Best / Popular Hausa Novels

Maradams Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt

Chapter 18 of 18

Page 26

hankalin maryam ya qara tashi Kuka take sosai da iyakacin karfinta tana furta duk wata adduar data zo bakinta domin neman cikawa da imani dan gabadaya ta sadaukar da rayuwarta akan mutuwa zatayi yayinda hindu ke tsaye rungume da hannuwanta duka a qirji tana sakar mata murmushi farinciki tana kallon yadda motar ke tahowa wajen motarta da maryam ke ciki ."

maryam ta kamkame jikinta sosai tana mai sake fashewa da wani gigitaccen kuka jira kawai take taji saukar motar akanta amman sai taji shiru sai ma jiniyar motar ' yansanda ta jiyo dan haka da sauri ta ware idanunta dan tabbatarwa kanta gaske ne ?ganin motar yansanda ta sha gaban motar yasa ta sauke wani naunayen ajiyar zuciya da numfashi atare ,yayinda mutumin dake ciki motar ya soma qoqarin fitowa domin ya tsire amman cike da hanzari yansanda suka samu nasarar damke bala ,cikin tsananin tashin hankali yake masu bayanin komai dan gabadaya ya gama rud'ewa "

Yayinda hindu ke tsaye awaje kamar an dasata tsabar firgitar da tayi zufa ce kawai ke karyo mata dan kana kallonta zaka fahimci yadda hankalinta yayi mugu mugun tashi , gashi tana son guduwa kamar yadda bala yayi qoqarin yi amman ta kasa aiwatar da hakan har sanda ' yansanda suka samu nasarar daba masa ankwa a hannuwansa tana tsaye kikam kamar mashi ."

Zuciyar hindu ta shiga bugawa da matsanancin karfi nan take ta shiga sake sake hade da jerowa kanta tmby "wa yasan shirinta ?wa ya turo 'yansanda ?"yaakayi suka san inda zata aiwatar da shirinta akan maryam ?ita dai tasan daga Allah sai bala da zasu yi aikin tare suka san komai dan hatta babanta bata bari ya sani ba ."

shiru tayi kawai har zuwa lokacin da yansanda suka qaraso zuwa inda take tsaye suka tsaya a gabanta
a wulakace ta d'aga kanta tana kallonsu d'aya bayan d'aya tare da bude bakinta zata soma zazzaga masu ruwan bala'in 'bata mata shirinta da sukayi amman sai taga daya daga cikin police din dake tsaye a gabanta ya ciro I'd card daga gaban aljihunsa yana nuna mata kasancewar babu uniform ajikinsu da alamun cid ne ."

wani dogon tsaki taja tana cewa "ai ni ba makauniya bace, ko baka fito da I'd card dinka ba nasan ku din yansanda ne "? dan sanda ya gyada mata kai kawai yana kallonta a tsanake kafin daga baya ya soma magana "da fari ki miko mana key motar hannnunki a fito da wacce kikayi yunkurin kashewa " furzar da iska mai zafi tayi daga bakinta kafin daga baya cike da maseefa tace "bazan bayar ba ,dan tunda nayi niyyar kawar da maryam daga duniya a yau din nan sai nayi babu fashi idan yaso nima daga baya akasheni tana qarasa maganar tabi gefensa zata wuce har tayi taku biyu taga wata gajeruwar macen yansanda ta harde mata kafafu sai gata dim a kasa ta zube bisa gwiwowinta inda key'n hannunta ya fadi kasa ."

Macen yansanda ta qaraso inda hindu take wargaje a kasa cikin azaba ,kallo daya zaka ma macen yansanda kasan babu rahma a fuskarta ta d'auki keyn daya fadi ta mikawa d'ansandar dake tsaye a kusa daita"ungo naziru maza ka fito da yarinyar" ya karba keyn daga hannunta da sauri ya nufi inda motar take ."

Macen yansanda ta fito da ankwa daga cikin aljihunta tana duban hindu a tsanake kafin daga bisani ta soma qoqarin kamo hannunta domin da'ba mata ankwa amman hindu ta fixge tana zabga mata harara "ki miko hannunki na saka miki ankwa ko kuma na harbe kwakwaluwar kanki yanzu ." wani murmushin bakinciki ya bayyana akan fuskar hindu "bazan so faruwar haka ba ,dan bazan so na bar duniyar nan batare dana kawar da mutun biyu din nan a duniya ba,wannan hatsabibiyar yarinyar da kuma wanda zai aureta, duk da na shiga hannu amman ban yi nadama ba ,dan ni kadai nasa me nake ji a zuciyata yadda zan rasashi dole itama ta rasashi ."

Ta sake yin murmushi wanda kana gani na takaici da bakinciki né da rashin cimma buri "duk da na shiga hannun amman nasan zan fito dan mahaifina zai yi iya qoqarinsa sannnan zai kashe ko nawa ne akan yaga na fito tana gama fadar haka ta mika mata hannuwanta duka , sai da suka kalli juna da sauran yansanda nan take suka fahimci yanayin cewar hindu bata cikin hayacinta ,ta daba mata ankwa a hannuwanta tana cewa "duk abida kike taqama dashi wanda yasa muka bibiyi rayuwarki har zuwa yau din nan ya fiki kuma yafi mahaifinki komai ."

"idan taqamar mahaifinki nada kudi ya zartashi dan haka kisani matsawar bashi ne ya lamunce ki fito ba ubanki bai isa ba ,kuma bashi da kudin da zai fito dake oya muje ."ta qarasa mgnr alokacin da aka qaraso da maryam wacce ke kuka har lokacin ga wata zufa dake tsatsafo mata a dukkanin ilahirin jikinta kallo daya zaka wa maryam ta baka tausayi ."

Wani wulakantaccen kallo hindu tayiwa maryam sannan ta yunkura ta mike tsaye cike da d'agawa da isgilanci ta kalli macen yansanda tace "koma waye shi ina mai tabbatar miki mahaifina yana da karfin ikon da zai sa shi ya lamunce a fito dani ta qarasa maganar tana sake watsawa maryam mugun kallo "Ke kuma ki jira fitowata wallahi karon mu bazai yi kyau ba, bazan ta'ba barin kiji dadin rayuwarki ba, baqar makira wallahi nice ajalinki ki rubuta ki ajiye ."

wasu hawaye masu zafi suka gangaro acikin idanun maryam hankalinta ya qara tashi fiyye da lokacin da take cikin mota ,yayinda zufa ke sake karyo mata muryarta a raunane. tace "police kunji abinda take fad'a wai zata kasheni itace ajalina "ki kwantar da hankalinki babu abinda zata iya miki daga hannunmu sai kotu zaa kaita daga kotu kuma sai gidan kurku kinga babu wata hanyar data sauran mata "karya kake munafukin Allah bani ce zani kurku ba uwarka ce zata kurku shegu matsiyata kawai tass tasss!! taji saukar mari har sau biyu ajere akan kuncinta nan da nan ta rikice ta dinga zaginsu tana tsine masu albarka mrym tana kallo aka tasa keyar hindu da bala abayan motar yansanda ita kuma aka sakata cikin wata motar aka d'auki hanyar gida daita ."

Acikin mota hindu ta kalli macen yansanda taja wani dogon tsaki ta bude baki zatayi magana kenan taji sauka mari tasss!! ta sauke mata wani lafiyayyun mari "kina sake bude mana wannnan rubabben bakin naki zan qara miki wasu marukan dan haka ki kama kanki ki bari salin alim mu kai ki office idan ba haka ba zan sakar miki harsashi yadda taga matar tana mgn tana zazzaro mata idanuwa tana huci tasan da gaske take zata iya aikata fiyye da haka amman bata jin zatayi shiru ."

Ta dinga kallon matar zuciyarta na cigaba da yi mata zafi ranta da zuciyarta na wani irin tafasa ta dinga zagin yarsadar can kuma tayi shiru tana son sani waye yyi mata wannnan shishigi da katsalandar cikin rayuwarta ? cure hannuwanta tayi waje daya tana bugawa da juna batayi tsamanin shirinta zai ruguje haka ba ta dauka zatayi komai ta gama babu wanda yasani taci bulus ,wato mutuwar maryam ya tafi a banza bata kawo abun zai zame mata haka ba ."

Suna isa police station ta ciro wayarta daga cikin jaka zata kira number babanta amman taji an bata warning tare da kwace komai dake hannunta aka turata cikin wani qaramin daki wanda aka tanada domin masu laifi irin nata sannan suka maida kofar suka rufe garam ."kukan bakinciki bata cima burinta ba gashi kuma ta shiga hannun hukuma ya kufce mata ,dan haka ta soma maganganu cikin zafin rai tana zage zage tana tsine masu amman babu wanda ya kulata har sai data gaji dan kanta tayi shiru ta fara bin d'akin da take ciki da kallo kusuruwa kusuruwa banda duhu da zarni ba abinda ke tashi ciki ,ga kukan tsoro tun yanzu data kasance ranar allah ce ina ga dare yayi ? tsayuwa tayi taki zama dan bata ga wajen zama ba koina ta kalla kazanta né shiru tayi kawai tana tunanin mafuta ."

Cikin wani irin tashin hankali maryam ta shiga part din hajiya zulai tana kuka a parlour'n ta iske nana hauwa'u da mami zaune suna ganinta gabadayansu suka mike cikin tsananin damuwa suka isa inda take mrym ta zube jikin mami tana yi mata bayani abinda ya faru gaban mami yayi wata irin faduwa "yanzu d'an rashin imani hindu tayi qoqarin kasheki ? ta qarasa mgnr tana mai sake kamo maryam din zuwa jikinta ta rungume tana cewa " yanzu ina hindu take ? police sun wuce daita ."

Mami ta dafe kanta cikin yanayi na tsarkakkiya da shiga tashin hankali ,cikin tsananin' bacin rai mami ta zaunar da maryam ta soma magana "aikuwa wannna karon bazan yarda ba ,bazan zuba ido su kashe min ke ba ,"wannan ma ai rashin sanin darajan d'an adam ne ,wallahi da nasan police station din aka kaita da sai naje naci ubanta inji cewar nana hauwa'u " zagi kam babu wanda hindu bata sha shi a wajen nana hauwa'u ba, ita kuwa mami har da kwallar takaici ta zubar tana mai jin tausayin maryam wacce har lokacin kuka take ."

Suna cikin wannan halin na tashin hankali ATA ya turo kafar parlour'n ya shigo tare da sallama duk da bai bude muryarshi sosai ba fuskarshi kamar koda yaushe, cike da ladabi ya gaishe da mami yana mai zama akan kujera idanunshi a runtse ta amsa tana masa bayanin abinda ya faru "yanzu da wani abu ya faru da maryama shikenan taci bulus "

"Ina fa taci bulus ".
ya fad'a haka acikin ransa amman a filli yace "ai ni data samu nasarar kasheta ma da ta taimakawa rayuwata "ya fad'a yana ciza gefen lip's dinsa da d'an karfi yanayin yadda yayi maganar ya bala'i daurewa hajiya zulai kai ,tayi matukar mamakin jin abinda ya fad'a, ba ita ba hatta nana hauwa'u tayi mamakinsa kuma taji babu dadi aranta "yanzu abinda zaka fada kenan adamcy ? yayi shiru kawai yana lumshe idanuwanshi "rayuwar mutun kake fadar haka kamar rayuwarta baa bakin komai yake ba "?me zan fada sweetheart da wuce haka nifa kasancewarta a raye babbar matsala ce arayuwata ."

"Ka kuwa san abinda kake fada adamcy "?
"iyakar gskiyata kenan na fada sweetheart kuma kin san bana fadar abinda bashi né acikin zuciyata ba ,wannan kawai ya isa ki fahimci irin rashin son da bana mata ,wallahi da zata mutu da gaske da zanfi kowa jin dadi " ni kake fadawa haka adamcy ?a gabana kake wulakata min 'ya dan baka da mutunci na rantse da girman allah sai na sa'ba maka akan wannan maganar kuma matsawar baka d'auki mataki akan abinda akayiwa maryama ba sai ka had'u da fushina da baka gani ba ."

maryam ta sunkuyar da kanta kasa tana sheshekar kuka zuciyarta na wani irin bugawa da karfin gaske wani irin tsoro ne ke ziyartar zuciyarta bata ta'ba sanin qiyayyar da yake mata ta kai haka ba sai yau din nan cike da fushi mami ta cigaba da magana "idan banda rashin mutunci irin naka agabana adamcy ,nice fa da kaina na zaba maka maryam yau ko aljanna ce maryam nace ka aura ai baka mata fatan mutuwa ba bare diyar mutun diyar ma tawa ko ka manta matsayin maryam ne a wajena "?

Yana jin mami yayyi shiru dan duk abinda ta fad'a din ya sani "wallahi ban ta'ba sanin rashin mutuncinka ya kai haka ba sai yau ,mutun sukuntu guda kuma jininka da ubanta da ni uwarmu d'aya ubanmu d'aya fa, amman dan rashin mutunci kayi mata wannan fatar ,wallahi yadda zakayi farinciki da mutuwar maryama nima nasan zakayi farinciki idan na fadi na mutu "ya bude baki zai yi magana tayi saurin katseshi ta hanyar cewa "wallahi idan ka sake min wata maganar banza a nan zan iya kafa maka hakora "bai ce uffan ba ya mike tsam ya haye samansa, jiki a matukar sanyaye mami ta mike tana goge kwallar idanunta ta nufi hanyar d'akinta."

tashin mami ya bawa maryam damar rushewa da wani kuka "banason na kawo damuwa acikin familes ,sister ya zaa yi a fasa auren nan kowa ya huta ? nana hauwa'u ta rungumeta tsam ajikinta tana rarrashinta"sister ki duba yadda yake nuna tsanata qarara wannan wani irin kiyayya ne haka me na kashe masa ?"."yasan adadin mutane dake bukatar aurena aka daukeni aka bashi ba dan ya cancata ba ?" wallahi gara na mutu tun kafin zuwan auren nan dan nima zanfi bukatar mutuwa ina jin kamar na kashe kaina da kaina kowa ya huta har ma dashi mai tsanartawa dasu masu bukatar ganin rayuwata ta tagayyara dan nasan aurena da
yaya Adam babu abinda zan tsinta acikinsa sai bakinciki ?ta qarasa mgnr tana sheshekar kuka ."

"maryam !
nana hauwa'u ta kira sunanta "me yasa kike fadar haka ai bashi zaki duba ba "sister wa zan duba ?zan rayu tare dashi ?karki manta tare zamuyi rayuwa dashi kuma acikin gida daya idan ma ta kama a daki d'aya idan damuwa yake kunsa min ni kadai zan shanye ,haka zalika idan farinciki ne ni kadai zan ji duk wani abu da zan tsinta acikin gidansa akaina zai qare kina tunanin zanyi farinciki a gidan mutumin da baya sona ?"bana jin akwai halittar da yaya adam ya tsana kamar ni, a wasu lokutan na Kan zauna nayi tunanin me yasa yake tsanata haka ?ta sauke numfashi mai hade da sheshekan kuka ya Adam yayi mugu mugun tsanata sister ."

"Na fada yanzu ma zan sake fad'a aurena dashi babu abinda zai haifar sai damuwa domin kuwa bazai yi yadda kowani magidanci yake a gidansa ba ,bazai dauki duk wani responsibility dina ba,zai watsawa mami qasa a idanunta domin zuciyarsa bata tattare da tsoron kowa ko shakkun kowa na sha jin yadda yake fadawa ya hisham da yaya bello cewar baya sona ,nima idan banki auren ba sister me kike son nayi ?ni da akwai yadda zanyi na tsaida maganar auren nan wallahi da nayi domin nafi bukata hakan ko kuma mutuwata dan wallahi zan so faruwar haka da dai na kasance a gidansa abar wulaqantawa ."

nana hauwa'u ta riko hannuwanta duka cikin tsananin damuwa tana cewa "tabbas akwai ciwo sister ciwo kuma mai zafi acikin zuciyarki nasan yaya Adam bai sonki sister amman bazan daina baki shawara akansa ba domin ina ji ajikina zai canza zaki canzasa sister ."maryam ta girgiza mata kanta alamun "a'a ! bazan iya ba sister bazan iya canzasa ba ,yaya adam yafi karfina yafi karfin hada rayuwa dani babu wanda yasan abinda Ke ransa gabadaya acikin halayensa bai gama fitowa dashi fili ba saboda babu wanda Ke rayuwar akarkashinsa ,sister zuciyata zata buga matsawar aurena ya tabbata dashi nasan nan gaba kadan zan mutu dan bazan cigaba da rayuwa mai dadi ba ".

"kiyi addua sister dayawa anyi irin aurenku karshe kuma yayi kyau kuma anyi farinciki ki hasasowa kanki haka ki daina tunanin bad things a tsakaninku ."at every step sister ta ina kike hango min jin dadi ki duba irin abubuwan da yake ta yaya kike son nayi scricfied din rayuwata akanshi ?"nasani sister amman ki bari ayi ki gani daga ranar ki fara Kirgawa day by day wata rana soyayya zata kasance a tsakaninku wallahi inada wannan tabbacin kirki zubawa mami kasa acikin idanunta domin kuwa ta yarda dake ta fad'a ta sake jadaddawa cewar zaki mata biyayya bazaki zuba mata kasa a ido ba dan allah karki karyar da yardar data tayi miki ."

"mami tayi alkwarin muddin tana raye sai anyi auren nan kuma sai kin samu farinciki a gidan yaya kuma ma shi ya Adam ya amince zai aureki har yau din nan bai ce ya fasa aurenki ba "bisa umarnin mami ba ?cewar maryam tana duban nana hauwa'u hawaye na turereniyar zubowa bisa kuncinta "ina ..!ina jin bazan .."sai kuma tayi shiru ta kasa cigaba da maganar gabanta na wani irin faduwa da karfin gaske." dan allah ki bar maganar nan haka sannan ki bar kuka nan tashi muje d'aki ki kwanta ki huta jiki a matukar sanyaye da taimakon nana hauwa'u ta mike tsaye tana jin wani irin sanyin a gabobinta tana jin kafafuwanta sun gaza daukarta nana hauwa'u ta rikota sosai ta makaleta a gefen jikinta suka nufi daki ."

ATA ya sauko tsaf cikin wata dakakkiyar gezner tamkar ranar zaa daura masa aure dinki ya balain yi masa kyau takalmin kafafunsa cover shoes ne yayi matukar dacewa da shigarsa kanshi babu hula sai agogon fata dake daure da tsintsiyar hannunsa
ahankali yake taka step yana saukowa yana duba agogon hannunsa har zai fita sai kuma ya dawo baya ya dauki hanyar dakin mami, ya tura kofar dakin a natse ya shiga ya isketa zaune hannunta rike da waya wanda ya nuna masa alamun waya ta gama tana ganinsa ta sake hade fuska tamkar bata ta'ba dariya ba dan kalamansa sun ta'bata sannan sunyi mata ciwo matuka a tunaninta ko mai aikinta bata cancanci adam yyiwa mummunar fata haka ba bare diyar danuwanta wanda su kadai iyayensu suka haifa suka bari a duniya."

cikin kankanin alokacin yaga sweetheart dinsa ta canza ganin irin kallon da yake mata yasa ta kawar da fuskarta aranshi yace "har abun ya kai haka ?."shiru yayi kawai yana dubanta a tsanake shi a ganinsa babu wani laifi acikin maganarsa dan so ba karya bane haka zalika rashin so ba karya bane , hakuri yake son ya bata amman daya tuna akan maryam ne sai yaji ya fasa ,yayinda ita mami hakurin tayi tsammanin ya shigo ya bata dan shi take bukata daga garesa amman sai taji sautin muryarsa can kasan makoshi kamar koda yaushe yana cewa "sweetheart ni zan fita amman bazan wani jima ba" bata juyo ta kallesa ba bare tace masa wani abu jiki a sanyaye ya fice daga gidan gbdy can qasan zuciyarsa cike da bakinciki da fargaban shirun sweetheart dinsa dan a duk sanda tayi shiru haka matsaloli ne zasu biyo baya ."

Daga shi sai direbansa acikin mota kira ne ya shigo wayarsa yana duba screen din wayar sunan aunty shahida ya gani bai dauka ba dan yasan kararsa mami ta kai wajenta yana kallo har kiran ya katse wani kiran ya sake shigowa sai datayi masa kira biyar bai dauka ba haka aunty khadija kiranta biyar har suka isa station kiransa suke yi amman yaki dauka ya fito daga cikin mota kai tsaye office din dpo ya nufa ya tareshi cikin farinciki ya mika masa hannu suka gaisa yana nuna masa wajen zama da hannunsa a hankali suka fara tautaunawa akan hindu."

"ranka shi dade yarinyar nan bata da mutunci ga rashin kunya ga bakinta baya mutuwa an kawo mata abinci ma ta kwafar tana zagin wanda ya kawo mata tun daaka kawota bakinta bai yi shiru ba sai tsinewa mutane take "dubansa ATA yayi yana cewa "baku ladabtar daita bane shiyasa "ai yalla'bai na dauka kamar wancar yarinyar ce da kace kar ataba lafiyar jikinta shiyasa nayi masu gargadi amman dai tasha mari a wajen inspector romoke numfashi ya sauke
"abinda ya kawoni yanzu ina son a tsanata bincike akanta fiyye da wanda akayi akan nuzla idan ta kama da duka duk ayi mata domin ta amsa laifinta ."

"bare ma wannnan yarinyar cikin sauki zata amsa laifinta dan ta tabbatarwa da jami'an da suka kamota muddin ta fito sai tayi ajalin yarinyar dakasa a bibiyeta ga dukkanin alamun itace mashekiyar da muka dade muna nema ATA ya gyada kai kawai yana saurarensa."dpo ya cigaba da magana "ko akawo maka ita ne ?ya fadi haka ne ko zai bukaci ganinta kamar yadda ya bukaci ganin nuzla."

ya girgiza masa kai kawai alamun baya bukata "abinda nake so bana son maganr kamata ta fita zuwa koina har ku gama bincikenku akanta sannnan bana son kowa yasan inda take har sai ta fad'a maku itace ta kashe mubina cikin girmamawa ya amsa masa da to "matsawar ta amsa itace ta kashe mubina ina son tasan girman laifin data aikata ku kaita kotu batare da sanin kowa ba alqali ya yanke mata hukunci daidai da laifinta a turata kurku wannan shine kawai abinda nake bukata "in sha allahu yalla'bai zaayi duk yadda kake so "tare da dpo suka fito yana sake jadaddawa dpo baya son tana tsare ya fito da kudi masu yawa kamar wancan ranar ya damkawa dpo sannan ya wuce ya tafi ."

Ahankali yake takawa har ya isa cikin dakin mami ya sameta zaune a saman abun sallah tana jan carbi kana kallon idanunta kasan kuka tayi kuma ba kadan ba ya qarasa ya zauna a gabanta ya riko hannunta daya cikin nashi yana kiran sunanta "sweetheart!"da kyar ta dago kunburarrun idanunta ta tsura masa sannan ta zare hannunta cikin nashi tana cigaba da jan casbaha jikinsa ya sake yin sanyi bai ta'ba ganin wannnan yanayin atattare daita ba sai yau duk abinda zai mata bata taba daukar zafi dashi irin haka hasalima a inda abun ya faru anan take barinsa ."

Ahankali ta mike tsaye ta koma bakin gado ta zauna shiru yayi kawai yana kallon yatsun kafafunta kafin daga bisani ya yunkura ya mike tsaye ya isa inda remut din ac yake ya dauka ya kunna saboda zafin da yake ji ya zauna kusa daita ta sake mikewa ta fito daga dakin ta barshi zaune yabi bayanta da kallo sannan ya biyo bayanta ,koda ya fito parlour'n bai ganta ba sai sautin muryarta yajiyo sama sama daga dakinsu nana hauwa'u dan haka ya haye samansa."

Tun bayan  fitar hindu hajiya aljannatu Ke kwance tana bacci ,acikin baccinta ne tayi mafarkin wai ga wasu mutane sun zagaye hindu wanda batasan ko su waye ba ,macen dake cikinsu taje ta samu tana tambayarta lafiya suka zagaye ta amman tayi mata shiru tana kallonsu zasu wuce daita tace  "ina zaku wuce min da yarinya ?da wannan kalmar ta farka daga mafarkinta tare da kallon sugura dake zaune akan dadduma da alamun ta idar da sallah né tace "sugura ina hindatu ?"ai tunda ta fita bata dawo gidan nan ba "ta fad'a mata haka sannan ta cigaba da laziminta bandaki umma ta shiga tayi alwala ta fito tayi sallah tana idarwa tace "wallahi duk jikina ciwo yake "sannu Atu " dake haka suke kirata ."

"yauwa sugura dauko min wayata na kira naji inda take "sugura ta mike ta dauko mata wayar ta mika mata ta fita atu ta soma neman  layin hindu sai dai abu daya aka fad'a mata a karon farko "switch off ta sake maimaita kiran the same thing tayi shiru rike da wayar tana jin wani iri ajikinta da tunanin inda taje  dan  ita ba mai yawon leke leke bace acikin estate din bare tace a dubota koda yaushe tana gida idan kaga ta fita zata siyan abu ne ko kuma da shiga gidan hjy zulaihat ."wasa wasa har dare babu hindu ba alamunta nan fa hankalin mahaifiyarta dana yayyunta ya tashi nan da nan baba qarami ya fita nemanta tare da sauran yan'uwanta amman duk inda suka je basu ganta ba ,dan haka suka qarasa police station mafi  kusa dasu sukayi report sannan suka dawo gida cikin matsanancin tashin hankali."

Har washgari baa ga hindu ba  koda hjy zulai ta samu labarin abinda ya faru batayi sanya a gwiwa ba ta d'auki kafafunta taje gidan baba babba  tayi masa  bayani  komai ,shine ya kira baba qaramin  koda ya  shigo ko kallon inda mami take bai yi ba sai bayan da baba babba ya   sheida masa  aiko cikin tashin hankali da  zafin rai yake tmbyrta police station din daaka wuce daita "ina zan sani tunda daga sama allah ya kawowa maryam dauki "bangane hausar baki sani ba "iyakar abinda nasani kenan na fada sai ka bazama zuwa duk wani  police station dake kusa da nesa domin nemanta idan kuma angata lokacin ni kuma zan shigar da qarar abinda ta aikata ."

wani mugun kallo ya watsa mata yana cewa "ki kalleni da kyau  zulai kinga nayi miki kama da irin wadan nan mutane ?kisani ni ba wannan shashan bane da danki ya garkame masa 'ya kwana da kwanaki bai dauki mataki akai ba dan haka wulakancinki da isarki  ta tsaya akansa ke kuma ki tsaya a iyakarki.." idan ba haka ba me zai kayi ?bai yi magana ba illa nunata da babban dan yatsansa da yayi alamun gargadi sannan ya juya kamar zai tashi sama naunayen ajiyar zuciya baba babba ya sauke yana cewa  "kiyi hakuri  kin rigada kinsan halinsa "nasani amman a haka yake son na bawa d'ana umarnin ya auri hindu ?ai wallahi dana bari adamcy Ya auri hindatu gara nuzla bancin hisham dake tsakani nan suka cigaba da tautaunawa akan matsalar ."

ATA ya sauko a natse cikin shigar suit a hankali yake takowa yana kallo koina a parlour'n har ya qarasa saukowa , babu kowa parlour'n har sweetheart dinsa bata nan ,wanda adaidai lokacin daya sauko daita yake fara cin karo agabanta zai ci abinci har sai ya bar gidan take tashi ta shiga ciki wani lokacin kuma ta cigaba da zama amman yau babu ita babu alamunta ."

kallon dining yayi da alamun an gama shirya masa breakfast numfashi ya sauke ya nufi hanyar dakinta ya shiga bai ganta ad'akin ba ,dan haka ya samu waje ya zauan a bakin gado yana jijiga kafarsa a tunaninsa ko tana ciki bayi kusan minti goma yana zaune amman shiru ,ya mike tsaye ya fito yana neman layinta kiran na shiga amman bata dauka ba, layin nana hauwa'u ya kira tana dauka yace "ina sweetheart ? okay ya fad'a takaice yasa kai ya wuce zuwa office bai tsaya bin takan abinci ba ."

Bangaren baba qarami da yayansa duk wani office din police na kusa dasu sunje amman babu labarin hindu duk inda suka je sai ace ba nan aka kawota ba dan haka suka bazama zuwa headquarters sukai report ,da yamma koda ATA ya dawo bai iske mami ba sai dai tasa an a shirya masa dining amman bata tsaya ba tunin ya gano manufar mami akanshi tashin hankali kenan wanda baa saka masa rana idan kowa zai iya barin rayuwarsa ya hakura amman banda sweetheart dinsa bazai iya ba zai iya komai akanta zai iya sadaukar da farincikinsa gareta ."

wanka ya shiga byn ya fito ya sauya kaya zuwa na shan iska ya sauko ya shiga dakin mami tana zaune tare da maryam tana shirya mata kaya a kwaba tana ganinsa ta dauke idanunta zuwa kan maryam "Yauwa maryam kwashe wannan kayan ki maida su sama, jiki a sanyaye ta dauki kayan ta ajiye kamar yadda mami ta buqata sannan ta maida murfin kwaban ta rufe ta raba ta gefensa ta fice daga dakin ."

Ya sauke numfashi "ammm sweetheart "kada kace min komai please dan banason jin komai daga bakinka yadda na zuba maka ido kaima ka zuba min ido kowa yayi tsabgar gabansa kayi abinda kaga ya fiyye maka arayuwarka mami ta fad'a tana nuna masa kofa .."sweetheart "dan allah adamcy ka bar min daki tunda ba kai ka gina min shi ba fita kafin nayi maka abinda bazai mana kyau ba "sweetheart ." ya fad'a a karo na biyu zuciyarsa cike da matsanan cin tashin hankali "ka fita adamcy ka fita bana son ganinka fita ta fad'a tana kawar da fuskarta ."

"Da gaske dai sweetheart dinsa bata son ganinsa me yayi da zafi haka ?a ganinsa shi bai yi laifin komai ba juyawa yayi ya fita yana waiwayenta yana jin kuna acikin rashi tun daga lokacin mami ta fita harkarsa shi kuwa abun ya damesa idan ya sauko yaga bata nan baya tsayawa karya wa zai wuce office washegari ya kasance weekend yana saukowa kai tsaye dakin mami ya shiga ya sameta zaune ya gaisheta cike da ladabi ta amsa tana qoqarin mikewa saboda har lokacin tana jin zafi da radadin abinda yayi mata har tayi taku biyu taji ya riko hannunta "dan girman allah sweetheart kiyi hakuri da abinda nayi ya fad'a cikin rawar murya."

wani sanyi dadi taji ya lullubeta daman abinda take bukata kenan daga garesa sai dai taki kallonsa ahankali ya dawo gabanta ya tsugunna bisa gwiwowinsa "ina mai neman afuwarki sweetheart ki yafe min nima ba yin kaina bane ki fahimceni wallahi bana jin son yarinyar nan araina ."
"amman sai kayi mata mummunar fata ?ta fad'a abun na ta'ba ranta ayi ganganci da rayuwar yarinya tankar mai fa adamcy wallahi a tunanina ko dabba na ajiye a gidan nan akayi mata haka bazaka fad'a haka ba bare mutun wacce kasan tana da mahimanci arayuwata" ta qarasa maganar adaidai lokacin da aunty shahida da aunty khadija suka turo kofar dakin suka shigo shiru kawai tayi tana dubansu ."

A natse suka qarasa shigowa cikin dakin sosai suka samu waje suka zauna mami ma ta zauna tana dubansu daya bayan daya "mami kin tashi Lfy?lafiya lau ya kwanan yaran ?"duk suna lafiya suka amsa mami ta dubi babbar diyarta tana cewa "a yau nake sa ran jama'a zasu fara sauka domin zuwa bikin adamcy da maryam amman sakamakon abinda yayi na janye maganar aurensa da maryam ya d'ago kanshi da sauri ya zuba ma mami idanunshi ."

"Ku sheida na yafe masa duniya da lahira yaje ya kawo min wacce yake son ya aura ita kuma mrym in sha allahu zan samo mata wanda zai min biyayya ya aureta" wani sanyi dadi ya lullubesa na farinciki jin maganarta ta farko amman kuma a karshe yaji wani irin tarin damuwa na shiga zuciyarsa matsowa yayi daf daita yana cewa "sweetheart ai na baki hakuri dan allah kiyi hakuri "na hakura adamcy amman da wani abu yaje ya sameta a sanadiyyarka kazo kana murna da jin dadi gara a fasa ."

Shiru yayi ya kasa cigaba da magana "mami dan darajan allah kiyi hakuri tunda yayi nadama har ya baki hakuri sannan babu abinda zai samu maryam zata cigaba da rayuwa kamar kowacce yar adam Kiyi hakuri ki yafe masa kin rigada Kinsan halin adam bai iya magana ba duk maganar data fito bakinsa haka yake cabawa inji cewar aunty khadija wani mugun kallo ya wurga ma mai hade da harara ."

"Me yasa bazai zama mutun na farko da zai ji ciwon abinda akayi mata ba? maryam fa matar da zai aura ce, matar da zai raba duk wani farinciki da akasin haka ce daita ,kuma yaruwa mafi kusanci da rayuwarsa amman ya dinga nunawa duniya baya sonta , wallahi ina matukar qaunar zamansu tare amamn tunda abun ya kai ga haka nima na hakura sannan bana fushi dashi na yafe masa duniya da lahira ya kawo wacce yake so ta qarasa mgnr kuka na kwance mata .."cikin muryar kuka aunty shahida da khadija suka durkushe agaban mami suna kuka suna bata hakuri "dan allah mami Kiyi hakuri karki bari a fasa auren nan bayn an gama komai ."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

             Page 27

  Cikin muryar kuka mami tace  "har yau na kasa fahimtar me yasa adamcy baya son maryam ?me maryam ta rasa ? me yasa yake jin idan ta mutu zai ji dadi zai  huta?" ta qarasa mgnr tana goge hawayenta "Kiyi hakuri mami  zai sota in sha allahu nan suka dinga  rarrashin mami shi kuwa ATA ya qasa cewa komai sai ma ya mike   cikin yanayi na tashin hankalin ganin mahaifiyarsa na zubar da hawaye akanshi  ya bar  d'akin  zuwa nashi yana furzar da  numfashi  mai zafi ."

ko bayan fitarsa hakuri sosai  aunty shahida da aunty khadija sukai  ta bawa mami da kyar suka samu ta sauko ta hakura "kiyi hakuri mami ki yafe masa sannan ki kwantar da hankalinki muddin muna raye adam bashi da wata mata sai maryam kuma bazamu ta'ba barin tasha wahala a gidansa ba sai inda karfinmu ya qare ."sanyayyen numfashi mami ta sauke tana mai sake gyara zamanta  tare da riko hannuwansu cikin nata "na yafe masa dan ko baku nemar masa  yafiya  ba  zan yafe masa domin iyaye ne kadai suke iya yafewa ya'yansu batare da ya'yan  sun nemi yafiya daga garesu ba  ,gaba dayanku allah yayi maku albarka allah kuma ya albarkaci rayuwar ya'yanku kuje ku cigaba da shirye shiryen  biki ina alfahari daku ta qarasa  mgnr tana murmushi ".

wani farinciki ne ya mamaye zukansu suka mike  suka  fito daga dakin mami  zuwa  d'akin ATA
alokacin yana kwance flat akan  kujera  yana fidda numfashi sama sama ."Jin motsin shigowarsu ya sashi bude idanunshi da kyar sai dai  bai mike  ba har sanda suka samu waje suka zauna  suka tsura masa idanuwansu suna kallonsa, kusan mintuna goma suka d'auka suna kallonsa da nazarinsa sannan   aunty shahida ta kira sunansa "adam !"
yana jinta amman yaki  amsawa  sai ma sauke ajiyar zuciya yayi tare da furzar da zazzafar iska daga bakinsa "

"kana jina fa  adam ?"eh ina jinki ki fad'a abinda zaki fad'a  ya fad'a a takaice tare da mikewa ya zauna  yana kallon wani bangaren dabam  yana ciza gefen lip's dinsa  yayinda idanuwanshi suka canza kala dan bai ta'ba shiga tashin hankali  irin na yau ba ganin mahaifiyarsa na zubar da hawaye ,"shi kuwa me zaiyi da maryam arayuwarsa ?ai har abada bazai ta'ba sota ba zai dai yi biyayya wa mahaifiyarsa  ."

Aunty shahida ta danne abinda taji na haushin abinda yayi mata yanzu ta  soma magana cikin fushi "wallahi adam kabi duniya ahankali da girmanka da komai amamn ka dinga  sa mahaifiyarka kuka a zatonka yadda kake yiwa mami zaka ci bulus ne ?cikin yanayi na tashin hankali ya waigo ya tsura mata tsumammun idanunshi dake cike da matsanamcin tashin hankali duk da magana yake son yi amman ya kasa bude bakinsa dan haka ya runtse idanuwanshi kawai  yana janyo wani irin numfashi mai zafi yana fesarwa ya maida kanshi jikin kujera ya kwantar ."

"tsawon shekaru fa take binka akan aure ,ka mance kaine kaki fito da mata har yasa ta yanke wannan hukuncin akanta  ?"iyaye ne kadai suke son  ganin cigaban ya'yansu mami na son ganin gobenka tayi kyau ne yasa  ta hadaka da mrym sannan  karka manta kai ma aure zakayi  yanzu kuma zaka haihu yaya zakaji duk ranar da kacewa d'anka  ko 'yarka ga abinda kake so suka  ce aa ba zasu maka  biyayya ba abinda suke  só shi zasuyi   ?

"to ni yanzu me nayi kuma ?ya fad'a a matukar hassale tare da gyara zamansa ya  bude idanuwanshi a hankali ya zuba masu ya cigaba da motsa labbansa "yarinyar nan ce  bana só kuma bana jin zan sota ,sai kuma na kasa fad'ar albarkacin bakina ko ana so dole ne  ? yayi  tambayar  a dan fusace yana kallonsu ,ku tsaya na tmbyeku daga Ke har khadija auren dole mahaifinmu yayi maku ?"sukayi shiru suna kallonsa dan basu da amsar da zasu bashi "gbdynku kuna son mazajenku kuka  auresu  to me yasa sai ni dana kasance nmj  zaa wa auren dole kuma a hanani mgn ?".

"amman ai ba dole sai ka fad'a a gaban mami ba ,wannan kalmar da kake fad'a ita Ke sa mami jin wani abu aranta , dannewa ya kamata kayi ka rungume maryam ."har yanzu baku bani amsar tmbyta ba tukun kafin ku shigo da wata ,auren dole akayi maku ?"zuba masa idanu sukayi kowannensu da abinda yake sakawa aransa ,ahankali ya lumshe tsumammun  idanunshi tare da sanya hannunsa daya a saitin qirjinsa yana murza daidai inda zuciyarsa take beating very fast "gbdynku bazaku iya fahimtar quna da radadin da nake ji acikin zuciyata ba  ,so ne dai na fad'a bana sonta kuma wallahi ko yanzu aka fasa auren nan murna zanyi  mutun daya ce kawai ta samu kyakkyawan mazauni anan  itace mafarkina ,me zaayi da wannan guntuwar yarinya yarinyar Kmr agwagwa  kawai fari ne ya taimaketa ya qarasa mgnr yana cigaba da shafa zuciyarsa yana lumshe ido ."

"Wani haushinsa ya kama aunty khadija  ranta a matukar bace tace "Idan zaka  manta mafarkinka ka manta ka sanya mrym  a zuciyarka dan wannan auren mutuwa ce kawai zata ra.."Kafin ta qarashe  maganar ya jefa mata wani mugun kallo wanda yasa tayi gaugauwar yanke maganarta babu shiri ,dan girman allah adam kayi qoqari kasanya maryam ko kad'an a zuciyarka "bazan iya ba"ya fad'a atakaice "zaka iya adam kayi qoqarin kwatantawa please."
  "bama da ikon waye zamu so waye zamu fad'a soyayya dashi   bazan iya yi maku karya cewar zan sanyata a zuciyata ba   daga baya kuga akasin haka dan bazan iya karya maku zuciya daga baya kuji haushina ba ,kuyi hakuri  kawai  bazan iya ba ,sannan kusan wani abu  a kullum ina fad'a  maku amman kun kasa fahimtata kuskure zaayi a auren  nan yakamata abar maganar auren nan haka mu cigaba da rayuwarmu daita  irin ta yan'uwantaka."

"zamuyi rayuwa daita ta har abada shine maanar aure,  akwai abubuwa acikin rayuwar aure,aure   ba abu bane na takaitaccen lokaci idan anyisa anyisa kenan sai fatan mutuwa ce zata raba zata bukaci farinciki ni  km bazan ta'ba bata farinciki ba saboda ni kaina zuciyata bata tare da farinciki komai zuciyata a rufe take da soyayyar wata wato mafarkina kenan ,itama ina neman adduarku allah ya yaye min tunaninta na huta yayi maganr Kmr zai zubda hawaye . yayi shiru tare da rungume hannuwansa duka a qirjinsa yana jin wani irin tuttukin bakinciki."

"to Allah  yaye maka tunaninta kai bama tunaninta ba ni zanyi addua allah ya mantar da kai ita gbdy  kaji ka tsaneta  fiyye da komai a duniya inji cewar aunty khadija ,numfashi kawai ya sauke yana kallonta a dage batare da yace komai ba dan shi yasan ba abune mai sauki ba ya mantata.yanzu ga shirye shiryen biki  zaa shiga daga jibi ya kenan ?"
"babu ruwana da duk wani abinda zaayi na shirin biki ,ni dai abinda nasani aure ne na amince zan aureta amman batun wani shirye shirye babu ruwana" har maganar rabon iv ?"ya ina fad'a maku bani da wata damuwa da komai  da zaa gudanar kuna qara shigo min  da wani maganar rabon Iv ."yayi mgnr da fushin zuciya .

"rabu dashi aunty  shahida duk abinda ya dace salim da hisham  sunyi  ,kai kuma kaje can  ka karata da mugun halinka allah ya ganar da kai mu zamuyi komai kuma aure babu fashi sai an cikawa mami burinta  sai dai idan mutuwa zakayi ka mutu nonsense kawai  "bai sake cewa komai ba har suka mike suka bar d'akin ya koma ya kwanta lamo yana kallon saman d'akin ,ranar yini yayi kwance a d'aki cikin tsananin damuwa ."

da misalin karfe takwas na dare ya sauko kamr yadda aka saba an shirya masa dining da kalolin abinci dabam dabam ya zauan akan kujera shiru babu mami haka nan ya kasa ci ya kai hannu ya shafa kanshi zuwa fuskarsa duk tsananin yunwar da yake ji ya kasa sakawa cikinsa komai ya cigaba da zama shiru sai kusan karfe tara mami ta fito daga dakinta sanye ciki riga da zani na atamfa super tana kwallawa auta da maryam kira atare suka fito daga dakinsu suna amsawa mami ta dan yi taku zuwa dining area taja kujera ta  zauna tana cewa "maryam zuba mana abinci jikinta a sanyaye ta bude kular farko tana tmbayarta "mami me zan zuba miki  ?"

" bani rice  ma ya isa amman kadan zaki zuba min ta zuba mata ta ajiye agabanta sannna ta zuba abinda tasan ATA yake so rice and stew da miyar kayan ciki da cowslow ,ta zuba shinkafar a plet dabam haka ma miyar daban tayi  masa  ta ajiye a gabansa sannan ta zuba nasu ita da nana hauwa'u ta dauka ta wuce."
Ahankali mami take cin abinci amman ATA ko kallon abincin gabansa bai yi ba saboda haushin mami  taki kallonsa ballatana yaga faraarta taki furta komai garesa idan zasu hada ido sai ta dauke kanta sosai ya shiga damuwa hankalinsa ya tashi "to me yayi mata da zafi haka ?shi kam bazai ta'ba boye felling dinsa akan maryam ba yadda zuciyarsa bata sonta haka bakinsa bazai qasa furtawa ba sai dai tayi hakuri dashi ."

Ganin yaki ci yasa mami taji babu dadi aranta ta dauki spoon ta sanya cikin abincinsa ta sake tura masa tana tsaresa da idanunta jiki a sanyaye ya sauke numfashi zuciyrasa na sake  karyewa allah sarki sweetheart yasan bazata iya dogon fushi dashi ba ,haka ya dinga cusawa cikinsa abinci tana tsiyaya masa ruwan lemu sai data ga ya koshi sannnan ta mike ta soma tafiya ya dago kanshi yana kallon bayanta zuciyarsa cike da tausayinta ya sani  cewar tana matukar son maryama ,da wani ne yayi abinda yayi mata koda kuwa acikin ya'yanta ne sai ya hadu da fushinta fiyye da yadda ta dauka dashi amman shi allah ya saka mata hakuri dashi komai zai mata tana shanyewa har ma ta kasa daukar dogon fushi dashi." tashi yayi ya haye saman d'akinsa babu laifi   zuciyarsa ta d'an samu  natsuwa."

Da misalin karfe hudu na ranar baki  suka fara sauka a gidan mami murna a wajen mami ba'a  magana  ranar a kasalance maryam  tayi komai daga karshe ta shige daki ta kwanta ta huta dan ta samu zuciyarta da gangar jikinta su samu natsuwa da suka rasa
tun da taga jama'ar sun fara sauka hankalinta ya tashi jikinta yayi sanyi ."washegari aka fara shirye shirye biki , zaune suke  a falon aunty shahida masu gyara  jiki nata faman shafa masu dilka ajiki  yayinda yanuwa suka zagayesu ana hira daga maryam har nuzla kana kallonsu zaka fahimci suna cikin damuwa da rashin son auren dan fuskarsu kamar zasuyi kuka gidan mami ya sake cika da yan'uwanta  har yau friday da zaayi kamu mutane suna cikin zuwa ."

a wani hadadden hall akayi  kamu amare sunyi kyau sosai sai dai ango ATA  bai je koina ba yana kwance a gida ,bangaren maryam ita kadai ce zaune akan kujerar daaka tanada dominsu dan juyin duniya  aunty khadija tayi dashi  amman yaki zuwa aranshi yace "ko bikin da yake so ne zaayi bazai je wani kamu ba bare wanda zaa masa na dole ."mrym kuwa juya  kai kawai take   zuciyarta a jagule bare idan ta kalli hisham da nuzla yadda hisham Ke jefa mata kallon soyayya  da kaffa kaffa daita sai taji kamar ta daura hannuwanta duka  aka ta saka ihu  ko taji saukin zafin da zuciyarta take mata ta sake kallon  hisham taga ya  makale  nuzla sai d'aukarsu hoto ake amman ita nata ango ya wulakantata."

aunty shahida tayi  mata duban tsanake nan da nan ta fahimci halin da take ciki ta qaraso inda take zaune tana cewa   "Ki kwantar da hankalinki mrym da rashin zuwan adam kema Kinsan halinsa gara rashin zuwansa daya zo ya kunyata mu ta hanyar wulakanta mu amman muddin muna raye bazakiyi bakinciki a gidansa ba."maryam  tayi narai narai da idanu zatai kuka "qul karki  daga hankalinki bare Kiyi asarar hawayenki da zarar an daura shikenna ya zama naki na har abada  a hankali ta dinga rarrashinta har ta dan samu natsuwar zuciya sai dai taji haushi da bakinciki rashin zuwansa domin  dai so yake lallai sai duniya tasan irin auren da zasuyi ."

bayan an gama kamu amarya maryam ita kadai a bayan mota direba yajata suka dauki hanyar zuwa gida  yayinda hisham da nuzla suke zaune abayan tasu motar direbansu na qoqarin kunna mota hisham ya kafeta da ido sosai Kmr zai cinyeta kafin ya sauke ajiyar zuciya ya kamo hannunta  cikin nashi yana  kallo yace "Woow my nuzla gsky lallen yayi kyau my wife waya miki shi ?

hade rai tayi sosai  tamkar bata ta'ba yin dariya ba a tsawon rayuwarta tana zame hannunta cikin nashi tace "ka tsaya iya matsayinka karka sake ta'ba min jiki dan wannan jikin ba naka bane "na waye "? ya tambayeta yana matsota sosai Kmr zai shige jikinta "tambayarki nake "jikin waye ?"stil dai shiru tayi  masa " jibi iwar haka kina cikin gidana watakilla ma muna kwance acikin bargo daya makale da juna "wani kuka ta fashe da shi tana qara matsawa ".

" to to!!  shikenan na bari  Kiyi hakuri amman dai Kinsan dole zamu kasance tare? tsaki taja ta kawar da fuskarta gefe a haka suka qaraso   gida ."mota bata tsaya a koina sai a kofar gidansu bayan motar ta tsaya   ta fito hisham ya biyota suka jira yana yi mata magana amman taki kulashi tana  qoqarin shiga  gida ya riko hannunta daya cikin nashi ta juyo a matukar fusace tana kallonsa shima kallonta yake with a broad smile a fuskarsa sai itace ta  dauke kanta tana lissafi yadda zata gudu ta bar shi da wahalarsa  ".

"anya kuwa zata iya gudu ta bar iyayenta  bayan a yanzu bata iya zuwa koina ta kwana batare dasu ba ?ta tambayi kanta nan take zuciyarta ta bata amsa da" wannan shine mafuta a gareki  idan komai ya natsa sai ki dawo wanda zuwa lokacin dole kowa ya hakura ." ta sake kallonsa taga har lokacin ita yake kallo yana murmushi wanda bata san ko na meye ba ."cike da jin haushi ta  fix hannuta tana mai bakinciki dan  komai ya faru da rayuwarta shine sila shekara da shekaru bata ta'ba tunanin barin iyayenta ba sai a dalilinsa ita kam tsakaninta dashi sai dai allah ya isa  da wannan bakinciki ta shige gida  ta barshi tsaye  yana kallon bayanta ".

Sai bayan data shiga  gida sannan ya juya ya wuce  kai tsaye wajen ATA ya wuce koda ya shiga parlour'nsa yana tsaye akan dadduma yana sallar magrib bai zauna ba shima bathroom ya shiga ya dauro alwala ya fito ya bisa sallah ,bayan sun idar ya fara tsokanar ATA "ango ango !!amman gsky kai dai anyi dan iskan ango ,wallahi baka kyautawa maryam ba, ka barta ita kadai allah sarki wallahi na tausaya mata, wallahi abokina kabi a hankali ina guje maka ranar da zaka rufta "wani dogon tsaki yaja yana  watsa masa harara tare da cewa "ka maida hankalinka jikinka da wannan shirmen da kake yi  karka sake min maganar auren nan" hisham  yayi murmushi  yana cewa "ai hankalina yana jikina nan dai yayita jan ATA."

Nuzla tsaye a dakinta hawaye na zubo daga kwarnin idanunta alokacin da take daukar abubuwan amfanita masu mahimanci tana tuna rayuwar kuncin da iyayenta zasuyi idan suka laluba basu ganta ba ,bayan kamar awa daya nuzla  ta fito zuwa babban parlour'nsu koina  ta kalla mutane a parlour'n yan'uwan mahaifiyarta gbdy  zaune kai tsaye ta shiga dakin hjy salema bata dade ba ta fito ta rasa yadda zaayi ta sake fita dan haka  ta koma ciki d'akinta  tana tunani hanyar da zata bi ta  kubta  daga wannan wahallen auren ."

byn Kmr mintuna goma ta sake fitowa har ta kai bakin kofa aunty maijidda tace "ina zaki kuma adaidai wannan lokacin ? Ta fad'a tana kallon agogon dake manne a falon ,nuzla ta dan diririce sannan tace "yaya hisham ne ya kirani yana waje" tana gama jin abinda ta fad'a  ta juya tayi d'akin da baki suke  ita kuma nuzla  ta samu damar fice wa daga gidan gabadaya ."

yan'uwan hjy salema suna ta kikiniyar da hadahadar abincin  gobe diner sam babu wanda ya fahimci nuzla bata gidan  har karfe goma sha biyu na dare ."Hjy salema dake zaune a bakin gadonta haka   nan jikin ta   ya dinga mata wani iri ,ta fito ta shiga dakin nuzla bata ganta ba dan haka ta juya ta fito daga dakin  tana  tmbayr   aunty rabi wacce ta kasance diya kanwarta  ce "umma  bansa inda take ba amman bari na dubata a dakinta "ai  daga dakin nata nike bangata ba shiyasa ma na tambayeki ." to bari naje na tmbyi aunty maijidda ko tasan inda taje da sauri ta wuce hjy salema."

A bakin kofar fita daga parlour'n suka hadu  da aunty maijidda "Yauwa aunty maijidda ina nuzla ko ta fad'a miki inda zata "eh d'azu tace min zata wajen hisham amman bari na kirata nan  ta soma qoqarin kiran layin nuzla sai dai numberta na shiga bata dauka  dan haka ta kira layin hisham tana tmyrsa nuzla amsar daya bata yasa ta  shigo d'akin hjy salema da mugun sauri  ta isketa tsaye cikin faduwar gaba ."

Aunty maijidda batayi magana ba  ta cigaba da kallon hjy salema "maijidda ko nuzla ta fad'a miki inda zata ?ta bude bakinta kenan zata bata amsa idanunta suka ci karo  da envelop asaman dress mirrow din hjy salema  an rubuta wannan sakon na umma da abba ne kallon da takewa envelop din yasa hankalin hjy salema ya kai kanshi "

gabadayansu gabansu ne ya shiga dokawa dan basusan me Ke kunshe a cikinsa ba  tun baa kai ga budewa ba hjy salema ta soma furta kalmar "innalilahi inna ilahi rajiun  azuci  da fili dan ta gama shiga rudani "hannun aunty maijidda na rawa ta dauka  ta bude  envelop ta soma karantawa  a fili hannunta da jikinta na wani irin wara ."

_Assalamu alaikum iyayena nasan aloakcin da zaku nemi ni ku rasa zaku ji babu dadi acikin ranku amman ina mai baku hakuri da neman afuwarku akan halin damuwar da zaku shiga a dalilina na tafe ne adalilin bana son aurena da yaya hisham  na fito  maku da manufata  amman kun kasa fahimtata dan haka na yanke shawarar barinku ba dan raina yaso ba ina sonki ummanah ina sonki fiyyr da komai haka kai ma abbanah ina sonka zanyi kewarku sosai_

rabi ta nike takadar ta mayar cikin envelop din tana kallo  hjy salema data zube kasa  jinta ne ya dauke dip  sakamakon abinda wasikar Ke dauke dashi  duk wani kuzari da karfin jiki babu atattare da ita baya ga tashin hankali "ji  take kmr ba ita bace anya nuzlarta ce  kuwa ta ajiye mata wannna sakon  ?

Aunty rabbi duk ta rude sai zufa take fitarwa  nan da nan aka kira baba babba da yayyen nuzla maza har ma da hisham da ATA aunty rabi tace baba "kaji wani sabon  tashin hankali  nuzla ta gudu
ta mika wa yaya Ibrahim wasikar  ya duba ,hannu  hjy salema  ya kama dan ta kasa motsin kirki binshi takeyi kmr rakumi da akala har  uwar dakanta ya kamota yana qoqarin zauna daita taki zama tana fashewa da wani gigitaccen kuka tana furta sunan "nuzla! "ku nemo yarinyata dan allah ku nemo yarinyata abinda kawai take iya furtawa kenan "

"Ki kwantar da hankalinki hajiya zaa nemota yanzu ki zauna ki samu natsuwa ta girgiza masa kai tana mikewa ta fito tana kuka tana kiran sunan nuzla dole ya biyota damuwace karara ajikinsu, dukkan su da abinda suke sakawa cikin sanyi muryarshi wanda koda yaushe a haka take cikin sanyi ATA ya dinga kwantar wa da hjy salema hankali da tabbacin zaa ganta  sai lokacin tadan dawo da ga mummunan mafaarkin da take dan gani take tamkar a dream ne ,, ta dan dawo haiyacinta sai dai kalmr INNALILLAHI INNAILAIHI RAJIUN take maimaitawa "

Numbobin yanuwa da abokan arziki aka shiga kira sai dai koina sai ace bata je ba duk suka rude kar ma hisham yaji labari   duk ya rude ya rasa inda zai sa kansa idanunsa suka kada sukayi jajir  gbdy ya nemi natsuwarsa ya rasa ji yake kamar zuciyarsa zata buga."gabadaya yan mazan babu wanda aka bari duk sun bazama nemanta hisham kam  baya fahimtar komai duk maganar da salim yake masa baya shiga kunnuwanshi shiyasa yaji Kmr ya  fita daga cikin motar ya taka da  kafarshi watakilla nashi gudun zai fi na motar duk jikinsa tsuma yake kwakwaluwarsa ta hargitse kamar hauka zai kamashi a haka suka qaraso   babban titin unguwarsu suna gama tsayawa ya fito da sauri yana dube dube amman babu ita babu alamunta ."

Numberta ya dinga kiran taki shiga  har karfe  biyun dare basu ganta ba suka dawo gida cikin damuwa baba babba yace kowa ya tafi kawai makwancinsa sai gobe aga abinda zaayi ."ranar kwanan zaune sukayi duk hankularsu a tashe hjy salema kuka kawai take zainab da aunty maijidda ce masu dan dauriya matar salim kuka take hjy salema duk ta rikice masu sai sunan nuzlata take kira ,hisham kwana yayi yana kiran layinta gbdy ya zare sai salim ne ya dinga kwantar masa da hankali ."

Washegari duk esatate din ya hargitse da labarin guduwa nuzla fad'ar irin tashin hankali da suka shiga bata baki ne  yan biki sun cika gida babu abinda ake sai jajantawa juna ATA ya  bada cigiyarta a duk kafafen  sadarwa, lokacin da  iyayen hisham suka qaraso daga masaukinsu dan su ba zaune suke a qasar ba hankalinsu  ya tashi matukar most especially mahaifinsa sakamakon jin mummunar labarin abinda ya faru dan kallo daya yayiwa hisham ya fahimce sam hankalinsa bai jikinsa ga wata katuwar rama da yayi acikin kwana daya ."
amman ita mahaifiyarsa byn tashin hankali data shiga har 'bacin   rai ta tsinci kanta ciki ranta   ya baci matuka bare da ta samu labarin akan bata son d'anta  ne  ai sai taji soyayyar da takewa nuzla din  ta juye zuwa tsana mai karfi  "

Nana hauwa'u na  zaune acikin dakinsu tare da maryam da diyana har ma da humaira , gabdayansu suna cikin jimamin abinda nuzla ta aikata "humaira tace "bansan me zai sa na gudu na bar iyayenta akan zaa aura min wanda banaso ,kowani iskanci mata sune kan gaba ku duba kuga shi nmj komai zaayi masa bazai ta'ba guduwa ya bar iyayensa ba amman sai kaga mace wai ta gudu wallahi nuzla really disappointed me ."

"maganarki gsky ai ko maryam ta isheta darasi gashi dai bata son yaya adam amman haka ta daure ta karbi kaddararta cikinsu babu wanda bata  fadi albarakcin bakinta ba suna cikin wannan halin aka turo kofar dakin aka shigo hade da sallama gabdayansu suka waigo bayan suka kalli kofar dakin domin ganin wanda ya shigo ,hajiya zulfa'u suka gani sanye cikin doguwar riga na alfarma hannuwanta da wuyanta da yatsun hannunta duk gwal nd tayi kyau matuka sai dai kana kallon fuskarta zaka fahimce bata cikin natsuwa ."

Ta qarasa shigowa sosai yayinda gabadayansu suka maida hankalinsu gareta suka  gaisheta cike da girmamawa ta danyi murmushi wanda kana ganin kasan na karfin hali  sannan ta amsa , ahankali ta samu waje ta zauna agaban nana hauwa tana cewa "ku bani waje zanyi magana da nana hauwa'u gaban nana hauwa'u yayi wani irin faduwa ta hade hannuwanta waje daya tana wasa da yatsun hannunta har zuwa sanda suka fice daga dakin ".

"nana hauwa'u!" ta kira sunanta tare da jawo hannunta ta zaunar daita kusa daita bisa kujerar da take zaune akai "meye matsayina a wajenki ? tmbyr ta dan bawa nana hauwa'u mamaki amman dai ta bude baki ta bata amsa da "mahaifiya !" na gode mahaifiya zata iya yanke kowani irin hukunci akan diyar ta sai dai ni bazan yi haka ba sai dai na neman alfarma a wajenki ,nana hauwa'u tayi shiru kawai tana sauronta."

hjy zulfa'u ta cigaba da magana "ina neman alfarmar   ki auri dana kuma yayanki hisham "
cikin wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da tsoro abinda take shirin aikatawa ta dago da kanta ta tsura mata ido cike da tashin hankali "nasan zaki iya min fiyye da haka ,ki taimkeni kar na kunyata a gobe nazo da tarin jama'a ban san me zance masu ba idan baa daura auren nan a gabe ba ,cikin tsananin tashin hankali da firgici da tsinkewar zuciya da tsoro tare da kyarma nana hauwa'u ta fuskanci kanwar mahaifinta" dan Allah karki bani kunya nana hauwa'u ki amince min zaki samu dukkanin kulawa a gidan hisham cikin zuba mata ido tace "mumy yaya hisham..! karki ji komai kawai amincewarki nake nema "

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
   MAR'ADAMS
   💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

       Page 28

..... Hajiya zulfa'u ta sake riko hannun nana hauwa'u gam cikin nata tana cewa "karki ji komai aranki hisham zai kula dake bazai ta'ba wulaqantaki ba wani yanayi nana hauwa'u ta dinga ji a gbdy ilahirin jikinta, kyarma da jikinta yake ya sake qaruwa ,babu abinda yazo mata alokacin kamar rayuwar maryam da yayanta adam yadda yake nuna rashin qauna garara agaban ko waye ,duk da mami dake tsakaninsu hakan bai sa ya hakura ya rungumeta a matsayin matar da aura ba."

ta daure ta cije amman tunaninta na zuwa kan maryam da yayanta ta fara hawaye saboda tasan me zai iya faruwa daita matsawar ta amincewa wannan auren ita kad'ai tasan yadda take jin zuciyarta a halin da take a lokacin wani irin tsananin tsoro ne ya shigeta ."

Kukanta ya d'aga hankalin hjy zulfa'u, jikinta ya soma kad'awa kamar mazari tana jin tsoron karta ki amincewa da muradinta amman duk da haka ta sanyawa jikinta jarumta tace "dan allah nana hauwa'u karki ce mun a'a rashin amincewarki zai sa naji kunya.wannan buqatar bawa ni kad'ai zakiyi ba har da martabar danginmu zaki yiwa kuka nana hauwa'u ta cigaba da yi har da shesheka tana mai tausayawa kanta ."

" tana son taki amincewa amman kuma bazata iya karya wa mumy zuciya ba tunda tasan ba ita kadai bace budurwa da bata yi aure a family ba ta tsallake kowa ta miki kokon baranta zuwa gareta ahankali ta d'ago idanunta dake cike da ruwan hawaye ta zuba mata "sosai ta tausayawa yanayin da hjy zulfa'u ta shiga dan a shirye take tayi komai akan amincewarta."

"Nasan kina tunanin halin da zaki tsinci kanki né a gidan hisham amman kisa aranki duk abinda zai faru na wani lokaci ne da sannu zaki zama tauraruwar agidansa idan kuma kikaji bazaki iya zama dashi ba ki fad'a min idan yayi miki wani abu na rashin kyautatawa just give me a call aurenku bazai qara ko second daya ba zan raba "ta fad'a tana jin d'acin kalmar aranta dan bazata so aurensu ya rabu zataso su kasance da juna har karshen numfashinsu."

Still dai shiru nana hauwa'u tayi tana zubar da hawaye "ki tausaya min diyata kar naji kunya ." ire iren sambatun da take mata kenan wanda ya haddasawa nana hauwa'u jin tausayinta mai tsanani bugu da qari ita din mutun ce mai mahimanci arayuwarta sannan taji dadin kalamanta tana ganin abun zai zo mata da sauki ta hanyar mumy muryarta a matukar sanyaye tace "mumy mami fa? "ina ..ina ganin ya kamata muji ta bakinta ?ta qarasa mgnr muryarta na rawa cike da in ina tare da sake sunkuyar da kanta ."

Hajiya zulfa'u ta d'aura hannunta daya akan nana hauwa'u tana shafawa tana jin wani irin sonta na shigarta fiyye da soyayyar dataji tana yiwa nuzla, har cikin bargon zuciyarta take jin nana hauwa'u wanda abun ya hade mata ne soyayyar mahaifinta da kuma na d'anta tilo da take dashi wanda a yanzu bata da kamarhi a duniya "nana hauwa'u maminki tasan da komai hasalima gurinta na fara zuwa har ga allah aunty zulai ta amince, tace daman burinta kenan taga kinyi aure kafin allah ya dauki ranta taga yan jikokinta na wajenki kullum adduarta fatan miji na gari take miki ,gashi kin samu domin hisham danuwanki yafi kowa cancata dake nmj né da idan mace ta samesa zataji dadin rayuwa dashi ,domin kuwa miji na gari né allah ya hadaki dashi ta amince dari bisa dari kawai a nemi amincewarki

  Ta dago kanta tana kallonta
murmushi tayi ga kuma hawaye na gangaro mata tace "shikenan mumy tunda mami ta amince nima na amince kuma nayi miki alkwarin zan zauna lafiya dashi zan kawo miki farinciki arayuwarsa zakiyi farinciki da kasancewarmu ."
Nan take hajiya zulfa'u ta rungumeta tsam ajikinta cikin tsananin farinciki tana hamdala a fili "Alhamdulillah diyar albarka na gode nana hauwa'u ,kin tabbatar min da ina da matsayi a wajenki kuma zakiyi farinciki a gidan hisham in sha allahu bazakiyi kuka ba 'allah yayi miki albarka ta riko hannunta Tare da d'agata tsaye ta soma tafiya daita, binta kawai take har lokacin da suka fito zuwa falon gidan wanda a daidai wannan lokacin da karfe shadaya na safiyar ranar ta buga babban falon baba babba ya cika da gabdaya ahalin yaya Alhaji Abdallah."

dayawa daga cikinsu zukantasu na cikin da tsananin tashin hankali bangaren baba qarami wanda har lokacin bai san inda diyarsa hindu take ba ,haka baba babba wanda ya rasa diyarsa a daren jiya bangaren mahaifin hisham shima zuciyarsa cike take da damuwar halin daya baro dansa ciki haka hajiya salema tunda ta zauna hawaye kawai take gogewa wasu na sake zubowa haka zalika uban gayya ATA da zaa yiwa auren dole tun daya zauna idanunshi ke kallon sama tunani kawai kwakwaluwarsa keyi ."

babban parlour'n ya dauki shiru na kusan mintuna goma sha biyar kowannensu da abinda zuciyarsa take saqawa ,baba babba yayi gyaran muraya sannan ya fara magana a tsanake "zan fara da jajantawa kanmu halin da muka tsinci kanmu a ciki wannan lokacin amman nasan allah yana tare damu ,fatanmu allah ya bamu ikon cin jarabawar data fad'a mana nida dan'uwana" .

"ni ai ikon allah da kuma rashin qarar kwana ne kawai yasa har yanzu ban mutu ba akan rashin hindu inji cewar baba qarami jin abinda baba qarami ya fad'a cike da damuwa yasa ATA sauke kanshi ya kallesa kawai yana ta,be baki at the same time zuciyarsa na tsananta bugawa yana jin ina ma shine hisham da nuzla ta gudu ta barshi , ina ma shima wannan guntuwa shegiyar yarinyar ta gudu ya huta tunda itama ba son shi take ba "zaune amman zuciyarsa bata gaji da adduar samun sausauci daga wajen allah ba ".

" in sha allahu allah zai bayyana su gabdaya suka hada baki suka ce "Ameen allah ya kawo mana mafuta sun dade suna tautaunawa akarshe baba babba yace "yanzu ya zamuyi ? "dawa zaa maye gurbin nuzla a wajen hisham domin dai bazaa fasa d'aurin aurensa ba ?ya qarasa maganar adaidai lokacin da hajiya zulfa'u ta shigo falon hannunta rike dana nana hauwa'u tana cewa "karku damu ga wacce zata maye gurbin nuzla a wajen hisham nan domin kuwa na nemi alfarma a wajen diyata nana hauwa kuma ta amince da zata auri hisham tsakanin da allah ."

Da wani irin saurin hjy salema da kanta ke duke ta d'ago tana kallon fuskar nana hauwa'u zuciyarta cike tashin hankali mara misaltuwa yayinda idanuwanta suka sake cikowa da ruwan hawaye, kallo daya nana hauwa'u tayi mata ta fahimci halin damuwar da take ciki ga dukkanin alamun bata ji dadin hukuncin ba ,ahankali tayi kasa da kanta dan bazata juri kallon cikin kwayar idanunta hjy salema ba dan wani irin tausayinta ne ya lullubeta ,itama bata só haka ba
sannan ba yin kanta bane babu yadda zatayi , da ahlinta su kunyata gara ta rungumi qaddarar auren yaya hisham ,kuma ma ai asirinsu zata rufa gabadaya har ita nuzla domin idan basu na gida da suka san ta gudu ba babu wanda zai sani ".

Kafin hjy zulfa'u ta sake magan tuni ATA wanda hankalinsa ya tashi matuka da jin maganarta yace "da gaske nana hauwa'u kin amince ko kuwa kina son yiwa mutane wasa da tunani né "?jikin nana hauwa'u a matukar sanyaye ta jinjina masa kai jikinta na kyarma jin yadda jikinta Ke rawa yasa hjy zulfa'u ta rikota sosai ta had'eta da jikinta saboda tsabar farinciki data haifar mata "amman dai nana hauwa'u kin kyauta Allah kuma yayi miki albarka allah yasa ki gama da duniya lafiya lafiya inji cewar baba babba ."

"Gsky kin kyauta sam ban yi tsamanin zaki mana haka ba hakika kin fitar da alhalinki jin kunyar duniya ,allah yayi miki albarka yasa ki gama duniya lafiya yadda kika rufa mana asiri kema allah ya rufa miki asiri duniya da lahira hajiya jamila mahaifiya ga aunty abida ta fad'a cike da jinjina mata."

gabadaya mutanen dake parlour'n addua suke mata tare da gode mata amman ban hjy salema da mami wacce tayi alkunya ,yayinda ita hjy salema bakinciki né Kmr ya kasheta ,duk da irin qaunarta ga nana hauwa'u sai taji a yau babu ita ta juye zuwa qiyayya mai zafi "me yasa zata amince da wannan auren bayan diyarta ce tafi cancata da auren hisham ?"ko bama haka ba a tunaninta ko auren wasu zaayi dabam ya kamata a d'aga shi sakamakon rashin diyarta da tayi amman hankalin kwance suke bayyana farincikinsu ."

wani sanyin dadi ne ya lullube nana hauwa'u jin dadin yadda ahlinta sukai alfahari daita ."muryarta a matukar sanyaye tace "me yasa zakuyita gode min dan Allah ku daina gode min nayi saboda kare martabar gidanmu né ,bazan so ahlina suji kunya ba a idon duniya ba halin yanzu abinda nafi buqata daga gareku shine addua kuma kunyi min "ta qarasa maganar muryarta na rawa hajiya zulfa'u tayi saurin cewa "yar albarka karkiyi kuka idan kikayi kuka nima zanyi ".

Cike da zafin zuciya take cigaba da kallon hjy zulfa'u da nana hauwa'u dake drama dan abinda ta d'auka kenan ,ahankali ta mike tsaye ta tsaya a yayinda bakinciki da zafin zuciya ke kutimemeya daita ita kam nana hauwa'u kunyata ce ta kamata da kuma kunyar hada ido da hajiya salema ta sauke ajiyar zuciya sannan ta soma magana cikin fushi "hakika baku min adalci ba ,kowa anan yasan yadda mukayi fama da nuzla akan hisham "yanzu da abinda zaku saka min kenan ?diyata ta gudu saboda bata són auren nan amamn shine zaa dauki wata a maye gurbinta daita ni ko oho kenan shikenan na rasa diyata ?."ta qarasa mgnr tana wani irin kuka" kusani bazan ta'ba manta wannan ranar ba a tarihin rayuwata yadda aka sauya nana hauwa'u da nuzal tana gama fadar haka ta nufi hanyar fita cikin gagarumin tashin hankali."

ATA da yayi mutuwar zaune ya mike tsaye zumbur ya soma takowa zuwa inda nana hauwa'u take tsaye, kansa nayi masa wani irin sara ya qaraso ya tsaya gaban nana hauwa dake kallon kasa yasa hannu ya d'ago ha'barta ya zuba kwayar idanunshi cikin nata yana kallon cikin kwayar idanunta da hawaye ke kwance acikinsu sakamakon jin furuncin hajiya salema ."

Muryarsa a kasalance ya soma motsa labbansa "daman kina son hisham ne ?ta girgiza masa kai alamun a'a "to me yasa zaki amsa zaki auresa ?ta sake girgiza masa kai "ki bude baki Kiyi min magana yayi maganar a tsawace wani tsoro né yayi ma nana hauwa'u diran makiya taji kmr ta saki fitsari a wajen tsabar tashin hankali da sauri ta bude baki tace "a'a?"!To kiina hauka ne ko kin fara shaye shaye ne ?gabanta ya dinga bugawa gbdy duk wata gaba da allah ya halitta ajikinta rawa take kallo daya zaka mata ka gane hankalinta a matukar tashe yake "kin kuwa san irin hatsarin da zaki jefa rayuwarki ciki ?jikinta na rawa ta girgiza masa kai "kin kuwa san me ake nufi da aure ?aure na nufin mutuwa ce kawai zata raba ko kinsan auren da duk baa ginasa akansa soyayya ba baa samun farinciki acikinsa ,maza maza ki fad'a masu cewar kin fasa wannan auren yana gama maganar ya juya zai fita daga d'akin tayi saurin shan gabansa ta durkushe a gabansa ta rike kafafunsa da hannuwanta "kayi hakuri yaya bazan iya ba na rigada nayiwa mumy alqawari kayi min addua tare da fatan alkhairi , kai ne fa ka hada auren hisham da nuzla ba dan tana sonshi ba sai dan ka faranta masa kuma babu wanda yayi maka mutsu bare jayayya akan hukuncinka me yasa alokacin bakayi tunanin auren da duk baa ginasa akan soyayya ba baa samun farinciki?ni da nuzla duk abu daya ne a wajenka idan har zaka iya yanke hukunci akan nuzla kowa yayi na'am dashi kai ma ka amincewa hukuncin mumy akaina".

Numfashi ya janyo da kyar ya fesar yana qoqarin janye kakafusa ta sake rikewa gam tana zubar da hawaye "please yaya karka ki amincewa mumy bata takura min ba ni na amince daga qasan zuciyata kuma zan zauna da yaya hisham tsakanina da Allah."

"Auta me yasa bazaki fahimta ba ?"me yasa zakiyi sacrifice din rayuwarki akan farinciki wasu ?idan Ke zaki iya rayuwar kunci ni bazan iya ganin rayuwarki cikin kunci ba ,bazan so rayuwarki ta qare a wahala ba, ciwon zuciya né zai kasheki saboda zai ta kunsa miki bakinciki né tunda ba kece zabinsa ba "kayi min addua kamar yadda kowa yayi min shine kawai abinda nafi buqata ahalin yanzu ta qarasa mgnr tana shesheka kuka runtse idanunshi yayi tare da dafe kanshi dake cigaba da sarawa "akwai damuwa auta ,akwai zafi da radadi ,yau ace nmj ne Ke son mace komai mai sauki ne, na yanke hukunci akan nuzla ne sanin zatayi farinciki tunda hisham na sonta ke fa ?" bai ta'ba kawowa rayuwarsa ke ba, sam sam bai ta'ba tsara rayuwarsa dake ba idan kina kallon mumy na sonki ba shi ya zamanto zakiyi farinciki a gidansa ?

"please yaya !ta fad'a tana wani irin kuka mai d'aga hankali kalmamin mumy da ta dinga fad'a a wannin data gabata wanda mami ta fad'a mata ne ya dinga dawo mata daki daki ,tunda har mami ta amince da aurenta da yaya hisham bazata ta'ba kin auren nan ba, domin tayi imani ace yaya hisham ba na gari bane mami bazata yarda da hadin ba hannunsa yasa ya d'agota yana share mata hawaye dake gangaro mata sannan ya rungume ajikinsa yana d'an dukan bayanta" wannan shine karo na farko da yayanta yayi mata haka a tun tasowarsu " daman haka yake tsananin sonta ?daman akwai ranar da zai nuna damuwarsa da kulawarsa gareta "?shiru tayi ajikin yayanta tana sauke numfashi ."

Ahankali ya zareta ajikinsa ya zuba mata idanuwanshi itama shi take kallo hawaye na sake cikowa a idanunta "shikenan auta allah yasa albarka yana gama fad'ar haka ya juya Jiki babu kwari ya fice daga d'akin cikin wani irin yanayi na tashin hankali "shi dai har ga allah wannan hadin bai yi masa ba babu yadda zaiyi ne kawai ."

Sunkuyar da kanta kasa tayi ta kasa hada idanu da jamar dake falon babu wanda bata burge ba hatta baba qarami ya jinjina mata domin yasan ba kowa bane zai iya yin abinda tayi haka muke fata a kowani lokaci idan mukayi umarni ya kasance kunyi mubaya'a wannan shi zai sake tabbatar mana da irin tarbiyar da muka baku mun gode da biyayya da hukuncin da muka zartar akanki dan haka ina miki albishir da cewar zaki samu farinciki inji cewar hajiya zulfa'u ta kamota zuwa jikinta "my dear dan Allah ki ramin bala direba zai kai wani waje " kai kawai ya gyada mata sannan ya ciro wayarsa ya soma neman layinsa yayinda tayi hanyar waje da nana hauwa'u ta barsu suna cigaba da tautaunawa har d'akinsu inda ta d'aukota ta maidata tana cewa "bani wasu mintuna zan dawo yanzu kai kawai ta gyada mata sannnan hjy zulfa'u ta juya ta fita daga dakin alokacin bala direban ya iso yana tsaye a haraban gidan ya juya kan mota yana jiranta yana ganin fitowarta yayi saurin fitowa ya bude mata gidan baya ta shiga motar ta zauna tana bashi umarnin inda zai kaita ya amsa mata da "tô!."ya rufe mata murfin motar ya shiga mazaunin direba ya tada mota suka fice daga haraban gidan ."

Hjy zulfa'u na fita daga dakin nana hauwa'u ta kwanta lamo ranta duk babu dadi tunani ne ya lullubeta ita kanta tasan gsky yayanta ya fata mata aure ana ginasa ne akan soyayya domin samun zaman lafiya kuka nana hauwa'u ta fashe dashi wanda har maryam da diyana suka shigo bata sani ba mrym ce ta isa wajenta tare da dafe qirji tana cewa " Sister lafiya me ya faru ?kuka ta cigaba dayi batare da ta bata amsa ba dan girman allah ki fada min me ya faru ."

Diyana ta riko hannunta "me ya sameki hk kike wannan uban kuka haka "nice zan maye gurbin nuzla a wajen yaya hisham "what ?suka had'a baki ta kwanta ajikin mrym da tafi diyana shiga tashin hankali hawayenta take ji ajikinta ta ma rasa me zatace "nima shikenan rayuwata tazo karshe nasan yaya hisham bazai so ni ba tunda nuzla yake matukar só? mrym ta d'agota daga yadda ta kwanta ajikinta "wai wa ya zarta da wannan hukunci ?"shigowar da mumy tayi d'azu nan tayi musu bayanin komai "am very sorry kema da laifinki taya zaki amince mata inji cewar diyana ."

"yaya zanyi bazan iya zuba mata qasa a ido ba mumy ta wuce hk awajena bani ba nasan ko ke tayi wa mgn zaki amince mata bugu da gari mami ta amince diyana bata sake cewa komai ba tunda taji mami ma ta amince ,mrym kam rarrashinta take tana karkafa mata gwiwa "tunda mami ta amince ki kwantar da hankalinki kece fa ke bani kwarin gwiwa kina són naji bani da wannan kwarin gwiwar né ."?ta girgiza kai "tô dan girman allah kiyi hakuri kiyi shiru mu barwa allah komai ."

bangaren ATA zuciyarsa a cunkushe ya shiga d'akinsa bakinciki abinda nana hauwa'u da auren dole da mahaifiyarsa zata masa na sake ninkuwa ,wani irin zafi zuciyarsa ke masa zuciyarsa na matukar zafi ya bud'e qaramin fridge dinsa ya d'auki gorar ruwa tare da kafawa a bakinsa sai daya shanye tas sannan yayi wurgi da roban."

Ahankali ya zame ya zauna akan kujerar kushin "wai me yake faruwa dani né komai ya zama worst agareni shine tambayoyin daya cigaba dayiwa zuciyarsa sam ruwan bai sanyaya masa ransa ba dan damuwarsa na nan bata ragu ba babu abinda yake bukata kamar sigari dan irin sarawar da kanshi yake a yau din nan dole ya had'a da sigari idan ta kama har da giya a hada masa dan yana buqatar ya bugu iya bugawa ya kira daya daga cikin yarasa yace ya kawo masa ta'ba sigari kwali ashirin yana gama wayar ya kwanta yana jiran Peter ."

Bai dade da kwanciya ba aka soma knocking kofar falon yana daga kwance runtse idanushi daga shi sai wondo baki da riga hamles ash colour ya bada umarnin shigowa peter ya shigo cikin falon hannunsa rike da leda cike da girmamawa ya rusuna ya gaisa da ogansa ATA ya yunkura ya mike zaune ya amshi ledar had'e da bude wata durowa dake gefensa ya zaro bandir din fararen yan dubu day day ya mika masa sannan ya bude ledar ya zaro kwalin sigari ."

karba peter yayi ya cigaba da tsayuwa "kaje ka siyo min giya kwalba biyar mai kyau ka kawo min yanzu yanzu ."ya fad'a yana d'aura sigari abakinsa Kallonsa peter yayi cike da mamaki dan tabar ma ya jima bai aikesa ba ".

"amman boss ....." just leave "babu shiri peter ya juya da sauri ya fice daga falon sigari ya soma zuka ko kafin peter ya dawo ya shanye kwali biyu yana kan na uku cike da girmamawa zai ajiye masa yace ya bashi kwalbar giya biyu yasa sauran a fridge ya nuna masa fridge sannan yace d'auko masa glass cup ya d'auko ya mika ya kama gabansa yana janyo masa kofar ."

ATA ya kashe wayoyinsa gabadaya sannan ya balle kwalba giya ya tsiyaya a glass cup ya kai bakinsa bai ji komai ba dan babu abinda yafi bukatar alokacin kamar ya bugu ,yana son ya manta komai ciki kuwa har da mafarkinsa ya shanye tass ya sake tsiyaya wani yana sha yana zukar sigari wani irin zuka yayi wa sigarin yana kwantar da kanshi akan kujerar da yake zaune sai daya dauki second biyar sannan ya d'ago ya kalli sigarin hannunsa daya kusan qarewa ya sake kaiwa bakinsa ya zuga da kyau ya d'auki cup din giya ya shanye yana fesar da hayakin sigari ."

sosai ya bugu ya fita haiyacinsa can ya mike yana layi ya shiga d'ayan d'akinsa ya d'auko tanga memen hoton zanen princess dinsa ya rungume tsam a qirjinsa yana jin wani tsantsar soyayyarta na ratsashi "ina ...ina sonki princess wai a ina zan ganki ne?
" ki fada min inda zangaki mana yana magana yana kallon hoton ya fito falo ya zube akan kujera rungume da zanen a qirjinsa daga nan wani bacci mai nauyi ya daukesa bai sake sanin halin da yake ciki ba ."

Hisham yana zaune yana faman kiran layin nuzla mahaifiyarsa hajiya zulfa'u ta amshe wayar hannunsa tana dubansa "zaka kashe kanka ne akan yarinyar data gudu saboda bata sonka ko me ?"haba mumy ko nuzla ta gudu dan bata sona still akwai yan'uwantaka a tsakaninmu" ban son iskanci ba yanuwantaka ba kune ma kashin awaki qarewar yan'uwanta duk yan'uwantakan dake tsakaninku ya kai ta nida mahaifinta ?

"karka manta nida mahaifinta uwarmu daya uban daya dan haka wallahi Kayi maza ka cireta aranka ai dana san gantalliyar yarinyar nan bata sonka bazan kashe kaina akanta ba "mumy ki barni naji da damuwa dake damuna please "damuwa ai ta qare kamar yadda aka saka ranar daurin aurenka a gobe tabbas a gobe zaa daurashi "Yauwa mumy har kin sa naji dadi bari na tashi na fita nemanta ko allah zai sa na ganta ."

Wani dogon tsaki taja tana dubansa "hisham ka natsu da kyau zaa daura aureka ne amman da wata ba nuzla ba kuma acikin family din nan kamar yadda muka yanke hukunci "what mumy ? haka nake nufi dan allah mumy karki min haka wallahi ni nuzla kawai nike so bazan iya rayuwa da wata ba ,dan allah kar abinda tayi yasa ki yanke wannan hukunci akwai kuruciya a tattare da nuzla wallahi bata da wayon kanta ."

" min shiru a nan kuma karka sake min maganar wata nuzla idan ba haka zaka hadu da mummunar baci raina da baka ta'ba gani bata da wayon kanta tasan ta gudu ta bar gida "? tana gama fadar hk ta tashi zata bar falon ya riko hannunta cikin nashi duk ilahirin jikinsa babu inda baya rawa hatta hannunsa dake rike da hannun mahaifiyarsa kirrrma yake yana sake damke hannunta da kyau "ki tausaya min ,ni zaki duba mumy da halin da zan shiga nuzla wata abace mai daraja acikin rayuwata karki maye min gurbinta da wata cike da jin haushi ta fixge hannunta "for the last time karka sake min maganarta sha sha kawai da bai son ciwon kansa ba yarinya ta gudu ana gobe daurin aurenku amman ka tsaya kana fad'a min tana da daraja acikin rayuwarka tunda ta gujeka na tsaneta Ka shirya karka manta karfe hud'u daidai zaa tafi diner "what? ai kasan da zuwa wajen diner dan hk karka bata lokaci tana gama fadar haka ta bar dakin kai tsaye wani haddaden office din gyaran jiki ta nufa ."

Nan da nan ya kira salim cikin tsananin tashin hankali bayan sun gaisa ya fad'a masa halin da yake ciki salim din ma kwantar masa da hankali ya dinga yi" kayi hakuri da hukuncinsu hisham ya rude ya rasa abinda Ke masa dadi amman me yasa zaa min haka bayan an bada cigiyarta a kafafen sadarwa to dawa zaa hadani auren "?shiru salim yayi na second goma sannna yace "nana hauwa'u "

"Wata irin zabura hisham yayi yana cewa "what !? wace nana hauwa kenna ?ya fad'a a rude idanunshi suna qara canza kala tsabar tashin hankalin da yake ciki ganin irin rudewar da yayi salim yace "ka natsu ka sausautawa kanka, haka rayuwa take hisham kullum tana zuwa da sauyi sauyi bisa izinin allah wanda bawa bai isa ya canzawa kansa qaddararsa ba hisham kayi hakuri nana hauwa dai da kasani kanwa ga ATA ."

"Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun ya shiga furtawa yana maimaitawa rike da waya salim ya dade yana rarrashinsa da yi masa nasiha yanzu dan rashin Imani mai yasa zaa bani nana hauwa'u?me zanyi daita ya qarasa maganar ya hadiye wani abu daya tsaya masa a makoshi "ka taimaka hisham karka kunyata iyayenmu karka manta mutane bilaadadin ne zasu halarci dauren auren nan kuma kowa ya rigada yasan dauri aure biyu zaayi ita kanta nana hauwa'u dan kar kimar gidana ta zube yasa ta amince "shiru yayi kawai ya sauke wayar a kunnensa yana kallon saman dakin ."

Yana cikin wannan halin dad dinsa ya shigo da sauri ya kalli mahaifinsa cike da rauni ya mike alokacin da dad dinsa ya zauna kusa dashi hisham ya riko hannunsa yana cewa "abba kaji mumy wai zaa daura aurena da nana hauwa'u dan allah abba kada ka bari a daura auren nan ya qarashe maganr cikin tashin hankali da bacin rai ,cikin zuba masa ido abban shi yace "me yasa zaa bari ?kanshi ya shiga girgiza masa tare da hade hannunwansa waje daya da nashi yace "saboda banasota a bawa wani ita amman banda ni." hisham gsky auren nan fa kamar an daura shi an gama babu wani mahalukin daya isa ya hana wannan daurin auren gara ma ka kwantar da hankalinka tunda ka jurewa auren wacce bata sonka ai sai ka jurewa wacce zata taimakawa rayuwarka sannan wacce zata cire iyayenka cikin shiga kunya "pls abba "kai babu fashi dole sai ka aureta cikin jin haushi ya mike ya shige d'aki ya rufo kofar da karfi ."

Hajiya salema ta zube a kasa tana cigaba da hawaye a gaban baba babba dake zaune yana qara karanta wasikar da nuzla ta ajiye musu sannan ya d'ago ya kallesu gbdy "kar ma sake ganin kowanne acikinku ya shiga damuwa akan nuzla tunda ta zabi barin gida tô ina ganin ta ciremu daga cikin mutane masu mahimanci ne arayuwarta dan haka muma yana da kyau muyi saurin cireta daga zuciyarmu a firgice hjy salema ta dago ta kallesa tace "amman alhj kana gani wannnar maganar daka fada babu wani gyara acikinta taya zamu haifi yarinya da cikinmu ace kuma mu manta da ita "?kafin ta qarasa mgnr har baba babba ya mike ya shige d'akinsa dan yaji bakinciki abinda tayi acikin mutane ."hjy salema fashewa tai da kuka suma ya'yanta mata suka fashe da kuka zukatansu nayi musu zafi kamar zata fito."

Mmn sudaisi

💗💗💗💗💗💗
   MAR'ADAMS
   💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi  byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

       Page 29

   Ahankali yaya Ibraheem ya shigo parlour'n hankalinsa yayi matukar tashi sakamakon yanayin daya ga mahaifiyarsa da yan'uwansa ciki ,hajiya salema tana kuka aunty amina da aunty zainab suna tayata kuka tamkar ransu zai fita ,sai daya numfasa sannan ya fara magana a natse "amina ,zainab bana son wannan kukan ,idan kuna kuka ya kuke son hajiya tayi ? kune fa ya kamata ku dinga bata kwarin gwiwa da rarrashi amman sai ku tasata gaba da kuka ".

"Sam yaya baka ta'ba duba damuwarmu ."koda wani lokaci laifinmu kake kallo idan bamu taya mahaifiyarmu kukan ahalin da take ciki ba me zamuyi ?" Inji cewar amina "shikenan mun rasa nuzla shi kuma hisham an bashi wata amadadinta yarinyar nan fa bata son shi aka takura mata gashi ta gudu an barmu da matsalarmu nasan ko mutuwa tayi basu da asara "zainab ta qarasa mgnr tana zubar da hawaye."

Zainab tasa gefen mayafinta ta goge hawayenta kana ta cigaba da magana "kai ma yaya kasan ba'a kyauta mana ba kuma koda wani lokaci baba abayansu yake baka san abinda hajiyarmu take ji acikin zuciyaarta ba , wallahi matsawar baa ga nuzla a rayuwarmu a haka zata qare ,tabbas raywarmu zata qare cikin damuwa amman wallahi kowa sai ya d'and'ani kud'arsa dan wallahi i bazamu yarda ba wannan d'aurin auren bazaa d'aurashi ba sai an nemo mana nuzla zumunci ya dade bai lalace ba kowa yayi ta kansa kawai .."

"Kada kuyi haka amina gara mu mika komai
zuwa ga allah "yaya Ibrahim ya fad'a yana kamo hannuwansu ya zaunar dasu akan kujera suka zauna suna zubar da ruwan hawaye ,ya kamo hajiya salema itama ya zaunar daita yana dubansu ,kallo daya yayi masu ya gano cewar gabadayansu basa cikin haiyacinsu "sam sam kalmanku basu min dadi ba kuma kun bani mamaki dan banyi tsamanin wadan nan kalaman zasu iya fitowa daga bakunanku ba ,kun kuwa san yadda naji da kuka fadi lalacewar zumunci ? dan allah ku dawo hankalinku sam baba bazai ji dadin duk wani abu da zaku kunno kai dashi cikin ahlinsa ba ."

Ya maida hankalinsa sosai ga hajiya salem yace "hajiya Kiyi hakuri ki barwa allah komai ita rayuwar dan adam cike take da qudirin ubangaji kala kala ,dukkan rayuwa rubutacce alamari ne daga Allah duk wani d'an adam ya kamata yasan wannan ,haka Allah ya qaddaro nuzlah ba matar hisham bace duk yadda yake sonta yake muradin aurenta bazai aureta ba wata zai aura ,haka zalika itama nuzla ba abokin rayuwarta bane muyi fatan allah yasa hakan ya zama alkhairi agaresu ,ita kuma nana hauwa'u kuyi mata fatan nasara a rayuwar aurenta ita kuma nuzla allah ya karkato mana da hankalinta ta dawo gida."

  hawaye ne ya gangaro daga cikin idanun aunty zainab da aunty amina bakinsu ya kasa furta komai sai kuka ita ma hajiya salema ta qara sautin kukanta sosai ,babu abinda bakinta ke furtawa sai ku nemo min yarinyata sosai jikinta ya dauki zafi rarrashinta kawai suke amman taki yin shiru bakinta ya cigaba da furta ku nemo min yarinyata "hjy ki barwa allah komai sannan ki kwantar da hankalinki ayi komai dake in sha allahu ana gama bikin nan zaa cigaba da neman nuzla ."

sanyayyen ajiyar zuciya ta sauke ga kuma hawaye na gangarowa akan kuncinta jin bai biyewa mahaifinsa da yace kowa ya cireta arai ba muryar cike da sautin kuka tace "Allah yayi maka albarka babu abinda yake damuna kamar rashin nuzla yau da diyata tana tare dani aka samu wannnan sauyin bazan ji 'bacin rai haka ba ,dan Allah ka nemo min nuzla zuciyata na cike da kewarta ,nayi nadamar goya masu baya alokacin da zaa hada auren nan ,banci na amince da yanzu yarinyata na kusa dani cikin kwanciyar hankali wallahi nayi nadama ku nemo min nuzla dan bazan iya jurar rashinta ba."

yaya Ibraheem ya dafe goshinsa yana jin zafin zubar hawayen mahaifiyarsa tana matukar bashi tausayi ya zai yi ya nemo nuzla ta ina zai fara ?sautin qarar wayarsa ce tasa ya sauke hannunsa ya ciro ya duba a gaban aljihunsa ya duba a hankali ya mike tsaye yana cewa "ku samu wani abu ku bawa hajiya taci sannan ku hada mata da maganin zazzabi tasha jikinta yayi zafi daywa zan dan fita amman bazan dade ba dan Allah ku cire damuwa da kudirinku ayi komai daku sannna kuyi qoqarin kwantarwa hajiya da hankali ".ya qarasa fada tare da ficewa daga parlour'n ya bar hjy salema da ya'yanta."

Cikin mintunan da basu wuce talatin ba sai ga hjy zulfa'u ta dawo masaukinta da meera mai lalle da make up ,ta shigo falon bakinta dauke da sallama tana cewa "my dear ina son yake ?"bai dade da shiga daki ba, ban san me ke damun hisham ba kinga yadda ya d'aga hankalinsa ya dinga hadani da allah akan lallai sai an fasa auren nan dan rashin sanin ciwon kai irin nashi ."

"rabu dashi zan sauke masa duk wani abinda yake kanshi tana gama fad'ar haka kai tsaye dakin da yake ta nufa ta tura kofar ahankali ta shiga yana kwance idanusnhi a runtse cikin tsnanin tashin hankali ."yaji motsin shigowarta amman yaki bude idanunshi har sai data qarasa shigowa sosai ta tsaya akanshi tana kiran sunansa "hisham !da kyar ya bud'e idanushi ya zuba mata cikin tsananin damuwa "tashi muje kayi min rakiya"

"zuwa ina kenan mumy ?kai dai ka tashi muje ta miko masa tafin hannunta ya mike da kyar yana cewa "dan girman allah mumy kiyi hakuri ki bar maganar auren nan nuzla ce rayuwata bazan iya rayuwa babu ita ba wannan yarinyar da zaa hadani aure daita bazata ji dadin rayuwa dani ba saboda ba ita zuciyata take so ba ,"bana son maganar banza hisham yarinyar data rufa min asiri kake fada min haka akanta idan baka kiyayeni ba zan mugun saba maka akanta amman mumy kina ganin ya kamata ki tsani nuzla irin ha .."?

"Kada kace komai dan banason jin komai daga bakinka matsawar tozarci né ga nana hauwa'u a halin yanzu bana ji bana gani ita kawai nake só itace rayuwata yanzu tunda zata rayu da kai kuma zan iya yin komai akanta dan ita zan iya sadaukar da farincikina hisham tashi muje ta sake miko masa tafin hannunta zuciyarsa cike da tashin hankalin ya sanya hannunsa cikin nata ."

suka fito zuwa parlour'n zasu  wuce dady yana waya tace " my dear sai mun dawo ya d'aga masu hannu suka fito suka shiga gidan baya suka zauna yayinda meera mai lallae ke zaune agida gaba gama zamansu keda wuya direba yaja motar suka fice ahankali motar ke tafiya hajiya zulfa'u na cewa "hisham ka kular min da nana hauwa'u kada ka wulakanta min 'ya dan bazan lamuncewa hakan ba ,daidai satin zuciyarsa ya dafe dan zafin maganarta yake ji "ples mumy ki bar maganr haka zuciya zata tarwatse numfashi ta sauke da karfi bata qara cewa komai ba ."

kai tsaye abdullahi estate suka nufa bayan sun firfito daga cikin motar suka shiga gidan hajiya zulai falon gidan cike da mutane ,ana ganinta falon ya hargitse da hayaniya nan aka fara gaishe gaishe ana ga uwar ango da amarya shi kam hisham kanshi na kasa duk yadda abokan wasansa ke jansa bai dago kashi ya kalli kowa ba kusan ya matsu mumynsa ta sallamesa ya kama gabansa ,sai da hjy zulfa'u ta gama taja hanunsa suka nufi dakin nana hauwa'u inda ta iskesu zaune cirko cirko cikin zullumi .

suna ganinsu suka tattara hankalinsu ga mumy da hisham , ahankali hisham ya daura idanunshi akan nana hauwa'u sai dai kallo daya yayi mata ya dauke kwayar idanunshi akanta ita kam ta bala'i kafeshi da idanunta tana son gano yayinsa amman kallo dayan data ga yayi mata ya d'aga mata hankali wanda yasa gabanta ya dinga dukan tara tara ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta muryata a matukar sanyaye tace "mumy barka da dawo ."yauwa diyar albarka sannuki da qoqari kinji allah yayi miki alabarka ,allah ya jikan mahaifinki "Ameen!" nana hauwa'u ta amsa tana cigaba da wasa da yatsun  hannunta yayinda gabanta Ke cigaba da faduwa."

" meera ga guri ki zauna ki fara aikinki ga wacce zakiyiwa lalle ."ta nuna mata nana hauwa'u "lalle zaayi mata to shi meye na zuwa dashi ?ya d'ago a natse ya kalli hajiya zulfa'u fuskarsa da alamun tambaya , shiru tayi masa tai masa nuni da kujerar dake fuskantar nana hauwa'u kin zama yayi ya cigaba da tsayuwa ,meera ta fara hada lallen da zatayi wa nana hauwa'u "ka zauna mana ka wani tsayawa mutane aka "ni mumy abinda ban fahimta ba me zanyi idan na zauna ?".

"ina son ayi mata lallen agabanka "what !? ya fad'a a hargitse ta gyada masa kai cike da mamaki yake kallonta nana hauwa ta sauke numfashi ta d'ago ta d'an saci kallonsa "mumy ki fahimceni ko ina son auren nan bazan zauna acikin mata ba bare bana só shiru mumy tayi zuciyar na rawa kafin ahankali ta motsa labbanta tace "ni zaka fadawa haka hisham ?"Shikenan na gode amman ka zauna  kamar yadda na buqata ."gsky mumy sai dai Kiyi hakuri dan wallahi bazan iya zama ba "yana gama fadar haka ya juya cikin tsnanin damuwa ya nufi kofar fita "hisham! hisham !! hajiya zulfa'u ta dinga kiran sunansa amman ina tunda ya nufi kofar fita bai juyo ba, ta gyada kai kawai tare da samun waje ta zauna zuciyarta na mata wani irin zafi ."

"Mumy !
Nana hauwa'u ta kira sunanta muryarta a sanyaye ta d'ago tare da zuba mata idanunta "dan allah karki damu ki kwantar da hankali karki yi fushi dashi dole kowaye ya tsinci kanshi cikin halin da yaya hisham ya tsinci kanshi ya shiga damuwa ,a yanzu rarrashi yafi buqata ba takurawa ba "ta qarasa maganar tana mai sunkuyar da kanta tare da danne kukanta "na gode sosai diyar albarka in sha allahu muddin ina raye sai kinyi farinciki agidan hisham "murmushi nana hauwa'u ta sakar mata ba dan tana cikin farinciki yin murmushi ba sai dan ta kwantar da hankalin mumy ."

Ahankali meera ta fara zana mata jan lalle yayinda mumy Ke jan nana hauwa'u ajiki ta hanyar yi mata hira su kansu diyana da humaira har ma da maryam mumy ta burgesu matuqa ,ana zanawa nana hauwa'u lallen mumy na yabawa "Woww gsky lallen nan yayi matukar kyau meera ai kudin lallenki yafi karfin yadda kika caza dole ma na qara miki kudi ."gabadayansu sukai dariya meera tace "na gode hajiya koda meera ta gama mata bata wuce ba dan zata tsaya tayi mata make up din zuwa wajen dinner kowacce ta kama gabanta domin shirya kanta aunty shahida tazo ta d'auki maryam  ta wuce daita domin shiryata ."

karfe uku daidai aka fara tsara wa nana hauwa'u kwaliya sosai tayi kyau cikin doguwar rigar less red wanda mumy ce ta kawo mata daman kuma ta tanada ne dan nuzla komai red tayi amfani dashi kasancewarta fara sol tayi kyau sosai abun sai wanda ya gani shima a 'bangaren hisham red din yadi yasa ba qarami had'uwa yayi ba nana hauwa'u gani take ba ya ita amma tana ganin hisham ta raina kanta saboda wani irin kyau da yayi mata ya zarta kyau sosai  ."

Tsura masa ido tayi tana kallonsa tsaye shi kuwa ko kallon inda take bai yi ba illa ma cigaba da amsa wayar da'aka kirasa yayi ,wata qawar mumy ce ta riko hannun nana hauwa'u ta kawota kusa da yaya hisham suka jero suka shiga mota zuwa hall koda suka shiga mutane suna ta d'aukansu pic jikin nana hauwa'u yayi sanyi sakamakon kalon baza da yaya hisham yake mata ji tayi kamar ta hana daukar hoton amamn bata damar aikata haka duk tajita a takure kamar ta koma gida ."

Bangaren maryam kuwa an tsara mata kwaliya ta ban mamaki tayi kyau iya kyau cikin wani hadadden lace farin anyi mata dinki weeding gwan duk wanda ya daura kwayar idanunshi akanta sai dai yace Masha allah dan kyau kam tayi shi sai daukarta a hoto ake kafin angonta ya bayyana yayinda ango na can a buge mb, salim ,yasir suna tsaye akanshi sun zuba masa idanunsu cikin tsnanin tashin hankali dan sun razana da ganin halin da yake ciki hannunsa ya kai daidai saitin qirjinsa yana murza daidai inda zuciyarsa take bugawa da karfi yayinda gefensa hoton zanen princess dinsa ne yana kallonta yana zukar sigari."

Ahankali ya dauke gajiyayyun idanunshi da suka canza kala saboda bugawar da yayi akanta ya dan waresu akansu yaga still shi suke kallo kwalban whisky's guda uku agabansa inda yake dagasu daya bayan daya yana sha yana zukar sigari cikin tashin hankali ,idanunshi sun qara rikidewa sunyi ja sosai ,ganin bashi da niyyar daina shan giyar yasa a matukar zuciye mb ya ture cup din daga gabansa yace "why ATA ?" akanka aka fara irin wannna auren ?wallahi ka sani shan wannan abu bazai amfaneka da komai ba don't forget mami yau tana cikin farinciki kuma ta tara jamaa me kake tunani zataji idan taganka cikin wannan halin ?kana son heart attack ya kamata ne ?."

'Dago jajayen idanunshi yayi ya kalli mb bai ce masa komai ba ya kunna sigari ya kai bakinsa yana zuka yana kallon wani bangaren dabam "wannan wani irin kaskanci ne haka ATA kalli fa ,kalli irin rayuwar da ka jefa kanka daga shan sigari ka dawo giya ni har yaushe ka fara shan giya ?"ban sani ba kuma babu ruwanka da rayuwata haka ya kamata nayi ko na zama wannan ciwona ne ni kad'ai babu ruwan kowa dani ."

"why ATA? saboda wata soyayyar banza zaka kashe kanka akan wata yarinyar banza da ba gaskiya bace kana qoqarin 'bata rayuwarka, ka manta da wannan yarinyar ka kama wacce aka baka ka d'aura rayuwarka daita "salim !"ya kira sunansaa tsawace shiru salim yayi yana dubansa ya dauki kwalban giya ya kai bakinsa sai daya shanye tass sannan ya fuskancesu "akan mafarkina nake yi wannan abu ko ba akanta bane ni dai abinda nasani soyayyar da nake mata gaske ce kuma har abada domin Itace duniyata tana cikin nan  a duk inda take nasan itama tana jin yadda nike ji acikin zuciyata."

"dan allah princess ki tausaya min bazan iya rayuwa babu Ke ba , idan babu Ke bazan iya cigaba da rayuwa ba ,ya mike da kyar yana layi ya dauki kwalbar giya ya fasa sannan yace "an hadani aure da wata guntuwar yarinya ita kuma nana hauwa'u an hadata da heart attack ,ajiyar zuciya ya sauke sannan yace idan hisham ya cutar da nana hauwa'u zan yanke komai dake tsakanina dashi wallahi wallahi I promise to make his life in to hell he will end his life in prison a firgice suke kallonsa zukatansu na duka tara tara idan kuma ban kaishi prison ba zan kashesa matsawar ya cutar min da yaruwata ."

ya nufi kofar bedroom dinsa sauran kadan ya fadi mb yayi saurin kai hannu zai tarosa ya buge masa hannu yana cewa "don't don't touch me just leave my room ya fad'a yana shigewa dakinsa yana shiga ya kwanta flat akan bed tamkar wani matacce ."
Dakin suka shigo gbdy suka rufa akanshi kamr zasuyi hauka mb ya hauro har saman gadon ya dagosa ya kwantar dashi ajikinsa ya kai hannu ya kamo fuskarsa yana dan marin kuncinsa tare da kiran sunansa "ATA ka tashi please karka zama haka yayi maganr yana kuka me yasa zaka mana haka ?"

salim da Yasir ma sunansa suke kira "wannan fa ya rigada ya bugu babu inda zai iya zuwa kamata yayi a fadawa mami "wa zai iya wannan karfin halin ?wa zai iya tun karar mami da wannan maganar ?bazan so mami ta gansa cikin wannna halin ba inji cewar yasir "to meye mafuta yanzu me zaa bashi ya dawo daidai ?abu daya ne zaa iya bashi shine kokin shi kuma yana fara shanta matsala ne arayuwarsa gara kawai duk mu kwashe duk wani kayan maye dake dakin mu barsa yayi bacci idan ya farfado zai dawo daidai ."

Ahankali ya motsa lip's dinsa "I can't marry this stupid girl I can't marry her coz she's not my type shine maganar da yake fitowa daga bakinsa "yanzu me zamu cewa mami ?a gaya mata gsky kawai yasir je kazo da mami ."Okay ya fad'a yana mikewa tsaye ya nufi kofar fita tare da mami suka dawo ai tana ganinsa ta daura duka hannuwanta bisa kanta ta fashe da wani irin kuka tana kallonsa tana furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun tana qoqarin zubewa kasa ganin gaba d'aya ATA baya cikin haiyacinsa ,dan tuni bacci yayi awon gaba dashi jikinsu a sanyaye ganin mami na neman zaucewa suka tarota suna cewa "kiyi hakuri mami Kiyi masa addaua " yanzu abinda adamcy zai min kenan ana gabe daurin auresa?" yanzu ka kyauta min adamcy ?

"gsky bai kyauta ba mami amman Kiyi hakuri girgiza kai mami tayi sannan ta sauke naunayen ajiyar zuciya ta mike da kyar ta fice daga dakin ."da kyar take jan kafafunta ta sauko ta tashiga 'daki  tana kuka Allah ya taimaketa babu kowa acikin dakin domin mutane duk sun wuce zuwa hall ta kulle dakinta kuka mami take sosai ta kira aunty shahida kiran na shiga amma bata 'dauka ba dan haka ta kira aunty khadija ita kuma wayarta a kashe mami tarasa abinda Ke mata dadi sai da zaa fito da maryam aunty shahida ta lalubo wayarta nan taga missed call din mami yafi goma cike da jin tashin hankali ta soma neman layinta mami ta dauka cikin yanayi na damuwa tace "shahida !".

"Naam mami ya naji muryarki haka wani abu na damunki ne ?babu komai shahida ku wuce da maryam hall yau ma dai kamar jiya ita kadai zata zauna "shiru aunty shahida tayi kafin daga baya tace "mami ina adam din yake ?hakan nan mami ta kasa fad'a mata halin da yake ciki tace "yana kwance babu yadda yake bashi da lafiya ina maryam din take "gata nan a kusa dani "bani ita aunty shahida ta mika mata waya ,ta karba tana jin faduwar gaba mai tsanani".

"hello mami !" maryam ykk ? lafiya lau mami ya naji muryarki kamar kinyi kuka ? babu komai maryam fatan kinci abinci ? ta gyada mata kai tana cewa "Eh naci numfashi mami ta sauke "kina jina mrym ? tace "eh mami ina jinki "nasan zaki fahimceni zaa wuce dake hall yanzu yau ma kamar jiya Ke kadai zaki kasance bana son kisa damuwa acikin ranki kinji ki dinga tuna kina dani "to mami !" ta fad'a hawaye na cika idanunta aunty shahida ta girgiza mata kai alamun karta yi kuka jiki a sanyaye ta mikewa aunty shahida wayr sukai sallama da mami ."

Shiru aunty shahida tayi tana tunanin yadda yau ma maryam zata zauna ita kadai batare da ango ba ,bata ki maganar mami ba domin tasan rashin mafuta yasa ta fadi hakan amman ita dole ta nemo mafuta dan baza bari maryam ta zauna ita kadai ba ko hisham daya tsinci kanshi da auren nana hauwa'u acikin kwana daya ya yarda ya amince har ma sun isa hall bare adamcy da aka dauki sama da watanni ana abu daya ,sosai kwakwaluwarta ta shiga tunanin abunyi zuciyarta ta bata shawarar ta nemi salim ya maye gurbin ango tunda daman jiya babu wanda ya gansa ."

da sauri zuciyarta ta amince da haka nan da nan ta shiga neman layin salim kira daya tayi masa ya dauka adaidai lokacin da suke shirin shiga mota dan zuwa hall "yaakayi my aunty ?kana ina salim ?gamu muna shirin zuwa hall ,yauwa salim dan allah kazo ka maye gurbin adamcy babu dadi maryam taje wajen diner ita kadai kafadansa ya daga alamun babu damuwa yace "okay shikenan an gama aunty ya yi discounneting din kiran yana duban sauran abokan tafiyarsa tare da yi masu bayani ,gsky aunty ta kawo shawara wallahi maryam na bani tausayi dan allah ya hadata da wani irin mutun mai shegen taurin kai, bari mu jira a fito daita sai mu mubi bayan motar ku, suna tsaye aka fito da maryam salim ya bude mata bayan mota ta shiga ta zauna shima ya shiga ya zauna aka rufe murfin mota yayinda mb da sauran abokan ango suka shiga motocinsu suka bar gida ."

Tamkar ango da amaryarsa salim yayi active suka jera har zuwa mazaunin ango da amarya aunty abida ta kallesu ta kwashe da dariya tana kallon mahaifiyarta ,"mumy kinga abinda nagani kuwa ?na gani abida jiya bai zo ba ga yau ma ,ai halin adam sai ahankali ,shiyasa nake ganin da wahala ki iya shawo kanshi ya auri sultana"kai mami karki hada sultana da wannan yarinya sultana ta kereta a komai duk yadda zamuyi ta shiga gidansa sãi nayi idan allah ma ya taimakemu sai ya sota kinga komai zai zo mana da sauki ato allah yasa ,wannan lamari yayiwa abida dadi dan haka ta dinga jinta cikin tsananin farinciki ."

Hall ya cika makil da jama'a ta bangare dabam dabam maryam tayi shiru tana rike da jaka yayinda masu hoto da vedio suka dinga daukarsu hoto har sanda aka kira hisham da amaryarsa zuwa fili ahankali ya mike atare suke daga kafafunsu suka tsaya a fili tamkar wasu gumaka hajiya zulfa'u ta shigo da 'kawayenta da ankonsu iri daya ta dinga likawa nana hauwa'u 1k amma ko kalon hisham bata yi ba MC ne yayi magana wai ya yaga hajiya iya amarya takewa liki ."

murmushi tayi tace mishi "ai itace tafi cancata yar albarka yar gidan arziki gaba da baya irin albarka kaga dole ita ta dace da naiwa liki" aikuwa gurin ya 'dau shewa da tafi mutane wasu suce " wannan haka yake hajiyarmu Allah ya 'kara arziki hisham kuwa ya cika makil dan ganinsa tozarci ne abinda mumynsa tayi masa suka koma suka zauna aka kira maryam da angon bugi,maryam dake zaune wasu irin hawaye masu ciwo suka zubo mata ta yunkura ta tashi tsaye salim ya rike hannunta cikin nashi saurin kallonsa tayi sam bai damu ba ya kauda kanshi kawai ya soma tafiya daita ba dan ta soba ta dinga daga kafafuwanta ."

da zata taka step ya tsaya ta sauko ahankali yana daga mata rigarta d'an kar ya hardeta abun ya burge mutane mc kuwa ya dauka angon gaske ne nan ya fara zuba "kai wannan ango yana ji da matarsa yana son matarsa see love ai nan hankalin mutane ya sake karkata kansu aunty abida tace "dama shi ya aureta muka huta dan sunfi dacewa dashi sultana kuma da adamcy "ke dai kina qaunar sultana da wannan mai shegen taurin kan tsiya "duk zai daina ne bari dai ya shigo hannun mace ."

sosai salim ya kwashi rawa tare da maryam lokacin da aunty abida ta tashi taje liki byn tai liki ta kai bakinta daidai kunne maryam "karshe mai naci kenan da kin nuna baki raayi kamar yadda ATA yayi da yau baki wayi gari da aron ango ba wannan kawai ya isheki misalin irin halin bala'i da zaki shiga a gidansa "har aka gama taron aka watse aunty abida tana mata habaici wanda bata san dalilinta nayi mata hakan ba salim ne ya maida ita gida kai tsaye ta fito ko kallon inda yake batayi ba tashige gida ta rabu dashi dan taji haushin hannunta daya rike shima bai damuba yai tafiyarshi gida mrym tana shiga dakinsu kuka ta saka ranar  yadda maryam taga rana haka taga dare ga kuka datasha kamar ranta zai fita."

Karfe daya daidai ata ya farka daga baccinsa ya mike da kyar ya shiga bathroom yayi wanka ya dauro alwala ya fito ya sanya vest da boxer sannan ya daura jallabiya mai garen hannu akai ya qarasa inda daddumarsa yake ya tada sallah bayan ya idar da salolinsa ya zauna yana tunanin awannin daya kwasa yana bacci , can ya mike ya fito zuwa falonsa ya bude fridge bai ga whisky dinsa ba ya kalli inda ya ajiye kwalayen sigari ko karan sigari daya bai samu ba ya maida murfin fridge din ya rufe da karfi yana jan tsaki ."

ya koma ya zauna ya zubawa zanen princess dinsa idanu yana kallonta yana zaune mami ta turo kofar dakin ta shigo idanunta ya sauka akanshi idanunshi sunyi wani irin girma ta zauna a kusa dashi bai yi magana ba har sanda ta soma mgn "adamcynah ka tashi ?"eh na tashi! ya fad'a kawai yana duban zanensa yanayin yadda ya amsa kamar yana jin haushinta."

ta numfasa kana tace "me yasa baka tashi lalata rayuwarka ba sai alokacin bikinka ?me ya kaika shan giya adamcy ?yanzu ka kyauta min kenan ?ka kunyatani acikin mutane kowa sai tmbyrka yake ka kuwa san adadin karyar da nayiwa mutane ? "ni fa bikin nan bashi da wani mahimanci agareni dan Allah sweetheart ki daina min magana akanshi sake daga min hankali yake "jin haka yasa ta canza magana "me zaa kawo maka? "shiru yayi yaki cewa komai dan idan ya bude bakinsa ba abinda zai ce a kawo masa sai giya da sigari su kawai yake buqata "bari naje na kawo maka abinci ta fad'a tana mikewa ta shafa kanshi sannan tayi gaba ."

Tana fita Ya kira yaronsa yace ya siyo masa giya amman wacce tafi duk wanda yake sha karfi da sigari yana ajiye wayar mami ta dawo dakin ta ajiye masa plet din abinci agabansa kaci yanzu da zafinsa ta wuce bai ci abincin ba har sanda yaronsa ya kirasa ya dauka yana cewa "ka shigo mana " mami tana falo okay ina zuwa ya mike tsaye ya sauko lokacin daya sauko mami ta tashi ta shige dakinta ya fita "ya ka dade ?yallabai go slow yafi yawa a shagon siyar da giya fiyye da shagunan siyar da abinci bare adaidai wannan lokacin "okay kaje kawai ya karbi ledar hannunsa kwalba biyar ne aciki sai kwalayen sigari ya dawo dakinsa ya ciro daya ya balle bai tsaya sirkawa ba ya kafa abakinsa bai sauke ba sai daya shanye tass sannan ya daura da sigari haka yayita sha har karfe biyu da rabi ya koma bedroom dinsa wanda alokacin ya shanye kwalba hudu yana kan ta biyar ."

*****
Washegari sunday ya kama daurin aure hisham bai tashi ba mumy ta dinga kiransa a waya gajiya yayi da kiranta ya dauka ya mike zaune yaji dalilin takura masa da take yi, yana dauka ta rufeshi da bala'i "wallahi hisham ka kiyayi fushina  idan ba so kake nayi maka baki ba wallahi ka natsu ka shiga hankalinka ka bari ayi komai a gama lafiya "yanzu mumy me nayi ?daurin aure ne a daura mana ai ba lalle sai naje ba "okay ni zaka fadawa haka ?" to dan girman allah karka zo "da taimakon salim hisham ya shirya tsaf cikin wata dakakkiyar shadda gezner fara sol koda suka fito mutane sun cika acikin haraban estate din ."

Ahankali mb da sauran abokansu suka shigo falon ATA kowannensu sanye da farin yadi mai shegen tsada ,basu ganshi ba dan haka mb ya tura kofar bedroom dinsa anan ya gansa kwance a kasa shame shame tamkar matace ,da wani irin sauri ya qarasa inda yake kwance ya durkusa a gabansa yana cewa" Kai adam ka tashi mana lokacin zuwa daurin aure yayi fa "ya fad'a yana kallon kofar shigowa dakin "kai yasir kuzo ku ganshi ya qara shan giya ya bugu fiyye da jiya ya sake kallon fuskar ATA yana shafa fuskarsa ," kai wai meye haka ne ?subuhallah ya bugu kuma? inji cewar salim da yasir da suka shigo atare cikin tsananin tashin hankali."

" kamo shi mb yayi yana cewa "ku taimaka min mu daga shi gbdy suka kamo shi zuwa kan bed dinsa suka kwantar dashi suka dinga jijiga shi" ka tashi dan girman allah lokacin daurin aurenka  yayi ,amman shiru kake jin ATA dan ko motsi baya yi numfashi ma da kyar yake fitarwa yasir ya kai hannu ya bude idanunshi yana kiran sunansa," kai ku duba fa kugani kwayar idanunshi sun dauke inna lillahi wa inna ilaihi rajiun kai abokina ka bude idanunka muna tare da kai dan allah karka min haka bana son na rasaka ."mb ya fad'a cikin tsananin tashin hankali mara iyaka .

"kana jina abokina ka bude idanunka yana magana yana jijiga shi amman har lokacin ATA bai motsa ba bai ma san a halin da yake ciki ba duk yadda sukayi su tashesa amman abun yaki cikin tashin hankali mb yake kallonsa gabansa na faduwa acikin kwana biyu kacal da soma shirye shiryen biki ya zare ya fita haiyacinsa bai ta'ba tsamanin zai shiga wannan halin ba da shi karon kashi ya shawarci mami a hakura da auren kawai kowa ya huta ."

sosai mb yaji babu dadi ganin halin da amininsa yake ciki da sauri mb ya nufi kofar fita daga dakin kunnensa manne da waya yana cewa "hello sadiq kana ina ? "dan girman Allah ka ..ka taimaka min ATA nan ya zayyane masa komai cikin tashin hankali eh kazo da allurar please ya katse kiran ya koma cikin dakin har lokacin kwayar idanunshi bai dawo daidai ba ko dan sambatun nan na bugaggu bai yi ba ."

suna tsaye sadiq ya shigo ya fara dubasa "yana da rai numfashinsa ne yayi nisa sakamakon buguwar da yayi amman zan masa allura nan da wasu yan awanni zai dawo daidai ya ciro sirinji daga cikin bakar jakar daya shigo dashi ya hada duk allurar zaiyi masa bayan yayi masa ne suka fito daga cikin dakin dukkaninsu jikinsu a sanyaye inda zuciyar mb Ke bugawa da karfi kamar wasu kurame haka suka sauko babu ango, ganin mami yasa duk suka dan saki fuska dan karta gane akwai abinda yake faruwa sai dai kallo daya tayi masu ta fahimci akwai matsala tun kafin su kai ga fita ta nufi hanyar dakinsa ."

Tana shiga dakin yana kwance a buge Kmr jiya ta tsura masa ido bata ko liftawa ga wani tashin hankali data tsinci kanta ciki wanda bata ta'ba jin irinsa ba ,bta ta'ba nadama da danasani ba sai a safiyar yau din nan ,gabadaya jikinta ya dauki rawa kasa dauke idanunta tayi akanshi wadan da tuni sun rikice suna qoqarin zubar da hawaye cikin wani irin salo na yan shaye shaye taji yana kiran sunan "my princess kece rayuwata kece duniyata kinki bayyana min kanki saboda baki sona laifin me nayi miki ?yadda yayi maganar da sunan da yake ta faman kira ba qaramin rudar da mami yayi ba ,da sauri ta fito daga cikin dakin tana goge hawayen nadama da danasani sam sam bata ga laifinsa ko jin haushinsa ba domin itace sila jefa rayuwarsa cikin wannan halin ."

mutane masu mahimanci suna zaune acikin massalaci dake cikin estate din abdullahi auren Adam Tariq abdullahi aka fara daurawa tare da maryam abdulra'uf akan sadaki kankani bisa umarnin mami sannan aka daura na hisham Muhammad sani tare da nana hauwa'u tariq abdullahi  duk yadda hisham yake son yayi jarumta amman a karshe sai da kwalla ta zubo masa jin an daura aurensa da wata ba da nuzlarsa ba .wani irin bakinciki ne mara misaltuwa ya lullube zuciyar hisham hannunsa salim ya rike cikin cool voice yace "ka sausautawa kanka sannan ka sanya aranka daman can nuzla ba matarka bace ."

Ana gama daurin aure maroka suka fara shela acikin mutane hamdala mami tayi alokacin daakce mata an daura auren sai dai zuciyarta bata cikin jin dadi sannan bakinta bai daina  ambaton sunan Allah ba maryam kam fadawa tayi jikin aunty khadija tana fashewa da kuka mai karfi "aunty khadija ta soma rarrashinta kukan murna da kukan bakinciki maryam take bakincikinta yaya adam baya sonta na farinciki kuma burinta ya cika ta auri abun qaunarta ."hajiya zulfa'u ta kira salim cewar suzo da hisham bangaren hjy zulai suka shigo a tare da abokan ango hisham ko kallon inda nana hauwa'u take bai yi ba nan masu daukar hoto dake biye dasu suka shiga aikinsu anyi hotuna sosai ."

Da misalin karfe biyu na rana mami ta shiga dakin ATA tare da mrym yana kwnace adduoi ta dinga yi tana shafa masa a fuskarsa yayinda maryam ta qaraso ta kafeshi da ido tana kallonsa tana jin wutar sonshi na qaruwa acikin zuciyarta qoqarin mikewa yake nan mami ta kama masa ya tashi ta jingina masa pillow a bayansa kallonsu kawai ya tsaya yi kafin ya rufe idanunshi yana sauke ajiyar zuciya "adamcy nah yau ka zama cikakken mutun ina cikin farinciki an daura aurenka da maryam sannna ina cikin bakinciki irin halin daka jefa kanka ciki ta qarasa mgnr tana kuka ".

"meye kuma abun kuka bayan burinki ya cika ?ya fad'a yana goge mata hawaye "kukan murna da bakinciki ne , yau ina cikin farinciki da bakinciki ka taimaki rayuwar mahaifiyarka karka canza daga adamcy data sani ,rayuwa qaddara ce sannan kai muslim ne ka yarda da qaddara kayi farinciki da auren nan ka barwa allah komai "numfashi ya sauke baya jin zai yi wani farinciki da wannna auren maryam kam idanunta na kanshi har sai da taji sautin muryar mami ta doki dodon kunneta "maryam jeki hado masa tea ki kawo masa ta fice daga dakin."

Bayan fitarta da kyar mami tasa shi ya tashi ya shiga yayi brush da wanka sabbin kayansa ya saka lokacin da mami ke fesa masa turare maryam ta turo kofar dakin ta shigo mami ta karfi cup din hannunta da kanta ta dinga bashi a baki tana masa nasiha ita kam mrym duk hankalinta na kanshi sai faman kallonsa take shi kanshi mamakin irin kallon da take masa yayi wanda kallo ne mai dauke da tsantsar soyayya acikin lokaci kankani...."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
   MAR'ADAMS
   💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi  byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

       Page 30

Ahankali ya d'auke kwayar idanunshi zuwa wani bangaren dabam yana jan tsaki dan bazai iya cigaba da kallonta ba "me yasa sweetheart take masa haka ?tasan baya son ganin yarinyar atare dashi amman ita burinta bai wuce taga sun kasance a waje d'aya ba."

"dan Allah adamcy ka cire damuwar nan aranka ka kwantar min da hankali ahalin yanzu babu abinda nake buqata kamar natsuwarka da kwanciyar hankalinka ,duk duniya babu wanda zai so maka kwanciyar hankali da farinciki kamar ni mahaifiyar ka saboda nice nafi kowa sanin ciwonka ."

"daga ni har kai da duk wani mai qaunarka babu wanda zai so ka qarasa rayuwarka haka batare da ka ajiye iyali ba , sannan zamanka kai kad'ai illa ne ga rayuwarka, idan wasu sun yarda da kai akan baka aikata komai na sa'bo ,wasu bazasu yarda ba, wasu zasu d'aukeka a matsayin mai neman mata ne duba da irin tarin dukiyar da allah yayi maka ,dan haka kayi hakuri ka rungume wannan rayuwar domin itace qaddararka dan adam bai isa ya canzawa kanshi qaddararsa ba."

sosai ya fad'a cikin kogin tunani hankalinsa ya bar duniyar da yake wanda hakan ya bawa maryam damar cigaba da kallonsa son ranta tana jin tmkr ta fad'a jikinsa ta rungumeshi ta rarrashi kayanta ,jin saukar hannun mami jikinsa ya sanyashi dawowa cikin natsuwarsa ya d'ago kanshi ya zuba mata idanunshi dake cike da matsanancin damuwa ."

"Ina neman alfarmar a wajenka a karo na biyu  " wata irin razana yayi yayinda zuciyarsa ta soma bugawa da karfi kamar zai fasa qirjinsa domin bai san wace irin alfarma zata sake nema a wajensa ba ,bai ce mata komai ba ya cigaba da kallonta da tsumammun idanunshi yana mai allah allah yaji abinda zata fad'a."

"na gode maka da alfarmar da kayi min na farko na amincewa auren maryam da kayi alfarmar ta biyu ka taimakeni adamcy kayi min alkwarin bazaka sake kai kwalbar giya bakinka ba bare sigari " tayi maganar Kmr zata zubar da hawaye dan tuni kwayar idanunta sun canza kala ."

Wani naunayen ajiyar zuciya da numfashi ya sauke atare dan bai d'auka abinda zai fito daga bakinta ba kenan, ya d'auka zatayi masa magana ne akan tarewar yarinyar "kayi dan Allah dani amadadin giyar da zaka yita sha kana buguwa gara ka rike addua adamcy ,jikinsa yayi sanyi da jin maganarta ya risinar da kanshi kasa batare daya bude bakinsa ba a ransa yace "wannan rayuwarta ce ,ciwona ne ".

ta cigaba da kallonsa shi kuwa bai ce mata uffan ba dan baya son yayi mata aqawarin da bazai cika ba ,bugu da qari baya son a shiga rayuwarsa a barshi da damuwarsa kawai sannan abar shi ya sha giyarsa da sigarinsa son ransa domin a halin da yake ciki su kad'ai ne abinda suke rage masa rad'ad'in damuwarsa ."

Kallonsa maryam ta cigaba da yi ko kifta idanunta bata són yi akanshi "kallonsa kad'ai ya isa ya harzikawa mutun brain dinsa ,namijin duniya ne ko daga yanayinsa ,wani murmushin farinciki na samun nasara ya subuce mata "duk Kinsa da aureta gashi dai allah ya bata sa'a a karshe ta zama mallakinsa na har abada, domin tasan muddin mami na numfashi a doron duniya bazata barshi ya wulakantata ba bare akai ga maganar saki atsakaninsu zasu rayu tare har karshen numfashinsu dan haka zata  iyawarta da komai ta makallakesa har ma ta zama wani sashin na rayuwarsa ."

Duk da ba kulata yake ba bare kallota amman da kyar take iya control din kanta akanshi don kallonsa yana cikin abinda ke sata fita haiyacinta tama rasa a duniyar da take ,a duk lokacin da tayi saa ya kalleta kuwa hakan na matukar sata natsuwa ,ta lumshe idanunta acikin ranta tace "adamcy nah ni kad'ai ,komai naka yayi min ilarka dai baka son rainin da zafin zuciya uwa uba tsanar mutane na babu gaira babu dalili ."

Kamar ance ya d'ago kanshi dake risine yaga idanunta akanshi ,a zaunen da yake ransa ya fara 'baci ,zuciyarsa ta dinga tafarfasa sakamakon kallon da take masa na kurrulla irin kallon daya fi tsana arayuwarsa ,numfashi ya sauke ahankali tare da sake kau da kanshi muryarsa a tsarke ya kiran sunan da yake kiran mahaifiyarsa dashi "sweetheart !"ya'akayi adamcy nan? "ta amsa cike da tsananin kulawa "Kece wa yarinyar nan ta bar d'akin nan" a d'an firgice mami tace "wace yarinyar kuma ?"

Shiru yayi yana sake 'bata rai mami ta kalli gabadaya parlour'n babu kowa daga ita sai shi da maryam ne acikinsa "kenan dai maryam yake nufi ?"adamcy matarka ce fa ?"oh my god sweetheart ki kalli kiga irin kallon rainin hankalin da take min ." yayi mgnr a d'an tsawa ce mami ta waiga ta kalli maryam wacce tun soma maganarsa tayi saurin d'auke idanunta akanshi ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta ."

"Ba nasara akayi akaina ba ni naga damar amincewa aurenta dan naga sai wani kallon gani gani take min ,wallahi tun da wuri ki ja mata kunne kar taga an d'aura  min ita ta nemi ta dinga min kallon iskanci idan ma tana tunanin wani abu acikin ranta wallahi tayi maza ta cire  dan hakan ba abu ne mai sauki ba ."

"Da me zan ji ?aurenta da aka min dole ,ko da kallon iskanci da take min ? amman barni da zazzafar qaddarar data rufta min shekaru goma sha .." yayi shiru yana sauke zazzafan numfashi ,ya gyara zamansa tare da kai hannuwansa duka ya rufe fuskarsa dashi yana jin kamar yayi kuka kafin daga bisani ya cigaba da sakin bakaken maganganu masu zafi da ta'ba zuciya duk magiyar da mami take masa akan yyi shiru bai yi ba har sai daya samu natsuwa sannan ya saurara inda ya kwanta akan kujera ya juyar  da kanshi gefe yana sauke numfashi ."

mami ta kallesa na second biyar sannan ta juya ta kalli maryam dake tsaye gabadaya ta rasa me zata ce ."yayinda maryam Jiki a matukar sanyaye ta matsa daga kusa dasu tare da juya masu baya tana jin faduwar gaba mai tsananin , tsanarsa gareta yana matukar d'aga mata hankali sosai taji bacin rai ,taji kamar ta fice daga d'akin mummansa ganin yadda ya juya baya ko mami yaki kallo ."

mami ta qara matsowa kusa dashi tace "Adamcy ka daina zafafa kiyayyar matarka a gaban idanunta saboda ban fidda rai wata rana shakuwa mai qarfi na iya shiga tsakaninku ba dan haka ka dinga qoqarin dannewa ka barwa zuciyarka please " tana gama fadar haka ta mike tsaye ta qarasa inda maryam take tsaye tare da riko hannunta suka fito daga d'akin."

Suna fita mami ta soma qoqarin rarrashin maryam ,tayi saurin cewa mami "karki wani damu mami banji komai araina ba," idan da sabo na rigada na saba da halinsa fatana allah yasa aurenmu ya zame mana alkhairi arayuwarmu gabadaya."shiru tayi kafin ta cigaba da magana "mami ni dai ki qara tayamu da addua akan wacce kike mana duk da har yanzu yaya adam bai amince dani ba amman yau kawai naji wani sanyi da samun 'yanci a zuciyata ."

Murmushi mami tayi dan tun tuni ta fahimci wani abu akan maryam din hakan kuma yayi mata dadi domin ko babu komai zatayi hakuri da duk wani wulakanci d'anta cike da farinciki tace"na gode sosai maryam in sha allahu zan cigaba da yi maku addua allah yayiwa rayuwar aurenku albarka allah ya azurtaku da samun zuria masu albarka ko ni yau zuciyata ta rage nauyi duk da rayuwar da adamcy ya d'auko ya rage kashi sabain na farincikina amman duk da haka naji zuciyata ta rage nauyi saboda nayi imani ko bayan raina zaki kula da rayuwar dan'uwanki ."

"Maryam adamcy rayuwata ne Kiyi hakuri dashi , Kiyi hakuri da halinsa ki kular min dashi "in sha allahu mami zanyi iyakar qoqarina " na gode maryam allah yayi miki albarka "ameen na gode mami allah ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani "Ameen Ameen mryam shiyasa nake qara sonki akwai ki da hakuri dasanin yakamata ."suka cigaba da takawa ahankali suna magana har suka sauko qasa fuskarsu d'auke da murmushin farinciki ."

Bayan saukowar mami ta aika akira mata hisham dan tun safe yana bangaren baba babba tare dasu salim tana zaune a d'akinta yayi sallama sai data bashi izinin shigowa sannan ya turo kofar d'akin ya shiga kanshi a risine a kasa kallo d'aya zaka masa ka fahimci jikinsa a mace yake , hisham ya rusuna ya gaishe da mami cike da girmamawa ,ta amsa masa cike da kulawa tana nuna masa kan kujera amman yaki zama ya zauna akan daddumar daya gani a shimfide akan kafet."

"Hisham ya akaji da taro ?kamar bazai amsa ba amman ya kasa ko babu komai mami tana da kima gareshi bazai ta'ba yi mata banza ba,dan haka ya bude bakinsa da kyar yace "alhamdulillah mami ya naku ?to Alhamdulillah hisham allah yayi maku albarka gabadayanku, allah kuma ya baku ikon cinye jarabawa rayuwar, kowani bawa rayuwarsa tattare take tafiya da jarabawa iri iri ."

"Kayi hakuri akan sauyin daka samu ka dauki hakan a matsayin jarabawa da kuma qaddara, auren auta yana daga cikin qaddararka wanda baka isa ka goge faruwar hakan ba ,abinda nake son ka fahimta Idan allah bai nufeka da samun wani abu arayuwarka ba sai ka gode masa domin allah sonka yake kuma duk abinda allah ya qaddara shi zaka samu, abinda allah bai qaddara zaka sameshi ba duk yadda abun ya kusantoka at end of the day bazaka sameshi ba duk kuwa son da kake yiwa abun ."

"Wannan kuma duk hukuncin ubangaji ne , idan da yau mun sanya hakan acikin zukantamu da zamuyi rayuwa cikin jin dadi cikin annashuwa batare da wata damuwa ba ,idan mun samu allah ne ,idan mun rasa allah ne" wama tasha una illa anyasha allahu rabbul alameen duk yadda kaso idan allah bai so ba bazai ta'ba yuwa ba ."

"wannan hukunci ne na allah ,allah yasa hakan shine mafi alkairi wata killan ma idan ka samu auren nuzla arayuwarka ta zame maka maseefa da tashin hankalin da sai kayi nadama ,ta zama bala'i arayuwarka yanzu rashinta sai ya zame maka alkhairi arayuwarka kayi hakuri da sauyin da allah yayi maka da sannu zaka ga irin sakayya da allah zai maka domin duk wanda ya yarda da allah allah zai isar masa ."

"idan kuma akwai alkhairi a tsakaninka da nuzla sai kaga anan gaba ka qara daita wannan duk kadan ne daga hukuncin ubangiji fatanmu allah ya zaba mana abinda yafi zama alkhairi arayuwarmu kar allah ya barmu da zabinmu "duk wannan maganar da mami take kanshi na kasa ya kasa d'ago kanshi har sai data dasa aya ta hanyar saka masa albarka sannan ya d'ago yayi mata godiya ya mike a natse ya fice daga gidan gabadaya."

Karfe biyar daidai motoci guda goma na alfarma sukai parking a kofar gidan mami domin d'aukar nana hauwa ,mutanen da suka zo gabadaya sun kasance kawaye ne ga hajiya zulfa'u ,kowacce cikin shiga ta alfarma domin kallo daya zaka masu ka fahimci kudi ya zauna ajikinsu shigar kowace tana wane na wane , sai dai mami tace hisham take son yazo ya d'auke amaryarsa da kanshi lokacin da sakon ya samesa yaji abun wani iri ranshi ya 'baci matuqa ."

"duk kawayen mumynsa da abokansa da suka tafi d'aukota basuyi ba sai shi da kanshi yaje kamar wata zinariya ?yayi wa kanshi tmbyr yana jan tsaki bana jin zan iya zuwa dan nasan nauyi kawai mami take són d'aura min ya lalubo wayarsa yana qoqarin kashewa kiran mami ya shigo "ya salam !"ya furta a fili yana mai dafe kanshi kiranta né yayita shigowa har sai daya d'auka ,yana d'auka tace "hisham d'ana kazo ka d'auki matarka " babu yadda ya iya dole ya amsa da "tô mami ganinan zuwa"ransa a matukar 'bace ya tashi ya shirya cikin wani d'anyen voyal fari sol ya shiga d'akin hjy zulfa'u ya fad'a mata inda zashi sannan ya fito ya kamo hanyar zuwa abdullahi estate."

zaune nana hauwa'u take agaban mahaifiyarta sanye da fararen kaya tun daga kan takalmi mayafi pos din dake rike a hannunta agogo komai na jikinta fari ne sol jikinta lullube cikin mayafi , shape din fuskarta kawai ake iya gani ,wani irin qamshin jikinta Ke fitarwa mai sanyin dadi da sanya natsuwa tare da kwantar da hanakali yayinda yan'uwata mata ke zaune akan kujera kowace cikin shiga iri d'aya ."

nasiha mai matukar ratsa jiki mami take mata tana tunatar daita hakin daya rataya a wuyanta cike da gamsuwa nana hauwa take gyada mata kai tana zubar da hawaye adaidai lokacin ATA ya shigo d'akin sakamakon kiransa da mami tayi bai qarasa inda suke ba ya samu waje ya tsaya ya jingina bayansa da bango d'akin ya rungume hannuwansa duka a qirjinsa yana kallon nana hauwa'u dake zubar da hawaye yayinda aunty shahida ta mike daga mazauninta tana  faman rarrashinta tana goge mata hawaye ."

Ahankali hisham ya turo kofar dakin ya shigo ya tsaya yana jin wani iri a gabadaya ilahirin ajikinsa kafafuwansa sukai masa nauyi ya kalli inda ATA yake tsaye rabonshi da ganinsa yau tsawon kwana uku kenan ,numfashi ya sauke yana qoqarin danne abinda yaji yana taso masa kafin ahankali aunty shahida ta qaraso inda yake ta riko hannunsa ta zaunar dashi kusa da nana hauwa'u agaban mami ."

"hisham ga amanar nana hauwa'u nan na danqata a hannunka ba dan ina tunanin zaka cutar daita yasa na damka maka amanarta ba sai dan yanayin rayuwa da kuma yadda aurenku ya kasance, aure ne da babu wanda yayi tsamanin faruwarsa amman dake haka allah ya qaddara babu tsimi babu dabara sai ya kasance ,kema nana hauwa'u ga amanar hisham d'ana na damka miki, kisan mahimanci amana ko ban gaya miki ba aure amana ce atsakanin ma'aurata kuma duk wanda yaci amanar dan'uwansa allah bazai barshi ba."

" na tabbatar d'ana hisham bashi da matsala idan naga wata matsala daga gurin ne zaki  kuma ki kuka da kanki dan bazan ta'ba d'aga miki kafa ba ko baki uzuri ba dan haka ki kiyaye "aunty shahida dake durkushe kusa dasu tace "hisham ga amanar auta nan allah ya tayaka riko "aunty khadija da zabiba ma dai abinda suka fad'a kenan "shi dai ya shiga ukunsa yanzu mumynsa ta gama damka masa amanarta kafin ya fito tana jadda masa ko rama taga nana hauwa'u tayi sai ya hadu da mummunar fushinta ,yanzu kuma ga mami dasu aunty shahida shi ya suke son yayi da rayuwarsa ?" shifa baya jin zai iya rike wata amana amman babu yadda ya iya muryarsa a sanyaye yace "in sha allahu mami zan kiyaye allah ya qara girma ya qara lafiya" Ameen Ameen hisham allah yayi maku albarka ."

Banda kuka babu abinda nana hauwa'u Ke faman yi wanda hakan Ke sake d'aga hankalin ata kwata kwata irin wannan rayuwar bata burgeshi zaa akai mutun gidan miji amman yana kuka irin haka kamar zaa kai shi kabari ,a tunaninsa wannan zalinci ne sam bai kamata a had'a irin wannan auren ba gara idan nmj ke so komai na zuwa da sauki canza rayuwar mace ba abu bane mai wahala ga d'a nmj amamn canza raayin nmj abune mai bala'i wahala ahankali yaga an mikar da nana hauwa'u tsaye shima hisham ya mike suka jero."

Kamar ance nana hauwa'u ta d'aga kanta idanunta ya sauka akanshi tsaye cike da sanyin jiki ta soma tahowa zuwa inda yake tsaye yana ganin haka ya kau da kanshi gefe yana sauke numfashi har suka qaraso inda yake bai waigo ba ,nana hauwa'u ta kasa wucesa kowa yayi mata fatan alkhairi tare da damka amanarta a hannun hisham amman banda shi tasan halinsa shirunsa yana nufin abubuwa dayawa a gareta dan haka ahankali ta dawo ta duka agabansa tana masa sallama sautin kukanta na tashi."

jikinsa yayi sanyi gayayyun idanunshi ya ware akanta still tana durkushe tana kuka yayinda tafin hannunta ke kife a saman kafarsa wani abu ya had'iye mai d'aci daya tsaya masa a makoshi bai ta'ba sanin cewar yana qaunar qaramar kanwarsa ba sai da aka samu wannan canjin ,babu yadda zai yi daita né domin itace da kanta ta  amince, da tursasata akayi sai dai ayi bala'i da zaayi amman bazai yarda ba ,kukanta ya dinga ta'ba zuciyarsa bai san lokacin da ya kira sunanta ba "nana hauwa'u!"

Kanta ta d'ago wanda ke cike da ruwan hawaye ta zubawa yayanta tattausan murmushi ya sakar mata kafin ya mika mata hannunsa alamar ta kama ta mike tsaye ,da wani irin sauri ta kama hannunsa tana ganin kamar a mafarki yake mata murmushi "ina mafarkine ko kuwa ? tayi maganar a fili tana kuka " menene auta ?murmushinka yaya wannan shine karo na farko danaga irin wannan murmushin akan fuskarka" ya qarasa mikar daita tsaye ya kwantar daita akafad'arsa yana shafa bayanta " kiyi hakuri kukan ya isa haka auta "lafewa tayi sosai ajikinsa Kmr wata baby "yaya ka yafe min ban bi umarninka ba "karki damu dani ki kula da kanki ".

shi kuwa hisham zuba masu ido yayi yana jin wani zallar 'bacin rai na ratsashi "ki daina kuka auta idan kinga da matsala ki kirani babu wani uzuri da zanwa hisham shima kuma yasan halina bazai yi any thing nonsense ba "wani irin kallo hisham din yayi masa kamar yace masa "me zai yi idan aka samu matsalar sai ya duba idanun mutane dake wajen mami bazata ji dadi ba hka sauran yanuwata da suke da kima a idanunshi ,sannna idan ya fad'a haka mumynsa bazata d'aga masa kafa ba idan taji labari ."

ATA ya kamo hannunta ya saka acikin na hisham ya damke waje d'aya "ga amanar auta please ka kular min daita fiyye da yadda zaka kula da kanka" shiru hisham yayi masa yaki cewa komai, Jiki babu kwari suka fice daga d'akin, aunty shahida da aunty Khadeeyja da zabiba na biye dasu suna qarasowa parlour'n hisham ya zare hannunsa cikin nata yayi gaba shiru tayi kawai tana duban bayansa kawayen hajiya zulfa'u mutun uku da suka tsaya suka mike tsaye maryam ta qaraso ta rungume nana hauwa'u tana cewa "shikenan sister zaki tafi ki barni" ta qarasa mgnr tana fashewa da kuka "ai baku rabu ba mrym tunda duk mazajenku 'yan gidan nan ne ,kusan kullum suna nan inji cewar hjy nurriya."

Da kyar aka 'bam'bare maryam ajikin nana hauwa'u hjy sumayya ta riko hannunta suka fito zuwa haraban gidan ta bud'e mata bayan mota ta shiga ta zauna ta rufe murfin ,yayinda hisham ke qoqarin qarasawa wajen abokansa hjy summaya ta kwalla masa kira ya dawo ya tsaya gabanta "shiga"mumy kuje kawai daita zan biyoku "aa hisham ba'a yin haka shiga kawai sai wani daga cikin abokanka yajaku "kai !"ya furta a fili sannan ya shiga ya zauna ko kallon inda take bai yi ba ."

Su biyu ne zaune abayan motar sai salim a mazaunin direba hawaye yaki tsayawa a idanun nana hauwa'u,wani sabon kuka ne ya kufce mata sanda suka fito daga estate dinsu suka hau titi ,gefe tayi da kanta tana damke hannuwanta cikin juna "salim kasan wani abu ?salim dake tuki yace "aa sai ka fada "wai ATA ke bani amana" salim naji haka ya manna ipod a kunnensa ya cigaba da tuki "aikin banza sai kace shi ya iya rike amanar' yar wasu da yake son shi a rike masa amanar kanwa, mutun sai shegen son kan tsiya sai kazo kasani dole na rike maka amana."

kunnuwan nana hauwa'u ya jiyo mata maganarsa acan kasan makoshi kamar ta juyo inda yake sai kuma ta fasa ta cigaba da kallon titi ya sake motsa bakinsa kmar zai yi magan sai kuma yayi shiru ya ciro wayarsa dake ringing yanayin yadda ya amsa ta fahimci yaya amar ne "kaga amar dan allah ku barni da damuwata kowa amana amana !! wai me kuke nufi  dani ne ?" me yasa bakuje kuncewa ATA ya rike amanar maryma ba sai ni zaku dameni da wata amana saboda kun rainani ?"dan girman allah ku barni na huta naji da damuwata no no!! bazan fa gane ba wayar salim ce ta d'auki qara ya danna iPod din dake makale da kunneshi yana cewa "okay mumy an gama har ya gama wayar musayar magana hisham yake akarshe dai ya kashe yana furta aikin banza kawai ."

Tafiyar mintuna ta kawosu ikeja gra atare suka qaraso gbdynsu har abokan ango sanda salim yayi parking a haraban gidan hajiya sumayya tayi parking a haraban gidan, hisham ne ya fara fitowa yayi gaba ,jiki a matukar sanyaye nana hauwa'u ta fito hjy sumayya ta qarasa da sauri ta riko hannunta cikin nata suka biyo hisham abaya cikin natsuwa har zuwa bakin kofar shiga parlour'n hajiya zulfa'u tana zaune cikin kawayenta ."

wata kawarta marry wacce ta kasance yoroba ta mike da sauri hannunta rike da cup wanda Ke cike da ruwa ta tsaida nana hauwa'u abakin kofar shigowa ta zuba mata ruwan akafafunta tana cewa "barkanki da shigowa gidan d'ana yadda kika shigo cikin koshin lafiya haka zaki qare rayuwarki cikin koshin lafiya ,gidan nan bazai miki zafi ajiki ba ,gidan nan zai zame miki tamkar ruwan sanyi ne yadda muka ga wannan ranar allah ya nuna mana sabuwar shekara munzo suna haka akarshe ta rungumeta ajikinta ."

ta shigo daita parlour'n kai tsaye marry gaban hajiya zulfa'u ta nufa da nana hauwa'u ta duka a gabanta hjy zulfa'u ta kai hannunta ta d'agota ta zaunar daita a gefenta kamar yadda hisham ke zaune abokansa gbdy suka shigo nasiha tayi masu mai ratsa jiki abokan ango na jiran abasu amarya su wuce daita gidanta mumy tace su wuce sai tayi sati anan gabadaya sukai mata sallama suka kama gabansu ahankali ta riko hannun nana hauwa'u ta nufi dakin dake kusa da nata suna shiga ta zaunar daita a bakin gado tare da cewa" ina zuwa ."!bata jima ba ta dawo hannunta rike da cup ta mika mata "ki shanye!" babu mutsu ta karba wani abu ta gani kamar zuba ta kafa kanta ta shanye tana yatsina fuska "akwai d'aci né ?"ba sosai ba "!ta bata amsa da hakan "okay  bari akawo miki abinci nasan da wahala idan kinci wani abu ta juya ta fita ."

Ahankali ATA ya juya zai bar d'akin mami aunty shahida da aunty khadija suka dawo d'akin "yauwa a she ma ya nan mu koma magana zamuyi da kai "bai ce masu uffan ba ya koma ya tsaya tare da tura duka hannuwansa acikin aljihun wondonsa ,aunty khadija da aunty shahida suka zuba masa ido suna tunanin ta inda zasu fara masa magana ahankali ya lumshe tsumammun idanunshi na second biyu sannan ya budesu fes akansu tare da tsura masu ido alamun yana sauraronsu " .

"adam !"
aunty shahida ta kira sunansa bai amsa ba illa tsura mata idanunshi da yayi "me yasa ka zabi ka 'bata rayuwarka akan auren nan ?giya fa adam meye hadinka da shan giya saboda allah ? kai babu wanda ya isa da kai kana ganin mahaifiyarmu zata zaba maka abinda zai zame maka matsala né arayuwarka?mami kullum só take taga cigabanmu amman kai da yake mara mutunci né kullum qoqarin kake ka 'ba.""dan allah malama ya isa haka nasan da wannan nasan tana son cigabanmu amman me zanyi  da wuce hkn?yayi shiru yana fesar da iska zata zauna yace  "meye next dan ina son naje na  huta ya katseta ta hanyar fad'ar haka numfashi ta sauke kawai  batayi mamakin abinda ya fad'a ba dan tasan halinsa zai iya ma fadar abinda yafi haka ."

Aunty khadija tace "dan allah adam karka qara shan gi..."nifa bazan daina shan giya ba kawai ku barni da rayuwata tunda ni kad'ai damuwarta ta shafa abarni da damuwata kawai ,fuskarsa a daure ya cigaba da magana "wai me yasa kuke manta wani bazai iya ji da ciwon wani ba ?"wannan ciwona ne ni kad'ai abarni kawai naji da ciwona yana gama fadar haka ya juya a fusace ya bar d'akin yana fesar da numfashi."mami ta girgiza kai Kawai cike da taikaci take masa addua.

A parlour'n mami na biyu suka kusan cin karo da maryam da sauri taja baya gabanta yayi wani irin mummunar faduwa sannan ta d'ago ta saci kallonsa adaidai lokacin daya d'ago idanunshi suka tsarke cikin nata wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki wanda babu tantama na tsoro da qaunar da take masa ne , wani irin mugun kallo yayi mata mai firgitarwa sannan yaja tsaki yana furta" nonsense"! a fili ya wuceta jiki a sanyaye tabi bayansa da kallo "ya rabbi me zanwa wannan bawa naka ya soni ?rashin qaunarsa gareni yana damuna ya allah ka nuna min hanyar da zanbi ya soni ."

Kai tsaye samansa ya hau ranar yau din ata jinsa yake dabam ,jinsa yake kamar an sauyashi daga adam din daya san kanshi zuwa wani adam din dabam ,wani irin bakinciki ke ratsa shi wanda ga duk wanda yasan shi yasan aininhin zahirin fuskarshi zai ga alamun komai ya qara sauyawa agaresa, domin sauyawar yafi na da muni fuskar nan tashi sam babu rahma attare daita ta dawo tamkr ta kumurcin macijin ."

Har karfe bakwai sauran wasu mintuna nana hauwa'u na zaune a bakin gado ta zabga tagumi sosai tayi shiru tayi zurfi cikin tunani jefa jefa tana zubar da ruwan hawaye da kallon kular abincin daaka kawo mata da ko bud'esa batayi ba ,tun baaje koina ba ta fara kewar gida wani irin ta dinga ji a ilahirin ajikinta tasan adaidai wannan lokacin da take cikin kad'aici da auren soyayya tayi da dole tasan mijinta yana kusa daita yana rarrashinta bazai barta ta kasance ita kad'ai ba ,amman da yake bai sonta ya bawa banza ajiyarta yayi zamansa a parlour'n ."karfe bakwai da minti goma ta mike tsaye ta shiga bathroom din dake manne da d'akin ta dauro alwala ta fito ta gabatar da sallar magrib tayi adduointa ta sake komawa ta zauan kamar yadda take a d'azu tana cigaba da zubar da hawaye ."

hajiya zulfa'u ta turo kofar dakin ta shigo bakinta dauke da sallama yyinda hannunta ke rike da wani cup ba irin na d'azu ba,nana hauwa'u tayi saurin goge hawayenta ta bud'e baki da kyar ta amsa mata sallamar da tayi "har yanzu kina nan a zaune diyata ?"ki rage kayan jikinki mana ki sha iska."nana hauwa'u tayi murmushi kawai d'an bata da wannan kwarin gwiwar bare ta samu karfin zuciyarta aikata haka , burinta a yanzu bai wuce taga yaya hisham ya saki fuskarsa kamar yadda yake mata ada kafin ta zama mata agaresa ba ."

tana buqatar sakin fuskarsa ko kadan ne daga garesa ,ahankali ta zare mayafin jikinta ta ajiye cike da jin kunyar hjy zulfa'u,cup din hannunta ta miko mata tana cewa "ungo ki shaye "a natse tasanya hannuta ta karba cike da girmamawa ta kafa kai ta shanye tana yatsina fuska dan kamar irin na d'azu ne kawai kalarsu ne ba iri daya ba ta mika mata cup tana cewa "na gode mumy allah ya qara girma "dan ko bata fad'a mata ba ta fahimci irin maganin da take bata "karki qara yi min godiya dan na baki abu ni fa mahaifiya ce agareki ,ki saki jikinki dani kinji ki cin abinci dana sa akawo miki ?tayi shiru tana tunanin amsar da zata bata kafin tayi mgn har hjy zulfa'u ta qarasa ta bud'e kula abincin yana nan Kmr yadda aka kawo mata "ya baki ci abinci ba ?ki cire komai aranki kice abinci kinji "nana hauwa ta gyad'a mata kai alamun taji " idan kinyi wanka ga kaya can ki canza "tana gm fad'ar hk ta juya ta fice daga dakin ."
 

Wani abinci hjy zulfa'u tasa aka sake kawo mata wace ta kawo abinci na fita ta dawo dakin wanda kafin ta fita a dakin sai data lallabata dan dole ta fara cin abinci bata wani ci daywa ba ta mike ta shiga bathroom tayi wanka da alwala ta fito ta sauya kaya tayi sallah ishai byn ta idar ta kwanta a gefen gado tana kukan , ita kanta kukan ya isheta haka amman da zarar ta tuna yanayin yaya hisham sai kukan ya sake dawo mata ."

hisham daya shigo dakin yaja tsaki karo na farko da yaji ya tsani kukan da take duk da yasanta tun tashinta yasan yadda mami take ji daita ya santa da saurin kuka but ba irin haka ba ,tasan bata són shi me yasa ta amince aka daura masu aure ?dan yasan itama raahin sonahi né yake sata kuka, lalle ko akwai aiki dan wannan na cikin dalilin da zai sa yaji ya qara tsanarta shi kuka idan bana nuzla bane ai aikin banza né a wajensa ,nuzla itace macen da zai iya jurar komai nata tasoshi ko karta só shi he does care wannan alqawarinsa ne ko a wani hali take zai jure matukar akanta ne saboda yana matukar sonta bai zauna ba ya juya ya fice daga dakin daman mumynsa ce ta tursasa masa shigowa ."

******

Da misalin karfe goma na dare ranar lahadi maryama na zaune a d'akinta akan kujerar roba tana zane domin yanzu yana cikin abinda ya fara rage mata damuwa da ta zame mata jiki ,yusif kuwa tuni ta fidda shi aranta da dawowarsa da rashinsa duk daya ne a wajenta ,shi kuwa baba gali tun sanda yayi mata maganar sauyi akan yusif taji duk duniya babu wanda ta tsana kamar shi hatta gaisuwar da take shiga bangaresa ta gaishesa ta daina zuwa ,ko ganinsa tayi a waje gaisuwar sama sama take masa tunda ta rigada ta tabbatarwa kanta baya qaunarta ,ta kuma tabbatarwa kanta baba gali makiyinta ne da keda fuska biyu har ma gara aunty salma dashi ita daman can bata ta'ba nuna tana qaunarsu ba, amman shi baba gali wani lokaci yana nuna yana sonsu ,akan ya'yansa  ne ma wani lokaci suke fuskantar tsana shi kuma wannan daman ta ajiyesa a matsayin uban wani da ya'yan wani akwai bambamci ."

Ta numfasa sannan ta dakata da abinda take tare da tura bakin pencil a bakinta tana tunani "life goes on maryama karki qara yarda ko amincewa wani d'a nmj arayuwarki da sunan soyayya, ba lalle sai da aure zaki yi rayuwa ba ,ko da aure ko babu zaki rayu dan haka ki natsu ki qara kwantar da hankalinki ki qare bautar kasa ki samu aiki mai kyau wanda zaki kula da kaninki da mahaifiyarki ki ajiye wani batu na aure dan muddin aunty salma aunty hassana baba gali da sauran yanuwan mahaifinki  na raye bazasu bari kiyi aure ba "na karbi qaddarata allah ka bani ikon cin jarabawa sanyayyen numfashi ta sauke ta cigaba da abinda take."

Washegari ya kama monday tun da asuba ta tashi tayi sallah bata koma ba ta shiga ayyukanta data saba ,bayan ta gama tayi wanka tayi shirin na fita aiki ta fito parlour'n alokacin  bakwai da wasu yan mintuna , ta isa inda ta hango mahaifiyarta zaune tana jiran fitowarta ta zauna kusa daita tana gaisheta "aunty ina kwana ?kin tashi lafiya sarauniyata?alhamdullai qaunata ,aunty ta tura mata kofin koko da kosai gabanta ahankali ta soma sha i har ta kammala ta dauki kofi da faranti data ci kosai ta kai shi kitchen zata wanke aunty tace "barshi ki kama hanya ki wuce lokaci ya fara tafiya tayi mata sallama ta fito ta shiga side din umma suka gaisa sama sama tayi mata addua ta fito ."

Abakin kofar fita gidan taga baba gali zaune yana sauraron radio ta gaishesa cikin murya mai jin nauyinta ya amsa ta cigaba da tafiya ta jiyo sautin muryarsa yana kiranta ta juyo tare da amsawa ta nufi inda yake zaune yana sauraron radio ta durkusa ta sake gaishesa akaro na biyu ya kalleta sosai sai daya jinjina kai sannan yace "maryama saboda na yanke miki hukunci da abinda yafi dacewa dake shine kike nuna halin damuwa saboda bani na haifeki ba ?".

Ta kallesa kawai saboda ita bata san abinda tayi da zai nuna baiyyanar da damuwarta ba maganar bashi ya haifeta ba ai kowa yasan wannan domin da shi ya haifeta bazai mata bakinciki ba amman sai ta kawar da wannan tace "baba ni ba fushi nike da hukuncinka ba sannan banga abinda zai sakani damuwa ba saboda nayi imani rabona bazai taba wuce ni ba matukar yusif mijina ne babu tsumi babu dabara zai aureni idan kuma ba mijina bane nawa mijin zai zo shi kuma ya auri matarsa bare ma ni tuni na manta da babinsa yanzu kai ya kamata kasan abinda zaka fadawa mahaifinsa akan alkwarin da kayi masa ."ya dan gyara zama "wani alkawarin?

Tayi shirin domin bazata iya fad'a ba tunda shine yayi alkwarin tuna masa din me zatayi ?duk abinda kike nufi maryama ba abinda zai kawo dakushewar soyayyarki da alhj alqasim abinda ya sanar dake na tabbatar dani ya fara zance amman idan kika duba kunyar mahaifin mlm yahuza babban mutun ne acikin unguwar nan ba qaramin kuskure nayi ba wajen saurin amincewa buqatar alhj alqasim daya zo daita tsakanin ke da sauran yammatan gidan nan kinga shi mlm yahuza Ke yagani yace yana so dan haka Ke din ce wacce yake so ba shukura ba daace zai karbi shukura amadadinki dana bashi ita Ke kuma kin auri yusif ."

Shi kuma nasan alhj alqasim zai karbi shukura ko sakina adalilin rashinki tun da daman shi zuria gidan nan yake bukata dan haka ki natsu ki kwantar da hankalinki wannan ba wata matsala bace tunda ni zan tunkaresa da maganar komai ta sunkuyar da kanta kawai tana jinsa tana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta ita yanzu bata jin mlm yahuza acikin ranta tunda tagansa da shukura har abada babu ita babu shi ko mutuwa zaiyi akanta wallahi bazata auresa ba sannan wannan magana ce kawai baba gali yake batun soyayya tsakanin mlm yahuza da shukura sunyi kawai dai anje an warware aiki ne komai dake faruwa da sanin aunty salma ita Ke shirya komai ."

Sarai baba gali ya karanceta dan hk muryar a fusace ya cigaba da mgn "tunda naga kamar kin kamu da soyayyar yusin din allah ya baku zaman lafiya da yusif ita kuma shukura ko sakina allah ya kawo masu nasu rabon "uhm kawai ta furta dan tasan ya fad'a haka ne ba har acikin ranshi ba ,ta dago ta girgiza kai cikin takaici irin rayuwarsu "ni baba bana ja da maganarka a yau ida ka shirya aura da kowacce daga cikinsu ga yusif kayi ." ya sauke ajiyar zuciya yana cewa tô shikenan na gode na tabbatar daman bazaki aikata abinda zai jawo min zagi ba su yusif din zasu zo karshen satin nan dan mun gama magana da mahaifinsa cewar shukura zai aura shima yusif din ya amince da hakan dan haka ko yau mlm yahuza ya kiraki ki amshesa kije ."

Nan taji gabanta ya fadi jin wai abba ya amince da kuma amincewar yusif daman yusif ba soyayyar gsky yake mata ba tabbas duk maza mayaudara ne babu nmj dan goyo kalamansu daya haka salon yausararsu daya haka ta mike tsaye jiki babu kwari ga lokacinta daya bata mata ga bakinciki daya kunsa mata abun yayi mata yawa ,bakinta na rawa tace "baba Allah ya tabbatar da alkhairi sai dai ka fadawa mlm yahuza ya nemi matarsa a gaba dan ni a halin yanzu gbdy babu mgnr aure a gabana bazan yi aure ba har karshen rayuwata tana gama fadar haka ta soma daga kafafunta bayanta yabi da kallo yana kwabe baki alamun matsalarta."

Yau sunyi very busy a wajen aiki dan daga maakatarsu kwasasur akayi zuwa ma'aikatan man petir  dake apapa saboda kwarewar wasu daga cikinsu ranar haka tayi aiki cikin sanyin jiki da wahala ita ba soyayyar yusif bace damuwarta tunda daman bata fara son shi ba mamakin baba gali ne ya addabeta tmbyr duniya subai'a tayi mata tace babu komai ."bayan an tashi daga aiki ta fito bakin get ta tsaya tana jiran fitowar subai'a su wuce gida ,ta tura hannunta cikin jakarta zata ciro nikaf dinta adaidai lokacin wata mota reven rover ta sanyo kai zata shiga cikin ma'aikatan ,gani tayi motar taja ta tsaya motar bata shiga ciki ba haka zalika bata juya ba mutumin dake zaune a bayan motar taga ya fito jikinsa sanye da suit bakake."

da wani irin sauri ta dan matsa gefe ,shi kuwa fuskarta yake kallo daga inda yake tsaye cike da faduwar gaba tabbas wannan fuskar idan ba mafarki yake ba fuskar da mai gidansa yake gani ce acikin duniyar mafarkinsa ."duk da fuskar zane ce  ,amman ya rantse da wanda ke busa masa numfashi itace wace zuciyar mai gidansa take muradi kasancewa tare daita, gbdy idanunwansa sun rufe akanta baya ganin tarin jama'ar dake gurin burinsa ya isa gareta tana qoqarin sanya nikaf taji ya rike mata hannu jikinsa na wani irin kirrrma kafin tayi wani abu taga ya janyo hannunta da sauri zuwa cikin ma'aikatan qoqarin fixge hannunta take cikin tsananin tashin hankali amman yaki sakar mata hannu ."

Ana zan dataka sai a book 2 in sha allahu wadan da suke bibiyarmu a arewabooks inshaallahu zasu cigaba da ganin update dinmu kmar yadd muka saba ."
Alhamdulillah

Mmn sudais

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.