Maradams Book 1 Complete Hausa Novel
Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt
Chapter 11 of 18
Page 11
" har tsawon wannan lokacin yana tsaye yana mata kallon kaskanci kafin daga bisani ya d'an motsa labbansa " biyayya Kawai zan yiwa mahaifiyata na aureki sai dai zakiji jiki sai kinyi da kin sanin kalmarki gareni, zakin san kin ta'boni yana gama fad'ar haka ya d'auke kafarsa tare da shure mata kafa ya nufi cikin part din mahaifiyarsa ransa a dagule .
girgiza kai mryam ta shiga yi kafin daga baya ta rarrafa ta shige parlour'nsu ta ra'be a bakin kofar d'akin tana kukan zuci , cikin yanayi na tashin hankali take furta "me na tsare maka ya adam ? "me yasa baka sona ? "me yasa ka tsaneni hk ? haka tayita jerowa kanta tambayoyin da bata da mai bata amsa sai shi shi din kuma bata isa ta tuknkaresa ba gbdy Idanunta sun canza qala tsabar tashin hankalin data tsinci kanta ."
kuka take son yi sai dai zafin da zuciyarta ke yi yasa hawayenta yaki diga sai idanuwanta gbdy sun burkice " baka sona amman ya zama dole na jurewa komai muddin ina son rabuwa da iyayena lafiya , bazata manta kalman mahaifinta ba alokacin da zata dawo daga abuja domin sun samu kyakkyawan mazauni acikin kwalkwaluwarta "maryam muddin ni ne wanda nayi sanadiyyar zuwanki duniya Kuma kina son gamawa da duniya lafiya ki auri adam bisa umarnina Kuma ki zauna dashi zama na amana bisa umarnina , yau ace ba yar'uwata ce ta nemi wannan hadin ba sam bazan takura miki ba zan barki har sanda zaki kawo min irin mijin da kike so .."
A bakin gado ya iske hjy zulaiheart ta cika tayi bam ,cikin sanyi jikin nan nashi ya k'araso ya zauna a gabanta yana neman gafararta , ko kallon Inda yake bata yi ba daga karshe ma ta kawar da fuskarta gefe al'amun bata son ganinsa ya runtse idanuwanshi sosai yana sauke numfashi ,byn kmr second biyar ya bud'e idanunshi ya fara Kame kame "uhm ammm kiyi hakuri sweetheart , afuwa sweetheart I will not do it again , inshallahu I promise you zan aureta ."
"hjy zulaiheart taji dadin jin furucinsa har cikin ranta sai dai ta share tana jan tsaki a fili. "ki yarda sweetheart duk duniya babu wanda zai soki da son farincikinki kmr ni ,kiyi hakuri bazan juri ganin 'bacin ranki ba ya fad'a yana riko hannunta , naunayen ajiyar zuciya ta sauke batare data fuskancesa ba ,duk da zuciyarta ta d'an yi sanyi dan daman fushin na dole ne yanxu kuwa ta hakura .
damuwarta daman yayi aure tana son taga aurensa taga ya'yansa kamar yadda taga na sauran yaranta amman duk da haka bazata sakar masa fuska ba dan tasan halinsa kamar yunwar cikinta canzawarsa bai da wuya ya d'auki mintuna masu tsawo agabanta bata daga Kai ta kallesa ba sai ma ta mike zata bar masa d'akin , ya mike da sauri jikinsa na kyarma ya tareta dan sosai ya hango damuwa qarara akan fuskarta ya sake kamo hannuwanta duka cikin nashi , ta fizge a fusace tana watsa masa harara "sweetheart kiyi hakuri dan girman Allah wallahi zan aureta trust Adamcy zai aureta tunda yace zaiyi wallahi wallahi zan aureta Koda kuwa zan rasa rayuwata....."
hannunta d'aya tasa ta zare hannunta daga cikin nashi ta tsura masa idanunta "wallahi ban san Inda ka d'auko halinka ba , sam mahaifinka ba haka yake ba mutumin kirki ne, mahaifinka baya uhm baya uhm bare miskilanci , kullum cikin neman yadda zai kyautata mana daku ya'yansa da 'yan'uwansa yake , a kullum mahaifinku so yake ku zama na gari a rayuwa sannan masu jin kan iyaye da tausayi Allah ya duba bayan mahaifinku cikin kaf ya'yan mahaifinka Kai ne kawai ka fita dabam acikinsu da wasu halaiya Kai ma Kuma wannan halin miskilancin da zafin zuciyar ne illarka tun kafin ya rasu ya fad'a yace bashi ka d'auko ba .bari na fad'a maka gsky wannan halin naka sam ba nashi bane Kai ka san Inda ka samo abunka dan shi ba haka yake yi ba, dan ta mahaifinka duniya bazai tashi ba ,ga rikon addinin ga tsananin zumunci da sanyi hali ."
ga lokaci yazo daya kamata ka tattara biyayyar Uba da uwa ka had'a kayi min amman kullum cikin musguna min kake akan zance aure auren da kai ne kaji dadinsa , wallahi duk macen data samu miji irin mai halin mahaifinka ta gama dace a duniya da lahira ni kaina kullum kukan da nake yi kenan mahaifinka ya bauta mana ya sangartani sannan ya bautawa zumunci Allah ya jikansa yasa aljanna ce makomarsa ka canja idan zaka canza tana gama fad'ar haka ta fita ta barshi cike da zafin zuciya."
Jiki a sanyaye ya bar d'akin zuwa nashi yana shiga d'akinsa ya shiga zariya kwalkwaluwarsa ta shiga tunani , sai dai Kansa ya toshe ya cunkushe guri d'aya ya kasa tunanin komai ya zauna a bakin gado ya had'e hannunwansa duka a ha'barsa yana tunanin can byn wasu mintuna ya mike ya koma kan bedside ya zauna yayi shiru yana kallon d'akin ,sake mikewa yayi ya d'aura Kashi akan katifa yana Jin quna a ransa.
zuciyarsa na dokawa da matsanacin karfin gaske ya tashi ya nufi falonsa ya bud'e fridge ya d'auki kwalin stute superior cranberry me sanyi ya d'auki glass cup ya d'aura drink akan center table ya juya jiki a mace ya koma zuwa d'akinsa ya d'auko kwalin sigari rotimax ya dawo ya koma kan kujera ya zauna ya tsiyaya ruwan lemun ya d'aura kafafuwansa akan table tare da hard'esu guri d'aya ya Kai Karan sigari bakinsa ya kunna ya fara zuka a hankali yana fitar da hayaki "yaushe rabonsa da sha ? sam bazai tuna yaushe rabonsa dasha ba cike da izza itama sigarin yake zuka idan ba an fad'a maka ba bazaka ta'ba sanin shi din mashayin shigari bane koda yake baya sha sai idan ya tsinci Kansa cikin ' bacin rai mai tsanani " .
yayi shiru yana zuka sigari yana tunani mahaifinsa yasan da yana raye duk runtsi da hkn bata faru dashi ba , shiyasa yake son mahaifinsa Sosai wasu hawaye masu zafi suka zubo masa wanda rabonsa daya zubar da hawaye har ya manta a tsawon rayuwarsa amman yau ya tuna qalbinsa masoyinsa , ana cewa mutun yafi son mahaifiyarsa akan mahaifinsa shi dai sai dai
sonsu yazo d'aya a ransa , yasan soyayyarsu suyi kanka da juna ,mahaifinsa ya soshi har cikin ransa idan yana cikin damuwa sai ya fishi shiga damuwa , haka idan yana cikin farinciki ,daf da zai rasu da zarar ya kyalesa sai ya fashe da kuka alokacin hjy zulaiheart ke tmbyrsa dalilin kuka sai yace "ba kowa nake wa kuka ba sai Adam ,Ina jin tausayin rayuwar Adam bashi da dan'uwa kamar sauran mutane naso sun kasance su biyu ya samu abokin shawara "a she tabbas shi din abun tausayi ne bai ta'ba sani ba sai a tsakanin wannan lokacin da abubuwa suka kwa'be masa yan'uwansa mata sun had'e kai da mahaifiyarsa yasan da yana da dan'uwa nmj zai iya bin bayansa Koda kuwa zaa fi karfinsa ne hawaye ke gangaro masa kamar karamin yaro yana cigaba da busawa cikinsa hayaki ."
ranar a zaune ya kwana cikin tsananin tashin hankali Kash da Kashi damuwar auren dole da za'a masa da tunanin Nurul qalbinsa dan da zarar ya runtse idanuwanshi dan bacci sai yaga hoton princess dinsa tana gargadinsa akan auren da zai yi tana gudu tana binsa tana furta kar yayi aure ya barta .tsawon sati guda tunda daya amince da batun auren mryam bai sake zuwa Inda mami take ba yana d'akinsa yaki barin ya had'u da kowa dan gbdy fita ya fita ransa gbdy soyayyar princess ya dawo masa sabo fil ganin tunanin bazai bar kanshi ba yasashi mikewa daga kwance da yake tare da zura takalmi silifas ya fito ya shiga d'akin zanensa ya tsaya a gaban hotonta shiru yana kallonta kmr yayi mata mgn ta amsa fuskarta d'auke da murmushin da shine ya zanata ."
Hannu ya kai ya ja hoton a zuciye ya yaga yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa"A ina kike tsawon shekaru ?"a Ina zan ganki ?"kin hanani ganinki,kin hanani sukuni daga yau kin zamo tarihi gareni bazan sake damuwa dake ba ,bazan sake tunaninki ba zan manta dake arayuwata ,zan cire soyayyarki a zuciyata tunda baki da imani baki da tausayi ya fad'a yana wani irin ihu tare da daga hannuwansa duka sama "haaaaaaaa!!!
"Hauka yake sosai yana wargaza komai dake cikin d'akin tare da cigaba da yaga hotunan zanenta yana filinging dasu har da system dinsa da tsarkar wuyansa wanda zanen hotonta ne aciki , gbdy ya hargitsa d'akin yana watsi da komai har sanda mahaifiyarsa ta shigo hannunta rike da cup wanda yake d'auke da ruwan coffee, bedroom dinsa ta shiga bata gansa ba dan ita kanta ta kasa jurewa rashinsa na tsawon kwanaki , ganin baya ciki ta fito har zata fita ta jiyo sautinsa a hargitse dan haka ta shigo d'akin ."
ta tsay a bayansa ta cigaba da kallonsa cikin tsananin tashin hankali mara misaltuwa bai sani ba yayi zurfi cikin tsananin damuwa cikin haka ya sake d'aukar hoton zanen princess yay sama dashi sai akan fuskar hjy zulaiheart ta runtse idanunta da sauri jikinta na rawa kamar ance ya juyo ya ganta tsaye tana kallonsa cikin tsananin tashin hankali sanye da doguwar rigar shadda milk colour mai dogon hannu kyam idanunta a kanshi ta kasa daukewa ."
cikin sauri dunkule hannunsa ya naushi iska tare da durkushewa kasa ya soma tattara kayan daya hargitsa yana cewa "so..sorry sweetheart am really sorry cikin in Ina, numfashi ta sauke da ajiyar zuciya sannan ta zauna a bakin gado batare da ta ajiye cup din hannunta ba sai dai har lokacin idanunta na Kansa tana jin ciwo da zafin halin da yake ciki ,kusan minti biyar tana zaune tana kallonsa yana faman tattara d'akin yana mata sannu sannan ta fara magana a tsanake ." kayi hakuri Adamcy karka damu da wannan"
ya k'arasa kwashe kayan da yayi waste dasu zuciyarsa na zafi da quna "kana jina Adamcy ita rayuwa babu takurawa idan baka sameta anan ba wata Killa zaka sameta a aljanna ,yakamata ka gane hakan , karka shiga rud'ani idan an fad'a maka gasky illa ka dinga yarda dashi , komai na duniya babu sauki kmr yadda ka d'aukeshi sai an jajirce be a man Adamcy karka lalata rayuwarka akan yarinyar mafarkinka ."
"kamar yadda na sha fad'a maka ba kowani mafarki ke zama gaskiya ba , ta mike a hankali ta k'araso gurinsa ta riko hannunsa tayi taku biyu ta zaunar dashi akan kujera kwaya d'aya dake d'akin , madadin ta bashi coffee din hannunta sai ta fita gabanta na dokawa da matsanacin karfi dan nan duniya idan akwai abinda ta tsana to bai wuce damuwar tilon d'anta ba , sam bata son ganinsa cikin damuwa ko wannan auren ma zata yi masa ne dan dole saboda tasan muddin batayi masa ba zai iya kare rayuwarsa haka batare da yayi ba ."
ko cikakken minti biyar batayi ba ta dawo da gorar ruwa mai sanyi ta mika masa , babu mutsu ya kar'ba ya kafa a bakinsa bai cire ba sai daya shanye tasssss sannan ajiye yana sauke numfashi taja hannunsa zuwa bedroom dinsa yana biye daita yana zance zuci .ya yarda tabbas mahaifiyarsa na sonshi kuma gsky take fad'a masa akan yarinyar mafarkinsa sai dai ya rasa dalilin da har wannan lokacin ya kasa yarda iya mafarki ne kawai soyayyarsa zata tsaya ..."
Tana shiga d'akinsa ta zauna akan gado ya kwanta ya d'aura kanshi akan cinyarta yana mai Jin damuwarsa tana raguwa , a hankali ta Kai hannunta saman sumar kanshi ta fara shafawa tana mai sake jin tsananin son d'anta Ina ma zata ga wannan yarinyar a zahiri da babu abinda zai hana bata mallaka masa ita ta kowani hali ba ."
ta dade zaune har bacci yayi awon gaba dashi Sannan ta d'auke kanshi ta maida kan pillow ta lullu'be masa rabin jiki ta sauko ta qara masa karfin ac ta kashe masa wuta ta duka tayi kissing din foring head dinsa tana sake shafa sumarsa sannan ta nufi kofar fita tana rufo masa kofar ."
Koda ta koma d'akinta kasa runtsawa tayi tana tsaye akan ka'fafunta tana Kai wa Allah kukanta akan lamarin tilon d'anta sai da tayi sallah asuba sannan ta d'an kwanta Shima bata wani dade ba ta farka ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin doguwar riga ta sanya awarwaro da zobin ziniri ta feshe ilahirin jikinta da turaren humura mai sanyi kamshi hjy zulaiheart kenna Allah yayita da son kwaliyya da son kamshi tun tana matashiyarta har zuwa wannan lokacin da tsufa yazo mata ta fito zuwa babban parlour'nta tare da danna bell din bangaren masu aiki kafin kace me gbdy sun hallara sun zube a gabanta suna gaisheta cike da girmamawa. ta dubesu tare da amsawa cikin tsananin farinciki dan tana da sakewa da masu aikinta bata zalintarsu sannan bata son su zalinceta yadda take jin dadin zama dasu haka suma suke yabonta da yi mata fatan alkhairi a rayuwarta .
Fuskarta a sake ta bawa 'yan aikinta umarni abinda take bukata su dafa a ranar wanda zai zamo na sadaka ne kasancewarsa juma'a "yau za'a yi abincin sadakan da aka saba yi amman ina son a qara hannu sannan a had'a da wake da shinkafa Ina son a rabawa yara kanana suka amsa da "to" sannan kowace ta soma k'okarin mikewa "ke tabawa ..." wacce aka kira da tabawa ta tsaya sauran suka kama gabansu dan fara aiwatar da aiki "ki shirya breakfast wa sauran jamar gida idan kin gama ki hanzarta sanar dani ."
"shikenan hajiya itama ta fad'a tare da juyawa da sauri ." Hjy zulaiheart tana zaune mrym da nana hauwa'u suka shigo duk suka zauna suka sanyata a tsakiya kowacce hannunta empty babu Komai kamar Koda yaushe sun baro wayoyinsu na gado a d'akinsu d'aya byn daya suka gaisheta ta amsa cike da sakin fuska a fili tace "yau dai babu danne danne waya ko Kuma an gaji da rike wayar ne ?
sukayi murmushi nana hauwa'u tace " ai tun wuri nayiwa marsi kashedi muddin yaya adam zata aura ta saukakawa kanta akan shiga yanar gizo "wannan haka ne domin zai iya kawo rashin jituwa a tsakaninsu abinda bazan so faruwarsa ba kenan nafi bukatarta zaman lfy atsakaninsu.
ta Kalli bangaren da nana hauwa'u take zaune tace " ya batun shari'a da ake da yarinyar da ake zargi ta kashe mubina ne har yanzu na kasa fahimtar gskyr magana gashi Adamcy nata k'okarin shiga cikin maganar uncle jay ya hana ?"ai gsky gara da uncle jay ya hana wani shari'a za'a yi mami Abar ko waye da Allah kawai mubina dai ta rigada ta mutu bazata dawo ba komai za'ayi ,haka Allah ya qaddaro mata nata mutuwar zata rataya a wuyan wani inshallahu ruhinta na aljanna suka had'a baki gurin cewa" Ameen "
" mrym tashi ki shiga ki d'auko min wayata a daki na kira naji yadda ake ciki ta mike tsam ta shiga cikin bedroom din hajiya zulaiheart ta iske wayar akan katifarta ta d'auka tana duba fuskar wayar nan take gabanta yayi wani mummunar fad'uwa sakamakon idanunta daya sauka akan hoton ATA tayi shiru tana kallonsa cikin suit bakake idanunshi manne da farin glass yayinda fuskarsa ke d'auke da murmushin gefen baki wanda bai gama bayyana ba hakan km qara masa kyau yake , ta lumshe idanunta tana Jin wani iri a gbdy ilahirin jikinta ,ada sam bata jinsa aranta amman tun sanda yasa akayi kiranta akan batun soyayyarsa ta soma Jin wani Abu akansa komai nashi mai kyau tamkar shi ya hallici kansa ."
jiki a sanyaye ta Kai mata wayar ta amsa tana kokarin neman layin uncle jay byn sun gaisa take tmbyrsa halin da'ake ciki "mgn dai daya ce nace abarwa Allah abar ruhin diyata ya samu salama ".
"uncle jay taya zaka fadi haka byn kasan zuciyar sha'awanatu bazataji dadi ba ? "nasani amman yarinyar nan da ake tuhunma ba itace tayi kisan ba , tabbas makashin mutun d'aya ne da wanda ya kashe mubina da wanda ya kashe sadear mutun d'aya ne amman ba wannan yarinyar bace, ita dai ta taka tsawun barawo ne gbdy bincike ya nuna makashin da hannun hagu yayi kisan ita Kuma hadiza hannun dama take amfani dashi sam gbdy babu alamun sheidar hannunta ,yanzu haka an gama duk wani bincike ranar monday kotu zata wanke yarinyar Allah dai ya jikan mubina yasa ta huta "Ameen Hjy zulaiheart ta furta a fili tana mai tausaya masa "ko me suka yiwa wannan makashi da yake musu kisan gilla? "Allah masani "sun dan jima suna waya sannan sukayi sallama .
"Maryam ...!" mami ta kira sunanta gbdy ta tattara duk wani attention dinta zuwa gareta tana kallonta "Ina saka rai zuwa karshen satin nan za'a yi mgnr bikinku da Adamcy " gabanta ne ya sake fad'uwa kmr zai fasa qirjinta yayo waje "ya kamata ki sake kwarewa agurin girki da sauran abubuwan da yake da bukata dan haka daga yau kice zaki cigaba da kulawa da komai na bangaren abincinsa kinji ko ".
ta gyada mata Kai kawai tare da amsawa da "to !" hawaye na ciccikowa acikin kwarnin idanunta tayi saurin dennewa ta rasa dalilin da take tsananin Jin tsoronsa da tsoro aurensa."
" ki samu natsuwar zuciya ki tashi kije yanzu ki tmbayesa abinda yake bukatar ci a hankali ta mike jikinta na rawa kamar mazari ta nufi part dinsa
akan hanyarta ta tsaya tana daidaita natsuwarta sannan ta k'arasa kofar shiga falonsa tayi sallama ba'a amsa ba har ta juya taji sautin muryarsa yana cewa ",waye ne ? ta juyo da sauri "ni ...nice ta fad'a da sauri jikinta da bakinta na rawa "ke wa kenan ? ya sake tmby tayi shiru jikinta na cigaba da rawa hawaye na sake cikowa a idanunta ta rasa dalilin hawayen nata Jin shiru yasa ya taso da kyar yana mika daga shi sai gajeren wando army green iya cinyarsa da farar singlet wanda suka bayyana surar jikinsa a fili ake iya ganin kwantaccen sumar dake kwance a cinyarsa da qirjinsa haka kan nipples dinsa sai farin silifas dake sanye da kafafunsa da farin agogo da alamun aiki yake ."
A tsaye ya ganta a bakin kofar gbdy bata cikin haiyacinta a hankali ta d'ago ta kare masa kallo saboda kusancin da suka samu muryarsa a kasalance yace "ke lafiyarki tsayuwar me kike yi anan ya fad'a fuskarsa a murtuke"kayi hakuri please mami ce tace nazo na tambayeka abinda zaka ci a girka maka " ya tsuru mata Ido a zahiri yake iya hango yadda qirjinta ke bugawa wani dogon tsaki yaja a fili ya juya ya koma ciki ya barta tsaye . juyawa tayi tana daga kafafuwanta da kyar ta dawo parlour'n ta tsaya hjy zulaiheart ta dubeta "yaakayi me yace zai ci ?hannuwanta ta tsarke cikin juna sannan ta bud'e baki da kyar "wai a dafa masa komai."
mami ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi , ita Kuwa nana hauwa'u sarai ta fahimci wani abu a tattare da marsi tasan sarai ba abinda yace mata kenan ba "to shikenan maza ki shiga ki dafa masa abinda yazo cikin tunaninki amman ki natsu sosai kinji. "ta gyada mata tana cewa "sister muje ki tayani "me .....?dan girman Allah ki rufa min asiri na tsira da mutuncina ke dai kije Allah ya bada sa'a kiyi kokari yayi dadi sosai ta k'arasa maganar tana kakkabe hannunta. "haba sister ki taimaka mana kin san fa komai tare mukeyi ,nasani amman ban da wannan wallahi bazan Saka hannu ba abinci yazo bai yi dadi ba ya had'amu yaci ubanmu" hjy zulaiheart tayi murmushi "Kai Adamcy hukuma kowa tsoronsa yake ji amman Kuma fa yana da sauki Kai Kinga mryam yi tafiyarki kinji duk abinda baki gane ba kizo ki tambayeni Simi Simi ta juya ta shiga kitchen kmr ta daura hannunta tayita kuka dan tasan muddin tayi kuskure sai yaci ubanta duk iya k'okarinta na dafa masa rice and stew bai ci ba ya wuce juma'a ."
*****
Da misalin karfe biyu na rana bayan an sauko daga massalaci hajiya zulaiheart da kanta ta fito zuwa haraban gidan ta fara rabawa yaran dake shigowa haraban estate din sadaka wake da shimfa acikin takeaway fari tare naira dari biyar biyar sababbin yayinda ATA ke tsaye daga can nesa kadan da inda take kunnensa manne da waya yana tafiya a hankali irin na jinin saurarata dan sauranta yaki barin jininsa komai nashi irin nasu ne sanye yake cikin farin yadi voil kafafunsa sanye da takalmi fari haka ma Kansa sanye da hula fari mai ratsin baki yayinda tsintsiyar hannunsa ke d'aure da agogon silver rolex yayi kyau sosai kamar ka sacesa ka gudu sai dai kallo d'aya zaka masa kasan zuciyarsa dakushe take da tsananin damuwa ."
tsayawa yayi cak yana cigaba da kallon mahaifiyarsa cikin haka ta juyo nan take suka had'a Ido daita ya sakar mata taadaddaden murmushinsa dake sake bayyanar da ainihin bawar kyawun da Allah yayi masa wanda wannan murmushin babu mai ganinsa sai ita , murmushi
ta sakar masa cike da farinciki ganin murmushinsa da ba kowa yake gani ba tana tsananin son kyakkyawan tilon d'anta shi din dabam ne acikin zuciyarta ,uwa Uba nagarta tana masa so mai tafiyar da ruhi shine karfin gwiwarta ."
a hankali ya soma takowa zuwa Inda take har ya k'araso gareta ya tsaya kusa daita yana tayata rabawa yaran kudi duk wanda ta bawa takeway sai ya mika masa kudi ,tana raba abinci tana dubansa tana murmushin jin dadi "thank you my beloving prince " you're welcome my queen ya fad'a yana kallonta bayan sun gama tare suka koma ciki suna tautaunawa a falonta sukayi masauki ya zauna yana runtse idanuwanshi."Adamcy nah...." !
ya amsa can kasan makoshi" inshallahu wannan satin zanyiwa su baba babba maganar aurenku ayi a wuce gurin muryarsa a raunane yace "to sweetheart kuyi duk abinda ya dace na sallama miki komai ."
"bangane ka sallama min komai ba kana nufin bazaka tabuka komai ba ?"me kike son nayi sweetheart idan akwai abinda kike bukatar nayi ki sanar min zanyi ganin idan ya cigaba da biye mata maganar auren zasuyitayi yasa yay saurin runtse idanuwanshi yana cewa "wayyohhhly sweetheart cikin kwantar da murya tace "ya'akayi Adamcy ? "sweetheart yunwa nake ji cikina har ya fara zafi murmushi tayi "ko kunya baka ji ba kmr wani jinjiri ka dai rage wannan shagwabar ka bar wa yaranka "a'a sweetheart ki barni nayiwa uwata suma idan sunzo ga guri nan kowa yayiwa mamansa "to ai shikenan bari nasa maryam ta samarmaka abinda zakaci "wace mrym kuma dan Allah kiyi min da kanki karki rage min Jin dadi wannan yarinyar babu abinda ta iya Kuma ma nafi son Ina cin abinci daga hannunki ni dai gsky banason abincinta "ya Isa sarkin naci amman dole kaci daga hannun matar da zaka aura wata rana ."
"naji amman ayi sauri ayi min please dariya ya bata sosai wai ayi sauri ayi mishi ATA kenan ko yaushe idan yana tare da mahaifiyarsa daukar kanshi yake kamar karamin yaro hjy zulaiheart ta d'auki wayarta ta soma Neman layin maryam sai dai bai shiga ba ta ajiye wayar tana Kiran daya daga cikin masu aiki ."
Tana zaune a d'akinsu hjy zulaiheart ta Aiko mai aiki akirata da hanzarinta ta Isa parlour'n tace "kije ki kawowa Adamcy wani Abu yaci yunwa yake ji ta Dan saci kallon Inda yake tana Jin mummunar fad'uwa gaba sannan ta gaishesa sai dai bai Kalli Inda take ba bare ya amsa gaisuwarta ,Kai tsaye kitchen ta nufa sai dai ta rasa me zata dafa masa shap shap yaci ,kawai tayi tunanin daura masa indomi da kwai ta kawo masa a lokacin data fito bata tarar da hjy zulaiheart ba sai aunty khadeja zaune agurin suna magana da ATA ta ajiye akan table din dake gabansa tare da gaishe da aunty khadeja kamshin indomin da yaji ya ziyarci hancinsa ya balain ta'ba zuciyarsa na take ransa ya baci .
a hankali ta juya zata wuce dan Sam bata jurar tsayuwa a duk Inda yake muryarsa a kasalance yace"ke meye wannan kika kawo ? ta dawo a hankali ta tsaya tare da cewa "indomi da ......"a fusace ya dan gyara zamansa ya tsaidaita "shine abinda kika iya dafawa? jikinta na rawa ta dubi aunty khadeja dake zaune tana juya masa Kai "nace shine abinda kika iya dafawa ?ta girgiza masa kai jikinta na rawa gbdy a tsorace take a tsaye,shi kuwa kallonta kawai yake da seyx eye's dinsa wanda hakan yasa hantar cikinta cigaba da kadawa lumshe idanunshi yayi tare da yin shiru ya koma ya jingina jikinsa da kujerar da yake zaune ya soma motsa labbansa "wai irin wannan matar ake min sha'awar ajiyewa a gidana ?yayi mgnr a fili yana sake jan tsaki a fili "wacce irin sakariya mata ce wannan khadeja saboda rashin tarbiya indomi fa me zanyi da ita ?
"tuni idanunta suka kawo kwalla bakinta na rawa tace " kayi hakuri bari naje na sake dafa maka wani abu bude idanunshi yayi fesss akanta Yana cewa "shut up me yasa baki dafa ba tun farko ? ya karasa maganar yana buga mata wata hadaddiyar tsawa nan take jikinta ya kama rawa da hannu aunty khadeja tayi mata alamar ta wuce kmr jira take tayi gaba da sauri tana haki ."
"kayi hakuri adamcy da sannu zata iya komai "har sai yaushe khadeja ? nifa akan wannan matsalar zamu tabbata muna samun matsala daita bazan juri zama da macen da bata iya komai ba?" shekara ashirin da biyar da wani abu amman ace mace bata iya girka komai ba sai yaushe ? "gsky gsky ni dai an ....... " sai Kuma yayi shiru ya kasa cigaba da mgn "yanzu dai kayi hakuri me zaka ci ni sai na shiga na girka maka da kaina a fusace yace "barshi kawai juyin duniya yaki yace bai ci haka ta hakura ta barshi ."tsaki ya dinga ja bai san me ma ya jashi cewar zai ci abinci ba mikewa yayi ya bar gidan gbdy Aunty khadija tabi da kallo gsky akwai kuskure atattare da maryam dan rashin iya girki babban matsala ne a gidan miji ba wai shekara ashirin da biyar da yan kai ba a tunaninta maryam zata kai talatin dan tsirarau da auta babu yawa .."
******
Maryama na zaune da yammacin ranar monday tana wanke kayan Aunty salma da kayan kanwarta sakina wacce ta kasance diya ga Aunty salma duk da lokacin makarantar islamiyya ne amman ita bata samu damar zuwa ba saboda aikin da matar yayan mahaifinta ta sata , wanke take da iyakar karfinta har ya zamo bata iya wankewa da karfinta sakamakon gajiyar data tsarketa domin ta jima batayi irin wannan aikin ba tun karfe biyu lokacin data taso daga makarantar boko gashi har yanzu biyar ta wuce sallace kawai ta tasheta daga tsugunno datayi tana faman dikar wanki ."
Sakina ta shigo cikin haraban gidan da sallama babu sukuni a fuskarta dan kallo daya tayi mata ta fahimci haka ganin halin data ganta yasa ta sake shiga cikin damuwa ta matso kusa daita ta tsaya cikin bacin rai " maryama daman wanki kika tsaya shine dalilin da yasa baki zo makaranta ba yau .?"
ta fad'a ranta a bace tana kallon cikin falon Aunty salma."
da kyar maryama ta kirkiro murmushin dole wanda yafi kuka ciwo dan komai ya wuce a zuciyarta dan bata qaunar sa'insar sakina da mahaifiyarta akanta muryarta a sake tace "kayan makarantar nawa ne basu bushe ba shine nace Aunty salma ta kawo wankinta na wanke da naki dan zaman bazai min dadi ba tunda bazan samu zuwa makaranta ba ta fad'a mata haka cikin zaro wani kaya daga cikin tarin kayan dake ajiye a gefe guda tana qoqarin dannashi cikin ruwan wanki sakina ta fixge cikin fushi tana cewa "wallahi karya ne nafa san halin mama itace ta hadaki da wannan aikin aikin daya yafi karfin ace mutun daya ne zai yi ni ban san me yasa mama take yin haka ba ..."
Aunty salma ta fito daga cikin dakinta sakamakon jin maganar diyarta "sakinata har kin dawo sannu da dawowa sakinata ta fad'a tana qarasowa ta dafa kafadarta cike da kulawa da tsantsar soyayya sakina ta zumburo baki "haba mama yanzu abinda kikayi ya dace dan meye zaki lodawa maryama uban wanki haka alhalin kina sane da cewa ko mu duka muka hadu bazai qare acikin kwana biyu ba haba ni wallahi wallahi bana só abinda kikeyi wa yaruwata sautari umma tana sanar dake illar haka karfa ki manta maryama ba baiwa bace a gidan nan ' ya ce kamar kowani d'a acikin gidan nan ko bakya kaunarta ita da mahaifiyarta bai kamata ace kina daukar abubuwan wahala kina sakata ba tunda ko babu komai yaruwata ce ko dan ni ya kamata kina son maryama saboda ina sonta ina qaunarta in har soyayyar da kike min ta gskiya ce ."
Aunty salma ta kwabe baki "sannu sarkin yan iyayi ta fad'a a zuciyarta amman a zahiri cewa tayi "meye acikin dan wannan aikin yanzu dan na saka maryama dan wannan aikin zai sa Kiyi zargin bana sonta ne ko wani abu ? tô idan baki sani ba bari na fad'a miki ina mata kwadayin samun lada ne shiyasa nake sakata aiki yanzu Ke kin san irin ladan da zata samu har idan ta gama min ."?
"To ni me yasa baki sani ba tunda aikin lada ne in har idan kwadayin lada Kike mata ?" Ki dinga hadawa dani daita gsky ni banaso ." maryama na durkushe hawaye suna son zubo mata daga cikin kwarnin idanunta amman ta dannesu dan kawai bata son sakina ta fuskanci damuwarta dan tasan dole sai ta qarawa yiwa mahaifiyarta bori ita km abinda bata só kenan taga suna samun sabani akanta da mahaifiyarta domin ita kam tarasa gane maanar hakan rashin kunya ce ko gaskiya take fadawa mahaifiyarta da ta kasance damuwa atattare daita da tata mahaifiyar "
"shikenan sakina daga yau na daina Kiyi hakuri ina sata ne dan tafiki kuzari yanzu muje kici abinci ai kuwa sakina taki binta "wani irin muje naci abinci ki dai zo mu hadu har dake mu qarasa wanke sauran kayan Aunty salma tabi wanki da maryama ta wanke sama da rabi ta waigo ta dubi sakina "a'a ki bari ta qarasa tunda sauran ka.." A'a wallahi ki tsaya dai mu qarasa tas ita ba mutun bace tun rana take ta faman aiki kamar wata inji."
Aunty salma tayi shiru tana duban yarta ta ja tsaki ta nufi hanyar dakinta tana cewa "ai sai dai idan ke zaki iya ni dai babu abinda zanyi taka nas naje na arota wajen uwarta shine dan tsabar iyayi irin naki zaki ce ga zance ga magana da yanzu Ke na saka bazakiyi ba dan yanzu kinga na saka maryama shine zaki zo da shegen iyayi shikenan ki tayata ku qarasa tare ta wuce tana bala'i maryama na tsaye batare da tace uhm ba bare uhm uhm dan bata son tayi laifi dan a yanzu ma tana hankalce da Aunty salma harararta take sakina ta gyara botiki ta cire hijab dinta ta sunkuya ta tura mayafinta da maryama Ke qoqarin turawa cikin ruwan wanki ta fara wankewa da sabulu data tsinta acikin ruwa ."
"Why sakina ? mai haka ki barni na qarasa mana bana son naga kina sai sa da mahaifiyarki akaina ki daina babu kyau tunda kinga ni bana yiwa Aunty haka "itama ai abinda take miki babu kyau ko dan ba itace ta haifeki ba kullum sai ta dinga zuwa tana aroki dan taga Aunty shiru shiru bata son magana aikin yau da dabam na gobe dabam ta hanaki zuwa makaranta malam mustaphata sau uku yana shigowa tambyarki nace bakizo ba kina gida bakya jin dadi "ai ba ita kadai Ke sakani aiki ba umma ma ina yi mata "eh kina yiwa umma amman ita tasan daidai dan bazata barki kina aiki har wannan lokacin bakije islamiyya ba kar ma ki hada mama da umma dan ba abu daya bane ."
maryama tayi shiru Tare da sunkuyar da kanta kasa tabbas akwai bambamci tana son aikin umma fiyye dana kowa ko babu komai tana qaunar mahaifiyarta kum tana tausayawa rayuwarsu tun kafin mahaifinsu ya bar duniya ta kalli sakina tana son hanata wanki amman tasan bazata yarda ba kawai ta cigaba da kallonta ita yanzu abinda yafi damunta yunwa take ji sosai domin Aunty salma bata bata ko ruwa ba wai sai ta gama sallah ma da kyar tayi ."
Sakina ta cire hannunta ta shiga kitchen ta dauko plet din abinci ta fito ta daura mata akan cinyarta "kici !ta tsurawa abincin ido tana kallona batasani ba itama sakina ita take kallo ta matsota da sauri tana son sani abinda yasa tayi shiru bata fara cin abinci ba maryama tayi tsuru itama haka ta kalli abinci ta kalli maryama "ko abinci yayi kadan ne?ta fad'a girgiza kai maryama tayi "ya ma yi min yawa "to me yasa kikayi shiru kina tunani ?" Kai sakina kina son damun kanki akaina ta fad'a tana soma cin abinci jikinta babu kwari ga rawar da yake saboda yunwar da take ji maryama bata bar bangaren su sakina ba sai daf da magariba shima da taimakon sakina ne ."
A matukar gajiye ta shigo part dinsu ta zauna akan kujera jikinta tattare da tsananin gajiya Aunty ta qaraso ta tsaya akanta "ya naga duk kinyi wani iri ko kin aikin da yawa ne ? numfashi ta fesar tare da waskewa dan bata son nunawa mahaifiyar ta damuwarta domin duk hakurinta taji irin aikin datayi yau sai taji ciwo aranta dan haka ta dubi mahaifiyarta tace "babu komai ai aikin ma bashi da yawa kuma har munyi mun gama tare da sakina sai lokaci ta saki jikinta ta zauna kusa daita "sannu princess dina shiyasa nake qara jin sonki araina ta fad'a Tare da shafa kanta da yake sunan datake kiranta dashi kenan atare sukayi shiru Aunty na matukar tausaya mata ita da danuwanta habib kasancewar sun taso cikin maraicin uba gashi dangin ubansu ba qaunarsu suke ba idan aka cire mahaifiyar babansu da yayan babansu da matarsa to babu mutun daya da zata cire."
Mmm sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS
AYSHABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.