta zaunar daita akan kujera tana kallonta cike da tausayawa kusan mintuna ashirin sannna ta numfasa tana cewa "ku din ba shegu bane ku din yan halak ne" naunayen ajiyar zuciya maryama ta sauke tana kamo hannu umma cikin nata "kinsan kowani d'an adam da yadda yake kar'bar gaddararsa . wasu mutane basa gane rayuwa duk yadda allah ya rubutawa bawa babu wanda ya isa ya canza maka ita,ita qaddara kuma tana fadawa bawa daidai da yadda allah ya hukunto masa qaddara bata san talaka ba bata san mai kudi ba ,qaddara ce da rabonku ta nisanta mahaifiyarku da yan'uwanta yan'uwanta sun kasa kar'ban qaddarar data fad'a mata amatsayin su na muslimai amman mgn ta gsky ku din yan halak ne sai dai akwai yan'uwanki da'aka samesu bata hanyar aure ba .."
nan take jikin maryama ya kama rawa tmkr mazari ta tsaya tana kallonta tana assessing maganarta umma ta damke mata hannu gam cikin nata tana kallonta tana jin yadda jikinta Ke rawa tamkr mazari , maryama tayi imani bancin a zaune take da ta tabbatarwa kanta kafafuwanta bazasu iya d'aukar ba, da zuwa yanzu ta zube kasa."cikin kyarrrma wasu hawaye masu zafi suka shiga turereniyar zubo mata tana jin wani zafi a qirjinta mara misaltuwa cikin ikon allah allah ya bata ikon furta kalmar "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun shi tayita furtawa tana maimaitawa still jikinta da zuciyarta na rawa ."
Umma ta kalleta cikin sarewa ta cigaba da magana "wannan qaddara ce maryama km kowani bawa da tashi irin kalar qaddarar bata wuce Kan kowa ba , ki godewa allah da yasa ta hanyar aure aka sameku bilkisu na bani tausayi matuka kullum idan na kalleta sai na zubar mata da hawaye , da gatanta da komai tana rayuwa tmkr bata da kowa ,tana rayuwa cikin kaskanci alhalin bata cancanci haka ba tunda taji an samu wasu babu aure taji komai ya tsaya mata cak hatta shi karan kanshi labarin taji ya fita kanta ."
Mahaifiyarki haifaffiyar wannan gari ce anan aka haifeta aka haifi iyayenta ke hatta kakaninta ana aka haifesu sune asalin yan kasa "Idan mutun ya shigo jahar lagos din nan ya tmbyi family's din alhj rafi'u giwa to babu wanda bai san mahaifinta ba ."mahaifinta ko nace dangin mahaifiyarki gbdy masu arziki ne ."mahaifinta alhj rafi'u giwa yana da mata hud'u kinga kenan suna da yan uba a qalla guda talatin sai dai bazan iya kawo miki sunansu ba ina dai jin Aisha , hauwa wacce suke kira da jiddah abakinta gbdy a gidansu bilkisu ce auta a mata sai kannenta biyu maza dake binta daga kanta mahaifiyarta bata sake haihuwar mace ba haka ma sauran bangaren matan sun daina haihuwa wanda hakan yayi sanadiyar da soyayya mai karfi ya shiga tsakaninta da mahaifinta da yan'uwanta gbdy kowa yana sonta kasancewarta auta a mata "
gabadaya yan'uwan bilkisu masu kudi suka aura daga wanda yake london sai wanda yake Canadá ko American ,mafi yawa daga cikin yan'uwanta suna wata kasa daga maza har mata idan kuma anan ne zaki iske su cikin VI ita kadai ce ta auri talaka marashi ,dan gbdy asalin mahaifinki talakawa ne idan aka cire abban sadam wanda yake da d'an rufin asiri dan yana da gidan bread da kowa ya dogara dashi amman basu da komai ."
"bilkisu ta taso cikin gata da soyayya da kulawar iyaye tun daga tasowarta har zuwa girmanta duk abinda take so shi takeyi ta taso cikin soyayyar iyaye dana yan'uwa kowa yana sonta sannan ta taso da farinjin samari acikin family's dinsu kasancewarta kyakkyawa hasalima kyawun jikinta kika d'auko fuskarki ce ta mahaifinki amman km shi din ma baki dauko farinsa ba dan shi fari ne sol tmkr bature kmr yadda kike ganinsa a hoto ." kowa na sonta da nuna mata soyayya ,acikin masoyanta akwai mubarak dake mutuwar sonta, mubarak cousing dinta ne da ubansa da uwarta uwa daya uba daya kuma shima mahaifinsa mai kudin gaske ne km shi kadai suka haifa ,bilkisu na da shekara shabiyar a duniya alokacin tana ss 1 a secondary school alokacin mahaifiyarta da mahaifin mubarak sukai alkwarin aure a tsakanin yaransu dan mubarak din zai yi tafiya zuwa american qaro karatu , sun bar mgnr atsakaninsu idan ta gama karatunta na secondary sai ayi musu aure ."
mahaifinki ussein adam shima asalin haifaffen garin nan ne haka iyayensa sun kasance su takwas ne a wajen iyayensu mata hud'u maza hud'u umar ,fatima ,gali saadatu ,nazifi fadeela Kmr yadda kikasani , hassana da ussein ne auta ."
yana da shekara ashirin da takwas a duniya ya fara aiki a gidansu bilkisu ta sanadiyyar abokin abban sadam abdulwahab wanda shi gadi yake a makotansu ." mahaifinki ussein ya kasance direban ne gidansu bilkisu wanda Ke kaita school , idan lokacin tashi yayi ya koma ya d'aukota duk inda zata shike kaita hussein ya kasance mutun ne mai tsananin kirki gashi kyakkyawa aji farko illarsa dai shi din ya kasance talaka ne mai son jin dadi arayuwarsa km yana harka da yammata da shaye shaye sai dai bai ta'ba barin gidansu bilkisu sun san da zaman wannan halin nashi ba a boye yake yi saboda tsira da aikinsa ."
Maryama ta runtse idanunta tana jin wani tuttukin bakinciki a zuciyarta. ta d'aura kanta akan cinyar umma ko zata samu sausaucin zugin da zuciyarta take ,dan tun baaje koina ba ta fara datasanin jin labarin iyayenta , mahaifinta manemin mata ne ga shaye shaye a iyan nan ma kad'ai ta raina kanta ta sake yarda su din marasa gata ne ."
" tun farkon ganin bilkisu da ussein taji ya burgeta daman shi Allah yayi masa farinjin mata dan atarihinsa bai ta'ba cewa yana son mace ba dan har prouding yake , wannan yasa ya qara samun kusanci daita sosai , duk abinda taci sai ta rage masa idan zai kaita school ta bashi tun abun yana bashi mamaki har yazo ya daina bashi mamaki ya ajiye abun amatsayin ita din mai alkhairi ce , shima kma yana kulawa daita sosai dan hatta murfin mota kafin ta fito ya fito ya bude mata sannan idan sun iske an gama assembly zai tabbatar da ta shiga class akan idanunshi sannan zai juya ya koma gida ,ga iya bada labari, ussein ya iya bada labarin da zai saka mutun nishadi amman fa ga wanda yake da mahimanci a wajensa duk wannan yana cikin abinda yasa bilkisu ta sake sakewa dashi , shiyasa kullum bata da magana sai na fadar kirkinsa a wajen iyayenta wanda har hakan yasa iyayenta suke son batunsa tana sa ayi masa alkhairi na mussaman kullum da irin kyautar da take sa ayi masa ."
haka rayuwa tai ta tafiya mubarak na kiranta a waya amman sam bata bashi lokacinta yayinda wata irin shakuwa mai karfin gaske ta shiga tsakanin ussein da bilkisu lokacin da ta kai shekaru sha bakwai ta fahimci ba shakuwa bace kawai a tsakaninsu soyayya ce mai karfi wanda shima zuwa lokacin ya kamu da matsanancin soyayyarta ta yadda ya kasa hakuri sai daya zaunar dani ya fad'a min ciwon dake zuciyarsa yace zai yi qoqarin ya boye nashi domin itama bilkisu ya fahimci irin son da take masa bazai ta'ba barin wannan soyayya ya tabbata a tsananinsu ba domin dai yasan tafi karfinsa tafi karfin aurensa ita din ba sa'ar
aurensa bace babu ta yadda zai sameta arayuwarsa ."
"Nima na karfafa masa gwiwa ya danne abinda yake ji akan bilkisu na nuna masa bambamci dake tsakaninsu daita samun auren irinsu akwai wahala duk da babu yadda allah baya al'amarinsa shi yayi talaka kum shi yay mai kudi nace yayi addua sai allah ya kawo masa sauki da mafuta , amman alokacin ya sheida min zai ajiye aiki ya nemi wani still dai nice na hana na bashi kwarin gwiwa ya cigaba da aikinsa ya dai rage sakar mata fuska da kusanci daita ."
yana cikin wannan halin kwatsam bilkisu ta bayyana masa soyayyata da fari yaki amincewa hakan yasa ta shiga damuwa mai tsanani har rashin lfy ta kwanta batare da iyayena sun san akanshi take ciwon ba wanda ta kai har dakin daaka bashi a gidan take biyosa tana kukan ya amshi soyayyarta "ya zaunar daita ya fad'a mata gsky soyayya atsakaninsu ba abu ne mai yuwu wa ba duba da matsayinta da nashi , kuka take tana nuna masa babu wani bambamci a tsakaninsu dashi duk abu daya ne a wajen Allah da kalamai masu sanyaya zuciya da soyayya tasa ussein ya amince tunda daman shima yana sonta ranar daya amince aranar yan gidansu suka ga ikon allah domin dai bilkisu ta warke daga rashin lfy da take suka fara gudanar da soyayya ."
" tun tana boyewa har tazo ta fara bayyanawa zuwa lokacin a family's duk wanda yasan bilkisu yasan ussein idan har kana son kaga kyautar bilkisu ko yalwataccen fararta to kayi mata mgnr ussein family's dinta babu wanda bai san ussein direba ba idan ya dauko ta daga school zasu samu waje su parka su sha soyayyarsu ussein yana da yammata masu son shi amman soyayyar bilkisu tayi karfin da bazai iya cigaba da soyayya dasu ba ,wata irin soyayyar ussein Ke nuna mata mai karfi wanda har ta kai yana iya ta 'bata batare data hanashi ba nasan wannan ne saboda ussein na kawota gidan nan wajen mahaifiyarsa akwai lokacin dana shiga bangaren hajiya bata nan na iske su a dakin tana kwance ajikinsa sanye da kayan makaranta ajikinta suna romance ."hajiya mahaifiyar ussein ba ƙaramin jin daɗin haɗuwar bilkisu da ussein tayi ba ganin yadda yaron nata ya fara natsuwa ba kamar daba ba yanzu duk wani harkar mata ya jinginar da ita, haka zalika shaye shayensa yayi sauki sai wanda ba'a rasa ba."
Bayan bilkisu ta kammala karatunta na secondary akace ta fito da miji saboda masoya sunyi mata yawa kowa na sonta da aure km mafi yawansu cikin yanuwa ne sai kawai ta gabatar da ussein amatsayin mijin da zata aura hajiya rahma na gama jin abinda bilkisu ta fad'a ta mike tsaye tana dubanta abun ya mugun girgizata a matukar firgice tace "bilkisu banji abinda kika fad'a da kyau ba ina son ki sake maimaita min ,fad'a min naji da kyau tayi magana a tsawace batare da wata fargaba ba ta sake maimaita abinda ke ranta ai nan take mahaifiyarta da yan'uwanta da suka fito ciki d'aya suka nuna rashin amincewarsu mamakinta ne ya kamasu daman shakuwarsu ba iya nan ta tsaya ba ,har ta kai matakin soyayya juyin duniya akayi daita tace ussein take so har da ikirarin muddin zatayi aure to shi zata aura ,nan fa suka fara raba jaha da mahaifiyarta yan'uwanta kowa zaginta ya shiga yi me zatayi dashi ta rasa wanda zatayi soyayya sai direba common direba zata aura ? ita dai jinsu kawai take amman ita aranta ta kudurta komai zai faru sai dai ya faru amman ita ussein take so km har lokacin mahaifinki na shaye shayensa sai dai ba kowa ke iya fahimtar hk ba km nasan yawon tsaftansa da amfani da turaruka masu kamshi yasa baa ganewa amman mu dake rayuwa a gidan nan mun sani tunda idan yana gida yana shan kayansa a bayan dakin salma lokacin baa gina ba ."
Tashin farko mahaifiyarta tasa akayi kiransa cike
da matsanancin fargaba da tashin hankali ya nufi part dinta bakinsa dauke da sallama ya shiga falon tana zaune akan kujera na alfarma bata amsa sallamar da yayi ba haka zalika bata dubeshi ba tun kafin ayi masa gurin zama yayiwa kanshi yana mai yi sunkuyar da kanshi a kasa agabanta tmkr mai neman gafara ahankali ya furta" hjy barka da dare ta dago kai daga Kan tv ta maida kanshi tana qare masa kallon tsab tana nazarinsa ko kayan kirki ma babu ajikinsa kana kallonsa kasan mataiyaci ne mai yaci bare ya bawa bilkisu shi kuwa kallo daya zaka masa ka tabbatar da cewar ba cikin natsuwa da kwanciyar hankali yake ba tunda ya samu kiran gaugauwa daga hajiya rahma bai sake samun kwanciyar hankali ba har zuwa yanzu da yake durkushe agabanta sai data gama qare masa kallo sannan ta numfasa ta fara magana a kausashe "meke tsakaninka da bilkisu ?da sauri ya girgiza mata kanshi alamun babu komai ."
Shiru tayi tana cigaba da kallonsa kafin daga bisani ta cigaba da magana cikin bacin rai "kace babu komai ?da sauri ya girgiza mata kai alamun Eh !
"ni nasan akwai komai amman tunda kai da kanka kace babu komai to ya tsaya a babu komai din domin idan ya zamo akwai komai zaka hadu da mummunar bacin raina zan maka abinda har ka matu bazaka manta dani ba sannan daga wannan lokacin aikinka ya qare acikin gidan nan ya dago da sauri yana kallonta a tsorace "haka nake nufi ko kana bin mu bashi ne da ka wani tsareni da ido .?"
ya sake girgiza mata kai alamun a'a ! "to maza ka tashi yanzu yanzu ka tattara komai naka ka bar mana gidan matsiyaci banza kawai ,kaga yarinya qarama shine kake son kayi mata wayo, guda nawa bilkisun take da zata auri me shekarunka ? Idan km kwadayin kudin ubanta kake kayi kad'an kaci . matsayinka bai kai nan ba, ka bari ya'yan manya ya'yan masu arziki irinta su more ba kai matsiyaci ba , matsiyacin ma wanda ko rigar kirki baka dashi tana zuba ruwan bala'i ya zabura ya mike da sauri zai wuce tace " ba estate din nan ba ko a bakin get din estate din nan aka gaya min anganka wallahi wallahi sai nasa an daure min kai ko nasa a 'batar min da kai idan ma ba son abun duniya da son zuciya irin naka ba ina kai ina bilkisu? kai yanzu kaga dacewarku daita ?da sauri ya girgiza kai "a she kasan gsky maza tashi ka bani guri matsiyaci banza kawai ko maza sun qare a duniya mai bilkisu zatayi da kai da sauri ya qarasa barin falon bai tsaya jin sauran karashen zancen ba yana fita daga falon bilkisu ta fito daga d'akinta daman km hayaniyar mahaifiyarta ce ta fito da daita ta tmbyeta ita da wa ye ."
"Nida wannan matsiyacin ne dake neman cutar da rayuwarki "ta bata amsa atakaice tana dauke kanta bilkisu tayi shiru tana nazarinta idan har ta fahimceta da ussein take ? da sauri ta nufi kofar fita ta dakatar daita "idan kika sake kika bar falon nan sai na tsine miki albarka cak ta tsaya tana kallon mahaifiyarta " shasha shar banza da bata san ciwon kanta ba duk cikin yanuwanki wani dan iskan kika ga ya kawo miji Kmr wannan tsukakken da ko kayan kirki babu ajikinsa kullum yana yawo cikin kodaddun kaya ,kisani ko zaki mutu bazaki auresa ba na haramta miki aurensa ke intakaice miki baki da miji sai mubarak dan albarka in sha allahu
a ranar useein ya tattara ya bar gidan ya dawo dakinsa dake nan byn makaranta faidiyya ."
Tun daga ranar lamari ya sake lalacewa domin tunda bilkisu tasan ya bar gidan hankalinta ya tashi ta shiga damuwa sosai ta kauracewa kowa numfashi kawai take acikin gidansu amman rayuwarta da komai nata yana wajen ussein ta kirasa yafi sau babu adadi bai daukar kiranta da kyar da ban hakuri da turo sakonin ya sauko sannan ta dawo daidai, acikin satin tasan yadda tayi suka hadu da ussein maganar gsky ussein na sonta shima bazai iya rayuwa babu ita ba ,sai dai wulakancin da mahaifiyar bilkisu tayi masa da kiransa matsiyaci da tayi shi yafi komai tunzurashi ,domin duk gargadinta a banza ya daukesu babu abinda yasa aransa kamar cima burin sake kwace mata yarinya ta kowani hali sannan bai boye ma mahaifiyarsa komai da irin wulakanci daakayi masa itama kwarin gwiwa ta bashi tunda yarinyar tana son shi a matsiyaninsa talaka kar ya kuskura ya rabu daita ai su suke da mace sune a wahala , ina son nayi mgn alokacin amman babu halin yi a gabanta domin ussein shine auta km soyayyarsa dabam ce acikin yayanta amman dana fad'a masa gsky ya janye kudinrinsa ya rabunmusu da yarinya "
"nasan duk wannan ne sbd ni abokiyar hirarsa ce
dan duk gidan nan da yan'uwansa mata bai yarda
da kowa ba sai ni domin yace ina da sirri wasu abubuwan ma a gabana suka faru ,ussein ya sha kawo min bilkisu bangarena ta yini anan bilkisu na da matukar kirki da son mutane sannan bata da rowa idan zata zo wajena tana kawo min abubuwan amfani ga aiki da take min sam bazakice diyar mai kudi bace bata da son jikinta tana son aiki sosai da son mutane sadam kam ya sha gata a wajenta dan komai ta gani na yara zata siyo ta kawo masa wanda hakan yasa naji ina matukar qaunarta har cikin raina nake jin tausayinta domin tana sakewa ta fada min damuwarta da duk halin da take ciki a gidansu da yawon mgnr aurenta da mubarak da mahaifiyarta ke mata tana nuna mata mubarak yafi ussein sam bata dace da ussein ba ."
"ni kaina nazo na gano bata dace da ussein ba a wani zuwa datai na zaunar daita nace ina son nayi magana daita a matsayinta na kanwata da muka fito ciki daya baa matsayin matar da kanin mijina keso ba ta bani hankalinta ni kuma na fara magana bilkisu ko kinsan ussein yana shaye shaye ? ."tace min "eh !tasani km tayi masa mgn yace da zarar ya auret zai daina ,na numfasa nace "ke kin yarda zai daina ?tace min "eh ! Ko kinsan yana da yammata byn ke ?ta sake ce min eh ai ya rabu dasu Ina son na bata shawara ta auri mubarak ta bar ussein amman ina jin tsoro kar taje ta kwashe ta fada masa tunda idanunta sun rufe shi kuma ya fadawa mahaifiyarsa na samu matsala na kama bakina amman duk wanda ya kalli bilkisu km yasan family's dinta gsky yasan basu dace da juna ba ."
Soyayya ta sake yin karfi a tsakanin ussein da bilkisu dan babu abinda barinsa gidansu bilkisu ya janyo sai tabarbarewar rayuwar bilkisu dan a tunanina ussein ya fara saduwa da bilkisu batare da aure ba ni kaina alokacin naso ace iyayenta sun barta ta aureshi tunda ita taji kuma tagani amman mutanen nan suka ki saboda kyamar talaka , dan da irin rayuwar da suke gara ace aure sukayi, bazan ta'ba mantawa ba wata rana bilkisu ta sameni tana kuka na tmbyeta bata boye min ba ta fada min ciki gareta nan take na shiga damuwa mai tsanani nace "haba bilkisu me yasa zaki sakewa nmj jiki haka ?bakya jin tausayin iyayenki da yan'uwanki bakya gudun ranar da ussein zai juya miki baya ?ina ta mata fad'a Kmr kanwata ta jini ita km tana kuka tace ."na taimaketa acire mata cikin nace babu ruwana bazan saka hannu a kashe rai ba ,muna cikin wannan halin hjy ta shigo ashe taji duk mgnr mu itama cewa tayi abarshi kar acire taje gida zata samu iyayenta sai ayi mgnr aure kawai abu ya bani mamaki kamar wasu yoroba tunda sune ake irin wannan rayuwar dasu sai kayi ciki zaa yi aure km su yin ciki ba wani aibu bane a wajensu murna ma zaayi da samunsa tun daga nan na fahimci duk abinda ussein yake da saka hannun hjy ciki ."
Tô tun daga ranar ban sake saka bilkisu acikin idanuna ba a she byn ta bar wajena ussein ya bata maganin zubar da ciki ta sha koda ta koma gida sai ciwon ciki kwana tayi tana murkususu ciwo har garin allah ya waye ,cikin yaki fita ga ciki yaki daina ciwo iyayenta dai suka gaji suka kira doctor ya dubata byn ya gama dubata ya rubuta mata scan tô a wajen scan ne likita yaga ciki a mahaifarta tunda likita ya soma bayani mahaifiyarta ta rikice ta dimauce ta kasa gane takamaiman abinda yake fada ganin ta rude yace mata wani abu ya gani me kama da gas a mahaifarta amman ta kira wani daga gida yazo nan ta kira Aisha yayar bilkisu hankalinta a tashe tazo ta samu hjy rahma a reception zaune tayi tagumi bilkisu zaune a gefenta cikin tsoro da fargaba scan taso cikin ya fita cikin sauki batare da kowa yasani ba hjy rahma tace Aisha tashiga taji me doctor yake nufi da gas din da ya gani a mahaifar bilkisu ta shiga nan likita ya fad'a mata komai itama tashin hankali tashiga mai tsanani amman sai ta boye ta fito tana cewa uwar ulcer ke damunta nan hankalin mahaifiyarsu ya dan kwanta suka koma gida ."
Aisha ta kira bilkisu zuwa gidanta tana qarasowa bata tsaya wata wata ba ta rufeta da duka sai datayi mata mai isarta kamar zata kasheta sannan ta barta byn ta gama dukanta ta kira kaf yan dakinsu ta sheida masu sannan tasa akayi mata wankin ciki aka cire cikin lokacin da hjytr ussein taji babu cikin Kmr ta mutu dan bakinciki har da kuka tayi an cire mata jikanta dan karfin halin irin nata har da tmbyr bilkisu tayi wa ya cire mata jikanta ita km kuruciya ta fad'a mata tun daga lokacin hjy ta tsani Aisha da yan gidansu bilkisu amman km tana son bilkisu ace warta bazata tsaneta ba dan tana son danta."
Hajiya rahma ta lura tun da bilkisu ta dawo daga gidan Aisha ta warke sumul babu kwana ciwon ciki ta cigaba da abubuwanta sai dai Aisha ta kira hjy rahma tace kar a sake barin bilkisu fito koina har sanda mubarak zai dawo a daura masu aure abinda bilkisu ta tsani ji kenan dan ta tsani mubarak tsana mai girma bata ma son ana yi mata maganarsa karki ce shima mubarak din mummuna ne dogo ne sosai Kmr ussein sai dai shi baki ne kyakkyawan gaske dan sai dana sa ta nuna min hotonsa a istagram
an kafa wa bilkisu takunkunmi rashin fita koina hatta islamiyya ta daina zuwa alokacin sai datayi wata uku babu shiga babu fita kawai tana gida zaune km babu waya a hannunta an kwace da wayar hjy rahma take mgn da mubarak ."
Ganin Kmr ta kwantar da kai suna soyayya da mubarak Kmr gske yasa mahaifiyarta ta dauka ta cire komai aranta kuma taji dadin hk kulawa da soyayyarta ya qaru ta zaunar daita tayita nuna mata illar ussein tana qawata mata mubarak zataji dadin rayuwa agidan mubarak alokacin ta tmbayeta ta yarda zata auri mubarak tace eh ta amince wanda ba haka bane acikin ranta wata rana yan'uwanta gbdy suka zo gidan suna zaune a falon mahaifiyarsu yayanta abubakar wanda ya kasance first born a dakinsu yace a barta ta cigaba da rayuwata ta koma islamiyya Kmr kowa dan lokacin saukar alqurninsu ya kusa duk da bata zuwa baa cire sunanta acikin yan walima ba ba dan me ma zaa hanata rayuwa sbd wani matsiyacin banza Aisha da sauran yanuwata mata sukace a'a basu yarda da fitarta koina ba shi km yace abashi dalili gbdy suka kasa sheida masa dalili su dan haka yace dole ta koma islamiyya nasan kuna tunani ko zata hadu da wannan yaron ne yace su barta dashi idan ta isa tayi Kuskuren haduwa da ussein nan take uwar tace "ai bilkisunta ta canza bama zata kunyatata ba yanzu mubarak ne agabanta ."
Cikin satin aka dinka mata sabon uniform ta fara zuwa islamiyya Kmr abun arziki sai dai aranar ta samu waya ta kirasa bai shiga ba sai ta kirani nan na tmbyeta kwana biyu da halin da take ciki ,bata boye min komai ba a karshe tace na fadawa ussein ya kunna wayarsa nace mata "to! na qara da yi mata fad'a kar ta sake yarda dashi tace taji nan fa suka sake din kewa da ussein soyayya ta sake karfi har tafi nada da zara ta fito daga gida suke haduwa dashi km ni na tabbatarwa kaina bazasu ga junansu su bar junansu hk ba tunda sun dandani juna dole sai sunyi wani abu duk da shiedar zina tana da wahala "to ! bazan manta ba ranar wata asabar da safe ta fito daga gidansu da nufin zuwa islamiyya kai tsaye dakin ussein ta zarto ashe ana biye daita abaya batasani ba har ta shiga dakinsa tana shiga suka fara abinda suka saba suna cikin wannan halin sai shigowar mutanen gidansu sukaji tana rungume ajikinsa aiko ranar munga tashin hankalin da bamu ta'ba gani ba ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 18
"wato afa akan dai yarinyar nan ce da nazo akanta yar kanin mijina daya mutu ya barmana amatsayin riko to malam kamar yadda kasani banason yarinyar nan na tsani na ganta dan ina ji ajikina akwai nasarori da anan gaba zata iya samu domin soyayyar da mutane suke nuna mata kamar ma aikinka na farko bai ci ba, yanzu haka samari sunfi biyar da suka nuna suna sonta sai dai dadin abun da zarar sun zo lokaci kad'an sai su gudu ."
"to ga aikin nan yaci zaki ce kamar aiki bai ci ba , ai haka zasu dinga zuwa suna 'bata mata lokaci suna wucewa batare da tasamu wanda zai aureta ba babu fa wanda zai like mata acikinsu sai matsiyaci da zarar masu arziki sunzo zasu gudu ."
"Ai ni ba abinda nake só kenan ba ,ai bana son ko matsiyaci ma yazo wajenta nafi son ta qare rayuwarta a kaskance a bauta da wahala , sai tawa yar saurayin da yake sonta mutun d'aya ne kuma ba wani mai abun kirki bane gashi kace yarinyata zata samu farinjin samari masu kyau da kudi sai gashi sa'banin haka nake gani madadin maryama tayi bakin jini acikin mutane da samari duk banga haka ba ."
"kullum farinjinta sake qaruwa yake jamaa suna matukar qaunarta basa son kula ya'yana koina akaje sai dai ace a gaishe da maryama amman banda ya'yana , wani abun bakinciki afa har yaran nawa suma kullum maryama , suna matukar sonta sunki su gane ita din matsalarsu ce, ko wani abu nayi mata sai dai kaji suna min fad'a suna nuna min rashin daidai nan ta tsaya ta sauke numfashi da ajiyar zuciya ,afa yace "to yanzu ki takaita matsalarki me kike son ayi ?
Aunty salma ta gyara zama tace "ina son a fara rabata da ya'yana ina son naji sun tsaneta fiyye da yadda nake jin tsanarta acikin raina wannan shine kawai muradina kafin nazo neman wani bukatar ."afa yayi murmushi yace "ai wannan shi yafi komai sauki ki tafi gida kawai zaki ga aiki da cikawa cikin sati biyu masu zuwa , amman ina son ki dawo kafin kwanakin su cika akwai abinda zan baki indai har na baki ki kai amfani dashi magana ta qare amman yanzu zan fara jaraba 'yan abinda bazaa rasa ba ."
aunty salma tayi godiya ta ajiye masa kudi ta fice tana faman zuba godiya tana cigaba da zagi da maseefar kiyayyarta da maryama har ta fice daga gidan afa ta dawo gida tana saka da warwara dan ita ko kashe maryama afa zai yi tana só saboda tsanar datai mata yarinya sai kace lu'u lu'u ai muddin tana cikin gidan sai ya'yanta sun rigata samun gidan aure kafin tayi ,idan kuma har zata yi auren zata sa afa yayi mata aikin da zata auri matsiyacin daya fi ubanta talauci ."
*****
Bayan kwana biyu da faruwar wannan alamarin maryama tana tafiya cikin kayan islamiyya ta Ardus-salam yayinda hannunta ke rungume alqurani , yammaci ne duk mazan unguwarsu sun dawo daga aiki duk inda ta wulga sai an kalleta da shaawar tafiyarta tmkr bata son taka qasa tana cikin tafiya taji tafiya abayanta bata juya ba dan hakan baya daga cikin d'abiarta , sai ma qara saurin da tayi ta cigaba da tafiyarta saboda tasan kowaye ita yake bi zarginta ma cikin samarin unguwarsu ne dan akwai masu nuna suna sonta acikinsu ."
"maryama wannan uban sauri haka da kike zabgawa ko dan gudun kar na biyoki ne ?ta tsaya cak lokacin data fahimci muryar malamin islamiyyarsu ne na Ardus-salam mlm yahuza ta juyo a natse ta dubeshi cikin nikaf dinta tare da girmamawa ta gaishesa ."ya gyara tsayuwarsa yana kallonta , kunyarta ita tafi komai tsoratashi ,duk iya takun saurayi in har ya had'u da mace mai kunya yana samun karaya matuka a zuciyarsa ."
yayi dan murmushi irin nasu na ustaz "maryama har kullum zuciyata bata da sukuni jiddan wala khairan ,na kasa mantawa dake ,bani da wani sukuni face na samu amsarki game da bukatata dana kawo miki ."yayi shiru tare da tsayawa yana sauraron yaji me zatace nan take tayi kicin kicin tamkar wacce aka tsare da wuka zaa yankata sai da ta dauki second goma sannan tace "uhm !sai kuma tayi shiru ta qasa qarasa abinda zata fad'a maganar ta makale acikin zuciyarta shi kanshi ganin motsa lip's dinta bai sawa ranshi cewar zatace uffan ba bayan abinda ta furta ba ."
ba yau bane farko haka zalika yasan ba yau bane zai zama karshe ya saba tareta a hanya ta kasa ko ambaton sunan shi bama shi kadai ba kusan mutane suna yawon fad'ar haka akanta bata da yawon surutu da saurin sabo da mutun duk wanda ka ganta dashi tana d'ar d'ar alamun tsoro shima dan matsayin da yake dashi na malaminta ne yasa har ta tsaya akan hanya babu wanda ya kai ta tsaya dashi akan hanya ".
"Maryama idan na lura da yanayin fuskarki ba soyayyata bace baki amsa ba amman kuma bazan tabbatar akan cewar kin amsa ba ,tunda a kwayar idanunki kawai nake iya karantawa shine kunya ce ta hanaki ki fad'ar abinda Ke cikin zuciyarki maryama ki daure ki sanar dani menenê acikin zuciyarki akaina ko zuciyata zata samu sukuni da natsuwa ?".
shirun dai da baya só shi tayi dan bata da abinda zatace masa ,bazata iya wata soyayya ba da'ace ta d'aurawa kanta soyayyar samari da lokacin da suke guduwa suna barinta da ba qaramin tashin hankali zata shiga ba gara ta qarasa rayuwarta haka tunda soyayya ba dole bane arayuwar mutun haka ma aure sunah ne matukar mutun zai iya rike kanshi domin acikin
Sahbbai ma akwai wad'an da suka mutu basuyi aure ba dan haka mutun zai iya zamansa haka kuma aure da haihuwa bashi bane karshen duniya a ganinta ko babu shi mutun zai iya rayuwarsa ."
"hakika maryama duk cikin unguwar nan kai garin nan ma gbdy har cikin islamiyyarmu banga diya macen da take burgeni kuma zuciyata take dawainiya da tarin soyayyata kamar ki ba ki samar da amsar soyayyata a cikin zuciyarki ko zan samu farinciki da sukuni koda ta wata sigace da zan fahimta ."sosai hankalinta ya kai kololuwar tashi tama qasa tsayuwa bisa kafafunta , kafafunta suka shiga karkarwa ,yana son ya bata dama ta wuce gida saboda halin daya karanta atattare daita amman kuma bai gaji da kallonta ba kuma shi yasani ko zai kwana tsaye atare daita bazai gaji ba , sakina da kanwata ne suka zo zasu giftasu malam yahuza yayi sauri yace "sakina ku tsaya ga maryama tsaye ku wuce gida tare ."
Shukura ta kallesa tana jin wani irin tuttukin bakinciki acikin zuciyarta abun yayi matukar bata mamaki maryama tare da mlm yahuza malamin da take matukar só amman tsoro da shakkansa ya hanata fito da soyayyarsa
"malam ! kawai tace tayi gaba tana jan tsaki acikin ranta dan tasan muddin tayi a fili ta kad'e har ganyenta dan mlm yahuza babu wasa wajen disfila d'alibai da iya karatu da d'aukar wanka ga tsantsar kyau shiyasa kowani d'alibi ke matukar jin tsoronsa a kaf ardus-salam babu malamin da'ake shakka da só kamarsa da yawa yammata na qaunarsa ."sakina kam jikinta a matukar sanyaye ta wuce batare datayi mgn ba maryama ta bita da idanuwanta wani abu ya soki zuciyarta domin tun safiyar yau ta lura sakina ta canza mata abun ya matukar d'aure mata kai amman tayi mata uzuri da cewa yanayin rayuwa ne ."
Mlm yahuza bai sake magana ba sai tunanin kunyar shi da sakina taji dan ganinsa da maryama yasa ta kasa tsayawa dan haka yace "maryama sai gobe idan mun had'u a makaranta amman fa kisani bazan ta'ba daina tsaidake anan ba har sai ranar dana samu na cire kunyar nan kika amince min "Kanta kawai ta gyada masa muryata a matukar sanyaye tace "sai da safe ta juya ta cigaba da tafiya a natse bai bar wajen ba sai da tayi nisa sosai ta 'bacewa ganinsa ."
yana juyawa sukai ido biyu da mlm umar mai hausa atare sukai murmushi "wato kai har kullum bazaka daina wahalar da kanka akan maryama ba ko ?"Mlm yahuza ya qarasa inda mlm umar yake ya tsaya yana cewa "ya zanyi umar allah ya jarabeni da soyayyar maryama bazan iya hakura daita ba "kai kuma allah ya jarabi mata dayawa da sonka ba ?"wannan kuma damuwarsu ce ,ai dama haka zaka fad'a duk kuna son maso wani ,kai ma ka tausayawa masu sonka sai allah ya duba lamarinka ".
"Allah ma ya sani babu wacce nasan tana sona bare na tausayawa ya fad'a yana wani sham kamshi "Uhm uhm mutumina banda fad'ar son rai duk wanda ka fadawa haka zai d'auka bakasan abinda kakeyi ba ,"kaga umar rabani da wannan zance mu barta matsawar bata sarauniyar mata zaka min ba "karka duba yanayin gidansu maryama amman dai kai kanka kasan tafi karfin aurenka , maryama macece daya kamata wani hamshakin mai kudi yayi wuf daita ."
dan murmushi mlm yahuza yayi yace "haka ne amman ai duk mace bata fi karfin auren nmj ba kuma kowani mutun yana da nashi matsayin da zai iya burge mace , kuma ina dashi ina da quality da mace zata soni koda kuwa bani da kosisi bugu da qari ita mace ba kudi take bukata a soyayya da kulawa take so ni nan kuma zan kula da maryama ."
"da me zaka kula daita ?karka manta ita din cikakkiyar 'yar boko ce , yarinyar da idan ta fara aiki yanzu sai ta d'auki nauyin ciyar da mutanen gidanku gbdy dan haka banga abinda zai sa ka dinga wahalar da kanka kana 'batawa kanka lokaci akanta ba , kayi hakuri ka rabu daita domin dai babban goro sai magogin karfe ."
Mlm yahuza ya dan ji zafin maganar malam umar dan haka ya rage farar fuskashi "wai me kake nufi ? kana nufin dan ita din yar boko ce tana da kyau na bugawa a jarida kana tunanin zata samu aiki nan gaba zai sa ta iya fin karfin halittar ubangiji "? yahuza abinda nake son ka fahimta duk wad'an nan abubuwa da kake gani fifiko ne a tsakaninka da maryama kawai abinda nake so kaji aranka tafi karfinka tafi karfin aurenka ."
"kaga dan allah mlm ka barni ka zuba min ido ba wahalar banza nake yi ba ina cikin zuciyarta kunyar da take yawon nunawa akaina ta wadatar dani cewar nayi mata , nan gaba kad'an zata fahimtar dani ."Ka dai bi a sannu kar wata rana kana zaune wani hamshakin mai kudi ya shigo har cikin unguwar nan ya aureta .".
"bari kaji babu wani mai kudin da zai aureta domin suma masu kudin sunfi son ya'yan masu kudi yanuwansu , ita maryamar da ba galihu ne daita ba ,ai ba uban da zai shigo cikin wannan rubabbiyar unguwar ya kwashta ai duk wannan kyawun nata akan irinmu zai qare "yana gama fadar haka ya juya dan baya son ya sake 'bata masa rai ."
Tafiya kawai maryama take zuciyarta cike da kunci da tunani barkatai ba kuma akan mlm yahuza ba sai sabon sauyin data gani akan fuskar sakina dan na shukura mai sauki ne idan da sabo ta saba ita da yaran aunty hassana haka suke mata amman sakina fa basu saba haka ba suna matukar qaunar junansu tun suna yara su din masoya ne na hakika ."
da wannan tunani ta qarasa cikin gidansu kai tsaye ta nufi bangaren su sakina domin tambayarta dalilin sauyawarta ashe wahala ce ta shigo daita tana sallama aunty salma tace " Yauwa maryama d'auki tsintsiyar ki share min d'akuna tas shine amsar sallamar da aunty salma tayi mata kamar tace bazatai ba amman ta kasa ta ajiye alquranin dake hannunta ta d'auko tsintsiya ta fara shara batare da wata damuwa ba ."
tana shara aunty salma na zaginta ita da shukura amman sakina na zaune batace komai ba sa'banin da da bata yarda a zageta ko sakata aiki akan idanunta ,tana shara wani gurin da simiti wani gurin babu ga kuma sakina na zaune ta d'ago idanunta a natse ta kalleta taga kurar sharar na zuwa inda take muryata a sanyaye tace "sakinata ina ganin sai kin d'an tashi kinga kurar tana zuwa inda kike ta wani watso mata harara "ai gudun ruwanki nake kallo naga zaki shareni ko kuwa ."?
maryama tayi shiru tsaye tana karantarta akwai wulakanci acikin maganarta "ke kika kyaleta aunty sakina amman banda jakanta irin nata tana kallon mutane suna zaune zatace su matsa , banza shasha kawai mai siffar mayu ." inji cewar shukara dake zaune kusa da aunty salma abun bai yiwa aunty salma dadi sosai ba domin kuwa sakina taso ta furta ma maryama haka ba shukura ba ,sakina kam tun maganar farko datai bata qara ba ta tashi cikin bacin rai ta shige daki tana jin wani zazzafan kiyayyar maryama ."
Maryama tayi shiru kawai tana bin shukura da kallo "me kuma hakan yake nufi dani ? me na yiwa sakina ni kuwa daga jiya zuwa yau take fushi daita hk ."tayi wa kanta tambayar da bata da mai bata amsa sai sakina ita zagin shukura bai dameta ba kamar sauyawar sakina ta gyada kanta ta cigaba da shara tana tunanin laifin da taiwa sakina har ta qarasa ta wanke hannunta da kafafunta ta d'auki quraninta ta shiga d'aki inda sakina take zaune akan gado tana cika tana batsewa tana ganin maryama ta sake had'e rai Kmr taga mugun abu maryama bata damu ba ta zauna kusa daita ta soma janta da mgn taso tmbyrta laifin da tayi mata amman ganin yadda take barsarwa yasa tayi shiru daga karshe ta wuce zuciyarta cike da matsanancin damuwa ."
*******
Da misalin karfe d'aya na ranar laraba wanda yayi daidai da sauran kwana uku jirgin mr ata ya tashi zuwa france amman har lokacin jikinsa sai a hankali daga matsanancin ciwon kai ya dawo masa ciwon gabobin jiki dan ko miyo baya iya had'eyewa sosai mami ta sauko daga saman d'akin mr ata tare da likitansa byn mami ta sallame doctor rafeeq ta dubi maryam da nana hauwa'u tace "yayanku fa yau tsawon kwana biyu bashi da lafiya ku shiga ku gaishesa keda maryama ,jiki sanyaye suka ce" to! suka mike atare suka hau sama ."
A natse sukai knocking wanda nana hauwa'u ce tayi mryam na bayanta ara'be kusan second goma suka d'auka tsaye sannan ya basu damar shigowa d,akin ,da sallama suka shiga parlour suka gansa kwance akan doguwar kujerar kushin ya runtse idanuwanshi yana sanye da riga fari sol da gajeren wondo iya gwiwarsa yayinda hannunsa d'aya Ke daidai saitin zuciyarsa ya d'an bud'e idanuwanshi kad'an ganinsu yasa ya maida idanuwanshi ya runtse gam."
nana hauwa'u tace "sannu yayanmu ya jikin naka kayi hakuri walllahi bamu san baka da lafiya ba sai yanzu da mami ta sauko take fad'a mana " shiru yayi bai amsa mata ba nan da nan maryam ta shiga hankalinta dan tasan ita kam sai ya had'a mata da tsaki muddin tayi masa sannu suna zaune shiru nana hauwa'u ta d'an ta'ba maryam tana mai mata alamar ta gaishesa wani abu mai d'aci daya tsaya mata a wuya ta had'iye ta bud'e baki muryarta na rawa "yaya sannu "ta fad'a atakaice ilai kuwa tunaninta ya tabbata dan kuwa bai amsa ba sai ma tsakin daya ja yana cewa "auta ya bani abun na sha a fridge da saurinta ta mike ta isa inda qaramin fridge dinsa yake ta bud'e donsimo ta d'auko masa ta had'a masa da ruwa ta ajiye masa akan table din dake gabansa ."
"gashi yaya Allah ya baka lafiya ya d'an motsa lip's dinsa alamun ya amsa ya mike zaune da kyar batare daya kalli inda mrym take ba itama bata sake kallon inda yake ba sai ma fuskarta dake kallon wani katon hotonsa dake manne da bangon falon sanye cikin kananan kaya riga da wondo milk colour touch of black ya zura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa idanuwanshi manne da farin glass fuskar nan tashi a had'e Kmr koda yaushe "auta !
Ya kira sunan nana hauwa'u ta amsa da "na'am yaya! "shiga bedroom ki d'auko min wayoyina da sauri ta shiga wayoyin na kan katifarsa ta d'auko tana danna gefen wayar inda nan take wayar ta kawo haske screen ta duba fusakar wayar wata kyakkyawar fuska ta gani kanta babu d'ankwali gashin kanta ya zubo kad'an ya rufe mata gefen idanunta ."
ta tsurawa hoton ido sosai nan ta gane zane ne ba asalin hoto ba ahankali take tafiya tana kallon fuskar wayar duk da zane ne ,amman yarinyar tayi matukar yi mata kyau ta kai masa tana cewa "yaya zanen dake kan screen din wayarka yayi min kyau sosai wacece ?"tayi masa tmbyr tana duban mrym da hankalinta baya kansu yana can kallon mr ata , tana kallon kyaun da allah yayi masa ba abinda yafi burgeta dashi kamar sheidar sallarsa daya fito masa a saman goshinsa yayi baki tmkr tawadar Allah ."
ahankali zuciyar mr ata ta soma bugawa da karfin gaske yana jin tmkr ta kunno masa emotion's din da yake ta qoqarin dannewa acikin zuciyarsa nan da nan idanunshi suka canza kala cikin tunanin da maryam take taji yana cewa "yarinyar mafarkina ce dana zanata da hannuna, itace cikar burina ce farincikina ina matukar sonta itace mace ta farko da zuciyata take so .." jin haka yasa gaban maryam yayi wani mummunar faduwa sakamakon jin abinda ya fad'a ta juyo ahankali ta tsura masa idanunta duk da ba karon farko kenan ya ta'ba fadar haka agabanta ba amman na yau din yasa taji wani iri a gbdy ilahirin jikinta ta lura baya iya boye fellings dinsa akan zanen ."
ina ma zata ga fuskar yarinyar taga dame tafita da har zuciyarsa ta zabeta alhalin ita din ba gsky bace ?tuna zane ce yasa ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya mai had'e da zallar kishi "ina matukar sonta auta amamn na rasata a yanzu haka ina son raba rayuwata da tunaninta da duk abinda ya shafeta yana magana yana kallon screen din wayarsa wanda Ke dauke fuskarta "mun dace da juna ko ?ya tambayi nana hauwa'u yana lumshe tsumammun idanuwanshi dake cike da azaban ciwo ."
Nana hauwa'u bata bashi amsa tmyr da yayi mata ba ta kalli maryam dake tsaye tana dubansu idanuwanta cike da kishi ajiyar zuciya ta sauke tace "yaya zamu ce allah ya baka lafiya "na tambayeki baki bani amsa ba ya fad'a a mutukar fusace yana watsa mata harara "me kace ?" shiru kawai yayi tare da tsura mata idanuwanshi itama kallonsa take tasan abinda ya tsana kenan dan hk muryarta na rawa tace "kun..." kun dace sosai kawai dai matsalar ita din ba genuine bace wani dogon tsaki yaja yana cewa "nonsense !"you and this stupid girl should leave this room right now "ya fad'a yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa da sauri ta kamo hannun maryama suka fice daga d'akin ."
Bayan fitarsu kwanciya yayi yana cigaba da kallon hoton screen din wayarsa dayawa daga cikin hotunta ya konasu hatta tsarka zanenta dake wuyansa always yayi flushing dinsa ,kadan ne daga cikin zanenta suke cikin d'akinsa sai na kan screen din wayarsa suma nan kusa yana sa rai zai rabu dasu ya huta da tunaninta sosai yake kallonta "muguwa "ya furta a wahalacce "kin addabi rayuwata kin hanani zaman lafiya ke wace irin muguwa ce da zaki damun rayuwata ?ya tambayi kanshi yana mai kawar da kansa daga kallonta yana tunani "anya bazan dinga zagawa cikin anguwane anguwani ba ko allah zai sa na ganta "? wannan ai hauka ne mr ata kake shirin yi ,me yasa bazaka yarda cewar yarinyar nan ba gsky bace Kmr yadda aka Ke fad'a maka ?
shiru yayi yana jin wani irin buguwa da zuciyarsa ke yi akanta sosai yake son raba kanshi da tunaninta ."
Bangaren maryam kuwa suna taka step tana maseefa "nifa shiyasa bana son zuwa inda yake bashi da aiki sai maseefa da disga mutun sannan wulakancinsa baya qarewa akan kowa sai akaina ko ban shiga tsabgarsa ba sai ya hada dani ni wallahi bana son auren zan dai yi ne kawai dan kun dameni , dan allah ku raba ni da aurensa na huta tunda ba'ayin aure mutun daya ." murmushi nana hauwa'u tayi "na lura kishi kike da zane fa "babu wani kishi sister amman ka auri mutun zuciyarsa na mafarkin wata aljana can wannan ai sai su shafi mutun azo arasa meke damuna "hhhhhhh nana hauwa tayi dariya "yarinya kina da aiki kam dan fasa wannan auren sai dai idan daya daga cikinku ne ya mutu maryam taja tsaki ta d'auki hanyar da zata kai ta d'aki ta shige tayi kwanciyarta dan kar mami tayi amfani da zamanta a parlour tayita aikenta d'akinsa shi kuma ya samun damar ci mata mutunci ."
Mr ata na kwance akai knocking kofar falon yana daga kwance ya bawa mai yi knocking din izinin shigowa hisam ne ya shigo cike da kulawa ya qaraso ya zauan yana cewa "a she bakaji dadi ba ? ya amsa da kai kawai "oh my god amman dai ba matsalar nan bace ? "no ! wannan muguwar yarinyar ce "
maganar ta daki kunnuwan hisham ya dan tsaya yana kallonsa yana nazarin maganarsa "yes muguwa ce taki barin na ganta a zahiri taki barin zuciyata ta zauna yanzu ko mafarkinta nayi bata min magana , bata min murmushi this love is so hurt wallahi muguwa ce amman har yanzu ina jin sonta hisham na qasa cireta araina ."
ya sake kallonsa ya girgiza kai cike da tausaya masa ya mike da kyar ya shiga bayin dake ciki ya zubar da yawu ya dawo ya zauna ya sake kallon hisham yaga shi yake kallo fuskarsa da mamaki ya sake girgiza kai dan gbdy ya fahimci wa yake nufi "gsky wannan yarinyar tana baka wahala " ya langwabar da kanshi gbdy ya koma kalar tausayi "wallahi yau shekara nawa ina faman da soyayyarta amman sam sam yarinyar nan bata tausayina yayi mgnr duk jikinsa ya sake kana kallonsa kasan bashi da lafiya ."
"da ba dan baka da lafiya ba ai da mun dan dinga zagawaya cikin unguwani ko zamu ganta ko wanda yasanya nima nayi wannan tunanina hisham amman bazan iya ba ya fad'a yana lumshe ido yana jin wani d'aci a bakinsa wanda ya rasa na meye ,"karka ce haka ata ka bari idan ka samu sauki kaje france ka dawo lafiya sai mu fara nemanta " nace bazan iya ba wannan muguwar yarinyar kona ganta damuwa zata zame min
a zuciyata ."
Zuciyarsa na zafi yace tashi muje ka d'a zaga gari ko jikinta zai rage nauyin da yake "ya fad'a yana jin tsantsar soayyarta na ratsashi koina ajikinsa ya mike da kyar "ata kayi zauna gida wallahi jikinka babu kwari "karka damu muje kawai tunda kana tare dani bani da wata matsala ahankali suka sauko falon qasa babu kowa a falonta farko da alamun mami tana falonta na uku yaso sheidawa mami amman yasan zata hanashi fita koina dan haka ta kofar baya suka fice dan baya son escourt dinsa su bishi ya zauna shiru a gefen hisham dake tuki yana ciza lip's dinsa "ina muka dosa "?cewar hisham ".
muje gra dan ina ji ajikina a irin wuraren nan zamu samu muguwar yarinyar nan "hisham ya kwashe da dariya har da dukan stearing mota shi kuwa gogan ya hade rai a she a fili yayi mgn ba "wai muguwar yarinyar nan wallahi ata baka da dama
,yanzu dai wani gra ne a kusa damu ?mr ata yayi masa banza ya maida kallonsa gefen titi yana kallon mutane da motocin dake kai kawo "duk da kaki kayi mgn bari muje ikeja gra nan ma shiru yayi yaki cewa komai "gskiy ata ka iya bada suna pricess ta tashi da sarauniya ta dawo muguwa"dan allah malam ban son isknaci ka maida hankalinka ga tuki " ya fad'a yana nuna masa gaban mota da hannunsa "naji amman yanzu ace taki sa'a ka ganta a zahiri zaka ganeta "wallahi zan ganeta ". daga haka bai sake yin magana ba shiru motar tayi babu wanda ya sake cewa komai har suka d'auki titin ikeja ."
Ahankali Ummah da aunty da maryama suke tafiya a hanyar fitowarsu titin unguwarsu domin su dauki hanya zuwa marcaz duba jikin hafsat diyar aunty fati , maryamah ta hango mlm yahuza ya nufo hnayar da suke da littafi a hannunsa da alamar islamiyya zashi tun daga nesa ya fara raragefen alamun Kamala ya durkusa har kasa ya gaishe da aunty da Ummah tare da cewa "unguwa zaku né ? maryama ta d'an kallesa ta d'an basar dan kar aunty da umma su fahimci akwai wani abu atsakaninsu tace" rakiya zanyiwa aunty tare da umma zuwa bakin titi ."
" allah sarki ya sake durkusawa har kasa ya gaidai umma da aunty duk da yasan tahirin rayuwarta amamn bai ta'ba sanya mahaifiyarta acikin kwayar idanunshi ba amman ya gane aunty ce mahaifiyarta dan ko dan yanayin tsawonsu iri daya ne , mlm yahuza yayi murmushi yace "dan allah ku dan jirani minti uku kafin ku isa titi ma na dawo amman dan allah karku tafi a kafa Ummah ta d'an yi murmushi tace "kada ka damu dan allah , kada ka wahalar da kanka ba wani nisa da inda zamu ba mu gode Kwarai da gaske ."
" a dai min Afuwa ina zuwa yanzu Ummah tace tô shikenan mlm yahuza yayi murmushi ita dai maryama ta bisa da kallon mamaki dan bata san me yake nufi da kafin suje titi ya qaraso ba ummah ta dubeta cikin mamaki "wannan kuma wanene ? wallahi malamin mu né na makaranta islamiyya ummah tayi shiru domin ta danyi zargin son maryama din yake itama dai marayam taso ta fada mata kasancewar bata boye mata komai amman ganin fadar bashi da wani amfani tunda da zarar ta amincewa mutun ya fara zuwa kwana biyu sai ya gudu batare da laifin komai ba ."
suna tafiya suna hira har suka karaso bakin titin gwagulori wanda ya dawo sabon titi a yanzu sakamakon gyaran daaka masa suna tsaye kawai sai ga mota ta nufo inda suke maryama tasha jinin jikinta domin dai tasan bashi da mota amman babu mamaki ko ta abokinsa ce yayi burki agabansu ya fito daga cikin motar "umma ku shigo na kaiku har inda zaku "maryama shiru tayi mamaki ne ya damu zuciyarta tunda take bata ta'ba jin mlm yahuza ya dan burgeta ba sai yau sosai tayi farinciki da abinda yayiwa mahaifiyarta da ummanta ido kawai ta tsura masa ta cikin nikaf dinta tana kallonsa cikin farinciki shi kanshi ya fuskanci hakan ."
ya zagaya ya bude masu mota suka shiga kafin ya zagaya bangaren direba ya jefa mata wani kallo mai nuna tsantsar so kawai itama ta tsinci kanta da mayar masa da murmushi suka wuce ita kuma ta koma gida duk da abinda yayi mahaifiyata da ummah a yanzu bata ji ta fara jin mlm yahuza acikin zuciyarta ba amman ta kudirce zata danne zuciyarta ta fara sauraronsa ."
Hud'u daidai ta shirya zuwa islamiyya bata tsaya jiran sakina ba ta kama gabanta acikin aji sune na farkon zuwa ita da kawarta subai'a wacce suka qare karatu tare ahankali suke hira fitowar result dinsu kafin malamin da zai daukesu darasin qurani ya shigo sosai taso tayi mata hirar mlm yahuza amman ta kasa har aka cika a ajin mlm abbas ne ya shigo nan da nan suka fara karatu ita dai karatun yau dai tazo makaranta tayisa amman zuciyarta fal da walwala da irin farantawar da mlm yahuza yayi mata dan tana matukar qaunar mahaifiyarta da umma duk wanda yaga girmansu kuma ya mutunta matasu tô lallai zai samu wani babban matsayi acikin zuciyarta most especially mahaifiyarta tana tausayin halin data tsinci kanta ciki yana daya daga cikin abinda yasa ta d'auki komai nata da mahimmanci ."
"ta godewa allah ta kuma ta godewa mahaifiyarta da umman tare da abban sadam domin sun tsaya akan ganin sun ingata rayuwarta da karatun boko da Arabic tun alokacin da take secondary babu wanda yasa rai zata cigaba da karatunta zuwa jamia sai gashi kwatsam allah ya taimakesu ita da subai'a sun samu scholarship daf da zaa tashi ta shigowar mlm yahuza makaranta ,taso Kwarai ta gansa tayi masa Godiya ta fito tana duddubawa ko zata gansa amman bata ganshi ba zuciyarta taso ta gansa farincikin da yasa iyayenta take son tayi masa godiya dan tasan dole zai ji dadi acikin ranshi ."
Bayan an tashi daga makaranta bai biyota ba kamar yadda ya saba sai dai kafin ta isa gida kanwarsa nafisa tayi saurin isa inda take daman kuma tasanta sai dai ba aji daya suke ba tana gaba daita sosai suka gaisa tare daita suka cikin gidansu inda suka iske aunty salma a tsakar gida tana zaune tana waya ganinta tare da nafisa yasa aunty salma kashe wayar suka gaisheta suka wuceta suka shiga bangarensu maryama." suna shiga ta nuna mata wajen zama "nafisa ki zauna ga waje tayi murmushi ta zauna akan kujera ita kuma ta shiga dakin aunty ta duba inda aunty tasaba ajiyar kudi taci saa ta samu naira dari ta dauka ta fito tana cewa nafisa "ina zuwa ."
"nafisa ta mike ta biyota ina zaki bari muje tare maryama tayi dan Jim dan taso ta zauna taje ta siyo mata lamurje ta kawo mata amman bata da choice dole ta barta suka sake fitowa tare kai tsaye bangaren aunty hassana suka shiga tayi sallama ta isketa zaune tare da yaranta babu wanda ya amsa sallamarta bare ya kalli inda take bata damu ba dan ta saba "aunty hassana ina yini akwai lamurje?
"Akwai na nawa zaki tsiya "?amm.. na naira dari ne wani dogon tsaki taja "ai nasan bazaki canza zani ba daga na naira darin babu qari kullum ana waje daya baa cigaba ni bani kudin ki shiga ki dauka ki bace min da gani ."
Zuciyar nafisa ta cika da mamakin aunty hassana maryama ta mika mata kudin ta shiga ciki ta dauka suka fito ta mikawa nafisa gashi nafisa babu yawa "kai haba ai babu komai ai danasan ma kashe kudinki zakiyi da tun farko na hanaki " karki damu ai ba wani abu bane maryama ta fada tare suka shiga bangaren Ummah duk inda maryama tasa kafarta nan nafisa take ajiyewa ta share wa umma gida ta gyara mata koina tare da nafisa suka fito zasu wuce aunty salma ta kirata cike da isa ta isa inda take "kije kiyi min shara "
"Shara !"
Maryama ta furta a hankali?eh ko bazakiyi bane kika tsaya kina maimata min abinda na fada ?zanyi ta fada a taikaice tare suka shiga bangaren aunty salma ta fara shara "aunty maryama kawo na share miki da sauri dan akwai abinda ya kawoni "? itama tashi jinin jikinta dan tunda suke da nafisa bata taba zuwa inda take ba sai yau "no ki barni na share nima yanzu zan gama ta zauna akan kujera sakina da shukura suka shigo shukura na ganinta ta washe mata hakora "nafisa yau kece agidanmu ?ta tambayeta murmushi ya sake bayyana akan fuskarta "eh nazo wajen aunty maryama ne "aunty kuma ?ta fada a rude "eh mana aunty ce ai maryama tunda zuciyar babban yayanmu ta kamu da matsanancin sonta dan har wani kirki ya kirkirawa kanshi dan kawai ya aikoni wajenta ta fada batare da wani shakka ba ."
shukura batace komai ba ta zauna kusa da nafisa " inata son nazo gidanku amman ban samu damar zuwa ba saboda makaranta nafisa tayi murmushi "ai kuwa sai ki arawa kanki lokacin ki dinga zuwa gidanmu tunda yayana ya kamu da soyayyar maryama nasan naki matsayin sai yafi nawa zance bai yiwa shukura dadi ba dan haka kawai taji bata son wata halaka a tsakanin maryama da mlm yahuza haka kawai take jin rashin jin dadi aranta ."
Maryama tana gama shara ta fara kokarin wucewa yayinda nafisa take qoqarin mikewa shukura kuma tana janta da hira "kinga bari na isar da sakon da aka aikoni gobe ma hadu a islamiyya ta tashi tabi bayansa maryama suka jera har cikin falonsu atare suka zauna akan kujera nafisa na cewa "aunty nah "maryama tayi murmushi "kai nafisa da ki daina ce min aunty kullum fa da sunana kike kirana "ai yanzu komai ya canza baki ji yan karin magana ba sunce idan kidi Ya canza dole ma rawa ta canza nafisa ta fada tana dariya "ya karatu yanzu uzukin nawa ?maryama ta sauya magana dan bata son wata maganar soyayya mlm yahuza yayi mata mutunci Kwarai kuma ta yaba masa amman batu na soyayya bata jin zata iya
yayana ne yace na fad'a miki zai zo zuwa anjima maryama tayi murmushi amman shine tun dazu baki fad'a ba kika zaunar da kanki "ai ina sane na zauna ina qarewa zabin yayana kallo naga shin haukan da yake akanta ya dace abun mamakin sai naga tafi gaban tunanina ashe da kawai kallonki nake ta fad'a tana dariya "kai nafisa a she haka kike kema?maryama ta fad'a tana murmushi santi nake yi yayana ya iya zabe wallahi maryama nayi matukar farinciki da yaya ya sanar dani Ke yake so kuma har kin amince nan fa yanayin maryama ya sauya daga murmushi da take zuwa mamaki "ita a ina ta amince masa da zai qarar .?
"kun dace da yayana sosai ni daman ina tunani wa yahuza zai dauko mana acikin yammatan dake mutuwar sonshi saboda tsananin kyawunsa da kyawun halinsa uwa uba ilimi kema kuma munyi saa a komai kina dashi taso kwarai ta tsaida nafisa akan yayanta amman kuma sai ta kasa har zuwa lokacin data ciro wata karamar takarda ta bata tace gashi inji yaya in baki hanuna da naki ta fad'a tana shirin tashi daga kan kujerar da take zaune itama maryama ta tashi ganin tana alamar fita domin rakiyarta da hannunta ta dakatar da maryama "zauna abunki ba sai na wahalar dake ba ki zauna ki karanta sakon yayana cikin tsigar wasa maryama tace "ban son iskanci nafisa naga alamun raini ya fara shiga tsakaninmu ta bude baki "ni kuma asuwa na raina aunty amman dai Kiyi zamanki wallahi na gode ?"
Ta koma ta zauna ganin idan ta biye mata sai su kai dare bata gama iskancin ba ta fice ita kuma ta samu waje ta zauna ta bude takarda da nafisa ta bata ."
_Ina son ki takaita kanki da abinda kikasan zai war gaza farinciki dana gani akan fuskarki ina bukatar ganinki cikin farincikin dana ganinki dashi yau my maryama ina son jin muryarki cikin kunnuwana ina son jin hirarki zanzo yau byn sallah ishai_
Ta sake karantawa ta sauke naunayen ajiyar zuciya ita sam bata jin wata soyayyarsa wata killa da a shekaru biyu da suka gabata yazo lokacin tana shekara shatakwas kuma alokacin maza basu zama abun tsoro a wajenta ba da babu mamaki taji tana sonshi har ma ta iya aurensa amman zatayi kokari ko yaya ta fahimtar dashi illa soyayya gareta ."
ahankali ta jingina jikinta akan kujera tana jin bakinciki abubuwan da suke faruwa daita allah ya bata kyau ya bata ilimi tana da nagarta amman bata san dalilin da maza suke gutunta bayan sun kawo kansu wajenta ba , tana zaune tana tunanin taji sautin muryar aunty salma"maryama !maryama!!ke dan uwarki wannan wani irin rashin mutunci né kalmarta ta katse mata tunaninta ta dawo haiyacinta tana magana cikin bacin rai "au zama ma kikayi dan iskanci ni nawa mijin bai kwanta ya huta ba yana can neman abinda zaku ci shine ke zaki zauna saboda sakarci banza da tunanin banza daga yarinya tazo tana sakarci da munafurci sai ki nemi waje ki zauna kina tunanin iska dana banza da wofi allah dai yasa komai zai faru abanza né tunda bashi da wani amfani ana da kyau amman ya zama na banza ."
"tô ai dole ya zama na banza tunda mugun hali yayi yawa "
tarasa me ta tsarewa aunty salma acikin gidan nan zuwa yanzu bata tunanin iya kiyayya ce kawai ta fara tunani har da hassada take mata akan halittar da allah ya bata idan ba haka ba tana mata komai iya bakin gwargwado tayi mata shara tayi mata wanki idan ta kama wanke wanke duk tana yi dan dai a zauna lafiya da kuma kar ayi masu gorin ciyar dasu daake acikin gidan shiyasa sau tari bata son fita tsakar gidansu tafi son tayi zamanta a daki dan da zarar ta fita ko ita ko aunty hassana sai an samu wanda yasata aiki ko ya zageta ko mata gori ."
muryarta a sanyaye tace "yanzu ni aunty salma me nayi miki ?akwai abinda kike bukata da banyi miki ba ?ta rike baki au tambayata ma kike yi saboda yanzu kin kawo karfi an balaga an balallage an zama iyayen mata ? "
"allah yasa ba ita kadai ta balaga ta zama iyayen mata ba wadan da suka balaga suka zama iyayen mata suna da yawa " suka tsinkayi muryar habib abayansu yana harararta ta juya tana kallonsa
"zo ki fitar mana daga daki kafin na miki dukan mutuwa "uwarka da ubanka basu isa ba bare kai qaramin dan iska bazan fita ba idan kana iyawa zo ka fitar dani tattaccen d'an iska ."
Jin haka yasa cikin fusata ya nufota gadan gadan maryama ta mike da sauri ta shiga tsakani tana cewa "Uhm uhm after dad babu ruwanka daita "tô wallahi kice mata ta fita ta bar mana dakinmu "au har wani takama kake da dakin aro? "dakin aro ne a aka bawa uwarka byn kai a kusa da dakin kashi aka haifeka idan bakasani ba kasani ga dakin daaka yi cikinka ga masai Shege ma shegen girman tsiya anyi mugun gado a wajen uwa ".
Ya daga hannu zai kai mata mari maryama ta rike hannunsa a rikice cikin muryar kuka tace "haba habib ka barta mana ta fadi duk abinda take son fad'a ai bakinta ne tunda mu din ba shegu bane meye abinda zai dameka arziki kuma na allah né "kinga makira banason iskanci da munafurci ki barshi yayi min abinda ya ga dama amman gamawarsa ke da wuya zanci uwarsa da shi kansa dan wallahi duk iskanci da yayi akan uwarsa zan rama dan ita ce daidai ni ba shi qaramin dan tasha ba ,yana yawo suki suki duk yunwa ta gama cinyesa tayi maganar cikin daga murya ".
"Dan allah kiyi hakuri karki saka aunty cikin fadan nan habib yayi Kuskure amman kiyi hakuri bazai sake ba habib ka bata hakuri ".
"What!"
"Allah ya tsareni na bawa wannan matar hakuri kar allah yasa tayi hakuri ko ki fitar mana da wannan mahaukaciyar matar koni yanzu najata na fitar daita sha shar mata mara sallah mai dotti kawai hannu aunty salma ta daga zata wanke masa mari taji ya rike mata hannu sannan ya tsura mata idanunshi cikin sarkewar murya yace "kin gama ta'ba lafiyar kowa acikin gidan nan yanzu ke har yanzu a tunaninki kin kai matsayin da zaki cigaba da marena na kyaleki ? tô idan kina wannan tunanin ki daina yanzu dan zaki ya girma ya wuce wannan tozarcin dan bake ba hatta wanda ya ajiyeki acikin gidan nan kanin mahaifina kenan ba bai isa ba bare ke banza jaka dabba mai hali irin na dabbobi mara hankali ."
a fusace ta fixge hannunta tare da cewa "da uwarka kakeyi itace jaka dabba ai ,dan marasa mutunci irin tsiya irin jaraba tana fada yana maida mata ita kuwa maryama sai faman kuka take tana bawa aunty salma hakuri data gaji ma sai tayi shiru kawai tana kuka tana kallon fuskar habib dake tsine mata yana hadawa da yaranta da kaf dangin mahaifinsu da yasan basa qaunarsu a maganganunsa ta fahimci babu wanda ya tsana kamarsu aunty salma ta fice cikin fushi ta bar dakin cike da tsananin damuwa ."
Maryama ta zauna jagwaba akan kujera tana mai runtse idanunta habib ya lumshe idanunshi "shiyasa kullum suke takura miki wannan sanyin naki yayi yawa ki zama mutun ki nuna masu zamani ki nuna ma kema yar zamani ce sai ku dawo daidai dasu ba kullum ki zauna kina asarar hawayenki a banza ba .""haba after dad mutunci aunty zamu duba yanzu kasan halin matar nan sai taje tayi mana wata kullaliyar a wajen baba gali ".
"taje dan kutumar ubanta shima dan kutumar ubansa yazo daidai nake da kowa allah ya taimakesa yazo idan ban raba masa kanshi gida hudu ba kice Shege ne , anan zan jira zuwansa ya fad'a yana huci tmkr zaki ta mike ta kamo hannunsa ta zaunar dashi ta zauna kusa dashi tana shafa masa baya dan ta fahimci ya dauki zafi dayawa "kayi hakuri komai me wucewa ne wata rana sai labari abinda ya baka dariya wata shi zai saka kuka ka bar aunty salma da duk wanda zai fad'a son rashi acikin gidan nan akanmu."
ita fa aunty salma bata da laifi gani tayi yanuwan mahaifinmu suna yi mana yau da sun ga kima da darajanmu wallahi bata isa ba amman nasan wata rana idan ance tayi bazatayi ba kayi hakuri kaji danuwana rarrashinsa tayita har ya sauko tace "kaje kayi sallah nima zanje nayi kafin aunty su dawo ni na godewa allah ma da bata nan bare taga abun bakinciki kuma allah yasa kar aunty salma ta fad'a wa baba gali "ta fad'a masa mana Ke kike tsoronsa yazo ni yau a gida ma zanyi sallah ina jiran duk abinda zasu dashi bari ma naje na nemo atakobina wacce zan fellewa mutun kai dashi ."
"Dan girma Allah kayi hakuri meye hadinka da takobi kai ba dan daba ba "na zama yau "allah ya tsareni allah kiyaye bazaka zama haka ba Kiyi adduar karsu zo da hauka ya fad'a tare da shigewa dakin aunty kofar tabi da kallo kafin daga baya ta mike taje tayi alwala ta fita ta tada sallah tana cikin sallah tajiyo sallamar aunty tana kiran sunanta tana jin habib ya fita yana cewa "sallah take aunty sannu da zuwa "
"Yauwa habib a she kana gida ?nima ban jima da shigowa ba ina kika je ne ?kai habib zaka fara tambayoyinka kenan babu damar kaga na fita murmushi yay yana sake cewa "aunty ina kike je ?munje duba jikin hafsat ne ta haihu amman cs aka mata ".bai sake cewa komai ba saboda ya fahimci kowace hafsa take nufi diyar aunty fatima yayar mahaifinsu aunty ta mike ta shige dakinta domin yin sallah ."
Byn mintuna goma maryama ta fito daga dakinta zuwan dakin aunty duk jikinta a sanyaye lokacin aunty tana kan dadduma ta idar da sallah tana dai zaune "aunty sannu da zuwa "yauwa my princess ya zaman gida ?ta gyada mata kai alamun Lfy!"ya na ganki wani iri ko akwai abinda me damunki ne ?tayi shiru kawai tana jin faduwar gaba "kin dan daura mana wani abu kuwa ?ta bude bakinta ahankali tana shirin bawa aunty amsa suka jiyo hayaniya shiru tayi tare da kasa kunne muryar baba gali ne ta mike da sauri jikinta har rawa yake ta nufi kofar fita itama aunty ta biyo bayanta a tsakiyar falon suka gansa tsaye tare da aunty salma da aunty hassana sai hargagi suke tamkar wasu karnuka yayinda habib ya shiga kitchen ya dauko zabgegiyar takobinsa mai tsine ya koma bakin dakalin kofar fita ya zauna yana wasa takobinsa ,aunty hasana ta nufo inda yake shi kuwa habib kanshi na kasa yana cigaba da wasa takobinsa jira kawai yake suyi masa wata maganar banza ."
Aunty ta kalli maryama ta kalli habib tana bukatar qarin bayani cikin fusata aunty salma tace babu irin qare maku zagin da wannan tantirin yaron bai yi ba ta uwa ta uba har da ce mana dabbobi jakuna aunty hasana tace "da ubansa yake Shege dan Shegiya "da sauri ya mike yana zagayesu da takobi kiiiii kake jin tsinin bakin takobi asimintin falon basu ba hatta aunty da maryama sun tsorata "kai ko ka fara shaye shaye ne ko meye ?"da sauri ya juyo kan baba gali da yayi mgn fuskarsa a tsuke alamun bai son ya kawo masa raini "dan ubanka da kake zare masa idanu ka dauka zamu ji tsoronka ne ?"
"a'a nasan bakwa jin tsorona kamar yadda nima yanzu babu wannan tsoron duk wanda ya nemi zaman lafiya ayi wanda yace sabanin haka yake bukata bismillah ni bazan bata bakina ba sassara mutun kawai zanyi na aika sa lahira ."ya fad'a yana tsoka takobi daidai kafar baba gali ."
Da wani saurin gabadayansu suka ja baya suna kallonsa da mamaki kamar yadda aunty Ke kallonsa "tunda ku kun zama ahlin sheidan bakwa jin wani yare sai na dabbobi bismillah nima zan nuna muku akwai digon wannan dabbar ajikina ,tunaninku me zakuyi da kuka wani kwaso jiki gbdynku kuka zo ?
"To wallahi yau koni ko ku duk wanda ya zagi uwata da yaruwata sai na yanke masa harshe byn na raba kanshi gida hudu ."
zaro idanuwa sukayi suna sake ja baya dan ya daga takobin hannunsa daga aunty hassana har aunty salma suka koma bayan baba gali suka boye cikin karfin halin yace " bamu bane dabbobi da uwarka kake aiko jin haka Ke da wuya habib yayi kansa gadan gadan zai sara mata takobi aunty ta rike masa hannu tana zabga masa mari cikin muryar kuka tace "meke damunka habib ta fad'a tana kwace takobin tayi jifa dashi "zaka kasheni ne ?
"Ai da zai kashe dabba irinki da mun samu kwanciyar hankali "inji cewar aunty salma .
aunty kina jinsu ko bani takobina na sassara
shegu yan kutumar uba .."inna lillahi wa inna ilaihi rajiun allahumma ajirni fi musibatihi Waklifli khairan minha tana gama fadar haka ta durkushe kasa tana cewa "yanzu habib irin tarbiyar dana baka kenan ?maryama ta durkusa kusa daita tana mai rike hannunta tana ma habib wani irin kallo mai cike da tashin hankali ".
"Me yasa bazaka koyi danne fushinka ba ?me yasa zaka min haka habib ? me nayi maka dana cancanci haka habib ? "Kuji makira ina allonki allonki yana jahannama ,makira mata kin gama koya masa yadda zai ci mutunci mutune shine yanzu kizo kina kukan munafurci yau zamanku ya qare acikin gidan nan ku hada ina ku ina ku ku bar mana gidan nan mun gaji da ganinku daga Ke har wadan nan mataiyatan yayan naki bama bukatarku."inji cewar baba gali ."
nan da nan habib yayi kan baba gali duk da yaso ya rabu dashi ganin mahaifiyarsa tana kuka dan a duniya babu abinda ya tsana sama yaga ana cin mutunci mahaifiyarsa da yar uwarsa baya son ana zagar masa su bare a zagi qaddararta da binta da muyagun kalamai ko zubar hawayenta ,wuyan baba gali yake shirin damka ya
jiyo sautin muryar aunty cikin kuka tana cewa "wallahi habib idan ka ta'ba shi sai na tsine maka albarka "cak ya tsaya yana kallon baba gali ido cikin ido jikinsa na wani irin rawa tamkar mazari ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 16
Ahankali maryama ta mike daga cinyar umma hawaye ne sha'be sha'be akan kuncinta
ta tsurawa umma manyan idanunta wad'an da suka canza kala tana kallonta batare da tace uffan ba ,duk yadda taso ta daure ta tsaida hawayenta kasawa tayi hawaye take zubarwa sosai cikin tashin hankali mai tsanani ita kad'ai tasan halin bakinciki data tsinci kanta ciki adalilin jin labarin iyayenta ."labarinsu yayi matukar d'aga mata hankali "a she wahaalarsu da tsanar da'aka yi musu acikin family's ta samo asali ne daga soyayyar iyayensu ? haka nan taji tausayin kansu na sake shigarta . "
Koina ajikinta yayi sanyi yayinda falon ya d'auki shiru ,yadda maryama tayi shiru tana zubar da ruwan hawaye tana sake tariyo halin da iyayenta suka tsinci kansu adalilin soyayya haka ma umma bata sake cewa komai ba " ahankali wani irin so da qaunar mahaifiyarta da qaninta habib ya qara shigarta" allah sarki aunty "hakika kinga rayuwa, hakika ahlinki sun d'auki zafi dayawa akanki ."
"hukuncinsu yayi tsanani dayawa domin allah Ke had'a soyayya alokacin daya so ba dabarar mutun ba ,ba son ran mutun bane ,domin kuwa idan da dabarar mutun ne ko son ran mutu da mutanen duniya dayawa basu tsinci kansu cikn
ta ba ."
a qalla sun d'auki minti goma a haka suna kallon juna sannan maryama ta lumshe idanunta da sukai jajur alamun tarin quna da bakinciki ahankali umma ta numfasa "maryama ! ta kira sunanta a natse , ahankali ta motsa lip's dinta alamun ta amsa dan zafin da zuciyarta keyi ya danne fitowar muryarta "ki godewa allah ba kuka ya kamata kiyi ba maryama."
"ki godewa allah daya qaddara aure a tsakanin iyayenki da har aka sameku ta hanyar sunanh " "Alhmd!ta furta a can kasan makoshinta tana dafe kanta dake sara da mugun karfi "ya kai ki godewa allah ki sake gode masa ko bai kai ba ? kanta ta gyada mata alamun "eh!.
"To ki manta da duk abinda na fad'a miki muje Kiyi sallah kici abinci ki kwanta ki huta " da karfi maryama ta fizgo magana "bazan iya manta komai ba ,a halin yanzu ma ganin komai nake kamar a yanzu ya faru har nayi danasani umma nayi danasani jin wannan mummunar labarin rayuwa irin rayuwar da iyayena sukayi rayuwar kaskanci ne a wajena."
"why umma? "me yasa komai yake faruwa damu haka ?ahankali ummah ta shafa kanta
zuwa gadon bayanta tare da cewa "kiyi hakuri maryama kowa da kalar irin tasa qaddara a yanzu jajurcewa zaki qara akan wanda kikayi har kika samu cikar burinki na zamowa cikakkiyar mai ilimin lissafi ,kiyi qoqari ki tsaya bisa kafafunki domin tallafawa rayuwar mahaifiyarki daya qaninka domin ina hango tarin nasara da kwanciyar hankali atattare dake , bilkisu na bukatar farinciki ,maryama nasan da sannu zaki zamewa bilkisu sanyin idaniya amman fa sai kin manta komai maryama kin rungumi qaddarar rayuwarku ."
"Na yarda da qaddara ummah domin yana daga cikin cikar imani mutun , na yarda da qaddara amman umma aunty tayi kuskure arayuwarta bance laifi bane dan taso mahaifina amatsayin da yake amamn iyaye fa umma ? "manzon sallahu alaihi wa salam yace "ridal lahi fi ridal walidaini , wa sakad'ul lahi fi sakad'il walidai ."yarda allah yana tare da yarda iyaye, haka zalika fushin allah yana tare da fushin iyaye allah ya fifita iyaye akan komai most especially uwa ummah ,babu uwar da taza ji dadin irin rayuwar da aunty tayi ."
umma tayi shiru kawai tana sauraronta "misali na kwatantawa aunty irin abinda tayiwa iyayenta ya zataji ? na kawo mata in responsible man nace naji nagani sai shi duk tarbiyar da tayi tsawon shekaru tana bani nasa kafa na rugujeta ya zataji ?" magana ta gaskiya iyeyenta da yan' uwanta sun d'auki zafi dayawa amman aunty ta fisu laifi kuma lallai ya kamata taje ga iyayenta ta roki gafararsu sannan ta koma cikin danginta zuciyarta ta samu salama ."
"wallahi yadda nake jin habib araina bazan iya barinsa saboda wani ba bare iyayena da suka kawoni duniya ba ,abun da ciwo ummah ba kamar yadda kuka d'auka bane kema uwa ce ummah , aunty ta kona zuciyar mahaifiyarta dayawa, yanzu na gano duk aunty ce silar shigarmu cikin matsala , iyayenta na can suna fushi daita har yau ta yaya kike tunanin zataji dadi ?"ta yaya kike tunani zan iya bata farinciki byn ga inda zata samu fiyye da nawa ."?
maryama ta kalli umma cikin sarewa ta cigaba da magana " umma abun na da matukar ciwo irin ciwon dake cin zuciya da bargo ,ciwo ne da bashi da magani da mafuta har sai ka had'u da mahad'inka , shiyasa a kullum idan na kalli aunty sai naji tamkar tana boye mana wani abu mai mahimanci ga rayuwarta , ashe gsky né hakika bakinta bazai iya furta mana komai akan rayuwarta ba matsawar ita din uwa ta gari
ce , dan allah umma Kiyi min rai ki raba zuciyarta da wannnan rayuwar idan kuma baki yi ba ni zanyi ,zan rabata da nauyin dake daskare a qirjinta ."
Tana gama fadar haka ta mike a hankali tana share hawayen idanunta da suka gagara tsayawa tana jin wani zafi a qirjinta , bazata cigaba da d'aukar wannna nauyin ba , koda aunty bata amince ta koma ga yan'uwanta ba ,lallai ita zata nemosu a duk inda suke acikin garin nan ."muryarta a sanyaye tace "umma ni zan wuce sai da safe " kai kawai ummah ta gyada mata sannan maryama ta fara tafiya umma tayi shiru tabi bayanta da kallo tana kallon yadda take d'aga zara zaran yatsun kafafunta da kyar tamkar wacce bata da laka ."
" A inda ta bar mahaifiyarta anan ta sameta tare da habib suna hira da alamun shi baya cikin damuwa kamar ita." bata tsaya ba byn tayi sallama tace "aunty sai da safe tana gama fadar haka ta wuce ta nufi d'akin baccinta bayanta suka bita da kallo , yanayinta kad'ai ya fahimtar da aunty akwai tarin damuwa atattare daita shiru kawai tayi tana tunani "har yaushe maryama zata yi farinciki arayuwarta ?".
A natse aunty ta mike tabi bayan maryama tana jin tsinkewar zuciya haka shima habib akan kujerar da take zama idan zatai zane suka isketa ta dafe kanta tana sheshekar kuka atare suka qaraso suka zauna abakin gado suna fuskantarta shigowarsu yasa ta tsaida kukanta wanda taso tayisa sosai har taji natsuwar zuciyar."
dogon numfashi aunty taja tare da cewa "na shiga uku ni bilkisu " ta furta cikin tsananin tashin hankali dan bata qaunar abinda zai d'agawa yaranta hankali shi kuwa habib hannun maryama ya kamo cikin nashi ya damke da karfi cikin tsananin tashin hankali " heartbeat meke damunki ?." muryarta a raunane tace "babu komai after dad "ya babu komai zaki shigo cikin damuwa , yanzu mun shigo mun ganiki kina kuka amman kice babu komai ki fad'a min idan akwai abinda ke damunki ."
shiru tayi tana cigaba da shesheka "ki sani bamu saba boyewa juna komai ba idan kika min haka baki min adalci ba ,ko km damuwar dazu ce ? still dai shiru tayi ,sosai suka d'aga hankalinsu ita kuma taki cewa komai sai faman ajiyar zuciya ta saukewa ." damke hannunta ya sake yi sosai yana rokonta "dan allah heartbeat karki daga mana hankali ki fad'a min kukan me kike yi ?kallonsa kawai tayi tana lumshe idanuwanta ganin yadda hankalinsa yay matukar tashi da yadda ya d'aga hankalinsa ya matukar bata tausayi daman kuma haka ne idan daya yana cikin damuwa dole ne daya shima ya tsinci kanshi cikin damuwa."
"Yanzu princess bazaki koyi dauriya akan kowacce irin damuwa bace domin ki tsira da rayuwarki da rayuwarmu gabadaya ,Ke kenan kullum cikin zubar da hawaye akan damuwa me yasa zaki dinga asarar hawayenki tare da qoqarin kashe kanki abanza ."?
"Gara dai ki fada mata gsky aunty domin ita rayuwar nan da take ganinta wani lokacin idan abubuwa suka wa mutun tsanani dole mutu ya rage wasu abubuwa domin tsira da rayuwarsa da lafiyarsa."
hawayen da take qoqarin maidawa ne suka samu nasarar gangarowa bisa kuncinta cikin sauri tashiga gogewa wasu na sake gangarowa duk yadda suka dinga kwantar da kai da murya dan suji damuwarta amman taki fad'a masu komai domin da zarar ta bude baki hawaye da sheshekan kuka Ke hanata magana dole tasa suka daga mata kafa suka fice d'aya bayan d'aya daga dakin da zumar zasu lalla'bata gobe ta fad'a masu dalilin kukan ."
tafi mintuna goma byn fitar aunty da habib zaune sannan ta yunkura ta tashi tana sauke naunayen ajiyar zuciya ta shiga bayi ta d'auro alwala ta fito ta gabatar da sallahr magariba da isha'i tare da shafa'i da wutiri byn ta idar ta koma kan katifa ta zauna tare da jingina bayanta da pillow ta rungume hannuwanta duka a qirjinta ."
ahankali ta runtse idanunta tana tariyo komai daya faru dasu tun suna yara "Kenan adalili rasa mahaifi da kaka yasa rikonsu ya dawo hannun abban sadam ."tun tana qarama yar shekara hud'u a duniya ta taso cikin so daga bangaren abban sadam da umma da mahaifiyarta amman daga bangaren aunty hassana da sauran 'yan'uwan mahaifinta kuwa saboda haushin da kiyayyar mahaifiyata yasa suka dinga nuna masu tsana da tsamgwama , sun ci wuyarsu sosai most especially Ita ganin kiyayyar dangin mahaifinsu da irin tsanar da baba gali yayi masu ya bawa aunty salma damar cin kashi akansu da mahaifiyarta ."
tun daga lokacin kuruciya har zuwa girmanta abinda yake rage mata zafin gidan shine soyayyar umma bancin ita kowa a gidan baya sonsu amman kuma wani lokaci shi kanshi baba gali ya kan tausaya masu in dai ba fad'a sukai da sakina ba ko yarshi qarama ba , idan tayi mata laifi ta d'an daketa shine zai fito da 'bacin ransa har ya fito da zallar kiyayyarsa ,kuma tun da ta lura son ya'ya ne dashi domin ba ita ba ko uwar data tsugunna ta haifesu baya raga mata akan ya'yansa ."
"yayan baba gali uku ne aliyu sakina wacce sa'artace sai mai bi mata salamatu wacce taci sunan hajiya kakarsu ana kiranta da shukura bata fi shekara sha bakwai ba a yanzu ,itama babu yabo babu fallasa suna d'an shiri daita sai dai idan taga uwarta na fushi da zagina bata hanata sai ma dai ta zugata domin itama tana nuna kishinta akainta idan taga umma tana tarairayata ko wani ."
Baba gali dinki yake ada rasuwar abban sadam yasa gidan buredi da rikonsu ya koma hannunsa alhamdulillah babu laifi ita din mai qokari ce ta kowani fanni boko da arabic ga baiwar zane da Allah ya bata ."
Alokacin baya kullum ta allah sai aunty tayi masu special lesson ita da habib kusan kokarinta ta samu ne a wajen mahaifiyarta ,duk unguwar da makarantarsu ana maganarsu akan ilimi bokon da suke dashi haka duk gidan ba masu jin turanci kamar ita da habib ko wani abu za'a tambaya ita ko habib ake tambaya mahaifiyarsu ta tsaya masu akan karatunsu shiyasa ma education dinsu yayi very fast kuma à sanadiyar qoqarinta ita da kawarta subai'a yasa gwanati ta dauki nauyin karatunsu zuwa lagos state university ".
bangaren sakina da sauran yaran gidan matsalar iyayensu ne dan basa maida hankali akan karatun yaransu gashi sam basu da isashen ilimin boko ko Arabic barin ma aunty salma karta ji labari ba arabi ba boko sai uban girman kai ,sau tari idan shukura tazo koyon wani abu a wajenta bata só sai ta nuna ai itama tasani dan me zatazo wajenta akarshe idan tayi mata zero take samu a makaranta shiyasa da yarinyar ta gane ta daina bata idan tace ta kawo kai tsaye take ce mata bataso zero zataci ."
hatta alwala ba daidai aunty salma take yi ba kuma sallah ma bata dameta ba ,tun suna yara baba gali Ke mata fad'a akan tarukun sallah din da take yi amman taki ta daina shi kansa daya gaji sai ya rabu daita ya dinga Kwa'bar yaransa da yin sallah sanin in har dan uwarsu ne sai dai kar su yi babu abinda ya dameta dan idan ma koyi zasu yi daita sai dai su koyi taruku sallah."
Su kuwa aunty bata yarda tana gama dauro alwala zata tura habib zuwa masalaci ita km ta umarceta taje tayi alwala sannan a kullum dare auty ta kan fito tsakar gidan tare dasu har sakina kasancewar tana qaunarta ta koya masu darasin lissafi , tana daukar lokaci akansu har sai taga sun gane sannan ta bukaci wanda yake da damuwa a bangaren karatunshi ko baka da matsala zatai 'yan tambayoyi ana bata amsa idan bata gamsu da amsar ba ta qara yi masu bayani , bangaren karatun alqurni kafin suyi bacci sai aunty tasa sun karanta izawaka da tabaraka kafin su kwanta da safe kuma sai sunyi murajaa alqurni sannan su shirya su wuce school ko islamiyya ."
A ranar batayi isashen bacci ba ga tsananin tunani ga kwadayin son ganin yan'uwan mahaifiyarta gargadin kanta ta shigayi akan fad'awa soyayya da ma ko waye idan kuma soyayyar ta zama dole sai dai tayi a gidan aurenta ga duk wanda ta aura har asuba tayi maryama batai wani yi baccin kirki ba shiyasa kiran sallahr farko acikin kunnenta akayi ta gyara kwanciyar ta koma ta kwanta bacci kad'an tayi ta lalubo wayarta ta duba taga biyar da rabi saura lokacin sallah yayi dan har an tada sallah a matsalacin unguwarsu ."
a hankali ta mike zuciyarta cike da damuwa bakinta dauke da adduar tashi daga bacci ta kai tafukan hannunta tana shafa fuskarta sannan a natse ta zuro kafafunta ta sauko ta shiga bayi ta dauro alwala ta fito cike da sanyin jiki ta gabatar da sallah asuba byn ta idar ta d'auko alqurni ta soma karatu cikin suratul baqara anatse ta kai idanunta ga window d'akin taga gari ya fara sha tayi azkar din safe tana nan zaune tana lazimi har shida saura sannan ta koma ta kwanta akan sallaya nan da nan bacci mai nauyi ya dauketa ba ita ta tashi ba sai goma saura ."
Ta mike da kyar bakinta dauke da salati sakamakon qirjinta dake wani irin bugawa ta
gyara gadonta ta fita ta dauko tsintsiyar shara
ta share d'akin ta fito har falo ta shiga d'akin mahaifiyarta bata ganta ba tasan may be ko tana byn gida wajen yin wanki ,dan wannan kaida ne kullum safiya sai tayi wanki kayanta wani lokacin da nasu ta share d'akin tasss ta fito da sharan zuwa falo ta shiga kitchen ta hada kayan wanke wanke ta wanke atake ta goge koina ta sharo sannan ta hada da share falo tayi mopping ta koma daki ta cire kayan jikinta ta shiga wanka bata wani jima ba tayi alwala ta fito kai tsaye ta shimfida daddumar sallah ta sallacci salatul duhu byn ta idar ta shirya kanta ta kwanta lamo cikin zullumi ta kamkame jikinta waje daya wani iri take ji a duk gbdy ilahirin jikinta soyayya irin wacce iyayenta sukayi bazata ta'ba yarda ta jefa kanta cikinta ba".
Ta godewa allah daya bata kyakkyawar zuciyar da bata da lokacin maza ,bata jin soyayyar ko wani nmj ta ratsa koina ajikinta ,duk wanda yazo da sunan sonta ya dawo ya gudu bata taba jin haushi ko kewarsa bare ta damu kanta akansa ita fa gsky tafi ganin laifin mahaifiyarta akan abinda iyayenta sukai mata kuma taji dadin mutuwar mahaifinta akan rayuwarsa domin daa kalleta ace ita din diyar dan shaye shaye da neman mata ne wallahi gara mutuwarsa akan rayuwarsa, data dangwama tana masa adduar shiruya allah gara ta qare rayuwarta wajen yi masa addua samun rahmar Allah ."
Da misalin karfe goma sha d'aya da rabi daidai na safe aunty duk ta damu tun jiya rabon tasa maryama a cikin kwayar idanunta ga dai alamun ta tashi dan har tayi ayyukanta na yau da kullum data saba dan ga parlour nan a gyare tsab sai zuba kamshi yake koina tsab daga ita har habib sun kasa samun kwanciyar hankali bare su karya ,sai ma wata faduwar gaban data ziyarci zuciyarsu ."
mikewa aunty tai ta nufi dakinta shima habib ya biyota kusan atare suka shiga dakin har suka shigo maryama batasani ba tana can duniyar tunani tare da rafka uban tagumi da sauke numfashi a hankali ahankali, da sauri suka qarasa gareta dan yadda suka ganta ya matsifar daga masu hankali fiyye da jiya dan har wani doguwar rama tayi atare suka kira sunanta suna tmbyrta "wai maryama menene damuwarki ne ?"
"heartbeat banason ganinki cikin damuwa saboda duk duniya babu wanda nake so byn Allah da aunty sai ke karki bari tunani yasa mu rasaki ya fad'a idanuwanshi na kanta "bansan me yasa kike son kashe kanki akan damuwa ba wanda ni a tunani kowace irin damuwa ce zaki iya hadiyeta". aunty ta qarasa maganar tana furzar da iska me zafi daga bakinta a hankali ta mike ta koma kan kujerar aikinta ta dauko farar takardar daya ta ajiye akan table domin samun damar cigaba da aikinta ta zaro pencil har kala uku ta fara zane sai dai zuciyarta rawa take nan da nan idanunta suka cika da ruwan hawaye tarasa dalili daga jiya zuwa yau ta sake rasa sukuni da farincikinta, bata jin shaawar komai babu abinda take so da bukata kamar ta kadaice kanta ."
Aunty ta dakatar daita daga abinda take tana dubanta zuciyarta na mata wani irin suya a game da halin da take ganin maryama din ciki wanda bata san silar faruwar haka ba maryama bata dago ta kalleta ba ta cigaba da abinda take gbdy kamaninta ya canza ,ahankali habib ya shiga rarrashinta da nasiha mai kashe jiki gbdy fuskarsa ta canza Kmr zai yi kuka , Ita kam aunty kasa furta komai tayi ta zuba masu idanunta tana jin tarin damuwa ganin hk yasa maryama ta soma magana kamar bata son yi "abinda muka bukaci Auny ta fada mana taki jiya umma ta fada min babu abinda ta boye min sai wanda batasani ba." ta karasa mgnr tana dago kanta Tare da sauke naunayen ajiyar zuciya sannan ta sakin wani sabon kuka lokaci daya shima kwayar idanunshi suka kada suka canza nan take yaji tsanar dangin aunty ya shigesa kasamcewarsa nmj kuma duk nmj dole yayi kishin mahaifinsa nan take ya yanke cewar a zuciyarsa bazai furtawa aunty komai akan yanuwanta ba koda kuwa ita kanta uwar gayya ta amince zata koma garesu amman shi babu shi babu su har abada ."
"Tô princes kinji kadan daga cikin tarihin rayuwata kuma ina fatan kin gamsu ?shiru kawai maryama tayi tana kallonta tare gyada mata kai "good my princess kinga rana ya fara ki tashi kici abinci ki kwanta ki dan huta kafin lokacin sallah yayi ta fada tare da mikewa tsaye "yanzu aunty haka rayuwa zata cigaba da tafiya ?tayi maganr cikin raunin murya aunty taja ta tsaya tana dubanta tare da nazarin maganarta "ina nufin haka zamu cigaba da rayuwa batare da kin san matsayinki a wajen iyayenki ba ?
"karki damu dan ni har yanzu bana bukatarsu arayuwata ina ganin kuma ku ciresu acikin zuciyarku "ni daman a yanzu dana gama jin komai na ciresu araina dan basu da wani amfani a wajenmu gara mu qarasa rayuwarmu haka batare dasu ba "haba habib me yasa zaka fadi haka shikenan ita aunty haka zata qare rayuwarta ? kai yanzu zaka iya rayuwa babu ita da kake goya mata baya ?"tayi maganr cikin tsananin fushi "kai daya kamata mu taru mu shawo kanta shine zaka ce haka .?"
guntun numfashi ya sauke yana cewa "lallai heartbeat kina da aiki mutanen da suka wulaqanta mana mahaifi dan kawai talaka ne shine zamu tashi muje wajensu alhalin bamu da komai muna nan dai a yadda suka san mahaifinmu babu wani cigaba da muka samu gsky ni bazanje inda suke ba kuma har abada "gsky habib ya kamata ka tsaya kayi tunani da kyau abinda ubanka yayi bai kyauta ma iyayen aunty ba, ni nan naji dadin dana girma baya raye wallahi da cigaba da ganin rayuwarsa gara mutuwarsa a wajena ."kallonta habib yayi yadda ta zuba masa idanunta cikin bacin rai tana fidda numfashi da kyar "ni babu wani tunani da zanyi akan wannan matsalar ke ma kuma ki bar magana a iya nan dan banga abinda zai sa naje gurin makiyanmu ba kuma ni banga abinda mahaifinmu yayi ba daya cancanci tozarci irin wanda akayi masa ba tun kafin ya qarasa maganar qirjin aunty yayi wani irin bugawa da karfi duk da bata bukatar iyayenta arayuwarta amman bataji dadin kalmar habib din ba ."
"wallahi wallahi habib idan ka sake furta wannna kalmar zan balain baka mamaki "kinga ni tafiyata ya nufi kofar fita yana cewa "allah dai ya baki hakuri amman babu abinda zai kai mu gurin makiyanmu ya qarasa fita ,jikin aunty yayi sanyi ta bude baki zata yi magana sai kuma ta kasa cewa komai "aunty !.
maryama ta kira suannata ,a hankali aunty ta motsa lip's dinta "naam !"karki dauki maganar habib da mahimmanci domin shi yaro ne ke uwa ce da muke kallo muke koyi daita kuma kece malamammu dake nuna mana daidai da ba daidai ba ,ki natsu aunty da kyau ke mai ilimi ce allah subuhanahu wata ala yace acikin suratul ahkhaf aya ta arabin da biyar وَوَصَّيْنَا الْإِنْسَانَ بِوَالِدَيْهِ إِحْسَانًا ۖ حَمَلَتْهُ أُمُّهُ كُرْهًا وَوَضَعَتْهُ كُرْهًا ۖ وَحَمْلُهُ وَفِصَالُهُ ثَلَاثُونَ شَهْرًا ۚ حَتَّىٰ إِذَا بَلَغَ أَشُدَّهُ وَبَلَغَ أَرْبَعِينَ سَنَةً قَالَ رَبِّ أَوْزِعْنِي أَنْ أَشْكُرَ نِعْمَتَكَ الَّتِي أَنْعَمْتَ عَلَيَّ وَعَلَىٰ وَالِدَيَّ وَأَنْ أَعْمَلَ صَالِحًا تَرْضَاهُ وَأَصْلِحْ لِي فِي ذُرِّيَّتِي ۖ إِنِّي تُبْتُ إِلَيْكَ وَإِنِّي مِنَ الْمُسْلِمِينَ
Allah yana yiwa mutane wasiha ne akan su kyautatawa iyayensu , mahaifiya ta d'auki cikin mutun ,tana mai shan wahala ,kuma ta sauke shi cikin wahala ,da daukar cikin da yaye d'a na tsawon wata talatin har lokacin da karfin mutun zai kai girma yasan ciwon kansa har zuwa karshen ayar ,cikin girmamawa ta cigaba da magana "kiyi min wannnan alfarmar aunty , wallahi dan kinje garesu a halin yanzu ba kasawa bane bugu da qari iyayenki suna da hakki akanki babu ruwan allah da abinda sukai miki ".
"maryama mu bar maganar nan ta wuce dan allah sannan ki fito ki karya kar abincinki yayi sanyi tana gama fad'ar hk ta juya ta fice daga dakin shiru tayi kawai tare da bin kofar dakin da kallo idanunta na kawo ruwan hawayen tana tausayin mahaifiyarta bata san meke damun mahaifiyarta ba akan iyayenta sam sam bata son ana mata maganarsu tamkar wanda akayiwa farra'u amman tasan abinda zatai zata janye jikinta tare da tsananta addua akan lamarin allah ya daidaita da iyayenta da yanuwanta ,yinin ranar a daki ta yini taki fitowa taci komai ."
*****
Tun karfe takwas na safe maryam da mami da masu aikinta ke faman kai kawo a kitchen suna qoqarin had'awa mr ATA breakfast sosai mami take lura da yadda maryam take gudanar da aikinta , babu laifi tafi da kokari sosai sannan ta rage son jikin da take dashi wajen girki suna girki suna hira mami ta cigaba da nuna mata wasu abubuwa suna cikin aiki sai ga sallamar hindu ta shigo maryam ta amsa tare da lekawa tace "hindu ce ki shigo muna kitchen muna aiki ne."
wani irin kallon tayi mata wanda yasa maryam taji wani iri ajikinta ,hindu ta tsaya bata shiga kitchen din ba kamar yadda maryam tace ta samu waje ta kame akan daya daga cikin kujerun falon ,mami ta dawo inda maryam take tsaye tana kallonta "sannuki maryam gsky kinyi kokari sosai yau kin aikatu da kyau haka ake so, maryam tayi murmushi kawai tana jin dadin yabon da mami tayi mata "na gode sosai ai nan gaba zan kware na zama professional ta bangaren girki bazan ta'ba baki kunya ba ."
mami tayi murmushi tace "da alama zaki wanke zuciyar mamnki ta gyada mata kai alamun "eh !"
"To ni zan hau sama na dubo adamcy Idan kin kammala komai ki shirya dinnig kije kiyi sauri Kiyi wanka ki shirya ki dawo Kiyi saving din sarkin zuciyar Kiyi komai a natse kin dai san halinsa dan oya oya ne yafi son komai cikin sauri sauri bare yau din nan sai ahankali ."mami dan allah ki zuba masa da kanki mana"idan kunyi aure nice zan dinga zuwa gidanku ina zuba masa ?"dakewa zakiyi maryam ai ya kamata ace kin saba da halinsa "wallahi mani babu mai iya sabawa da halinsa sai ke nifa mugun tsoro yake bani idan na gansa hatta kayan cikina karkarwa suke mami tayi murmushi tana cewa ni na wuce "To mami sai kin fito ta fad'a cikin murmushi mami ta fito zuwa parlour'n."
hindu na ganinta ta saki fuskarta sosai tare da gaishe da mami cike da sakin fuska mami ta masa tana tmbyrta mutanen gidansu ta amsa da lafiya lau kowa yake "mami ina ya adam ne ko har yanzu bai tashi ba ?"eh!hindatu ina tunanin bai tashi ba amman yanzu haka ma samansa zani na taso shi dan yace idan ya wuce tara bai tashi ba na tashesa rausayar da kwayar idanunta tayi tana jin wani zazzafan sonshi ."
Mami ta nufi saman dakinsa tana mamakin hindu su dai yaran zamani basu da ta ido akan nmj so na mugun rufe masu ido shiyasa har kullum take ganin girma da kimar maryam, a dai barta da son social media dinta amman rawan kai akan maza sam bata dashi dan tasan bancin itace ta hadata da adam to har abada bazata iya bude baki tace tana son shi ba ."
Maryam ta kammala komai a natse ta fito a yatsine hindu ke binta da kallo tana shirya dining ,ita kuma tana tunanin yadda zasu buga kishi daita idan tai nasara shigar gidan ya adam dinta dan dole ta fita ta bar mata gidan ta zauan ita kadai ,dan idan bata kaita lahira ba lallai zata raunatata dan irin son da takewa ya adam ba na wasa ba so ne wanda bazata iya sharing dinsa da kowa ba ."
Marayam ta sha jinin jikinta da irin kallon wulakancin da hindu Ke mata dan duk lokacin data kallo bangarenta sai taga kamar hararata take wanda ta rasa dalilin faruwar hakan ,sai da maryam ta tabbatar da komai yayi neat babu abinda mr ATA zai gani yayi complain sannan ta wuce ta nufi dakinsu cikin sauri still tana mamakin hindu ."
tana shiga dakin bathroom ta shiga ta fara wanka sai dai matsalarta bata iya wanka cikin sauri ba idan ta shiga wanka a qalla tana daukar awa daya a bayi amman kasamcewar zatayi saving din mr ATA yasa ta tsakaita tayi wanka ta fito ta dauki man shafa warta wanda shima shafa man kanshi aiki ne domin tana daukar a qalla mintuna talati bare aje ga make up ta shirya cikin doguwar rigar shadda bazin har kasa bata gama kammala shiri ba taji sautin muryar mami na kiranta da d'an sauri ta fito zuciyarta na rawa kuma har lokacin hindu na zaune a parlour'n tayi shiru tana yi masa kallon tsab komai nashi yayi mata irin wanda take so nmj ne sai kallonsa take yayinda mami ke qoqarin jawa mr ATA kujera baya"
Wani abu mai mugun daci ya hadiye tare da zama yana mai runtse idanunshi ganin mami na son bawa maryam umarnin saving din mr ATA hindu tayi sauri ta mike tsaye tana cewa "mami bari nayi saving din yayana ta fad'a tana mai sunkuyar da kanta alamun kunya "amm...! "Sweetheart bari tayi kawai ya fad'a atakaice mami ta kallesa na second biyu dan sam bataji dadin hukuncinsa ba dan tasan da wata manufa hindu ta fadi hk shi kuma gudun karyaci daga hannun maryam ya fadi haka dan tasan shi tasan halinsa baayi masa gwaninta ranta ya baci sai dai danne damuwarta ."
Madadin mami ta zauna kusa dashi kamar yadda ta saba sai ta koma kan kujera ta hankince ta nunawa maryam kusa daita"maryam zauna anan kinji yar albarka ta maida hankalinta kan tv mr ATA yaji babu dadin yadda mami taja jikinta amman sanin dan maryam tayi haka yasa ya share ya dauki wayarsa yana duba sakonin dake shigowa yayinda hindu ke zuba masa abinci acikin wani haddaden plet ta matso daf dashi Sannan ta ajiye plet din a gabansa."
cike da girmamawa ta kira sunansa"ya adamccccyy...!yadda ta kira sunan cikin slow voice yasa daga maryam har mami suka waigo suna dubanta murmushi ta sakar masu wanda ke nuna tana cikin farinciki sannan ta dauke kanta ta maida kanshi wanda shi gogan har lokacin bai daina abinda yake ba bare ya dago ya kalleta sai faman ciza lips din yake yana kallon screen din waya ."
kira ne ya shigo wayarsa ya dauka a natse "ok but I think kasan nan da 1week zan wuce france ya aikin gunka ina fatan akwai nasara ya hade rai sosai haba hisham you should know me by now ka ta'ba ganin inda akayi haka ?kawai dan na tattara hankalina zuwa wani waje kawai su kamawa yiwa mutane barna ,ka kuwa san adadin kudaden da mukayi asara kuwa ?kowa acikinsu kanshi kawai yasani ba cigaba AGC bane agabansu well sai na shigo dai hindu ta marairaice murya sosai tace "ya adamcy ga abincin ka dan ajiye waya kaci abinci ".
Banza yayi mata ya cigaba da wayarsa "a lokacin zuwa office muke gashi naji ya sultan yace yau kuna da zama na mussaman "bai kalli inda take ba bare ma ta samu matsayin ya bata amsa hakan kuwa yayi wa maryam dadi sosai ,sauran kadan ta fashe da dariya amman ta danne ,ta kalli mami wacce itama ita take kallo suka sakarwa juna murmushin jin dadi sai daya gama wayarsa ya ajiye sannan ya fara cin abinci babu irin kwarkwasan da batayi masa ba da jansa da magana amman bai ce uhmm ba bare uhmm uhm ba illa ma mikewa da yayi tsaye yana gyara yar saman suit dinsa ya dan qarasa kusa da mami muryarsa a dake yace "ni zan wuce kuma kai tsaye daga nan AGC zani "to Allah ya tsaye sai ka dawo yace" Ameen!
"har ya juya ta kirasa "adamcy ! ya dan tsaya yana saurareta "kabi komai a hankali dan Allah karka dauki zafi dayawa ahankali ake bin komai ka tsaya ku fahimci juna da yanunwaka".
Kai kawai ya gyada mata ba dan zai yi abinda tace din ba dan yau kusan sai ya tashi rabin mutanen kamfanin kuma daga aiki wanda dayawa yanuwa ne a natse ya juya ya fice yana fita hindu tabi bayansa har tayi taku biyu mami tace "amm...hindu yau yayanku baya cikin moon mai kyau ba kin kuma san halinsa bare idan yana jin miskilancinsa idan kika nemi ki tsaida shi komai zai iya faruwa ko kina son wani abu ya faru ne ?"
Hindu ta girgiza mata kai alamun a'a daman ba tsaida shi zanyi ba gida zan wuce "to shikenan sai anjima sai data fice mami ta dawo da kallonta kan maryam "mami me kika karanta akan hindu ni yau gani nayi tana wasu abubuwa kamar son ya adam take mami ta tabe baki "wai son shi take amman shi har yanzu bai sani ba dan dayasani bazai bari tayi saving dinsa ba" maryam ta dan ware kananun idanunta sanna tasa dariya tana cikin dariya sai ga nana hauwa'u "sister yi sauri kizo kije wani sabon rigima da sauri ta qaraso tana cewa "bani na sha matar yayana "wai hindu Ke son ya adam wace hindu kuma ?"
Wacce hindu mike dashi a gidan nan data wuce ta gidan baba qarami wallahi har na tausaya mata dan idan ya kirani guntuwa ita km fa me zai kirata ?"
gabdaya suka sa dariya har mami "wanna kam gsky ne ina zai kaita ? ga wani cream na organic tasha duk ya canza skin dinta ta dawo farar karfi da yaji ,shi daaka bashi farar mace sol yace bai so ina ga mai shafa cream? ni wallahi da zai karbeta ma ya barni da naji dadi anan ne mami tasa baki "kar na qara jin kin fadi haka ai babu wacce zaki barwa shi da sannu zai koyi sonki dan nasan you are so different daga sauran mata ai shiyasa nace a saka sati uku ayita ta qare burina ki rage media ki janyo hankalinsa cikin kankanin lokaci ku zo juna ."
"mami kina ganin komai zanyi ya adam zai soni ?"
Mai zai hana maryam zai soki mana aure nawa akayi irin naku km a karshe ya zama soyayya mai karfi ,ni dai ina ji ajikina aurensa zai sa ku rasani da wuri tun lokacina bai yi ba." maryam ta fad'a idanuwanta na kan Mami "ki daina irin wannan tunani babu abinda zai faru sai alkhairi zai soki ki so shi babu abinda zai rabaku sai mutuwa shiru maryam tayi tana jin mami ."
Motocinsa na tsayawa a haraban AGC escout dinsa suka firfito daga cikin motocinsu mutun biyu na qoqarin bude masa murfin mota ya bud'e ya fito fuskar nan tashi sam babu annuri yana miqawa na hannun hangunsa wayoyinsa ya nufi cikin kamfanin kallo daya zaka yi masa zaka qara jin tsoronsa fiyye da yadda kake ji ."
tunda ya samu information barnar daake yi a kamfanin walwalarsa ta ragu sosai babu inda zaka kalla a fuskarsa kaga rahma ganinsa yasa kowa ya shiga hankalinsa domin a irin wannan ziyarar da yake kawowa yake korar mutun daga aiki yana tafiya ana gaishesa cike da girmamawa yayinda sectary dinsa some na biye dashi abaya hannunta rike da files wanda ake bukatar saka hannunsa duk cikin wad'an da suke gaishesa babu wanda ya masawa daya daga cikin escout dinsa yayi saurin bude masa kofar office dinsa ya shiga a natse yana duba agogon rolex din dake daure a tsintsiyar hannunsa ."
ya qarasa mazauninsa ya zauan ransa a matukar bace, cike da girmamawa some tace "good morning sir ?kanshi kawai ya gyada mata batare daya amsa ba "sir ana bukatar saka hnnunka acikin wadan nan file's din ta fad'a muryarta na rawa dan ta tsorata da yanayinsa na yau gabansa ya nuna mata alamun ta ajiye cike da girmamawa ta ajiye tana rusuna masa "ya tsurawa file's din ido kawai yana kallo kafin a hankali ya dauki daya ya rabashi gida biyu a matukar tsorace ta dinga binsa da kallo har ya gama yagasu gabdaya ya watsasu sama suka tarwatse yana hura hanci sannan yace "are you crazy some ?
Mmm sudais
💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.