Best / Popular Hausa Novels

Maradams Book 1 Complete Hausa Novel

Reading file: MARADAMS book 1 BY AYSHA A BAGUDO.txt

Chapter 12 of 18

Page 12

Aunty tayi shiru tana duban maryama yanayinta kamar kazar da'aka tsamo cikin ruwa gaba daya alamu sun nuna gajiya a tattare daita amman dan karfin halin irin nata take boye mata damuwarta , hawayen da suka cicciko acikin kwarnin idanunta tayi qoqarin maidawa tana danne damuwarta saboda farinciki diyarta ."
ahankali ta dauke kwayar idanunta aKan tilon diyarta zuwa wani bangare dabam tana tunanin rayuwa da abubuwan da sukai ta faruwa daita ta sha wahala arayuwarta shiyasa batason maryama ta sha wahala irin wanda ta sha ,wannan aikin da aunty salma kesata yana matukar ta'ba zuciyarta domin ko ita da tayi sanadiyyar zuwanta duniya bata sakata aiki haka koda tace zatayi ma bata yarda ta bar mata tayi ita kadai sai dai suyi a tare amman bata da yadda zatayi da rayuwata dan bazata iya hanawa ba "tabbas bata da yadda zatayi kuma bata isa ta hanata ba tunda zaman gidan ya zame mata dole dan bata son rasa yaranta kuma bata son ta koma ga danginta ." tayi maganar a kasan ranta .

maryama ta kalli mahaifiyarta duk da bata san me ya canza yanayinta ba amman tasan meke yawo acikin kwakwaluwarta ta matsota sosai tana jijiga Aunty wacce tayi nisa cikin tunanin rayuwa "meke damunki Aunty ?firgigib ta dawo haiyacinta tana dubanta duba mai tattare da damuwa tana cewa " babu abinda Ke damuna princess " ta fad'a tana mai jin tausayinta domin dai duk halin da suka tsinci kansu aciki itace sila, itace silar janyowa ya'yanta rayuwar wahala wacce bata kamacesu ba duk wani abu daya faru da ya'yanta itace ta janyo masu adalilin zunzurutun Kaunar data nunawa mahaifinsu ya janyo mata rasa komai domin ta zabi
Mahaifinsu ta bar danginta wanda yasa kowa acikin danginta yaji babu dadi akanta."

"me yasa kowa ya tsanemu acikin gidan nan ?" bayan mahaifinmu da granny da umma da abba babu mai qaunarmu acikin gidan nan gashi abba ya rasu ya barmu kamar yadda mahaifinmu ya barmu why Aunty ?me yasa basa qaunarmu ? "Me yasa suka tsanemu ko kin yi masu wani laifi ne ?ina son nasan abinda ya kawo wannan kiyayyar ?shiru kawai Aunty tayi tana dubanta dan bata da abinda zata fad'a mata domin kare kanta maryama yarinya ce da bata wuce shekara ashirin a duniya ba but she's smart in ance smart ana nufin mutun wanda ya kasance mai tsananin hankalin da kwakwaluwa tare da kaifin baseera sannan yarinya ce mai fadar gsky komai d'acinta zata fad'a she's very shap akan komai dan wani lokaci har mamaki take bata idan tayi wani abu kanta naja sosai fiyye da yadda take tunanin tasan muddin taji ta zabi mahaifinta ne akan iyayenta yasa dangita suka juya mata baya tabbas zata fad'a mata gskyr data kasa amsa daga ahlinta "Ina danginki suke Aunty ?ta jeho mata tambayar data nemi bugar mata da zuciya tana mai d'aura kanta a saman cinyarta ."

tsura mata ido tayi tana kallonta kafin daga bisani tace "suna nan ! "suna nan amman me yasa bakya zuwa inda suke kamar yadda Aunty salma keyi ?"babu komai "ta bata amsa atakaice tana jin wani tuttukin bakinciki acikin ranta mai tattare da damuwa "Aunty karki ce babu komai lallai akwai dalili akwai abinda yasa bakya son zuwa inda suke har yasa bamu sansu ba ,mahaifiya mahaifi yan'uwa duk ba abun wasa bane domin suna da matukar mahimanci arayuwar mutun ."

Naunayen ajiyar zuciya aunty ta sauke tana sake tsura mata ido "dan baki san abinda suka aikata gareni bane maryama shiyasa zaki fadi haka ta fad'a hk a zuciyarta " ahlinki suna da matukar mahimanci sannan suna da hakki akanki most especially iyaye yana da kyau a dinga basu hakinsu domin hakan zai samarwa mai yi kwanciyar hankali ,meye acikin duniyar da babu albarka iyaye acikinta ?yadda kike iya hakurin rashin zuwa ga iyayenki bazan iya barinki daidai da second daya batare dana daura kwayar idanuna akanki ba saboda qaunar da nake miki ina sonki aunty fiyye da komai dake cikin duniyar nan dan haka Kiyi qoqarin kije garesu nasan suma zuciyoyinsu na cike da kewarki da qaunarki tunda kika haifeni na girma na kai wannan shekarun ban ta'ba ganin ranar da kika shirya kika ce zakije ga ahlinki ba , kullum muna cikin dangin dady cikin kaskanci da wulakanci ya kamata ko sau daya ne muje domin nima ina son ganinsu ina son ganin danginki zaki je ga ahlinki ? tayi mata tmbyr tana mai tsura mata kyawawan idanunta masu matukar kyau ."

Kusan minti goma aunty bata amsa mata ba har sai data sake maimaita abinda ta fad'a sannan tace "to maryama zanyi qoqarin zuwa." ta fadi hakan ne ba dan zata aikata hakan ba sai dan abar maganar ta wuce "da gaske kike Aunty zaki ga ahlinki ? murmushi tayi mata domin bata son damuwarta dan ta fahimci yau din nan tana cikin damuwa ."

maryama ta rungumeta tsam tsam ajikinta tana mai jin dadi "naji matukar dadi Aunty ina son ganin ahlinki nasan habib ma zai ji dadi yaushe zamu je ? ta fad'a tana zare jikinta daga na Aunty yayinda idanunta Ke kallonta aunty tai shiru tana dubanta hakan nan ta tsinci kanta cikin farinciki wanda tasan maryama ce sila tana matukar son farincikin yaranta murmushinsu murmushinta ne haka zalika damuwarsu damuwarta ce tana matukar qaunarsu fiyye da komai dake cikin duniyar nan dan sune iyayenta yayyaenta kannenta komai nata daman tasha yin addua ko a can baya Allah ya bata ya'ya masu albarka wadan da zasu maye mata gurbin yan'uwa."

"aunty !
Ta kira sunanta cikin sanyayyar muryarta mai tsananin kashe jiki a duk sanda tayi mata magana da wannan muryar tana tuno mata da mahaifinta ko habib da ya kasance nmj bai dauko sanyin muryar mahaifinsu ba sai ita "na'am my princess ta amsa tana dubanta tana saurararta "a ina danginki suke zaune ?"tayi mata tmbyr fuskarta na nuna farinciki."

"suna zaune acikin garin nan" "cikin garin nan ? maryama ta maimaita abinda mahaifiyarta ta fad'a cike da mamaki Aunty ta gyada mata kai alamun" Eh!wani sabon mamaki ya sake cunkushe zuciyar maryama "suna zaune a gari daya amman duk tsawon wannan shekaru bata taba zuwa dasu inda suke ba bare su sansu gashi ta zauna tana rayuwa cikin kunci da babu tamkar wacce bata da kowa acikin duniyar nan ,numfashi ta janyo da kyar ta fesar a hankali kafin ta bude bakinta da kyar "yaushe zamu je wurinsu ?".

"karki damu sarauniyata in sha allahu zamu " cike da farinciki maryama ta kai hannunta ta dauki remut tana mai kunna tv tare da maida hankalinta Kan program din daake yi a tashar galaxy tv tana mai jin farinciki da natsuwar zuciya "Aunty zan so naji ranar da zamu na soma lissafa kwanaki "canza fuska tayi batare datai auni ba kafin daga bisani ta kawar da kanta gefe dan karta fahimci damuwarta dan gbdy ta soma neman natsuwarta ta rasa bazata iya zuwa garesu ba ,haka zalika ya'yanta ma bazasuje ga danginta ba most especially mahaifiyarta ta barsu har abada kamar yadda suka barta zata karasa rayuwarta a haka cikin kunci ."

a qalla sun dauki mintuna goma zaune suna duban tv babu wanda ya sake yunkurin cewa komai
Kafin ahankali cikin sanyi jiki maryama ta mike daga kwanciyar da tai akan cinyar mahaifiyarta ."Aunty lokacin sallah yayi bari naje nayi sallah gashi ina son na danyi zane kafin na kwanata ga bacci da nake jin yana fixgata tamkar zan fadi ni zan shiga ciki sai da safe dan gabadaya yau ko gurin umma bazan shiga ba idan sakina ta shigo kice mata na shiga bacci dan bazan sake fitowa ba allah ya bamu alkhairi ."tana gama fadar haka ta juya ."

har tayi taku biyu Aunty ta dakatar daita ta hanyar kiran sunanta "princess!
Ta dan tsaya tare da waigowa "abinci fa ? maryama ta dan yatsina face dinta tana ciza gefen lips dinta sannan ta girgiza mata kai alamun "a'a ! "to amman karatun jarabawa ya kamata kiyi ba zane ba ko gobe baku da exam ne ? muna da shi zanyi karatu sannan na d'an yi zanen sai na kwanta " "kiyi karatu da kyau maryama Kinsan a final year kike, ni da son samuna ne da kin bar zanen nan har sai kin gama karatu " karki ji komai Aunty duk zan iya Kiyi min addua da fatan samun nasara ."

Aunty ta sauke numfashi tana cewa "allah ya bada saa yayiwa rayuwarki albarka "Ameen sai da safe "
"okay to shikenan allah ya bamu alkhairi "Ameen ! ta sake juyawa tana rausaya tamkar zata karye dan rashin jikin da Allah ya bata , har sai da Aunty taga ta shiga cikin d'akinta sannan ta dauke idanunta daga kallon bayanta ."

Tana shiga dakin bayi ta shiga tayi wanka hade da dauro alwala ta fito cikin sanyi jiki tana goge gashin kanta da towel tana goge jiki tana mamakin abinda yasa mahaifiyarta bata son zuwa ga danginta alhalin suna gari daya ,"me yasa haka? " zata so tasan dalilin dayasa bata son zuwa garesu da wannan tunanin ta saka doguwar rigar bacci fara sol har kasa ta qarasa inda take ajiye sallaya ta dauka ta shimfida ta kai hannunta ta dauki zumbulelen hijab dinta ta saka ta kalli gabas a natse ta tada sallah ."

byn ta idar ta mike ta cire hijab ta ajiye a gefen gadonta ta zauna akan kujera kwaya daya dake dakin wanda gabansa dan qaramin table ne mai dauke da tarin textbook da fararen takardu na zanenta ta janyo textbok daya daga ciki sannan ta zaro farar takarda kwaya daya ta ajiye a gabanta ta soma karatu tana joting kusan mintuna talatin sannan ta rufe ta maidashi inda yake ta sake zaro wata takarda ta ciro pencil da kayan aikinta ta fara zane wanda ya kasance abinci ruhinta a duk lokacin da zaka ga maryama a natse zaka ganta kuma akan aiki idan bata makaranta boko tana islamiyya idan bata islamiyya tana Kan aikinta na Architect wanda dashi take samu take taimakawa mahaifiyarta batayi karatu akanshi ba kawai baiwa ce daga allah ya bata babu abinda bata iya zanawa tun tana qarama take Zane dashi ta girma ."

cikin kankanin lokaci ta fara zana wasu hadaddun mutane sanye da kaya na maaurata guda biyu macen sanye da wedding gwan yayinda nmj kuma ke sanye da suit sunyi matukar kyau kamar a kirasu su amsa tayi shiru tare da tura pencil cikin bakinta tana taunawa tana kallon zanen ahankali ahankali tana lumshe idanunta alamun bacci "bari na bar aikin nan haka tunda ba urgent bane zuwa gobe na qarasa idan na dawo daga school ta tattara ta bude durowar table dinta ta tura ta mike tsaye ta sake daukar hijab ta sanya ta tada sallah ishai tayi addua ga mahaifinta da alummar muslimai ta mike ta nade dadduma ta maida inda yake ta hau gado ta kwanta ko cikakken minti uku batayi ba bacci ya dauketa ."

A can falo kuwa Aunty zaune kawai take duk hirar da habib da sakina ke zubawa da idanu kawai take binsu hankalinta na wani waje karfe goma daidai sakina tayi masu sallama ta wuce tana fita Aunty ta mike tsaye tana cewa habib "ka rufe koina ni zan shiga ciki allah ya tashemu lfy ta nufi hanyar dakinta har zata shiga ta hango haske a dakin maryama dan haka ta dawo ahankali ta shiga dakin ."

tana kwance ta dungule waje daya a tsakiyar katifa ta cusa kanta cikin jikinta kwanciya mai tattare da damuwa duk wanda kaga yayi irin wannan kwanciya tabbas yana cikin damuwa ko maraici kuma a duk sanda taga tayi irin wannan kwanciyar ba komai take tunawa ba illa kanta take tunawa alokacin baya irin kwanciyarta kenan wanda damuwa ne silar nata kuma tasan damuwar ce ta janyo mata itama ta qarasa shigowa d'akin har inda take kwance ta kai hannu ta gyara mata kwanciya ta janyo abun rufa ta lullube mata jiki ta shafa gefen fuskarta tana sake jin soyayyarta acikin ranta ya'ya sune farinciki iyaye amman ita ta rasa wannan gatan daga nata most especially mahaifiyarta ."

"abinda mahaifiyarta tayi mata abu ne da mutun zai iya yafewa amman bazai ta'ba iya mantawa ba kuma abu ne da bazata ta'ba yiwa ya'yanta ba zata so ya'yanta tamkar rayuwarta bazata iya kuntata masu ba bazata iya azabtar dasu ba sannan bazata iya hanasu cikar burinsu ba zata basu farinciki duk abinda suke so zata basu matukar bai sabawa shari'a ba, fatanta dai allah ya raya matasu cikin aminci "ta mike tsam har lokacin idanunta na Kan maryama dake qoqarin sake dunkulewa waje daya ta kashe mata hasken d'akin sannan ta fito tana mai janyo mata kofar dakin ta shiga dakinta "

Ahankali ta zauna a bakin gado zuciyarta cike da zullumi har kusan shabiyu na dare tana zaune sai dai zuwa wannan lokaci tayi rigingine tana kallon saman dakin daya byn daya maganar maryama Ke dawo mata "me yasa bakya son zuwa inda danginki suke ?" mahaifi mahaifiya yan'uwa suna da matukar mahimanci arayuwar mutun ahlinki suna da hakki akanki most especially iyaye yana da kyau a dinga basu hakinsu domin hakan zai samarwa mai yi kwanciyar hankali,meye acikin duniyar da babu albarka iyaye acikinta ?nan take taji wasu hawaye masu zafi ya ganganro gefen idanunta."

"tabbas gaskiy diyar cikinta ta fad'a mata amamn ai sune sukace babu ita babusu har abada me zataje tayi masu a yanzu da take cikin damuwa da bata da komai tasan ko taje garesu wulakanci ne zai biyo baya gara ta cigaba da zamanta hk babu dangi har karshen rayuwarta ,maryama da habib sun isheta komai , sheshekar kuka take sosai wanda batasan tanayi ba maraici sosai take ji alhalin ita din ba marainiya bace ta daura hannunta daya a saman kanta ko zataji saukin zafin da zuciyarta take mata ."

tana cikin wannan halin taji an turo kofar dakinta da sauri ta dago tare dawowa haiyacinta tana mai goge hawayen idanunta da hannuwanta duka habib ne ya shigo wanda sakamakon sheshekan kukanta ya shigo dashi sai daya mata kallon tsanake sannan yace "me ye damuwarki male? dake shi kuma haka yake kiranta dashi ta sake sanyawa jikinta jarumta tana girgiza masa kai " alamun babu komai."
"karki fad'a min haka byn kukanki ne ya shigo dani ya fad'a yana kafeta da fararen idanunshi qara maimaita tmbyrta yayi tayi kasa da kanta sakamakon hawayen daya sake cika mata ido domin kwalkwaluwarta ta toshe ta kasa fad'a masa dalili "ya sake matsota sosai male ki fad'a min damuwarki domin bazan bar dakin nan ba muddin baki fad'a min ba domin dai damuwa Ke saka mutun kuka irin wannna kuma tunda nake ban ta'ba ganin kukanki irin haka ba kuka mai fitowa daga kasan zuciya ."
Ya kai hannu ya dago habarta yana kallon hawayenta dake zuba yabi hawayen da kallon hankalinsa na sake tashi cikin tsananin tashin hankali yace "wanene ya bata miki ranki haka? ta girgiza masa kai kawai "wai meye haka ne male kina son zuciyata ta kasa sukuni ne ko me ?ta sake girgiza masa kai ya juya a fusace zai bar dakin "bari naje na taso heartbeat.."

ta riko hannusa da sauri "karka tashe ta bacci dan baccinta yayi nisa gashi gobe tana da exam's "to ki fad'a min damuwarki kamoshi tayi ta zaunar dashi a gefenta ya zauna yana sauraronta kusan second goma sannan ta zayyane masa komai sai daya numfasa kana ya soma mgn "male duk abinda heartbeat ta fad'a is right and it good dan daman nima ina neman hanyar da zan miki wannan tmbyr domin abu ne daya dade cikin kwakwaluwata har ya Kan hanani kwanciyar hankali Kiyi tunani male
gsky heartbeat ta fad'a miki ya kamata kije ga danginki ko mu ki fad'a mana inda suke muje domin muna bukatarsu "

Jin haka yasa ta barke da wani sabon kuka "baku san me suka min ba baku san irin wahalar dana sha a hannunsu ba ,na sha wahala kuma duk akan mahaifinku ne bana tunanin zasu qaunaceku shiru yayi yana dubanta cike da mamaki "me dady yayi masu haka ?sannan wani irin wahala kika sha a hannunsu ?yayi mata tmbyr a jere cikin tsananin tashin hankali kafin a hankali ya kai hannu yana goge mata hawaye shiru tayi ita kanta tana son ta basu labarinta amman bata san yadda zata dauki abun ba "tana son mahaifiyarta tana tausaya mata tana gudun bacin ranta ,bata son ganinta cikin damuwa amman a karshe itace abar kyama itace abar wulakantawa, itace mara mutunci a idanunta
har tana cewa allah yasa mijinta ya wulakantata Allah ya hanata haihuwa Allah yasa ya saketa mijin da take tsananin so duk akan ta zabeshi a matsayin jikin aurenta ."

Kuka sosai take tmkr ranta zai fita tana furta "na yafesu har abada zan zauna na qarasa rayuwata ni kadai "yayinda habib Ke share mata hawaye yana kuka yana bata hakuri domin yasa duk abinda yasata kuka irin haka mai girma ne muryarsa a sanyaye yace "kiyi hakuri male ki daina kuka kukanki na balain daga min hankali na hakura da son jin komai domin jinsa bazai zame min alkhairi ba amman kema kiyi qoqarin ki manta abinda ya rigada ya
wuce amman iyaye da yanuwa duk abinda sukayi baa yafesu ."yana gama fadar haka ya juya har ya fita ya rufe mata kofar dakin hawaye ne yake fita dga idanunta "yaya suke son tayi da rayuwarta duk abinda suka fad'a mata tasan gsky ne amamn har yanzu zuciyarta ta saka mantuwa akwai wani abu da yake tsaye acikin zuciyarta ta rufe idanunta ta sake jingina jikinta da pillow daya saka mata a bayanta tana jujjuya maganganun yaranta tana yin filla filla dasu tana son kawar da bukatarsu amman tasan gsky suka fad'a mata bata taba daukar ya'yanta zasu girma da son danginta irin haka ba kasancewar suna cikin dangin mahaifinsu."

*****
mrym zaune a d'akin hjy zulaiheart tana shirya mata  kayanta  da mai gugansu  ya kawo  tana tsaka da aikin aunty shahida  ta shigo bakinta d'auke da sallama ta amsa tana gaisheta fuskarta d'auke da murmushi  "aiki kike yi ne haka  amaryar  ATA tayi mgnr cike da zolaya " sannu da zuwa auntynmu me kika zo mana dashi ta fadi haka dan kawar da maganarta ,cikin dariya aunty shahida ta zauna akan sofa tana cewa "kayan dadi da bazasu fad'u ba maryam tayi murmushi yasu madina kwana biyu shiru  kmr anyi ruwa an dauke "ke dai bari madina exam ne ya sakata gaba Amman Ina ganin ma zuwa wani sati zasu kammala ".

"okay to Allah Bada sa'a "Ameen ta amsa tana cewa "wata shawara nazo miki dashi a tsakaninki da ATA jin haka yasa ta dan tsaya ta kasa cigaba da abinda take hankalinta gbdy ta tattara shi kan aunty shahida " Ina sauraron shawara daga bakin aunty nah maganin kukana " Marym please ki sanya kunnen baseera akan abinda zan fada miki "ta sake mika mata hankalinta sosai " kin dai san halin wanda zaki aura  yana da kyau ki dan rage wasu abubuwa sannan ki koyi wasu abubuwa nasan kin fahimci abinda nake nufi ki zamo mai kwantar da kai da iya girke girke dan bazance girki ba ,daga ke har nana na fuskanci Kuna da matsala ta wannan bangaren dan haka ki dage ki koyi kowani irin girki da tsafta duk Inda zaki kasance acikin gidanki  the next thing shine kamshi domin shi din ma'aboci son dadd'adan girki ne da son kamshi ki zamo mai hakuri da lallabashi domin ta haka zaki yi saurin dakusar da duk wani taurin Kansa abubuwan social media Shima ki rage "dan kinsan bazai yarda dashi ba wasu daukar hoto kullum ana d'aurawa a duniya Shima bazai yarda ba  ".

"shikenan naji aunty inshallahu Kuma duk zan d'auki shawararki ki dai tayani da addua biyyaya zanyi a aurena da ya Adam Allah yasa ya zamemin alkhairi "Ameen byn biyyaya har da soyayya sai kunyi aure zaki fahimci hk "Kai aunty babu wata soyayya "  ki rubuta ki ajiye a Inda bazai goge ba ko na mutu sai kin fada "Kai aunty shahida bana tunanin yaya zai soni a yadda yake nunawa ni dai zanyi iya yina kawai "karki tsaya iya yinki kiyi kokari ki canzasa gbdy ta yadda zai manta  da mafar.."

"wannan Kuma  impossible aunty bazata iya ba  " suka ji sautin muryarsa acikin dodon kunnensu a tare suka juyo a firgice  suka  Kalli Inda yake tsaye sanye da farar jallabiyya mai gajeren hannu ajikinsa gashi kan nan nashi sai sheki yake zubawa  tamkar balarabe kallon second biyar mrym  tayi masa tayi saurin  d'auke kanta sakamakon mugun kallo da yake jifanta dashi  .matsowa kusa da aunty shahida yayi sosai  fuskarsa a hade babu alamun murmushi "babu abinda za'a ta iyayi wanda zai dakusa wannan soyayyar dake dawainiyya da zuciyata da gangar jikina   Ina son princess so mai girma sannan gara ki fad'a mata babu iskanci da sakarci a gidana  dan bazan dauka ba ."

Take kwakwaluwar  mrym  ya shiga ceculating abinda mgnrsa take nufi  kenan akwai  wacce yake so  aka takura masa aurenta ?take jikinta ya kama kyarma ya ware hannuwansa duka cikin jin dadi  "okay a she fa bata san da wannan zance ba fa ?"gsky ya kama ta san cewar  akwai wata acikin zuciyar Adamcy Kuma ko ba dade ko bajima muddin na ganta zata kasance cikin rayuwata bukatata na ganta domin nafi bukatarta fiyye da komai  ."

gbdy mrym dake zaune taji babu dadi acikin ranta "tabbas wannan shine dalilin dayasa bai maraba da aurenta  wani bakinci ya ziyarci qirjinta ta mike tsam zuciyarta cunkushe ta nufi kofar fita tana fita aunty shahida ta soma magana cikin fushi "wai me yasa kake yin hk ne sam bai dace ba?  "me Kuma nayi byn gskyr dake cikin Raina na fada gara tasani ?  ''idan kana yiwa mrym hakan bazamu ji dadi ba , rainmu  zai dinga  baci fiye da bacin ran daka gani yanzu acikin kwayar idanuna ,dan bazamu  yarda ka fifita wata banza can akanta ba banzar ma da ba gskiya bace  .

"duk son da nake   maka zan   iya ajjiyeshi gefe   na hukuntaka hukunci mai tsanani akan mryam ,kada  ka sake makamancin wannan maganar a gabanta  wannan ya zamo Karo na karshe  ya jiyo sautin mahaifiyarsa wacce ta shigo byn fitar mrym nunfashi ya fesar yana cewa ''relax  sweetheart  insha Allahu  an gama ya fice ya barsu   "Allah ka shirya Adamcy na rasa meke damunsa "  meke damunsa kuwa ban da iskanci aunty shahida ta katse hjy zulaiheart , nifa wani lokacin sai naji kmr Abar had'in nan kar yazo ya bata zumunci   ."babu wani zumunci da zai bata wannan auren Allah ya rigada ya hadashi tunda gashi har ya amince ayi ,da yarda Allah rayuwar gaba zatai dadi "Allah yasa inji cewar aunty shahida.
Da fari  baba qarami hjy zulaiheart taso ta kira ta sanarwa hukuncin data yanke kasancewar shi yana bangaren baya inda mallakinsa yake sai dai tayi tunanin ta fara sanarwa baba Babba kasancewarsa babba a tsakaninsu a yanzu   saji  daga bakinsa
tayi murmushin Jin dadi dan tasan baba qarami zai ji dadi sosai  idan labarin auren adamcy dan kusan kullum sai yayi mata maganar ."

*****
a natse ta fara  neman   layin qanwarta    hjy nuriyya   wacce ta kasance abokiyar wasanta iyayensu uwa d'aya Uba d'aya Kuma akwai shakuwa  sosai a tsakaninsu tana  zaune  a kasar  london  tun aurenta har zuwa wannan lokacin acan ta haifi yaranta duka iyakarta da naija ziyara ko wani sha'ani mai mahimmam. suka gaisa cike da farinciki  Inda hjy zulaiheart take sanar mata batun hada Adamcy aure da maryam  " Kai  alhamdulillah masha Allah gsky abu yayi kyau  sosai Allah ya sanya alkhairi ya  nuna mana lokaci ,wannan karon zanyi k'okari na shigo kasar  kafin lokacin  domin ayi biki dani ".

Hjy zulaiheart tace "gsky kam anyi  bukukuwa duk baki  samu  damar shigowa  naija ba "haka ne kam  amman inshallahu  zan shigo wannan bikin nayi ne no any excuse ta k'arasa maganar tana murmushi suna cikin hirar hjy zulaiheart  tace "nuriyya wai kuwa  kina jin  labarin bilkisu  ?dip hjy nuriyya  tai tmkr an d'auke wuta nepa tana jin  wani irin daci acikin ranta sai data yi kusan minti biyar sannan tace  "bana Jin labarinta Kuma bana son na  ji labarin Inda take ,  kuma  Ina son ku shareta ku cireta acikin zuciyarku har abada  Kmr yadda mukayi yarinyar data nuna mana bamu Isa daita  ba ,sannan  bata  sonmu  ta zabi rayuwa ko babu mu me yasa zamu damu daita ?

"ni dai duk wanda zai nemata acikinku yaje amman  ni nuriyya bana ciki kuma babu hannuna  babu kafa ta ciki  "naunayen ajiyar zuciya hjy  zulaiheart  ta sauke tana cewa " dan Allah nuriyya kiyi hakuri ko babu komai rayuwarta qaddara ce Allah ne ya d'aura mata wannan rayuwar babu yadda zata gujewa qaddararta ,wallahi  duk sanda ta fado min sai na zubar da hawayen tausayinta , da nasan Inda zanganta  wallahi zan nemota  .
"Kune fa kuka damu daita ko nace ke dan duk  cikinmu babu me zanceta wallahi sai ke ,bata ga wuya bane shiyasa bata dawo ba, wallahi nafi son rayuwa ta juya mata baya ta dawo tana kuka  tana  rokonmu  kullum mummunar adduar da nake mata kenan sannan Ina adduar duk tsanani karta dawo mana da zuria Kmr yadda hhyrmu take addua ."

"wannan addua ta rashin haihuwa a tsakaninsu batayi ba ku daina mata mummunar addua gskiya "ai babu abinda ya kamaceta da wuce mummanar addua " yanzu dai kiyi hakuri  muyita mata addua da fatan alkhairi a duk Inda take lokaci nata tafiya a lisafinsa shekaru ashirin kenan rabonmu  daita , kiyi hakuri dan mu barwa Allah komai sannan muyi mata adduar Allah yasa ta waiwayo mu cikin koshin lafiya naunayen  ajiyar  zuciya hjy nuriyya tayi  sannan tace  "shikenan big sister ai abinda  kikace shi zamuyi  cike da qauna yar'uwarta hjy zulaiheart sukayi  sallama da yaruwanta suna gama wayar uncle Umar ta kira ta sheida masa tana son ganinsa  ."

Ranar asabar   da misalin karfe hud'u na yammaci  baba bAbba   yazo   bisa Kiran da hjy zulaiheart tayi masa , byn sun  gaisa   hjy  zulaiheart ta karanto  masa hukumcinta   akan ATA cike  da farinciki uncle Umar yace "masha Allah wannan hukuncin yayi  Kuma mun gamsu dari bisa dari dan burin mu bai wuce muga adam ya ajiye iyali ba  ,bugu da Qari zaa sake  karfafa zumunci a tsakanin   inshallahu  zan sheidawa sauran yan'uwana sai mu saka ranar da zamu ga alhj saidu  dan  zamu so a daura auren nan  kusa". "wannan  maganar tayi Kuma naji  dadinta  sosai dan  haka a fara sheidawa  baba qarami dan  nasan murnarsa sai tafi  ta kowa domin duk yafi  mu d'auki son ganin  Adamcy  yayi aure ta k'arasa maganar tana murmushin jin dadi  "ai kuwa daga nan ma bangarensa zan shiga na fara sheida masa  Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana lokaci "Ameen ya Allah,Allah  kadai yasan murnar da zaiyi  idan yaji  ya sha lemu da kayan snaks din da'aka jera masa suka zarce da  tautaunawa  kafin daga bisani sukayi  sallama ."

Baba qarami   na zaune akan  kujera me zaman mutun uku  sai ga baba Babba   wanda ya kasance yaya  garesa Kuma Kani ga   mahaifin ATA yana ganinsa ya saki fuska tare da farincikin ganinsa  ya d'an  mike tsaye cike da girmamawa ya bashi hannu  suka gaisa sannan ya nuna masa mazauni atare suka zauna "sannu da zuwa yaya ! "ya gida da iyalin  fatan  suna lfy?"alhamdulillah kowa Lafiya yake ya naka iyalin  ?"Suna lfy ya bashi amsa yana murmshi ya mike ya  dauko masa abun sha "bazan sha komai ba daga bangaren hjy zulaiheart nake na sha "  .
suka yi shiru na second biyu sannan baba babba ya fara magana a tsanake " kamar yadda na fad'a mk  daga bangaren hjy zulaiheart nake tayi decide ta had'a Adam aure da diyar kaninta abdulrauf " what ?"when ?ya fada a matukar rude yana Jin wani  irin abu ya  caki kahon zuciyarsa , yayi saurin runtse idanuwanshi "zulaiheart na bukatar wannan labarin ya zamo Kaine ka fara jinsa   bisa kokarinka na son ganin adam ya ajiye iyali dan haka nan da sati me zuwa zamu gana da yayan mahaifin yarinya alhj  saidu  ."

shiru  baba qarami yayi har sanda yayansa ya dasa aya  ya mike tsaye"to ni zan wuce duk abinda ake ciki zan kiraka a waya a fusace baba qarami   ya mike Shima  yana cewa "yaya wannan wace irin maganar banza ce kazo min dashi  sannan kana k'okarin sa kai ka wuce ka barni  ? yayi mgnr  a fusace yana sa hannu ya daki center table din dake tsakiyar falonsa wanda ke d'auki da ruwan lemu kala dabam  dabam ,nan take wasu glas cup  suka  tarwatse yana huci yake kallonsu "yanzu ni dana cin burin ya zabi daya daga cikin ya'yana ya aura shine dan munafurci zata hadashi da diyar kaninta saboda son Kai irin nata ?

"ya'yana  yafi  dacewa Adam  ya aura ba wannan yarinyar ba ya sake dukan table wanda hakan yasa gbdy ahlin da ke numfashi a part din suka bayyana" burina bai wuce ya'yana ko jikokina su had'a  iri da dashi ba yayi mgnr yana kallon cikin kwayar Idanu dan uwansa  ."me yasa zaka fadi haka idris?  "eh na fad'a yayi mgnr yana cakunar wuyan dan'uwansa da iyakacin karfinsa  yana maxurai  abinda bai taba faruwa ba a tsakankanisu ,hindatu wacce suke kira da hindu     ta samu guri ta zauna tana kallonsu zuciyarta na rawa dan ta dade a tafkin qaunar ATA mahaifinta ne ya hana a fito da soyayyar a cewarsa yana jiran lokaci yau ga lokaci ya zo masu a wani iri .
sauran kuwa hankalinsu ne yayi kololuwar tashi ganin yadda mahaifinsu ke rike da wuyan dan'uwansa uwa d'aya Uba d'aya .Wallahi yaya Kai kare ne  da bai san ciwon kanshi ba ! "shin ya'yana basu dace dashi bane ka  bani answer ?uncle Umar yayi shiru kawai yana kallon hannun uncle idris dake rike da wuyansa batare daya ce uffan ba.

"me yasa kazo min da  wannan banzar labarin mara dadin ji ?ya k'arasa maganar yana sakar masa wuya yana dubansa yana huci "saboda mu bamu Isa ta hada jini damu ba shiyasa ta za'ba masa acikin dangi ta ?"to me zai faru idan na hana auren ?"zan hana wannan auren ta karfin tsiya yayi mgnr yana d'aga hannunsa sama  sannan  ya dungule ya  naushi bangon  falon sai da gurin ya tsage  ya tsaya yana huci da kallon wani bangare ."

Baba babba ya tsaya abayansa hankalinsa a matukar tashe  " maganarka gaskiya yayanmu suka fi dacewa da aurensa   sai dai kayi hakuri dan'uwana bana tunanin da wata manufa zulaiheart ta had'a  wannan auren   ,idan baka manta ba  shekara nawa ana fama da yaron nan akan ya fitar da mata yayi aure  bana  tunanin zata ki had'a  zuria da daya daga cikinmu  sannan da kasan kana da wannan burin me yasa baka fito dashi ba ?

Baba qarami bai ce uffan ba illa numfashi da yake sauke da sauri sauri gumi na karyo masa  "dan   haka kayi hakuri karka bari wannan matsalar ta zamo Silar da za'a samu matsala ka bar  wannan burin  bayan anyi wannan auren sai ayi maganar a had'ashi da daya daga cikin yaran".
"Kai kare idan ka sake yin min  wannan maganar  banzar sai  na datseka gbdy Komai naka   banga ta yadda nawa burin zai zama daga baya ba muddin d'aya daga cikin yarana basu yi nasarar shiga sawun farko ba babu wacce ta Isa ...."
"kayi hakuri ka yafe min ban  fad'i  haka dan quntata  maka ba ya fadi hk kasancewarsa me saukin Kai sannan marason tashin hankali  yafi son yayi rayuwarsa cikin  salama  duk maganar da baba babba yake sam baba qarami bai juyo ba  ",shi wannan  Karen  zai  wuce sai kaji daga garesa sai dai  ya kamata ka sakin ranka dan wata rana ....saurin d'aga masa  hannu baba qarami   yayi still bai juyo ba sai dai  qirjinsa sai faman bugawa yake  Uncle Umar  ya juya cike da matsanacin firgici da  yanayin dan'uwan nasa ."

sai lokacin  baba qarami ya juyo yabi bayansa da wani  irin  mugun Kallo   Idanunsa a waje  har sanda takunsa ya kai uku bai juyo ba haka  shima baba qarami   bai daina kallonsa  ba .a sanyaye  fahad dansa   yabi bayan baba babba zuciyarsa na rawa dan shi kansa ya koka da  abinda mahaifinsa yayi  ya raka uncle Umar  sai dai bai Kai shi har bakin get ba a tsakiyar hanya ya barshi yana bashi hakuri "karka damu fahad na gode allah yayi maku albarka ya amsa da Ameen ya dawo part dinsu da sauri  .

falon ya d'auki shiru na tsawon lokaci yana tsaye yana  tunanin  bayanin daya samu daga bakin dan'uwansa  a yanzu   wanda  yake jinsa tamkar dalma acikin zuciyarsa , "uhmmmm yanzu dai ta  nuna mana cewa itace  uwar  Adam  Kuma ita  kadai ke da iko akan shi ?sai mugani  idan shi din d'an mace ne  Baba qarami yay  maganar yana jan tsaki a fili tare da watsa katuwar harara da mugun kallo kamar  tana gabansa fahad     ya  d'auki farin  glass cup ya tsiyaya masa   tattacen  ruwan inibi  ya mika masa "kasha baba kaji sanyi a ranka  yasa hannu ya Kar'ba ya  rike shi gam a hannunsa  sai dai bai sha  ba haka zalika bai ajiye ba."

"zan iya kasheki akan wannan haukan da kika yi zulaiheart  domin Ina da tanadi da buri akan adam ya karasa maganar yana filinging da  cup din hannunsa a fusace Wanda yasa take  yaransa maza da mata tare da matarsa suka sake  shiga rud'ani   cike da matsanacin firgici suna kallonsa gabansu na faduwa ban da   Hindu    data samu  guri ta kame akan kujerar da mahaifinta ya tashi  zuciyarta tafi ta kowa zafi da tuttukin bakinciki tare da shiga tashin hankali" Fahad ...." !
  ya kira sunan dansa Wanda aka kira da hkn   ya d'ago ya kallesa a matukar  tsorace batare da yace komai ba "abinda na fada Ina nufi har cikin zuciyata gara ta bar duniya ko ita yarinyar ta bar duniya akan rasa burina yayi maganar yana nuna sa da d'an yatsansa "wannan shine Karo na sau babu adadi da take kawo mana tashin hankali tun dan'uwanmu na raye dan haka Ina son kasheta na huta da ganinta a doron duniya  muddin ba daya daga cikin ya'yana  adam zai aura ba ."

daya bayan daya suka shiga kallon junansu cike da mamakin jin furunci mahaifinsu hatta hindu wannan karon atsorace take kallon mahaifinta  ta gigita kwarai  da gaske "a kullum kokarina naga na kawar daita a duniya darajan halakar da nake son qullawa adam yasa na barta  ya karasa maganar a kausashe .yayi taku daya biyu ya tsaya gaban hindu   yana kallonta "kece ya kamata ace kin auri adam ba wannan yarinyar ba kije kiyi rayuwa tamkar sauraniya   a gidansa ki taka kowa yadda kike so sannan ki juya duk Wanda kika ga dama  wannan hannun nawa babu abinda yasani a halin yanzu kamar ya wahalar da zulaiheart  ya gigita ta hanyar azabtuwa mai muni  ,ya matso kusa da hindu   Sosai suna fuskantar juna "wannan karon fuskarsa da murmushin mugunta akanta  "ke hindu ko zakiyi iya karfin halin kashe min zulaiheart?

Wani sanyayyayen murmushi ne ya bayyana akan fuskarta wanda mahaifinta ne kawai ya fahimci manufarsa ganin yadda ahlinta suke kallonta a tsorace yasa tayi saurin waskewa  tace "baba me yasa kake mgn fiyye da kaida ?gsky sam sam hakan bai dace ba tayi maganar tana kawar da idanunta gefe al'amun bata ji dadi ba  gumin da ya tsatsafowa   sauran yanuwanta suka shiga  gogewa suna sauke numfashi da ajiyar zuciya atare  Jin abinda tace daman km ita kad'ai ke iya fadawa mahaifisu mgn kai tsaye batare da shayi komai ba , a hankali ya juya yana taku cikin tsananin damuwa da tashin hankali   suka juya gbdy  suna kallon bayansa har ya shige bedroom dinsa yana shirya yadda zai kawar da hjy zulaiheart ko mrym daga doron duniya   .."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

              
               Page 13

"Baba   qarami  na  kwance har  kusan   tsakiyar  dare  ya kasa runtsawa  dan  sam bacci yaki  zuwan  masa sai  faman  juyi  yake  akan  makeken  katifarsa  ,yayinda matarsa   hjy  aljannatu  ke d'akinta  kwance   tana  sharar  bacci  amman  shi  kuwa  baba  qarami sai  tufka  yake  yana  warwara ya d'an  zabura  ya  mike  zaune  daga kwanciyar  da  yay, ya  had'e hannunwansa  duka  waje  d'aya "babu  tantama  hjy zulai tana da manufar  had'a  wannan  auren  yasan  tayi  haka  ne dan  kar wani acikinsu  yaci arzikin   d'anta , kunga   idan  ta had'asu  aure  da  diyar   d'anuwanta dole dai  arzikinsa yana tare  daita , dan da  zarar mrym  ta  haihu dashi   komai  na adam zai  dawo  nata  gbdy  zuwa yanzu dai  bai san abinda ya kamata  yayi  ba  ko hanyar  da   zai  bullo  masu   a maida auren  Kan  diyarsa ."

Sosai  kwakwaluwarsa  tayi  zurfi cikin  tunani  neman  mafuta har bai  san  sanda  hindu ta shigo d'akin  ba ,  ta  matso  kusa dashi ta tsaya tana  jijjiga baba  qarami  wanda  yayi  nisa cikin  duniyar  tunani "baba  baba !! " ta  kira  sunansa  har  sau biyu  ajere   sannan  yayi  firgigib  ya dawo haiyacinsa " wai meye haka  baba?" me yasa  zaka  damu  kanka akan   wannan 'yar qanqanuwar matsalar ?"  baba qarami  bai  iya amsa wa  ba sai  zuba  mata rinannun  idanunshi  da yayi yana dubanta   har  lokacin yana maimaita  abinda  ta  fad'a " ai a wajensa  wannan  ya wuce gagarumin  matsala  ba qanqanuwa ba  ko ita  kanta  tasan da zaman  haka  ta  dai  fad'a ne  dan  kwantar  masa da hankali  shi  kuwa  hankalinsa  bazai  ta'ba  kwanciya ba  matukar  ba  ganinta  yayi a matsayin matar adamu ba ."

"Dan   girman  Allah baba ka kwantar da hankalinka  mubi  komai a hankali  idan  muka  bari suka fahimci wani  abu  attare damu bazamu iya  nasara  akansu  ba "  cikin wani irin murya  mai  gyaraye da tashin hankali  had'e  da rud'ani  yake furta  "bazan  iya  ba hindatu , bazan  iya kwantar da hankalina  ba muddin  ba  ganinki  a gidan  adamu  nayi a matsayin  matarsa  ba  ,maganar  aurensa  da  mrym    ta dokeni  fiyye da tunaninki  ,Allah Allah nake gari ya   waye  naje  ga  zulai ayita ta qare  domin   kece kika fi dacewa da  Adam  ba wannan yarinyar ba dan  wannan  tsantsar muguta ne  kawai  take  son  nunawa"kai dai  baba ka  dan  boye damuwarka baba" .

    D'akin  ya  d'auki  shiru  tamkar  babu  wasu halitta  acikinsa   sai  na  qara  ac  dake  aiki  da kuma saukar  numfashinsu  haka  zalika baka  jin  motsin  komai  daga  sai  na  tsuntsaye   dake  shawagi  kasancewar  a  gra suke  hindu ta sauke numfashi tana mai kamo  hannunta  mahaifinta  cikin  nata "idan  kaje  me  zaka  cewa  mami  akaina ? " zan so nasan   abinda  zakace  baba  idan  ma  hali  kaje tare dani  ayi  komai  akan  idanuna  shekaru  sha biyar kenan ,  tun   inada  shekaru  sha  shida  nake  dakon soyayyarsa  bazan  iya  jurar  rasashi  ba, bazan zuba idanu  wata ta mallakesa ba "zan fad'a mata komai akan  soyayyarki  ni   ko  ta  biyu ce kizo  bazan damu   ba  burina  ki  kasance matsayin   mata  acikin  gidansa , ki zama tmkr sauraniya, ki yi yadda kike so  nima  nayi  yadda  nake só da  kamfanunuwansa  ."" nan  take ta  had'e  fuska  tamkar  dariya ba  muryarta  a  kausashe  ta  cigaba da mgn "muddin  a ta  biyu  zanzo  nasan   bazai ta'ba aurena ba , ya  adam  fa yana da tsari  acikin  rayuwarsa  shi  din ba mutun bane  kamar sauran mutane bashi da raayin tara mata "wa yace  miki  bashi  da  raayin haka ? zai yi raayi   dan uwarsa  Allah dai ya kai mu gobe tare zamu wajen  uwarsa  kafata  kafarki ."

Baba  qarami ya   mike  tsaye ya goya  hannunwansa abaya  yana  girgiza  kai yana duban hindu kafin daga  bisani  ya matso kusa daita sosai  ya  soma mgn   can  kasa kasa  kusan mintuna goma yana mata  mgn murmushin  jin dadi  né ya  bayyana akan fuskarta " idan bata  yarda ni na zama  matarsa  ba  I will  killed mrym  idan ni ban samesa  ba  to babu wacce  zata mallakesa anan  gidan  duniya yadda take  mgnr zaka fahimci da gaske  take  kuma  har cikin ranta abinda  take nufi  kenan ganin byn maryam ."

Washegari  da   misalin  karfe  goma na   safiya  a kofar  shiga  bangaren  hjy  zulaiheart  tayi masu  kai tsaye a babban  falon  gidan suka  iske  mami zaune  yayinda  d'aya  daga  cikin  masu aikinta ke zaune   tana  mammatsa  mata  yatsun  kafafunta sallamarsu baba  qarami tasa mami  dauke idanunta  daga  Kan tv ta maida kansu  tana  sakin fuska  sai  dai kallo d'aya tayi  masa  ta  fahimci  akwai damuwa  atattare  dashi  ,aranta tayi addua  allah yasa ba wata matsalar  bace  ta taso , ta amsa sallamarsu  tana cewa "sannuku  da zuwa !" baba  qarami  ya samu waje ya  zauna akan kujerar  dake  fuskantarta yayinda  hindatu  ta zauna a kasa kan kafet  a gaban mami ta  sunkuyar da kanta  kasa  tmkr mai neman  gafara  tare da gaishe da mami cike da ladabi  ta amsa  tana  mami  ta maida hankalinta ga baba qarami   tana   nazarin fuskarsa sannan ta kalli yarinyar  dake zaune a gabanta tace "salaha tashi kije   Ki  bamu  guri  cikin  sauri  yarinyar  ta mike tare da fadin  "tô !"

       Mami  ta sake maida hankalinta sosai  garesu sannan ta fara magana a natse "baba qarami fatan dai lafiya  dan naga yanayinka  ba kamar yadda na saba ganinka ba  yace "lafiyar dai da sauki "ta gyara zamanta cikin tsananin damuwa "daman dai na lura da hakan dan ba haka yanayinka yake ba kai din mutun ne mai faram faram duk sanda za'a ga fuskarka cikin murmushi take tô ina jinka fad'a abinda ke  tafe da kai ."

Naunayen ajiyar  zuciya ya sauke yana sake gyara zama  yace "zulai  jiya baba babba yazo min da wata magana akan hukuncinki akan Adam"  ta gyada kai tana  sauke  numfashi "haka ne nasan zaka fi kowa jin dadi "tabbas  naji  dadi  sai  dai   wani  hanzari ba gudu  ba nima na dade ina son had'asu  aure da hindatu   "mami tayi shiru tana dubansa da hindu dake   zaune  tana  nazarinta tana son gano wani abu atattare  da hindu domin dai ita din macece mai tsananin  baseera tare da saurin karantar mutun sai data  numfasa sannan tace "ita hindatu tana son shi ne ?

"tabbas  tana tsananin sonshi na tsawon shekaru tunda tashi da soyayyarsa ta tashi ni ne mutun na farko data fara sheidawa da fari na nuna mata illar rayuwar data jefa kanta na afkawa soyayya da qarancin shekarunta  alokacin na tmbyeta meye dalilinta  na son shi  ? me  ya  dauki hankalinta akanshi  ? tace ba dan yana dukiya  da kyau ba ,yau da  zai  wayi  gari  bashi da  komai  bashi da hannu bashi da kafa  koda akan titi zasu rayu zatai  rayuwa dashi kawai son shi ta keyi dan  Allah alokacin shekarunta shashida né  kawai  wanda ni nake ganin bata san  ma me take ba bama tasan meye soyayyar ba yasa take fadin haka ahankali baba qarami ya fayyacewa  mami komai akan soyayyar da hindu ke ma ATA  babu abinda ya rage numfashi mami tayi ta saukewa tana girgiza kai cikin tausayawa tana kallon hindu data sake dukar da kanta kasa sosai ."

"Masha allah naji dadin wannan abu sosai soyayya mai hade da zumunci allah ya bamu ikon sada zumunci dan allah ba dan kwadayin ko neman wata biyan bukata ba ". ta sake numfasawa ta cigaba da magana  "nima daman tun farko burina kenan adamcy  yayi aure biyu"  ahankali baba qarami ya kalli inda hindu take wacce mgnr mami yasa ta dan dago kanta mami ta cigaba da magana "zan yi iya  kokarina hindu na kawo karshen damuwarki duk da adamcy baya da raayin ajiye mata biyu amman zanyi convincing   dinsa  domin  kawo farinciki arayuwarki da  yarda  allah ."

    da  sauri  hindu ta kalli mahaifinta shima din ita yake  kallo domin dai yasan diyarsa da tsananin kishi zata fi bukatar ganin ita kadai ta mallakesa Kmr yadda ta sheida masa kallon da takewa mahaifinta só take yace a fasa auren da mrym gbdy ya aureta  shi kuwa baba qarami a hakan ma maganar tayi  masa dadi "fatana  mu hadu muyi addua akan lamari sannan mu nemi zabin allah allah kuma yasa  gogan naka ya yarda ya amince ya  hadasu su biyu din , ku bani lokaci kadan zan yi magana dashi duk abinda mukayi dashi zan nemeka da  wannan maganar suka kawo karshen zance sukayi  mata sallama ."

   Suna shiga  dakin baba qarami   hindu ta fara zubar da hawaye acikin slow voice tace " baba ina ji ajikina ya adam bazai aureni ba dan dai idan amincewarsa zaa tsaya nema wallahi bazai ta'ba amincewa ba bugu da qari ni banason sharing dinsa da kowa nafi son ni kadai dan sam ban dace da zama da  wata aba kishiya ba zan só mu rayu dagani sai shi  ta karashe mgnr tana shesheka murmushi baba qarami yayi tare da fadin "hindu kalleni nan " ta tsura masa  idanunta Kmr yadda ya bukata "ki kwantar da hankali babu wani abu acikin ya haduku biyu din amincewarsa shine abinda muka fi bukata a yanzu dan zaki iya kawar daita byn auren ki zauna ke kadai keda kike da baiwa iri iri nasan zaki bawa babanki mamaki haka dai baba qarami ya tasa hindu a gaba yana kwantar mata da hankali babu laifi hindu ta saki jikinta  tare da  karfafa zuciyarta sai dai ta rantse muddin bata samesa babu wata mace da zata mallakesa tana raye ."

****
Sanye  ATA  yake  cikin  farin yadin vol  mai shegen haske da tsada  a hankali yake  taku yana gyara  zaman  hullarsa  baki  haka zali takalmin dake sanye da kafafunsa black cover shoes ne tsintsiyar hannunsa daure  da  agogon rolex   yana dumfaro falon kamshi turarensa ya mamaye koina Kmr  shagon turare yana gama qarasowa yace wa hisham "muje ko ".kai me yasa bakasan ka bawa mutun rai ka bashi hakuri ba duk lokacin dana bata ina zaman jiranka da muje ko  zai qare  " ina laifin kace hisham Afuwa kayi hakuri muje abokina km danuwana."
Dogon tsaki yaja kawai batare dayace uffan ba .

"matsalata da kai kenan ka gama bata lokaci amman zaka wani jawa mutane tsaki still bai ce komai ba 
ya nufi hanyar dakin mami tana zaune ya shigo ta  dago a natse tana duban kofar ganin shine cikin shigar da tafi qauna ta saki fuska cikin tsananin farinciki  tace "Masha allah adamcy nah kayi kyau sosai allah yayi maka albarka  ,sai dai wannan uban wanka  da kashi haka kmr yau  daurin aurenka,  ai ko yau né daurin aurenka sai  iyakarka hk kai  ni kamar ma har da hoda ka shafa ko? Tsuke bakinsa yayi  dan tsokanar sweetheart dinsa na yau yazo da wani salo ana zaman lfy me zai yi da wani hoda shi ba mace ba  ."

"sweetheart ni zan fita amman zan dan jima ban dawo ba dan yau zaa bude kamfanin tace mai petir da sinadarin gas "Alhamdulillah masha ,allah allah yasa albarka  arayuwarka data kasuwancinka allah ya  tsare  min  kai  ,yadda zaka fita lafiya allah ya dawo da kai lafiya  sharrin mutun da aljani Allah rabaka  dashi  yace "Ameen !atakaice  ya juya a natse yana taku  tmkr wani jinin saurata "sai na dawo sweetheart  ." a dawo lafiya adamcy nah ta fad'a tana cigaba da kallon bayansa "yau  tsawon  kwana uku kenan tana   son sheida masa bukatar baba qarami amman ta kasa, ita  kanta tana jin tsoron tunkararsa , tayi  dukkanin tunaninta ta rasa ta ina zata fara  shigo  masa da maganar , auren mrym ma  da yaya ya amince yanzu  kuma ta sake kawo masa mgnr wata tasan tattara wa  kawai zai yi ya gudu ya barta dasu  ."

har ya kai bakin kofa yana shirin d'aura hannunsa akan handling din kofar ya  tsaya cak  ya waigo
bayansa adaidai lokacin  da mami ta sauke numfashi  da  girasa ya tambayeta  ,ta girgiza masa kai kawai tamkr   wata   marainiya "ko akwai damuwa ne ?ta sake numfasa wa kana tace " babu  komai  adamcy nah  ina dai kallonka ne kayi min kyau sosai shigar ta amshi jikinka "me  yasa  bazanyi amfani da wannan damar  na fad'a masa  bukatar kanin mahaifinsa ba ? tayi mgnr acikin ranta  da sauri zuciyarta ta gargadeta "karki soma yace ya fasa auren  gbdy gashi goben  nan zaa je neman masa auren mrym  numfashi ya fesar "saboda Ke nayi shigar dan nasan zaki ji dadi gaahi yau  juma'at  "ai kuwa naji dadi kwarai da gaske na kuma  gode sosai allah ya baka zuria masu  albarka yadda kake ji dani kake min biyayya Allah baka masu yi maka bai amsa ba ya sa kai ya fice daga dakin  zama ta cigaba da yi tana tunanin  mafuta zata jajurce da tsayuwar dare domin neman zabin allah  dan shine kawai mafuta agareta."

Aunty  abinda  na gama  jin bayanin  ibrahim  taji kafafunta suna  barazanar kasa daukarta lokaci  daya  zuciyarta na barazanar  tarwatsewa Ibraheem ya matso yana girgiza Aunty abinda wacce ta dawo tmkr mutun mutumi "abida abida!! lafiyarki what's wrong abida?abida tayi shiru kawai tana sauke numfashi batare data amsa ba " baba babba zasuje nemawa ATA auren maryam  gobe goben nan idan dai ba karya kunnuwanta suka jiye  mata ba haka taji ya fito daga bakinsa  " ibrahim me naji kace ? tana bukatar ya sake maimaitawa babu bata lokaci ya sake maimaita mata " wai tukunna wace maryam zai aura ?"maryam dai wacce Ke zaune a gidan mami diyar  kaninta  ita zai aura  "da gaske ka tabbatar mrym zai aura ? ya gyda mata kai kawai  yana maida hankalin Kan wayarsa dake qara "

"ina sam sam wannan aure bazai taba yuwa ba ta runtse idanunta da karfi  ATA jarumin nmj né uwa uba kyau da natsuwa da Kamala ga tarin dukiya dasanin yakamata ai babu macen data dace dashi sai sultana gani yana mata wani irin kallo tayi saurin dawowa haiyacinta  sunanta ya sake kira tare da jawo hannunta ya zaunar daita akan kujerar daya tashi cike da rauni tare da yin kasa da murya yace "abida meke damunki ?babu abinda ke damuna nidai dan Allah kar aje neman auren nan wai ma waye ya hada wannan auren ?shi ATA din da kasan  ne ya zabi auren mrym din ?"ta karasa maganar cikin tsananin tashin hankali da bacin rai akan fuskarta ."

    "me yasa ?saboda me kar aje neman auren  ?"
Meye  damuwarki da aurensu ? kanta ta rike da duka hannuwanta ta fuskancesa cikin sanyin murya tace "sbd sultana né bazan só ATA ya auri wata ya bar sultana ba "ita sultana tana son shi ne ?eh ammm daman umma ce ke ...."sai km tayi shiru ta kasa qarasa mgnr. "auren nan fa kamar anyi shi an gama domin babu wani abu ko mahalukin daya isa ya hana wannan auren mami da kanta ta hadata wannan auren ,ATA nason yarinyar ko baya sonta wannan shine bansani ba amman zuwa neman aure wannan dole ne gara ma ki binne duk abinda ke ranki karki shigo da wata magana da zata janyo matsala cikin jin haushi tace "idan kuma rabon sultana né fa ?har ya bude baki zai bata amsar tmbyrta  wayarsa ta sake daukar  qara ya dauka yana duba screen din wayar sunan ATA yaga yana yawo cikin sauri ya mike ya dauka ya soma mgn yana juyawa zuwa kofar fita tana ganin fitarsa ta  mike tsaye ta soma zagaye falon tana maimaita abinda  ya  fada mata ashe kuwa zaayi wulakanci acikin gidan nan ko ta wani hali koda tsiya koda tsiya tsiya sai tayi duk abinda zatayi sultana ta shiga gidansa koda ata biyu ce ."

*****
  "Maryama kyakkyawar budurwa ce mai   kyan  gaske  doguwa ce sambal dan tsawonta bai sa  ta  rankwafa ba sai dai ita din ba fara  bace haka zalika baza'a  kirata  da baka kirin ba  chocolate colour ce  tsayinta ya fito  sosai  domin irin matan nan ne masu  shape din cocakola  tana da siririn  hanci  da manya  idanuwa masu  matukar d'aukar hankali  dan duk wanda tsautsayi yasa ya kalli  cikin kwayar idanunta sai ya kusan  suma saboda wasu sirrika da Allah ya hallita acikinsu masu kallon cikinsu  ne kawai zasu iya karar da yanayin da suke tsintar kansu ."

idan tayi murmushi kuwa zaka ga siraran wushiriyarta sama da kasa sun bayyana wanda  sune suke  qara  haskaka  kyawunta  ,ga gaban  goshinta kwance suke  da suma  luf luf !! duk  da kanta a daure  yake a koda yaushe da d'ankwali  amman kallo  daya  zaka  mata  ka  gano irin matan  nan  ne  masu  yalwan  gashi  sannan tana  da  kafa  mai kyau haka ma   yatsun  kafafunta zara zara ne  lullube  da farata masu matukar haske haka zalika muryarta idan tana  magana dan dole ka tsaya ka saurareta  kuma dole ka kalleta ."

Maryama ta  samu tarbiya mai kyau  daga  gurin  mahaifiyarta tayi  karatunta na   primary  har zuwa  matakin  jami'an  acikin jahar lagos  kuma   duk  akarkashin kulawar  gwanaty  , haka bangaren karatun  alqurni  baa  barta abaya ba  domin tun tana primary ta sauke alqurni  km hakan bai sa ta daina zuwa islamiyya ba idan kaga bataje ba sai dai wani aiki ne ya sha kanta ."

    kyawun maryama mai  tsayawa ne arai sai dai duk da wannan kyawu  nata bata da wani  tsayayyen saurayi  duk wanda yazo  neman aurenta dayazo sau d'aya zuwa sau biyu zai daina zuwa  batare da wani dalili ba  koma  karshe  taga  ya koma gurin kaulat diyar  kanwar   babanta  Aunty  hassana  gata   da kyau sosai na bugawa a jarida amman  mutane  na  mata  kallon  mai bakin  jini  abun yana d'an  damunta  sai dai bata nunawa dan ba samari bane a gabanta karatunta  ya fiyye mata  komai mahimanci  koda yaushe ka kalli fuskar maryama  zaka ganta a daure sakamakon rashin farinciki shiyasa  mutane  suke mata kallon mai  tsananin girman  kai   ."

Sannu  ahankali  maryama take tafiya tamkar tana  jin tausayin qasa  ko  macijiya dan babu wani karfi  a tattare daita cikin shiga ta Kamala  riga da sket dinki zamani da  kuma  dogon  hijab  mai  hannu  har  qasa  fuskarta  manne yake da bakin  nikaf  kalar hijab din jikinta wanda ya zame mata jiki a duk sanda zaka ganta a waje ko a makaranta   da wannan nikaf din zaka  ganta  sam bata yarda ta fita koina   batare dashi  ba  a cikin gidansu ne kawai zaka iya ganinta sadaka  yayinda  kafad'arta Ke makale da  jaka baka mai dogon igiya ,a zahiri kana kallonta kasan a matukar gajiye take dan yanayin tafiyarta ma ya qara yin slow sa'banin na sauran lokuta  sakamakon ranar data kwaso  gefe da gefenta  qawayenta ne  subai'a  da sumaiya ne suka sakata a tsakiyarsu ."

   Tafiya  suke  a natse  suna hirar  yadda  jarabawar su ta qarshe  ta kasance adaidai jeaction din ummahani street   suka rabu da kawarta  sumaiya tayi hanyar hagu da zai kaita unguwar daji suka cigaba da takawa da subai'a itama dai tafiya kadan sukai tayi dama wato markaz ya saura ita kadai ta cigaba takawa zuwa  unguwarsu market street batayi  wani  doguwar tafiya ba ta  qaraso  unguwarsu bata tsaya akoina ba sai   kofar  qaramin  get din gidansu  wanda  kallo daya zaka masa  kasan na masu rufin asiri  ne  dan bazaa kira gidan da gidan mai kudi ba haka zalika bazaa kiran gidan  da gidan  talaka fútik ba daidai misali  gidansu   ginin  da ne kuma ginin kasa ne  filasta  ne ya rufawa ginin gidansu asiri da kuma jamar dake rayuwa  acikin  gidan ."

a natse ta  shigo  haraban gidan nasu idanunta ya sauka akan kaulat  wacce  ta sha kwaliya cikin atamfar  chiganvy gold black touch of milk  ,kallo daya tayi masu  ita da wanda ta gani tsaye ta dauke   idanuwanta  zuwa wani bangaren  tana cigaba da tafiya dan wanda suke tsaye  da kaulat din ba bako  bane a wajenta tasha ganinsu tare  ."duk da   bilal  baya ganin faukarta amman  duk  sanda ya ganta yana rasa natsuwarsa a kullum burinsa yaga fuskarta yaga yaya take ,kasa cigaba da motsi yayi  daga inda yake tsaye  yabi tafiyar maryama da wani irin  kallo  komai nata a natse  most especially tafiyarta abun burgewa shi kam ina ma zata yarda ko sau d'aya ta bude nikaf din  yaga fuskarta yasan zatai kyau duk da  bai  ta'ba ganin  fuskarta ba."

Kaulat  na ganin irin kallon da yake mata  taja  dogon  tsaki yayinda maryama bata sake  duban inda suke tsaye ba ta cigaba da tafiya zuciyarta na matukar jin tausayi kaulat dan babu abinda tasa gaba sai  aikin tara masu samari  marasa inganci  a gida  maimakon tai concentrate akan  karatunta da kullum yake yin baya   sai ta maida hankalinta ga tara  samari  marasa amfani , tare suka  shiga  jss one  ,sukai  jss1 tare, sukai  jss 2 tare  sukai exam na zuwa  jss3  ta barta suka  wuce ss 1  ita  da sakina itama sakina lokacin  da zasu shiga ss2 tayi fail ta  wuceta  sai dataje ss3  sannan  kaulat   taje  ss1 sakina taje ss2   gashi  ita  yanzu daga rubuta jarabawar karshe ta fito  amman  ita  kuma har kullm cikin repeating take a qalla a tunaninta tayi repeating  ya kai sau hudu   allah yayi  mata jarabawa ta rashin ilimin  dan  babu  abinda tasani  daga bokon  har islamiyyar zero ce amman  ita da mahaifiyarta kullum cikin cin zarafin mutane suke barin ma ita  da tarasa dalilin dayasa suka  tsaneta suka tsani ganin wani  tare daita  duk wanda zasu gani tare daita wala mace wala nmj sai  sunyi qoqarin rabasu "

"Wai bilal meye haka ne ? ka wani karkace  kai kana kallon maryama gbdy ma ka manta ina tare da kai idan kasan ba wajena kazo ba na qara gaba dan na fahimci duk sanda kaga wucewarta sai ka maida attention dinka wajenta ko zuciyarka na kanta ne sai kayi min bayani  nasani ba wai ka raba hankalinka gida biyu ba alhalin ina tare da kai  "?

"wallahi da tun  asali ita na fara gani  to da babu abinda zai kawoni wajenki  yayi mgnr  acikin zuciyarsa  amman a zahiri cewa yayi  "meye laifi dan kalli halitta mai  natsuwa  ?  ta zaro idanuwata waje  tana masa wani irin kallo kafin  daga baya cikin d'aga murya cike  da  maseefa tace "ko zaka koma  wajenta ne ko me kake nufi da wannan maganar ?da zan samu haka  wallahi da naji dadi sosai "ya sake  fad'a acikin ransa "ai daman haka halinku maza yake da zara kunga mata sai kama 'bare 'bare  to du ka gama 'bare 'barenka ka hakura dan ita wannnan dai ko ka  koma wajenta ma dole ka gudu da kafarka dan idan kasan akanta matsalar  duniya ta qare, kana fara soyayya  daita  komai  daka mallaka  zai  qare idan kayi sa'a ma wani  mummunar bala'i bai sameka ba  tayi samari day day sun kai guda hud'u kuma duk da aure suke sonta amman da zarar sun fara zuwa zance wani mummunar bala'i Ke samunsu ganin ta inda take shiga ba nan take fita ba yasa ya matsota sosai ya rage murya ya soma magana  ."

"Haba kaulat banda sharri fa dan kawai mutun yace yana sonta sai wani mummunar bala'i ya samesa sai kace wata annoba ,wannan ai tafi annoba "to  ko zaki hadani daita kawai ina son naga tasirin bala'in dake tattare daita ?tayi shiru kawai tana nazarin maganarsa idan zata kintata daidai son maryama yake cikin karayar da murya kaulat tace "me kake nufi da wannan mgnr ?ya tsura mata idanunshi kawai "kaga bilal banason wannan maganar karka qara min  hk da kuka ta qarasa maganar dan duk cikin samarinta tafi qaunar bilal "ya salam !meye kuma abun kuka anan daga wasa ?kuka kaulat take sosai ganin haka hankalinsa ya tashi sosai "kinga wallahi ni wasa nake ya ciro hankacip ya mika mata "wip your tears karki min asarar hawayenki da kyar ya samu ya rarrasheta ta daina kuka ."

Da sallama  maryama ta shiga part dinsu inda ta iske habib na  zaune akan wata tsohuwar kujera mai zaman mutun uku  yana ganinta ya saki fuska yayinda aunty ke zaune akan daddumar sallah  , " heartbeat sannu da zuwa "yauwa after dad  ta fad'a tana  cire  nikaf din fuskarta da hijab din jikinta " yau baka fita bane na ganka a gida ?"wallahi na fita ban dai  jima  bane  saboda  ranar  daake  yau  tayi zafi da  yawa "gsky  kam  yau  an zuba   rana ga doguwar tafiyar  mun   kwaso  wallahi a matukar gajiye   nake  da kyar na  qaraso  gida , kasan tun daga dopemu da kafa  muka  shigo agege ya zaro ido yana cewa "halan matsalar mota ?ta gyada masa kai tana rausayar da kwayar idanunta ."

Ya mike  tsaye   ya  qarasa inda  d'an  qaramin fridge dinsu  thermocool yake wanda ya gaji dan murfin ma ya balle idan an bud'e da kyar ake maidashi a rufe ya ciro pure watar mai sanyi ya ajiye akan hannun kujera ya maida murfin  fridge  din da kyar ya qaraso inda take "heartbeat ga ruwa ki sha  "yauwa after dad  na gode  sosai  ya koma Kan kujera daya tashi yana cewa "ya exam din fatan yazo da sauki ?sai data zuke ruwan sannan tace "babu wani sauki amman muna fatan samun nasara daga Allah bata sake cewa komai ba sannan bata zauna ba ta qaraso bayi ta dauro alwala ta fito ta d'auki wani dadduma sallah daga inda suke ajiyewa ta shimfida kusa da mahaifiyarta dake zaune har lokacin tana kaiwa allah kukata akan yaranta most especially maryama wacce ta fita jarabawar karshe ta tada sallah a natse ."

Bayan ta idar da sallah  ta mike tsaye  tana  ninke sallayar ta samu waje ta zauna kusa da habib tana sauke numfashi "kai wallahi ban ta'ba gajiya irin na  yau ba wannan hanyar ta yanoba akwai matukar wahala alhamdulillah  daga yau dai mun huta bata gama  rufe  bakinta   ba taji an bako kofar shigowa falon nasu  da  karfi atare suka kallo kofar kaulat ce tare  da mahaifiyarta tsaye suna huci Aunty hassana tace "yauwa gara da Allah yasa na sameku  gbdy uwa da ya marasa  mutunci  to wallahi na gaji  ki jawa wannan tantariyar yartaki mai  suffar  manufukai kunne ta shiga  hankalinta  bata tashi dawowa  gidan nan daga yawon karywancinta  sai yamma tayi lokacin  da manema  auren yarana suke zuwa ta dinga wannan yar iskar tafiyar tata  simi simi kmr macijiya dan kawai ta dauki hankalin samarin  ya'yanmu to wallahi kinyi kadan  bake  ba hatta uwar  data kawoki  duniya ga tanan tayi kad'an bare Ke karan  kada miya ,ko su sukayi koba dinki?

" ko su sukace maza su dinga gudunki  ?ko Kuma su suka sanya mugun balai ajikinki da maza ke gudunki ? babu daya da sukayi aciki dan haka daga yau banason sake ganin gyallinki idan bilal yazo gidan nan  aikin banza  kawai kyau  har kyau amman bashi da amfani , ana  fakewa da karatu ana  yawon karuwanci "tana kawo nan habib ya zabura ya mike jikinsa na rawa  tare da daga hannu zai zabga ma Aunty hassana mari...."

aunty  wacce ta mike tsaye tun fara maganr Aunty hasana tayi  saurin rike masa hannu tana cewa " qul  habib  karka fara ko ka manta wacece ita da matsayinta agurinka?  "amman male  bakiji kalmar da take fad'awa heartbeat ? "an fada Kuma an sake fada dan uwarka da ubanka kayi duk abinda zakayi karya na fada ba yawon karuwanci take ba ?" idan bashi take ba me yasa samarinta suke gudu su barta ?idan baka sani ba kasani daga yau ai raba masu kanta take kmr MTN shiyasa suke gudu suna barinta  jairi kawai da wani katon kanka can shegu marasa mutunci jinin marasa mutunci ai da bakayi haka ba bazansa kayi gadon dangin uwarka ba masu arziki amamn matsiyatan mutane  ."

Tunda ta fara magana hanakalin maryama yay  kolowar tashi sosai ta firgita da kalaman aunty hassana  ba idanuwanta suka cika da ruwan hawaye ta kalli inda kaulat take da kyar ta bude baki cikin sanyayyar muryarta mai tsananin kashe jiki "mama Ke kanki sheida ce akaina Kinsan bazan ta'ba aikata wani abu da zai 'bata sunan ahlina ba ,walalhi bana aikata komai karatu kawai nake zuwa  sannan mama ko babu komai ni din diyar d'anuwanki ce kuma abar tausayi a irin wannan rayuwar da muke wacce babu wani yanci acikinsa sai tsabar kaskanci kece mutun ta farko da daya kamata ki cetomu amamn sai gashi kece mutun ta farko dake bibiyarmu da mugun alkaba'i  ta sake kallon inda kaulat take tsaye tana zabga mata harara."

"ga kaulat nan idan zata fadi gsky babu wani abu danayi hassalima ko magana banyi ba ta gefensu na raba zan .." dakata dan Allah malama  banson manufarci bangane atambayeni ba ta fad'a cikin zafi rai kafin daga baya  ta dawo gabanta ta tsaya "duk abinda mama ta fad'a gsky ne kisa kunnen baseera ki  ji abinda aka fad'a miki ,ki tsaya iya matsayinki ki kiyaye shigowa alokacin da bilal yake zuwa tana magan tana nuna maryama da yatsan hannunta "idan karuwanci zakiyi sai ki san inda zakiyi ba ..." tas tas !! habib ya dauketa da gigitaccen mari "da uban wa kike wannan maganar ?da ubanka nake banza kawai mara kunya  ta fad'a tana dafe kuncinta .

  "idan kika sake zagina ko zagin yaruwata wallahi sai nayi miki jina jina anan shegiya yar iskar banza kakar  ubanki ce karuwa..."ai bai gama rufe baki  ba Aunty hassana ta sauke masa nashi mari ji kake tas tas !! sau biyu ajere "dan uwarka a gabana zaka mari yata ?" jakar gidan uwarka ce da zaka mareta ?"
habib ya bude baki zai sake yin  magana aunty ta sake dakatar dashi" karka Kara cewa komai wannan idan da sabo tuni princess ta saba  dan haka komai hassana zata fada akanta  banason ka  sake cewa  uhm bare uhm uhm dan yarta ce halak malak idan karuwa ce ita tayi silar zuwanta duniya ."

aikuwa ransa yayi massefar bacci ya dinga Jin wani tuttukin bakinciki na taso masa "ke ai da kin kuskura ya sake ta'ba min lafiya 'ya wallahi da yaga aika aika da yau mun kwashi Yan kallo dake dan kece saar yina basu ba habib bai daddara ba  yace "allah Aunty  ki kama girmanki Kafin na miki abinda bakya tunani koda yake ai ba girma atare dake mahaifiyarmu tafi karfinki sai dai Kiyi damu ba arabi ba boko shiyasa baki san haramcin abinda kikeyi ba "da uwarka da dangin uwarka kake ba dani ba tana gama fadar haka taja hannun kaulat suka nufi kofa tana cewa"dan kutumar uba kawai ."

Kuka  maryama  take  sosai  a wajen  tamkar ranta zai fita  aunty  ta qaraso  wajen da take tsaye  tare da dafa maryama  me ye kuma na kuka  bayan wannan ba sabon abu bane ? Kuka taci gaba dayi  habib ya matso "dan allah heartbeat ki daina kuka idan ba haka ba nima zanyi kuka tana kuka habib na kuka nan da nan aunty ta samu waje ta zauna ta d'aura kanta a hannun kujera itama kukan take da karfi
A hankali suka qaraso suka durkushe kasa kusa da kafafun Aunty tare da daura kansu a saman cinyarta  suna  cigaba da rera Kuka    wanda har  umma ta shigo   basu saniba" umma  ta qarasa shigowa da sauri  tare da dafe qirji  bilkisu  me ya faru Kika tasa yara gaba kuka ? Kuka  suka  ci gaba dayi ba tare da sun bata amsa   ba..."Ke maryama taso muje ki gayamun me yafaru da ke  da mamanki da kaninka haka  kuke kuka ? ."

hannunta umma  ta riqo suka nufi bangarenta Aunty salma  dake tsaye taga wucewarsu maryama na goge kwalla tasan ba lafiya ba  ta biyo bayansu da sauri umma   ta zaunar da ita  a Kan kujera ,a lokacin kukan nata ya fara raguwa"me ya sameku  haka kuke wannan uban kuka haka maryama ? Jin shirun da tayi ne yasa aunty  Salma   ta tunzura "wani mahaukacin tsawa ta sakar mata wanda sai  da ta burkice  "wai  ba magana ake miki ba ne?sai lokacin umma tasan da shigowarta ta dago tana kallon tana mamakin hali munafurci irin nata ko wa ya kirata data shigo ? umma ta hade rai tana cewa    "a'a salma   ba haka akeyi ba ki barni daita kawai karki hargitsa mata lissafi ki barta zatai magna."

"uhm ina jinki maryama fad'a min damuwarki cikin sheshekar kuka ta zayyanewa umma komai da ya faru naunayen ajiyar zuciya ta sauke "gsky bata kyau ba , amman  Kiyi  hakuri ita rayuwa ta gaji haka komai da  kika gani  kafin a samu nasara sai anyi  hakuri   in sha allahu wata rana zai zama labari ,ku ya kamata ku dinga kwantar wa da mahaifiyarku hankali ba wai ku dinga tayata kuka ba yi hakuri kinji maryama   Ki bar komai a wajen Allah in sha allahu sai kin zama madubi abar dubawa acikin gidan nan masu takaki wata rana sai  sun zama fadawanki "wallahy aunty aseeya  har da laifinki wajen iskanci yarinyar nan kawai daga yar wannan mgnr zasu zauna suna kuka Kmr mutuwa akayi ke km   sai  ki zauna kina  bata lokacinki ."

" babu ruwanki dole na rarrashi diyata  mikewa tayi ta fice cikin fushi umma tabi bayanta da kallo karki qara damuwa da sharrinsu idan kina kuka suna ganin rauninki to kin shiga matsala dan kullum da abinda zasu dinga miki amman idan kika jajurce kece zaki ga rauninsa ta fad'a hk tana goge mata fuska da gefen zaninta  "kin ci abinci ma kuwa ?ta girgiza kai alamun a'a to maza jeki ki rarrashin mahaifiyarki da danuwanki ki dawo ga abinci kizo kici ta mikar daita ta rakata har bakin kofar fita  da kyar ta fito zuwa bangarensu wanda lokacin tuni aunty ta daina kuka suna zaune da habib  tana gama shigowa taji  saurin muryar Aunty  "my princess taho kici abinci nasan kina tattare da yunwa."

Babu yadda ta iya ta sakar mata murmushin gefe baki  tana dubanta tace  "kamar kin sani Aunty gbdy suka qarasa  zuwa Kan kujerun roba dake zagaye da qaramin table wanda shima din na roba ne aunty na zaune tare da yaranta suna cin abinci amamn ita  tayi shiru tana tunani  ta kasa cin abinci "male kici abinci mana ta dago ta kalli habib maryama ta ajiye spoon din hannunta ta soma magana a tsanake kamar ba yanzu ta gama kuka ba."

"kiyi hakuri aunty akan duk abinda Ke faruwa a gidan nan wani lokacin  Allah yana gwada mutane ya gwada imanin bawa kinsan al'imanu yazidu wa yankus imani na raguwa yana qaruwa to Ke aunty a mizanin da kike allah yana son ya gwada imaninki ne Kan wasu abubuwa dake faruwa damu  duk duniya bani da abar yabo da koyi da hali mai kyau sama danaki sannan kowa yasan ke din mutuniyar kirkice hatta makiyanki suna fadan hk a bayanki to me yasa abubuwanki sukaki  daidaita duk wannan hakuri naki da juriyar amman ba komai bane  kawai Allah yana son ya gwada imaninki da jin tsoronsa ne dan duk allah yana sane ya tsara  haka  hk ."

"Mu  qara hakuri hakuri ne kawai zai kawo mana sauki kuma Allah yace annan nasara maasabarin duk wani nasara na rayuwa yana tare da hakuri ,
hakuri da kike dashi yana cikin tsani da zai kai  mutun zuwa aljanna, hakuri halin manzon allah ne  wal hilmi wal sabri duk kina dashi aunty kina da dauriya kina da juriya kina da tawakkali kina da imani kina da ibada so duk wani abu da kike ganin yana samunki mara kyau ko yana shirin faruwa dake to wallahi jarabawa ce km kina ta cinye jarabawar sai kiga allah ya tsara bazakaji dadi anan duniya ba sai a lahira ,wallahi aunty da ace kana da rabo a duniya baka dashi a lahira wallahi gara ace kana dashi a lahira  baka dashi a duniya ."

"sai abu daya  da nake   son ki fad'a mana" ta dago da rinannun  idanunta ahankali tana duba kyakkyawar  diyarta son kowa kin wanda ya rasa  abar tinkaho  kuma yar baiwa domin samun irinta sai an tona "aunty idan bazan takuraki ba  ina son ki fad'a mana inda danginki suke muna son musani domin na fara tunanin akwai wani mummunar abu daya faru a baya dake ,dan idan babu komai bazai yuwa kana  da dangi kuma kuna gari daya amman bakwa ziyar juna"tunda maryama ta fara magana idanun aunty  suka sake  cika da hawaye basu samu nasarar zuba ba sai data kawo karshen mgnrta "ki fad'a mana mu yaranki ne  bazamu taba juya miki baya ba duk runtsi duk wuya muna tare dake koda kuwa kice kika batawa yan'uwanki zamu kasance dake  domin kece karfin gwiwarmu  ta qarasa mgnr tana riko hannun mahaifiyarta ."

Mmm sudais

💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.