Best / Popular Hausa Novels

Maradams Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt

Chapter 11 of 18

Page 11

"  har tsawon wannan lokacin yana tsaye yana mata kallon kaskanci kafin daga bisani ya d'an motsa labbansa " biyayya   Kawai zan  yiwa  mahaifiyata na aureki   sai  dai  zakiji  jiki  sai   kinyi  da kin sanin  kalmarki  gareni,  zakin san kin  ta'boni   yana  gama   fad'ar   haka ya d'auke   kafarsa  tare da   shure   mata  kafa  ya nufi  cikin part  din  mahaifiyarsa ransa a dagule . 

girgiza  kai  mryam ta  shiga  yi  kafin  daga baya  ta  rarrafa  ta shige  parlour'nsu     ta  ra'be a bakin   kofar d'akin tana  kukan zuci , cikin   yanayi  na tashin   hankali  take  furta    "me  na  tsare maka  ya  adam  ? "me yasa   baka   sona  ? "me yasa   ka   tsaneni hk ? haka tayita  jerowa kanta   tambayoyin da bata da mai bata amsa  sai shi shi din kuma bata isa ta tuknkaresa ba   gbdy  Idanunta   sun canza qala tsabar tashin hankalin data tsinci kanta ."

kuka   take  son yi sai  dai   zafin da zuciyarta    ke yi  yasa  hawayenta yaki diga sai idanuwanta gbdy sun burkice    " baka sona   amman  ya zama   dole  na  jurewa  komai  muddin  ina  son rabuwa da iyayena   lafiya , bazata  manta kalman mahaifinta   ba alokacin da zata dawo daga  abuja   domin sun samu kyakkyawan  mazauni  acikin kwalkwaluwarta "maryam  muddin  ni  ne  wanda   nayi  sanadiyyar zuwanki  duniya  Kuma kina  son  gamawa da duniya  lafiya  ki auri adam  bisa umarnina Kuma ki zauna dashi  zama na amana bisa umarnina , yau ace ba yar'uwata ce  ta nemi wannan hadin ba sam bazan takura miki ba zan barki har sanda zaki kawo min irin mijin da kike so   .."

A  bakin  gado  ya iske hjy zulaiheart   ta  cika tayi bam   ,cikin   sanyi  jikin nan nashi  ya k'araso   ya  zauna  a gabanta   yana  neman gafararta  ,   ko  kallon Inda   yake   bata yi  ba daga   karshe  ma ta  kawar   da   fuskarta  gefe  al'amun  bata  son ganinsa   ya   runtse idanuwanshi  sosai yana sauke  numfashi ,byn  kmr  second biyar ya bud'e  idanunshi  ya fara  Kame  kame  "uhm ammm   kiyi hakuri   sweetheart   , afuwa sweetheart   I will not  do  it  again , inshallahu  I promise  you  zan aureta ."

"hjy zulaiheart taji  dadin jin    furucinsa     har  cikin   ranta  sai  dai ta share  tana  jan tsaki a fili. "ki yarda  sweetheart duk  duniya   babu  wanda  zai  soki  da son farincikinki   kmr ni  ,kiyi  hakuri  bazan  juri  ganin  'bacin   ranki ba   ya fad'a yana riko hannunta ,  naunayen ajiyar zuciya ta  sauke batare  data  fuskancesa ba  ,duk  da  zuciyarta ta d'an  yi sanyi  dan daman fushin na dole ne yanxu kuwa ta   hakura .

damuwarta  daman yayi   aure  tana  son  taga aurensa  taga  ya'yansa  kamar  yadda  taga na sauran  yaranta   amman  duk  da  haka  bazata sakar  masa fuska  ba dan tasan halinsa kamar yunwar cikinta canzawarsa  bai da wuya  ya  d'auki  mintuna masu tsawo  agabanta bata  daga  Kai ta  kallesa ba sai ma  ta mike zata  bar masa  d'akin , ya mike da sauri  jikinsa na kyarma  ya  tareta  dan sosai ya hango  damuwa qarara akan  fuskarta  ya sake kamo hannuwanta  duka cikin nashi  , ta  fizge  a fusace tana watsa masa harara   "sweetheart  kiyi hakuri  dan girman Allah  wallahi  zan  aureta  trust Adamcy  zai  aureta tunda  yace  zaiyi wallahi wallahi zan aureta Koda kuwa  zan rasa rayuwata....."

hannunta d'aya  tasa ta zare  hannunta daga cikin  nashi   ta tsura masa  idanunta  "wallahi  ban  san  Inda ka d'auko halinka  ba ,  sam mahaifinka   ba haka yake  ba  mutumin kirki  ne, mahaifinka baya  uhm  baya  uhm bare miskilanci ,  kullum cikin neman   yadda  zai kyautata  mana daku ya'yansa da  'yan'uwansa yake ,  a kullum mahaifinku  so  yake   ku  zama na gari a rayuwa  sannan  masu  jin  kan iyaye  da tausayi  Allah ya  duba  bayan mahaifinku  cikin kaf  ya'yan  mahaifinka   Kai ne  kawai  ka  fita dabam acikinsu  da wasu halaiya Kai ma  Kuma wannan  halin miskilancin da zafin zuciyar  ne  illarka tun kafin ya  rasu ya fad'a  yace bashi  ka d'auko ba .bari na  fad'a maka gsky  wannan halin naka sam ba  nashi  bane  Kai ka san  Inda ka samo  abunka dan shi ba haka yake yi  ba,  dan ta mahaifinka    duniya  bazai  tashi ba  ,ga rikon addinin  ga  tsananin zumunci da sanyi hali ."

ga lokaci   yazo daya kamata  ka tattara biyayyar  Uba  da  uwa ka had'a   kayi  min amman kullum cikin musguna min  kake akan zance aure  auren da kai ne kaji dadinsa ,  wallahi duk macen  data  samu  miji   irin mai  halin mahaifinka  ta gama dace  a duniya da lahira ni kaina  kullum kukan da nake  yi  kenan mahaifinka  ya bauta mana  ya sangartani   sannan ya bautawa  zumunci  Allah   ya  jikansa yasa aljanna ce makomarsa  ka canja  idan  zaka  canza tana gama  fad'ar  haka ta  fita ta barshi cike da zafin zuciya."

Jiki  a  sanyaye  ya bar d'akin  zuwa nashi  yana shiga   d'akinsa  ya shiga zariya   kwalkwaluwarsa ta  shiga tunani , sai dai  Kansa ya  toshe  ya  cunkushe guri d'aya  ya kasa tunanin  komai ya  zauna a bakin gado ya  had'e  hannunwansa duka  a  ha'barsa  yana  tunanin  can  byn wasu mintuna   ya  mike ya koma  kan  bedside ya zauna  yayi shiru yana kallon  d'akin  ,sake  mikewa  yayi  ya  d'aura Kashi  akan  katifa  yana Jin   quna a ransa.

zuciyarsa  na  dokawa  da matsanacin karfin  gaske ya  tashi ya nufi falonsa ya  bud'e  fridge  ya d'auki kwalin   stute superior cranberry   me sanyi ya d'auki  glass  cup ya d'aura  drink akan  center  table  ya  juya jiki a mace ya  koma  zuwa  d'akinsa ya  d'auko kwalin sigari  rotimax   ya  dawo    ya    koma  kan  kujera ya zauna  ya  tsiyaya ruwan lemun   ya d'aura kafafuwansa  akan table tare  da hard'esu guri d'aya  ya Kai  Karan sigari bakinsa  ya  kunna ya fara  zuka a hankali yana fitar  da  hayaki "yaushe rabonsa da sha ? sam bazai tuna yaushe rabonsa dasha ba  cike da izza itama sigarin yake zuka idan ba  an fad'a  maka ba bazaka  ta'ba  sanin  shi din mashayin    shigari  bane koda yake  baya sha  sai idan ya tsinci Kansa cikin ' bacin   rai mai tsanani  " .

yayi  shiru  yana zuka sigari  yana  tunani   mahaifinsa   yasan  da yana raye duk runtsi  da hkn  bata faru  dashi ba , shiyasa yake son mahaifinsa  Sosai wasu hawaye  masu zafi suka zubo  masa  wanda  rabonsa  daya zubar da hawaye  har  ya manta a tsawon rayuwarsa amman  yau  ya tuna qalbinsa masoyinsa  , ana  cewa mutun  yafi  son mahaifiyarsa  akan mahaifinsa  shi  dai sai dai
sonsu  yazo d'aya  a ransa , yasan soyayyarsu suyi  kanka  da juna  ,mahaifinsa ya  soshi  har  cikin  ransa  idan  yana  cikin damuwa  sai ya  fishi shiga  damuwa ,   haka idan yana cikin farinciki  ,daf  da zai  rasu  da zarar ya kyalesa sai  ya  fashe  da kuka alokacin  hjy zulaiheart  ke tmbyrsa  dalilin  kuka  sai  yace  "ba kowa nake wa kuka  ba  sai  Adam ,Ina jin  tausayin  rayuwar Adam  bashi da  dan'uwa kamar sauran mutane naso sun kasance su biyu ya samu abokin shawara  "a  she tabbas shi  din  abun  tausayi ne bai  ta'ba  sani ba sai a  tsakanin   wannan lokacin da abubuwa  suka  kwa'be masa  yan'uwansa mata sun had'e kai da mahaifiyarsa yasan da yana da dan'uwa nmj zai iya bin bayansa Koda kuwa zaa fi  karfinsa  ne hawaye ke gangaro  masa  kamar  karamin yaro  yana  cigaba da  busawa  cikinsa hayaki  ."

ranar  a zaune ya kwana cikin   tsananin   tashin  hankali  Kash da Kashi  damuwar auren dole da za'a masa da  tunanin  Nurul qalbinsa   dan   da  zarar  ya  runtse  idanuwanshi dan bacci  sai  yaga hoton princess dinsa  tana  gargadinsa  akan  auren da zai yi  tana gudu tana binsa  tana furta kar yayi aure ya  barta  .tsawon sati  guda  tunda daya amince  da  batun auren mryam  bai sake zuwa Inda  mami   take  ba yana  d'akinsa  yaki barin ya  had'u  da kowa   dan gbdy  fita  ya fita ransa gbdy  soyayyar princess ya  dawo  masa sabo fil  ganin  tunanin  bazai bar kanshi  ba yasashi  mikewa daga kwance da yake  tare  da  zura  takalmi  silifas   ya  fito ya  shiga d'akin  zanensa ya tsaya a gaban hotonta  shiru yana  kallonta kmr yayi mata  mgn  ta amsa fuskarta  d'auke da murmushin  da shine ya zanata  ."

Hannu  ya  kai  ya  ja hoton  a zuciye   ya  yaga  yana  furzar da iska mai zafi daga  bakinsa"A ina kike  tsawon shekaru  ?"a Ina  zan  ganki ?"kin hanani  ganinki,kin hanani sukuni   daga yau kin zamo tarihi  gareni  bazan sake damuwa  dake ba ,bazan sake tunaninki ba zan manta dake arayuwata ,zan cire soyayyarki a zuciyata tunda baki da imani baki da tausayi ya fad'a yana wani irin ihu tare da daga hannuwansa duka sama "haaaaaaaa!!!

  "Hauka  yake  sosai yana  wargaza  komai  dake  cikin  d'akin tare da cigaba da yaga hotunan zanenta  yana  filinging  dasu  har  da  system  dinsa da tsarkar wuyansa wanda zanen hotonta ne aciki , gbdy  ya  hargitsa d'akin  yana  watsi  da komai   har  sanda  mahaifiyarsa  ta shigo  hannunta  rike  da cup wanda  yake d'auke  da ruwan coffee,  bedroom dinsa  ta shiga bata gansa ba dan ita kanta ta kasa jurewa rashinsa na tsawon   kwanaki , ganin baya ciki ta fito har zata fita   ta jiyo sautinsa  a hargitse dan haka ta shigo d'akin ."

ta tsay a bayansa  ta cigaba da kallonsa cikin tsananin tashin hankali mara misaltuwa  bai sani ba  yayi  zurfi  cikin tsananin  damuwa  cikin haka  ya  sake d'aukar hoton  zanen princess  yay  sama dashi sai akan fuskar hjy zulaiheart ta runtse   idanunta da sauri   jikinta na  rawa kamar   ance  ya juyo  ya ganta  tsaye  tana kallonsa  cikin tsananin tashin  hankali  sanye da doguwar  rigar shadda  milk  colour mai  dogon hannu    kyam   idanunta a  kanshi  ta kasa daukewa  ."

cikin  sauri  dunkule hannunsa ya naushi iska tare da durkushewa   kasa  ya  soma tattara kayan  daya  hargitsa yana  cewa "so..sorry  sweetheart am really  sorry    cikin  in Ina, numfashi  ta sauke da ajiyar  zuciya  sannan ta zauna  a  bakin  gado batare  da  ta ajiye  cup din hannunta ba sai dai har lokacin idanunta na Kansa tana jin ciwo da zafin halin da yake ciki   ,kusan minti biyar tana zaune tana kallonsa yana faman tattara d'akin yana mata  sannu  sannan ta fara magana a tsanake  ." kayi hakuri   Adamcy  karka  damu  da  wannan"

  ya  k'arasa  kwashe  kayan  da  yayi waste dasu  zuciyarsa  na zafi  da quna  "kana jina  Adamcy   ita  rayuwa  babu  takurawa  idan baka sameta  anan ba wata  Killa  zaka sameta a aljanna  ,yakamata  ka gane   hakan , karka  shiga rud'ani  idan an  fad'a maka  gasky  illa  ka dinga  yarda   dashi , komai na duniya  babu  sauki  kmr yadda  ka d'aukeshi sai   an   jajirce  be a man Adamcy  karka lalata rayuwarka  akan yarinyar  mafarkinka ."

"kamar  yadda  na  sha fad'a  maka ba kowani mafarki  ke  zama gaskiya ba , ta mike a hankali   ta k'araso  gurinsa ta riko hannunsa  tayi  taku  biyu ta  zaunar dashi akan kujera  kwaya d'aya  dake d'akin , madadin ta bashi coffee  din hannunta sai  ta  fita  gabanta na dokawa da matsanacin karfi dan nan duniya idan akwai abinda ta tsana to bai wuce  damuwar tilon d'anta ba , sam  bata son ganinsa  cikin damuwa ko  wannan auren ma zata yi masa ne dan dole  saboda tasan  muddin batayi masa ba zai iya kare rayuwarsa haka  batare da yayi ba  ."

ko  cikakken minti  biyar  batayi ba ta  dawo  da gorar   ruwa  mai  sanyi  ta mika  masa , babu  mutsu ya kar'ba  ya  kafa a bakinsa bai  cire ba sai daya shanye  tasssss sannan ajiye  yana sauke numfashi taja hannunsa zuwa bedroom dinsa yana biye daita  yana zance  zuci .ya yarda  tabbas  mahaifiyarsa na sonshi kuma gsky take fad'a masa akan yarinyar  mafarkinsa  sai dai ya rasa dalilin da  har wannan lokacin ya kasa yarda iya mafarki  ne  kawai  soyayyarsa  zata tsaya ..."

Tana shiga d'akinsa ta  zauna akan gado  ya kwanta  ya  d'aura kanshi akan   cinyarta  yana mai Jin   damuwarsa tana raguwa ,  a hankali ta Kai hannunta  saman  sumar kanshi ta fara  shafawa   tana mai sake jin  tsananin  son  d'anta  Ina ma  zata ga wannan yarinyar a zahiri da babu abinda  zai  hana bata  mallaka masa  ita  ta kowani  hali  ba ."
ta  dade  zaune har bacci yayi  awon gaba dashi Sannan ta d'auke kanshi ta  maida kan pillow ta lullu'be  masa rabin jiki ta sauko  ta  qara  masa karfin  ac ta kashe masa wuta   ta  duka tayi  kissing  din foring head dinsa tana sake shafa  sumarsa sannan ta  nufi  kofar fita  tana  rufo  masa kofar ."

  Koda ta koma d'akinta  kasa  runtsawa tayi   tana tsaye akan ka'fafunta tana Kai wa Allah  kukanta akan lamarin  tilon d'anta  sai da  tayi  sallah asuba sannan  ta d'an  kwanta Shima  bata  wani dade ba  ta farka ta  shiga wanka ta fito  ta shirya cikin  doguwar  riga   ta sanya  awarwaro da zobin   ziniri ta feshe ilahirin jikinta da turaren humura  mai sanyi kamshi hjy zulaiheart  kenna  Allah yayita  da son kwaliyya da son kamshi  tun tana matashiyarta  har zuwa wannan lokacin da tsufa yazo mata  ta  fito zuwa  babban  parlour'nta  tare da  danna bell din bangaren   masu aiki kafin  kace me  gbdy sun  hallara   sun   zube  a gabanta  suna gaisheta cike da girmamawa. ta  dubesu  tare da amsawa cikin tsananin farinciki dan tana da sakewa da masu aikinta bata zalintarsu sannan bata son su zalinceta yadda take jin dadin zama dasu haka suma suke yabonta da yi mata fatan alkhairi a rayuwarta .

Fuskarta a sake ta bawa 'yan aikinta  umarni abinda  take bukata su dafa a ranar wanda zai zamo  na sadaka ne  kasancewarsa juma'a  "yau  za'a yi  abincin sadakan   da aka saba yi amman ina son  a qara  hannu  sannan a had'a da  wake  da shinkafa Ina son a rabawa  yara kanana  suka  amsa  da "to"  sannan kowace ta soma k'okarin  mikewa "ke tabawa ..." wacce aka kira da tabawa ta tsaya sauran  suka kama gabansu dan fara aiwatar da aiki "ki shirya breakfast  wa sauran jamar gida idan kin gama ki hanzarta sanar dani  ."

"shikenan hajiya itama ta fad'a  tare da juyawa da sauri ." Hjy zulaiheart tana zaune mrym da nana hauwa'u suka  shigo  duk suka zauna suka sanyata a tsakiya  kowacce hannunta empty   babu Komai kamar Koda yaushe  sun baro wayoyinsu    na  gado  a d'akinsu  d'aya byn daya suka  gaisheta   ta amsa cike da sakin fuska a fili  tace   "yau  dai babu danne danne waya ko Kuma an  gaji  da rike wayar ne ?
sukayi murmushi  nana hauwa'u tace " ai tun wuri nayiwa marsi kashedi muddin yaya adam zata aura ta saukakawa kanta akan shiga yanar gizo "wannan haka ne domin zai iya kawo rashin jituwa a tsakaninsu abinda bazan so  faruwarsa ba kenan  nafi bukatarta zaman lfy atsakaninsu. 

ta Kalli bangaren da  nana hauwa'u take zaune  tace " ya batun shari'a da ake da yarinyar da ake zargi ta kashe mubina ne har yanzu na kasa fahimtar gskyr magana gashi Adamcy nata k'okarin shiga cikin maganar  uncle jay ya hana ?"ai gsky gara da  uncle jay ya hana  wani shari'a za'a yi mami  Abar ko waye da Allah kawai mubina dai ta rigada ta mutu bazata dawo ba komai za'ayi ,haka Allah ya qaddaro mata nata mutuwar zata  rataya a wuyan wani inshallahu ruhinta na aljanna suka had'a baki gurin cewa" Ameen "

" mrym tashi ki shiga  ki d'auko min wayata a daki na kira naji yadda ake ciki  ta  mike  tsam ta shiga cikin  bedroom din hajiya zulaiheart ta iske wayar akan katifarta ta d'auka tana duba fuskar wayar nan take gabanta yayi wani mummunar fad'uwa  sakamakon idanunta daya sauka akan hoton ATA  tayi shiru tana kallonsa cikin suit bakake  idanunshi manne da farin  glass yayinda  fuskarsa ke  d'auke da murmushin gefen baki wanda bai gama bayyana ba hakan km qara masa kyau  yake , ta lumshe idanunta tana Jin wani iri a gbdy ilahirin jikinta ,ada sam bata jinsa aranta amman  tun sanda  yasa  akayi kiranta akan batun soyayyarsa ta soma Jin wani Abu akansa komai nashi mai kyau tamkar shi ya hallici kansa ."

jiki a sanyaye ta Kai mata wayar  ta amsa tana kokarin neman layin uncle jay byn sun gaisa take tmbyrsa halin da'ake ciki "mgn dai daya ce nace  abarwa Allah abar ruhin diyata ya samu salama  ".
"uncle jay taya zaka fadi haka  byn kasan zuciyar  sha'awanatu  bazataji dadi ba   ? "nasani   amman  yarinyar nan da ake tuhunma  ba itace tayi kisan ba , tabbas makashin mutun d'aya ne da wanda ya kashe mubina da wanda ya kashe sadear mutun d'aya ne  amman ba wannan yarinyar bace, ita dai ta taka tsawun barawo ne gbdy bincike ya nuna makashin da hannun hagu yayi kisan  ita  Kuma hadiza  hannun dama take amfani dashi  sam gbdy babu alamun sheidar hannunta  ,yanzu  haka an gama duk wani bincike  ranar monday kotu zata wanke  yarinyar Allah dai ya jikan  mubina yasa ta huta  "Ameen Hjy zulaiheart ta furta a fili tana mai tausaya masa "ko me suka yiwa wannan makashi da yake musu kisan gilla?   "Allah masani  "sun dan jima suna waya sannan sukayi sallama .

"Maryam ...!" mami  ta kira sunanta gbdy ta tattara duk wani attention dinta zuwa gareta tana kallonta "Ina saka rai zuwa  karshen satin  nan za'a yi mgnr bikinku  da  Adamcy  " gabanta ne ya sake fad'uwa kmr zai fasa qirjinta yayo  waje "ya kamata ki sake kwarewa agurin girki da sauran abubuwan da yake da bukata  dan haka daga yau kice zaki cigaba da kulawa da komai na bangaren abincinsa  kinji ko ".
ta gyada mata Kai  kawai tare da amsawa da "to !" hawaye na ciccikowa acikin kwarnin  idanunta tayi saurin dennewa  ta rasa dalilin da take tsananin Jin  tsoronsa da tsoro  aurensa."

"  ki  samu natsuwar zuciya ki tashi kije yanzu ki tmbayesa abinda yake bukatar ci a hankali ta mike jikinta na rawa kamar mazari  ta nufi part dinsa
akan hanyarta ta tsaya tana  daidaita natsuwarta sannan ta k'arasa kofar shiga falonsa tayi sallama ba'a amsa ba har ta juya taji sautin muryarsa yana cewa ",waye ne ? ta juyo da sauri "ni ...nice ta fad'a da sauri jikinta da bakinta na rawa "ke wa kenan ? ya sake tmby tayi shiru jikinta na cigaba da rawa hawaye na sake cikowa a idanunta  ta rasa dalilin  hawayen  nata  Jin shiru yasa ya taso da kyar yana mika  daga shi sai gajeren wando  army  green  iya cinyarsa da farar singlet wanda suka bayyana  surar  jikinsa a fili ake iya ganin  kwantaccen sumar dake kwance  a cinyarsa  da  qirjinsa haka kan nipples dinsa  sai farin silifas dake sanye da kafafunsa da farin agogo da alamun aiki yake ."

A tsaye ya ganta a bakin kofar gbdy bata cikin  haiyacinta a hankali ta d'ago ta  kare masa kallo saboda kusancin da suka samu muryarsa a kasalance yace  "ke lafiyarki  tsayuwar me kike yi anan  ya fad'a fuskarsa a murtuke"kayi hakuri please mami  ce tace nazo na tambayeka abinda zaka ci a girka maka "  ya tsuru mata Ido  a zahiri yake iya hango yadda qirjinta ke  bugawa wani dogon tsaki yaja a fili ya juya ya koma ciki ya barta tsaye . juyawa tayi tana daga kafafuwanta da kyar ta dawo parlour'n ta tsaya hjy zulaiheart ta dubeta "yaakayi me yace zai ci ?hannuwanta ta tsarke cikin juna sannan ta bud'e baki da kyar "wai a dafa masa komai."

mami  ta fad'ad'a fuskarta da murmushin jin dadi , ita Kuwa nana hauwa'u sarai ta fahimci wani abu a tattare da marsi tasan sarai ba abinda yace mata  kenan ba   "to shikenan maza ki shiga ki dafa  masa  abinda  yazo cikin tunaninki amman ki natsu sosai kinji. "ta gyada mata tana cewa "sister muje ki tayani "me .....?dan girman Allah ki rufa min asiri na tsira da mutuncina ke dai kije Allah ya bada sa'a kiyi kokari yayi dadi  sosai ta k'arasa maganar tana kakkabe hannunta. "haba sister ki taimaka mana kin san fa  komai tare mukeyi ,nasani amman ban da wannan wallahi bazan Saka hannu ba abinci yazo bai yi dadi ba ya had'amu yaci ubanmu"  hjy zulaiheart tayi murmushi "Kai Adamcy hukuma kowa tsoronsa yake ji amman Kuma fa yana da sauki Kai Kinga mryam  yi tafiyarki kinji  duk abinda baki gane ba kizo ki tambayeni Simi Simi ta juya ta shiga kitchen kmr ta daura hannunta  tayita kuka dan tasan muddin tayi kuskure sai yaci ubanta duk iya k'okarinta na dafa  masa rice and stew bai ci ba ya wuce juma'a ."

*****
Da  misalin  karfe  biyu  na  rana  bayan  an  sauko  daga massalaci  hajiya   zulaiheart  da  kanta  ta fito  zuwa  haraban  gidan ta fara  rabawa yaran dake shigowa haraban estate din sadaka  wake da shimfa  acikin takeaway fari tare  naira dari  biyar biyar sababbin yayinda  ATA  ke tsaye daga can nesa kadan da inda take kunnensa manne da waya yana tafiya a hankali irin na jinin saurarata dan sauranta  yaki   barin jininsa komai nashi  irin nasu ne sanye yake cikin farin yadi voil  kafafunsa sanye da takalmi fari haka ma Kansa sanye da hula fari mai ratsin  baki  yayinda tsintsiyar hannunsa ke d'aure da  agogon silver rolex   yayi  kyau sosai kamar ka sacesa ka gudu  sai dai kallo d'aya zaka masa kasan   zuciyarsa dakushe take  da tsananin damuwa ."

tsayawa yayi cak yana cigaba  da kallon mahaifiyarsa  cikin haka ta  juyo  nan take  suka had'a  Ido daita ya sakar mata  taadaddaden murmushinsa dake sake bayyanar da ainihin bawar kyawun da Allah yayi masa wanda wannan murmushin babu mai ganinsa sai ita , murmushi
ta sakar masa cike da farinciki ganin murmushinsa  da ba kowa yake gani ba tana tsananin son kyakkyawan tilon  d'anta shi  din dabam ne acikin zuciyarta  ,uwa Uba nagarta   tana   masa so mai  tafiyar da ruhi shine karfin  gwiwarta ."

a hankali  ya soma takowa zuwa Inda take har ya k'araso gareta ya tsaya kusa daita yana tayata rabawa yaran kudi duk wanda ta bawa takeway sai ya mika masa kudi  ,tana raba abinci  tana dubansa tana murmushin jin dadi "thank you my beloving prince  " you're welcome my  queen ya fad'a yana kallonta  bayan sun gama  tare suka koma ciki  suna tautaunawa a falonta  sukayi  masauki ya zauna yana runtse idanuwanshi."Adamcy nah...." !
ya amsa  can kasan makoshi" inshallahu wannan satin zanyiwa su  baba babba maganar aurenku ayi a wuce gurin muryarsa a raunane yace "to sweetheart kuyi duk abinda ya dace na sallama miki komai ."

"bangane ka  sallama min komai ba kana nufin bazaka tabuka komai ba ?"me kike son nayi sweetheart idan akwai abinda kike bukatar nayi ki sanar min zanyi ganin  idan  ya  cigaba da biye mata  maganar auren zasuyitayi yasa yay  saurin  runtse idanuwanshi yana cewa "wayyohhhly sweetheart cikin kwantar da murya tace "ya'akayi Adamcy ? "sweetheart  yunwa nake ji cikina har ya fara zafi murmushi tayi   "ko kunya baka ji ba kmr wani jinjiri ka dai rage wannan shagwabar ka bar wa yaranka  "a'a sweetheart ki barni nayiwa uwata  suma idan sunzo ga guri nan kowa yayiwa mamansa "to ai shikenan bari nasa maryam ta samarmaka abinda zakaci "wace mrym kuma dan Allah kiyi min da kanki karki rage min Jin dadi wannan yarinyar babu abinda ta iya Kuma ma nafi son Ina cin abinci daga hannunki  ni dai gsky banason abincinta "ya Isa sarkin naci amman dole kaci daga hannun matar da zaka aura wata rana ."

"naji amman  ayi sauri ayi min please dariya ya bata sosai  wai ayi sauri ayi mishi  ATA  kenan ko  yaushe idan yana tare da mahaifiyarsa daukar kanshi yake kamar karamin yaro hjy zulaiheart ta d'auki wayarta ta soma Neman layin maryam  sai dai bai shiga ba ta ajiye wayar tana Kiran daya daga cikin masu aiki ."

Tana zaune a d'akinsu  hjy zulaiheart ta  Aiko mai  aiki akirata da hanzarinta ta Isa parlour'n tace "kije ki kawowa Adamcy wani Abu yaci yunwa yake ji ta Dan saci kallon Inda yake tana Jin mummunar fad'uwa gaba  sannan ta gaishesa  sai dai bai Kalli Inda take ba bare ya amsa gaisuwarta  ,Kai tsaye kitchen ta nufa sai dai ta rasa me zata dafa masa shap shap yaci ,kawai tayi tunanin daura masa indomi da kwai ta kawo masa a lokacin data  fito  bata  tarar da  hjy zulaiheart ba sai aunty khadeja  zaune agurin suna magana da ATA ta ajiye akan table din dake gabansa tare da gaishe da aunty khadeja kamshin  indomin da yaji ya ziyarci hancinsa ya balain ta'ba zuciyarsa na take ransa ya baci .

a hankali ta juya zata wuce dan Sam bata jurar tsayuwa a duk Inda yake muryarsa a kasalance yace"ke meye wannan kika kawo ? ta dawo a hankali ta tsaya  tare da cewa  "indomi da ......"a fusace ya dan gyara zamansa ya tsaidaita  "shine abinda kika iya dafawa?  jikinta na rawa ta dubi aunty khadeja dake zaune  tana juya masa Kai "nace shine abinda kika iya dafawa ?ta girgiza  masa kai jikinta na rawa gbdy a tsorace take a tsaye,shi kuwa  kallonta kawai yake da seyx eye's dinsa wanda hakan yasa hantar cikinta cigaba da kadawa  lumshe idanunshi yayi tare da yin shiru  ya  koma ya jingina  jikinsa  da kujerar da yake zaune ya soma motsa labbansa   "wai  irin wannan matar ake min  sha'awar  ajiyewa a gidana  ?yayi mgnr a fili  yana sake jan tsaki a fili "wacce irin  sakariya mata ce wannan khadeja saboda rashin tarbiya indomi fa me zanyi da ita ?

"tuni idanunta suka kawo kwalla bakinta na rawa tace " kayi hakuri bari naje na sake dafa maka wani abu bude idanunshi yayi fesss akanta Yana cewa "shut up me yasa baki dafa ba  tun farko ? ya karasa maganar yana buga mata  wata hadaddiyar tsawa nan take jikinta ya kama rawa  da hannu aunty khadeja tayi mata alamar ta wuce kmr jira take tayi gaba da sauri tana haki ."

"kayi hakuri adamcy   da sannu zata iya komai "har sai yaushe khadeja ? nifa akan wannan matsalar   zamu tabbata muna samun matsala daita bazan juri zama da macen da bata iya komai ba?" shekara ashirin da biyar da wani abu amman ace  mace bata iya girka komai ba  sai yaushe ? "gsky gsky ni dai an  ....... " sai Kuma yayi shiru ya kasa cigaba da mgn "yanzu dai kayi hakuri me zaka ci ni sai na shiga na girka maka da kaina  a fusace  yace "barshi kawai  juyin duniya  yaki yace bai ci haka ta hakura ta barshi  ."tsaki ya dinga ja bai san me ma ya jashi cewar zai ci abinci ba  mikewa yayi ya bar gidan gbdy Aunty khadija tabi da kallo gsky akwai kuskure atattare da maryam dan rashin iya girki babban matsala ne a gidan miji ba wai shekara ashirin da biyar da yan kai ba a tunaninta maryam zata kai talatin dan tsirarau da auta babu yawa .."

******

Maryama na zaune da yammacin ranar monday tana wanke kayan Aunty salma da kayan kanwarta sakina wacce ta kasance diya ga Aunty salma duk da lokacin makarantar islamiyya ne amman ita bata samu damar zuwa ba saboda aikin da matar yayan mahaifinta ta sata , wanke take da iyakar karfinta har ya zamo bata iya wankewa da karfinta sakamakon gajiyar data tsarketa domin ta jima batayi irin wannan aikin ba tun karfe biyu lokacin data taso daga makarantar boko gashi har yanzu biyar ta wuce sallace kawai ta tasheta daga tsugunno datayi tana faman dikar wanki ."
Sakina ta shigo cikin haraban gidan da sallama babu sukuni a fuskarta dan kallo daya tayi mata ta fahimci haka ganin halin data ganta yasa ta sake shiga cikin damuwa ta matso kusa daita ta tsaya cikin bacin rai " maryama daman wanki kika tsaya shine dalilin da yasa baki zo makaranta ba yau .?"
ta fad'a ranta a bace tana kallon cikin falon Aunty salma."

da kyar maryama ta kirkiro murmushin dole wanda yafi kuka ciwo dan komai ya wuce a zuciyarta dan bata qaunar sa'insar sakina da mahaifiyarta akanta muryarta a sake tace "kayan makarantar nawa ne basu bushe ba shine nace Aunty salma ta kawo wankinta na wanke da naki dan zaman bazai min dadi ba tunda bazan samu zuwa makaranta ba ta fad'a mata haka cikin zaro wani kaya daga cikin tarin kayan dake ajiye a gefe guda tana qoqarin dannashi cikin ruwan wanki sakina ta fixge cikin fushi tana cewa "wallahi karya ne nafa san halin mama itace ta hadaki da wannan aikin aikin daya yafi karfin ace mutun daya ne zai yi ni ban san me yasa mama take yin haka ba ..."

Aunty salma ta fito daga cikin dakinta sakamakon jin maganar diyarta "sakinata har kin dawo sannu da dawowa sakinata ta fad'a tana qarasowa ta dafa kafadarta cike da kulawa da tsantsar soyayya sakina ta zumburo baki "haba mama yanzu abinda kikayi ya dace dan meye zaki lodawa maryama uban wanki haka alhalin kina sane da cewa ko mu duka muka hadu bazai qare acikin kwana biyu ba haba ni wallahi wallahi bana só abinda kikeyi wa yaruwata sautari umma tana sanar dake illar haka karfa ki manta maryama ba baiwa bace a gidan nan ' ya ce kamar kowani d'a acikin gidan nan ko bakya kaunarta ita da mahaifiyarta bai kamata ace kina daukar abubuwan wahala kina sakata ba tunda ko babu komai yaruwata ce ko dan ni ya kamata kina son maryama saboda ina sonta ina qaunarta in har soyayyar da kike min ta gskiya ce ."

Aunty salma ta kwabe baki "sannu sarkin yan iyayi ta fad'a a zuciyarta amman a zahiri cewa tayi "meye acikin dan wannan aikin yanzu dan na saka maryama dan wannan aikin zai sa Kiyi zargin bana sonta ne ko wani abu ? tô idan baki sani ba bari na fad'a miki ina mata kwadayin samun lada ne shiyasa nake sakata aiki yanzu Ke kin san irin ladan da zata samu har idan ta gama min ."?

"To ni me yasa baki sani ba tunda aikin lada ne in har idan kwadayin lada Kike mata ?" Ki dinga hadawa dani daita gsky ni banaso ." maryama na durkushe hawaye suna son zubo mata daga cikin kwarnin idanunta amman ta dannesu dan kawai bata son sakina ta fuskanci damuwarta dan tasan dole sai ta qarawa yiwa mahaifiyarta bori ita km abinda bata só kenan taga suna samun sabani akanta da mahaifiyarta domin ita kam tarasa gane maanar hakan rashin kunya ce ko gaskiya take fadawa mahaifiyarta da ta kasance damuwa atattare daita da tata mahaifiyar "

"shikenan sakina daga yau na daina Kiyi hakuri ina sata ne dan tafiki kuzari yanzu muje kici abinci ai kuwa sakina taki binta "wani irin muje naci abinci ki dai zo mu hadu har dake mu qarasa wanke sauran kayan Aunty salma tabi wanki da maryama ta wanke sama da rabi ta waigo ta dubi sakina "a'a ki bari ta qarasa tunda sauran ka.." A'a wallahi ki tsaya dai mu qarasa tas ita ba mutun bace tun rana take ta faman aiki kamar wata inji."

Aunty salma tayi shiru tana duban yarta ta ja tsaki ta nufi hanyar dakinta tana cewa "ai sai dai idan ke zaki iya ni dai babu abinda zanyi taka nas naje na arota wajen uwarta shine dan tsabar iyayi irin naki zaki ce ga zance ga magana da yanzu Ke na saka bazakiyi ba dan yanzu kinga na saka maryama shine zaki zo da shegen iyayi shikenan ki tayata ku qarasa tare ta wuce tana bala'i maryama na tsaye batare da tace uhm ba bare uhm uhm dan bata son tayi laifi dan a yanzu ma tana hankalce da Aunty salma harararta take sakina ta gyara botiki ta cire hijab dinta ta sunkuya ta tura mayafinta da maryama Ke qoqarin turawa cikin ruwan wanki ta fara wankewa da sabulu data tsinta acikin ruwa ."

"Why sakina ? mai haka ki barni na qarasa mana bana son naga kina sai sa da mahaifiyarki akaina ki daina babu kyau tunda kinga ni bana yiwa Aunty haka "itama ai abinda take miki babu kyau ko dan ba itace ta haifeki ba kullum sai ta dinga zuwa tana aroki dan taga Aunty shiru shiru bata son magana aikin yau da dabam na gobe dabam ta hanaki zuwa makaranta malam mustaphata sau uku yana shigowa tambyarki nace bakizo ba kina gida bakya jin dadi "ai ba ita kadai Ke sakani aiki ba umma ma ina yi mata "eh kina yiwa umma amman ita tasan daidai dan bazata barki kina aiki har wannan lokacin bakije islamiyya ba kar ma ki hada mama da umma dan ba abu daya bane ."

maryama tayi shiru Tare da sunkuyar da kanta kasa tabbas akwai bambamci tana son aikin umma fiyye dana kowa ko babu komai tana qaunar mahaifiyarta kum tana tausayawa rayuwarsu tun kafin mahaifinsu ya bar duniya ta kalli sakina tana son hanata wanki amman tasan bazata yarda ba kawai ta cigaba da kallonta ita yanzu abinda yafi damunta yunwa take ji sosai domin Aunty salma bata bata ko ruwa ba wai sai ta gama sallah ma da kyar tayi ."

Sakina ta cire hannunta ta shiga kitchen ta dauko plet din abinci ta fito ta daura mata akan cinyarta "kici !ta tsurawa abincin ido tana kallona batasani ba itama sakina ita take kallo ta matsota da sauri tana son sani abinda yasa tayi shiru bata fara cin abinci ba maryama tayi tsuru itama haka ta kalli abinci ta kalli maryama "ko abinci yayi kadan ne?ta fad'a girgiza kai maryama tayi "ya ma yi min yawa "to me yasa kikayi shiru kina tunani ?" Kai sakina kina son damun kanki akaina ta fad'a tana soma cin abinci jikinta babu kwari ga rawar da yake saboda yunwar da take ji maryama bata bar bangaren su sakina ba sai daf da magariba shima da taimakon sakina ne ."

A matukar gajiye ta shigo part dinsu ta zauna akan kujera jikinta tattare da tsananin gajiya Aunty ta qaraso ta tsaya akanta "ya naga duk kinyi wani iri ko kin aikin da yawa ne ? numfashi ta fesar tare da waskewa dan bata son nunawa mahaifiyar ta damuwarta domin duk hakurinta taji irin aikin datayi yau sai taji ciwo aranta dan haka ta dubi mahaifiyarta tace "babu komai ai aikin ma bashi da yawa kuma har munyi mun gama tare da sakina sai lokaci ta saki jikinta ta zauna kusa daita "sannu princess dina shiyasa nake qara jin sonki araina ta fad'a Tare da shafa kanta da yake sunan datake kiranta dashi kenan atare sukayi shiru Aunty na matukar tausaya mata ita da danuwanta habib kasancewar sun taso cikin maraicin uba gashi dangin ubansu ba qaunarsu suke ba idan aka cire mahaifiyar babansu da yayan babansu da matarsa to babu mutun daya da zata cire."

Mmm sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS
AYSHABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.