Best / Popular Hausa Novels

Maradams Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt

Chapter 14 of 18

Page 17

" are you crazy some "?ya furta a zafafe yana hura hancinsa har zata girgiza masa kanta alamun "a'a ! sai kuma tayi sauri ta gyada masa kanta alamun "Eh! dan ko giya ta sha bata isa tace masa "no ! ba bare tana cikin hankalinta "what's wrong with mr ata I did not do anything wrong ? tayi maganr acikin ranta tana mai sake kama kanta dan karta yi wani kuskuren da zai dakatar daita na wasu satittuka koma ya dakatar daita aiki gabadaya ."

" ahankali ya mike tsaye ya kamo lip's dinsa na kasa yana cizawa ahankali ahankali !! magana yake son yi amman ko ya bud'e bakinsa maganar bazata fito ba , daga can bakin kofa akayi knowking tare da cewa "may I coming sir ?". shiru yayi yaki cewa komai sannan yaki kallon kofar , some dake tsaye cikin tsananin tsoro da fargaba ta kalli glass din kofar taga prosper ne tsaye hannunsa rike da file mai cover green wani yawu ta hadiye sannan ta saci kallon inda mr ata yake tsaye taga baya kallonta ta sake juyawa tayi wa prosper alama da hannunta ya koma da sauri ya juya ya bar bakin kofar ."

Mr ata yasa hannu ya d'auki wani file mai white cover dake ajiye akan makeken table dinsa yana dubawa , lokaci me tsawo ya d'auka yana dubawa yana shawagi acikin makeken office din nasa zuciyarsa na tafarfasa yayinda wata irin zufa ke tsatsafo wa some akan goshinta kamar an watsa mata ruwa .duk lokacin da taga mai gidan nata cikin damuwa itama sai ta tsinci kanta ciki dan kusan duk abinda yaje ya dawo akanta zai
qare tunda itace sectary dinsa duk abinda zai shiga ya fita ta sani ."

Ya sake kamo gefen lip's dinsa. na qasa yana cizawa hannunsa dake rike da file ta zubawa ido tana tausayawa duk matar datai ganganci aurensa , tana goge zufan goshinta dake ta tsatsafo mata duk da karfin sanyin ac dake ratsa office din ."Cikin kulawa da girmamawa tace "sir !" ko zan iya kiran metting a yanzu ?"
"ahankali ya lumshe lumtsatsun idanuwanshi da suka d'an canza kala alamun tarin 'bacin rai yake ji acikin ransa "sir !ta sake kiransa a karo na biyu ahankali ya motsa lip's dinsa "go !" ya fad'a atakaice batare daya kalleta ba da sauri ta juya ta fice daga cikin office din tana sauke naunayen ajiyar zuciya ."

Cikin kankanin lokaci ta dawo ta tsaya a gefe cike da kamewa da girmamawa tace "sir komai ya Kamala kai kawai ake jira." a natse ya goya hannuwansa duka abayansa ya soma daga kafafunsa dake cikin hadadden black canvers tana biye dashi abaya hannunta rike da wata takarda mai bango ja , tafiya kad'an sukai sai ga hisham da yaya Ibrahim tare da wasu manyan maikata guda biyar suka marasa baya suna takawa ahankali har zuwa qasan kamfanin madadin yabi hanyar da zai kai shi comference room sai suka ga ya karya yabi wata doguwar hanya , nan take some tayi gaba da sauri domin ta fahimci inda yake son zuwa kafin ya shiga conference room yayinda sauran suke take masa baya, bai tsaya akoina ba sai abakin wani makeken kofar glas wanda ya kasance anan ake ajiye duk wasu ayyukansu masu mahimanci ya zura duka hannuwansa acikin aljihun wondonsa yana kallon wajen yana bukatar a bude masa ya shiga tare da qarin bayani ."

Ahankali ta danna madan nan bude waje suka shiga gabadaya a natse ta shiga yi masa bayani tana nuna masa kayayyakin dake ciki da kuma wanda aka fitar kudinsu basu shigo ba duk abinda take fad'a yana jinta kuma yana fahimtarta , amman ko tari bai yi bai yi ba ."
runtse idanuwanshi yayi sosai domin ransa ya gama kololuwar 'baci , daga nan wani bangaren suka nufa inda suka dinga wuce maikata da masu zuwa sarin kaya ,ba qaramin barna akayi masu ba ,yaya Ibrahim "yanzu kuna kallo akayiwa kamfani barna mai girma haka ? ya fad'a yana sake runtse idanushi dan baya ganin komai sai wani irin azababen duhu na 'bacin rai ."

Yayi shiru na kusan second goma sannan ya sake motsa lip's dinsa "yanzu har kunnuwanka sun manta abinda dady ya fad'a mana kafin rasuwarsa .?" Ka manta umarninsa akan wannsn kamfani ?" duk wannan maganr da yayi Idanunshi na runtse sannan cikin tsadadden turancinsa yayita " ban manta komai ba adam "ban manta umarnin dady ba amman bani
da yadda zanyi ne kai kasan halin sultan da sauran yanuwansa kowa abinda yaga dama zaiyi yanzu dai tunda kazo Komi dawo daidai amman kuma kabi komai a hankali kar asamu damuwar da zata haifar da matsala a tsakaninmu wani irin azaban ciwo yaji yana saukar masa har cikin kahon zuciyarsa yana sukarsa zuciya tazo masa wuya , baya jin zai d'agawa duk wanda yake da saka hannu acikin 'barnar dakayiwa kamfanin kafa ba ,bai sake cewa komai ba ya juya da sauri suka rufa masa baya ."

conference room ."d'akin ne da'aka tanada domin tautauna mahiman abubuwa masu matukar mahimanci , dogon table ne zagaye da kujeru bakake na alfarma yayinda jikin bangon d'akin ke manne da hoton mr president na lokacin da gwanar jahar lagos ,sai hotonsa dake tsakiyar hotonsu da certificate dinsa na kasuwancinsa ."mafi yawan mutanen dake zaune aciki room din yan'uwansa ne dake aiki akarkashin kamfanin ,a natse ya shiga d'akin taron ya yana shan kamshi tsit baka jin motsin kowa sai ac dake aiki da kuma na mutane dake fita a hankali , bai kalli inda suke zaune ba ya qarasa kujerarsa wanda ya kasance mallakin mahaifinsa ne ada ya zauna cikin nuna isa."

ido sultun ya runtse da karfi saboda bakinciki ganin yadda mr ata yayi wani irin zauna akan kujera na nuna isa da jarumta da kamala duk da cikin yanayi na bacin rai yake amman hakan bai hana ainihin sahihin kyawunsa fitowa ba daman kuma shi haka yake fushi ko damuwa baya hana aga kyawunsa hasalima kyau yake qara masa."
wani dogon tsaki sultan yaja wanda bai san a fili yayisa ba sai daya ga gabdaya mutanen dake gurin sun juya suna kallonsa banda uban gayya mr ata wanda ya sake daure fuska alamun babu wasa ,sai dai zuciyarsa banda tafasa babu abinda take ahankali ya runtse tsumammun idanuwanshi domin saisaita kanshi daga aikata abinda ke taso masa ahankali ya motsa lip's dinsa ya soma magan a natse tamkar baya son magana sai dai jin maganar kasan magana ce ta masu hankali ce ."

"The journey of thousands miles begings with a step as you all know ,ya numfasa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa sannan ya cigaba d'an lokacin da muka dauka bamu ziyarci wannan kamfanin ba yasa kowa yayi abinda ya ga dama "hakika anyi mana barna mai girman da bazamu iya bari ba , bayan acikinmu kowa yasan adadin wahalar daaka sha kafin wannan kamfanin ya samu kar'buwa a idanun duniya gabadaya ,but what's more important is that duk wanda yasan yana da hannun acikinku wajen danne kwandala acikin dukiyarmu ya gaugauta dawo dashi a yanzu kafin na dauki mataki akan kowa ye acikinmu dan bazan ragawa kowa ba ,bayanin mr ata yayiwa wasu daga cikin yanuwa dadi most especially mukhtar wanda Ke rike da wayarsa yana daukar vedio tautaunawa da'ake wanda kusan duk lokacin da zaa gudanar taro haka ana yi wani lokaci a daurashi a social media wani lokaci kuma baa daurawa ."

"Ina jiranku wad'an da sukayi taadanci da fashiwa kamfani domin su san kansa ba sai na fadesu ba sannan sun san number asusun kawasuwancinmu mintuna shabiyar kacal na bayar a maida kudaden daaka hamdame cikin asusu "malam ka dinga sanin yadda zakayi ma mutum magana yaji dadi (Al kalimatu dayyibat sadaqat)kazo kana wa mutane magana cike da isa da izza wa kaajie anan ? sannan su waye suka yiwa kamfani taadanci da fashi da hamdame kudin kamfani ?"sun san kansu !mr ata yayi mgnr tmkr ba daga bakinsa mgnr ta fito ba ,ya cigaba da sauraron some ."

D'akin taron ya sake yin shiru babu wanda ya sake magana hatta yaya Ibrahim bai tofa albarkacin bakinsa ba illa ya zuba tagumi yana ji kuma kallonsa kuma hukuncin adam yayi masa daidai muryarsa a dake mr ata yace " ina jiranku rashin dawo da kudad'an nan fa daidai yake da bari aiki acikin wannan ma'aikatan ya fad'a yana kallon gefensa inda some Ke zaune tana qara masa bayanin wasu a abubuwa" idan haka ake son mutun yasan kuskurensa har gyara da mutane dayawa basu gyara kuskurensu ba sannan dan haka malamanmu suke koyar damu wallahi da babu wanda ze juri zaman islamiyya ba kafi fili ka fad'a mana su waye masu laifi musani ba ka tsaya jin kai da girman kai ba ,dan anan babu wanda ka ajiye , yadda kake iko da wannan kamfanin haka muke..."

"Enough ! ya fad'a a matukar fusace yana dukan table "ka shiga hankalinka ,su waye mahamdama macuta yan fashi daya wuce ku " sam gaku nan tamkar. mutane amman baku da bambamci da dabbobi ,sam babu jin tsoron allah acikin zuciyarku , sultan ,fahad , hamid a wani goma sha biyu kawai na baku ku dawo da komai idan ba haka ba..... "me zakayi ?sultan ya katseshi cikin zafin rai "me ka isa kayi ?babu abinda ka isa kayi "
"kunsan su dabbobi basu gane yaren biladam sai na dabbobi yan'uwansu dan Allah karku dawo da kudaden nan alokacin da nace "yana gama fadar haka ya mike tsaye ya tura kujerar daya tashi baya ya fice ."nan hayaniya ta kaure kowa na fad'ar albarkacin bakinsa kai tsaye mr ata office dinsa ya koma ."

Karfe biyu daidai na rana mami na zaune a parlour tare da yaranta maryam da nana hauwa'u suka jiyo sallamar baba qarami sai da gaban mami yayi wata irin mummunar faduwa ya qarasa shigowa yayi wa kanshi mazaunin nana hauwa'u ta gaishesa haka ma maryam ya amsa fuskarshi babu yabo babu fallasa mami ta kallesu alamun su basu waje ,bayan sun tashi sun wuce mami ta fuskancesa alokacin da shima ita yake kallo "zulai naji shiru akan maganarmu banji kin neme ni ba har gashi an saka ranar auren adamu da wacan yarinyar yana da kyau nasan inda maganarmu ta kwana abun nan zai yuwa ko kuwa ?".

mami ta numfasa gabanta na faduwa domin dai ita kam bazata iya sake kuno wa danta wata damuwar ba maryam ma da yaya ya karbeta ?gara kawai ta ari bakin adamcy tace masa a'a tunda tasan ko ta tunkaresa da batun bazai ta'ba amincewa ba cikin shakkakiyar murya tace "nayi masa magana ammm..."sai tayi shiru tana jin nauyin fitowar maganar "amman me ki fada min abinda yace "Uhm daman cewa yayi wai mace daya ta .."
shiru tayi ta qasa qarasa maganar ganin wani irin kallon da baba qarami ke mata ido cikin ido furzar da iska yayi ya lashi lebansa na kasa sannan ya hade hannunwansa still idanunshi na kan fuskarta cikin danne fushinsa dan baya son ta gane fushinsa a fili saboda abinda kan iya zuwa yazo bare su suyi zargin da hannunsu ,cikin dakewa yace "yanzu dai kin nuna min bazan iya zuwa neman alfama wajenki kiyi min ba ko ?sam sam ba haka bane kai ma kasan halin adamcy idan kuma zaka iya masa magana da kanka to kayi kamar ma haka zai fi "no ba sai nayi masa kema uwarsa da kika haifesa bai ji maganarki ba maganar ubanwa zai ji ? " iya abinda ya iya fada kenan ya tashi ya kama gabansa ya barta cikin zullumi."

Mr ata a matukar gabalaice ya qaraso gida zuciyarsa tamkar zata kama da wuta , sai dai cike da qasaita ya shigo parlour'n Mami babu kowa parlour'n sai qarar tv da motsin masu aiki a kitchen ya zauna akan doguwar kujera ya d'ora kafarsa d'aya akan d'aya yana ciza gefen lips dinsa ,ko cikakken second goma bai yi da shigowa ba sai ga hindu ta shigo dan akan danunta ya shigo tunda mahaifinta ya fad'a mata yadda sukai da Mami ta kasa tsaye ta kasa zaune , zama tayi a kujerar dake fuskartashi ta tsura masa idanunta tana kallonsa tamkar ranar ta fara ganinsa tana qoqarin bude baki tayi masa magana ya mike tsam ya kwashe wayoyinsa ya haye samansa yana jan tsaki dan shi ya tsani yawon kallo , kamar ta dakatar dashi amman ta kasa ta cigaba da zama zuciyarta na mata wani irin bugawa akanshi ."

tana nan zaune har mami ta fito sanye cikin doguwar rigar na atamfar super exclusive sabuwar bugu ,mami bata tsufa saboda tsanani tsafta da gyaran jiki fuskarta a sake tace "a'a hindu yaushe kika shigo ?ban wani jima ba mami nazo wajen yaya ne "to ai bai shigo gidan ba tukun .
ya shigo yanzu ya hau sama "to shikenan bari naje dakin nasa nazo har ta juya hindu ta kirata sunanta cike da rauni "mami !"
Cak mami ta tsaya tare da juyowa ta tsurawa hindu ido "mami da gaske kin yiwa yaya adam maganata yace miki a'a ?"shiru mami tayi shiru ta rasa me zatace mata kafin mami tayi wata magana hindu ta cigaba da mgn cikin rawar murya "dan girman allah mami karki yi min tsakani da ya adam kullum zuciyata tafasa take akan sonshi Ke kad'aice zaki iya taimakawa zuciyata idan ba haka ba zan mutu cikin rawar murya mami tace "mutuwa kuma ?"kanta ta gyada mata tare da cewa "da gaske zan kashe kaina shine fansa akan soyayyar ya adam "na shiga uku ni zulai "mami ta furta acikin zuciyarta "kiyi addua hindu ni kaina zan só adamcy ya auri mata fiyye da biyu amman raayinsa ne auren mace daya macen dayan ma da kyar ya amince amman Kiyi addua nan gaba idan rabo sai ya qara dake da sauri ta runtse idanunta kana ta koma ta jingina bayanta da kujerar da take zaune tana jin wai irin faduwar gaba mai tsanani ahankali take zubar da hawaye ganin da gaske tarasa farincikin rayuwarta "anya kuwa mami nada tausayi da imani ."Anya mami bata da son zuciya ?"Tayi wa kanta tambayar tana jin radadi acikin zuciyarta bazata iya jurar rashinsa ba ,bazata iya ganin da wata a matsayin matarsa ba, yadda bazata zama matarsa a farko ba to babu wacce zata zama "hindu bari naje naga yayanku nazo hindu ta bude idanunta da kyau tana kallon bayan mami dake taku ahankali."

Kai tsaye kitchen ta shiga ta bud'e firdge kwalin dynsimo mai sanyi ta ciro ta rufe ta qarasa inda cup's suke ta dauki daya ta daura akan qaramin tray ta fito ta wuce a parlour ta samesa zaune akan kujera yana sanye da singlet da gajeren wondo ta bude kwalin juist din ta tsiyaya a glass cup taja qaramin table din glass din dake tsakiyar dakin ta dora tray ta mika masa cup ya girgiza mata kai tace "na kawo maka ruwan sanyi ?ya sake girgiza mata kai "coffee fa ? still dai kai ya girgiza aranta tace yau dai akwai damuwa ta d'an zauna gefensa "ka daina barin damuwa na hana zuciyarka sukuni "naji sweetheart amman ba wani damuwa bane zazzabi nake ji kawai "sannu bari naje na kawo maka magani ka sha "no need sweetheart thank you "kai har yanzu bakasan ka girma bane meye abun gudu a magani ?ni dai kawai bana só né da zarar na kwanta nayi bacci zanji daidai ,tô karka kwanta yanzu magariba ta kusa ya gyada mata kai yana mai runtse idanuwanshi ta mike tana cewa "me zaka ci dan tuwon shimkafa kayi yau idanunshi ya dan bude kadan "karki damu sweetheart yau bazan ci komai ba amman zuwa anjima I need coffee tasan haka tsarinsa yake wani lokaci sai ya kwana ya yini bai ba ."

*****

Tsawon kwana Uku kenan rabon maryama ta shiga harka mahaifiyarta har ma da habibi hakan kuwa ba qaramin taga masu hankali yayi ba gabadaya gidan yayi wani iri saboda rashin walwalar maryama ,ta kuma san duk akan abinda take son tayi ne domin tasan halinta tasan abinda take so da abinda bata só tana da tsananin hakuri amman idan kaga ta kafe akan abu to dole abun zai zama gaskiya ne ko alkhairi ga rayuwar mutun ,ta sani gsky take fad'a mata amman bazata iya abinda take bukata ba bazata ta'ba komawa garesu ba duk runtsi duk wahala zata daure ta cigaba da rayuwarta a yadda take yi , maryama fa ta dauki zafi sosai akan aunty da habibi duk lokacin da ta fito parlour'n tagansu sai ta koma daki ko taje bangaren umma bata dawowa sai dare da zarar tashigo kuma zata shige daki tayi kwanciyarta ko ta dauko kayan zanenta ta fara aiki ."

Da misalin karfe tara na daren ranar litini maryama tana zaune akan kujera ta cilla pencil a bakinta tana taunawa a hankali idanunta na kallon celling dakin tana nazarin abinda zata zana taji an turo kofar d'aki ahankali ta kai dubanta ga kallon kofar dakin ,aunty ta gani tsaye ,ta dauke kanta daga kallonta, aunty ta maida murfin kofar ta rufe ta soma takowa zuwa inda maryama take tana ganin haka ta mike tsam ta haye saman gado tayi kwanciyata tare da kamkame jikinta tana jin tausayin kansu na sake ratsa ko ina ajikinta musamman  take jin kewar yanuwan mahaifiyarta da bata taba daura kwayar idanunta akansu ba amman tana jin ajikinta zasu samu kulawarsu da soyayya a duk sanda suka had'u kamar kowani dangin uwa tana kallo aunty ta zauna daidai inda fuskarta take dan hk da sauri ta runtse idanunta tana son tayi bacci ."

bacci bai samu nasarar d'aukarta ba ta juya dayan bangaren sakamakon kukan da Ke shirin kufce mata dan ita kanta dauriya kawai take akan sabon canjin data kawo a tsakaninsu hakan bai hana aunty ganin abinda take ba ,daidai inda  fuskarta ke kallo ta dawo ta zauna tana dubanta hade da kamo hannuta cikin nata "me nayi miki my princess kike qoqarin Kaurace min byn Kinsan bani da kowa bani komai sai ku ? Kafin maryama tayi yunkurin cewa wani abu aunty ta sake jiho mata wata tmbyr "yanzu na cancaci haka a wajenki ,"?"Na lura kina bukatar rayuwata princess "idan kika bari damuwarki ta kasheni shikenan sau ki huta ai .... "
a d'an zabure maryama ta mike zaune daga kwance da take suna fuskatar juna da aunty yayinda hawayen idanunta suka shiga xubowa sharrrrrrrrr....."

  " meye kuma abun kuka daga magana "kiyi hakuri aunty nasan damuwata na damunki ina kukan ne saboda an cuceki an rabaki da yanuwanki da iyayenki alhalin suna sonki , bansan yadda zan misalta miki yadda nakeji ba, aunty ki taba zuciyata kiji yadda take bugawa tayi mgnr tare da  kai hannuta ta kamo hannu aunty ta d'aura daidai saitin zuciyarta dake wani irin bugawa tamkar ana buga mata guduma, tabbas aunty taji kokawar da zuciyar keyi amman bata yadda zatayi gurin raba zuciyar da damuwa addua dai ce kuma tana kanyita babu dare babu rana kuma tasan  ubangijinta baxai barta haka ba batare daya duba lamarinta ba.

cikin murya me cike rudanin rayuwa maryama ta cigaba da mgn "bansa me zanyi abubuwa su dawo mana daidai ba har ki cigaba da rayuwarki kamar da? " aunty ki daina daukar iyayenki da yanuwanki a matsayin makiyanki ,iyayenki suna sonki fiyye da tinaninki ,sun nuna miki so da kauna tattare da kulawa da gata alokacin da kike zaman lafiya dasu aunty kema kanki Kinsan irin soyayyarsu garenki "aunty !!! ki daina ganin laifinsu sannan ki dai jin zafinsu dan su dauki fushi dake ?"

Su iyaye ne zasu iya yin komai suci lafiya a yanayin yadda rayuwa tazo miki cike da rudanin  yaci ace zuwa yanzu kin samu y'anci ki tsinci kanki cikin  farinciki da jin dad'in rayuwa kwana uku kawai da baki ga walwalata ba kin daga hankalinki inga bana cikin gidan nan ?"ina ga nabi wani na barki ya zakiji ? wallahi iyayenki suna can cikin tsananin kewarki kwatankwacin yadda kike jin namu da zaki koma garesu zasu karbeki su kuma yafe miki " kiyi hakuri aunty ki daina ganin laifinsu ta karasa fadar haka tana xubda wasu zafafan hawaye hade da rike hannun aunty gam tana me tausayawa rayuwarta ."

"Idan abubuwan dake faruwa suka cigaba da faruwa bana tinanin zuciyar dake kirjina zata cigaba da baguwa ni dai ki koma cikin yanuwanki dan Allah ki roki gafarar iyayenki su yafe miki mu cigaba da rayuwarmu kamar yadda muka saba . ahankali aunty tashiga bubbuga bayanta "kukan ya isa haka
Inshaallahu zan .. zan.. koma garesu da izinin Allah sosai aunty ta dinga rarrashinta da gaya mata maganganu masu dadi da sanyaya rai har  ta soma bacci ajikita cike da samun kwanciyar hankali .

Washegari kowa yasan maryama na cikin kwanciyar hankali wanda hakan ya kwantar da hankalin babib da aunty tare suka ci abinci kamar yadda suka saba ,maryama tana zaune a falo byn tayi wanka ta shirya tana kitsa gashinta gida hud'u sakina ta shigo suka sha hirarsu duk aunty na jinsu sosai taji dadi aranta ganin maryama ta saki ranta ,har sakina ta fita ta dawo "maryama amman yau zaki islamiyya?"eh!zani idan na gama zan biyo miki sakina ta qarasa fita ita kuma ta mike ta shiga daki tai sallah ta qara shiryawa ta dauki alqurani ta fito ta tsaya a bakin part dinsu sakina tana jiranta byn ta gaishe da aunty salma sakina ta fito ta tsaya kusa da maryama tana mata magana kasa kasa aunty salma ta bisu da harara har suka fice ,ta nemi guri ta zauna zuciyarta na tafasa ."

ta rasa yadda zata kawo karshen shakuwar sakina da maryama duk duniya bata da abinda ta tsana tamkar maryama tayi shiru cikin tsanani tunani abubuwa da dama take sakawa in dai da rai da lafiya sai ta rabasu domin itace kadai hanyar da zata nunawa maryama tsangwama da tsanar datayi mata shegiyar yarinya kamar mayya ko aljanna zatace banda abun sakina ai maryama matsala ce arayuwarta, yanzu ko saurayi idan sakina tayi yayi ido biyu da maryama ai tuni zaice shi ga wacce yake so yarinyar ta cika kyau haka kamar ita tayi kanta ta fad'a acikin ranta ta mike tsaye cikin takaici to ko afa zata kaiwa kukanta , zuciyarta ta kawo mata dauki da wannan tunani aikuwa hakan shine mafuta afa shine zai kawo mata karshen komai da karshen wannan shakuwartasu mayafinta ta dauka ta yafa ta fice daga gidan tana surutai ita kadai kamar yadda na shiga na fita na rabaki da duk wanda yazo da sunan yana sonki da aure yanzu ma sai na rabaki da sakina takowani hali ki cigaba da rayuwarki Ke kadai Kmr mayya acikin gidan nan ."

Tayi sallama aka amsa mata daga ciki dan haka ta shiga ta tsaya afa da yake ciki bai amsa ba yayi gyaran murya hakan ya tabbatar mata akwai wani aciki ta dan jira na rabin awa sannan wacce take ciki ta fito suka gaisa ta fice a karo na biyu tayi sallama ta shiga cikin dakin ta durkusa ta gaishe shi yana zaune akan daddumar sallah wani katon tray mai cike da katon kasa da wuri na duba ya amsa mata cike da kulawa "meye ma sunanki yaushe rabon na sakaki a idona ?"Aunty salma tayi murmushi tace afa kenan abine sai ahankali idan ka ganmu tamu ce ta kawo mu yayi murmushi ya dan shafa gemunshi yana lashe lebensa "to ina jinki fara bayanin abinda Ke tafe dake kafin na duba naga gskyar lamari ".

Mmm sudais
💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura wa wannan 0913691 8331  alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

        Page 15

"Aisha ,  saber, da   mahamud ,  ta  gani   tsaye  akansu  suna   huci   kamar   zakuna  cikin  matsanamcin  tashin  hankali   mara misaltuwa  suna   kallonta   kamar   zasu  cinyeta  ai  babu  shiri  daga  bilkisu  har  ussein   suka   mike   daga   jikin   juna  hankalinsu yayi  mugu  mugun   tashi   ."

    bilkisu  ta  tsaya  tana  kalle  kallen   inda  zata  boye  acikin d'akin  tare  da  cure  hannayenta  waje   d'aya  jikinta  na sake d'aukar  rawa  bata  ta'ba   shiga  tashin  hankali  da  nadama  irin  na  ranar  ba domin  har  ga  Allah  bata  ta'ba  tunanin   zasu   bibiyi takunta  ba ."

Nan da  nan  idanunta  ya   kawo ruwan  hawaye ba  tace  komai  ba, ta    durkusa qasa  bisa  gwiwo
winta   dan  tasan  sai   na  lahira  ya  fita  jin  dadi  mahamud  ya  rike  kungunsa  yana  cigaba  da  kallonta  ,mamakinta  kawai   yake  dawainiya   dashi  idan  aka  fad'a   masa  cewar   zata  biyo  nmj   har  d'akinsa   bazai  ta'ba yarda  ba,  watakilla   ma  da  sai  ya  wankawa   wanda  ya  fad'a  masa  hakan   mari  "dan   girman  Allah  kuyi   hakuri   ku  yafe   min  ku rufa  min  asiri   kar  mumy   tasani  ta  karashe   mgnr   tana   kuka  cikin  tashin  hankali mahamud   ya  buga  mata  wata  razananniyar  tsawa  data  hargitsa  mata  lissafi "yi  min  shiru  makira  bana  son   jin  komai  daga  bakinki ."

nan   take   tayi   shiru  kukanta ya  qaru ta   kalli  inda  ussein  yake  tsaye    shima   kana  kallonsa  kasan  baya  cikin natsuwarsa  "mahamud   tsayawa  kayi  kallonta  bazaka   fara cin  ubanta  tun  anan  ba ?  Aisha  ta  fad'a  tana  mata  wani   irin kallo  shi kuwa wanda aka kira  da  mahamud  tunanin yake  idan  yace  zai  ta'bata to  babu  shakka  zata  mutu  idan kuwa bata  mutu  ba  zata  jikata ."

"dan  girman  allah  Aunty ai.."ai  bata  kai  ga  fad'ar  abinda  take  son fad'a  ba  taji  wani   gigitaccen mari   hagu  da dama akan  kuncinta "you  are  very  stupid   bilkisu  , akanki  aka  fara  soyayya?"  kin  haukace  kin  makance  akan  wannan  banzar  ,me  yasa zaki  mance  ko  ke  wacece ?  wato soyayya  tasa  kin  manta  matsayinki ? cikin  muryar  kuka tace " a'a   Aunty  aisha   ban   mance   ba  amman  kuyi  hakuri  wallahi  bazan   sake  ba  "hayaniyar  yan   yan'uwanta  ya sake   d'aga  mata  hankali   shi kuwa   ussein  sunkuyar  da  kanshi. kasa  yayi   yana  tunanin  ficewa ya  bar  d'akin  dan  yasan Allah ne kawai  zai   kwacesa  a  hannunsu ."  

Kai   tsaye   bilkisu   ta  nufi   bayan kofa  ta   boye  jikinta  na  wani  irin rawa  sakamakon   jiyo  muryar hajiya  rahma  tana  cewa "ina bilkisu  take  naga kun  tsaya  jugun   jugun  ko  ta  gudu ne ?  kafin  kace  me  an  samu  wanda   yazo ya  fad'a  mana   halin   da'ake  ciki a guje  na  bazamo  na   bar  hajiya  dan   bazan  iya   jiranta   ba kasancewar  tana  fama da  lalurar  ciwon kafa ."

" ina  tafiya  ina  neman layin  yan' uwansashi   da  kyar  na  samu ta  abban  sadam  yana  gama  jin bayanina  cewa  yayi  babu  ruwansa  dan  yasan  halinsa da tara  yammata , babu  yadda banyi dashi  ba yace  bai  zuwa  koina  ya kashe  wayarsa  jin abinda  ya fad'a yasa  na  kira  yayyensa   mata ."

Ina   shiga   unguwar  naga   jamaa  sun   yi   cirko   cirko!!  ga   manya  manyan   motoci  na  gidansu  bilkisu  jere a  kofar  gidan ,haka  ina  shiga   cikin  gidan  mutane  na gani  makil   kowa  na   fadar  albarkaci   bakinsa ,yayinda  muryar   mahaifiyarta  ya  karad'e  koina   acikin   gidan   "da  gaske  ne  bilkisu   tana  cikin wannna  ru'babben  d'akin ? Aisha ta  nuna  mata   bayan   kofar d'akin  "tana  ciki   kuwa  ga  makira  nan a bayan  kofa   ta  fad'a  tana   zubar  da  hawayen  takaici  ."

"inna  lillahi !  hjy  rahma ta furta  a fili  cikin  tsananin  tashin hankali "kunji   abinda  naji  kuwa  wallahi  ji  nayi   zuciyata  kamar ta  buga ?hankalin  bilkisu  ya bar duniyar da  muke  alokacin  dan  sai  wuri  wuri  da  idanu  take  shi  kansa  ussein kana  kallonsa  kasan  nadama  ne  acikin   ransa  nadama  irin  wacce bata  da  wani rana ."

" amman  bilkisu  bakince  min kin rabu  dashi  ba  ?jikinta  na  rawa ta  shiga  gyada  mata kai  alamun Eh! tana   bawa mahaifiyarta  hakuri  da  wani  irin  fushi  ta  juya  inda  ussein  yake   cike  da  nadama ta shiga  zabzabga  masa  mari  ta koina "bana  ce maka  ka rabu  mun  da  yarinya ba  ? ba  banace karka  sake   shiga   rayuwarta  ba?"Ko kaga  yarinyata   tayi  kalar  wacce  zaka ce  kana so ? ta  juya  zuwa  ga  bilkisu  " Ke yanzu  har  wannan  qazamin  ne  abun  so  a wajenki  ? ta  fad'a tana sake   juyowa ta  d'aga hannu  zata  sake  tsinkawa  ussein  mari  nayi saurin   rike   mata  hannu  ina bata hakuri  "kiyi   hakuri  hjy sam  ussein  bai  kyauta  ba  daya  bawa  yarinyarki damar  zuwa  inda  yake  ,ya  karbi laifinsa  ayi  masa  afuwa   in sha allahu  hakan  bazai  sake   faruwa ba   Kinsan   kowa da irin jarabawarsa  dukkanin  rayuwa  rubutaccen   lamari ne daga  Allah ,kuma   kowani  dan  Adam yasan  da  haka  ,yanzu  tunda  abun  ya  zama  haka ku bamu  dama  sai  mu  turo ayi maganar  aure "."

Wani  irin  kallo  gabadayansu suka  bini  dashi  ,hjy  rahma  tace  "Allah ya  tsareni  na   had'a  zuria da wannan  ta  nuna  ussein  da  yatsanta  tana  hararsa "wallahi   bilkisuna  tafi  karfen  aurensa  ki kalleta  sama da qasa  ki  kallesa ta  ina   hadin yayi daidai  ?  duk  nasan  da  haka  hjy  amman  a wajenta  shine daidai    bugu da qari   rayuwar  yarinyar ku  zaku duba  domin  ita  diya  mace ce zata  iya fad'awa  kowani hali ."

"Ba kowani  hali  zata  fad'a ba ko  mutuwa  zatai  sai dai ta mutu na yarda  na   rasata   gbdy  akan na bawa wannan   matsiyacin aurenta ta  numfasa  tare  da sa  tafin hannunta ta  share hawayen idanunta  "hjy  ki  daina furta  haka  shi  soyayya   allah ne  yake had'awa  , kuma  babu  ruwan soyayya  da  tsiya ko arziki  yarinyar  nan tana  qaunarsa  shima kuma  yana  sonta dan  girman  allah  ki  barsu  suyi  aurensu  kowa ya huta  sannna  babu  wanda  yasan matsiyaci ko  mai arziki  sai Allah  sannan babu wanda  yasan mai gobe  zata  haifar  ku barsu  su  aure juna   domin   samun  kwanciyar hankali ."

bata   kulani  ba  har  na  dasa aya ta fuskanci  bilkisu  yayinda  gabadaya  yanuwanta   kacokan  suka  maida  hankalinsu Kan  ussein  duk  sun qagu  suga hukunci  mahamud  akan  ussein kasancewarsa  soja ,  hjy  rahma  ta  matso  sosai  kusa da  bilkisu tana cewa  "ba  dai  ni  zaki  wulakanta   akan namiji  ba ? ."babu  irin  rarrashin da ban miki ba ,babu  irin  hakurin da ban baki ba ,me  kike  son  dani  ? "wallahi  zanyi  dake  bilkisu , yau  zaki ga tozarci  ganin  idanunki  tunda kika nemi ki  wulakantani akan wani banza  can  wanda  ba kowan kowa  bane  shi  ,ba kowa bane  iyayensa   a  duk  fadin  garin nan hasalima rayuwarsa  a  banza take ."

"zaki  wulakantani  akan  wani nmj banza da  wofi  wallahi  zanyi  dake muddin  kika  ce  shi  zaki aura sai na  tsine  miki  na  tsinewa  auren ,wallahi auren  bazai  ta'ba  yin albarka tana  mgn  tana   zabga mata  mari a fuskarta da bayan hannunta  , yayinda  azaba tasa bilkisu ta shiga  karewa  dan kar marin yayi mata illa amman matar nan sai zabga mata maruka take kuma a fuska na rantse miki da girman allah maryama tayi mata mari yafi guda tara ajere ana goma ne bilkisu ta rike mata hannu kuma nasan azaba ce tasa tayi haka ,aiko matar nan ta  danneta da iyakacin karfinta ta dinga dukanta  tana cewa ni zaki rikewa hannu in sha allahu kema sai ya'yanki sun miki abinda kika min ,sai sun hanaki kwanciyar hankali kamar yadda kika hanani kwanciyar hankali a karshe  kafa mata hakori a  damtsen  hannunta."

"wani irin  gigitaccen  qara  bilkisu ta saki mai ban  tausayi  tana  kuka  tana neman  d'auki  gashi  babu wanda ya  kwaceta  daga  hannun mahaifiyarta sai dukanta  take tana hadawa  da  zagi  ganin  haka yasa ussein  ya  nufi   hjy rahma cikin tsananin  fushi  kamar mayunwanci zaki  idanunshi  sun kad'a sunyi jajur   yasa  duka hannunsa zai d'agata  daga  Kan  bilkisu ai  ganin ya  ta'ba  mahaifiyarsu  gbdy yan'uwanta  suka yo Kanshi shi da  bilkisu  cike  da  jin haushi suka dinga dukan su  kamar zasu kashesu suna furta mahaifiyarmu zaka  duka ? azahiri gaskiya ba wai dukanta yayi  ba  kawai ceton bilkisu zai yi  daga dukanta, ina kuka ina basu  hakuri ina qoqarin kwatarsa daga hannunsu amman ina sarkin yawo yafi sarkin karfi dan sai suka daina dukan bilkisu suka cigaba da dukansa  shi kad'ai har sanda hjy  ta shigo zubewa tayi kasa tana kuka tana cewa "zaku kashemun d'a ne to wallahi idan kuka kasheshi hukuma ce zata rabamu  daku dan wallahil azim  bazan ta'ba  yarda ba ".

"kar Allah yasa ki yarda daman kece uwar matsiyaci ?  "nice  uwarsa  kuma  gatansa kuma ni d'ana ba matsiyaci bane dan me zaku masa haka ?
"ai yarku zaku jawa kunne ta daina zuwa inda yake shi meye laifinsa ? "laifinsa kulata da yake yi idan baya  kulata bazata zo inda yake ba ,idan yace baya sonta karta sake zuwa inda yake ni nasan bilkisu bazata zo inda yake  ba ki fad'a masa da babban murya ya rabu da kanwarmu  ya zauna lafiya idan ba haka ba zamu 'batar dashi agarin nan ,kina ji kina gani zaki rasa d'anki har abada  "hjy  na fad'a 'yanuwan bilkisu na maida mata martani kuma basu daina dukansa ba ."

"neman layin 'yanuwasa mata na sake yi saadatu na d'auka na saka mata kuka ina cewa "bazaku zo ba sai an kashe maku da'nuwa ?dan girman allah kuzo ku hanzarta karku bari su illatashi "bilkisu cikin kuka ta rarrafa ta rike kafafun mahamud domin duk yafi dukan ussein cikin kuka tace "yaya dan girman allah kayi hakuri ka barshi karku kashe min rayuwata sannna karku rabani da dashi wallahi bashi da laifi nice mai laifi" .

"ya salam! ya furta a matukar fusace "wai bilkisu me ke damunki ne  "?ta girgiza masa kai idanunta na zubar da ruwan hawaye  kuyi hakuri nayi maku alkwarin bazan sake zuwa inda yake ba "muryar hjy rahma ta sake karade d'akin Aisha riko hannun makaryaciya  karta gudu shi kuma sheidani ku fito min dashi yau zan nuna masa koni wacece agarin  nan zanga uban da ya isa ya kwaceka Aisha ta riko hannun bilkisu  gam bisa umarnin mahaifiyarsu sai dai bilkisu ta dinga turjewa nan ma wani marin aisha ta kai mata tuni daman fuskarta ta canza jini ya kwanta a duka idanunta ."

Mahamud kuwa qarasawa  yayi inda ussein yake yace ya kama kunnensa ussein ya kama kunensa cikin kaduwa dan gbdy bai fahimci abinda yake nufi ba mahamud yace "you're very stupid I mean kayi frog jump Aishat ashe ma illiterate ne wallahi ko da wasa naji ka qara shiga harkar bilkisu zan mugun baka mamaki  "mugun ma illiterate katon jahili liability kawai a haka zamu bashi aurenta sai kace kwakwaluwarmu ta juye  ai har abada ,ka wuce dashi kaci ubansa ta yadda ko mai kama daita ya gani da mugun mugu zai arce ."

bilkisu na kuka ussein na frog jump nima ina biye dasu ina basu hakuri haka hjy hakuri take basu hankalinta a tashe muna fitowa kofar gida sai ga saadatu da fatima a rude basu tsaya  neman baasi ba dan na rigada na fad'a masu komai  sausauci suke neman masa amman mutanen nan  suka ki banda cin mutunci babu abinda suke zubawa  unguwa kuwa ya cika makil da jama'a yan kallo kowa na fadin albakacin bakinsu wasu suna ganin daidai ne matakin da suka dauka dayawa kuma laifin bilkisu suke gani  ."

wani abu mai daci yan'uwansa suka hadiye  tare da matsowa  inda mahamud yake yana laftawa ussein belt a gadon bayansa "yanzu ina zaku dashi ?In ji cewar fatima  tayi maganar cikin tsananin fushi "zamu tafi dashi inda zamu sake koya masa hankali,"  ya fad'a cike da gadara da isa "amman yana  da kyau mu san inda zaku da d'anuwanmu kafin ku wuce dashi?  Eh ! yana da kyau sai dai  bani da wannan lokacin  'batawa idan aka koya masa hankali zaa iya sanar  daku kuzo ku d'auki abinda ya saura ajikinsa "

Hjy kuka saadatu kuka haka ma fatima muna cikin wannan halin sai ga gali yace shine yayansa suyi hakuri su bar komai a hannunsa zai sa ya rabu daita rabuwa ta har abada ,mahamud yace "da dai ya fiyye masa  kwanciyar hankali dan wallahi na sake dawowa akan case din nan sai dai ku dauki gawarsa" gali yace "to mun gode komai yazo karshe bilkisu ta bude idanunta da  suka mata nauyi  wani marayan kuka ta fashe dashi tana shesheka tana kallon kowa wanda ni nasan kukan da take alokacin bai wuce na rabuwa da ussein ba ."

fatima ta watsa mata harara hade da kallon banza tana cewa  "kukan uwar me zakiyi wa mutane duk bake kika jawo masa matsala ba  yana zaman zamansa muguwa  azzaluma kin janyo yanuwanki sun wulakanta mana d'anuwan an tozarshi, tunda muke anan unguwar aka haifemu muka girma mukayi aure baa ta'ba wulakantamu ba sai yau kuma duk akanki ,kinsa ana dukansa kamar an samu ganga na rantse da girman allah  matukar ussein..."

saurin toshe mata baki nayi ina cewa  fatima karki rantse  ,cikin fushi ta cire min hannu "ki barni  aunty nayi magana kalli yadda fuskarsa tayi duk jini saboda Allah yau ayita ta qare ta kama kanta ta daina zuwa inda yake ,yanzu da suka zo suna hargagin banza da wofi da wulakanci shi meye laifinsa? yarinyarsu ya dace suyi wa magana ta daina zuwa inda yake dan muddin ta sake zuwa inda yake kafin ku dauki mataki mu zamu dauka dan ba daga sama ya fado ba azzaluman banza kawai kuma allah ya isa tsakaninmu daku tana fad'a aisha na fad'a."dan girman allah fatima  karki sake cewa komai zo muyi magana na janyo hannunta " babu inda zani aunty ayita ta qare gwama su san muma bama son wannan diyar tasu kuma komai zai faru ..."
na sake toshe mata baki "dan Allah ki bar mgnr nan  sulhu ake nema ."

Cikin ko in kula hjy rahma tace  da wa zakuyi sulhu ?"kema  Kinsan ruwa ba sa,an kwado bane baku kai wannan matsayin ba yanzu ma wannan maganar da nake duk sai na fashesa akan wannan matsiyacin "nayi tsuru tsuru ina dubanta "tsayuwar  me kukeyi ku taho min  dashi da sauri  gali ya qaraso inda take hjy ai mun gama magana da yaronki, dan allah hjy kiyi hakuri ,in sha allahu tunda muka shiga cikin zance komai yazo karshe zanyi magana dashi  "babu irin hakurin da baa bawa hajiya rahma ba amman  tace sam sai an tafi dashi haka muna ji muna gani aka watsa useein abayan boot din mota aka wuce da
ussein ."

Kuka sosai maryama take kamar alokacin komai ya faru Kwantar da kanta umma tayi akan cinyarta tana rarrashinta "tabbas Aunty masoyiya ce ta gaskiya ,ta so mahaifinmu a halin babu ,ta zauna dashi har karshen rayuwarsa wallahi ba kowani d'an mai kudi bane mutumin kirki kamarta ,ta tsaya ta dubi mahaifinmu da kalmar so ta gaskiya
sai dai akwai illa umma Aunty ta jefa rayuwarta cikin matsala wanda a yanzu take shan wahala ".

" tabbas shine gskiyar dana dade ina nuna mata "baa jayayya da iyaye data yi hakuri tabi umarnin iyayenta tabbas zasu sauko dan kansu kasancewar akwai rabo a tsakaninta da mahaifinku ,cikin muryar kuka tace "mune silar jefa rayuwar mahaifiyarmu cikin wahala ko ? ta fad'a tana sheshekar kuka "karki ce haka maryama haka tata qaddarar take ,ita qaddara gata ko arziki ko nasaba bai isa ya canza maka ba ."umma ta numfasa sannan ta cigaba da magana ".

Bangaren su  bilkisu kuwa tunda suka dauki hanya  yan'uwanta suke magana suna zagin ussein cikin kuka bilkisu Ke rikon su "ku sani ussein bai muku laifin komai ba dan allah karku hukuntashi akan abinda bai yi ba"  mari mahaifiyarta ta kifa mata haka ma aisha dan ubanki ki kama mana baki har suka kai gida zaginta suke direba na ajiyesu ya wuce da mahamud da ussein ."

a matukar gigice bilkisu tabi byn  motar da kallo cikin tsananin firgici, keyarta suka tasa sai cikin bangaren hjy rahma ."Suna shiga part din hjy rahma suka turata daki  suka daureta da igiya tamau sukasa saber  ya dinga dukanta  adaure  tun tana ihu har tazo ta kasa a yadda ta fad'a min cewa tayi har da barkono  mahaifiyarta ta nika tasa mata a gabanta da cikin idanunta wanda yasa tayi suman wuncin gadi ."

Bangaren mu rana  babu wanda ya samu sukuni  acikinmu gali yafi kowa  shiga damuwa safa da marwa yake yana cewa "ban  ta'ba kawowa araina duk hakurin dana  basu ba zasu hakura ba , na dauka maganata zai sa su hakura amman ina kamar sake fusata mahaifiyarta nayi wadan nan mutane sam basu da imani ."wallahi basu da imani gali inji cewar hjy ka kalli irin duka da sukayi yarinyar nan bilkisu ko rikonta suke bai dace suyi mata irin wannan dukan ba ."

"wallahi ku sheida bilkisu bazata sha wannan wahalar a banza ba komai zai faru sai useein ya aureta ba dai bakinciki su kenan ba saboda suna takama da kudi ,ni bana da kudi amman ina da Allah alfarma annabi da alqurni sai wannan auren ya tabbata ko ina  raye ko byn na mutu mutane sam babu imani aransu bazai hakura da aurenta ba sai dai su mutu fatima zatayi magana ta dakatar daita "banason jin komai daga bakinku sai fatan wannan auren ya tabbata ."

abban sadam ya fito daga bayi daman zagayawa yayi yace "har yanzu bazaku hakura da wannan maganar ba ? hjy tace "taya zaa hakura?" da sukutun fa suka wuce min dashi ?naga diyarsu ce tunda sunce basaso tarayyarsu a hakura mana "bazaa  hakura ba bilkisu bazata  sha wahala akan ussein ya tafi a banza ba ina sonta tunda tana son jinina ta gama min komai ni yanzu ta'bo min abokika Abdul zanyi magana dashi babu irin kiran da baayiwa Abdul  ba amman wayar bata shiga ranar hjy bata runtsa ba kwana tayi tana kaiwa allah kukanta ."

Washegari ana idar da  sallahr asuba tasa aka cigaba da trying dinsa amman shiru baya shiga sai karfe uku na rana  ta shiga ya dauka da sallama byn sun gaisa hjy  tace "Abdul ko kasamu labarin abinda Ke faruwa da useein ?bansan me yake cewa hjy  ba amman naji tace "meye rashin kyautarwasa haramun ne dan  soyayya tashiga tsakaninsu ?saboda shi talaka ne yasa basu dace ba to shikenan nan in sha allahu gamu nan zuwa  ."

Tana gama waya tace muje gidansu  bilkisu mu samu mahaifinta   nace" a'a ta bari ni da gali da fatima  muje da kyar hjy  ta yarda  ta barmu muje babu ita sai dai fatima tace bata zuwa koina nace saboda me kai tsaye tace min ta tsani bilkisu da yan gidansu sai da saadatu da gali mukaje da taimakon Abdul muka shiga estate dinsu sai dai  baa bari mun shiga cikin  gidansu  ba a bakin get din gidan aka tsaidamu yayanta  abubakar muka samu gani muka gaisa dashi  babu laifi fuskarsa da dan rahma dan yafi mahaifiyarsa byn mun gaisa gali ya fad'a masa ko mu su waye  da  dalilin zuwanmu "ayi hakuri ranka ya dade ,hakika danuwanmu bai kyauta  maku ba domin ya shiga hurumin da banashi ba soyayya da diya irin taku shima yasan  bai dace ba , dan allah kasa baki ranka ya dade abamu ussein tun jiya da suka  wuce dashi baa dawo dashi ba ,dan  allah a maido mana dashi ."

shiru yayi ya kasa cewa komai ganin hk yasa gbdy muka kwantar da murya "ka taimaka kasa a sako mana ussein cikin ko in kula yace kuje zai dawo gida zuwa anjima amman kuja masa kunne ya fita a rayuwar bilkisu "in sha allahu komai yazo karshe cike da farinciki muka juya zuwa gida zaman jiran dawowar ussein ."bini bini sai mu leka waje ko zamu hangosa amman shiru har kusan karfe shadaya na dare har mun fidda rai dashi sai gashi an  shigo mana dashi bangaren hjy yana dingisa  kafa da kyar ."

da sauri muka taresa  dan gbdy muna tare har hassana wacce tafi kowa shan kuka hjy kam  cikin yanayi na tashin hankali ta isa garesa tana  kuka "yanzu haka suka maka ussein ,kawai dan kana soyayya da diyarsu allah ya saka maka ,allah ya bi maka hakinka alfarma annabi muhammadu sai bilkisu ta zama mallakinka "wai meye hk hjy ana kokarin ya rabu da yarinyar mutane ya huta da wahala  amman kina sake dagula masa lisaafi .

Gali ya fad'a yana kallon ussein "  kai ka rabu musu da yarinya idan ba haka ba wallahi komai ya sake faruwa babu ruwanmu  ,babu hannu babu kafarmu sai dai ka karata kai kadai dan bazamu iya wahala ba wadan nan mutanen marasa mutunci ne "wannan gsky ne  gali babu ruwanmu dan bazamu iya dasu ba inji cewar saadatu ,to ku yanzu laifinsa kuke gani bakwa ganin na yarinyar ?ai yarinyar tafi shi laifi domin ita Ke zuwa inda yake wallahi na tsani yarinyar nan ."

"koni  wallahi na tsaneta maryama  wannan shima mafarin tsanar yanuwan mahaifinki ga mahaifiyarki alokacin ina kallon ussein wani irin numfashi mai zafi ya fesar kana ya samu waje ya zauna da kyar ya daura kanshi akan  hannun kujera ya kwantar tare da lumshe idanun shi  yana jin duk abinda kowa yake fad'a daya byn daya bayan wasu mintuna  ya kuma budewa  yana kallon kowa cikin sanyayyar murya yace "in sha allahu na rabu daita har abada dan  kwana ne kawai a gaba da na mutu "ka kwantar da hankalinka muddin ina raye baka da mata sai bilkisu ka daina cewa ka rabu daita dan na nasan kana sonta har yanzu ."

"haba hjy wai me yasa kike fadar haka Kmr baki tausaya masa ? "yanzu ku yarinyar nan bata baku tausayi  ?ita ma ba laifinta bane soyayya ce da qaddara ke tangaliliya da rayuwarta dacen iyaye ne batayi ba shiyasa take shan wahala amman itama abar a tausaya mata ce "gsky mu dai bamu yarda ba kuma ta ina zasu bada aurenta byn kina kallon haukan da suke akanta ? kusa ido kuga ikon allah muna zaune zasu nemo mu da maganarta da izinin allah "babu wanda  yace uffan kowa ya mike ya kama gabansa ."

****
Bayan wata  biyu da faruwar komai  mahaifiyarta ta shiga neman taimako akan  bilkisu dan kawai ta rabu da ussein , yau akarbo taimako daga wannan malamin gobe akarbo daga wancan malami , akwai inda aka kaita sai data  d'auki alqurni ta rantse  akan zata rabu da ussein , hankalinta  ya tashi matuka taki amsa  ta firgita kwarai da lamarin mahaifiyarta  ."
fito da duka idanunta tayi tana furta tashi uku bataso ba amman mahaifiyarta na kallo mutumin yasa ta dauki alqurni tayi rantsuwa ta rabu da ussein har abada alhalin ita a zuciyarta ba haka bane "

babu laifi  bilkisu ta  zauna lafiya kamar sauran  lokutan baya ta cigaba da rayuwarta gudun kar qurani ya cita ,yanuwanta suka dan sake mata kadan haka mahaifiyarta  tun tana gudun abinda zai je ya dawo har ta hakura ta sake janyota jikinta kullum da irin nasihar da take mata  "bilkisu ki  zama mutuniyar kirki ba wai baa sonki bane yasa kika ga anayi miki duk abinda aka  miki ana sonki ne yasa ake gudar miki wahala ,auren wannan yaron wahala zai zame miki arayuwarki , bakya ganin sauran yanuwanki ?kowa na cikin jin dadi me yasa sai ke kadai ce zaki zabar wa kanki wahala?  "

tace "kiyi hakuri mumy ina tsananin son ussein amman zanyi  iya kokarin na cire sonshi araina "ko kunyi imole ne ?hjy rahma ta tmbyeta ."tayi shiru tana kallonta" baku ta'ba shan jinin juna ba ?ta girgiza mata kai  alamun a'a to ko ya ta'ba kwanciya dake ne ina nufin sex ?shiru tayi kawai ta kasa bata amsa tmbyrta "idan ya ta'ba kwanciya dake ne ki fad'a min nan ma shiru tayi kawai "karki manta Kiyi rantsuwa da alqurni akan zaki rabu dashi ta gyada mata kai "idan baki son mubarak naji na hakura amman ki kawo min wani banda wannan yaron dan banason shi  daga nan ta zarce da nasiha na kwantar da hankali  tana nuna mata rabuwa da ussein  shine alkhairi arayuwarta wanda alokacin mgnrta na shiga ta kunne na hagunta ne yana bin ta  dama ."

wannan  sakewar yasa ta samu damar  turawa ussein sako da duk wayar data  shigo hannunta byn ta tura text  sai ta goge haka haka dai har ta shirya barin gidan da yammacin ranar laraba ta fice daga gidan babu wanda ya sani sai lalubo wa sukayi bata gidan" abun bakinciki tana zuwa gidan nan da hassana ta soma cin karo lokacin ta dawo gida aurenta ya mutu "Ke tsaya ta daka mata tsawa me ya kawoki gidan matsiyata ?tace dan Allah Kiyi hakuri nazo neman ussein ne "ussein din kanin ubanki ne da kikazo nemansa ? yanzu har kin manta irin azabar daaka gana masa akanki ?"

"na sani amman Kiyi hakuri ta marairaice mata ta raba ta gefenta zata shigo tace "kina hauka ne ta kara buga mata tsawa wallahi kika shiga gidan nan da kaina zan fito dake na miki dukan mutuwa kuma bazan bari kiga ussein din ba har sai na danganaki da matsiyatan iyayenki masu kiran wasu matsiyata alhalin sune matsiyata , dan masu arziki basa yin abinda sukayi duk yadda akayi arzikin ma daga sama aka samu zaazo a ishe mutune "pata pata tayi mata batare da sanin hjy ba sannan ta korarta ."

bangaren hjy rahma taji shiru shiru bilkisu bata fito ba ta nufi dakinta sai dai wayam tagani babu kowa ta duba bayi nan ma still the same nan da nan duk ta rude sai zufa take fitarwa nan fa ta soma kiran yaranta tana tsaye sai ga aisha da mijinta haka ma sajida cikin tashin hankali aka kira abubakar da mahamud har sulaiman har khadija  jugun jugun sukai kafin daga bisani suka fito zuwa nemanta har 12 :00 na dare ba labarinta babansu yace kowa ya tafi kawai makwancinsa har zuwa gobe aga abinda allah zai yi ."

daga gidan nan bilkisu ta rasa inda zata domin dai tasan idan ta koma gida azaba zata sha duk yadda zata fad'a cewar bata hadu da ussein ba bazasu yarda ba dan haka ta wuce gidan kawarta farida daman su basa tare da mahaifiyarsu , mahaifinsu ne kuma bai cika zaman gida ba kasancewarsa  jamin tsaro in takaice miki kwana da kwanaki ana neman bilkisu baa ganta ba yayinda ussein yake gida abunsa idan kinga ya fita to zashi area ne kuma bini bini ya dawo gida  ".

muna zaune aka zo nemanta basu ganta ba suka wuce intakaice miki kullum sai sun shigo unguwr nan sai dai basa ganinta sai dai su ganshi shi kadai  duk inda suka je nemanta  bataje ba duk ahalinta sun rude mazan kuwa sun bazu nemanta abu kamar wasa har sati baa ganta ba abubakar ya kai report police station duk hankalinsu ya tashi haka zalika ussein shima bai zauna ba duk inda yasan zataje yaje bai ganta ba kullum wayarsa tana hannunsa km a kunne koda zata nemesa duk ya rude ya rasa inda zai sa kansa ."

kowa a gidansu bilkisu kuka yake daga bangaren
yan dakinsu har sauran bangarorin dan kansu a hade yake kuma suna qaunar juna  ,duk sun rikice sun baza cigiyarta koina kafofin sadarwa amman babu wanda yace ya ganta dan haka suka sa akayi arresting din ussein a tunaninsu ya boyeta sati daya yana tsare ana gana masa azaba har a underground aka saka shi , ranar daya cika sati biyu akabari muka gansa ,koda aka zube magana sune basu da gsky amman kudi yasa aka bamu rashin gsky muka dauka muna bada hakuri akazo dashi unguwar nan sarka hannu da kafa Kmr wani barawo aka bincika gidanmu daki daki lungu lungu baa ganta ba haka dakunan abokansa da dakinsa duk inda aka san yana zuwa sai da akaje dashi amman baa ganta ba aka sake dawo dashi station dokoki aka kafa mana .

daya daga cikin police tace tasan koina bilkisu take zata nemeshi dan haka da zarar ta kirasa ya tabbatar sun hadu ya kawota a haka aka bar maganar muka dawo gida wanda tsanar bilkisu ya sake girma a zukanta yan'uwansa hatta gali alokacin ya fadi maganganu marasa dadi akanta wanda shine har yau baya qaunrku da mahaifiyarku amman ita hjy tana sonta dan tayi kuka rashin ganinta da baayi ba ."

Kullum hjy tana cikin zullumi da addauar allah ya bayyana bilkisu wallahi hjy tana matukar qaunar bilkisu sam bata ganin laifinta komai zaa fad'a akanta bata gani , cikin ikon allah sai gashi ta nemi useein  da number farida ya tmbyrta inda take ta fad'a masa bai bata lokaci ba ya nufi inda take yana isa sai da yayi mata mari masu kyau har biyu cikin tashin hankali yaja hannunta daga can gidan nan  ya zarceto daita muna zaune sai gashi  ya shigo daita ."

hjy  duk tafi kowa jin dadi ta rungumeta ajikinta tana kuka mikewa tayi tace muje   police station
Muna   fitowa  ta nemi limamin masalacin unguwar nan tai masa bayanin komai shima kuma ya fahimci akwai matsala duba da yawon zuwan da yanuwanta suke muna isa aka kira yan'uwanta  ai a haukace  suka shigo sabeer yayi kan ussein "kace bakasan inda take ba ?  sukayar da  kansa yayi dan rasa me zaice ."

  liman da police suka  tsaidasu suna kwantar masu da hankali amman  suka kasa aiwatar da hakan suka rufeshi da duka hjy ta shiga tsakaninsu tana karesa tana kiran sai dai ku hada dani allah ya isa bata yafe ba ,ita kuwa bilkisu kuka take sosai tana fad'a masu bashi da laifi hasalima tunda ta bar gida bata hadu dashi ba sai yau  cikin fushi aisha tace "ya lalata miki ingantacciyar rayuwar da iyayenmu suka baki ya maidake yar yawo kororo "yayi miki ciki nasa aka cire miki amman duk  ba laifi bane ? "ko dan kinga an rufa miki asiri sai lokacin hjy rahma tasan da wannan maganar wanda hakan ya sake tunzurata da kyar dai da nasiha suka amshi diyarsu nasiha sosai liman yayi masu yace su jajurce da addua sannan  muka wuce da ussein ."

       "ai ranar ashe ruwan zafin uwar ta tafasa ta
kwarawa bilkisu a gabanta wanda yasa sai data suma a qalla sai da tayi kwana ta yini bata cikin haiyacinta sosai mahaifinta ya nuna bacin ransa akan abinda aka mata ,sai da tayi sati biyu tana jinya sannan ta dawo daidai   mahaifinta abun yafi karfinsa addua kawai yake allah yaye mata wannan masifa data daurawa kanta , amman uwar  izaya  da maseefa kawai tasa gaba ."

"yadda ake mata azaba haka zuciyarta take sake tunzura , dan zuciyarta da idanunta sun bushe basa ji kuma basa gani ,ta manta matsayinta babu ruwanta da kowa acikin gidansu ko ince miki ta tsani kowa km har lokacin bata cire ussein aranta ba duk lokacin datayi raayin ganinsa kawai fitowa take taje su hadu ta koma gida randa dare yayi mata kuma ta kwana a wajensa shima dai mutane suna cewa baya jin mgn wanda ni nasan so ne da tausayin bilkisu ke hanashi juya mata baya ."

Kwatsam sai ga bilkisu da wani cikin wata biyu cikin na uku ta fahimci ciki gareta alokacin shekararta shakwas cikin ta shatara hankalinsu ya tashi suka zo min da maganar ranar har da kuka nayi dan bakinciki nayi kuka kamar me cikin kuka tace zasu zubar nace a'a ta haifa sai ta bani tunda ni tun haihuwar sadam ban sake samun wani cikin ba shima sadam din da kyar na samesa kuka take tana cewa na taimaketa a zubar da cikin naki yarda
ranar tana komawa gida akasa sabeer yayi mata dukan fitar da tayi wanda yayi sanadiyyar fitar cikin alokacin na bawa ussein shawarar ya tura neman aurenta, hakan ta kasance abban sadam da kanin hjy suka je sai akace masu makaranta zatayi ba yanzu zaa aurar daita ba suka dawo suka fadawa ussein ya sameni da mgnr nace kar ya hakura ya sake turawa haka dai byn wani lokaci suka sake zuwa sai mahaifinta yace zai yi mgn da yan'uwansa duk abinda ake ciki zasuji daya samesu suka ce basu yarda ba daman shima bawai yana son aurenta da ussein din bane ."

Bayan sun koma akaro na uku ya turasu wajen yan'uwansa nan suka iske wani sabon tashin hankali domin cewa sukayi muddin yana son aurenta a wannan lokacin zai biya duk abinda aka kashe mata tun daga primary har secondary idan sun amince bisimillah ga list nan aka mika masu duk wani abu da suka kashe akanta jiki a sanyaye suka dawo suka miko min a tsorace na gama karantawa domin ko gidan nan da gidan bread muka saka a kasuwa bazai kai kudin da suka rubuta ba abban sadam ya numfasa yace "ki fadawa ussein ya hakura da yarinyar nan mutanen nan basu da mutunci km ko ya auri yarinyar nan wahala zai sha dan tafi karfin aurensa ni kaina na yarda da hakan kawai dai ayi auren ne dan kar suyita saduwa da juna suna ciki shima ussein koda ya samu labari yace ya hakura dan ina yaga million ashirin da biyar ."?

Haka dai suka cigaba da rayuwa duk sanda ta fita idan ta koma sai anyi mata duka tare da zagin tana warin maz gbdy kamanita ya canza ta fita haiyacinta tayi firi firi ta zuke ta rame  babbar yayarsu a gabdaya gidan wacce uwar gidan rafi'u giwa ta haifa hjy rabi ta samu yanuwan babansu har ma da baban akan abar bilkisu hakan nan kar rabo yaje ya kashe mutane gabadaya yanuwan mahaifinsu suka ki yarda  kuka ta saka masu ta zayyane masu abubuwan da basu sani ba akan bilkisu da ussein tunda sukaji ussein har ciki ya ta'ba mata suka zubar da makamansu , suka ce tunda taji ta gani abarta ta auresa tunda basu zasu zauna mata  dashi ba  shi dai mahaifinta bai uffan ba ."

tun daga wannan lokacin  da yan'uwanta da suke daki daya da mahaifiyarta suka ji hukuncin daaka yanke akan bilkisu suka shiga gana mata azaba iri iri batare da sanin kowa ba  aka dawo rikonta tamkar yar aikin gidansu yadda zakiga yan aikin gidansu na yawo haka ta dawo tana yawo babu shiga mai kyau babu komai amman hakan bai sa qaunar mahaifinku ta ragu acikin zuciyarta ba ."

aka saka ranar sati biyu kacal ana sauran sati daurin aure hjy rahma da ya'yanta kaf suka saka bilkisu a tsakiyarsu "duk ranar datasa kafa ta bar gidan zuwa gidan ussein amatsayin matarsa tasan cewar ta fita kenan har abada karta dawo gidan garesu ta nemi wani gidan ,ta nemi wata uwar ta nemi wani uban ,ta nemi wasu yanuwan ,fasa auren daidai yake da bin umarninsu ,amman zuciyar bilkisu bata girgiza ba ta cigaba da shirin aurenta dan Allaha allah take ta bar gidan ta huta acikin satin muka kai dan abinda muka hada na lefe wanda kusan hjy ce tayi komai wallahi in takaice miki maryama wulakanci har da wankan ruwan sanyi akayi mana byn an watsa mana abinda muka mai ."

Ranar  daurin aure babu mutun daya daya zo daga cikin ahlinta da wanda suke uwa daya uba daya da wadan da suke yan uba haka zalika mahaifinta bai je ba dan hjy rahma tace muddin yaje ita kuma zata bar masa gidansa kannen mahaifinta mutun uku ne suka je alhj saidu ,Alhaji umar ,Alhaji kaberu ana gama daurin aure aka nemesu aka rasa ,bayan an daura auren hjy rahma ta kira bilkisu ta tsinewa aure babu irin mummunar adduar da bayi ba, allah ya hadata da damuwa allah yasa ussein ya gallaza mata ya korota ,kar allah ya bata haihuwa dashi idan km ta haihu allah ya bata ya'yan da zasu dameta, idan basu dameta ba allah yasa suyi ta mutuwa a duk sanda ta haifesu , bilkisu tayita kuka tana jin Kmr ba hjy rahma bace ta haifeta dan lokacin da take fad'a min cewa tayi ita da uwarta har abada ta yafeta sai dai na fada mata baa yafe iyaye komai abinda suka aikata gareka."

lokacin da zaa kawo  bilkisu gidan mahaifinku babu wanda ya rakota saboda ta auri talaka daga ita sai mahaifinku suka  baro gidansu zuwa rubabben dakinsa  inji cewar hjy rahma dan wulakancin da sukai mana yasa babu wanda je dauko amarya .
babu abinda iyayenta sukai mata na kayan dakin kuma har yau yan'uwanta na jini babu wanda yasan inda  take sun dai san tana zaune acikin lagos din nan amman a ina take basu sani ba babu wanda ya ta'ba zuwa ."

Kusan bakin hjy rahma yayi tasiri akan bilkisu dan sai datayi shekara uku tare da ussein batare da tasamu ciki ba har aka auro salma bata samu ciki ba ussein bai bawa mara d'a kunya ba dan sosai ya dawo da shaye shayensa lokacin data masa mgn akan alkwarin da yayi mata na dainawa yace" yaushe sukayi haka ?sai byn da salma ta haifi ali sannan kwatsam sai ga ciki bilkisu ta samu har lokacin da tayi haihuwar fari tace  abarta  a gidan mijinta 
ni  nasan da wani mai arziki ta  aura ko bata je ba dole zaazo a dauketa  ,babu wanda yazo dan lokacin mahaifinku da kanshi yaje ya sheida masu ta haihu intakaice miki korar kare aka masa wai yazo rokon kudi shiyasa duk lokacin da mahaifinku ya bata mata  rai sai dai ni naji   mata haushi ita kuma  tayi kuka ta hakura dan bata san inda zata dosa ba mutane gidan nan gbdy sun daukenta  sha sha wai  ta tare a gindin miji to idan tace ma ta gaji ina zata ?

yau da'ace tayi saar uwa da tun tuni ta koma gareta domin tana  neman taimakonta amman no way domin zamanta a gidan ussein  shine gatanta kinga ta rasa gatanta shiyasa a kullum take ganin bata  da gatan daya wuce ussein daku yayanta komai yayi mata  take hakuri wanda kusan hakan yake cikin dalilin da yasa salma da hassana suke cin kashi akanta ta sha wahala sosai acikin yanuwan ussein bayan an haifi habib rashin Lfy ya kama  hjy haka ta dauko hannun bilkisu tasa a tafin hannuna tace na rike mata amanar bilkisu kar na bari tayi kuka idan ussein yasata kuka na tabbatar na wanke mata zuciya sannan ta qara da cewa byn ta mutu bilkisu ta dawo bangarenta ta cigaba da rayuwa acikisa  nace ta tara yayanta ta fad'a agabansu hakan kuwa akayi abun bai masu dadi ba amman haka suka yi hakuri kwana uku tsakani  tace ga garinku ."

Bilkisu tayi kuka kamar zata bita domin a gasky ita akayiwa mutuwa dan kusan nauyinta akan hjy yake itace komai nata bare Ke da kika ci sunan mahaifiyarta komai tasamu kece da bilkisu ne shekarar hajiya daya da rasuwa rashin lafiya ya kama mahaifinki  koda aka dubashi ciwon sigari ne ya kamashi har yayi masa illa bilkisu bata gujesa ba itace komai nashi  ,ita Ke kaisa asibiti gwanati ga ciwonsa na bukatar kudi amman babu ke babu irin wahalar da batayi ba har wankau tayi dan  ta rufawa kanta asiri cikin wannan halin rashin lafiya aka samu cikin habib har aka haifesa mahaifinku bashi da lafiya ranar da habib ya cika shekara daya a duniya  Allah ya dauki ran mahaifinku  ,yanzu shekaru ashirin da uku kenan rabonta da yan'uwanta da iyayenta kuma har zuwa wannan lokacin babu mutun daya daya nemi  inda take  to me  zai sa ku ku damu da   inda suke ?

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

        Page 19

A  matukar  zuciye  ya  sauke duka hannuwansa   yana  huci  sai dai har  lokacin  kwayar  idanunshi na kan  fuskar   baban   gali   yana masa  wani  irin  mugun  kallo  mai tattare  da  bakinciki  lokaci  d'aya kuma  yana  ta  qoqarin  danne  fushinsa  dan  baya  son  'bacin  ran  mahaifiyarsa  ."

baba   gali  ya  sakar   masa  murmushin  mugunta  sannan  ya kalli   aunty  hassana  da  aunty  salma  "kuga  wannan  tantirin  mara   mutuncin  yaron    wai  ni   zai  kai  hannunsa   jikinata  saboda   nace  zasu   bar  gidan  nan  kamar  da   kudin  ubansa  ko  da  kudin  uwarsa   aka  gina  gidan  nan  da zai  wani   d'aga  hankalinsa dan  Allah   ku kalli   Irin  kallon  da  yake  min  nasan  yana   jin  kamar  ya  kasheni  ne ."ya  qarasa  maganar  yana  dariya ,"

Murmushin  jin  dadi  aunty  hassana  tayi  itama  "ai  kuwa  bai  isa  ya  kasheka  ba  sai   dai  ya   kashe  uwarsa  ko  yaje  ya  kashe   wad'an  can  marasa  mutuncin  dangin  uwarsa  ba  amman  mu  nan  munfi  karfin  d'an  kutumar  uba,  shegen  gora  mai  falla  fallan  kunnawa , an  nace  mana  an  zo  an  haifa   mana   irin  jaraba  kuma  wallahi  sai  Kun  bar  gidan  nan  matsawar  bazaku   daina   mana   rashin  mutunci  ba  ."

cike  da   raunin   zuciya  habib  yace  "mahaukatan   banza   kawai  da  basu  san   ciwon  kansu  ba "
"mu   kake   cewa  mahaukata ?eh !lallai   yaron   nan  wuyanka  ya  isa yanka  ,amman  ka  sani  bamu ne mahaukata  ba  ga  mahaukaciya  nan a  gabanka  kana   kallo wannan  wannan  itace  mental  itace  mahaukaciya da ka  kiramu  dashi  aunty   hassana  ta  fad'a  tana  nuna  gefen  kanta ."

"Hassana !" ya  kira sunanta  a matukar  hassale
Aunty   hassana   tayi  saurin  zaro  idanuwanta  waje  tana  duban d'anuwanta   cike  da  mamakin  habib "yes  abinda  kunnuwanki  suka  ji  na  fad'a  kenan   dan haka ki  ma  daina  mamaki  zan ma iya fad'ar  abinda  yafi  haka " mutun takin  me  zan  tsaya  yi tunda  kin  kasa  mutunta  kanki ?"

ta  maida  hankalinta  da  idanunta  kanshi   sosai  tana  nazarin mgrsa sa  sai  daya   samawar  jikinsa   natsuwa sannan  ya  cigaba  da  zaro  magana  "Ki  kalli   aunty  tsab  ki  gani   Kinsan  dasu wa maganata  ta  dace ,ku  din  dai  kune  mahaukata  kuma  bazan  ta'ba   sauya  maganata ba."

  Hawaye  ne  yake  zubowa  daga  idanun   aunty   gashi  magana take  son  yi  dan  ta  basu  hakuri  sannan  ta  tsawatarwa  habib amman  ta  qasa  bud'e  bakinta  bare  ta  sarrafa  harshenta a wannan  lokacin  ita  kanta  taga ya dace  ta  koma  cikin  'yanuwa  cikin  asalin ta  amman kuma idan ta tuna  irin  rayuwar  datayi  har ta kawo  wannan  matsayin  sai  taga komawar   nata  bashi  da  wata  amfani  me  zata  cewa  alhj rafi'u  giwa  da mahaifiyarta  wacce  tafi  kowa  d'aukar  zafi  akan  kowa  wacce  ta  gindaya  mata sharadin  cewar  ta  manta daita ta manta da  kowa  nata  tunda ta zabi auren  ussein  ?".

  "gidan  nan  kowa  yasan  gidan  kakanmu  ne  wanda  ya  haifi mahaifinmu   yadda  kuke  taqamar  kuna  da  iko  akan   gidan  nan  haka  muma  ya'yan  ussein  muke da  iko  da   gidan  nan  matsawar  zamu  zauna  acikin   gidan   nan  dan  dole   mahaifiyarmu  ta zauna acikinsa   ."

" Ke  ! hassana   da  kike  cewa a dole  mu  bar  gidan  nan  kisani  bamu ya  kamata  mu  bar  gidan nan  ba  ke  da  ya'yanki  yafi  dace wa  ku  bar  gidan nan  dan   da   gidan  miji  mace  take  taqama  ba da  gidan  uba ba  , aunty  a gidan  mijinta  take   zaune  Ke  fa  ? da  har  yanzu  Ke da  ya'yanki  baku  san  garin   ubansu  ba  bare  su  san  dangin  ubansu  ,ki  fara zuwa ki  kai  ya'yanki  su  san dangin  ubansu  tukun  kizo  ki  kori  wad'an  da  su  muhalinsu  suke  ."

Cike  da  sanyin   jiki  maryama  ta  dinga  jan gwiwowinta  har  ta qarasa  gabansu  aunty  hassana jikinta  na  wani  irin  rawa   Kafin  tai  kai  ga yin mgn  taji  aunty  hassana  ta hau surfa  mata maseefa  "dan  ubanki  yau  dai  karki  kuskura ki bamu hakuri , shegiya  yarinyar  munafukar Allah taala kin wani  marairaice  fuska  kamar  ta  kirki  zaki bawa mutane  hakurin  gulma  wallahi   yau   shine  zamanku  na  karshe  acikin  gidan nan   sai  kun bar  mana  gidanmu  ,gara  ma  tunda  wuri   Ki  san yadda  zaki  d'auke wnn  uwar  taki  da wannan shegen  kannin naki mai falla  fallan kunnuwa Kmr na fir'una ku  bar  mana  gidanmu  mu  huta da jaraba  sanda  ussein  yana  raye  bai  barmu  mun huta ba sannan  bai  tsinana mana  komai  ba  sai  ruwan shaye shaye da d'auko  mana  magana  wanda sanadiyyar  haka  ya  kwaso  mana  wannan munafukar  uwar  taku  gashi  ya  mutu  ya  barmu da  mugun  iri ."

   "Kuka  maryama  ta  fashe  dashi  hade da  sake durkusawa a wajen  batare da tasan abinda zata fada ba,  tana  mai   bakincikin  irin   kalar   rayuwar  da  mahaifinta  yayi a  sanda yake  raye, gashi ya  bar duniyar  amma  basu  huta  ba , wannan wace  irin rayuwa  ce ? me yasa wasu yanuwa suke yin haka ? "tasani da ubansu mai  arziki  ne da  duk abinda yayi babu mai tuna masu  bare  har a zagesu   dashi  ."

tsaki   baba   gali  yaja  yana cewa  " Munafukar  banxa  sai  anyi  magana  kisa  mutane a gaba kina kuka,  da  ubannaku  bai shaye shaye  ba  zaa fada? daya  zauna da mutane lpy  zaa ki  fada ?kullum yana cikin d'auko  mana  magana  gashi ya mutu ya bar iri  an  iya  tujara iya tujara  sauran  shaye shaye .."

"Allah  bazai sa  ba  ,baba  ka daina masa mugun fata "me ya saura yaro ya zama dan daba ai sauran shaye shaye, habib zai yi  magana   maryama  tayi saurin dakatar  dashi  tana cewa "walalhi karka sake cewa komai ai ga  irin abinda ka haifar ko ?"ni dai na fada maku  maza ku san ynd zaku  yi  ku bar mana  gidanmu tunda  gdn bana ubanku bane,"

  maryama da  tarin  qunar  zuciya  da qunar  rai take zubar da hawaye  tafi  karfin minti  goma a durkushe  sai daga baya ta koma  inda  tabar aunty ta durkusa  kusa daita  hawaye na  zuba a idanunta Itama aunty  hawayene take zubarwa a  nata  idanun  tana  jin ciwon abinda  habib  yake  duk da tasan  gsky  yake  fad'a  masu  amman  bata só  yana  fadar duk  abinda yazo   bakinsu  dan  kome  zai faru bazasu  ta'ba  sonta ba  har   yau   tarasa  me  tayi   masu  mai  zafi  a duniya  da  suka  kasa  yafe  mata  sannan suka  kasa   danne  tsanarsu akanta  da  yaranta ."

Habib  ya  kalli  aunty  ya  kalli  maryama  itama  duk   kuka  suke  maryama  kam har  da  shesheka  tana  rarrashin  aunty " ku  sani  ku  daina wulakantamu na  kyale  ,  kusani  nadamarku  ta  kusan  zuwa  a nan  kusa  kuma  munafurcinku  ya  kusan  qarewa domin  bazan   sake  yarda  da  iskancinku  dan   kuwa  kun  bari  d'an  zaki  ya  girma yayi  girman  da  zai  iya  kasheku  d'aya byn  d'aya  ,gidan  nan kuma babu mai  korarmu  acikinsa  sai dai a d'aga sa  d'ungurungun  dinsa  a sakashi  a  kasuwa  a  siyar a bawa kowa  hakinsa  kowa  ya  kama gabansa"

"Ai  kuwa  baka  isa  ba  wannan  gidan  ubanmu  ne kai   har ubanka  ya  gama  iskancinsa  ya koma  ga  Allah  cima  kwance ne bai  da  gidan  da  zaka yi wannan taqamar  da   kake  yi  "kai  da ba cima  kwance  bane  sannan  bakayi    iskancin    ba  ina naka  gidan  daka  gida  yake  ? "sannan .."
"habib  dan   girman    Allah  .." saurin  d'aga wa  maryama  hannu  yayi   ta hanyar  dakatar  daita " ki  barni  dasu  heartbeat  wallahi  kowa  sai  na  bashi  size dinsa   yau  idan sunce basu da mutunci   zan  nuna  masu   ni  d'an  zamani  ne , ya  d'an  tsaya yana  kallonsu  d'aya  byn  d'aya ,nan  take   ya   hango   tsananin  tsoronsa   da shakkarsa   acikin   kwayar   idanunsu "oya   kuna  iya   wucewa   ku  bar  mu  cigaba  da  rayuwarmu  ko  sai  na   fitar  daku d'aya  byn  d'aya?".

A yadda  suke  kallonsa  sun  fahimci   zai  iya jansu ya  fitar  dasu  kmr  yadda  ya fad'a  dan  haka  aunty  hassana ta kalli aunty "sai  ki  daina kukan munafurci  tunda  burinki  ya  cika kin  haifa  mana  maseefa  amman in sha allahu  maseefar  akanki zai qare   tunda  ya  fara  zama  d'an daba    tana   gama   fadar  haka ta fice  daga   d'akin  tana zage zage 
aunty  tayi saurin  runtse  idanunta  tana  jin  zafin  kalmar  data  danganta  mata  d'a  dashi , itama  aunty  salma  tace   "shegu  a  haka  zaku  qare  jiya  iya  yau  babu   cigaba ta  nufi    hanyar  fita " da sauri  habib  yace "Ke  ina  naki  cigaban  da  kika  samu yake  ? "Ke  da  ko  sallah  bakya  yi ,  qazama  mara  sallah  mai   dotti  kawai  kije ki  gyara  tsakaninki  da  ubangijinki  zai  fiyye  miki  sauki  akan  shiga  rayuwar wasu  ."

shi  kam  baba  gali  cewa  yayi  "bilkisu  Ina  tarbiyar  taki ?yau a gaban  idanunki  d'anki  yake nuna min  iyakata "to  sai  me dan na nuna  maka  iyakarka  a gaban  idanunta ?  "kai  da  bakaji tsoron gaban  idanunmu kake  nuna rashin qaunar  mahaifiyarta ba   kiri kiri  kake  zaginta  agaban   idanunmu akwai  abinda  yafi  wannan ciwo ?  wallahi  idan bakasani ba kasani  yanzu  abinda  kukayi  mata a da  tayi hakuri  ta shanye yanzu  ta  haifi d'an da zai kwatar mata  'yanci  zan goge wannan tarihin  idan  ka  cigaba da tsayuwa zafin jinina  zai iya sa na d'auki takobin  can na file  maka kai  dashi ko na  raba  katon kan nan  naka   gida  hud'u  idan yaso  nima  akasheni  salin alin baba  gali ya fice batare da  ya sake  cewa   uffan ba."

Yana  fita habib  ya  qaraso inda  aunty da  maryama  suke  durkushe  suna kuka "cike da  girmamawa yace "ku daina kuka  in sha allahu ku daina kuka acikin gidan nan  , kun  daina  damuwa matsawar  ina  raye  zan tsaya maku , zan  kula daku da zarar na gama  karatu  zan ...."bana  son jin komai  daga  bakinka  habib na   fahimci  kana  bukatar  na bar muku  gidan  nan  shiyasa ka kirkiro  abinda za'a koreni daga cikinsa  tana gama fad'ar haka bata  tsaya  jin  abinda  zai  ce ba ta  mike  ta  shiga  d'akinta  ta d'auko  mayafinta  kawai  ta fito zata  fice  ta  bar masu gidan ."

Atare  maryamah  da  habib  suka sha  gabanta  cikin  tsananin tashin hankali  "haba  aunty  ya  zaki mana  haka  ?kiyi  hakuri  aunty hakika  habib  bai  kyauta ba amman  karki  tafi  ki  barmu ."maryama  dan'uwanki   baya  bukatata  acikin  gidan nan  yana bukatar  na  tafi  na bar  masa filin gidan  nan  ya cigaba da rayuwa  ta qarasa maganar  tana  zubar da hawaye  ta  tabi  gefen maryama zata raba  ta  wuce  ."

habib  ya  riko  mata hannu "kiyi hakuri  aunty  ki fad'a min abinda kike  bukata nayi miki  alkwarin  wallahi  zanyi  kisani  idan  kika bar gidan  nan  bashi  da  wani amfani a  wajenmu "yana da amfani mana tunda gashi  kayi  son  ranka  kasa an zageni  anci  mutuncina  anci na iyayena  ai gara na kama  gabana  tunda zamana acikinsa  babu abinda yake haifa min  sai  damuwa da bacin rai ".

Kuka ya  kufce  ma  maryama  ta  d'an  rufe  fuskarta da  tafukan  hannuwanta  saboda  tuttukin  da zuciyarta  Ke yi "kai  ma  kasan  abinda  kayi  ba daidai   bane  har  ka  iya  cire  hannu  zaka  doki baba  gali   wallahi  baka  kyauta  ba   tunda  kasan halinsu  to  meye  amfani  tsayawa  kana  fad'a yana fad'a "ki  fahimci wani  abu  heartbeat  wad'an nan mutane basa  qaunarmu  ,babu  abinda Ke cikin zukatansu sai tsanar mu " tunda mun san halinsu sai mu  kiyaye  abinda  zai  kawo  sa'bani  dasu  shima kukan   yake yi  "suna  nuna  mana  bambamci akan ya'yansu  ,suna  quntata  mana  suna  da  fuskar  gazawa  garemu  musaman   akan ya'yansu  yanzu laifin  me kikayi ma aunty salma ta shigo tana zaginki ?"maryama  bata  sake  cewa komai ba illa ta cigaba da kukanta haka ma aunty batayi magana ba illa qoqarin zare hannunta da take cikin nashi ."

"na  tuba  aunty  bazan sake ba ki fad'a min abinda kike so ,nayi miki alkwarin  bazan  sake  ba ya fad'a yana zubar da hawaye itama ta goge hawayen dake zuba  akan  kuncinta  ta cigaba da mgn "daga yau babu ruwanka da  kowa acikin gidan nan  duk abinda  zasuyi  ko  zasu fad'a akanmu ka kawo ido kasa masu , kai ba zagi  ko dukana zasuyi  babu ruwanka a rashin yace ba dai duka ba amman a zahiri yace "to aunty an gama ."wallahi  abinda kayi yau din nan ba irin tarbiyar daaka  bamu  bace "in sha  allahu  bazan  sake ba heartbeat  ki bata hakuri  bazan sake ba  kamo  hannun aunty maryama  tayi suka koma kan kujera mai  zaman  mutun uku da duk  ashon jiki ya  batattake suka zaunar  daita  tare  da sakata a tsakiyarsu  suna bata hakuri ."

Kamar  yadda  mlm  yahuza  ya sanarwa  nafisa  byn sallahr ishai zai  zo  sai ga  yaro yana sallama  da maryama  lokacin  suna zaune a falon aunty  ta dubeta amman ita ko  ajikinta sakon da yaro ya fad'a aunty tace "maryama bakiji  bane ?ta  d'an  dubeta ta share yaron ya tsaya yana jiran abinda zaace   "to sai  ki  tashi kije "ina kenan aunty?"bakaji ana sallama daita bane "gsky   babu  inda zata ban san dalilin da yasa da mutun yazo nemanta ba  sai ki bata damar fita baki  san ko waye ba mazan da duk 'yan  iska ne da zarar sun fara zuwa kamar abun arziki da zance aure ya shigo sai su gudu su barta  ni  gsky babu wanda zai sake zuwa ta fita ."

"Maryama  tashi  Kiyi  maza  kije ki dawo  saboda ki samu ki d'an huta   karki  dade  duk da nasan ba  dad'ewar zakiyi ba ,ina dalili da zakace  bazata  ba kai zaka aureta ?ya  marairaice  murya "bani  zan  aureta  ba  amman  at least  aunty  ki duba  lamarin  nan kawai  suzo  suna  'bata  mata  lokaci  da  dagula  mata  lissafi "Babu  wani  dagula  lissafi a haka  allah  zai  kawo  mata  wanda  zai  aureta  ,ina  son  kasan  wani  abu  habib   duk   cikin  masu  zuwa neman   auren  maryama  babu mijinta  acikinsu , duk  lokacin da mijin  yazo  to  babu  makawa  sai  anyi   domin  babu  mai  aurenta  matar  wani  kai  yaro  je  kace gata nan  zuwa  yaron  ya  juya  da sauri dan  daman  amsar da yake jira kenan  zata  fito  ko  kuwa  bazata fito ba  ."

maryama  ta  tashi  ta  shiga  d'aki dan  tasan  ko  waye  yazo  ta d'auki  hijab  dinta  ta  fito "amman dai  ni  aunty  a wajena  ba  daidai bane  ,ni  fa  kamar  mahaifinta ne a matsayina na  namiji  acikin  gidan  nan  amman  me yasa  sai a dinga  nuna  min  iyakata  acikin gidan  nan  , na  fiku  sanin halin mazan  wannan  zamani  babu komai  acikinsu  sai  tsabar  yaudara ".

Aunty  ta  kallesa  saboda yadda yake  maganar  tamkar  wani babban  mutun  tace "wai  har guda  nawa  kake  habib  ?" duka shabakwai  gare  fa  kawai dan allah  ya  baka  jikin  girma "ni dai gsky  ban  yarda  ta  fita  koina ba  girgiza kai aunty  tayi  tana kallon  yadda yake kamaninsa yake canzawa  a  kullum  yana  komawa na  mahaifinsa  tun ba yau ba kusan  kowa  yana  fad'in  kamanin nasu  "gaskiya  habib  kar  ka  zama  mai   hana   neman   auren ."

tsayawa   maryama  tayi   tana kallon  fuskar  habib  daya had'eta tmkr  ance  masa  idan  ta  fita guduwa  zaa  yi  daita ,ahankali ta kira  sunansa  "after dad "
"Karki  wani   kirani  da  wannan sunan  dan  dani  din  ina  da wannan  matsayin  da  za'a  dinga bin  umarnina " ta  qaraso ta zauna kusa  dashi  ta  riko  tafin  hannunsa  cikin  nata  tana kallonsa  da  idanuwanta  da  suka canza  kalla "after  dad me kake so dani ?"ta fad'a tana kallon yadda shima  ya  zuba  mata  ido  yana kallonta ."

"Abinda  nake  so  duk  wanda  yazo karki  qara  fita  koina idan abinda  ake  miki  acikin  gidan  nan  baya  damunki  ni  yana damuna  ,sau  nawa  kina yi  saurayi  agidan  nan a karshe  ko ya  gudu  ko a kwace  miki shi acikin  gidan  nan ?to  ai  duk ba mijinta acikinsu  ne ,no no aunty akwai cutarwa aciki "to   nufinka  yanzu  haka  zata  zauna  babu   mai  zuwa wajenta ?"allah  aunty dasu  dinga 'bata  mata  lokaci  gara  ta  zauna haka  idan  na  girma  na  qare karatuna  zan  mata  komai zan siya  miki  gida  da  mota  itama heartbeat  zan  siya  mata  zan kai ku  aikin  haji  ,kai  har  sojoji  zan daukar  maku  escort  duk  inda zaku  su  dinga  rakaku  aunty da maryama  basu  san  sanda murmushin  jin  dadi  ya  bayyana akan  fuskarsu  ba "shikenan  after dad  bazanje  koina  ba  domin kai  din tmkr  uba  ne  a gareni "yauwa  heartbeat  sai  yanzu  naji hankalina  ya  kwanta muyi  zamanmu ."

aunty  ta  kallesu  ta  girgiza  kai "wallahi  wannan ba rayuwa bace kin  wani  zauna  ya  tasaki  gaba  yana  miki  zakin  baki  ,wallahi ki daina  biye  masa  Ke  macece dole  kina  bukatar  Kiyi  aure shifa nan  gaba  kad'an  zai  ce  zai  yi aurensa  dan  wannan  da  son girman  tsiya  nasan .."no no aunty karki  hadamu da  heartbeat  babu wani  aure  da  zanyi  na  barta  idan  dole  sai  tayi  aure  ni  zan kawo  mata  miji  wanda  zai  dinga kwantar  mata  da  hankali  duk ranar da  yayi  gangancin ' bata mata  rai  na  zage  naci  ubansa ".

"Lah  lah  lallai  habib  abun  naka babba  ne  "allah  aunty  sai ma ya cika  qaidodina  sannnan "wannan  ai  gara kuje  kuyi  auren  kotu  ku  huta maryama  tai  murmushi  tana jin dadin  yadda  dan'uwanta  ke tsananin   qaunarta  "babu kotun da  zamu amman dole a kular min  da  heartbeat ko kuwa a tashi mutun aiki "uhm  kaga   tashina  ta  mike  tsaye  "  bari  naje na bawa  baba  gali da hassana  hakuri na dawo ."

"haba  aunty  ai  komai  ya  rigada ya wuce  wani  hakuri  kuma  zaki basu   salon  su  samu  damar ci miki  mutunci  "? A'a  sai  naje  zaman  lafiya  yafi  zaman dan sarki  ina  zan  iya  dasu  gara dai naje ."Yauwa  aunty  kije  ki basu hakuri  wannan  ai ba komai bane wata  rana  sai  labari  kai ma ya kamata  ka bita  kabasu hakuri wani  irin kallo ya watsa mata  yana cewa "allah  kiyaye ai ni .."sai  kuma  yayi  shiru  sakamakon tuna alkwarin  da  yayiwa  mahaifiyarsu ."

"ai  babu  abinda  zai  sa  naje da habib  sai ya  qara  dagula  lissafi sunan wani police a isokoko ni na wuce sai  na   dawo "to  aunty sai  kin  dawo  tasa kai ta fice daga dakin  ta barsu suka cigaba da hirarsu mai  cike  da  kulawa da soyayya shi kam mlm yahuza tsawon mintuna nan duk yana tsaye  yana jira   Fitowar maryama ya  duba  agogon  dake  daure da  taintsiyar  hannunsa  yaga lokaci  ya  tafi  daman  kuma  yaron daya  aika  ya  sheida  masa komai  dan haka a natse ya juya sai dai ya kudurce aransa  zai  dawo  gobe."

Ahankali  aunty  take  tafiya  tana tunane tunane abinda zatace idan ta isa gaban baba gali a natse tayi sallama  cikin  bangaren  nasu  basu amsa  mata sallamar ta  ba  dan haka  taji  gabanta ya shiga faduwa  kafin ta kai ga yin wata  magana taji aunty salma ta hau surfa mata maseefa  kamar kullum "me ya  kawo  bangarenmu  "ba komai bane  hakuri nazo baku akan  abinda  habib  yayi ,ya gama ci mana mutunci a gabanki shine  dan  munafurci  kika kwaso  jiki   bayarwa  , shegiyar  munafuka kin wani marairaice  fuska    bayan kin gama zuga d'anki yayi mata walima ta uwa da uba zaki wani kwaso jiki to yanzu hakurin  me kika zo bamu  ?".

Numfashi aunty ta sauke ta samu waje ta zauna kusa da baba gali da ko kallon inda take bai yi ba a tun sanda ta shigo "kuyi hakuri gabadayanku in sha allahu nayi maku alkawarin wannan shine karo na farko da karshe da hakan zai faru ...."dakata  bana son jin komai daga  bakinki  dan duk abinda zai fito daga cikinsa karya ne ni dai abinda nake buqata "ki dauki yayanki ku bar mana gidanmu tunda ussein yake raye bai tsina mana komai ba sai tujara gashi nan ya barwa dansa tsaraba har kamar ni wannan yaron zai dinga gasawa magana kuma a gabanki kina kallo  yaron da ya kamata kiyita dukansa har sai kin kusan auna shi lahira amman kika zauna dan tsabar son ya'ya kina kallonsa yana surfa mana zagi ta uwa da uba  ai wallahi bazai yuwu ba ."

Sake durkushewa tayi Kmr zatayi kuka batare da tasan abinda zata sake fad'a ba sai dai ita kanta a halin yanzu tana mai bakincikin hada  zuria dasu tsaki aunty salma  taja tana cewa "munafukar banza  munafukar wofi sai anyi magana ki wani  durkushewa mutane  "ni dai ba wani tashin hankali nazo dominsa ba nazo ne dan na baku hakuri dan nasan danku bai kyauta ba "ni wannan yaron ba d'a bane domin kuwa d'ana bazai min haka ba hakuri aunty  tayita basu da kyar baba gali yace komai ya wuce amman tajawa habib kunne aunty salma dai ce taki  hakura   ta mike tana masu sallama "sai da safenku allah kuma ya huci zuciyarku babu wanda ya kulata acikinsu har ta fice zaginta aunty salma take cikin tsananin tsana  ."

Daga bangaren baba gali na aunty hassana ta shiga itama dai  tujara  tayi  mata  ta uwa da uba kaf danginta  babu  wanda ta  bari  bare iyayenta zuciyarta  tayi  nauyi  kamar an d'aura mata dotse da kyar ta yunkura ta mike ta fito tana tafiya zuciyarta na  kokawa. a inda aunty ta fita ta bar yaranta anan ta dawo ta samesu zaune  suna  hira "har  kin  dawo  aunty  ?suka  had'a baki murmushi  tayi  tare da d'aga  mata kai  alamar" eh! my princess na dawo ".

"Yaya  kuka  qare fatan sun hakura "Eh to  sun hakura my  princess!ta fad'a zuciyarta cike da raunin kuka dan shi take bukatar yi a halin da take ciki  shi kam habib bai ce uffan  ba  illa  ya  cigaba  da  sauraronsu"my princess Kinga dare yayi  bamu  samu  girka komai  a gidan nan  ba ni yanzu ban san me zamu dan girka muci  ba "wallahi  aunty amman bari naje wajen Ummah watakilla bazamu rasa abinda zamu ci ba maryama  ta fad'a  idanun  habib  yana  kanta "ko  zaka   raka ni ne? ta  fad'a tare da miqewa..."Muje ! kawai abinda ya fad'a kenan maryama tayi murmushi "makalema kawai  "kima  ce  bita zai zai  ki  huta  gbdy muje  suka jera ."

Suna  fita suka had'u da yaya sadam  ya  fito  daga side d'in  din baba gali zai shiga side din ummah cike da farinciki habib ya qarasa suka gaisa! "A she rabon mu had'u ne yaya yasa heartbeat tace nayi mata rakiya ."ai ko baka fito ba  yanzu  nake  shirin  zuwa  tambayarka a wajen  aunty !Ya mika masa hannu ya kwana biyu  ina  fata dai komai  lafiya? "Lafiya  lau  habib  kawae aiki ne ya  boye  ni 2days ya karatu ?yace "alhamdulillah.!"

maryama ta bude baki da kyar ta gaishesa ya amsa mata cike da sakin fuska "Lafiya  su aunty maryam"ji tayi kunya ya kamata da kirata aunty da yayi ! Ya gida da karatu ?Alhmdllh! ta fad'a  cikin jin kunya"kema dazu   nake tambayarki  wajen Ummah take bani labari mai dadi lallai kin fita zakka acikin matan gidan  nan kin tsaya kinyi karatunki yadda ya kamata allah yasa muji sakamakon mai kyau you're  the  best  maryama  duk nmj daya sameki a matsayin mata baqaramin dacewa yayi  ba Allah yasa sawa karatu albarka dad'i maryama  taji sosai  dan duk cikin yanuwanta sadam ne kawai sai habib Ke mata fatan alkhairi idan wani abun farinciki ya sameta tace "na gode  sosai yaya ."

Habib yace "a she dai yaya  ka  gane  shiyasa sai  na zaba mata na durje mata  miji  dan ita din ba kalar kowani nmj bace "kaga yaya karka kulashi  mu je ciki  mu  qara gaisawa "wucewa sadam yayi side d'in Ummah  maryama da  habib  na biye da shi sunata hiran duniya..."

Zama sukayi a parlour'n  sadam ya fara kiran  "Ummah  Kina ciki ne? Eh! Ganin nan  zuwa dan albarka har ka dawo ne? sadam yace" eh ! gashi na  kawo  miki maryamarki "ban gane ka kawo min maryama ba maryama da muke yini tare dan gulma zakace ka kawo min ita Bari dai nazo ganin nan fitowa ."

Bata  wani bata  lokaci ba ta fito cikin  doguwar riga  qaton  tray ta aje  a gaban sadam  na fruits bismillah  sannu da zuwa yau har da habib  to duk sannuku "Ina yini "Habib  yace " lafiya lau  habib Ummah ta kalli sadam ta kalli maryama  sai taga sun maseefar dacewa ina ma su kasance maaurata suna hirarsu gwanin ban shaaawa  habib ya fahimci  maryama kunyar sadam take ji sosai dan taki fad'ar abinda ya kawo su gashi shi yunwa yake ji ."

Maryama  tace after dad  ya kamata mu wuce dare nayi  "a'a  har  zaku  tafi kenan maryama  to ai  bakuci  komai  ba "karki damu Ummah  "ban  gane  karta  damu  ba kinga nifa banason kunyar nan  take wai ma wa Kike jin kunya anan  umma  ko  yaya  sadam ,?maryama tayi shiru tana mai sunkuyar da kanta qasa tana wasa da yatsun hannunta "kinga  Ummah  nan ya fad'a  mata abinda ya kawosu "kai maryama  amman shine zaki jashi ku wuce to  kuci me idan kun wuce?  allah ya kyauta wannan kunyar taki  kaga habib bari nazo ta fad'a tana mikewa tsaye ta nufi kitchen ".

Bata wani bata lokaci ba ta dawo hannunta d'auke da wani madaidaicin kula cike da abinci sannan da wata leda cike da su cincin  wanda tayiwa sadam ta miqa ma maryama tace gashi  kai km habib ka  rike kula " mungode Ummah !Suka fito maryama nayi masa mitar abinda  yayi  dariya kawai  yayi yana cewa "ina ganin gara  kawai  ayi yar gida mu huta da samari masu  mana patrol  "kai dai kasani  ni nasani ko gaskiya suna tafiya suna jan juna har suka qaraso falonsu  habib ya zauna yana kiran "washhhh allah maryama ta cire hijab dinta ta ajiye  akan kujera  tace "habib bari na kira aunty  kanshi kawai ya gyada mata ."

Ahankali ta shiga d'akin sai dai abinda yayi matukar daga mata hankali shine ganin mahaifiyarta kwance rigingine akan katifa hannunta rike da wani hoto tana kallon hoton hawaye na zuba daga idanunta  tana tuna irin rayuwar dadin da tayi ada kafin shigowar ussein rayuwarta ,bata haskowa kanta irin rayuwar da take ba sai data hadu da ussein soyayyarta ta gurba tunaninta ."

yayinda maryama ke kallon mahaifiyarta da ita kadai ta rage mata a duniya yanzu a natse ta qara taku biyu domin son ganin hoton waye a hannunta take kallo tana kuka  wasu mutane tagani guda biyu cikin shiga na alfarma suna cikin koshin lafiya da farinciki ko baa fada mata ba tasan hoton iyayenta take kallo cike da nadama lumshe idanunta tayi "iyaye ba abun wasa bane , aunty iyaye suna da kimar da darajan da  bazaa iya mantasu ba ."

ahankali taji sautin muryarta tana fita  cikin kuka "nayi  kewarka baba , nayi kewarki mamana yanzu ku har yanzu  bakuyi kewata ba ?yanzu ku baku yafe min ba ko nemeni ba? wallahi ina sonku nayi kewarku ,nayi  kewar  kowa da kowa  ta fad'a tana mai daura hoto a saman  qirjinta tana shafawa tana kuka.."

Ahankali maryama ta juya tana zubar da hawaye masu zafi ta koma falo ta zauna kusa da habib tana sheshekan kuka nan take ya birkice ya soma tambayarta "heartbeat me kuma ya fara ?kukan me kike yi ? Ina aunty ?yayi mata tmbyr ajere cikin tsananin tashin hankali tasa gefen rigarta ta goge hawayen "yau aunty ta tuna da iyayenta tana daki tana kallon hotonsu tana kuka ni nasan zuciyarta na cike da qaunarsu shiyasa kaga ina son ta koma garesu ."

"habib  soyayyar  iyaye  da  yanuwa  baa  wasa  dasu wallahi a tsakaninsu soyayya ce mai karfi ka misalta hakan akanmu musan da qaddara  amman an cuci aunty an yi sanadiyyar rabata da kowa nata ,ta bar iyayenta akan soyayya gashi ta rasa soyayya taki bin umarnin iyayenta gashi duniyar taki mata dadi maryama tana kuka habib na rarrashinta har kukan nata ya ragu adaidai lokacin da sukaji tahowar aunty tayi saurin share hawayenta tana cewa ".

karka nuna mata komai da sanyi jiki ta qaraso "kun samo abinda zaku dan ci ?eh mun samu har da cinci tô maza kuci ku kwanta tayi maganr cike da rauni aunty kizo muci tare "aa ku dai kuci ku koshi aa wallahi tare zamu ci habib ya mike ya kamo hannunta ya zaunar daita ya bude kula abinci yana cewa kai abincin nan zai yi dadi maryama ta dauko spoon ta dibi abinci zata kai bakin aunty habib yayi sauri ya kwace spoon "bani ni zan bata da kaina suka sa da dariya ya soma bata abinci abaki yana fada mata kalamai masu sanyi ."

"idan nayi kudi bazan yi nesa dake ba zan kasance tare dake ,dan allah aunty ki daina damuwa akan komai kinji ki dinga tunawa cewa kina damu mu din zamu zame miki farinciki a rayuwarki Wallahi sai mun sa kinyi alfahari damu ki cigaba da addau ga heartbeat nan kwanan nan zata fara bautar qasa yanzu ma ina mata  processing yadda zaa dawo daita lagos né daga adamawa wannan farinciki  ya rage tarin qunar da zuciyar aunty take ciki  tace "allah yayi maku albarka yayiwa rayuwarku albarka in sha allahu bazaku dangwama haka ba allah zai saukaka maku rayuwa ,Allah nake roko ya daukaka min ku na yafe  maku duk abinda kuka min da wanda nasani da wanda ban sani ba suna cin abinci suna debewa juna kewa ."

******

da misalin karfe 9:00 na washegarin ranar lahadi mr ata ya fito  parlour'n  mami  ,duk  jikinsa yayi sanyi har wata  katuwar  rama  yayi  daman ya lafiyar kura ?ba wani jikin kirki bane dashi  kusantowar aurensa da maryam yasashi jin    kmr  ana  fixgar  ransa  ,shiru ne  ya  ziyarci  parlour'n yana tunane  tunane yana jin kamar idan ya tafi france  kar  ya  dawo  domin a lissafinsa sauran kwanaki goma cif a daura masa aure da yarinyar daya tsana fiyye da komai arayuwarsa   byn  kmr  mintina goma mami  ta qaraso  da kanta ta  had'o masa abun kari , chips  da soyayyen kwai  da  ruwan tea mai kauri , ta janyo qaramin table  gabansa ta  ajiye kana ta zauna kusa dashi ta tsura masa ido tana kallonsa batare datace komai ba ."

ya dauki cup din tea ya kai bakinsa ya kurbi kadan yana mai runtse  idanunshi  shiru har wasu mintuna suka shude yana zaune itama tana zaune tana kallonsa da kyar ya bude baki "sweetheart! "kaci abinci first before anything adamcy , sannan kar naji  kayi  magana  kaci abinci  kawai yaushe rabon ka sanyawa cikinka  abinci  bare a samu magani yayi aiki ajikinka ? ji yadda ka dawo acikin kwanaki uku kacal  ka taimakeni kaci wani abu  kanshi  kawai ya iya d'aga mata batare da ya kalli inda abinci yake ba, saboda sam  baya jin cikinsa  zai iya amsar komai  shima da zata taimakesa da tasa an fasa auren nan da yarinyar an hadashi da wata zai hakura da princess dinsa ya amshi koma wacece  duk da zuciyarsa princess kawai take so da son gani numfashi ya dinga  saukewa ."sweetheart  dina me yasa  kika  manna min wannan auren  haka?
" sweetheart  zaki  kasheni da kanki wallahi at least ki sake gara min dama koda  na  tsawon wata guda ne  ."

"to me  zan  maka adamcy nah daya wuce haka ?
"me  kake  son  nayi  idan  banyi maka  haka ba ?
gani nayi  kana  neman hargitsa min kwakwaluwa da qarar da rayuwarka a banza "me kake tunani mutane zasu ce idan   bakayi aure adaidai wannan lokacin ba ? wallahi zaka shiga zargin mutane ,mutun har mutun kamamme kamar ka ka zauna babu aure ko kana neman mata ne adamcy bansani ba da kake gudun aure ."

wani  irin kallo yayi mata mai nuna mata bayayi "to idan bakayi me kake jira ?maryam  yaruwarka ce fa "yanzu kai kafi son ka dauko min suruka daga waje alhalin ga wacce tasan darajata take sona nake sonta diyar danuwana yanzu idan an fasa auren nan  me kake son na cewa mutane da yan'uwana ,dan Allah dan annabi in banda   da rigima irin naka ba me ye laifin maryam ..?

"wani far yayi da idanu zuciyarsa na dokawa  da numfashinsa da yayi kokarin d'aukewa yayi saurin dawowa dashi gangar jikinsa sannan yace "sweetheart  ni bance tana da laifi ba amman  ki duba lamarin da  kyau  tunda nace bana sonta ai  sai a  hakura kawai  kowa ya kawo zabinsa . "kai rufe min baki ban son shirme banza, ka daina ganin ka had'a komai kana da kudi  kayi tunani zaka iya  juya ni  ."Wannan  aure sai  anyi shi muddin ina raye ."

ya marairace muryarsa  sosai  tmkr  mai shirin zubar da hawaye sannan yace "wai sweetheart me yasa kike ganin kmr  wannan yarinyar ce kawai zata iya kulawa dake  ? Allah  sweetheart ki daina mata kallon haka  saboda irinsu sune masu bawa dangi kunya  wallahi duk lokacin da naji kince min itace zata san darajarki  bakinciki nake ji kmr na kashe kaina saboda ni duk macen dana kawo miki dolenta ta soki tayi miki biyayya bama Ke ba sweetheart hatta yayyuna biyu din nan dolenta ta bisu  lalacewar mace daga miji ne  ni kuma bazan ta'ba bada wannan damar ba .. "

"Sauran kwanaki  goma a daura maka aure da maryam  a lissafina gobe  ko jibi jirginka zai cale zuwa qasar  france  fatana allah ya kaika lafiya ya dawo da kai lafiya shahida ta  gama shirya komai na aure  fatan alkhairi da dawo da niyyar  angeancewa lafiya and if you do anything  stupidty I will del with you kai ma kasani ina sonka fiyye da tunaninka amman hakan baya hana idan kayi ba daidai ba naki hukuntaka tana qoqarin mikewa hisham ya shigo ya gaishe da mami cike da girmamawa sannan ya zauna kusa da ata  daya   runtse tsumammun idanunsa tun byn da mami ta soma magana "yaakayi mutumina ya karfin jikin hope you are getting better?"numfashi kawai ya sauke wanda Ke nuna masa alamun ya amsa hisham ya cigaba da magana "har yanzu sultan da fahad basu dawo da komai ba fa  Kmr ma sun dauki abun matsayin shiririta tsabgogin gabansu kawai suke."

"ina sane da komai kai kasan bana canza maganata ina jiran na dawo daga france ne suna zaune suna hira mb ya shigo haka ma yaya Ibrahim ya shigo duba jikin mr ata tare da aunty abida har da yesmin wacce ta dane jikin mr ata haka ma yammatan gidan
d'aya byn daya  suka dinga shigowa suna gaisheshi da kyar yake bude bakinsa   yana amsa musu cikin rashin sakin fuska , cikin wasu  mintuna  aka cika gaban mr ata  da kayan motsa baki , amman babu abinda yaci  illa coffee daya dinga  tsiyaya a  cup yana  kurba ahankali ahankali   shima yana  sha ne kawai saboda  sabon da yayi dashi ."

Parlour'n ya dan rage mutane  ya saura daga hisham sai ata   nuzla da diyana  har ma da mrym da nana hauwa'u suka  shigo parlour'n bakinsu  d'auke  da sallama hisham na ganin nuzla ya saki fuskar  ganin masoyi yarsa  gbdy suka hada baki wajen yi ma mr ata ya jiki  banda nuzla  Kmr koda yaushe da kyar ya amsa  masu hisham  yana kallon fuskar nuzla yayinda  nuzla taja ta tsaya daga gefe can ta jingina bayanta da bango ta rungume hannuwanta duka bisa kirjinta tare da tsura ma mr ata  fararen idanunta tana kallonsa cike da matsanancin soyayyarsa  yadda ko kallon mrym da zai aura bai yi ba  abun yayi mata dadi sosai yadda bai son mrym abun na mata dadi har yana bata kwarin gwiwa dan tun daga ranar daaka saka ranar aurenau take jin haushinta sannan take cikin damuwa mai tsanani  ."

ahankali ta bud'e bakinta tace "yaya  sannu ya jiki banza yayi mata Kmr bai ji ba nan kuwa yaji sarai hisham yayi qasa da murya  yace "ata ana maka sannu da jiki "naji !ya fad'a atakaice  dan ya fahimci wani abu a attare daita ba tun  yau ba  yana hankalce da irin kallon da take masa a duk sanda zasu hadu tun a office din aunty shahida yaso yaci ubanta allah ya taimaketa "take gabanta ya shiga fad'uwa sbd fargaba dan ganin ko kallon inda take tsaye bai ba illa kur'ban ruwan coffee  daya cigaba dayi kuma taji amsar daya bawa hisham kuma tasan sauran ma
sunji abinda ya fad'a  ."

ahankali ta juya ta nufi kofar fita cikin bacin rai sannan sauran yanuwanta suka biyo bayanta "amman ai ya kamata ka amsawa gimbiyata ya sake yin mgn can qasa"gsky hisham baka da hankali km kana bani kunya yanzu kai da gaske sonta kake "?sosai ma kuwa ina sonta sai dai ita bata sona ..""what ?" Wallahi haka ta fad'a ai naso bikin a hadashi da naka amman ya zanyi tunda tace bata só na hakura amman nasan sonta ne zai kasheni "amman shine ka kyaleta baka ci ubanta ba?
aa babu wannan ai kai ma kasan yadda soyayya take ka duba yadda baka son mrym kake son yarinyar mafarkinka "ka daina kawo wannan misalin ni bana son wannan yarinyar ita ma kuma bata sona kaga akwai matsala wajen namu hadin ko ka fahimceni ."?

"Misali ina sonta to ya zama dole dan ubanta ta soni sannan misali da'ace tana sona nima bazan dinga jin tsanarta haka ba duk da nasan nawa rashin son ne babban matsala dan ita prentending ne kawai nasan babu macen da zata kalleni tace wai bata sona dama ne kawai bata samu ba ,ya fad'a yana jan tsaki ka kira min auta  "me zata maka  ?Kai dai kira min ita kawai   yau  yarinyar nan zataci ubanta da me  tafika da zata ce  bata sonka ?shiru hisham yayi yana kallonsa a she haka ata yake sonshi jiki a sanyaye ya dauki wayarsa ya kira nana hauwa'u cikin kankanin lokaci ta bayyana a falon "yaya gani "je kizo min da nuzla yanzu yanzu kafarta kafarki "okay yaya ta juya da sauri ."su kuma suka cigaba da tautaunawa ."

Bayan mintuna goma sai gasu sun shigo nana hauwa'u ta  kama  gabanta  ta bar nuzla tsaye cike da fargaba  ta dan saci kallon hisham dake zaune taga ya sakar mata murmushi  ta kalli mr ata taga ya hade rai sai kafarsa daya yake girgizawa har  kusan mintuna  shabiyar tana tsaye sannan tace "yaya gani wai ..."da sauri ya dakata daita ta hanyar daga mata "waye wannan ?ya nuna mata hisham dake zaune "yaya hisham ".

"Very good meye a tsakaninku ?nothing ta bashi amsa atakaice ba hisham ba hatta mr ata sai daya dago tsumammun idanunshi ya tsura mata yana kallonta "kika ce nothing kenan baki san yana sonki ba ?nasani but na fad'a masa gaskiya ni bana son shi dan ..."enough ! bana  bukatar  jin  maganarki ko wani abu  kije ki fara shirin aurensa nan da kwanaki  goma  ." cikin firgici da tashin hankali ta shiga d'aga kafafunta zuwa inda yake zaune  "me yasa  yaya ?" dan Allah kayi hakuri karka min haka  wallahi ni bana son shi a matukar tsawace yace "nace karki sake fad'ar wata  magana anan , karki   sake kula kowa  acikin masu sonki shima wanda kike so ki kashe  soyayyarsa  acikin zuciyarki ki so wanda yake sonki  .."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

           Page 20

jikinta  na  wani  irin  rawa  ta k'araso ta  durkushe a gabansa har  bata  san  sanda  ta d'aura hannuwanta  duka bisa cinyoyinsa  tana  kallon  cikin   kwayar  idanunsa da  suka  rikid'e  suka  canza   kala   a wulakance  ya   zame   jikinsa  yana  mai  kawar  da   fuskarsa   gefen  hisham  dake  zaune   tmkr   mutun  mutumi  yana   kallonsu   cike  da  matsanancin  tashin   hankali   ,shi   kuwa  mr  ata  alamun  baya  son  kallon  fuskarta  ne   yasa   shi    maida  idanunshi  kan  hisham  ".

"dan  allah   dan  Allah !!  yaya  adam  kayi   hakuri    ta  kai  hanuta  tana  qoqarin   juyo  da  fuskarsa  gareta  domin  su  fuskanci  juna , zuciyarta  na  wani  irin    bugawa  da  karfin  gaske  take  kallonsa haka  ma  hisham  zuciyarsa ce take ta bugawa fiyye da   kaida   ya  soma jin  wani sauyi na   daban  a gabadaya  ilahirin   jikinsa   wanda  ke  gauraye da tsantsar   tashin  hankali,  shi  kuwa  mr  ata  mamakinta   yasa   gbdy   ya qasa   magana   duk da maganar   yake  son  yi .

Kwayar   idanunta  suka   cicciko  da  ruwan   hawaye muryarta a sarke  tace "dan   Allah  yaya   kayi   hakuri   karka  bari  wannan  auren  ya  kasance  domin   zuciyata   bazata  iya d'aukar wannan  nauyin  ba,   wata razananniyar  tsawa  ya buga  mata  wanda  ya  kamata  ace ta  tsorata   ta dawo da  hankalinta   jikinta   amman   ina  sai  ma  sake  narkewa  tayi  a wajen  zuciyarta  babu  tsoron  komai  acikinta , muryarsa  a kausashe   yace " tashi   ki   bar  nan  ki   kuma  fara  shirinki   kamar  yadda   na  fad'a  miki   oya  leave ."

"dan  Allah  ka  saurareni  yaya  "ya  girgiza  mata  kai   yana   cewa "   I don't  want  to listing anything  from   you  just  leave  now "dan   allah  yaya  adam  kayi   hakuri  ka  saurareni    akwai  maganar  da  idan  na  fad'a  maka   nasan   zaka   fahimceni "ata dan  Allah  ka  barta  ta  fad'i  abinda  ke zuciyarta    Hisham  yayi  maganar   yana  qarewa  jikin nuzla  dake  rawa  tmkr   mazari  da   kallo  , yadda  take  cikin   tashin  hankali  haka  shima  ya  tsinci  kanshi  cikin   tashin  hankali  mai  tsanani  har  yana  jin  ma  kamar  ya  cire   mata  nata  damuwar  ya  qarawa   kanshi "

Hisham  yayi  tsuru   tsuru  yana  jira  yaji  abinda zata  fad'a  ,yayinda  mr  ata  bai  ce  uffan  ba  ya yunkura  ya  mike  tsaye  ya  kwashi  wayoyinsa  ya  fara   taka  kafafunsa  da   kyar   zai  bar  wajen kasancewar  bai  son  yawon   magiya  bare irin nata dake   hargitsa   kwakwaluwa  nuzla  tayi   saurin  shan   gabansa  tana   fad'in  "yaya  karka  wuce  ka  bar  zuciyata  cikin   maseefa  tayi  maganar  cike  da  tausayawa  ,bai  yi  mata  magana   ba  ya  cigaba  da tafiya  yana  mata  gargadi  da  hannunsa  alamun ta shiga  hankalinta , bata  daddara  ba ta sake  shan   gabansa  dan   gbdy  zuciyarta  ta  rigada  ta bushe  babu  abinda  take  qoqarin  aikatawa  face  ta  bayyana    masa  ciwon  dake  cikin  zuciyarta ."

Ya  tsaya   kawai   yana   mata   wani  mugun   kallo
yana  furzar  da  iska   mai   zafi   daga  bakinsa muryarta  cike  da  rauni  da  buqatar  atausaya  mata  ta  fara  magana  "bazan  iya  jure  ciwon  rabuwa  da  wanda  nake  só  na  auri  wanda  kake  só  ba ta  karasa  mgnr   tana   rungumeshi  ajikita   tana  kuka a matukar   zuciye  ya  fixgeta  daga   jikinsa   yana  sake  furzar da  iske  "are you out of  your sense ?ni sa'anki   ne  da  kike  shiga  gabana? "  ko  ina  wasa dake   ne  da  ina   magana  kina   magana ? ya fad'a yana   kawar  da  fuskarsa   akanta  domin  dai zuciyarsa  ta  fara  tausaya  mata  tausayawar  da  bata  da   wani  amfani  dan  bazai  ta'ba  iya  mata taimakon  da  take  nema  daga   garesa  ba ."

Hisham  ya  rasa   meke   faruwa   atsakaninsu  babu  abinda  zuciyarsa  bata  kissa  masa  ba  a zaune  da  yake  tmkr an  dasashi  irin  kallon da take  ata  da  rungumar da  tayi  masa  ya  fara  gasgata  zuciyarsa  akan  abinda  bai  niyyar  yarda  dashi  ba  yaso ya  mike  ya  qarasa  zuwa inda  suke  tsaye  yasan ko akan  me  take  masa  magiya   har  da  runguma amman  hakan  nan  yaji  gara  ya  cigaba  da  zama a  inda  yake  zai  fiyye  masa  alkhairi   kuma  bugu da qari    yayi  imani  ata  bazai  ta'ba  aikata  komai  ba face  abinda  yasan  zai  zamewa  rayuwarsa  farinciki   he really  trust  him  mutun  ne  shi  mai  kyakkyawar zuciya   akanshi ."

Hawaye  na  gangaro  mata  bisa  kuncinta  yayinda  magana  ya  fara  fitowa   daga  bakinta  "ina qaunar ka  yaya  ? bai  yi  mamakin    jin  fitowar  hakan  daga  bakinta  ba  domin  ya  rigada  ya  gama karantata  tsab  "na sani  sai  akayi  yaya  ?ya  fad'a yana   kallonta  yana  jin  kamar  ya  soma  yar yarfa mata  maruka  ta  dawo haiyacinta  "dan  Allah  yaya karka  ce  min  a'a !   a kowani  hali  zan kasance  tare  da  kai "  ta  maimaita  hkn  a fili   yafi  sau   goma tana  mai kai  hannu ta shafa  kasumbar  dake   kwance a  fuskarsa  ji  yayi  kamar  ta  shafa  masa garwashin  wuta ,shi  fa  duk  duniya  babu  macen da  yake  jin  zata  ta'ba  shi   yaji  wani  abu  ajikinsa sai princess  ita ma  din   yanzu  ya  soma  gogeta a zuciyarsa  da  rayuwarsa ."cikin  fita  haiyacinta
  ta riko  fuskarsa  sosai  ta  sanya  kwayar  idanunta  dake  tsiyaya  ruwan  hawaye  acikin nasa " ban  san  hka  soyayyarka  tayi  tasiri  acikin  zuciyata ba  sai  dana  qasa  amsar  soyayyar  kowa ."

"Ban  san  tasirin  soyayyarka  ta  kai  mizanin  da  zan  iya  rasa  rayuwata  ba  sai  da  naji   zaka  min  nisa  , yaya   kaine  duniyata ruhina  yana  tare  da  kai  ako   da  yaushe , nayi  yunkurin   bayyana  maka soyayyata a tun  lokacin  da  mubina Ke mutuwar  sonka   amman  na  gaza  aikata  hakan  ina  ganin  cewar   zan  iya   cire   soyayyarka  na cigaba  da  rayuwata  amman   still  na  qasa  domin  kuwa  every  each  second   nake  jin  sonka na  qaruwa a cikin  zuciyata ,  ina  ta  qoqarin  sheida  maka  halin  da  zuciyata  take  ciki  kwatsam  kuma  sai   ga  batun   aurenka  da  marsi  bance  ka bar  marsi  ba  amman dan  allah  ka  had'amu  ka auremu " rokonki bai  kar'bu   ba   bare   wata   alfarmar  ya kamata ku koyi  yadda  ake  iya  control  din  zuciya  "ka taimakeni  ban  san  ya  zanyi  ba  " kar    allah  yasa ki   sani   ya  fad'a  yana  jan   tsaki   ."

kuka   take  sosai   tana   kallonsa   tmkr  ranar   ta  fara  ganinsa  shi   kuwa  haushi  ne ya turnikesa  a  wajen  zuciyarsa   banda  tuttukin  bakinciki  babu  abinda  yake , a  ganinsa  ma  ta  balain  rainashi
shi  zata  kalla  tace   tana so  alhalin  ga hisham dake  mutuwar  sonta?  "kayi  hakuri  dan  girman Allah  nasan zakayi  tunanin  komai  akaina   wallahi  haka  ne , dan  na rigada na   haukace  akanka  bazan  iya jurar  abinda   nake  ji  akanka   ba  sannan  bazan iya amsar    soyayyar   yaya  hisham  ba  ,dan  kona auresa  gangar  jikina  ya  aura  zuciyata  da  komai nawa  yana  gareka   da  kawai  zan  iya  rayuwa ..."

Ta  riko  hannunsa  hawaye  na zuba   daga   idanunta  ta  soma tafiya   dashi  taku  d'aya  biyu  yayi ya  tsaya cak , itama  ta  tsaya  suna fuskantar  hisham naunaye  ajiyar zuciya  ta sauke  tana  goge hawayen  dake  tsiyaya  ,ahankali  ata ya zare hannunsa  dake cikin nata  ya  yarfar   sannna  ya  zura  cikin  aljihun wondonsa  yana  jan  tsaki "ya hisham! ta  kira  sunansa  a kid'eme  "banyi  niyyar  fito  da  sirrin  dake  zuciyata  ba  amamn  ya  zama  dole  na  fad'a  maka  tunda  na  fad'awa  yaya   adam babu  komai  acikin   zuciyata  sai..." karki   kuskura  kiyi  wannan ganganci  dan  kome  zaki  yi  tawa  zuciyar   bazata   amince   ba "to  kuwa  gara    ka  ksheni da hannunka  na  huta   dan  nima  bazan iya  auren  yaya  hisham ba , yana   sona  ni kuma kai nake   so.."you're  very  stupid  Kiyi  maza ki  danna  madannin  gogewa  ki gogeni  arayuwarki  da   zuciyarki  dan ni  mallakin  mafarkina   ce   " yana   gama   fad'ar  haka  ya juya  ya haye  sama  yana  taka  step   yana  magana " hisham  ka manta da shirmen   wannan  yarinyar  ka  soma  naka   shirin   domin   wannan  auren ko   zata  mutu  sai  anyisa  useless  girl  kawai  ga  inda ake  sonku  aka  damu daku   amman ku  dinga  kai  kanku  inda  bazaa  ta'ba  sonku ba nonsense "

Hisham  ya  runtse  idanuwanshi "kenan  hasashensa  ya   tabbata ,  zarginsa   ya   zama  gasky   kenan akan ata  yake  shan  wulakanci  da  tsana  da wahala a wajenta ?   ,"ya  kalleta  cike  da  tausayawa yace "daman  ata  Kike so ?jikinta  yayi mugu  mugun sanyi ta rasa  me  zata  cewa  hisham  illa ta  runtse  idanunta  gam  tana  jin  zafi  da  ciwo  mara   iyaka a zuciyarta  ,ta durkushe qasa  tana kuka tana nemawar   kanta  mafuta   dan  dole  tasan  abun  yi  kafin  a had'ata  aure  da  hisham shima  ya durkushe  gabanta  ya  dago  ha'barta  ya  sanya  kwayar  idanunshi  cikin  nata , tai  saurin  buge masa  hannu  tana  kallonsa  cike  da tsantsar  tsana "ka  kyaleni  ni wallahi  bana  sonka  tunda  burinka  kenan  na  soka  , dan  girman   allah  ka  rabu  dani  ka manta  dani,  ka  manta da maganar  ka  ta'ba  sona  arayuwarka , ka  mantani  ta qarasa  fad'ar  haka  tana  fidda huci  mai  zafi ."

"Dan  allah  kiyi  hakuri  nasan  irin ciwo da  zafin  da  Kike  ji  acikin zuciyarki  ciwo ne  kwatankwacin wanda  nake ji  acikin  zuciyata  nasan  zafin  ciwo da radadin  kana  son  wani  baya  sonka ,wallahi  na  tausaya  miki  amman  me  yasa nuzla ?"me  yasa  sai  ata  zuciyarki  zata  kamu da so byn ni  ina qaunarki  ya  kai hannunsa  yana  share   mata  hawaye"ata bashi  da  wannan  lokacin   wahalar da kanki da zuciyarki   kawai  zakiyi  babu  wannan  tausayin a zuciyarsa    a karshe  ya  rungumeta  ajikinsa   tsam  yana  shafa  bayanta   ahankali  ahankali  babu yadda ta iya dole ta  kasance  rungume  ajikinsa  domin tana  bukatar  wanda  zai  rarrasheta  kuka  take  sosai   tana  rungume   ajikinsa "ki daina  kuka  nuzla  dan  zuciyata  bazata  iya  ganin  hawayenki  da damuwarki  ina  matukar  sonki  da  zaki  bani  dama da  sannu  zaki  daina  son  ata  ki soni  ya  fad'a  yana  qara rungumeta  gam   ajikinsa   ahankali ya mike tsaye  tare  daita  ya  nufi  kofar  fita  tun kafin mutane su  shigo su  fahimci  halin da suke ciki ."

Washegarin  da  misalin  karfe tara na dare   ata ya  shiga d'akin mami  sanye  cikin  fararen kayan bacci wondo da  riga , hannunsa  rike  da black cup dinsa  dake  dauke  da ruwan coffee  ,yayinda  dayan  hannunsa Ke cikin aljihun  wondonsa  ya samu mami  tsaye a gaban wordrobe  dinta tana qoqarin  rufewa  tana ganinsa ta sakar masa murmushi tana cewa "Masha allah   adamcy nan ya karfin jikin ?alhamd sweetheart ya qoqari dani ?kwana  nawa ya saura ai Allah Allah  nike  Kayi tafiyar nan ka dawo mu sha biki  ranar bani da dama zan aurar da d'a daya tilo ya  girgiza  kai kawai yana  ajiye  cup din hannunsa  akan bedside dinta  ya tsura mata tsumammun idanunshi yana kallonta tmkr wani maraya "yaakayi adamcy nan duk sanda kayi haka akwai abinda kake son fad'a  "haka ne sweetheart kin fi kowa sanin halina alfarma nazo nema ."

"Alfarmar kuma ?mami ta maimaita abinda ya fad'a
"Eh  ina neman wata  alfamar a wajenki   sweetheart "ina sauroronka Allah yasa zan iya ,ya marairaice  murya sosai kafin ya soma mgn  "dan  darajan  Allah sweetheart ki   qara min  lokacin auren nan wallahi wallahi wallahi !!! kinji na rantse   miki zan auri yarinyar nan zabinki , wasu yan kwanakin kawai zaki qara min har naje na dawo dan  zan dauki lokaci a france daga nan ma zan wuce  hollond  yi wasu abubuwa  masu  mahimanci  a  yanzu  na samu sauyin  lokaci amman kuma idan kina ganin zaa iya yin komai ko bana nan  fine na amince a daura auren ayi komai  amman da zaa bari na dawo sai nafi farinciki kasancewar ina son a hada auren dana hisham da nuzla yadda take kallonsa ya fahimci kamar bata yarda dashi ba "na rantse fa duk   wanda  aka rantse wa bai yarda ba shi din bana allah bane nayi miki wannan alqawarin sweetheart zan aureta ".

"naji amman  har zuwa wani lokaci ni wallahi zaka sani jin kunya auren sauran kwanaki ace an daga "karki damu sweetheart idan akwai damuwa kawai ayi ko bana nan  amman na fi son ina nan ,sai kace wata tsiyar zaka kulla  ko  kana ?ya dan ciza gefen lips dinsa "bansani ba ko zan iya kulla wani abu a auren da bana só ?kaji  dashi  tunani tayi karta je a daura yaki dawowa ya bar  yar mutane da nauyi akanta  gara kawai ta qara masa lokaci idan ya dawo sai ayi"Kwanaki nawa zan  qara maka ?uhm ko  Kmr wata biyu haka yayi  "what ! kai adamcy ban yarda da kai ba ,wallahi ki yarda dani sweetheart bazan baki kunya ba,  ba kuma zan saba alkwari ba I promise you ,ka cika alqawari  adamcy ,karki damu sweetheart  na ranse fa ,shikenan  na yarda da kai ta fad'a  kafin su fad'a hirar duniya a nan yake bata labarin   nuzla  murmshi mami tayi tana cewa "adamcy  nah mai farinjini ."

Zaune  mr  ata yake  agaban hajiya zulaiheart sanye cikin suit wondo da riga bakake   jikinsa na fitar da wani  kamshi  na daga hankali   fuskar nan nashi dake kwance da kasumba tayi fresh tayi kyau tana fitar da wani haske na dabam mai daukar hankali abun ka ga fari mutun  sallama  ya shigo mata dan sauran awa daya jirgnsa ya daga zuwa kasar  france  "Allah   kiyayya ya tsare min kai , ka kular min da kanka sosai banda wasa da abinci aci abinci akan lokaci kamar yadda doctor ya fada  "in sha allahu zan kiyaye sweetheart. Allah ya qara girma,ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani kema ki kular min da kanki "Ameen summa ameen nayi maka wannan alkwarin Allah yayi muku albarka gabadaya ku "inji mami ,sannan taja musu addu'a suka shafa tana shafa masa na hannunta a fuskarshi ."a tare suka mike suka fito inda tawagarsa Ke jiransa  a haraban gidan shi kadai ne zaune a bayan motarsa   limozin sai driver a mazauninshi, hawaye ya tsiyayowa mami   sanda motocinsa suke qoqarin barin gidan sai take jin kamar kar  ya tafi  amman kamar yau ne  zai dawo gareta wannan karan mami  ta kasa daurewa sai da tayi qwalla, gefe tayi da kanta tana  dauke hawayenta ."

*****

Yau  tsawon  kwana uku  kenan   mlm  yahuza yana zariyar  zuwa gidansu  maryama amman kamar  kullum    bai samu  ganinta ba  yau  ma   daga  massalaci  ya  wuto  kofar  gidansu  yana  neman yaron  da  zai  aika  cikin  gidansu  ko cikakken minti goma bai  yi da  tsayuwa ba, sai ga yaya sadam ya fito daga cikin gidan , nan  ya mika masa hannu suka gaisa "ina  fatan dai  lafiya  kwana  biyu nan  kake zuwa  gidan nan ?"Lafiya  lau wajen  maryama  nake zuwa  sai  dai duk zuwan  da  nake  yi  bana samun ganinta ,shine  dan  naci kake ta zuwa ?to ya  zanyi  sadam  tunda  zuciyata ta  kamu da matsanancin sonta  duk  da bani  da  tabbacin  ko  tana  sona amman   nasan  tana  son  fitowa inda  nake  habib  ke  hanata  fitowa  yanzu  dai  taimaka min  ka fito min  daita  dan  nasan muddin  habib na cikin gidan  bazai  barta ta fito ba ,murmushi  sadam yayi  yana cewa "kai habib  hukuma ne wannan yaron  bari ina  zuwa  !ya  juya  ya  koma   cikin  gidan  ya  shiga  side  dinsu maryama ."

a  parlour  ya  iskesu  gabadaya   suna  hirar  duniya ya  zauna  yana  fuskantar  maryama  suka  gaisa  da  aunty   sannan   maryama  ta gaishesa haka  ma  habib ya  amsa masu da "lafiya  lau cikin sakin fuska  ,ya gida da aiki sadam  ?Alhamdulillah aunty mun godewa Allah yace yana  duban  maryama "ga malamin ku  yahuza  can a kofar  gida  yana  jiranki  yau  tsawon  kwana  uku  kenan  ina ganinsa  ashe  wai saboda  ke yake zuwa  amman  bakya  fitowa."wata  irin  kunya ta  kama  maryama  ta  sunkuyar  da  kanta  kasa  tana wasa da  zara zaran yatsun hannunta".

"ai ga  d'an  albarka dake hanata  fita  nan , ko shi zai aureta bansani  ba ?yaro  qarami dashi sai aikin nuna isa da iko ita kuma shegen son dan'uwa  tana biye  masa  aunty ta  qarashe maganar tana zabgawa habib harara  ,habib  bai ce komai  ba ya tashi ya shige ciki  dan  matsawar  yana zaune  a falon bazai iya barin maryama ta fita  zuwa koina ba km hakan zai sa yaya  sadam  yaji  babu  dadi "ai  yahuza mutumin  kirki ne kuma ga dukkanin  alamun da gaske yake aunty tace "allah  yasa shi wai habib dan matsalar daake ta samu akan masu zuwa suna tafiya né yake jin haushi "nima na fahimci haka  amman in sha allahu komai yazo karshe  dan nasan yahuza bazai  mata haka ba nima gsky na yaba da hankalinsa maza  tashi  kije maryama karki dade  maryama bata ji dadi ba ganin habib ya tashi ya barsu  km tasan duk akan mgnr fita ne  ,amman babu  yadda ta  iya  yaya  sadam da aunty suna da karfin  iko   arayuwarta  ta  mike ta fita ta bar aunty da yaya sadam   suna magana bata san abinda ya cigaba da wakana  atsakaninsu ba ."

acikin  duhu ta sheida murmushinsa  ganin hasken hakoransa ta dan saki ranta da kawar da damuwar fuskarta  barkanki  da fitowa  gimbiya  maryama "numfashi  ta fesar "kai  ya kamata a yiwa barka da zuwa da  kuma sannu da  qoqarin  zuwan  da kayita yi  baka  samun ganina da km qoqarin da kayi   da iyayena last week  na  gode sosai  " ya dan kyaleta "iyayenmu dai na gyara miki ."  maganarsa ta dan mata dadi wannan yasa ta dan sakin fuskarta kad'an "ya kamata mu samu waje mu zauna ko can ne ya dan nuna mata wani dakali dake makoftansu ."

tare  suka  qarasa  amman  shi  yaki  zama ya tsura mata ido ya kamata ace kece kika fara zama sannan ni tayi shiru dan tuni ta gane manufarsa ta dan kallesa da idanunta cikin sauri ta kawar da kai ganin kwayar idanunshi na kanta to shikenan na zauna kema ki zauna ta zauna tana gyara zaman hijab dinta sukai shiru na dan tsawon lokaci daga  bisani ya dago ya dubeta "Maryama zuciyata duk ta gama tattara komai agareki a yanzu bani da wani shakka ko kwankwanto akanki muradina ne na samu damar da zan kawo kaina ga iyayenki domin a samu tsayayyen magana a tsakaninmu ."

     Soyayyarki ta jima ajikina maryama nayi dawainiya da soyayyarki tun kafin ki kai wannan lokacin na koyar da zuciyata dabarun da kuma yadda na dauki hakuri dan kawai na samu soyayyarki ban ta'ba gazawa ba , ina sonki maryama da zuciya daya ban qara jin ina sonki ba sai danaji halin da ke da mahaifiyarki da kaninki kuke ciki a gidanku bazan boye miki ba ina jin tausayinku most especially mahaifiyarki domin ta fuskanci abubuwa dayawa akan rayuwa kuma tayi hakuri na tausayawa rayuwar da kuke  ciki ki daure ki samar dani acikin zuciyarki mu daga darajan uwa da kuma danuwa mu tallafi rayuwarta data kanin mu  dukkan wani muradinki zan bi na tabbatar kina da burin kiyi aiki byn kin qare  bautar qasa kamar yadda naji kawayenki suna fad'a,burinki kiyi karatu mai zurfi Kiyi aiki ni nan zan barki Kiyi komai kike só zan barki ya dan saurara yana kallonta hawaye taji akan kuncinta  tasan  su da mahaifiyarsu abun tausayi né suna cikin tsananin kunci da bazai yuwu a boyesa ba ."

ahankali  ta dubesa "naji dadin  yadda kace zaka tayani  kula da mahaifiyata da kuma danuwana mlm yahuza ina matukar son Mahaifiyata ina son na gatatan rayuwarta domin ita kadace dani na yarda da soyayyarka kuma na amince duk lokacin da kake da lokaci kofar neman aurena a bude take domin burin mahaifiyata kenan  na tsayar da mijin aure fatana ka rikeni amana tayi shiru saboda kunyarta ta motsa ya sauke ajiyar zuciya a zahiri take fahimtar farincikinsa dan bai boye ba ."

Yayi  murmushi  yana  shafa  fuskarshi "maryama amanarki  agareni  bake  zaki bani amanarki daga allah  daya  halicceni ce  domin  shi na dinga roko ya bani ke  amatsayin  mata aurena  allah ya amsa tunda  har kin amince min dan  haka shi ya bani  wannan amanar dan haka nayi alkawarin bazaki taba  ganin  sabanin  haka daga gareni ba ,ba kuma zakiyi  danasani ba , aurena zai zame miki abun alfahari  bazan  ta'ba gudunki  ba bazan ta'ba juya miki baya  ba ."Soyayyar sati uku  da  sukai da  mlm yahuza ta fuskanci  tsantsar  son da yake mata kulawa kuwa  har  da mahaifiyarta abun mamaki kowa a unguwarsu  yasan  da soyayyarsu wasu  nasa albarka wasu  nacewa  ba girin girin  ba  allah  yasa a d'aure  kar ya  gudu ya barta kamar sauran."

******

Cikin   wannan  lokacin  maryama da   kawarta  subai'a  suka  je adamawa  domin   suyi   cam for three  weeks  bayan  sunyi  sati uku  a adamawa  alokacin  mlm yahuza   yayiwa    wani  mutun magana  akayi   masu  change  of  location  ita  da kawarta   daga  adamawa   aka  dawo  dasu lagos inda  zasu  fara  bautar  qasa a   Z &A    comapany   dake  kan  titin  guness  bayan  ciku cikun  da  mlm  yahuza  yayi  masu domin  shine  ya  shiga  ya  fita  ya  kar'bo  masu   letter   suka  kai wa  nysc  aka kar'besu  a kamfanin  bayan sun dawo  lagos  suka  fara savieces  dinsu  wannan taimako da mlm yahuza yayiwa maryama  ya  wanke   zuciyar  habib  yaji ya shiga ransa har ma ya fara kiransa da  otherhaif kuma yake  girmamasa yana mai jin ba qaramin dace yaruwarsa tayi ba domin kuwa samun maza irinsa suna  da matukar wahalar samu ."

"gashi shi dai ba wani zurfi yayi  a boko ba dan karatunsa  iya  diploma  ne  amman  yana  da  hanya kuma yasan  mutane  sosai dan shugaban RRS  mai ci alokacin abokinsa ne tare sukayi karatun tun daga primary har zuwa secondary inda anan suka rabu amman har gobe suna mutunci  da abota , fara  bautar qasa yayiwa maryama dadi dan daman  zaman gidan ya isheta dan tun da suka qare karatu babu inda take zuwa bayan  islamiyya  gashi ita daman fita bai dameta ba saboda ita ba maabociya son yawo bace amman wahalar da take sha da yawon sata aiki da mutanen gidansu keyi yasa tayi maraba da da wannan fitar tata kullum fatan allah ya taimaketa tana qare bautar qasa ta samu aiki ."

Ranar  wata  asabar  tana  zaune  shiru a side dinsu  tana tunane  tunane  akan  sakina  tana matukar  qaunar sakina  aranta ta kasa jurewa   abubuwan da take mata batare da tasan laifinta  ba ,zuciyarta ta bata  shawarar taje ta tmbyeta  ko  wani laifi tayi  mata wanda yasa ta canza mata ,nan  take  ta amince da  shawarar  zuciyarta , dan hk ta mike tsam ta fito ta nufi side dinsu ta yi sallama a tsakar gida babu wanda ya amsa  mata  dan  haka  ta wuce daki  inda tafi  tunanin sakina take  mintuna sha uku da zamanta  amman  sakina  bata ko kalleta ba ."

Ahankali  maryama ta  tunkarareta  da abinda ya shiga  a tsakaninsu "haba "yar uwata  mai na yi miki ki ke fushi  dani  tsawon Lokaci  ko  magana ba kya min  mai  nayi miki  da hukuncina ya cancanci haka.?""Cewa na yi kin min wani abu?sakina  ta tambayeta tana  mai  kallo  cikin   idanuwanta  maryama ta sauke nata  idanun  ganin irin  kallon da Sakina ke mata. Ta ce"tô  Sakina tsawon  lokaci   naga  bakya min  magana, in da nayi miki laifi  ne sai ki sanar dani na nemi yafiyarki bana jin dadin yadda kike nuna ko in kula gareni  tsaki kawai sakina  taja ta fice tana magana cikin ranta wanda sam maryama  bata ji  dadin abinda tai  mata ba  "na shiga uku maryama   ta fada a ranta me  zai sa sakina ta yi min  haka  kawata kanwata kuma yaruwarta masoyiyarta?ya Allah  ka  sanyaya  zuciyar  sakina  akaina  idanunta   cike da hawaye ta baro  side dinsu ."

Ranar  wata  laraba  aunty  salma da yaranta biyu suna zaune a tsakar  gida  aunty  salma ta dubi sakina "wai  Ke  kwana  biyu  nan mai yake damunki ne  sai  ki dinga kadaita  kanki  kina wani shiru idan wani  abu   aka miki  bazaki fad'a ba  sakina tace" ko na gaya miki ba iya magance  min zakiyi ba duk da ku  ka jawo halin da muke ciki nida  yaruwata shukura ,maryama dake kokarin shigowa cikin side din nasu  ta  dan. tsaya  ta kasa kunne aranta tace "allah  sarki ashe  yaruwata  laifi akayi mata tayiwa gidan kudin  goro  kowa bata shiri  dashi."

aunty  salma tace " koma  me akayi  muku   zurfin cikinku ne ya janyo muku Ke kanki kinsani duk damuwarku  kema  kinsan zanyi qoqarin magance  muku   ita matukar  ina numfashi  acikin duniyar nan  sanar  dani  menene  aka muku  da har  yake saka ki  cikin kunci "kusan rabin yan makarantar islamiyyarmu  sun  san  yadda shukura ke son mlm yahuza  amman  kiri kiri  kuna kallo wannan banzar ta  juya abun ya koma  kanta gashi har ana batun saka  rana  aure ."

Da alamun  aunty  salma  taji dadin furucin sakina akan maryama  domin  duk irin kunci  da halin koin kula da suke ciki da sakina bata gani ba bare ta shiga cikin maganar  tayi musu sulhu "aunty salma tace" to meye  keda yaruwarki  ? maryama ta fahimci kalmar  cikin  zolaya tayi  maganar ,ai kuwa nan da nan sakina  da shukura suka bata rai cikin nuna tsantsar  tsana "wannan banzar ce yaruwarmu daace kun  koresu a gidan Kmr  yadda kika ce ai da bata yiwa  shukura  kwacen  saurayi  ba  yanzu  gashi nan muna  ji mun gani  wanda shukura take so  dole zata hakura "a'a waya  gaya maku ai  babu wani  maganar wani  hakuri  ,kuyi  hakuri tunda kun fad'a min ku bani  kwana uku zaku ga abinda zai faru."

hankalin maryama  ya tashi  kwarai da gaske har yasa  daga  nan bata  sake  sanin abinda suka cigaba da tautaunawa ba  saboda wani daci da  zuciyarta ta dauka ."jiki a matukar ta sanyaye ta dawo side dinsu "ita bata san shukura tana son mlm yahuza ba da sam  bazata  amince da soyayyarsa ba sai ma ta hadasu  amman yanzu ya zatayi ?ko da  yake ta fahimci wani sabon salon cin zarafi ne ake son bullo mata  mata  dashi  dan arabasu dan  haka zata bari adduarta tayi karfin  da bazasu samu nasara akanta ba  tun daga ranar bata sake runtsa idanuwanta ba wajen kiyamul laili  domin  kiyamullaili  tana  qarawa nauyin mizanin  bawa, tana qarawa mutun hasken  fuska  da  samun kwarjini da d'ga darajan mutun acikin mutane kariya ga dukkan sharri  tare da biyawa bawa bukata."

Duk  bayan  kwana  biyu  mlm  yahuza  yana  zuwa wajenta  Kmr yadda ta tsara  masu dan bata  son  yawon  zance ,tun bayan kwana biyu  sunyi da mlm yahuza zai  zo sai dai har  karfe  takwas na dare daya saba  zuwa   bai zo  ba amman ta rasa dalili hakan ta kasa  hakuri  ta  shirya  tsaf ta fito zuwa bangaren Ummah  ta iske  shukura  tana  zance  sai  dan kasancewar  dare  bata lura da wa take zance ba sai dai  kawai  kamshin  turarensa  yayi  mata kama dana  mlm yahuza amman  ko  kadan  bata kawo shi bane ta shiga bangaren umma tana zaune suka gaisa
Daga  nan  suka shiga hirar duniya har sanda shadaya ta buga ta mike tayi mata sallam ta  koma side dinsu  cikin  tsinkewar zuciya dan bgabanta banda luguden bugawa babu abinda yake ."

Shigowarta  kenan  daga  wani  kamfani  kai  zanenta domin  tallatawa  ,da  baba gali ta soma ci karo "yar gwal  idan kin huta ina son magana dake dam taji gabanta  ya  fadi  tun da take arayuwarta bata jin ranar da baba gali yace yana son magana makamanciyar   haka  ba  km  wai  yar gwal  yana son  magana  daita  tabbas  akwai  mahimmiyar magana , bata kawo komai aranta ba sai tunanin watakilla ko mgnr mlm yahuza ce tayi karfi tunda ya sha fad'a mata yana son manya su shiga ciki ta nufi bangarensu ta kammala komai nata  a natse ganin shima ya fita masaalaci tayi sallah har ishai sannan ta dawo parlour ta zauna zuciyarta na tunanin akan maganar da baba gali zai yi daita duk da bata san abinda zai sanar daita ba amman sai maganar ta tsaya mata arai cike sa  fargaba ."

Karfe tara daidai  umma ta aiko  a kirata  ita da aunty   nan fa   gaban  maryama   ya cigaba  da fad'uwar da yake , tare suka  fito  da aunty  alokacin shukura ta shigo daga zance tuni aunty ta wuce dan har ta kusan  isa  bakin side din  umma, haka nan ta kalli shukura dake  zaune  kusa da aunty salma dake cin abinci  atsakar gida ta sake gaishe da aunty salma ta wucesu ta shiga bangaren umma ta gaisheta cike da girmamawa  umma taji dadi sosai ta tmbyi lafiyar habib ."

shiru ne ya biyo  baya har na kusan mintuna asirin sai ga aunty salma da aunty  hassana sannan byn an gaisa umma  ta numfasa tace "Maryama wata tmby nake son nayi miki game da yaron nan dan gidan lawan yaro ?"dam  taji bugawar da qirjinta yake ya qaru , tayi shiru domin bata damar tmbyrta ta cigaba da magana "tsakanin keda shukura wa yace yana só né ?"

Maryama  tayi shiru lokacin da maganar ta doki dodon kunneta wannan  wace irin magana ce akwai abinda  umma batasani ba a tsakaninta dashi ?amman  dai koma menene  batasan abinda yasa take mata  wannan tmbyr ba, ta bude baki zata bata amsa abinda Ke tsakaninsu sai kunya ta hanata tayi kasa kawai  idanuwanta "Maryama tmbyrki nake baki ce komai ta  sake yin  shiru a karo na biyu tana son jin ba kece wacce kuka fara son juna ba har yake zuwa zance wajenki ba ? ta sake yin shiru tana son bata amsa sai dai bazata iya sanar daita ba tunda gashi ita da kanta tasani   kuma tana da masaniyar wajenta yake zuwa, ita me yasa umma zatayi mata wannan tmbyr akan abinda ta rigada tasani tunda sau tari ita ke cewa taje  idan yazo bata son fita ."

"Abinda yasa na kiraki nake tmbyrki shine dazu da yamma byn fitarki kai  zane  yan gidansu sunzo domin auren diya a gidan nan kuma sun bayyana wacce suka zo nema ni da azatona kece yahuza yake zuwa wajenki ashe yaruwarki shukura  yake so ."
ba idanuwanta  ba hatta numfashinta da kwakwa luwarta sai da suka daina aiki wani tsayawa tayi na wani lokaci kafin ta sauke naunayen ajiyar zuciya  ta juya idanuwanta kana  tashiga   tunani da kwakwa luwarta batace komai ba saboda tashin hankali daya risketa ta sunkuyar da kanta qasa kawai  tana jin damuwa mai tsanani "

"Magana nake maryama kinyi  shiru daman bake yake nema ba yauruwarki yake nema ?ta qara yin mata tmbyr bata san abinda zatace ba ganin zata batawa kanta lokaci da jama'ar dake wajen yasa ta dago kanta tace "tunda shi da kanshi ya sanar da wacce yake nema ai babu laifi umma , umma tayi shiru kawai tana dubata ina son gane abun ne domin ni a tunanina Ke din ce  yake zuwa wajen ki kawai ta dago tace "ba wajena yake zuwa ba wajenta yake zuwa tana gama fadar haka ta mike da sauri dan zamanta a waje zai yasa ta zubar da hawaye ta bayan bangarensu inda aunty Ke aiki ta labe tana kuka mara sauti dan kar wanda ya ganta ta tsaya anan ta rarrashin kanta ne dan karta dagawa  danuwanta hankali."

Sai datayi mai isarta sannan  ta fito ta shiga falo kai tsaye  ta wuce habib  dake  zaune yana  kallon ball dakinta ta shiga ta kwanta lamo akan katifa ahankali kalaman mlm yahuza daya dinga furta mata suka dinga dawo mata cikin kwakwaluwarta  da taimakonsa  gareta  hakika  bazata   ta'ba  mantawa dashi  arayuwarta ba ta  dinga  girgiza kai shikenan shima ta rasashi  ,hawaye  suka dinga zuba daga idanunta bata san tana shesheka ba sai dataji muryar  habib  yana cewa "kamar shesheka nake ji heartbeat  tayi  saurin  gyara kwanciyarta tayi shiru tare da lullube kanta tana tunani abinda ya kamata ta fad'a masa  idan ya qaraso gareta domin dai abinda yake gudar mata kenan gashi ya faru daita  ta runtse idanunta sosai alamun ta fara bacci ganin hk habib ya juya ya koma falo ."

Bangaren umma kuwa gyara zama aunty  tayi ta kallesu "hakika  bakuyi adalci ba  saboda ni nasan wannan yaron wajen maryama yake zuwa me zai sa shukura zata qaunaci wanda yake son maryama har ku iyayenta kusan hanyar da kuka bi kuka raba maryama dashi ?mgnr  tayiwa ummah dadi ko babu komai yau zata gwada kunjinta akan damuwarta
Aunty salma ta gyara zamanta itama tasoma magana Kmr tana jira "kada a kawo maganar rainin hankali acikin maganar nan kina tunanin shukura zatace tana son shi ne ?".

"to kisani diyata bazata ta'ba cewa tana son wani ba shine da kanshi yace yana sonta kuskure yayi yace yana son maryama dan kawai ya samu hanyar da zai ce yana son shukura bude kunnuwanki da kyau yahuza ya dade da soyayyar shukura acikin ranshi nauyinta kawai yake ji dan hk ya fara gwada soyayyar daga kan maryama ganin bata da wani matsayi da aji ya dawo hanyar madaidaiciya ba kuma diyata tace tana son shi ba idan kuma har abun ya dameki sai kisa diyarki ta sameshi kice ya daina son shukura ya dawo kanta."

"Uhm kawai aunty ta furta a fili  sannan a fili   tace allah kai ne allah kai ka kawo ma maryama yahuza amatsayin wanda yake sonta  byn ta rasa sauran kuma na tabbatar yahuza yana son maryama da gsky Allah kai kasan abinda akayi  aka shiga tsakaninsu ya Allah kayi mata sakayya  nasan zaka kawo mata wani wanda ya fishi   komai   "Wai me maganarki take nufi ?kina nufin an kwacewa maryama saurayi ne ko me ?"wannan ai gskyr da kowa ya rigada yasani ce maryama  yake so kuma dan ita yake zuwa gidan nan ,na rasa wannan maseefar babu damar aga maryama da cigaba duk yadda zaa yi sai anyi an rabata dashi ".

"Dakata dakata!!  su waye dasu waye idan zakiyi mgnrki Kiyi mgnrki a inda bazai zame miki damuwa ba , ina maryama take ?me ye tafi sauran mata  da idan ta samu cigaba ake rabata dashi ?ita din gwal ce ko me ? inji cewar aunty hassana "tunda yaro yace ga wacce yake so ai magana ya qare sai ayi shirin aure "a'a hasaana wannan ba magana bace  allah baya son zalinci kuma baya son wani bawan yayi ,hakika idan akayi auren nan an zalici maryama "umma ki rabu dasu hassada ke damunsu akan maryama ,amman maryama din da kuke gani tafi gwal wallahi kuma kaf zuriarku babu macen data kaita allah na tuba idan nayi alfahari  ka yafe min ba alfahari nayi ba gsky na fad'a ."da sannu  hassadar  zata cinyeku  ni natashi  allah ya bamu alkhairi  allah yayi mata zabin abinda yafi zama alkhairi arayuwarta da izinin allah maryama sai ta kawo maku wanda bazaki iya kwacewa ba tana gama fadar haka ta mike ta bar falon ."nan fa hayaniya ta kaure aunty hassana na zaginta aunty salma na qarawa ummah kuma tana basu rashin gsky ."

Aunty ta  shigo  parlour'n  tana  kuka  nan da nan hankalin habib ya tashi ta wuce shi ta nufi dakin maryama tana kwance  har lokacin tana zubar da hawaye  tana tuno daddan kalaman mlm yahuza gareta atare suka fad'a  dakin  ta qarasa ta zauna bakin gadon ta kamo hannun  maryama ta damke cikin nata jikinta  har ya  dauki  zafi  ta fashe da wani sabon kuka wanda yasa kukan maryama ya fito fili ta yunkura ta mike zaune  cikin  mawuyacin  hali tana cewa "why aunty ?me yasa kike asarar hawayenki akan dan wannan abun ? "duk fa abinda kaga  allah bai baka ba to ba rabonka bane Kiyi hakuri ki daina kuka  please cikin rawar muryar habib yace "aunty meke faruwa ,abinda kake gudu dai ne ya sake faruwa sun rabata da yaron nan yahuza yaron kirki "what !?"

"Wallahi habib sun rabata dashi wai shukura zai aura ba maryama ba amman babu komai  akwai allah  wani  irin ihu yayi yana kurma uwar ashariya  ya juya  maryama tayi saurin durowa ta rike masa hannu  ya juyo ya kalleta "ki sakar min hannu heartbeat  ba shukura ba hatta shi kansa mlm yahuza sai naci ubansa yau koni koshi girgiza masa kayi tayi "bashi da laifi nasan akwai abinda akayi masa domin da kunne naji  komai nan ta zayyana masu hirar aunty salma da yayanta akan  mlm yahuza, dan haka kasani mlm yahuza baya cikin haiyacinsa ,mlm yahuza mutumin kirki ne idan nace banji zafin rabuwa dashi ba nayi karya jikinsa a matukar sanyaye ya zame a zauna qasa ya dafe goshinsa da  hannunsa  daya  yana jin ciwon abinda ya faru" yanzu abinda shukura tayi mana kenan ya fad'a cikin jin haushin ,to ya zamuyi mu mun dogara da allah  aunty ta sake riko hannun maryamu "Allah yayi maku albarka a rayuwarku  ,allah ya baki miji na gari,  idan da rabo Allah ya juyo da hnkln yahuza  ya dawo gareki  ya kula dake ."

"Maryam tana kuka aunty tana yi tana goge mata hawaye "Kiyi  hakuri  maryama "kema aunty Kiyi hakuri  bana son ki  daga hnkln ki akan matsalar  nan ,in sha Allah nan  kusa  Allah zai bani wani "In sha Allah bazai  dade ba  Allah karka barmu da iyawarmu ka iya mana dukkanin abinda bazamu iya ba  har kusan karfe dayan dare suna tare kuma duk mgnr mlm yahuza suke aunty bata so tayi nesa da maryama  , tafi son bacci ya zo mata  tana  tare daita
don Allah ki daina damuwa kinji ' yata ki kwanta Kiyi bacci Allah yayi miki albarka yayi wa rayuwarki data ' ya'yan da zaki haifa  albarka,  In sha Allah bazaki dangwama a hk ba Allah zai saukaka mk  na yafe miki duka laifukan da kikayi min wnd na sani da wnd bn sani ba daga  hk  tayi shiru tana goge hawayen idanun maryama , amma tamkar sake kara mata su ake .

Ba  sosai  damuwa  yake  tasiri  acikin zuciyar maryama ba  bare irin wannan damuwar da idan da sabo ta  saba amman tabbas wannan damuwar ta doketa  sosai  dan duk kwanaki   bata iya bacci adduar nenan zabin allah  kawai takewa kanta zuciyarta chunkushe da bakinciki mara misaltuwa har akayi kiran sallah asuba bata runtsa ba hakan yasa ta mike da kyar ."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.