Maradams Book 1 Complete Hausa Novel
Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt
Chapter 14 of 18
Page 17
" are you crazy some "?ya furta a zafafe yana hura hancinsa har zata girgiza masa kanta alamun "a'a ! sai kuma tayi sauri ta gyada masa kanta alamun "Eh! dan ko giya ta sha bata isa tace masa "no ! ba bare tana cikin hankalinta "what's wrong with mr ata I did not do anything wrong ? tayi maganr acikin ranta tana mai sake kama kanta dan karta yi wani kuskuren da zai dakatar daita na wasu satittuka koma ya dakatar daita aiki gabadaya ."
" ahankali ya mike tsaye ya kamo lip's dinsa na kasa yana cizawa ahankali ahankali !! magana yake son yi amman ko ya bud'e bakinsa maganar bazata fito ba , daga can bakin kofa akayi knowking tare da cewa "may I coming sir ?". shiru yayi yaki cewa komai sannan yaki kallon kofar , some dake tsaye cikin tsananin tsoro da fargaba ta kalli glass din kofar taga prosper ne tsaye hannunsa rike da file mai cover green wani yawu ta hadiye sannan ta saci kallon inda mr ata yake tsaye taga baya kallonta ta sake juyawa tayi wa prosper alama da hannunta ya koma da sauri ya juya ya bar bakin kofar ."
Mr ata yasa hannu ya d'auki wani file mai white cover dake ajiye akan makeken table dinsa yana dubawa , lokaci me tsawo ya d'auka yana dubawa yana shawagi acikin makeken office din nasa zuciyarsa na tafarfasa yayinda wata irin zufa ke tsatsafo wa some akan goshinta kamar an watsa mata ruwa .duk lokacin da taga mai gidan nata cikin damuwa itama sai ta tsinci kanta ciki dan kusan duk abinda yaje ya dawo akanta zai
qare tunda itace sectary dinsa duk abinda zai shiga ya fita ta sani ."
Ya sake kamo gefen lip's dinsa. na qasa yana cizawa hannunsa dake rike da file ta zubawa ido tana tausayawa duk matar datai ganganci aurensa , tana goge zufan goshinta dake ta tsatsafo mata duk da karfin sanyin ac dake ratsa office din ."Cikin kulawa da girmamawa tace "sir !" ko zan iya kiran metting a yanzu ?"
"ahankali ya lumshe lumtsatsun idanuwanshi da suka d'an canza kala alamun tarin 'bacin rai yake ji acikin ransa "sir !ta sake kiransa a karo na biyu ahankali ya motsa lip's dinsa "go !" ya fad'a atakaice batare daya kalleta ba da sauri ta juya ta fice daga cikin office din tana sauke naunayen ajiyar zuciya ."
Cikin kankanin lokaci ta dawo ta tsaya a gefe cike da kamewa da girmamawa tace "sir komai ya Kamala kai kawai ake jira." a natse ya goya hannuwansa duka abayansa ya soma daga kafafunsa dake cikin hadadden black canvers tana biye dashi abaya hannunta rike da wata takarda mai bango ja , tafiya kad'an sukai sai ga hisham da yaya Ibrahim tare da wasu manyan maikata guda biyar suka marasa baya suna takawa ahankali har zuwa qasan kamfanin madadin yabi hanyar da zai kai shi comference room sai suka ga ya karya yabi wata doguwar hanya , nan take some tayi gaba da sauri domin ta fahimci inda yake son zuwa kafin ya shiga conference room yayinda sauran suke take masa baya, bai tsaya akoina ba sai abakin wani makeken kofar glas wanda ya kasance anan ake ajiye duk wasu ayyukansu masu mahimanci ya zura duka hannuwansa acikin aljihun wondonsa yana kallon wajen yana bukatar a bude masa ya shiga tare da qarin bayani ."
Ahankali ta danna madan nan bude waje suka shiga gabadaya a natse ta shiga yi masa bayani tana nuna masa kayayyakin dake ciki da kuma wanda aka fitar kudinsu basu shigo ba duk abinda take fad'a yana jinta kuma yana fahimtarta , amman ko tari bai yi bai yi ba ."
runtse idanuwanshi yayi sosai domin ransa ya gama kololuwar 'baci , daga nan wani bangaren suka nufa inda suka dinga wuce maikata da masu zuwa sarin kaya ,ba qaramin barna akayi masu ba ,yaya Ibrahim "yanzu kuna kallo akayiwa kamfani barna mai girma haka ? ya fad'a yana sake runtse idanushi dan baya ganin komai sai wani irin azababen duhu na 'bacin rai ."
Yayi shiru na kusan second goma sannan ya sake motsa lip's dinsa "yanzu har kunnuwanka sun manta abinda dady ya fad'a mana kafin rasuwarsa .?" Ka manta umarninsa akan wannsn kamfani ?" duk wannan maganr da yayi Idanunshi na runtse sannan cikin tsadadden turancinsa yayita " ban manta komai ba adam "ban manta umarnin dady ba amman bani
da yadda zanyi ne kai kasan halin sultan da sauran yanuwansa kowa abinda yaga dama zaiyi yanzu dai tunda kazo Komi dawo daidai amman kuma kabi komai a hankali kar asamu damuwar da zata haifar da matsala a tsakaninmu wani irin azaban ciwo yaji yana saukar masa har cikin kahon zuciyarsa yana sukarsa zuciya tazo masa wuya , baya jin zai d'agawa duk wanda yake da saka hannu acikin 'barnar dakayiwa kamfanin kafa ba ,bai sake cewa komai ba ya juya da sauri suka rufa masa baya ."
conference room ."d'akin ne da'aka tanada domin tautauna mahiman abubuwa masu matukar mahimanci , dogon table ne zagaye da kujeru bakake na alfarma yayinda jikin bangon d'akin ke manne da hoton mr president na lokacin da gwanar jahar lagos ,sai hotonsa dake tsakiyar hotonsu da certificate dinsa na kasuwancinsa ."mafi yawan mutanen dake zaune aciki room din yan'uwansa ne dake aiki akarkashin kamfanin ,a natse ya shiga d'akin taron ya yana shan kamshi tsit baka jin motsin kowa sai ac dake aiki da kuma na mutane dake fita a hankali , bai kalli inda suke zaune ba ya qarasa kujerarsa wanda ya kasance mallakin mahaifinsa ne ada ya zauna cikin nuna isa."
ido sultun ya runtse da karfi saboda bakinciki ganin yadda mr ata yayi wani irin zauna akan kujera na nuna isa da jarumta da kamala duk da cikin yanayi na bacin rai yake amman hakan bai hana ainihin sahihin kyawunsa fitowa ba daman kuma shi haka yake fushi ko damuwa baya hana aga kyawunsa hasalima kyau yake qara masa."
wani dogon tsaki sultan yaja wanda bai san a fili yayisa ba sai daya ga gabdaya mutanen dake gurin sun juya suna kallonsa banda uban gayya mr ata wanda ya sake daure fuska alamun babu wasa ,sai dai zuciyarsa banda tafasa babu abinda take ahankali ya runtse tsumammun idanuwanshi domin saisaita kanshi daga aikata abinda ke taso masa ahankali ya motsa lip's dinsa ya soma magan a natse tamkar baya son magana sai dai jin maganar kasan magana ce ta masu hankali ce ."
"The journey of thousands miles begings with a step as you all know ,ya numfasa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa sannan ya cigaba d'an lokacin da muka dauka bamu ziyarci wannan kamfanin ba yasa kowa yayi abinda ya ga dama "hakika anyi mana barna mai girman da bazamu iya bari ba , bayan acikinmu kowa yasan adadin wahalar daaka sha kafin wannan kamfanin ya samu kar'buwa a idanun duniya gabadaya ,but what's more important is that duk wanda yasan yana da hannun acikinku wajen danne kwandala acikin dukiyarmu ya gaugauta dawo dashi a yanzu kafin na dauki mataki akan kowa ye acikinmu dan bazan ragawa kowa ba ,bayanin mr ata yayiwa wasu daga cikin yanuwa dadi most especially mukhtar wanda Ke rike da wayarsa yana daukar vedio tautaunawa da'ake wanda kusan duk lokacin da zaa gudanar taro haka ana yi wani lokaci a daurashi a social media wani lokaci kuma baa daurawa ."
"Ina jiranku wad'an da sukayi taadanci da fashiwa kamfani domin su san kansa ba sai na fadesu ba sannan sun san number asusun kawasuwancinmu mintuna shabiyar kacal na bayar a maida kudaden daaka hamdame cikin asusu "malam ka dinga sanin yadda zakayi ma mutum magana yaji dadi (Al kalimatu dayyibat sadaqat)kazo kana wa mutane magana cike da isa da izza wa kaajie anan ? sannan su waye suka yiwa kamfani taadanci da fashi da hamdame kudin kamfani ?"sun san kansu !mr ata yayi mgnr tmkr ba daga bakinsa mgnr ta fito ba ,ya cigaba da sauraron some ."
D'akin taron ya sake yin shiru babu wanda ya sake magana hatta yaya Ibrahim bai tofa albarkacin bakinsa ba illa ya zuba tagumi yana ji kuma kallonsa kuma hukuncin adam yayi masa daidai muryarsa a dake mr ata yace " ina jiranku rashin dawo da kudad'an nan fa daidai yake da bari aiki acikin wannan ma'aikatan ya fad'a yana kallon gefensa inda some Ke zaune tana qara masa bayanin wasu a abubuwa" idan haka ake son mutun yasan kuskurensa har gyara da mutane dayawa basu gyara kuskurensu ba sannan dan haka malamanmu suke koyar damu wallahi da babu wanda ze juri zaman islamiyya ba kafi fili ka fad'a mana su waye masu laifi musani ba ka tsaya jin kai da girman kai ba ,dan anan babu wanda ka ajiye , yadda kake iko da wannan kamfanin haka muke..."
"Enough ! ya fad'a a matukar fusace yana dukan table "ka shiga hankalinka ,su waye mahamdama macuta yan fashi daya wuce ku " sam gaku nan tamkar. mutane amman baku da bambamci da dabbobi ,sam babu jin tsoron allah acikin zuciyarku , sultan ,fahad , hamid a wani goma sha biyu kawai na baku ku dawo da komai idan ba haka ba..... "me zakayi ?sultan ya katseshi cikin zafin rai "me ka isa kayi ?babu abinda ka isa kayi "
"kunsan su dabbobi basu gane yaren biladam sai na dabbobi yan'uwansu dan Allah karku dawo da kudaden nan alokacin da nace "yana gama fadar haka ya mike tsaye ya tura kujerar daya tashi baya ya fice ."nan hayaniya ta kaure kowa na fad'ar albarkacin bakinsa kai tsaye mr ata office dinsa ya koma ."
Karfe biyu daidai na rana mami na zaune a parlour tare da yaranta maryam da nana hauwa'u suka jiyo sallamar baba qarami sai da gaban mami yayi wata irin mummunar faduwa ya qarasa shigowa yayi wa kanshi mazaunin nana hauwa'u ta gaishesa haka ma maryam ya amsa fuskarshi babu yabo babu fallasa mami ta kallesu alamun su basu waje ,bayan sun tashi sun wuce mami ta fuskancesa alokacin da shima ita yake kallo "zulai naji shiru akan maganarmu banji kin neme ni ba har gashi an saka ranar auren adamu da wacan yarinyar yana da kyau nasan inda maganarmu ta kwana abun nan zai yuwa ko kuwa ?".
mami ta numfasa gabanta na faduwa domin dai ita kam bazata iya sake kuno wa danta wata damuwar ba maryam ma da yaya ya karbeta ?gara kawai ta ari bakin adamcy tace masa a'a tunda tasan ko ta tunkaresa da batun bazai ta'ba amincewa ba cikin shakkakiyar murya tace "nayi masa magana ammm..."sai tayi shiru tana jin nauyin fitowar maganar "amman me ki fada min abinda yace "Uhm daman cewa yayi wai mace daya ta .."
shiru tayi ta qasa qarasa maganar ganin wani irin kallon da baba qarami ke mata ido cikin ido furzar da iska yayi ya lashi lebansa na kasa sannan ya hade hannunwansa still idanunshi na kan fuskarta cikin danne fushinsa dan baya son ta gane fushinsa a fili saboda abinda kan iya zuwa yazo bare su suyi zargin da hannunsu ,cikin dakewa yace "yanzu dai kin nuna min bazan iya zuwa neman alfama wajenki kiyi min ba ko ?sam sam ba haka bane kai ma kasan halin adamcy idan kuma zaka iya masa magana da kanka to kayi kamar ma haka zai fi "no ba sai nayi masa kema uwarsa da kika haifesa bai ji maganarki ba maganar ubanwa zai ji ? " iya abinda ya iya fada kenan ya tashi ya kama gabansa ya barta cikin zullumi."
Mr ata a matukar gabalaice ya qaraso gida zuciyarsa tamkar zata kama da wuta , sai dai cike da qasaita ya shigo parlour'n Mami babu kowa parlour'n sai qarar tv da motsin masu aiki a kitchen ya zauna akan doguwar kujera ya d'ora kafarsa d'aya akan d'aya yana ciza gefen lips dinsa ,ko cikakken second goma bai yi da shigowa ba sai ga hindu ta shigo dan akan danunta ya shigo tunda mahaifinta ya fad'a mata yadda sukai da Mami ta kasa tsaye ta kasa zaune , zama tayi a kujerar dake fuskartashi ta tsura masa idanunta tana kallonsa tamkar ranar ta fara ganinsa tana qoqarin bude baki tayi masa magana ya mike tsam ya kwashe wayoyinsa ya haye samansa yana jan tsaki dan shi ya tsani yawon kallo , kamar ta dakatar dashi amman ta kasa ta cigaba da zama zuciyarta na mata wani irin bugawa akanshi ."
tana nan zaune har mami ta fito sanye cikin doguwar rigar na atamfar super exclusive sabuwar bugu ,mami bata tsufa saboda tsanani tsafta da gyaran jiki fuskarta a sake tace "a'a hindu yaushe kika shigo ?ban wani jima ba mami nazo wajen yaya ne "to ai bai shigo gidan ba tukun .
ya shigo yanzu ya hau sama "to shikenan bari naje dakin nasa nazo har ta juya hindu ta kirata sunanta cike da rauni "mami !"
Cak mami ta tsaya tare da juyowa ta tsurawa hindu ido "mami da gaske kin yiwa yaya adam maganata yace miki a'a ?"shiru mami tayi shiru ta rasa me zatace mata kafin mami tayi wata magana hindu ta cigaba da mgn cikin rawar murya "dan girman allah mami karki yi min tsakani da ya adam kullum zuciyata tafasa take akan sonshi Ke kad'aice zaki iya taimakawa zuciyata idan ba haka ba zan mutu cikin rawar murya mami tace "mutuwa kuma ?"kanta ta gyada mata tare da cewa "da gaske zan kashe kaina shine fansa akan soyayyar ya adam "na shiga uku ni zulai "mami ta furta acikin zuciyarta "kiyi addua hindu ni kaina zan só adamcy ya auri mata fiyye da biyu amman raayinsa ne auren mace daya macen dayan ma da kyar ya amince amman Kiyi addua nan gaba idan rabo sai ya qara dake da sauri ta runtse idanunta kana ta koma ta jingina bayanta da kujerar da take zaune tana jin wai irin faduwar gaba mai tsanani ahankali take zubar da hawaye ganin da gaske tarasa farincikin rayuwarta "anya kuwa mami nada tausayi da imani ."Anya mami bata da son zuciya ?"Tayi wa kanta tambayar tana jin radadi acikin zuciyarta bazata iya jurar rashinsa ba ,bazata iya ganin da wata a matsayin matarsa ba, yadda bazata zama matarsa a farko ba to babu wacce zata zama "hindu bari naje naga yayanku nazo hindu ta bude idanunta da kyau tana kallon bayan mami dake taku ahankali."
Kai tsaye kitchen ta shiga ta bud'e firdge kwalin dynsimo mai sanyi ta ciro ta rufe ta qarasa inda cup's suke ta dauki daya ta daura akan qaramin tray ta fito ta wuce a parlour ta samesa zaune akan kujera yana sanye da singlet da gajeren wondo ta bude kwalin juist din ta tsiyaya a glass cup taja qaramin table din glass din dake tsakiyar dakin ta dora tray ta mika masa cup ya girgiza mata kai tace "na kawo maka ruwan sanyi ?ya sake girgiza mata kai "coffee fa ? still dai kai ya girgiza aranta tace yau dai akwai damuwa ta d'an zauna gefensa "ka daina barin damuwa na hana zuciyarka sukuni "naji sweetheart amman ba wani damuwa bane zazzabi nake ji kawai "sannu bari naje na kawo maka magani ka sha "no need sweetheart thank you "kai har yanzu bakasan ka girma bane meye abun gudu a magani ?ni dai kawai bana só né da zarar na kwanta nayi bacci zanji daidai ,tô karka kwanta yanzu magariba ta kusa ya gyada mata kai yana mai runtse idanuwanshi ta mike tana cewa "me zaka ci dan tuwon shimkafa kayi yau idanunshi ya dan bude kadan "karki damu sweetheart yau bazan ci komai ba amman zuwa anjima I need coffee tasan haka tsarinsa yake wani lokaci sai ya kwana ya yini bai ba ."
*****
Tsawon kwana Uku kenan rabon maryama ta shiga harka mahaifiyarta har ma da habibi hakan kuwa ba qaramin taga masu hankali yayi ba gabadaya gidan yayi wani iri saboda rashin walwalar maryama ,ta kuma san duk akan abinda take son tayi ne domin tasan halinta tasan abinda take so da abinda bata só tana da tsananin hakuri amman idan kaga ta kafe akan abu to dole abun zai zama gaskiya ne ko alkhairi ga rayuwar mutun ,ta sani gsky take fad'a mata amman bazata iya abinda take bukata ba bazata ta'ba komawa garesu ba duk runtsi duk wahala zata daure ta cigaba da rayuwarta a yadda take yi , maryama fa ta dauki zafi sosai akan aunty da habibi duk lokacin da ta fito parlour'n tagansu sai ta koma daki ko taje bangaren umma bata dawowa sai dare da zarar tashigo kuma zata shige daki tayi kwanciyarta ko ta dauko kayan zanenta ta fara aiki ."
Da misalin karfe tara na daren ranar litini maryama tana zaune akan kujera ta cilla pencil a bakinta tana taunawa a hankali idanunta na kallon celling dakin tana nazarin abinda zata zana taji an turo kofar d'aki ahankali ta kai dubanta ga kallon kofar dakin ,aunty ta gani tsaye ,ta dauke kanta daga kallonta, aunty ta maida murfin kofar ta rufe ta soma takowa zuwa inda maryama take tana ganin haka ta mike tsam ta haye saman gado tayi kwanciyata tare da kamkame jikinta tana jin tausayin kansu na sake ratsa ko ina ajikinta musamman take jin kewar yanuwan mahaifiyarta da bata taba daura kwayar idanunta akansu ba amman tana jin ajikinta zasu samu kulawarsu da soyayya a duk sanda suka had'u kamar kowani dangin uwa tana kallo aunty ta zauna daidai inda fuskarta take dan hk da sauri ta runtse idanunta tana son tayi bacci ."
bacci bai samu nasarar d'aukarta ba ta juya dayan bangaren sakamakon kukan da Ke shirin kufce mata dan ita kanta dauriya kawai take akan sabon canjin data kawo a tsakaninsu hakan bai hana aunty ganin abinda take ba ,daidai inda fuskarta ke kallo ta dawo ta zauna tana dubanta hade da kamo hannuta cikin nata "me nayi miki my princess kike qoqarin Kaurace min byn Kinsan bani da kowa bani komai sai ku ? Kafin maryama tayi yunkurin cewa wani abu aunty ta sake jiho mata wata tmbyr "yanzu na cancaci haka a wajenki ,"?"Na lura kina bukatar rayuwata princess "idan kika bari damuwarki ta kasheni shikenan sau ki huta ai .... "
a d'an zabure maryama ta mike zaune daga kwance da take suna fuskatar juna da aunty yayinda hawayen idanunta suka shiga xubowa sharrrrrrrrr....."
" meye kuma abun kuka daga magana "kiyi hakuri aunty nasan damuwata na damunki ina kukan ne saboda an cuceki an rabaki da yanuwanki da iyayenki alhalin suna sonki , bansan yadda zan misalta miki yadda nakeji ba, aunty ki taba zuciyata kiji yadda take bugawa tayi mgnr tare da kai hannuta ta kamo hannu aunty ta d'aura daidai saitin zuciyarta dake wani irin bugawa tamkar ana buga mata guduma, tabbas aunty taji kokawar da zuciyar keyi amman bata yadda zatayi gurin raba zuciyar da damuwa addua dai ce kuma tana kanyita babu dare babu rana kuma tasan ubangijinta baxai barta haka ba batare daya duba lamarinta ba.
cikin murya me cike rudanin rayuwa maryama ta cigaba da mgn "bansa me zanyi abubuwa su dawo mana daidai ba har ki cigaba da rayuwarki kamar da? " aunty ki daina daukar iyayenki da yanuwanki a matsayin makiyanki ,iyayenki suna sonki fiyye da tinaninki ,sun nuna miki so da kauna tattare da kulawa da gata alokacin da kike zaman lafiya dasu aunty kema kanki Kinsan irin soyayyarsu garenki "aunty !!! ki daina ganin laifinsu sannan ki dai jin zafinsu dan su dauki fushi dake ?"
Su iyaye ne zasu iya yin komai suci lafiya a yanayin yadda rayuwa tazo miki cike da rudanin yaci ace zuwa yanzu kin samu y'anci ki tsinci kanki cikin farinciki da jin dad'in rayuwa kwana uku kawai da baki ga walwalata ba kin daga hankalinki inga bana cikin gidan nan ?"ina ga nabi wani na barki ya zakiji ? wallahi iyayenki suna can cikin tsananin kewarki kwatankwacin yadda kike jin namu da zaki koma garesu zasu karbeki su kuma yafe miki " kiyi hakuri aunty ki daina ganin laifinsu ta karasa fadar haka tana xubda wasu zafafan hawaye hade da rike hannun aunty gam tana me tausayawa rayuwarta ."
"Idan abubuwan dake faruwa suka cigaba da faruwa bana tinanin zuciyar dake kirjina zata cigaba da baguwa ni dai ki koma cikin yanuwanki dan Allah ki roki gafarar iyayenki su yafe miki mu cigaba da rayuwarmu kamar yadda muka saba . ahankali aunty tashiga bubbuga bayanta "kukan ya isa haka
Inshaallahu zan .. zan.. koma garesu da izinin Allah sosai aunty ta dinga rarrashinta da gaya mata maganganu masu dadi da sanyaya rai har ta soma bacci ajikita cike da samun kwanciyar hankali .
Washegari kowa yasan maryama na cikin kwanciyar hankali wanda hakan ya kwantar da hankalin babib da aunty tare suka ci abinci kamar yadda suka saba ,maryama tana zaune a falo byn tayi wanka ta shirya tana kitsa gashinta gida hud'u sakina ta shigo suka sha hirarsu duk aunty na jinsu sosai taji dadi aranta ganin maryama ta saki ranta ,har sakina ta fita ta dawo "maryama amman yau zaki islamiyya?"eh!zani idan na gama zan biyo miki sakina ta qarasa fita ita kuma ta mike ta shiga daki tai sallah ta qara shiryawa ta dauki alqurani ta fito ta tsaya a bakin part dinsu sakina tana jiranta byn ta gaishe da aunty salma sakina ta fito ta tsaya kusa da maryama tana mata magana kasa kasa aunty salma ta bisu da harara har suka fice ,ta nemi guri ta zauna zuciyarta na tafasa ."
ta rasa yadda zata kawo karshen shakuwar sakina da maryama duk duniya bata da abinda ta tsana tamkar maryama tayi shiru cikin tsanani tunani abubuwa da dama take sakawa in dai da rai da lafiya sai ta rabasu domin itace kadai hanyar da zata nunawa maryama tsangwama da tsanar datayi mata shegiyar yarinya kamar mayya ko aljanna zatace banda abun sakina ai maryama matsala ce arayuwarta, yanzu ko saurayi idan sakina tayi yayi ido biyu da maryama ai tuni zaice shi ga wacce yake so yarinyar ta cika kyau haka kamar ita tayi kanta ta fad'a acikin ranta ta mike tsaye cikin takaici to ko afa zata kaiwa kukanta , zuciyarta ta kawo mata dauki da wannan tunani aikuwa hakan shine mafuta afa shine zai kawo mata karshen komai da karshen wannan shakuwartasu mayafinta ta dauka ta yafa ta fice daga gidan tana surutai ita kadai kamar yadda na shiga na fita na rabaki da duk wanda yazo da sunan yana sonki da aure yanzu ma sai na rabaki da sakina takowani hali ki cigaba da rayuwarki Ke kadai Kmr mayya acikin gidan nan ."
Tayi sallama aka amsa mata daga ciki dan haka ta shiga ta tsaya afa da yake ciki bai amsa ba yayi gyaran murya hakan ya tabbatar mata akwai wani aciki ta dan jira na rabin awa sannan wacce take ciki ta fito suka gaisa ta fice a karo na biyu tayi sallama ta shiga cikin dakin ta durkusa ta gaishe shi yana zaune akan daddumar sallah wani katon tray mai cike da katon kasa da wuri na duba ya amsa mata cike da kulawa "meye ma sunanki yaushe rabon na sakaki a idona ?"Aunty salma tayi murmushi tace afa kenan abine sai ahankali idan ka ganmu tamu ce ta kawo mu yayi murmushi ya dan shafa gemunshi yana lashe lebensa "to ina jinki fara bayanin abinda Ke tafe dake kafin na duba naga gskyar lamari ".
Mmm sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura wa wannan 0913691 8331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 15
"Aisha , saber, da mahamud , ta gani tsaye akansu suna huci kamar zakuna cikin matsanamcin tashin hankali mara misaltuwa suna kallonta kamar zasu cinyeta ai babu shiri daga bilkisu har ussein suka mike daga jikin juna hankalinsu yayi mugu mugun tashi ."
bilkisu ta tsaya tana kalle kallen inda zata boye acikin d'akin tare da cure hannayenta waje d'aya jikinta na sake d'aukar rawa bata ta'ba shiga tashin hankali da nadama irin na ranar ba domin har ga Allah bata ta'ba tunanin zasu bibiyi takunta ba ."
Nan da nan idanunta ya kawo ruwan hawaye ba tace komai ba, ta durkusa qasa bisa gwiwo
winta dan tasan sai na lahira ya fita jin dadi mahamud ya rike kungunsa yana cigaba da kallonta ,mamakinta kawai yake dawainiya dashi idan aka fad'a masa cewar zata biyo nmj har d'akinsa bazai ta'ba yarda ba, watakilla ma da sai ya wankawa wanda ya fad'a masa hakan mari "dan girman Allah kuyi hakuri ku yafe min ku rufa min asiri kar mumy tasani ta karashe mgnr tana kuka cikin tashin hankali mahamud ya buga mata wata razananniyar tsawa data hargitsa mata lissafi "yi min shiru makira bana son jin komai daga bakinki ."
nan take tayi shiru kukanta ya qaru ta kalli inda ussein yake tsaye shima kana kallonsa kasan baya cikin natsuwarsa "mahamud tsayawa kayi kallonta bazaka fara cin ubanta tun anan ba ? Aisha ta fad'a tana mata wani irin kallo shi kuwa wanda aka kira da mahamud tunanin yake idan yace zai ta'bata to babu shakka zata mutu idan kuwa bata mutu ba zata jikata ."
"dan girman allah Aunty ai.."ai bata kai ga fad'ar abinda take son fad'a ba taji wani gigitaccen mari hagu da dama akan kuncinta "you are very stupid bilkisu , akanki aka fara soyayya?" kin haukace kin makance akan wannan banzar ,me yasa zaki mance ko ke wacece ? wato soyayya tasa kin manta matsayinki ? cikin muryar kuka tace " a'a Aunty aisha ban mance ba amman kuyi hakuri wallahi bazan sake ba "hayaniyar yan yan'uwanta ya sake d'aga mata hankali shi kuwa ussein sunkuyar da kanshi. kasa yayi yana tunanin ficewa ya bar d'akin dan yasan Allah ne kawai zai kwacesa a hannunsu ."
Kai tsaye bilkisu ta nufi bayan kofa ta boye jikinta na wani irin rawa sakamakon jiyo muryar hajiya rahma tana cewa "ina bilkisu take naga kun tsaya jugun jugun ko ta gudu ne ? kafin kace me an samu wanda yazo ya fad'a mana halin da'ake ciki a guje na bazamo na bar hajiya dan bazan iya jiranta ba kasancewar tana fama da lalurar ciwon kafa ."
" ina tafiya ina neman layin yan' uwansashi da kyar na samu ta abban sadam yana gama jin bayanina cewa yayi babu ruwansa dan yasan halinsa da tara yammata , babu yadda banyi dashi ba yace bai zuwa koina ya kashe wayarsa jin abinda ya fad'a yasa na kira yayyensa mata ."
Ina shiga unguwar naga jamaa sun yi cirko cirko!! ga manya manyan motoci na gidansu bilkisu jere a kofar gidan ,haka ina shiga cikin gidan mutane na gani makil kowa na fadar albarkaci bakinsa ,yayinda muryar mahaifiyarta ya karad'e koina acikin gidan "da gaske ne bilkisu tana cikin wannna ru'babben d'akin ? Aisha ta nuna mata bayan kofar d'akin "tana ciki kuwa ga makira nan a bayan kofa ta fad'a tana zubar da hawayen takaici ."
"inna lillahi ! hjy rahma ta furta a fili cikin tsananin tashin hankali "kunji abinda naji kuwa wallahi ji nayi zuciyata kamar ta buga ?hankalin bilkisu ya bar duniyar da muke alokacin dan sai wuri wuri da idanu take shi kansa ussein kana kallonsa kasan nadama ne acikin ransa nadama irin wacce bata da wani rana ."
" amman bilkisu bakince min kin rabu dashi ba ?jikinta na rawa ta shiga gyada mata kai alamun Eh! tana bawa mahaifiyarta hakuri da wani irin fushi ta juya inda ussein yake cike da nadama ta shiga zabzabga masa mari ta koina "bana ce maka ka rabu mun da yarinya ba ? ba banace karka sake shiga rayuwarta ba?"Ko kaga yarinyata tayi kalar wacce zaka ce kana so ? ta juya zuwa ga bilkisu " Ke yanzu har wannan qazamin ne abun so a wajenki ? ta fad'a tana sake juyowa ta d'aga hannu zata sake tsinkawa ussein mari nayi saurin rike mata hannu ina bata hakuri "kiyi hakuri hjy sam ussein bai kyauta ba daya bawa yarinyarki damar zuwa inda yake ,ya karbi laifinsa ayi masa afuwa in sha allahu hakan bazai sake faruwa ba Kinsan kowa da irin jarabawarsa dukkanin rayuwa rubutaccen lamari ne daga Allah ,kuma kowani dan Adam yasan da haka ,yanzu tunda abun ya zama haka ku bamu dama sai mu turo ayi maganar aure "."
Wani irin kallo gabadayansu suka bini dashi ,hjy rahma tace "Allah ya tsareni na had'a zuria da wannan ta nuna ussein da yatsanta tana hararsa "wallahi bilkisuna tafi karfen aurensa ki kalleta sama da qasa ki kallesa ta ina hadin yayi daidai ? duk nasan da haka hjy amman a wajenta shine daidai bugu da qari rayuwar yarinyar ku zaku duba domin ita diya mace ce zata iya fad'awa kowani hali ."
"Ba kowani hali zata fad'a ba ko mutuwa zatai sai dai ta mutu na yarda na rasata gbdy akan na bawa wannan matsiyacin aurenta ta numfasa tare da sa tafin hannunta ta share hawayen idanunta "hjy ki daina furta haka shi soyayya allah ne yake had'awa , kuma babu ruwan soyayya da tsiya ko arziki yarinyar nan tana qaunarsa shima kuma yana sonta dan girman allah ki barsu suyi aurensu kowa ya huta sannna babu wanda yasan matsiyaci ko mai arziki sai Allah sannan babu wanda yasan mai gobe zata haifar ku barsu su aure juna domin samun kwanciyar hankali ."
bata kulani ba har na dasa aya ta fuskanci bilkisu yayinda gabadaya yanuwanta kacokan suka maida hankalinsu Kan ussein duk sun qagu suga hukunci mahamud akan ussein kasancewarsa soja , hjy rahma ta matso sosai kusa da bilkisu tana cewa "ba dai ni zaki wulakanta akan namiji ba ? ."babu irin rarrashin da ban miki ba ,babu irin hakurin da ban baki ba ,me kike son dani ? "wallahi zanyi dake bilkisu , yau zaki ga tozarci ganin idanunki tunda kika nemi ki wulakantani akan wani banza can wanda ba kowan kowa bane shi ,ba kowa bane iyayensa a duk fadin garin nan hasalima rayuwarsa a banza take ."
"zaki wulakantani akan wani nmj banza da wofi wallahi zanyi dake muddin kika ce shi zaki aura sai na tsine miki na tsinewa auren ,wallahi auren bazai ta'ba yin albarka tana mgn tana zabga mata mari a fuskarta da bayan hannunta , yayinda azaba tasa bilkisu ta shiga karewa dan kar marin yayi mata illa amman matar nan sai zabga mata maruka take kuma a fuska na rantse miki da girman allah maryama tayi mata mari yafi guda tara ajere ana goma ne bilkisu ta rike mata hannu kuma nasan azaba ce tasa tayi haka ,aiko matar nan ta danneta da iyakacin karfinta ta dinga dukanta tana cewa ni zaki rikewa hannu in sha allahu kema sai ya'yanki sun miki abinda kika min ,sai sun hanaki kwanciyar hankali kamar yadda kika hanani kwanciyar hankali a karshe kafa mata hakori a damtsen hannunta."
"wani irin gigitaccen qara bilkisu ta saki mai ban tausayi tana kuka tana neman d'auki gashi babu wanda ya kwaceta daga hannun mahaifiyarta sai dukanta take tana hadawa da zagi ganin haka yasa ussein ya nufi hjy rahma cikin tsananin fushi kamar mayunwanci zaki idanunshi sun kad'a sunyi jajur yasa duka hannunsa zai d'agata daga Kan bilkisu ai ganin ya ta'ba mahaifiyarsu gbdy yan'uwanta suka yo Kanshi shi da bilkisu cike da jin haushi suka dinga dukan su kamar zasu kashesu suna furta mahaifiyarmu zaka duka ? azahiri gaskiya ba wai dukanta yayi ba kawai ceton bilkisu zai yi daga dukanta, ina kuka ina basu hakuri ina qoqarin kwatarsa daga hannunsu amman ina sarkin yawo yafi sarkin karfi dan sai suka daina dukan bilkisu suka cigaba da dukansa shi kad'ai har sanda hjy ta shigo zubewa tayi kasa tana kuka tana cewa "zaku kashemun d'a ne to wallahi idan kuka kasheshi hukuma ce zata rabamu daku dan wallahil azim bazan ta'ba yarda ba ".
"kar Allah yasa ki yarda daman kece uwar matsiyaci ? "nice uwarsa kuma gatansa kuma ni d'ana ba matsiyaci bane dan me zaku masa haka ?
"ai yarku zaku jawa kunne ta daina zuwa inda yake shi meye laifinsa ? "laifinsa kulata da yake yi idan baya kulata bazata zo inda yake ba ,idan yace baya sonta karta sake zuwa inda yake ni nasan bilkisu bazata zo inda yake ba ki fad'a masa da babban murya ya rabu da kanwarmu ya zauna lafiya idan ba haka ba zamu 'batar dashi agarin nan ,kina ji kina gani zaki rasa d'anki har abada "hjy na fad'a 'yanuwan bilkisu na maida mata martani kuma basu daina dukansa ba ."
"neman layin 'yanuwasa mata na sake yi saadatu na d'auka na saka mata kuka ina cewa "bazaku zo ba sai an kashe maku da'nuwa ?dan girman allah kuzo ku hanzarta karku bari su illatashi "bilkisu cikin kuka ta rarrafa ta rike kafafun mahamud domin duk yafi dukan ussein cikin kuka tace "yaya dan girman allah kayi hakuri ka barshi karku kashe min rayuwata sannna karku rabani da dashi wallahi bashi da laifi nice mai laifi" .
"ya salam! ya furta a matukar fusace "wai bilkisu me ke damunki ne "?ta girgiza masa kai idanunta na zubar da ruwan hawaye kuyi hakuri nayi maku alkwarin bazan sake zuwa inda yake ba "muryar hjy rahma ta sake karade d'akin Aisha riko hannun makaryaciya karta gudu shi kuma sheidani ku fito min dashi yau zan nuna masa koni wacece agarin nan zanga uban da ya isa ya kwaceka Aisha ta riko hannun bilkisu gam bisa umarnin mahaifiyarsu sai dai bilkisu ta dinga turjewa nan ma wani marin aisha ta kai mata tuni daman fuskarta ta canza jini ya kwanta a duka idanunta ."
Mahamud kuwa qarasawa yayi inda ussein yake yace ya kama kunnensa ussein ya kama kunensa cikin kaduwa dan gbdy bai fahimci abinda yake nufi ba mahamud yace "you're very stupid I mean kayi frog jump Aishat ashe ma illiterate ne wallahi ko da wasa naji ka qara shiga harkar bilkisu zan mugun baka mamaki "mugun ma illiterate katon jahili liability kawai a haka zamu bashi aurenta sai kace kwakwaluwarmu ta juye ai har abada ,ka wuce dashi kaci ubansa ta yadda ko mai kama daita ya gani da mugun mugu zai arce ."
bilkisu na kuka ussein na frog jump nima ina biye dasu ina basu hakuri haka hjy hakuri take basu hankalinta a tashe muna fitowa kofar gida sai ga saadatu da fatima a rude basu tsaya neman baasi ba dan na rigada na fad'a masu komai sausauci suke neman masa amman mutanen nan suka ki banda cin mutunci babu abinda suke zubawa unguwa kuwa ya cika makil da jama'a yan kallo kowa na fadin albakacin bakinsu wasu suna ganin daidai ne matakin da suka dauka dayawa kuma laifin bilkisu suke gani ."
wani abu mai daci yan'uwansa suka hadiye tare da matsowa inda mahamud yake yana laftawa ussein belt a gadon bayansa "yanzu ina zaku dashi ?In ji cewar fatima tayi maganar cikin tsananin fushi "zamu tafi dashi inda zamu sake koya masa hankali," ya fad'a cike da gadara da isa "amman yana da kyau mu san inda zaku da d'anuwanmu kafin ku wuce dashi? Eh ! yana da kyau sai dai bani da wannan lokacin 'batawa idan aka koya masa hankali zaa iya sanar daku kuzo ku d'auki abinda ya saura ajikinsa "
Hjy kuka saadatu kuka haka ma fatima muna cikin wannan halin sai ga gali yace shine yayansa suyi hakuri su bar komai a hannunsa zai sa ya rabu daita rabuwa ta har abada ,mahamud yace "da dai ya fiyye masa kwanciyar hankali dan wallahi na sake dawowa akan case din nan sai dai ku dauki gawarsa" gali yace "to mun gode komai yazo karshe bilkisu ta bude idanunta da suka mata nauyi wani marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka tana kallon kowa wanda ni nasan kukan da take alokacin bai wuce na rabuwa da ussein ba ."
fatima ta watsa mata harara hade da kallon banza tana cewa "kukan uwar me zakiyi wa mutane duk bake kika jawo masa matsala ba yana zaman zamansa muguwa azzaluma kin janyo yanuwanki sun wulakanta mana d'anuwan an tozarshi, tunda muke anan unguwar aka haifemu muka girma mukayi aure baa ta'ba wulakantamu ba sai yau kuma duk akanki ,kinsa ana dukansa kamar an samu ganga na rantse da girman allah matukar ussein..."
saurin toshe mata baki nayi ina cewa fatima karki rantse ,cikin fushi ta cire min hannu "ki barni aunty nayi magana kalli yadda fuskarsa tayi duk jini saboda Allah yau ayita ta qare ta kama kanta ta daina zuwa inda yake ,yanzu da suka zo suna hargagin banza da wofi da wulakanci shi meye laifinsa? yarinyarsu ya dace suyi wa magana ta daina zuwa inda yake dan muddin ta sake zuwa inda yake kafin ku dauki mataki mu zamu dauka dan ba daga sama ya fado ba azzaluman banza kawai kuma allah ya isa tsakaninmu daku tana fad'a aisha na fad'a."dan girman allah fatima karki sake cewa komai zo muyi magana na janyo hannunta " babu inda zani aunty ayita ta qare gwama su san muma bama son wannan diyar tasu kuma komai zai faru ..."
na sake toshe mata baki "dan Allah ki bar mgnr nan sulhu ake nema ."
Cikin ko in kula hjy rahma tace da wa zakuyi sulhu ?"kema Kinsan ruwa ba sa,an kwado bane baku kai wannan matsayin ba yanzu ma wannan maganar da nake duk sai na fashesa akan wannan matsiyacin "nayi tsuru tsuru ina dubanta "tsayuwar me kukeyi ku taho min dashi da sauri gali ya qaraso inda take hjy ai mun gama magana da yaronki, dan allah hjy kiyi hakuri ,in sha allahu tunda muka shiga cikin zance komai yazo karshe zanyi magana dashi "babu irin hakurin da baa bawa hajiya rahma ba amman tace sam sai an tafi dashi haka muna ji muna gani aka watsa useein abayan boot din mota aka wuce da
ussein ."
Kuka sosai maryama take kamar alokacin komai ya faru Kwantar da kanta umma tayi akan cinyarta tana rarrashinta "tabbas Aunty masoyiya ce ta gaskiya ,ta so mahaifinmu a halin babu ,ta zauna dashi har karshen rayuwarsa wallahi ba kowani d'an mai kudi bane mutumin kirki kamarta ,ta tsaya ta dubi mahaifinmu da kalmar so ta gaskiya
sai dai akwai illa umma Aunty ta jefa rayuwarta cikin matsala wanda a yanzu take shan wahala ".
" tabbas shine gskiyar dana dade ina nuna mata "baa jayayya da iyaye data yi hakuri tabi umarnin iyayenta tabbas zasu sauko dan kansu kasancewar akwai rabo a tsakaninta da mahaifinku ,cikin muryar kuka tace "mune silar jefa rayuwar mahaifiyarmu cikin wahala ko ? ta fad'a tana sheshekar kuka "karki ce haka maryama haka tata qaddarar take ,ita qaddara gata ko arziki ko nasaba bai isa ya canza maka ba ."umma ta numfasa sannan ta cigaba da magana ".
Bangaren su bilkisu kuwa tunda suka dauki hanya yan'uwanta suke magana suna zagin ussein cikin kuka bilkisu Ke rikon su "ku sani ussein bai muku laifin komai ba dan allah karku hukuntashi akan abinda bai yi ba" mari mahaifiyarta ta kifa mata haka ma aisha dan ubanki ki kama mana baki har suka kai gida zaginta suke direba na ajiyesu ya wuce da mahamud da ussein ."
a matukar gigice bilkisu tabi byn motar da kallo cikin tsananin firgici, keyarta suka tasa sai cikin bangaren hjy rahma ."Suna shiga part din hjy rahma suka turata daki suka daureta da igiya tamau sukasa saber ya dinga dukanta adaure tun tana ihu har tazo ta kasa a yadda ta fad'a min cewa tayi har da barkono mahaifiyarta ta nika tasa mata a gabanta da cikin idanunta wanda yasa tayi suman wuncin gadi ."
Bangaren mu rana babu wanda ya samu sukuni acikinmu gali yafi kowa shiga damuwa safa da marwa yake yana cewa "ban ta'ba kawowa araina duk hakurin dana basu ba zasu hakura ba , na dauka maganata zai sa su hakura amman ina kamar sake fusata mahaifiyarta nayi wadan nan mutane sam basu da imani ."wallahi basu da imani gali inji cewar hjy ka kalli irin duka da sukayi yarinyar nan bilkisu ko rikonta suke bai dace suyi mata irin wannan dukan ba ."
"wallahi ku sheida bilkisu bazata sha wannan wahalar a banza ba komai zai faru sai useein ya aureta ba dai bakinciki su kenan ba saboda suna takama da kudi ,ni bana da kudi amman ina da Allah alfarma annabi da alqurni sai wannan auren ya tabbata ko ina raye ko byn na mutu mutane sam babu imani aransu bazai hakura da aurenta ba sai dai su mutu fatima zatayi magana ta dakatar daita "banason jin komai daga bakinku sai fatan wannan auren ya tabbata ."
abban sadam ya fito daga bayi daman zagayawa yayi yace "har yanzu bazaku hakura da wannan maganar ba ? hjy tace "taya zaa hakura?" da sukutun fa suka wuce min dashi ?naga diyarsu ce tunda sunce basaso tarayyarsu a hakura mana "bazaa hakura ba bilkisu bazata sha wahala akan ussein ya tafi a banza ba ina sonta tunda tana son jinina ta gama min komai ni yanzu ta'bo min abokika Abdul zanyi magana dashi babu irin kiran da baayiwa Abdul ba amman wayar bata shiga ranar hjy bata runtsa ba kwana tayi tana kaiwa allah kukanta ."
Washegari ana idar da sallahr asuba tasa aka cigaba da trying dinsa amman shiru baya shiga sai karfe uku na rana ta shiga ya dauka da sallama byn sun gaisa hjy tace "Abdul ko kasamu labarin abinda Ke faruwa da useein ?bansan me yake cewa hjy ba amman naji tace "meye rashin kyautarwasa haramun ne dan soyayya tashiga tsakaninsu ?saboda shi talaka ne yasa basu dace ba to shikenan nan in sha allahu gamu nan zuwa ."
Tana gama waya tace muje gidansu bilkisu mu samu mahaifinta nace" a'a ta bari ni da gali da fatima muje da kyar hjy ta yarda ta barmu muje babu ita sai dai fatima tace bata zuwa koina nace saboda me kai tsaye tace min ta tsani bilkisu da yan gidansu sai da saadatu da gali mukaje da taimakon Abdul muka shiga estate dinsu sai dai baa bari mun shiga cikin gidansu ba a bakin get din gidan aka tsaidamu yayanta abubakar muka samu gani muka gaisa dashi babu laifi fuskarsa da dan rahma dan yafi mahaifiyarsa byn mun gaisa gali ya fad'a masa ko mu su waye da dalilin zuwanmu "ayi hakuri ranka ya dade ,hakika danuwanmu bai kyauta maku ba domin ya shiga hurumin da banashi ba soyayya da diya irin taku shima yasan bai dace ba , dan allah kasa baki ranka ya dade abamu ussein tun jiya da suka wuce dashi baa dawo dashi ba ,dan allah a maido mana dashi ."
shiru yayi ya kasa cewa komai ganin hk yasa gbdy muka kwantar da murya "ka taimaka kasa a sako mana ussein cikin ko in kula yace kuje zai dawo gida zuwa anjima amman kuja masa kunne ya fita a rayuwar bilkisu "in sha allahu komai yazo karshe cike da farinciki muka juya zuwa gida zaman jiran dawowar ussein ."bini bini sai mu leka waje ko zamu hangosa amman shiru har kusan karfe shadaya na dare har mun fidda rai dashi sai gashi an shigo mana dashi bangaren hjy yana dingisa kafa da kyar ."
da sauri muka taresa dan gbdy muna tare har hassana wacce tafi kowa shan kuka hjy kam cikin yanayi na tashin hankali ta isa garesa tana kuka "yanzu haka suka maka ussein ,kawai dan kana soyayya da diyarsu allah ya saka maka ,allah ya bi maka hakinka alfarma annabi muhammadu sai bilkisu ta zama mallakinka "wai meye hk hjy ana kokarin ya rabu da yarinyar mutane ya huta da wahala amman kina sake dagula masa lisaafi .
Gali ya fad'a yana kallon ussein " kai ka rabu musu da yarinya idan ba haka ba wallahi komai ya sake faruwa babu ruwanmu ,babu hannu babu kafarmu sai dai ka karata kai kadai dan bazamu iya wahala ba wadan nan mutanen marasa mutunci ne "wannan gsky ne gali babu ruwanmu dan bazamu iya dasu ba inji cewar saadatu ,to ku yanzu laifinsa kuke gani bakwa ganin na yarinyar ?ai yarinyar tafi shi laifi domin ita Ke zuwa inda yake wallahi na tsani yarinyar nan ."
"koni wallahi na tsaneta maryama wannan shima mafarin tsanar yanuwan mahaifinki ga mahaifiyarki alokacin ina kallon ussein wani irin numfashi mai zafi ya fesar kana ya samu waje ya zauna da kyar ya daura kanshi akan hannun kujera ya kwantar tare da lumshe idanun shi yana jin duk abinda kowa yake fad'a daya byn daya bayan wasu mintuna ya kuma budewa yana kallon kowa cikin sanyayyar murya yace "in sha allahu na rabu daita har abada dan kwana ne kawai a gaba da na mutu "ka kwantar da hankalinka muddin ina raye baka da mata sai bilkisu ka daina cewa ka rabu daita dan na nasan kana sonta har yanzu ."
"haba hjy wai me yasa kike fadar haka Kmr baki tausaya masa ? "yanzu ku yarinyar nan bata baku tausayi ?ita ma ba laifinta bane soyayya ce da qaddara ke tangaliliya da rayuwarta dacen iyaye ne batayi ba shiyasa take shan wahala amman itama abar a tausaya mata ce "gsky mu dai bamu yarda ba kuma ta ina zasu bada aurenta byn kina kallon haukan da suke akanta ? kusa ido kuga ikon allah muna zaune zasu nemo mu da maganarta da izinin allah "babu wanda yace uffan kowa ya mike ya kama gabansa ."
****
Bayan wata biyu da faruwar komai mahaifiyarta ta shiga neman taimako akan bilkisu dan kawai ta rabu da ussein , yau akarbo taimako daga wannan malamin gobe akarbo daga wancan malami , akwai inda aka kaita sai data d'auki alqurni ta rantse akan zata rabu da ussein , hankalinta ya tashi matuka taki amsa ta firgita kwarai da lamarin mahaifiyarta ."
fito da duka idanunta tayi tana furta tashi uku bataso ba amman mahaifiyarta na kallo mutumin yasa ta dauki alqurni tayi rantsuwa ta rabu da ussein har abada alhalin ita a zuciyarta ba haka bane "
babu laifi bilkisu ta zauna lafiya kamar sauran lokutan baya ta cigaba da rayuwarta gudun kar qurani ya cita ,yanuwanta suka dan sake mata kadan haka mahaifiyarta tun tana gudun abinda zai je ya dawo har ta hakura ta sake janyota jikinta kullum da irin nasihar da take mata "bilkisu ki zama mutuniyar kirki ba wai baa sonki bane yasa kika ga anayi miki duk abinda aka miki ana sonki ne yasa ake gudar miki wahala ,auren wannan yaron wahala zai zame miki arayuwarki , bakya ganin sauran yanuwanki ?kowa na cikin jin dadi me yasa sai ke kadai ce zaki zabar wa kanki wahala? "
tace "kiyi hakuri mumy ina tsananin son ussein amman zanyi iya kokarin na cire sonshi araina "ko kunyi imole ne ?hjy rahma ta tmbyeta ."tayi shiru tana kallonta" baku ta'ba shan jinin juna ba ?ta girgiza mata kai alamun a'a to ko ya ta'ba kwanciya dake ne ina nufin sex ?shiru tayi kawai ta kasa bata amsa tmbyrta "idan ya ta'ba kwanciya dake ne ki fad'a min nan ma shiru tayi kawai "karki manta Kiyi rantsuwa da alqurni akan zaki rabu dashi ta gyada mata kai "idan baki son mubarak naji na hakura amman ki kawo min wani banda wannan yaron dan banason shi daga nan ta zarce da nasiha na kwantar da hankali tana nuna mata rabuwa da ussein shine alkhairi arayuwarta wanda alokacin mgnrta na shiga ta kunne na hagunta ne yana bin ta dama ."
wannan sakewar yasa ta samu damar turawa ussein sako da duk wayar data shigo hannunta byn ta tura text sai ta goge haka haka dai har ta shirya barin gidan da yammacin ranar laraba ta fice daga gidan babu wanda ya sani sai lalubo wa sukayi bata gidan" abun bakinciki tana zuwa gidan nan da hassana ta soma cin karo lokacin ta dawo gida aurenta ya mutu "Ke tsaya ta daka mata tsawa me ya kawoki gidan matsiyata ?tace dan Allah Kiyi hakuri nazo neman ussein ne "ussein din kanin ubanki ne da kikazo nemansa ? yanzu har kin manta irin azabar daaka gana masa akanki ?"
"na sani amman Kiyi hakuri ta marairaice mata ta raba ta gefenta zata shigo tace "kina hauka ne ta kara buga mata tsawa wallahi kika shiga gidan nan da kaina zan fito dake na miki dukan mutuwa kuma bazan bari kiga ussein din ba har sai na danganaki da matsiyatan iyayenki masu kiran wasu matsiyata alhalin sune matsiyata , dan masu arziki basa yin abinda sukayi duk yadda akayi arzikin ma daga sama aka samu zaazo a ishe mutune "pata pata tayi mata batare da sanin hjy ba sannan ta korarta ."
bangaren hjy rahma taji shiru shiru bilkisu bata fito ba ta nufi dakinta sai dai wayam tagani babu kowa ta duba bayi nan ma still the same nan da nan duk ta rude sai zufa take fitarwa nan fa ta soma kiran yaranta tana tsaye sai ga aisha da mijinta haka ma sajida cikin tashin hankali aka kira abubakar da mahamud har sulaiman har khadija jugun jugun sukai kafin daga bisani suka fito zuwa nemanta har 12 :00 na dare ba labarinta babansu yace kowa ya tafi kawai makwancinsa har zuwa gobe aga abinda allah zai yi ."
daga gidan nan bilkisu ta rasa inda zata domin dai tasan idan ta koma gida azaba zata sha duk yadda zata fad'a cewar bata hadu da ussein ba bazasu yarda ba dan haka ta wuce gidan kawarta farida daman su basa tare da mahaifiyarsu , mahaifinsu ne kuma bai cika zaman gida ba kasancewarsa jamin tsaro in takaice miki kwana da kwanaki ana neman bilkisu baa ganta ba yayinda ussein yake gida abunsa idan kinga ya fita to zashi area ne kuma bini bini ya dawo gida ".
muna zaune aka zo nemanta basu ganta ba suka wuce intakaice miki kullum sai sun shigo unguwr nan sai dai basa ganinta sai dai su ganshi shi kadai duk inda suka je nemanta bataje ba duk ahalinta sun rude mazan kuwa sun bazu nemanta abu kamar wasa har sati baa ganta ba abubakar ya kai report police station duk hankalinsu ya tashi haka zalika ussein shima bai zauna ba duk inda yasan zataje yaje bai ganta ba kullum wayarsa tana hannunsa km a kunne koda zata nemesa duk ya rude ya rasa inda zai sa kansa ."
kowa a gidansu bilkisu kuka yake daga bangaren
yan dakinsu har sauran bangarorin dan kansu a hade yake kuma suna qaunar juna ,duk sun rikice sun baza cigiyarta koina kafofin sadarwa amman babu wanda yace ya ganta dan haka suka sa akayi arresting din ussein a tunaninsu ya boyeta sati daya yana tsare ana gana masa azaba har a underground aka saka shi , ranar daya cika sati biyu akabari muka gansa ,koda aka zube magana sune basu da gsky amman kudi yasa aka bamu rashin gsky muka dauka muna bada hakuri akazo dashi unguwar nan sarka hannu da kafa Kmr wani barawo aka bincika gidanmu daki daki lungu lungu baa ganta ba haka dakunan abokansa da dakinsa duk inda aka san yana zuwa sai da akaje dashi amman baa ganta ba aka sake dawo dashi station dokoki aka kafa mana .
daya daga cikin police tace tasan koina bilkisu take zata nemeshi dan haka da zarar ta kirasa ya tabbatar sun hadu ya kawota a haka aka bar maganar muka dawo gida wanda tsanar bilkisu ya sake girma a zukanta yan'uwansa hatta gali alokacin ya fadi maganganu marasa dadi akanta wanda shine har yau baya qaunrku da mahaifiyarku amman ita hjy tana sonta dan tayi kuka rashin ganinta da baayi ba ."
Kullum hjy tana cikin zullumi da addauar allah ya bayyana bilkisu wallahi hjy tana matukar qaunar bilkisu sam bata ganin laifinta komai zaa fad'a akanta bata gani , cikin ikon allah sai gashi ta nemi useein da number farida ya tmbyrta inda take ta fad'a masa bai bata lokaci ba ya nufi inda take yana isa sai da yayi mata mari masu kyau har biyu cikin tashin hankali yaja hannunta daga can gidan nan ya zarceto daita muna zaune sai gashi ya shigo daita ."
hjy duk tafi kowa jin dadi ta rungumeta ajikinta tana kuka mikewa tayi tace muje police station
Muna fitowa ta nemi limamin masalacin unguwar nan tai masa bayanin komai shima kuma ya fahimci akwai matsala duba da yawon zuwan da yanuwanta suke muna isa aka kira yan'uwanta ai a haukace suka shigo sabeer yayi kan ussein "kace bakasan inda take ba ? sukayar da kansa yayi dan rasa me zaice ."
liman da police suka tsaidasu suna kwantar masu da hankali amman suka kasa aiwatar da hakan suka rufeshi da duka hjy ta shiga tsakaninsu tana karesa tana kiran sai dai ku hada dani allah ya isa bata yafe ba ,ita kuwa bilkisu kuka take sosai tana fad'a masu bashi da laifi hasalima tunda ta bar gida bata hadu dashi ba sai yau cikin fushi aisha tace "ya lalata miki ingantacciyar rayuwar da iyayenmu suka baki ya maidake yar yawo kororo "yayi miki ciki nasa aka cire miki amman duk ba laifi bane ? "ko dan kinga an rufa miki asiri sai lokacin hjy rahma tasan da wannan maganar wanda hakan ya sake tunzurata da kyar dai da nasiha suka amshi diyarsu nasiha sosai liman yayi masu yace su jajurce da addua sannan muka wuce da ussein ."
"ai ranar ashe ruwan zafin uwar ta tafasa ta
kwarawa bilkisu a gabanta wanda yasa sai data suma a qalla sai da tayi kwana ta yini bata cikin haiyacinta sosai mahaifinta ya nuna bacin ransa akan abinda aka mata ,sai da tayi sati biyu tana jinya sannan ta dawo daidai mahaifinta abun yafi karfinsa addua kawai yake allah yaye mata wannan masifa data daurawa kanta , amman uwar izaya da maseefa kawai tasa gaba ."
"yadda ake mata azaba haka zuciyarta take sake tunzura , dan zuciyarta da idanunta sun bushe basa ji kuma basa gani ,ta manta matsayinta babu ruwanta da kowa acikin gidansu ko ince miki ta tsani kowa km har lokacin bata cire ussein aranta ba duk lokacin datayi raayin ganinsa kawai fitowa take taje su hadu ta koma gida randa dare yayi mata kuma ta kwana a wajensa shima dai mutane suna cewa baya jin mgn wanda ni nasan so ne da tausayin bilkisu ke hanashi juya mata baya ."
Kwatsam sai ga bilkisu da wani cikin wata biyu cikin na uku ta fahimci ciki gareta alokacin shekararta shakwas cikin ta shatara hankalinsu ya tashi suka zo min da maganar ranar har da kuka nayi dan bakinciki nayi kuka kamar me cikin kuka tace zasu zubar nace a'a ta haifa sai ta bani tunda ni tun haihuwar sadam ban sake samun wani cikin ba shima sadam din da kyar na samesa kuka take tana cewa na taimaketa a zubar da cikin naki yarda
ranar tana komawa gida akasa sabeer yayi mata dukan fitar da tayi wanda yayi sanadiyyar fitar cikin alokacin na bawa ussein shawarar ya tura neman aurenta, hakan ta kasance abban sadam da kanin hjy suka je sai akace masu makaranta zatayi ba yanzu zaa aurar daita ba suka dawo suka fadawa ussein ya sameni da mgnr nace kar ya hakura ya sake turawa haka dai byn wani lokaci suka sake zuwa sai mahaifinta yace zai yi mgn da yan'uwansa duk abinda ake ciki zasuji daya samesu suka ce basu yarda ba daman shima bawai yana son aurenta da ussein din bane ."
Bayan sun koma akaro na uku ya turasu wajen yan'uwansa nan suka iske wani sabon tashin hankali domin cewa sukayi muddin yana son aurenta a wannan lokacin zai biya duk abinda aka kashe mata tun daga primary har secondary idan sun amince bisimillah ga list nan aka mika masu duk wani abu da suka kashe akanta jiki a sanyaye suka dawo suka miko min a tsorace na gama karantawa domin ko gidan nan da gidan bread muka saka a kasuwa bazai kai kudin da suka rubuta ba abban sadam ya numfasa yace "ki fadawa ussein ya hakura da yarinyar nan mutanen nan basu da mutunci km ko ya auri yarinyar nan wahala zai sha dan tafi karfin aurensa ni kaina na yarda da hakan kawai dai ayi auren ne dan kar suyita saduwa da juna suna ciki shima ussein koda ya samu labari yace ya hakura dan ina yaga million ashirin da biyar ."?
Haka dai suka cigaba da rayuwa duk sanda ta fita idan ta koma sai anyi mata duka tare da zagin tana warin maz gbdy kamanita ya canza ta fita haiyacinta tayi firi firi ta zuke ta rame babbar yayarsu a gabdaya gidan wacce uwar gidan rafi'u giwa ta haifa hjy rabi ta samu yanuwan babansu har ma da baban akan abar bilkisu hakan nan kar rabo yaje ya kashe mutane gabadaya yanuwan mahaifinsu suka ki yarda kuka ta saka masu ta zayyane masu abubuwan da basu sani ba akan bilkisu da ussein tunda sukaji ussein har ciki ya ta'ba mata suka zubar da makamansu , suka ce tunda taji ta gani abarta ta auresa tunda basu zasu zauna mata dashi ba shi dai mahaifinta bai uffan ba ."
tun daga wannan lokacin da yan'uwanta da suke daki daya da mahaifiyarta suka ji hukuncin daaka yanke akan bilkisu suka shiga gana mata azaba iri iri batare da sanin kowa ba aka dawo rikonta tamkar yar aikin gidansu yadda zakiga yan aikin gidansu na yawo haka ta dawo tana yawo babu shiga mai kyau babu komai amman hakan bai sa qaunar mahaifinku ta ragu acikin zuciyarta ba ."
aka saka ranar sati biyu kacal ana sauran sati daurin aure hjy rahma da ya'yanta kaf suka saka bilkisu a tsakiyarsu "duk ranar datasa kafa ta bar gidan zuwa gidan ussein amatsayin matarsa tasan cewar ta fita kenan har abada karta dawo gidan garesu ta nemi wani gidan ,ta nemi wata uwar ta nemi wani uban ,ta nemi wasu yanuwan ,fasa auren daidai yake da bin umarninsu ,amman zuciyar bilkisu bata girgiza ba ta cigaba da shirin aurenta dan Allaha allah take ta bar gidan ta huta acikin satin muka kai dan abinda muka hada na lefe wanda kusan hjy ce tayi komai wallahi in takaice miki maryama wulakanci har da wankan ruwan sanyi akayi mana byn an watsa mana abinda muka mai ."
Ranar daurin aure babu mutun daya daya zo daga cikin ahlinta da wanda suke uwa daya uba daya da wadan da suke yan uba haka zalika mahaifinta bai je ba dan hjy rahma tace muddin yaje ita kuma zata bar masa gidansa kannen mahaifinta mutun uku ne suka je alhj saidu ,Alhaji umar ,Alhaji kaberu ana gama daurin aure aka nemesu aka rasa ,bayan an daura auren hjy rahma ta kira bilkisu ta tsinewa aure babu irin mummunar adduar da bayi ba, allah ya hadata da damuwa allah yasa ussein ya gallaza mata ya korota ,kar allah ya bata haihuwa dashi idan km ta haihu allah ya bata ya'yan da zasu dameta, idan basu dameta ba allah yasa suyi ta mutuwa a duk sanda ta haifesu , bilkisu tayita kuka tana jin Kmr ba hjy rahma bace ta haifeta dan lokacin da take fad'a min cewa tayi ita da uwarta har abada ta yafeta sai dai na fada mata baa yafe iyaye komai abinda suka aikata gareka."
lokacin da zaa kawo bilkisu gidan mahaifinku babu wanda ya rakota saboda ta auri talaka daga ita sai mahaifinku suka baro gidansu zuwa rubabben dakinsa inji cewar hjy rahma dan wulakancin da sukai mana yasa babu wanda je dauko amarya .
babu abinda iyayenta sukai mata na kayan dakin kuma har yau yan'uwanta na jini babu wanda yasan inda take sun dai san tana zaune acikin lagos din nan amman a ina take basu sani ba babu wanda ya ta'ba zuwa ."
Kusan bakin hjy rahma yayi tasiri akan bilkisu dan sai datayi shekara uku tare da ussein batare da tasamu ciki ba har aka auro salma bata samu ciki ba ussein bai bawa mara d'a kunya ba dan sosai ya dawo da shaye shayensa lokacin data masa mgn akan alkwarin da yayi mata na dainawa yace" yaushe sukayi haka ?sai byn da salma ta haifi ali sannan kwatsam sai ga ciki bilkisu ta samu har lokacin da tayi haihuwar fari tace abarta a gidan mijinta
ni nasan da wani mai arziki ta aura ko bata je ba dole zaazo a dauketa ,babu wanda yazo dan lokacin mahaifinku da kanshi yaje ya sheida masu ta haihu intakaice miki korar kare aka masa wai yazo rokon kudi shiyasa duk lokacin da mahaifinku ya bata mata rai sai dai ni naji mata haushi ita kuma tayi kuka ta hakura dan bata san inda zata dosa ba mutane gidan nan gbdy sun daukenta sha sha wai ta tare a gindin miji to idan tace ma ta gaji ina zata ?
yau da'ace tayi saar uwa da tun tuni ta koma gareta domin tana neman taimakonta amman no way domin zamanta a gidan ussein shine gatanta kinga ta rasa gatanta shiyasa a kullum take ganin bata da gatan daya wuce ussein daku yayanta komai yayi mata take hakuri wanda kusan hakan yake cikin dalilin da yasa salma da hassana suke cin kashi akanta ta sha wahala sosai acikin yanuwan ussein bayan an haifi habib rashin Lfy ya kama hjy haka ta dauko hannun bilkisu tasa a tafin hannuna tace na rike mata amanar bilkisu kar na bari tayi kuka idan ussein yasata kuka na tabbatar na wanke mata zuciya sannan ta qara da cewa byn ta mutu bilkisu ta dawo bangarenta ta cigaba da rayuwa acikisa nace ta tara yayanta ta fad'a agabansu hakan kuwa akayi abun bai masu dadi ba amman haka suka yi hakuri kwana uku tsakani tace ga garinku ."
Bilkisu tayi kuka kamar zata bita domin a gasky ita akayiwa mutuwa dan kusan nauyinta akan hjy yake itace komai nata bare Ke da kika ci sunan mahaifiyarta komai tasamu kece da bilkisu ne shekarar hajiya daya da rasuwa rashin lafiya ya kama mahaifinki koda aka dubashi ciwon sigari ne ya kamashi har yayi masa illa bilkisu bata gujesa ba itace komai nashi ,ita Ke kaisa asibiti gwanati ga ciwonsa na bukatar kudi amman babu ke babu irin wahalar da batayi ba har wankau tayi dan ta rufawa kanta asiri cikin wannan halin rashin lafiya aka samu cikin habib har aka haifesa mahaifinku bashi da lafiya ranar da habib ya cika shekara daya a duniya Allah ya dauki ran mahaifinku ,yanzu shekaru ashirin da uku kenan rabonta da yan'uwanta da iyayenta kuma har zuwa wannan lokacin babu mutun daya daya nemi inda take to me zai sa ku ku damu da inda suke ?
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 19
A matukar zuciye ya sauke duka hannuwansa yana huci sai dai har lokacin kwayar idanunshi na kan fuskar baban gali yana masa wani irin mugun kallo mai tattare da bakinciki lokaci d'aya kuma yana ta qoqarin danne fushinsa dan baya son 'bacin ran mahaifiyarsa ."
baba gali ya sakar masa murmushin mugunta sannan ya kalli aunty hassana da aunty salma "kuga wannan tantirin mara mutuncin yaron wai ni zai kai hannunsa jikinata saboda nace zasu bar gidan nan kamar da kudin ubansa ko da kudin uwarsa aka gina gidan nan da zai wani d'aga hankalinsa dan Allah ku kalli Irin kallon da yake min nasan yana jin kamar ya kasheni ne ."ya qarasa maganar yana dariya ,"
Murmushin jin dadi aunty hassana tayi itama "ai kuwa bai isa ya kasheka ba sai dai ya kashe uwarsa ko yaje ya kashe wad'an can marasa mutuncin dangin uwarsa ba amman mu nan munfi karfin d'an kutumar uba, shegen gora mai falla fallan kunnawa , an nace mana an zo an haifa mana irin jaraba kuma wallahi sai Kun bar gidan nan matsawar bazaku daina mana rashin mutunci ba ."
cike da raunin zuciya habib yace "mahaukatan banza kawai da basu san ciwon kansu ba "
"mu kake cewa mahaukata ?eh !lallai yaron nan wuyanka ya isa yanka ,amman ka sani bamu ne mahaukata ba ga mahaukaciya nan a gabanka kana kallo wannan wannan itace mental itace mahaukaciya da ka kiramu dashi aunty hassana ta fad'a tana nuna gefen kanta ."
"Hassana !" ya kira sunanta a matukar hassale
Aunty hassana tayi saurin zaro idanuwanta waje tana duban d'anuwanta cike da mamakin habib "yes abinda kunnuwanki suka ji na fad'a kenan dan haka ki ma daina mamaki zan ma iya fad'ar abinda yafi haka " mutun takin me zan tsaya yi tunda kin kasa mutunta kanki ?"
ta maida hankalinta da idanunta kanshi sosai tana nazarin mgrsa sa sai daya samawar jikinsa natsuwa sannan ya cigaba da zaro magana "Ki kalli aunty tsab ki gani Kinsan dasu wa maganata ta dace ,ku din dai kune mahaukata kuma bazan ta'ba sauya maganata ba."
Hawaye ne yake zubowa daga idanun aunty gashi magana take son yi dan ta basu hakuri sannan ta tsawatarwa habib amman ta qasa bud'e bakinta bare ta sarrafa harshenta a wannan lokacin ita kanta taga ya dace ta koma cikin 'yanuwa cikin asalin ta amman kuma idan ta tuna irin rayuwar datayi har ta kawo wannan matsayin sai taga komawar nata bashi da wata amfani me zata cewa alhj rafi'u giwa da mahaifiyarta wacce tafi kowa d'aukar zafi akan kowa wacce ta gindaya mata sharadin cewar ta manta daita ta manta da kowa nata tunda ta zabi auren ussein ?".
"gidan nan kowa yasan gidan kakanmu ne wanda ya haifi mahaifinmu yadda kuke taqamar kuna da iko akan gidan nan haka muma ya'yan ussein muke da iko da gidan nan matsawar zamu zauna acikin gidan nan dan dole mahaifiyarmu ta zauna acikinsa ."
" Ke ! hassana da kike cewa a dole mu bar gidan nan kisani bamu ya kamata mu bar gidan nan ba ke da ya'yanki yafi dace wa ku bar gidan nan dan da gidan miji mace take taqama ba da gidan uba ba , aunty a gidan mijinta take zaune Ke fa ? da har yanzu Ke da ya'yanki baku san garin ubansu ba bare su san dangin ubansu ,ki fara zuwa ki kai ya'yanki su san dangin ubansu tukun kizo ki kori wad'an da su muhalinsu suke ."
Cike da sanyin jiki maryama ta dinga jan gwiwowinta har ta qarasa gabansu aunty hassana jikinta na wani irin rawa Kafin tai kai ga yin mgn taji aunty hassana ta hau surfa mata maseefa "dan ubanki yau dai karki kuskura ki bamu hakuri , shegiya yarinyar munafukar Allah taala kin wani marairaice fuska kamar ta kirki zaki bawa mutane hakurin gulma wallahi yau shine zamanku na karshe acikin gidan nan sai kun bar mana gidanmu ,gara ma tunda wuri Ki san yadda zaki d'auke wnn uwar taki da wannan shegen kannin naki mai falla fallan kunnuwa Kmr na fir'una ku bar mana gidanmu mu huta da jaraba sanda ussein yana raye bai barmu mun huta ba sannan bai tsinana mana komai ba sai ruwan shaye shaye da d'auko mana magana wanda sanadiyyar haka ya kwaso mana wannan munafukar uwar taku gashi ya mutu ya barmu da mugun iri ."
"Kuka maryama ta fashe dashi hade da sake durkusawa a wajen batare da tasan abinda zata fada ba, tana mai bakincikin irin kalar rayuwar da mahaifinta yayi a sanda yake raye, gashi ya bar duniyar amma basu huta ba , wannan wace irin rayuwa ce ? me yasa wasu yanuwa suke yin haka ? "tasani da ubansu mai arziki ne da duk abinda yayi babu mai tuna masu bare har a zagesu dashi ."
tsaki baba gali yaja yana cewa " Munafukar banxa sai anyi magana kisa mutane a gaba kina kuka, da ubannaku bai shaye shaye ba zaa fada? daya zauna da mutane lpy zaa ki fada ?kullum yana cikin d'auko mana magana gashi ya mutu ya bar iri an iya tujara iya tujara sauran shaye shaye .."
"Allah bazai sa ba ,baba ka daina masa mugun fata "me ya saura yaro ya zama dan daba ai sauran shaye shaye, habib zai yi magana maryama tayi saurin dakatar dashi tana cewa "walalhi karka sake cewa komai ai ga irin abinda ka haifar ko ?"ni dai na fada maku maza ku san ynd zaku yi ku bar mana gidanmu tunda gdn bana ubanku bane,"
maryama da tarin qunar zuciya da qunar rai take zubar da hawaye tafi karfin minti goma a durkushe sai daga baya ta koma inda tabar aunty ta durkusa kusa daita hawaye na zuba a idanunta Itama aunty hawayene take zubarwa a nata idanun tana jin ciwon abinda habib yake duk da tasan gsky yake fad'a masu amman bata só yana fadar duk abinda yazo bakinsu dan kome zai faru bazasu ta'ba sonta ba har yau tarasa me tayi masu mai zafi a duniya da suka kasa yafe mata sannan suka kasa danne tsanarsu akanta da yaranta ."
Habib ya kalli aunty ya kalli maryama itama duk kuka suke maryama kam har da shesheka tana rarrashin aunty " ku sani ku daina wulakantamu na kyale , kusani nadamarku ta kusan zuwa a nan kusa kuma munafurcinku ya kusan qarewa domin bazan sake yarda da iskancinku dan kuwa kun bari d'an zaki ya girma yayi girman da zai iya kasheku d'aya byn d'aya ,gidan nan kuma babu mai korarmu acikinsa sai dai a d'aga sa d'ungurungun dinsa a sakashi a kasuwa a siyar a bawa kowa hakinsa kowa ya kama gabansa"
"Ai kuwa baka isa ba wannan gidan ubanmu ne kai har ubanka ya gama iskancinsa ya koma ga Allah cima kwance ne bai da gidan da zaka yi wannan taqamar da kake yi "kai da ba cima kwance bane sannan bakayi iskancin ba ina naka gidan daka gida yake ? "sannan .."
"habib dan girman Allah .." saurin d'aga wa maryama hannu yayi ta hanyar dakatar daita " ki barni dasu heartbeat wallahi kowa sai na bashi size dinsa yau idan sunce basu da mutunci zan nuna masu ni d'an zamani ne , ya d'an tsaya yana kallonsu d'aya byn d'aya ,nan take ya hango tsananin tsoronsa da shakkarsa acikin kwayar idanunsu "oya kuna iya wucewa ku bar mu cigaba da rayuwarmu ko sai na fitar daku d'aya byn d'aya?".
A yadda suke kallonsa sun fahimci zai iya jansu ya fitar dasu kmr yadda ya fad'a dan haka aunty hassana ta kalli aunty "sai ki daina kukan munafurci tunda burinki ya cika kin haifa mana maseefa amman in sha allahu maseefar akanki zai qare tunda ya fara zama d'an daba tana gama fadar haka ta fice daga d'akin tana zage zage
aunty tayi saurin runtse idanunta tana jin zafin kalmar data danganta mata d'a dashi , itama aunty salma tace "shegu a haka zaku qare jiya iya yau babu cigaba ta nufi hanyar fita " da sauri habib yace "Ke ina naki cigaban da kika samu yake ? "Ke da ko sallah bakya yi , qazama mara sallah mai dotti kawai kije ki gyara tsakaninki da ubangijinki zai fiyye miki sauki akan shiga rayuwar wasu ."
shi kam baba gali cewa yayi "bilkisu Ina tarbiyar taki ?yau a gaban idanunki d'anki yake nuna min iyakata "to sai me dan na nuna maka iyakarka a gaban idanunta ? "kai da bakaji tsoron gaban idanunmu kake nuna rashin qaunar mahaifiyarta ba kiri kiri kake zaginta agaban idanunmu akwai abinda yafi wannan ciwo ? wallahi idan bakasani ba kasani yanzu abinda kukayi mata a da tayi hakuri ta shanye yanzu ta haifi d'an da zai kwatar mata 'yanci zan goge wannan tarihin idan ka cigaba da tsayuwa zafin jinina zai iya sa na d'auki takobin can na file maka kai dashi ko na raba katon kan nan naka gida hud'u idan yaso nima akasheni salin alin baba gali ya fice batare da ya sake cewa uffan ba."
Yana fita habib ya qaraso inda aunty da maryama suke durkushe suna kuka "cike da girmamawa yace "ku daina kuka in sha allahu ku daina kuka acikin gidan nan , kun daina damuwa matsawar ina raye zan tsaya maku , zan kula daku da zarar na gama karatu zan ...."bana son jin komai daga bakinka habib na fahimci kana bukatar na bar muku gidan nan shiyasa ka kirkiro abinda za'a koreni daga cikinsa tana gama fad'ar haka bata tsaya jin abinda zai ce ba ta mike ta shiga d'akinta ta d'auko mayafinta kawai ta fito zata fice ta bar masu gidan ."
Atare maryamah da habib suka sha gabanta cikin tsananin tashin hankali "haba aunty ya zaki mana haka ?kiyi hakuri aunty hakika habib bai kyauta ba amman karki tafi ki barmu ."maryama dan'uwanki baya bukatata acikin gidan nan yana bukatar na tafi na bar masa filin gidan nan ya cigaba da rayuwa ta qarasa maganar tana zubar da hawaye ta tabi gefen maryama zata raba ta wuce ."
habib ya riko mata hannu "kiyi hakuri aunty ki fad'a min abinda kike bukata nayi miki alkwarin wallahi zanyi kisani idan kika bar gidan nan bashi da wani amfani a wajenmu "yana da amfani mana tunda gashi kayi son ranka kasa an zageni anci mutuncina anci na iyayena ai gara na kama gabana tunda zamana acikinsa babu abinda yake haifa min sai damuwa da bacin rai ".
Kuka ya kufce ma maryama ta d'an rufe fuskarta da tafukan hannuwanta saboda tuttukin da zuciyarta Ke yi "kai ma kasan abinda kayi ba daidai bane har ka iya cire hannu zaka doki baba gali wallahi baka kyauta ba tunda kasan halinsu to meye amfani tsayawa kana fad'a yana fad'a "ki fahimci wani abu heartbeat wad'an nan mutane basa qaunarmu ,babu abinda Ke cikin zukatansu sai tsanar mu " tunda mun san halinsu sai mu kiyaye abinda zai kawo sa'bani dasu shima kukan yake yi "suna nuna mana bambamci akan ya'yansu ,suna quntata mana suna da fuskar gazawa garemu musaman akan ya'yansu yanzu laifin me kikayi ma aunty salma ta shigo tana zaginki ?"maryama bata sake cewa komai ba illa ta cigaba da kukanta haka ma aunty batayi magana ba illa qoqarin zare hannunta da take cikin nashi ."
"na tuba aunty bazan sake ba ki fad'a min abinda kike so ,nayi miki alkwarin bazan sake ba ya fad'a yana zubar da hawaye itama ta goge hawayen dake zuba akan kuncinta ta cigaba da mgn "daga yau babu ruwanka da kowa acikin gidan nan duk abinda zasuyi ko zasu fad'a akanmu ka kawo ido kasa masu , kai ba zagi ko dukana zasuyi babu ruwanka a rashin yace ba dai duka ba amman a zahiri yace "to aunty an gama ."wallahi abinda kayi yau din nan ba irin tarbiyar daaka bamu bace "in sha allahu bazan sake ba heartbeat ki bata hakuri bazan sake ba kamo hannun aunty maryama tayi suka koma kan kujera mai zaman mutun uku da duk ashon jiki ya batattake suka zaunar daita tare da sakata a tsakiyarsu suna bata hakuri ."
Kamar yadda mlm yahuza ya sanarwa nafisa byn sallahr ishai zai zo sai ga yaro yana sallama da maryama lokacin suna zaune a falon aunty ta dubeta amman ita ko ajikinta sakon da yaro ya fad'a aunty tace "maryama bakiji bane ?ta d'an dubeta ta share yaron ya tsaya yana jiran abinda zaace "to sai ki tashi kije "ina kenan aunty?"bakaji ana sallama daita bane "gsky babu inda zata ban san dalilin da yasa da mutun yazo nemanta ba sai ki bata damar fita baki san ko waye ba mazan da duk 'yan iska ne da zarar sun fara zuwa kamar abun arziki da zance aure ya shigo sai su gudu su barta ni gsky babu wanda zai sake zuwa ta fita ."
"Maryama tashi Kiyi maza kije ki dawo saboda ki samu ki d'an huta karki dade duk da nasan ba dad'ewar zakiyi ba ,ina dalili da zakace bazata ba kai zaka aureta ?ya marairaice murya "bani zan aureta ba amman at least aunty ki duba lamarin nan kawai suzo suna 'bata mata lokaci da dagula mata lissafi "Babu wani dagula lissafi a haka allah zai kawo mata wanda zai aureta ,ina son kasan wani abu habib duk cikin masu zuwa neman auren maryama babu mijinta acikinsu , duk lokacin da mijin yazo to babu makawa sai anyi domin babu mai aurenta matar wani kai yaro je kace gata nan zuwa yaron ya juya da sauri dan daman amsar da yake jira kenan zata fito ko kuwa bazata fito ba ."
maryama ta tashi ta shiga d'aki dan tasan ko waye yazo ta d'auki hijab dinta ta fito "amman dai ni aunty a wajena ba daidai bane ,ni fa kamar mahaifinta ne a matsayina na namiji acikin gidan nan amman me yasa sai a dinga nuna min iyakata acikin gidan nan , na fiku sanin halin mazan wannan zamani babu komai acikinsu sai tsabar yaudara ".
Aunty ta kallesa saboda yadda yake maganar tamkar wani babban mutun tace "wai har guda nawa kake habib ?" duka shabakwai gare fa kawai dan allah ya baka jikin girma "ni dai gsky ban yarda ta fita koina ba girgiza kai aunty tayi tana kallon yadda yake kamaninsa yake canzawa a kullum yana komawa na mahaifinsa tun ba yau ba kusan kowa yana fad'in kamanin nasu "gaskiya habib kar ka zama mai hana neman auren ."
tsayawa maryama tayi tana kallon fuskar habib daya had'eta tmkr ance masa idan ta fita guduwa zaa yi daita ,ahankali ta kira sunansa "after dad "
"Karki wani kirani da wannan sunan dan dani din ina da wannan matsayin da za'a dinga bin umarnina " ta qaraso ta zauna kusa dashi ta riko tafin hannunsa cikin nata tana kallonsa da idanuwanta da suka canza kalla "after dad me kake so dani ?"ta fad'a tana kallon yadda shima ya zuba mata ido yana kallonta ."
"Abinda nake so duk wanda yazo karki qara fita koina idan abinda ake miki acikin gidan nan baya damunki ni yana damuna ,sau nawa kina yi saurayi agidan nan a karshe ko ya gudu ko a kwace miki shi acikin gidan nan ?to ai duk ba mijinta acikinsu ne ,no no aunty akwai cutarwa aciki "to nufinka yanzu haka zata zauna babu mai zuwa wajenta ?"allah aunty dasu dinga 'bata mata lokaci gara ta zauna haka idan na girma na qare karatuna zan mata komai zan siya miki gida da mota itama heartbeat zan siya mata zan kai ku aikin haji ,kai har sojoji zan daukar maku escort duk inda zaku su dinga rakaku aunty da maryama basu san sanda murmushin jin dadi ya bayyana akan fuskarsu ba "shikenan after dad bazanje koina ba domin kai din tmkr uba ne a gareni "yauwa heartbeat sai yanzu naji hankalina ya kwanta muyi zamanmu ."
aunty ta kallesu ta girgiza kai "wallahi wannan ba rayuwa bace kin wani zauna ya tasaki gaba yana miki zakin baki ,wallahi ki daina biye masa Ke macece dole kina bukatar Kiyi aure shifa nan gaba kad'an zai ce zai yi aurensa dan wannan da son girman tsiya nasan .."no no aunty karki hadamu da heartbeat babu wani aure da zanyi na barta idan dole sai tayi aure ni zan kawo mata miji wanda zai dinga kwantar mata da hankali duk ranar da yayi gangancin ' bata mata rai na zage naci ubansa ".
"Lah lah lallai habib abun naka babba ne "allah aunty sai ma ya cika qaidodina sannnan "wannan ai gara kuje kuyi auren kotu ku huta maryama tai murmushi tana jin dadin yadda dan'uwanta ke tsananin qaunarta "babu kotun da zamu amman dole a kular min da heartbeat ko kuwa a tashi mutun aiki "uhm kaga tashina ta mike tsaye " bari naje na bawa baba gali da hassana hakuri na dawo ."
"haba aunty ai komai ya rigada ya wuce wani hakuri kuma zaki basu salon su samu damar ci miki mutunci "? A'a sai naje zaman lafiya yafi zaman dan sarki ina zan iya dasu gara dai naje ."Yauwa aunty kije ki basu hakuri wannan ai ba komai bane wata rana sai labari kai ma ya kamata ka bita kabasu hakuri wani irin kallo ya watsa mata yana cewa "allah kiyaye ai ni .."sai kuma yayi shiru sakamakon tuna alkwarin da yayiwa mahaifiyarsu ."
"ai babu abinda zai sa naje da habib sai ya qara dagula lissafi sunan wani police a isokoko ni na wuce sai na dawo "to aunty sai kin dawo tasa kai ta fice daga dakin ta barsu suka cigaba da hirarsu mai cike da kulawa da soyayya shi kam mlm yahuza tsawon mintuna nan duk yana tsaye yana jira Fitowar maryama ya duba agogon dake daure da taintsiyar hannunsa yaga lokaci ya tafi daman kuma yaron daya aika ya sheida masa komai dan haka a natse ya juya sai dai ya kudurce aransa zai dawo gobe."
Ahankali aunty take tafiya tana tunane tunane abinda zatace idan ta isa gaban baba gali a natse tayi sallama cikin bangaren nasu basu amsa mata sallamar ta ba dan haka taji gabanta ya shiga faduwa kafin ta kai ga yin wata magana taji aunty salma ta hau surfa mata maseefa kamar kullum "me ya kawo bangarenmu "ba komai bane hakuri nazo baku akan abinda habib yayi ,ya gama ci mana mutunci a gabanki shine dan munafurci kika kwaso jiki bayarwa , shegiyar munafuka kin wani marairaice fuska bayan kin gama zuga d'anki yayi mata walima ta uwa da uba zaki wani kwaso jiki to yanzu hakurin me kika zo bamu ?".
Numfashi aunty ta sauke ta samu waje ta zauna kusa da baba gali da ko kallon inda take bai yi ba a tun sanda ta shigo "kuyi hakuri gabadayanku in sha allahu nayi maku alkawarin wannan shine karo na farko da karshe da hakan zai faru ...."dakata bana son jin komai daga bakinki dan duk abinda zai fito daga cikinsa karya ne ni dai abinda nake buqata "ki dauki yayanki ku bar mana gidanmu tunda ussein yake raye bai tsina mana komai ba sai tujara gashi nan ya barwa dansa tsaraba har kamar ni wannan yaron zai dinga gasawa magana kuma a gabanki kina kallo yaron da ya kamata kiyita dukansa har sai kin kusan auna shi lahira amman kika zauna dan tsabar son ya'ya kina kallonsa yana surfa mana zagi ta uwa da uba ai wallahi bazai yuwu ba ."
Sake durkushewa tayi Kmr zatayi kuka batare da tasan abinda zata sake fad'a ba sai dai ita kanta a halin yanzu tana mai bakincikin hada zuria dasu tsaki aunty salma taja tana cewa "munafukar banza munafukar wofi sai anyi magana ki wani durkushewa mutane "ni dai ba wani tashin hankali nazo dominsa ba nazo ne dan na baku hakuri dan nasan danku bai kyauta ba "ni wannan yaron ba d'a bane domin kuwa d'ana bazai min haka ba hakuri aunty tayita basu da kyar baba gali yace komai ya wuce amman tajawa habib kunne aunty salma dai ce taki hakura ta mike tana masu sallama "sai da safenku allah kuma ya huci zuciyarku babu wanda ya kulata acikinsu har ta fice zaginta aunty salma take cikin tsananin tsana ."
Daga bangaren baba gali na aunty hassana ta shiga itama dai tujara tayi mata ta uwa da uba kaf danginta babu wanda ta bari bare iyayenta zuciyarta tayi nauyi kamar an d'aura mata dotse da kyar ta yunkura ta mike ta fito tana tafiya zuciyarta na kokawa. a inda aunty ta fita ta bar yaranta anan ta dawo ta samesu zaune suna hira "har kin dawo aunty ?suka had'a baki murmushi tayi tare da d'aga mata kai alamar" eh! my princess na dawo ".
"Yaya kuka qare fatan sun hakura "Eh to sun hakura my princess!ta fad'a zuciyarta cike da raunin kuka dan shi take bukatar yi a halin da take ciki shi kam habib bai ce uffan ba illa ya cigaba da sauraronsu"my princess Kinga dare yayi bamu samu girka komai a gidan nan ba ni yanzu ban san me zamu dan girka muci ba "wallahi aunty amman bari naje wajen Ummah watakilla bazamu rasa abinda zamu ci ba maryama ta fad'a idanun habib yana kanta "ko zaka raka ni ne? ta fad'a tare da miqewa..."Muje ! kawai abinda ya fad'a kenan maryama tayi murmushi "makalema kawai "kima ce bita zai zai ki huta gbdy muje suka jera ."
Suna fita suka had'u da yaya sadam ya fito daga side d'in din baba gali zai shiga side din ummah cike da farinciki habib ya qarasa suka gaisa! "A she rabon mu had'u ne yaya yasa heartbeat tace nayi mata rakiya ."ai ko baka fito ba yanzu nake shirin zuwa tambayarka a wajen aunty !Ya mika masa hannu ya kwana biyu ina fata dai komai lafiya? "Lafiya lau habib kawae aiki ne ya boye ni 2days ya karatu ?yace "alhamdulillah.!"
maryama ta bude baki da kyar ta gaishesa ya amsa mata cike da sakin fuska "Lafiya su aunty maryam"ji tayi kunya ya kamata da kirata aunty da yayi ! Ya gida da karatu ?Alhmdllh! ta fad'a cikin jin kunya"kema dazu nake tambayarki wajen Ummah take bani labari mai dadi lallai kin fita zakka acikin matan gidan nan kin tsaya kinyi karatunki yadda ya kamata allah yasa muji sakamakon mai kyau you're the best maryama duk nmj daya sameki a matsayin mata baqaramin dacewa yayi ba Allah yasa sawa karatu albarka dad'i maryama taji sosai dan duk cikin yanuwanta sadam ne kawai sai habib Ke mata fatan alkhairi idan wani abun farinciki ya sameta tace "na gode sosai yaya ."
Habib yace "a she dai yaya ka gane shiyasa sai na zaba mata na durje mata miji dan ita din ba kalar kowani nmj bace "kaga yaya karka kulashi mu je ciki mu qara gaisawa "wucewa sadam yayi side d'in Ummah maryama da habib na biye da shi sunata hiran duniya..."
Zama sukayi a parlour'n sadam ya fara kiran "Ummah Kina ciki ne? Eh! Ganin nan zuwa dan albarka har ka dawo ne? sadam yace" eh ! gashi na kawo miki maryamarki "ban gane ka kawo min maryama ba maryama da muke yini tare dan gulma zakace ka kawo min ita Bari dai nazo ganin nan fitowa ."
Bata wani bata lokaci ba ta fito cikin doguwar riga qaton tray ta aje a gaban sadam na fruits bismillah sannu da zuwa yau har da habib to duk sannuku "Ina yini "Habib yace " lafiya lau habib Ummah ta kalli sadam ta kalli maryama sai taga sun maseefar dacewa ina ma su kasance maaurata suna hirarsu gwanin ban shaaawa habib ya fahimci maryama kunyar sadam take ji sosai dan taki fad'ar abinda ya kawo su gashi shi yunwa yake ji ."
Maryama tace after dad ya kamata mu wuce dare nayi "a'a har zaku tafi kenan maryama to ai bakuci komai ba "karki damu Ummah "ban gane karta damu ba kinga nifa banason kunyar nan take wai ma wa Kike jin kunya anan umma ko yaya sadam ,?maryama tayi shiru tana mai sunkuyar da kanta qasa tana wasa da yatsun hannunta "kinga Ummah nan ya fad'a mata abinda ya kawosu "kai maryama amman shine zaki jashi ku wuce to kuci me idan kun wuce? allah ya kyauta wannan kunyar taki kaga habib bari nazo ta fad'a tana mikewa tsaye ta nufi kitchen ".
Bata wani bata lokaci ba ta dawo hannunta d'auke da wani madaidaicin kula cike da abinci sannan da wata leda cike da su cincin wanda tayiwa sadam ta miqa ma maryama tace gashi kai km habib ka rike kula " mungode Ummah !Suka fito maryama nayi masa mitar abinda yayi dariya kawai yayi yana cewa "ina ganin gara kawai ayi yar gida mu huta da samari masu mana patrol "kai dai kasani ni nasani ko gaskiya suna tafiya suna jan juna har suka qaraso falonsu habib ya zauna yana kiran "washhhh allah maryama ta cire hijab dinta ta ajiye akan kujera tace "habib bari na kira aunty kanshi kawai ya gyada mata ."
Ahankali ta shiga d'akin sai dai abinda yayi matukar daga mata hankali shine ganin mahaifiyarta kwance rigingine akan katifa hannunta rike da wani hoto tana kallon hoton hawaye na zuba daga idanunta tana tuna irin rayuwar dadin da tayi ada kafin shigowar ussein rayuwarta ,bata haskowa kanta irin rayuwar da take ba sai data hadu da ussein soyayyarta ta gurba tunaninta ."
yayinda maryama ke kallon mahaifiyarta da ita kadai ta rage mata a duniya yanzu a natse ta qara taku biyu domin son ganin hoton waye a hannunta take kallo tana kuka wasu mutane tagani guda biyu cikin shiga na alfarma suna cikin koshin lafiya da farinciki ko baa fada mata ba tasan hoton iyayenta take kallo cike da nadama lumshe idanunta tayi "iyaye ba abun wasa bane , aunty iyaye suna da kimar da darajan da bazaa iya mantasu ba ."
ahankali taji sautin muryarta tana fita cikin kuka "nayi kewarka baba , nayi kewarki mamana yanzu ku har yanzu bakuyi kewata ba ?yanzu ku baku yafe min ba ko nemeni ba? wallahi ina sonku nayi kewarku ,nayi kewar kowa da kowa ta fad'a tana mai daura hoto a saman qirjinta tana shafawa tana kuka.."
Ahankali maryama ta juya tana zubar da hawaye masu zafi ta koma falo ta zauna kusa da habib tana sheshekan kuka nan take ya birkice ya soma tambayarta "heartbeat me kuma ya fara ?kukan me kike yi ? Ina aunty ?yayi mata tmbyr ajere cikin tsananin tashin hankali tasa gefen rigarta ta goge hawayen "yau aunty ta tuna da iyayenta tana daki tana kallon hotonsu tana kuka ni nasan zuciyarta na cike da qaunarsu shiyasa kaga ina son ta koma garesu ."
"habib soyayyar iyaye da yanuwa baa wasa dasu wallahi a tsakaninsu soyayya ce mai karfi ka misalta hakan akanmu musan da qaddara amman an cuci aunty an yi sanadiyyar rabata da kowa nata ,ta bar iyayenta akan soyayya gashi ta rasa soyayya taki bin umarnin iyayenta gashi duniyar taki mata dadi maryama tana kuka habib na rarrashinta har kukan nata ya ragu adaidai lokacin da sukaji tahowar aunty tayi saurin share hawayenta tana cewa ".
karka nuna mata komai da sanyi jiki ta qaraso "kun samo abinda zaku dan ci ?eh mun samu har da cinci tô maza kuci ku kwanta tayi maganr cike da rauni aunty kizo muci tare "aa ku dai kuci ku koshi aa wallahi tare zamu ci habib ya mike ya kamo hannunta ya zaunar daita ya bude kula abinci yana cewa kai abincin nan zai yi dadi maryama ta dauko spoon ta dibi abinci zata kai bakin aunty habib yayi sauri ya kwace spoon "bani ni zan bata da kaina suka sa da dariya ya soma bata abinci abaki yana fada mata kalamai masu sanyi ."
"idan nayi kudi bazan yi nesa dake ba zan kasance tare dake ,dan allah aunty ki daina damuwa akan komai kinji ki dinga tunawa cewa kina damu mu din zamu zame miki farinciki a rayuwarki Wallahi sai mun sa kinyi alfahari damu ki cigaba da addau ga heartbeat nan kwanan nan zata fara bautar qasa yanzu ma ina mata processing yadda zaa dawo daita lagos né daga adamawa wannan farinciki ya rage tarin qunar da zuciyar aunty take ciki tace "allah yayi maku albarka yayiwa rayuwarku albarka in sha allahu bazaku dangwama haka ba allah zai saukaka maku rayuwa ,Allah nake roko ya daukaka min ku na yafe maku duk abinda kuka min da wanda nasani da wanda ban sani ba suna cin abinci suna debewa juna kewa ."
******
da misalin karfe 9:00 na washegarin ranar lahadi mr ata ya fito parlour'n mami ,duk jikinsa yayi sanyi har wata katuwar rama yayi daman ya lafiyar kura ?ba wani jikin kirki bane dashi kusantowar aurensa da maryam yasashi jin kmr ana fixgar ransa ,shiru ne ya ziyarci parlour'n yana tunane tunane yana jin kamar idan ya tafi france kar ya dawo domin a lissafinsa sauran kwanaki goma cif a daura masa aure da yarinyar daya tsana fiyye da komai arayuwarsa byn kmr mintina goma mami ta qaraso da kanta ta had'o masa abun kari , chips da soyayyen kwai da ruwan tea mai kauri , ta janyo qaramin table gabansa ta ajiye kana ta zauna kusa dashi ta tsura masa ido tana kallonsa batare datace komai ba ."
ya dauki cup din tea ya kai bakinsa ya kurbi kadan yana mai runtse idanunshi shiru har wasu mintuna suka shude yana zaune itama tana zaune tana kallonsa da kyar ya bude baki "sweetheart! "kaci abinci first before anything adamcy , sannan kar naji kayi magana kaci abinci kawai yaushe rabon ka sanyawa cikinka abinci bare a samu magani yayi aiki ajikinka ? ji yadda ka dawo acikin kwanaki uku kacal ka taimakeni kaci wani abu kanshi kawai ya iya d'aga mata batare da ya kalli inda abinci yake ba, saboda sam baya jin cikinsa zai iya amsar komai shima da zata taimakesa da tasa an fasa auren nan da yarinyar an hadashi da wata zai hakura da princess dinsa ya amshi koma wacece duk da zuciyarsa princess kawai take so da son gani numfashi ya dinga saukewa ."sweetheart dina me yasa kika manna min wannan auren haka?
" sweetheart zaki kasheni da kanki wallahi at least ki sake gara min dama koda na tsawon wata guda ne ."
"to me zan maka adamcy nah daya wuce haka ?
"me kake son nayi idan banyi maka haka ba ?
gani nayi kana neman hargitsa min kwakwaluwa da qarar da rayuwarka a banza "me kake tunani mutane zasu ce idan bakayi aure adaidai wannan lokacin ba ? wallahi zaka shiga zargin mutane ,mutun har mutun kamamme kamar ka ka zauna babu aure ko kana neman mata ne adamcy bansani ba da kake gudun aure ."
wani irin kallo yayi mata mai nuna mata bayayi "to idan bakayi me kake jira ?maryam yaruwarka ce fa "yanzu kai kafi son ka dauko min suruka daga waje alhalin ga wacce tasan darajata take sona nake sonta diyar danuwana yanzu idan an fasa auren nan me kake son na cewa mutane da yan'uwana ,dan Allah dan annabi in banda da rigima irin naka ba me ye laifin maryam ..?
"wani far yayi da idanu zuciyarsa na dokawa da numfashinsa da yayi kokarin d'aukewa yayi saurin dawowa dashi gangar jikinsa sannan yace "sweetheart ni bance tana da laifi ba amman ki duba lamarin da kyau tunda nace bana sonta ai sai a hakura kawai kowa ya kawo zabinsa . "kai rufe min baki ban son shirme banza, ka daina ganin ka had'a komai kana da kudi kayi tunani zaka iya juya ni ."Wannan aure sai anyi shi muddin ina raye ."
ya marairace muryarsa sosai tmkr mai shirin zubar da hawaye sannan yace "wai sweetheart me yasa kike ganin kmr wannan yarinyar ce kawai zata iya kulawa dake ? Allah sweetheart ki daina mata kallon haka saboda irinsu sune masu bawa dangi kunya wallahi duk lokacin da naji kince min itace zata san darajarki bakinciki nake ji kmr na kashe kaina saboda ni duk macen dana kawo miki dolenta ta soki tayi miki biyayya bama Ke ba sweetheart hatta yayyuna biyu din nan dolenta ta bisu lalacewar mace daga miji ne ni kuma bazan ta'ba bada wannan damar ba .. "
"Sauran kwanaki goma a daura maka aure da maryam a lissafina gobe ko jibi jirginka zai cale zuwa qasar france fatana allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya shahida ta gama shirya komai na aure fatan alkhairi da dawo da niyyar angeancewa lafiya and if you do anything stupidty I will del with you kai ma kasani ina sonka fiyye da tunaninka amman hakan baya hana idan kayi ba daidai ba naki hukuntaka tana qoqarin mikewa hisham ya shigo ya gaishe da mami cike da girmamawa sannan ya zauna kusa da ata daya runtse tsumammun idanunsa tun byn da mami ta soma magana "yaakayi mutumina ya karfin jikin hope you are getting better?"numfashi kawai ya sauke wanda Ke nuna masa alamun ya amsa hisham ya cigaba da magana "har yanzu sultan da fahad basu dawo da komai ba fa Kmr ma sun dauki abun matsayin shiririta tsabgogin gabansu kawai suke."
"ina sane da komai kai kasan bana canza maganata ina jiran na dawo daga france ne suna zaune suna hira mb ya shigo haka ma yaya Ibrahim ya shigo duba jikin mr ata tare da aunty abida har da yesmin wacce ta dane jikin mr ata haka ma yammatan gidan
d'aya byn daya suka dinga shigowa suna gaisheshi da kyar yake bude bakinsa yana amsa musu cikin rashin sakin fuska , cikin wasu mintuna aka cika gaban mr ata da kayan motsa baki , amman babu abinda yaci illa coffee daya dinga tsiyaya a cup yana kurba ahankali ahankali shima yana sha ne kawai saboda sabon da yayi dashi ."
Parlour'n ya dan rage mutane ya saura daga hisham sai ata nuzla da diyana har ma da mrym da nana hauwa'u suka shigo parlour'n bakinsu d'auke da sallama hisham na ganin nuzla ya saki fuskar ganin masoyi yarsa gbdy suka hada baki wajen yi ma mr ata ya jiki banda nuzla Kmr koda yaushe da kyar ya amsa masu hisham yana kallon fuskar nuzla yayinda nuzla taja ta tsaya daga gefe can ta jingina bayanta da bango ta rungume hannuwanta duka bisa kirjinta tare da tsura ma mr ata fararen idanunta tana kallonsa cike da matsanancin soyayyarsa yadda ko kallon mrym da zai aura bai yi ba abun yayi mata dadi sosai yadda bai son mrym abun na mata dadi har yana bata kwarin gwiwa dan tun daga ranar daaka saka ranar aurenau take jin haushinta sannan take cikin damuwa mai tsanani ."
ahankali ta bud'e bakinta tace "yaya sannu ya jiki banza yayi mata Kmr bai ji ba nan kuwa yaji sarai hisham yayi qasa da murya yace "ata ana maka sannu da jiki "naji !ya fad'a atakaice dan ya fahimci wani abu a attare daita ba tun yau ba yana hankalce da irin kallon da take masa a duk sanda zasu hadu tun a office din aunty shahida yaso yaci ubanta allah ya taimaketa "take gabanta ya shiga fad'uwa sbd fargaba dan ganin ko kallon inda take tsaye bai ba illa kur'ban ruwan coffee daya cigaba dayi kuma taji amsar daya bawa hisham kuma tasan sauran ma
sunji abinda ya fad'a ."
ahankali ta juya ta nufi kofar fita cikin bacin rai sannan sauran yanuwanta suka biyo bayanta "amman ai ya kamata ka amsawa gimbiyata ya sake yin mgn can qasa"gsky hisham baka da hankali km kana bani kunya yanzu kai da gaske sonta kake "?sosai ma kuwa ina sonta sai dai ita bata sona ..""what ?" Wallahi haka ta fad'a ai naso bikin a hadashi da naka amman ya zanyi tunda tace bata só na hakura amman nasan sonta ne zai kasheni "amman shine ka kyaleta baka ci ubanta ba?
aa babu wannan ai kai ma kasan yadda soyayya take ka duba yadda baka son mrym kake son yarinyar mafarkinka "ka daina kawo wannan misalin ni bana son wannan yarinyar ita ma kuma bata sona kaga akwai matsala wajen namu hadin ko ka fahimceni ."?
"Misali ina sonta to ya zama dole dan ubanta ta soni sannan misali da'ace tana sona nima bazan dinga jin tsanarta haka ba duk da nasan nawa rashin son ne babban matsala dan ita prentending ne kawai nasan babu macen da zata kalleni tace wai bata sona dama ne kawai bata samu ba ,ya fad'a yana jan tsaki ka kira min auta "me zata maka ?Kai dai kira min ita kawai yau yarinyar nan zataci ubanta da me tafika da zata ce bata sonka ?shiru hisham yayi yana kallonsa a she haka ata yake sonshi jiki a sanyaye ya dauki wayarsa ya kira nana hauwa'u cikin kankanin lokaci ta bayyana a falon "yaya gani "je kizo min da nuzla yanzu yanzu kafarta kafarki "okay yaya ta juya da sauri ."su kuma suka cigaba da tautaunawa ."
Bayan mintuna goma sai gasu sun shigo nana hauwa'u ta kama gabanta ta bar nuzla tsaye cike da fargaba ta dan saci kallon hisham dake zaune taga ya sakar mata murmushi ta kalli mr ata taga ya hade rai sai kafarsa daya yake girgizawa har kusan mintuna shabiyar tana tsaye sannan tace "yaya gani wai ..."da sauri ya dakata daita ta hanyar daga mata "waye wannan ?ya nuna mata hisham dake zaune "yaya hisham ".
"Very good meye a tsakaninku ?nothing ta bashi amsa atakaice ba hisham ba hatta mr ata sai daya dago tsumammun idanunshi ya tsura mata yana kallonta "kika ce nothing kenan baki san yana sonki ba ?nasani but na fad'a masa gaskiya ni bana son shi dan ..."enough ! bana bukatar jin maganarki ko wani abu kije ki fara shirin aurensa nan da kwanaki goma ." cikin firgici da tashin hankali ta shiga d'aga kafafunta zuwa inda yake zaune "me yasa yaya ?" dan Allah kayi hakuri karka min haka wallahi ni bana son shi a matukar tsawace yace "nace karki sake fad'ar wata magana anan , karki sake kula kowa acikin masu sonki shima wanda kike so ki kashe soyayyarsa acikin zuciyarki ki so wanda yake sonki .."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 20
jikinta na wani irin rawa ta k'araso ta durkushe a gabansa har bata san sanda ta d'aura hannuwanta duka bisa cinyoyinsa tana kallon cikin kwayar idanunsa da suka rikid'e suka canza kala a wulakance ya zame jikinsa yana mai kawar da fuskarsa gefen hisham dake zaune tmkr mutun mutumi yana kallonsu cike da matsanancin tashin hankali ,shi kuwa mr ata alamun baya son kallon fuskarta ne yasa shi maida idanunshi kan hisham ".
"dan allah dan Allah !! yaya adam kayi hakuri ta kai hanuta tana qoqarin juyo da fuskarsa gareta domin su fuskanci juna , zuciyarta na wani irin bugawa da karfin gaske take kallonsa haka ma hisham zuciyarsa ce take ta bugawa fiyye da kaida ya soma jin wani sauyi na daban a gabadaya ilahirin jikinsa wanda ke gauraye da tsantsar tashin hankali, shi kuwa mr ata mamakinta yasa gbdy ya qasa magana duk da maganar yake son yi .
Kwayar idanunta suka cicciko da ruwan hawaye muryarta a sarke tace "dan Allah yaya kayi hakuri karka bari wannan auren ya kasance domin zuciyata bazata iya d'aukar wannan nauyin ba, wata razananniyar tsawa ya buga mata wanda ya kamata ace ta tsorata ta dawo da hankalinta jikinta amman ina sai ma sake narkewa tayi a wajen zuciyarta babu tsoron komai acikinta , muryarsa a kausashe yace " tashi ki bar nan ki kuma fara shirinki kamar yadda na fad'a miki oya leave ."
"dan Allah ka saurareni yaya "ya girgiza mata kai yana cewa " I don't want to listing anything from you just leave now "dan allah yaya adam kayi hakuri ka saurareni akwai maganar da idan na fad'a maka nasan zaka fahimceni "ata dan Allah ka barta ta fad'i abinda ke zuciyarta Hisham yayi maganar yana qarewa jikin nuzla dake rawa tmkr mazari da kallo , yadda take cikin tashin hankali haka shima ya tsinci kanshi cikin tashin hankali mai tsanani har yana jin ma kamar ya cire mata nata damuwar ya qarawa kanshi "
Hisham yayi tsuru tsuru yana jira yaji abinda zata fad'a ,yayinda mr ata bai ce uffan ba ya yunkura ya mike tsaye ya kwashi wayoyinsa ya fara taka kafafunsa da kyar zai bar wajen kasancewar bai son yawon magiya bare irin nata dake hargitsa kwakwaluwa nuzla tayi saurin shan gabansa tana fad'in "yaya karka wuce ka bar zuciyata cikin maseefa tayi maganar cike da tausayawa ,bai yi mata magana ba ya cigaba da tafiya yana mata gargadi da hannunsa alamun ta shiga hankalinta , bata daddara ba ta sake shan gabansa dan gbdy zuciyarta ta rigada ta bushe babu abinda take qoqarin aikatawa face ta bayyana masa ciwon dake cikin zuciyarta ."
Ya tsaya kawai yana mata wani mugun kallo
yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa muryarta cike da rauni da buqatar atausaya mata ta fara magana "bazan iya jure ciwon rabuwa da wanda nake só na auri wanda kake só ba ta karasa mgnr tana rungumeshi ajikita tana kuka a matukar zuciye ya fixgeta daga jikinsa yana sake furzar da iske "are you out of your sense ?ni sa'anki ne da kike shiga gabana? " ko ina wasa dake ne da ina magana kina magana ? ya fad'a yana kawar da fuskarsa akanta domin dai zuciyarsa ta fara tausaya mata tausayawar da bata da wani amfani dan bazai ta'ba iya mata taimakon da take nema daga garesa ba ."
Hisham ya rasa meke faruwa atsakaninsu babu abinda zuciyarsa bata kissa masa ba a zaune da yake tmkr an dasashi irin kallon da take ata da rungumar da tayi masa ya fara gasgata zuciyarsa akan abinda bai niyyar yarda dashi ba yaso ya mike ya qarasa zuwa inda suke tsaye yasan ko akan me take masa magiya har da runguma amman hakan nan yaji gara ya cigaba da zama a inda yake zai fiyye masa alkhairi kuma bugu da qari yayi imani ata bazai ta'ba aikata komai ba face abinda yasan zai zamewa rayuwarsa farinciki he really trust him mutun ne shi mai kyakkyawar zuciya akanshi ."
Hawaye na gangaro mata bisa kuncinta yayinda magana ya fara fitowa daga bakinta "ina qaunar ka yaya ? bai yi mamakin jin fitowar hakan daga bakinta ba domin ya rigada ya gama karantata tsab "na sani sai akayi yaya ?ya fad'a yana kallonta yana jin kamar ya soma yar yarfa mata maruka ta dawo haiyacinta "dan Allah yaya karka ce min a'a ! a kowani hali zan kasance tare da kai " ta maimaita hkn a fili yafi sau goma tana mai kai hannu ta shafa kasumbar dake kwance a fuskarsa ji yayi kamar ta shafa masa garwashin wuta ,shi fa duk duniya babu macen da yake jin zata ta'ba shi yaji wani abu ajikinsa sai princess ita ma din yanzu ya soma gogeta a zuciyarsa da rayuwarsa ."cikin fita haiyacinta
ta riko fuskarsa sosai ta sanya kwayar idanunta dake tsiyaya ruwan hawaye acikin nasa " ban san hka soyayyarka tayi tasiri acikin zuciyata ba sai dana qasa amsar soyayyar kowa ."
"Ban san tasirin soyayyarka ta kai mizanin da zan iya rasa rayuwata ba sai da naji zaka min nisa , yaya kaine duniyata ruhina yana tare da kai ako da yaushe , nayi yunkurin bayyana maka soyayyata a tun lokacin da mubina Ke mutuwar sonka amman na gaza aikata hakan ina ganin cewar zan iya cire soyayyarka na cigaba da rayuwata amman still na qasa domin kuwa every each second nake jin sonka na qaruwa a cikin zuciyata , ina ta qoqarin sheida maka halin da zuciyata take ciki kwatsam kuma sai ga batun aurenka da marsi bance ka bar marsi ba amman dan allah ka had'amu ka auremu " rokonki bai kar'bu ba bare wata alfarmar ya kamata ku koyi yadda ake iya control din zuciya "ka taimakeni ban san ya zanyi ba " kar allah yasa ki sani ya fad'a yana jan tsaki ."
kuka take sosai tana kallonsa tmkr ranar ta fara ganinsa shi kuwa haushi ne ya turnikesa a wajen zuciyarsa banda tuttukin bakinciki babu abinda yake , a ganinsa ma ta balain rainashi
shi zata kalla tace tana so alhalin ga hisham dake mutuwar sonta? "kayi hakuri dan girman Allah nasan zakayi tunanin komai akaina wallahi haka ne , dan na rigada na haukace akanka bazan iya jurar abinda nake ji akanka ba sannan bazan iya amsar soyayyar yaya hisham ba ,dan kona auresa gangar jikina ya aura zuciyata da komai nawa yana gareka da kawai zan iya rayuwa ..."
Ta riko hannunsa hawaye na zuba daga idanunta ta soma tafiya dashi taku d'aya biyu yayi ya tsaya cak , itama ta tsaya suna fuskantar hisham naunaye ajiyar zuciya ta sauke tana goge hawayen dake tsiyaya ,ahankali ata ya zare hannunsa dake cikin nata ya yarfar sannna ya zura cikin aljihun wondonsa yana jan tsaki "ya hisham! ta kira sunansa a kid'eme "banyi niyyar fito da sirrin dake zuciyata ba amamn ya zama dole na fad'a maka tunda na fad'awa yaya adam babu komai acikin zuciyata sai..." karki kuskura kiyi wannan ganganci dan kome zaki yi tawa zuciyar bazata amince ba "to kuwa gara ka ksheni da hannunka na huta dan nima bazan iya auren yaya hisham ba , yana sona ni kuma kai nake so.."you're very stupid Kiyi maza ki danna madannin gogewa ki gogeni arayuwarki da zuciyarki dan ni mallakin mafarkina ce " yana gama fad'ar haka ya juya ya haye sama yana taka step yana magana " hisham ka manta da shirmen wannan yarinyar ka soma naka shirin domin wannan auren ko zata mutu sai anyisa useless girl kawai ga inda ake sonku aka damu daku amman ku dinga kai kanku inda bazaa ta'ba sonku ba nonsense "
Hisham ya runtse idanuwanshi "kenan hasashensa ya tabbata , zarginsa ya zama gasky kenan akan ata yake shan wulakanci da tsana da wahala a wajenta ? ,"ya kalleta cike da tausayawa yace "daman ata Kike so ?jikinta yayi mugu mugun sanyi ta rasa me zata cewa hisham illa ta runtse idanunta gam tana jin zafi da ciwo mara iyaka a zuciyarta ,ta durkushe qasa tana kuka tana nemawar kanta mafuta dan dole tasan abun yi kafin a had'ata aure da hisham shima ya durkushe gabanta ya dago ha'barta ya sanya kwayar idanunshi cikin nata , tai saurin buge masa hannu tana kallonsa cike da tsantsar tsana "ka kyaleni ni wallahi bana sonka tunda burinka kenan na soka , dan girman allah ka rabu dani ka manta dani, ka manta da maganar ka ta'ba sona arayuwarka , ka mantani ta qarasa fad'ar haka tana fidda huci mai zafi ."
"Dan allah kiyi hakuri nasan irin ciwo da zafin da Kike ji acikin zuciyarki ciwo ne kwatankwacin wanda nake ji acikin zuciyata nasan zafin ciwo da radadin kana son wani baya sonka ,wallahi na tausaya miki amman me yasa nuzla ?"me yasa sai ata zuciyarki zata kamu da so byn ni ina qaunarki ya kai hannunsa yana share mata hawaye"ata bashi da wannan lokacin wahalar da kanki da zuciyarki kawai zakiyi babu wannan tausayin a zuciyarsa a karshe ya rungumeta ajikinsa tsam yana shafa bayanta ahankali ahankali babu yadda ta iya dole ta kasance rungume ajikinsa domin tana bukatar wanda zai rarrasheta kuka take sosai tana rungume ajikinsa "ki daina kuka nuzla dan zuciyata bazata iya ganin hawayenki da damuwarki ina matukar sonki da zaki bani dama da sannu zaki daina son ata ki soni ya fad'a yana qara rungumeta gam ajikinsa ahankali ya mike tsaye tare daita ya nufi kofar fita tun kafin mutane su shigo su fahimci halin da suke ciki ."
Washegarin da misalin karfe tara na dare ata ya shiga d'akin mami sanye cikin fararen kayan bacci wondo da riga , hannunsa rike da black cup dinsa dake dauke da ruwan coffee ,yayinda dayan hannunsa Ke cikin aljihun wondonsa ya samu mami tsaye a gaban wordrobe dinta tana qoqarin rufewa tana ganinsa ta sakar masa murmushi tana cewa "Masha allah adamcy nan ya karfin jikin ?alhamd sweetheart ya qoqari dani ?kwana nawa ya saura ai Allah Allah nike Kayi tafiyar nan ka dawo mu sha biki ranar bani da dama zan aurar da d'a daya tilo ya girgiza kai kawai yana ajiye cup din hannunsa akan bedside dinta ya tsura mata tsumammun idanunshi yana kallonta tmkr wani maraya "yaakayi adamcy nan duk sanda kayi haka akwai abinda kake son fad'a "haka ne sweetheart kin fi kowa sanin halina alfarma nazo nema ."
"Alfarmar kuma ?mami ta maimaita abinda ya fad'a
"Eh ina neman wata alfamar a wajenki sweetheart "ina sauroronka Allah yasa zan iya ,ya marairaice murya sosai kafin ya soma mgn "dan darajan Allah sweetheart ki qara min lokacin auren nan wallahi wallahi wallahi !!! kinji na rantse miki zan auri yarinyar nan zabinki , wasu yan kwanakin kawai zaki qara min har naje na dawo dan zan dauki lokaci a france daga nan ma zan wuce hollond yi wasu abubuwa masu mahimanci a yanzu na samu sauyin lokaci amman kuma idan kina ganin zaa iya yin komai ko bana nan fine na amince a daura auren ayi komai amman da zaa bari na dawo sai nafi farinciki kasancewar ina son a hada auren dana hisham da nuzla yadda take kallonsa ya fahimci kamar bata yarda dashi ba "na rantse fa duk wanda aka rantse wa bai yarda ba shi din bana allah bane nayi miki wannan alqawarin sweetheart zan aureta ".
"naji amman har zuwa wani lokaci ni wallahi zaka sani jin kunya auren sauran kwanaki ace an daga "karki damu sweetheart idan akwai damuwa kawai ayi ko bana nan amman na fi son ina nan ,sai kace wata tsiyar zaka kulla ko kana ?ya dan ciza gefen lips dinsa "bansani ba ko zan iya kulla wani abu a auren da bana só ?kaji dashi tunani tayi karta je a daura yaki dawowa ya bar yar mutane da nauyi akanta gara kawai ta qara masa lokaci idan ya dawo sai ayi"Kwanaki nawa zan qara maka ?uhm ko Kmr wata biyu haka yayi "what ! kai adamcy ban yarda da kai ba ,wallahi ki yarda dani sweetheart bazan baki kunya ba, ba kuma zan saba alkwari ba I promise you ,ka cika alqawari adamcy ,karki damu sweetheart na ranse fa ,shikenan na yarda da kai ta fad'a kafin su fad'a hirar duniya a nan yake bata labarin nuzla murmshi mami tayi tana cewa "adamcy nah mai farinjini ."
Zaune mr ata yake agaban hajiya zulaiheart sanye cikin suit wondo da riga bakake jikinsa na fitar da wani kamshi na daga hankali fuskar nan nashi dake kwance da kasumba tayi fresh tayi kyau tana fitar da wani haske na dabam mai daukar hankali abun ka ga fari mutun sallama ya shigo mata dan sauran awa daya jirgnsa ya daga zuwa kasar france "Allah kiyayya ya tsare min kai , ka kular min da kanka sosai banda wasa da abinci aci abinci akan lokaci kamar yadda doctor ya fada "in sha allahu zan kiyaye sweetheart. Allah ya qara girma,ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani kema ki kular min da kanki "Ameen summa ameen nayi maka wannan alkwarin Allah yayi muku albarka gabadaya ku "inji mami ,sannan taja musu addu'a suka shafa tana shafa masa na hannunta a fuskarshi ."a tare suka mike suka fito inda tawagarsa Ke jiransa a haraban gidan shi kadai ne zaune a bayan motarsa limozin sai driver a mazauninshi, hawaye ya tsiyayowa mami sanda motocinsa suke qoqarin barin gidan sai take jin kamar kar ya tafi amman kamar yau ne zai dawo gareta wannan karan mami ta kasa daurewa sai da tayi qwalla, gefe tayi da kanta tana dauke hawayenta ."
*****
Yau tsawon kwana uku kenan mlm yahuza yana zariyar zuwa gidansu maryama amman kamar kullum bai samu ganinta ba yau ma daga massalaci ya wuto kofar gidansu yana neman yaron da zai aika cikin gidansu ko cikakken minti goma bai yi da tsayuwa ba, sai ga yaya sadam ya fito daga cikin gidan , nan ya mika masa hannu suka gaisa "ina fatan dai lafiya kwana biyu nan kake zuwa gidan nan ?"Lafiya lau wajen maryama nake zuwa sai dai duk zuwan da nake yi bana samun ganinta ,shine dan naci kake ta zuwa ?to ya zanyi sadam tunda zuciyata ta kamu da matsanancin sonta duk da bani da tabbacin ko tana sona amman nasan tana son fitowa inda nake habib ke hanata fitowa yanzu dai taimaka min ka fito min daita dan nasan muddin habib na cikin gidan bazai barta ta fito ba ,murmushi sadam yayi yana cewa "kai habib hukuma ne wannan yaron bari ina zuwa !ya juya ya koma cikin gidan ya shiga side dinsu maryama ."
a parlour ya iskesu gabadaya suna hirar duniya ya zauna yana fuskantar maryama suka gaisa da aunty sannan maryama ta gaishesa haka ma habib ya amsa masu da "lafiya lau cikin sakin fuska ,ya gida da aiki sadam ?Alhamdulillah aunty mun godewa Allah yace yana duban maryama "ga malamin ku yahuza can a kofar gida yana jiranki yau tsawon kwana uku kenan ina ganinsa ashe wai saboda ke yake zuwa amman bakya fitowa."wata irin kunya ta kama maryama ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da zara zaran yatsun hannunta".
"ai ga d'an albarka dake hanata fita nan , ko shi zai aureta bansani ba ?yaro qarami dashi sai aikin nuna isa da iko ita kuma shegen son dan'uwa tana biye masa aunty ta qarashe maganar tana zabgawa habib harara ,habib bai ce komai ba ya tashi ya shige ciki dan matsawar yana zaune a falon bazai iya barin maryama ta fita zuwa koina ba km hakan zai sa yaya sadam yaji babu dadi "ai yahuza mutumin kirki ne kuma ga dukkanin alamun da gaske yake aunty tace "allah yasa shi wai habib dan matsalar daake ta samu akan masu zuwa suna tafiya né yake jin haushi "nima na fahimci haka amman in sha allahu komai yazo karshe dan nasan yahuza bazai mata haka ba nima gsky na yaba da hankalinsa maza tashi kije maryama karki dade maryama bata ji dadi ba ganin habib ya tashi ya barsu km tasan duk akan mgnr fita ne ,amman babu yadda ta iya yaya sadam da aunty suna da karfin iko arayuwarta ta mike ta fita ta bar aunty da yaya sadam suna magana bata san abinda ya cigaba da wakana atsakaninsu ba ."
acikin duhu ta sheida murmushinsa ganin hasken hakoransa ta dan saki ranta da kawar da damuwar fuskarta barkanki da fitowa gimbiya maryama "numfashi ta fesar "kai ya kamata a yiwa barka da zuwa da kuma sannu da qoqarin zuwan da kayita yi baka samun ganina da km qoqarin da kayi da iyayena last week na gode sosai " ya dan kyaleta "iyayenmu dai na gyara miki ." maganarsa ta dan mata dadi wannan yasa ta dan sakin fuskarta kad'an "ya kamata mu samu waje mu zauna ko can ne ya dan nuna mata wani dakali dake makoftansu ."
tare suka qarasa amman shi yaki zama ya tsura mata ido ya kamata ace kece kika fara zama sannan ni tayi shiru dan tuni ta gane manufarsa ta dan kallesa da idanunta cikin sauri ta kawar da kai ganin kwayar idanunshi na kanta to shikenan na zauna kema ki zauna ta zauna tana gyara zaman hijab dinta sukai shiru na dan tsawon lokaci daga bisani ya dago ya dubeta "Maryama zuciyata duk ta gama tattara komai agareki a yanzu bani da wani shakka ko kwankwanto akanki muradina ne na samu damar da zan kawo kaina ga iyayenki domin a samu tsayayyen magana a tsakaninmu ."
Soyayyarki ta jima ajikina maryama nayi dawainiya da soyayyarki tun kafin ki kai wannan lokacin na koyar da zuciyata dabarun da kuma yadda na dauki hakuri dan kawai na samu soyayyarki ban ta'ba gazawa ba , ina sonki maryama da zuciya daya ban qara jin ina sonki ba sai danaji halin da ke da mahaifiyarki da kaninki kuke ciki a gidanku bazan boye miki ba ina jin tausayinku most especially mahaifiyarki domin ta fuskanci abubuwa dayawa akan rayuwa kuma tayi hakuri na tausayawa rayuwar da kuke ciki ki daure ki samar dani acikin zuciyarki mu daga darajan uwa da kuma danuwa mu tallafi rayuwarta data kanin mu dukkan wani muradinki zan bi na tabbatar kina da burin kiyi aiki byn kin qare bautar qasa kamar yadda naji kawayenki suna fad'a,burinki kiyi karatu mai zurfi Kiyi aiki ni nan zan barki Kiyi komai kike só zan barki ya dan saurara yana kallonta hawaye taji akan kuncinta tasan su da mahaifiyarsu abun tausayi né suna cikin tsananin kunci da bazai yuwu a boyesa ba ."
ahankali ta dubesa "naji dadin yadda kace zaka tayani kula da mahaifiyata da kuma danuwana mlm yahuza ina matukar son Mahaifiyata ina son na gatatan rayuwarta domin ita kadace dani na yarda da soyayyarka kuma na amince duk lokacin da kake da lokaci kofar neman aurena a bude take domin burin mahaifiyata kenan na tsayar da mijin aure fatana ka rikeni amana tayi shiru saboda kunyarta ta motsa ya sauke ajiyar zuciya a zahiri take fahimtar farincikinsa dan bai boye ba ."
Yayi murmushi yana shafa fuskarshi "maryama amanarki agareni bake zaki bani amanarki daga allah daya halicceni ce domin shi na dinga roko ya bani ke amatsayin mata aurena allah ya amsa tunda har kin amince min dan haka shi ya bani wannan amanar dan haka nayi alkawarin bazaki taba ganin sabanin haka daga gareni ba ,ba kuma zakiyi danasani ba , aurena zai zame miki abun alfahari bazan ta'ba gudunki ba bazan ta'ba juya miki baya ba ."Soyayyar sati uku da sukai da mlm yahuza ta fuskanci tsantsar son da yake mata kulawa kuwa har da mahaifiyarta abun mamaki kowa a unguwarsu yasan da soyayyarsu wasu nasa albarka wasu nacewa ba girin girin ba allah yasa a d'aure kar ya gudu ya barta kamar sauran."
******
Cikin wannan lokacin maryama da kawarta subai'a suka je adamawa domin suyi cam for three weeks bayan sunyi sati uku a adamawa alokacin mlm yahuza yayiwa wani mutun magana akayi masu change of location ita da kawarta daga adamawa aka dawo dasu lagos inda zasu fara bautar qasa a Z &A comapany dake kan titin guness bayan ciku cikun da mlm yahuza yayi masu domin shine ya shiga ya fita ya kar'bo masu letter suka kai wa nysc aka kar'besu a kamfanin bayan sun dawo lagos suka fara savieces dinsu wannan taimako da mlm yahuza yayiwa maryama ya wanke zuciyar habib yaji ya shiga ransa har ma ya fara kiransa da otherhaif kuma yake girmamasa yana mai jin ba qaramin dace yaruwarsa tayi ba domin kuwa samun maza irinsa suna da matukar wahalar samu ."
"gashi shi dai ba wani zurfi yayi a boko ba dan karatunsa iya diploma ne amman yana da hanya kuma yasan mutane sosai dan shugaban RRS mai ci alokacin abokinsa ne tare sukayi karatun tun daga primary har zuwa secondary inda anan suka rabu amman har gobe suna mutunci da abota , fara bautar qasa yayiwa maryama dadi dan daman zaman gidan ya isheta dan tun da suka qare karatu babu inda take zuwa bayan islamiyya gashi ita daman fita bai dameta ba saboda ita ba maabociya son yawo bace amman wahalar da take sha da yawon sata aiki da mutanen gidansu keyi yasa tayi maraba da da wannan fitar tata kullum fatan allah ya taimaketa tana qare bautar qasa ta samu aiki ."
Ranar wata asabar tana zaune shiru a side dinsu tana tunane tunane akan sakina tana matukar qaunar sakina aranta ta kasa jurewa abubuwan da take mata batare da tasan laifinta ba ,zuciyarta ta bata shawarar taje ta tmbyeta ko wani laifi tayi mata wanda yasa ta canza mata ,nan take ta amince da shawarar zuciyarta , dan hk ta mike tsam ta fito ta nufi side dinsu ta yi sallama a tsakar gida babu wanda ya amsa mata dan haka ta wuce daki inda tafi tunanin sakina take mintuna sha uku da zamanta amman sakina bata ko kalleta ba ."
Ahankali maryama ta tunkarareta da abinda ya shiga a tsakaninsu "haba "yar uwata mai na yi miki ki ke fushi dani tsawon Lokaci ko magana ba kya min mai nayi miki da hukuncina ya cancanci haka.?""Cewa na yi kin min wani abu?sakina ta tambayeta tana mai kallo cikin idanuwanta maryama ta sauke nata idanun ganin irin kallon da Sakina ke mata. Ta ce"tô Sakina tsawon lokaci naga bakya min magana, in da nayi miki laifi ne sai ki sanar dani na nemi yafiyarki bana jin dadin yadda kike nuna ko in kula gareni tsaki kawai sakina taja ta fice tana magana cikin ranta wanda sam maryama bata ji dadin abinda tai mata ba "na shiga uku maryama ta fada a ranta me zai sa sakina ta yi min haka kawata kanwata kuma yaruwarta masoyiyarta?ya Allah ka sanyaya zuciyar sakina akaina idanunta cike da hawaye ta baro side dinsu ."
Ranar wata laraba aunty salma da yaranta biyu suna zaune a tsakar gida aunty salma ta dubi sakina "wai Ke kwana biyu nan mai yake damunki ne sai ki dinga kadaita kanki kina wani shiru idan wani abu aka miki bazaki fad'a ba sakina tace" ko na gaya miki ba iya magance min zakiyi ba duk da ku ka jawo halin da muke ciki nida yaruwata shukura ,maryama dake kokarin shigowa cikin side din nasu ta dan. tsaya ta kasa kunne aranta tace "allah sarki ashe yaruwata laifi akayi mata tayiwa gidan kudin goro kowa bata shiri dashi."
aunty salma tace " koma me akayi muku zurfin cikinku ne ya janyo muku Ke kanki kinsani duk damuwarku kema kinsan zanyi qoqarin magance muku ita matukar ina numfashi acikin duniyar nan sanar dani menene aka muku da har yake saka ki cikin kunci "kusan rabin yan makarantar islamiyyarmu sun san yadda shukura ke son mlm yahuza amman kiri kiri kuna kallo wannan banzar ta juya abun ya koma kanta gashi har ana batun saka rana aure ."
Da alamun aunty salma taji dadin furucin sakina akan maryama domin duk irin kunci da halin koin kula da suke ciki da sakina bata gani ba bare ta shiga cikin maganar tayi musu sulhu "aunty salma tace" to meye keda yaruwarki ? maryama ta fahimci kalmar cikin zolaya tayi maganar ,ai kuwa nan da nan sakina da shukura suka bata rai cikin nuna tsantsar tsana "wannan banzar ce yaruwarmu daace kun koresu a gidan Kmr yadda kika ce ai da bata yiwa shukura kwacen saurayi ba yanzu gashi nan muna ji mun gani wanda shukura take so dole zata hakura "a'a waya gaya maku ai babu wani maganar wani hakuri ,kuyi hakuri tunda kun fad'a min ku bani kwana uku zaku ga abinda zai faru."
hankalin maryama ya tashi kwarai da gaske har yasa daga nan bata sake sanin abinda suka cigaba da tautaunawa ba saboda wani daci da zuciyarta ta dauka ."jiki a matukar ta sanyaye ta dawo side dinsu "ita bata san shukura tana son mlm yahuza ba da sam bazata amince da soyayyarsa ba sai ma ta hadasu amman yanzu ya zatayi ?ko da yake ta fahimci wani sabon salon cin zarafi ne ake son bullo mata mata dashi dan arabasu dan haka zata bari adduarta tayi karfin da bazasu samu nasara akanta ba tun daga ranar bata sake runtsa idanuwanta ba wajen kiyamul laili domin kiyamullaili tana qarawa nauyin mizanin bawa, tana qarawa mutun hasken fuska da samun kwarjini da d'ga darajan mutun acikin mutane kariya ga dukkan sharri tare da biyawa bawa bukata."
Duk bayan kwana biyu mlm yahuza yana zuwa wajenta Kmr yadda ta tsara masu dan bata son yawon zance ,tun bayan kwana biyu sunyi da mlm yahuza zai zo sai dai har karfe takwas na dare daya saba zuwa bai zo ba amman ta rasa dalili hakan ta kasa hakuri ta shirya tsaf ta fito zuwa bangaren Ummah ta iske shukura tana zance sai dan kasancewar dare bata lura da wa take zance ba sai dai kawai kamshin turarensa yayi mata kama dana mlm yahuza amman ko kadan bata kawo shi bane ta shiga bangaren umma tana zaune suka gaisa
Daga nan suka shiga hirar duniya har sanda shadaya ta buga ta mike tayi mata sallam ta koma side dinsu cikin tsinkewar zuciya dan bgabanta banda luguden bugawa babu abinda yake ."
Shigowarta kenan daga wani kamfani kai zanenta domin tallatawa ,da baba gali ta soma ci karo "yar gwal idan kin huta ina son magana dake dam taji gabanta ya fadi tun da take arayuwarta bata jin ranar da baba gali yace yana son magana makamanciyar haka ba km wai yar gwal yana son magana daita tabbas akwai mahimmiyar magana , bata kawo komai aranta ba sai tunanin watakilla ko mgnr mlm yahuza ce tayi karfi tunda ya sha fad'a mata yana son manya su shiga ciki ta nufi bangarensu ta kammala komai nata a natse ganin shima ya fita masaalaci tayi sallah har ishai sannan ta dawo parlour ta zauna zuciyarta na tunanin akan maganar da baba gali zai yi daita duk da bata san abinda zai sanar daita ba amman sai maganar ta tsaya mata arai cike sa fargaba ."
Karfe tara daidai umma ta aiko a kirata ita da aunty nan fa gaban maryama ya cigaba da fad'uwar da yake , tare suka fito da aunty alokacin shukura ta shigo daga zance tuni aunty ta wuce dan har ta kusan isa bakin side din umma, haka nan ta kalli shukura dake zaune kusa da aunty salma dake cin abinci atsakar gida ta sake gaishe da aunty salma ta wucesu ta shiga bangaren umma ta gaisheta cike da girmamawa umma taji dadi sosai ta tmbyi lafiyar habib ."
shiru ne ya biyo baya har na kusan mintuna asirin sai ga aunty salma da aunty hassana sannan byn an gaisa umma ta numfasa tace "Maryama wata tmby nake son nayi miki game da yaron nan dan gidan lawan yaro ?"dam taji bugawar da qirjinta yake ya qaru , tayi shiru domin bata damar tmbyrta ta cigaba da magana "tsakanin keda shukura wa yace yana só né ?"
Maryama tayi shiru lokacin da maganar ta doki dodon kunneta wannan wace irin magana ce akwai abinda umma batasani ba a tsakaninta dashi ?amman dai koma menene batasan abinda yasa take mata wannan tmbyr ba, ta bude baki zata bata amsa abinda Ke tsakaninsu sai kunya ta hanata tayi kasa kawai idanuwanta "Maryama tmbyrki nake baki ce komai ta sake yin shiru a karo na biyu tana son jin ba kece wacce kuka fara son juna ba har yake zuwa zance wajenki ba ? ta sake yin shiru tana son bata amsa sai dai bazata iya sanar daita ba tunda gashi ita da kanta tasani kuma tana da masaniyar wajenta yake zuwa, ita me yasa umma zatayi mata wannan tmbyr akan abinda ta rigada tasani tunda sau tari ita ke cewa taje idan yazo bata son fita ."
"Abinda yasa na kiraki nake tmbyrki shine dazu da yamma byn fitarki kai zane yan gidansu sunzo domin auren diya a gidan nan kuma sun bayyana wacce suka zo nema ni da azatona kece yahuza yake zuwa wajenki ashe yaruwarki shukura yake so ."
ba idanuwanta ba hatta numfashinta da kwakwa luwarta sai da suka daina aiki wani tsayawa tayi na wani lokaci kafin ta sauke naunayen ajiyar zuciya ta juya idanuwanta kana tashiga tunani da kwakwa luwarta batace komai ba saboda tashin hankali daya risketa ta sunkuyar da kanta qasa kawai tana jin damuwa mai tsanani "
"Magana nake maryama kinyi shiru daman bake yake nema ba yauruwarki yake nema ?ta qara yin mata tmbyr bata san abinda zatace ba ganin zata batawa kanta lokaci da jama'ar dake wajen yasa ta dago kanta tace "tunda shi da kanshi ya sanar da wacce yake nema ai babu laifi umma , umma tayi shiru kawai tana dubata ina son gane abun ne domin ni a tunanina Ke din ce yake zuwa wajen ki kawai ta dago tace "ba wajena yake zuwa ba wajenta yake zuwa tana gama fadar haka ta mike da sauri dan zamanta a waje zai yasa ta zubar da hawaye ta bayan bangarensu inda aunty Ke aiki ta labe tana kuka mara sauti dan kar wanda ya ganta ta tsaya anan ta rarrashin kanta ne dan karta dagawa danuwanta hankali."
Sai datayi mai isarta sannan ta fito ta shiga falo kai tsaye ta wuce habib dake zaune yana kallon ball dakinta ta shiga ta kwanta lamo akan katifa ahankali kalaman mlm yahuza daya dinga furta mata suka dinga dawo mata cikin kwakwaluwarta da taimakonsa gareta hakika bazata ta'ba mantawa dashi arayuwarta ba ta dinga girgiza kai shikenan shima ta rasashi ,hawaye suka dinga zuba daga idanunta bata san tana shesheka ba sai dataji muryar habib yana cewa "kamar shesheka nake ji heartbeat tayi saurin gyara kwanciyarta tayi shiru tare da lullube kanta tana tunani abinda ya kamata ta fad'a masa idan ya qaraso gareta domin dai abinda yake gudar mata kenan gashi ya faru daita ta runtse idanunta sosai alamun ta fara bacci ganin hk habib ya juya ya koma falo ."
Bangaren umma kuwa gyara zama aunty tayi ta kallesu "hakika bakuyi adalci ba saboda ni nasan wannan yaron wajen maryama yake zuwa me zai sa shukura zata qaunaci wanda yake son maryama har ku iyayenta kusan hanyar da kuka bi kuka raba maryama dashi ?mgnr tayiwa ummah dadi ko babu komai yau zata gwada kunjinta akan damuwarta
Aunty salma ta gyara zamanta itama tasoma magana Kmr tana jira "kada a kawo maganar rainin hankali acikin maganar nan kina tunanin shukura zatace tana son shi ne ?".
"to kisani diyata bazata ta'ba cewa tana son wani ba shine da kanshi yace yana sonta kuskure yayi yace yana son maryama dan kawai ya samu hanyar da zai ce yana son shukura bude kunnuwanki da kyau yahuza ya dade da soyayyar shukura acikin ranshi nauyinta kawai yake ji dan hk ya fara gwada soyayyar daga kan maryama ganin bata da wani matsayi da aji ya dawo hanyar madaidaiciya ba kuma diyata tace tana son shi ba idan kuma har abun ya dameki sai kisa diyarki ta sameshi kice ya daina son shukura ya dawo kanta."
"Uhm kawai aunty ta furta a fili sannan a fili tace allah kai ne allah kai ka kawo ma maryama yahuza amatsayin wanda yake sonta byn ta rasa sauran kuma na tabbatar yahuza yana son maryama da gsky Allah kai kasan abinda akayi aka shiga tsakaninsu ya Allah kayi mata sakayya nasan zaka kawo mata wani wanda ya fishi komai "Wai me maganarki take nufi ?kina nufin an kwacewa maryama saurayi ne ko me ?"wannan ai gskyr da kowa ya rigada yasani ce maryama yake so kuma dan ita yake zuwa gidan nan ,na rasa wannan maseefar babu damar aga maryama da cigaba duk yadda zaa yi sai anyi an rabata dashi ".
"Dakata dakata!! su waye dasu waye idan zakiyi mgnrki Kiyi mgnrki a inda bazai zame miki damuwa ba , ina maryama take ?me ye tafi sauran mata da idan ta samu cigaba ake rabata dashi ?ita din gwal ce ko me ? inji cewar aunty hassana "tunda yaro yace ga wacce yake so ai magana ya qare sai ayi shirin aure "a'a hasaana wannan ba magana bace allah baya son zalinci kuma baya son wani bawan yayi ,hakika idan akayi auren nan an zalici maryama "umma ki rabu dasu hassada ke damunsu akan maryama ,amman maryama din da kuke gani tafi gwal wallahi kuma kaf zuriarku babu macen data kaita allah na tuba idan nayi alfahari ka yafe min ba alfahari nayi ba gsky na fad'a ."da sannu hassadar zata cinyeku ni natashi allah ya bamu alkhairi allah yayi mata zabin abinda yafi zama alkhairi arayuwarta da izinin allah maryama sai ta kawo maku wanda bazaki iya kwacewa ba tana gama fadar haka ta mike ta bar falon ."nan fa hayaniya ta kaure aunty hassana na zaginta aunty salma na qarawa ummah kuma tana basu rashin gsky ."
Aunty ta shigo parlour'n tana kuka nan da nan hankalin habib ya tashi ta wuce shi ta nufi dakin maryama tana kwance har lokacin tana zubar da hawaye tana tuno daddan kalaman mlm yahuza gareta atare suka fad'a dakin ta qarasa ta zauna bakin gadon ta kamo hannun maryama ta damke cikin nata jikinta har ya dauki zafi ta fashe da wani sabon kuka wanda yasa kukan maryama ya fito fili ta yunkura ta mike zaune cikin mawuyacin hali tana cewa "why aunty ?me yasa kike asarar hawayenki akan dan wannan abun ? "duk fa abinda kaga allah bai baka ba to ba rabonka bane Kiyi hakuri ki daina kuka please cikin rawar muryar habib yace "aunty meke faruwa ,abinda kake gudu dai ne ya sake faruwa sun rabata da yaron nan yahuza yaron kirki "what !?"
"Wallahi habib sun rabata dashi wai shukura zai aura ba maryama ba amman babu komai akwai allah wani irin ihu yayi yana kurma uwar ashariya ya juya maryama tayi saurin durowa ta rike masa hannu ya juyo ya kalleta "ki sakar min hannu heartbeat ba shukura ba hatta shi kansa mlm yahuza sai naci ubansa yau koni koshi girgiza masa kayi tayi "bashi da laifi nasan akwai abinda akayi masa domin da kunne naji komai nan ta zayyana masu hirar aunty salma da yayanta akan mlm yahuza, dan haka kasani mlm yahuza baya cikin haiyacinsa ,mlm yahuza mutumin kirki ne idan nace banji zafin rabuwa dashi ba nayi karya jikinsa a matukar sanyaye ya zame a zauna qasa ya dafe goshinsa da hannunsa daya yana jin ciwon abinda ya faru" yanzu abinda shukura tayi mana kenan ya fad'a cikin jin haushin ,to ya zamuyi mu mun dogara da allah aunty ta sake riko hannun maryamu "Allah yayi maku albarka a rayuwarku ,allah ya baki miji na gari, idan da rabo Allah ya juyo da hnkln yahuza ya dawo gareki ya kula dake ."
"Maryam tana kuka aunty tana yi tana goge mata hawaye "Kiyi hakuri maryama "kema aunty Kiyi hakuri bana son ki daga hnkln ki akan matsalar nan ,in sha Allah nan kusa Allah zai bani wani "In sha Allah bazai dade ba Allah karka barmu da iyawarmu ka iya mana dukkanin abinda bazamu iya ba har kusan karfe dayan dare suna tare kuma duk mgnr mlm yahuza suke aunty bata so tayi nesa da maryama , tafi son bacci ya zo mata tana tare daita
don Allah ki daina damuwa kinji ' yata ki kwanta Kiyi bacci Allah yayi miki albarka yayi wa rayuwarki data ' ya'yan da zaki haifa albarka, In sha Allah bazaki dangwama a hk ba Allah zai saukaka mk na yafe miki duka laifukan da kikayi min wnd na sani da wnd bn sani ba daga hk tayi shiru tana goge hawayen idanun maryama , amma tamkar sake kara mata su ake .
Ba sosai damuwa yake tasiri acikin zuciyar maryama ba bare irin wannan damuwar da idan da sabo ta saba amman tabbas wannan damuwar ta doketa sosai dan duk kwanaki bata iya bacci adduar nenan zabin allah kawai takewa kanta zuciyarta chunkushe da bakinciki mara misaltuwa har akayi kiran sallah asuba bata runtsa ba hakan yasa ta mike da kyar ."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.