Ciki Da Gaskiya Littafi Na Daya Complete Hausa Novels
Reading file: Ciki Da Gaskiya Part 1.txt
Chapter 30 of 40
*_part 1_*
(littafi na d'aya📕)
_Alkairin ALLAH ya iso agareku 'yan group d'in *MAMAN SHUEIM NOVELS & MAMAN SHAHEED FAN'S & UMMU NOOR NOVELS WORlD* ina godiya sosai da k'auna._.
_bilyn Abdul tana yinku_😄🙌🏻
😍😍😘😘
3⃣0⃣
Sanye yake cikin suit blue, sunyi masifar yimasa k'yau, k'yawun haibarsa da nagartaccen annuri yana nan, babu abinda ya canja agareshi. Saima k'yawu da kwarjini dataga yak'ara mata, fuskarnan ad'aure tamau kamar yanda tasanta ashekarun baya.
Kallon ido cikin ido sukaima juna, kowannensu saida tsigar jikinsa ta tashi, Aysha tayi azamar janye dara-daran idanunta daga kallon rikitattun nasa.
Bakinta yamata nauyi, tama rasa mizata furata, farin cikin ganin ya khaleel zatayi kokuma kuka? wanne yadace agareta arin wannan ranar?, gata ga abin sonta Wanda baimasan tanayiba.....
Maganarsace takatse mata tunaninsa, muryarnan tasa maisaka marajin magana nutsuwa tadaki dodon kunnenta, cikin harshen turanci yake maganar, dan baimayi zaton yarinyar tasan wani yare hausaba a duniya.
K! hankalinki yana a tsakkiyar kaine dabakisan abinda ke a gabankiba?.
Ba halin Aysha ne rashin kunya gana gaba da itaba, amma a yau saita samu kanta da murgud'ama ya khaleel d'in baki, tana magana k'asa-k'asa cikin k'unk'uni.
Da Hausa takeyin maganar, amma bayajin mitake fad'a, saibakinta daketa motsawa ya tsirama mayun idanunsa.
Bata ankaraba taji anbige mata baki, hannu tasaka da sauri tadafe bakin nata saboda zafin dataji ya ratsata, kafin kacemi hawayen sunfara gudun zirnaniya a kumatunta.
Yaja siririn tsaki yana hararta, saida yara6a ta gefenta zai wuce sannan yace, ''gobema kisake ma wani rashin kunya".
Wlhy ALLAH ya isana, Aysha tafad'a cikin harshen Hausa.
Tsayawa yayi cak daga tafiyar dayakeyi, baiji mitaceba, amma saiyaji tamkar Hausa tayi, kai kodai kunnenane yajiyemin k'arya?.
Ya khaleel yafad'a yana waigowa inda Aysha take.
Saidai tuni tayima nisa dawajen, amma kamar ance tajuyo, saigata ta waigo, suna had'a ido tamasa gwalo dasaka hannayenta a kunne kamar yanda yara keyi idan Suna tsokanar 'yan junansu😂.
Da d'an gudunta tashige bayan wasu samarin d'alibai ta 6uya.
(Ho Sholyn Anty meerah🤣🤣🤣)
Samun kansa yayi dasakin murmushi, tunda yake baita6a had'uwa da shashashar yarinya irin wanga d'iyaba, yakuma Jan k'aramin tsaki tareda juyawa yacigaba da tafiya, har sannan murmushin yakeyi Wanda shikansa baima San namiyeba.
Aysha naganin yatafi tafito daga gun 6uyanta, wani nishad'i nadaban takeji ayau d'innan, tadad'e batayi farincikiba a rayuwarta, wai yau itace tareda ya khaleel, tabbas tasanma bai ganetaba, to yama za'ayi yaganeta, tunda ko'a wancen lokacin bawai ta Isa yawani tsaya kallonta baneba, ita tundama take dashi basu ta6a kallon ido cikin idoba sai yau, ta lumshe idanunta tanamai tuna kwayar idon ya khaleel d'in maicikeda kwarjini da abubuwa masu wuyar fassara ga ma'abocin kallonsa.
Tasanma yanzu yadad'e dayin aure, k'ilama harda 'ya ko d'a, jitai wani bak'in cikin ya soki k'irjinta, taja tsaki tana fad'in yoni INA ruwanama da aurensa mtsowww.
Kekam wakikema tsuk'a?.
Cewar ifteehal data iso wajen Aysha da idanunta ke a lumshe har yanzu.
Da Sauri Aysha tabud'e idonta, tab yaushe kikazo?.
Yaza'ayi kisani, nifa sometimes kina bani mamaki, kina Acting like mai soyayya wlhy, shin kodai kinfad'a tarkon wanine a k'asar tamu?.
Harara Aysha tazabgama iftee, a'a Auren wani nakeyi k'arewar soyayya, ni muje muci abinci yunwa nakeji parrot kawai.
Tsaki iftee tayi, tayi gaba tana fad'in ai gwamma dani parrot ce, kekuma dutsi ko?.
Aysha tayi murmushi, Dan tasan ifteehal tashaki haushine, bataso ayshar nace mata parrot.
Gaba d'aya yau duk Wanda yaga yanayin Aysha yasan tana cikin farinciki, harma mom takasa hak'uri ta tambayeta.
Aysha tace lah babu komaifa mom exams d'in yaucedai tayi dad'i sosai.
Meerah dake zaune gefen mom dama suna list d'in abinda zasu Sayo Na shirin bikin ya Naufal d'in da meerah sukeyi.
Ta kalli Aysha tana nazarinta, ko kad'an bata yarda da zancen Na Aysha ba, zuwa yanzun kam saidai tabama wani labarin Aysha amma badai abataba.
Itama ayshar ganin kallon da Anty meerah kemata yasakata mik'ewa tashige d'akinsu itada ifteehal.
Mirmushi kawai meerah tayi, tacigaba da abinda takeyi.
______________________________
Taheer gobe idan ALLAH ya kaimu zamubar k'asarnan, Dan bincike ya tabbatarmin yarinyar ba d'iyarsa baceba, amma akwai yarinyarsa wadda matarsa tarasu tabari tana nan America Tana karatu, kuma daga nan Canada yawucene Domin dubata itama.
Ayanda ita wannan yarinyar take nunamin kamar d'iyar tasa batajin magana, so babbar hanyar dazamu sami bayanai akansa sosai shine d'ayanmu yayi soyayya da yarinyar ta kwana goma kacal.
OK Na fahim ceka, amma ina ganin awannan fagen kaiyakamata kataka rawar gani, Dan babu macen dazakace kanaso bata sokaba, saboda yanayin k'arancin lokacin damuke dashi.
Harara ya khaleel yasakarma youseef, amma bakada hankali alhaji, kaima kasan wannan ganganne wlhy.
Dariya suka yi suduka, Taheer yace, "boss ALLAH kuwa gaskiyar youseef, kaine kawai zaka samu damar samun zuciyarta cikin k'ank'anim lokaci, Dan nasan wlhy tun a zuwan farko zata amince maka.
Indai sainine zanyi soyayya da yarinyar nan to Ku tabbata bazamu kama Alhaji Alasan kwangila a nanba kuwa, kuma wannan itace damarmu ta k'arshe akansa.
Taheer kaine zakayi soyayya da ita.
Yana gama fad'a yatashi yashige d'aki.
Binsa kawai sukayi da kallo suduka, Taheer ya sauke ajiyar zuciya yana maida kallonsa ga youseef, anya kuwa j yanada lfy youseef?.
Miyasa kace haka kaikuwa Taheer?.
Gani nayi ko kad'an mata basa agaban j, tunda nake dashi banta6ajin yayi hirar maceba wlhy, kaduba yanda mata ke mutuwa akansa ammashi ko kallon arzik'i basu isheshiba, yakai lokacin dazai buk'aci mace kusa dashi amma banta6a ganin j yarik'e hannun wata yarinyaba ALLAH kuwa.
nida kai duk muna Neman mata, amma koda wasa wannan harkar bata ta6a birge j ba, saima fad'a dayake mana akullum akan muji tsoron ALLAH.
Humm hakane gaskiyarka Taheer, ALLAH bazan 6oye makaba abin nadamuna, Dan sosai ina k'aunar j, inajinsa tamkar d'an uwana najini bawai aboki ko oga a wajen aikiba kawai.
d'azu damuke jiransa amota cikin makaranta, sainaga kamar yatsaya da wata yarinya.
Ashe ka kula, nima nagansu, nadaiyi shirune kawai, amma nasan koda zamu tambayesa yanzu zaice babu komaine kawai.
Mugwada tambayar tasadai to, idan mun samu amsa to, kasansa maganarma ta kud'ice awajensa.
Dariya Taheer yayi yace Oga J kenan, shidai komai nasa yanada banbancin tsari dana sauran jama'a.
Ya khaleel kam wanka yakeyi hankalinsa a kwance, saidai tunanin yarinyar data masa gwalo yakasa barin zuciyarsa, murmushi yaketa saki aduk lokacin da zuciyarsa ta tariyo masa murgud'a bakin data masa da gwalo, ahankali ya furta mara kunyar banza kenan, ya ture tunaninta da k'arfin tsiya ya maye gurbinsa dana Alhaji Alasan kwangila, wanda sukebi tundaga Nigeria domin son kamashi, yaja wani dogon tsaki, a zuciyarsa ya furta kazo hannu aii insha ALLAH, duk Wanda yafad'a tarkon Ibraheem Abdallah dama yad'auka yagama shiga uku kawai.
Yasaki lallausan murmushinsa dasai yagadama yakeyi yana saka rigar wanka pink.
Haka kawai yakejin nishad'i tun lokacin dasuka had'u da yarinyar nan, shirmenta yayi tasiri a zuciyarsa, batareda yasan daliliba.
____________________________
Momy nifa maganar gaskiya zantaho da matarnan idan zamuzo meeting na k'arshen shekara.
Babu damuwa Zuwairah, kitaho da itad'in, aii yanzu komai ya wuce.
Alhmdllh, wlhy nikam dama ta isheni.
Kai zuwairah, nibansan lokacin dazaki fara son mutaneba? Daga ke har mijin naki halinku d'aya, gashinan kun koyama yaranku kuma.
Hhhh kai Momy ALLAH kinbani dariya nikam, ammafa kemad'in haka kike.
Yauwa wai kuwa Momy bazakima khaleel magana yayi aurebane? Kidubafa har matan su Sultan sun haihu, gashi ana shirin yima Mufeedah aure itadasu Amal, shi koniyyar auren ma baida ita.
Kinsandai halin Ibraheem sarai, amma idan kukazo wajen meeting sai ataru amasa magana, damage hajia Salma NATA damuna akan d'iyarta Abeeda, kinga saimuji idan yanada ra'ayinta, Dan Nima namasa sha'awar yarinyar k'yak'yk'yawace.
To shikenan, ALLAH ya kaimu lokacin, yasa kuma ya amince, kinsandai mird'ad'd'en halin d'an naki aii.
Shukurah tacemin dayaje k'asar yaje har gidanta, nace taci gari.
Gaskiya kam, aidama ki lura shida Shukurah suna d'asawa, saboda halinsu Na kamancece niya da juna, 'yar banzar yarinyar nan dana fad'a mata auren babanku cewafa tayi ALLAH yasanya alkairi.
Hhh kema dai Momy miye nama fad'a matan, kinsan dai Shukurah banza ce walhy.
Barta aizatazo ta iskeni, harda wani turo kayan jarirai wa makirar matarnan Fad'ima.
Dan ALLAH Momy da gaske?.
Wlhy kuwa, Ashe ban fad'a mikiba alokacin.
Kin manta baki fad'aminba, lallai Shukurah, amma yarinyarnan batada hankali, wai yaushema tasanta dahar tayimata aike?.
Yo saita Santa, ai zanma tufk'ar hancine, baradai tazo k'asar.
Shike nan Momy, bara nabarki kigaida autocinki.
To zasuji sai anjima.
Momy ta sauke waya tana cigaba da mitar cima mama mutunci, su Mufeedah sai k'ara tunzurata sukeyi.
(Nace ALLAH ya k'yauta dai).
Falo nafito inda mafi yawancin yaran gidan suke, su Amal da Shuhuda sai matan su ya Sultan, Abashiyya da Ummu-Ayman, Hamdiyya da Naseeba suna Jigawa sunje gidansu.
Sai Tasleem da maleeka, hira suketayi abinsu hankali kwance, sai dariya sukeyi, daka gansu kasan suna cikin nishad'i.
Musleem yafito daga d'akin mama d'aukeda Affan daketa tsula kuka, sai cillashi sama yakeyi yana ca6ewa danyayi shiru.
Aymana matar Mujahedeen tace, "wlhy Musleem kada ka kado yaron nan k'asa, Anty Mamie tacika tara ka kayar mata da auta".
Tsayawa yayi daga cilla Affan ya kalli Aymana d'in, lallaima Anty Aymana mikika maidanine?, kalleni da k'yau nakusa yin aure, shiyyasa nake koyon raino kafin matata tazo.
Dariya suka sanya masa, shikam yawani tsare gida alamar babu wasa amaganar tasa, Anty Mamie dake tsaye a dining tana shirya abinci tace, " sannu musleem kaji.
Idanu yazaro, kokad'an baiyi zaton Mamie Na a falonba.
Cikin sauri yashige 6angarensu, mama tayi dariya, dan itama daga kichin tana jiyosu, tace ai gaskiya yafad'a, kinga k'anne duk sai suriga babban Yaya aure, idan yaga sunayi shima yayi zuciya yayi aii.
Hum Yaya Fad'ima aini lamarin babanama tsoro yake bani, inaga saiya tsufa zaiyi Auren?.
Aniyarku tabiku annamimai, anzo antasamin yaro gaba za'a cinyeshi da baki, nibansan mi rashin auren Ibraheem yatsare muku ba agidannan, wlhy mugun bakinku saidai Yakoma akan 'ya'yanku.
Hajia babba ce kezuba masifa alokacin datake fitowa daga 6angarenta, su hasnah Na take mata baya, cikin gayu suke nafitar hankali, da'alama wani gurin zasuje.
Kowa kallonsa yamaido akansu, amma daga mama har Anty Mamie babu Wanda yakallima inda take.
Anty Amarya tashigo falon da sallama, da'alama dawowarta kenan daga aiki, Dan rik'e take da jibgegiyar rigar lauyeyi da handbag d'inta.
Itama tsayawa tayi tana kallon ikon ALLAH, dukda mutumce mara son shiga abinda bai shafetaba lamarin hajia babba nabata mamaki, ita kokad'an bata d'agama kowa hulaba agidan.
Yanda take zazzaga masifa kaikace 'ya'yanta takema fad'a.
Gashi falon yayi tsit kowa yana saurarenta.
Mama tad'ago cikin matuk'ar fusata tace, ''k! Hajia Laurah ya isheki haka mana, shin wai mud'in 'ya'yankine kokuwa kina mulkar wanine acikinmu? dazaki zauna agaban 'ya'yanmu kinacin zarafinmu?.
Baba dai matsayin d'a yake awajenmu, babu kuma yanda za'ayi ahanamu sakashi cikin hirar 'ya'yan gidannan.
Wai ko har yanzu bakisan kin girma baneba?.
Har hajia babba tabud'e baki zatayi magana baffah yadakatar da ita tahanyar fad'in, kar wanda tasake magana acikinku, yamaida dubansa akan yaransa da surukansa, kowanne yayi k'asa dakai, Amal harda kukanta, Dan abinda ke faruwa agidansu yana damunta.
Tsaki baffah yaja, yajuya zuwa 6angarensa yana fad'in kuduka hud'un kuzo Ku sameni.
Baijira cewarsuba yay shige warsa.
Tsaki hajia babba taja takama hanyar fita abinta tareda fad'in babu abinda ya'isa dakatar dani daga fitata, saidai adakatar dazaman harsai nadawo.
Babu Wanda yakulata taja 'ya'yanta daketa hararsu Anty Mamie saikace sa'anninsu suka fice.
Babu Wanda yasake fad'in komai, mama da Umme amarya da Anty Mamie suka nufi 6angaren baffah..........✍🏿
*_Love you all😘😘_*
[8/18, 8:08 PM] Aisha Galadima: *_Typing📲_*
🤰🏻
*_CIKI DA GASKIYA........_*
_{🔪wuk'a bata hudashi🗡}_
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_NIKA'DAI WRITER ASSO........_*😜
*_Sadaukarwa_*
_My sweet dady_
~(ALLAH ya gafarta maka)~
🤲🏻😭
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.