Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel
Reading file: Fin Karfi Part 3 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 6 of 9
Page 6
Ya ce "ai ni kece a gabana komai na Prettyna." Ta kuma shan mur.
Haka ya yi ta janta da magana tayi mai shiru har suka je kasuwa. Shagon wasu masu leshi da materials suka yada zango,ƴanmatane keta siyayya a shagon Dady yana daga ƙofar shagon yana duban Pretty ɗin shi suna taya M Bash zaɓe, duk abinda take yi baya gajiya da kallon ta, komai nata birgeshi yake yi.
Wasu ƴanmata da tun zuwansu gurin suka maida hankali kan Dady ya tafi da imaninsu,ɗayar ta ɗebi wasu lesuka guda biyu tazo gabanshi don Allah Malam muna musu ne wanne yafi ƙyau? Ya ce a'a ni ban san kayan mata ba, ga mata can ƴan uwanku. Sai cewa tayi to kai wanne yafi maka ƙyau? Nan take yasha kunu ya ce ban sani ba. Ya maida dubanshi ga Pretty ɗin shi suka haɗa ido ranta a ɓace a zatonta shi ya soma yi musu magana. Ya shiga falon kun gama? Yana magana yana kallonta ta juya mai kai.
M Bash ta ce ɗaya na ɗauka kayan su nada tsada, ya ce kema Sadiya ɗauki naki, shi kuma ya ɗauki biyu, ya haɗa ya biya suka sa musu a cikin ledoji, shagon wasu inyamurai suka shiga siyen jaka da takalmi ɗayan sai kallon Ruƙayya yake yi.
Dady yana kula dashi, Ruƙayya ta ce,a ɗauko mata ɗan mara tudu ya ce to Baby,su M Bash suka wuce wajen zaɓen jaka ya kawo mata takalmin ya ce "wannan zai dace dake kinada ƙyau fa." Ya tsugunna gabanta kamar zai kama ƙafarta yasa mata. Dady ya ce "tashi ki fito tashi." Ta dubeshi fuskarshi tamkar bai taɓa dariya ba ta miƙe ya ce Munira ku zo muje, suka ce bari in bashi kuɗin.
Ya tasa Pretty ɗin tashi a gaba suka nufi gurin mota,suma suka biyo su a mota sai masifa yake yi shi baya son irin wannan kasuwar, dubi kamar zasu taɓa mace ko baya nan be yarda ta kuma zuwa nan ba. A ranta ta ce ji irin ikon nashi, shi daya tsaya yana magana da ƴanmata amma ita daga gani yana kallonta ya ce su baro kasuwa. Wata super market ya tsaya suka shiga ya ce su ɗibi duk abinda suke so Ruƙayya dai bata yi yunƙurin ɗaukar komai ba tsayawa tayi tana kallon su, Dady ya wuce yana ɗiban abubuwa,sai da yayo leda huɗu aka haɗa aka gaya mishi kuɗin, ya biya duka da ya sauke su ya ce Pretty ga kayan nan, ta ce babu abin da zanyi dasu, ya aje ya ce ki barsu nan, ya figi mota ya yi gaba.
Munira da Armaya'u sai masifa suke yi mata, ta ce tunda ya yi muku siyayya ai dole ne ku dinga goyan bayan shi. M Bash ta ce shegen taurin kan kin nan ki rage shi yarinya da kishiya zaki zauna, tsaki ta ja sannan tayi gaba suka ce shegiya gara ma kinzo kin ƙwashe kayan ki,kishi na cinki,yara suka roƙo suka ƙwashe musu kayan.
*** *** ***
Dare ya aiko Sabi'u ya gaya mata jirgin ƙare baƙwai zata hau zuwa Legos ta shirya da wuri. Tun dare suka yi sallama da aminanta, bayan sun raba dare suna hira, daga sallar asubahi kowa ya hau shiri ya bada mota Sabi'u ya kai Armaya'u tasha ya yin da Munira direbansu zai zo ya ɗauke ta.
A cikin mota ya dubeta,ko ta bashi haushi yana dubeta sai yaji ya huce, cikin sanyin murya ya ce ba gaisuwa Pretty? Ko ba'a sona na ci arziƙin aure ko?" Ta ina gajiya ya Momy? Ya yi ajiyar zuciya sannan Ya ce tace in gaida ki." Bata amsa ba ya ce ina tunanin sati mai zuwa in yazo zan sama miki gida ƙarami ki koma, ta ce ban ce ba,ka barni inda ka ganni, ya ce shikenan na barki, ta ce wayata fa? Ya ce gata,miƙo mata wata sabuwar waya mai shegen ƙyau ya yi, ta ce ni tawa nike so, ya ce tuni nayi ƙyauta da ita har layin ma zan ɗauki komai amma ban da waya da wasu ƙattai sannan ki kiyayi wani Nuri da naga yafi kowa kiranki, kuma inbox ɗin ki ba text ɗin kowa sai nashi in ya yi wasa ba zai ji da daɗi ba kin jini?"
Yanda yake maganar rai a ɓace shine ya hanata yi mishi tsiwa, sai da yaga komai ya kammala har sun soma shiga jirgi sannan ya tafi ita kam tunani take yi a ranta yau gata a jirgi. A can ma tana sauka sai ga wani yazo ya ce itace Ruƙayya? Ta ce Eh, ya ce yazo ne zai kaita gurin aikin su. Abokan service ɗin ta suna ta mata murnar aure dan da yawa sai da suka yi mata ƙorafin rashin gayyatar su, ta ce aure kawai aka ɗaura wannan dinner ma abokan mijin ne suka haɗa, Nuraddeen ne kaɗai ta zayyane ma komai.
Tana ta fama da waya, waya taƙi tayi sai dai wasu daga numbers daga nashi daga nashi daya sa mata ta Mom sai ta Yayyanta da ta Munira da Armaya'u,sai dai nasa number na kira amma ba dai na.
Haka suka ci gaba da gungurawa, kullum Dady zai kirata tana dakewa tana komai, zasu yi magana ko yayi tayi taƙi amsa mishi, amma duk ranar da be bar kira ba bata da sauran ƙwanciyar hankali har sai ya kira sannan zata samu natsuwa. Tuni ya koma Abuja bakin aikin shi ranar da ya koma ranar Zainab ta dawo, duk da irin soyayyar da yaga tana nuna mishi tare da ƙaramar hukumar maji daɗi da take gayyatar shi suna lulawa besa ya kasa gano ƙaramar ƙwasƙwarimar da aka yi mata ba kuma be sa ya manta da Pretty ɗin shi ba wani lokacin ma a gabanta ma zai ma Pretty ɗin waya.
Wata rana da dare misalin ƙarfe goma Ruƙayya ta kira shi don ta sanar dashi gobe zasu yi tafiya gaida wata abokiyar aikinsu a ibadan kuma tayi tunanin ta yi tafiyar ta kawai sai kuma ta tuna doguwar hanya zasu hau don haka sai ta kirashi.
Lokacin sun soma nisa a hanyar ƙaramar hukumar majidaɗi shi da Zainab, waya ta soma ringing cikin kasala ya ɗauka yasa a kunne Hello Pretty?" Yanda taji Muryar shi sai da gabanta ya faɗi ba ko shakka yana tare da Zainab. Ta daure ta ce dama zamu je ibadan ne. Zainab ko tana jin ya ce Pretty ta shiga aika mishi da saƙwanni waɗanda suka sa shi ya kasa magana sai yace zan kira ki anjima, yanda taji muryar shi ma ta isa tasan cewa sunje majidaɗi ne,in ranta ya yi dubu duk sun ɓaci tayi data sanin kiranshi yafi a ƙirga. Daya sani bai ɗauka ba zai fi mata takaicin wannan abun da taji,awa ɗaya tana kuka can wayar ta soma ringing number ɗin shi ne kamar kada ta ɗauka, sai kuma tasa hannu ta ɗauka Muryar mace taji tana cewa "Hello Ruƙayya ke ce kuwa? Menene dallah na kira min miji muna cikin raya sunnah,bana son shiga rayuwar ki ba,ki bari sai kin samu ya yarda ki tare sannan sai ki dinga wannan shishshigin yanzu barni da mijina mu wala, Ruƙayya ta koma ta ƙwanta tare da sa sabon kuka.
*** *** ***
Dady ya fito daga wanka duk komai ya yi na samun natsuwa, amma duk hankalinshi yana gurin Pretty tunda bata taɓa kiranshi ba tun da ta tafi Legos, sai dai shi ya kira ta.
Ya zauna bakin gado ya dubi Zainab ya ce je kiyi wanka. Sannan ya ɗauki waya ya fara kiran Pretty tayi ta ringing tana katsewa, kamar bazata dauka ba sai kuma ta ɗauka tayi zaton ko Zainab ɗin ce ta maida mata martani, sai taji shi ya ce Prettyna takaici ne ya kamata a ranta ta ce namiji munafiki, ya ce kin kira ni ɗazun bana jin ki network kin ana matsalar shi ƙwanan nan, ta kayi haƙuri na kira lokacin da bai dace ba,ka ba matarka haƙuri ka ce banyi da nufi ba kamar yanda ta zata sai ta kashe wayar ta gaba ɗaya ma ta ƙwanta,ya zauna yana ta fassara maganar duk yanda akayi Zainab ta kirata ya shiga dialled calls yaga kam an kirata, Zainab ta fito ya dubeta me kika ce ma Pretty da kika kirata? Ta ce ni ban kirata ba ita ce ta kira kuma na shaida mata bana son haka,ban da rainin wayo sai ta kiraka muna tare?"
Haushi ya ƙara kama shi ya ce "kin san wacece Pretty? Duk ya ruɗe ya ce wallahi sai naci mutuncin ki,yarinyar da nike lallaɓawa shine dan kuturun wulaƙanci zaki ɓallo min Niger. Don yanzu ban san ta inda zan fara ba na samu na fara shawo kanta, ya ɗau wayar ya kuma kira a kashe take. Zainab dai sai da tayi data sanin bata kira Ruƙayya ba, domin ko bacci Dady bai yi ba itama faɗan da yake mata ya hana ta runtsawa asubar fari ya soma shiri.
*** *** ***
Ta dubi Salimat ta ce,don Allah in kun je kice ina gaida Sulafat,bana jin daɗi jiya da zazzaɓi na ƙwana,Salimat ta ce zan gaya mata, Nuri ya shigo ya ya dai amarya? Ance bazaki samu zuwa ba, ta ce Eh, Nuri ku gaida min ita, Salimat wata ƴar sabis ɗin su ce da tayi haɗarin mota hanyar ta ta zuwa gida ranar Lahadi, shine zasu je dubata a Ibadan, sakamakon abin da ya faru shine Ruƙayya bata samu iznin zuwa ba gashi ta ƙwana ba lafiya.
Bacci ya soma ɗaukarta ta ji magana a kanta shugaban su ne da kanshi yake sanar da ita tayi baƙo. Kan ta ce wani abu Dady ya shigo sam bata son ganin shi don sai take jin kamar a gaban ta suke jiyannan. Ta runtse ido ya shigo ya zauna kusa da ita.
"Pretty tashi tashi ki jini." Ta ce cikin kuka "me zan ji? Bakada sauran abin da zaka gaya min,baka dashi Dady na jima da sanin halin maza,kai kana cikin maza masu cin amana da yaudara ga karya alƙawari." Ya dubeta ta kauda kai ta ce"na tsane ka." Ya ce ban ci amanar ki ba ban yaudare ki ba,kin ƙi bani dama na nuna miki son da nake miki nasha wuya a kanki ina sonki.
Ta toshe kunne.
"Daina gaya min ƙarya,bana son ji,bana son ji." Ta faɗi tana kuka sosai,ya rasa me zai mata ya ce to yanzu tashi ki faɗi min hukuncina, laifi dai ko wane iri ne na ɗauka,ya duka saitin fuskarta yana shirin haɗa bakinta da nashi,ta tashi tana kare bakinta cikin kuka take maganar kaje ka sha bakin wata sannan kazo ka daɓa min na ce kaje na bar mata kawai ka sake ni....." Ya rufe bakinta da tafin hannu.
Ya ce "Babu wannan maganar a tsakanin mu." Kuka tayi ta mishi ya durƙusa gwiwa bibbiyu a gabanta dan Manzon rahama kiyi shiru na durƙusa ni mai laifine amma ina roƙon ki kiyi shiru. Ta daina kukan muryar ta har ta dishe ta ce ka tafi bana son ganin ka, ya ce in na tafi zaki huce? Ta yi shiru ya miƙe ya tafi.
Ta yi shiru yanda ya damu ya bata tausayi tasan gaskiyan su Armaya'u ne sai ta dage zata samu mijinta. Tasan tana son shi amma ta kasa hucewa bayan tayi wanka kusan biyu saura tana fashin sallah, don haka ta zauna yanzun ne zata karya,ta soma shan tea ta ɗauko waya ta kunna text ɗin shine suka soma shigowa duk na bada haƙuri ne tare da neman yardar ta na son shigowa anjima, tayi shiru tana tunanin yanda take da kishi da yawa. Koda yake tasan tana son shi da yawa . Ya shiga kiran wayar ta barta tana ta ringing tana katsewa ya yo text yana roƙon ta dan girman Allah ta ɗaga wayar shi,ta ɗauka ya ce don son Manzon Allah inzo kin ji don Allah." Ta ce "Um." Ya ce to gani nan nagode. Ta cigaba da kurɓar tea ɗin da ta haɗa cikin ƙaramin kofi da har yanzu bata shanye ba. Ya shigo ya zauna kusa da ita ya ya jikin? Bata tanka ba ya ce ki min magana zan ji sanyi Pretty yanzun da na sameki be kamata insha wahala ba, kuma kema kin san ko wacce ƴa mace bayan ki zata biyo ina sonki, Ina sonki kin san....." Ta ɗaga mishi hannu "bana so ban so indai kazo gani na ne ka ganni kawai." Ya kai hannu zai taɓa ta, ta ce kada ka taɓa ni,ya ce to yanzun Pretty kin ce baki son na taɓa ki yaya zanyi? Ta ce me zan ji a maganar ka Dady,ƙarya? Tayi murmushin takaici aini Dady na wuce ka tsareni ka tsarani halin maza guda dubu ƙila goma ne ban sani ba,dan haka kayi shiru zai fiye maka sai mu daɗe tare amma in kace dole sai ka tsara ni to gara ka tafi abinka, ya ce to nayi shiru can ya ce ban karya ba, da gayya ta cika mishi ƙaton kofi da tea ta tashi ta kawo mishi bread ta koma ta ƙwanta tana kallon shi ga mamakin ta sai gashi ya shanye tas kuma ya ci bread da yawa, ya ce ruwa Pretty ta tashi ta kawo mishi.
Tana kallon shi ya fito da wayoyi kusan huɗu ya kunna nan aka soma kiranshi ya amsa wannan ya amsa wancan yawanci duk abokan harkar kasuwanci ne ya kira Momy ya faɗa mata yana Legos gurin Pretty ta ce ya bata su gaisa ya ce to ya miƙa mata Pretty ga Momy ta amsa ta tashi zaune har wani ɗan russunawa take yi kamar tana gaban Momy, Momy ta ce ba wata damuwa ko? Ta ce a'a ba komai, ta ce yana kula dake ko? Eh yanayi Momy nagode. Ta ce To ki kula min dashi kinji ƴata kada ki damu namiji tamkar yaro ne yanda kika saba mishi zai ɗore mishi na yaba da tarbiyyar ki, kuma nasan zan samu jikoki masu albarka. Ta ce nagode Momy, ta ce to bashi phone ɗin, ta miƙa mishi suka ci gaba da magana kan abin da ya shafe su,yana ajewa wata wayar ta soma ringing tana kallonshi yaƙi ɗaukar wayar,har aka dena kira suna zaune shiru har uku da rabi ta duba lokacin sallah ya yi nan ya zube mata komai wayoyinshi da makullin mota ya tafi a ranta ta ce ƙila yana da mota ne a nan tunda taga itama da tazo, zuwa aka yi aka ɗauke ta.
Wayoyinshi suka shiga ringing tana É—auka tana gaya musu yaje sallah,can wannan wayar ta É—azun ta É—auki ruri taga an sa my wife ta ce dama wayace ba matarka ba ce? Sai da wayar tayi sau uku tana katsewa taga yakamata ta É—auka ko itama zataji yanda ta ji.
Ta ce "Hello who is on the line." Daga can Zainab ɗin ta ce matarshi ce,ke wacece ki ka ɗauki wayar mijina? Abin ya ɗan sosa ma Ruƙayya rai, ta ce Ok mijinki ya shiga wanka in ya fito me za'a ce mishi? Zainab ta soma masifa ke wacece ina tambaya? Ruƙayya ta ce in baki da saƙo in kashe wayar dan in muna tare dashi bashi ba ɗaukar wayarki tun ɗazun kike damun mu. Sai ki bari sai naga dama ya dawo." Ta kashe wayar.
Zainab ta kira Mamanta ta ce Hajiyata aiki bai yi ba, yanzun fa yana gurinta har tana É—aga waya ta tana gaya min magana.
Hajiya ta ce "amma yana miki wulaƙanci ne?" Ta ce a'a sai dai jiya ne ta kira shi muna tare shine da ya shiga wanka na gaggaya mata magana shine fa ya ƙwana yana masifa, ta ce kinyi amfani da duk kayan da ƴar Nijar ta baki? Ta ce sosai ma bakiga yanda yake fita haiyacinshi ba idan muna tare, ta ce to ki dage kafin ta shigo ki riƙe shi gam, ta ce to ki koma wajen malamin, Hajiyar ta ce ki dai tanadi kuɗi yana baki ko? Ta ce tam ko bai bani ba ai zan ɗiba kuma ba ganewa yake ba naga kamar sun mishi yawa, suka sa dariya har da shewa tamkar ƙawaye.
*** *** ***
Shi kam Dady har dare yana can sai dai ya yi sallah ya dawo, shi ya nemo musu abin da zasu ci,ita kam gimbiyar ƙin ci tayi yana gurinta har sha ɗaya tamkar kada ya tafi duk da basa hira, haka ya nufi masaukin shi.
Ta rungume tana tunanin shi har ga Allah ta ɗan huce,sai dai kishin ne yana damunta ta so ta auri Dadynta ita kaɗai ta kula dashi ta ririta shi ta maidashi abin sha'awa cikin abokanshi amma yanzun su biyu ƙila tana tufka waccen ta zama tana warwarewa.
Jirgin ƙarfe taƙwai zai bi dan haka ya yi sammako saboda suyi sallama,yau ya samu abokan ƙwananta dama su uku ne,ɗayar tayi mishi sannu da zuwa, duk suna sanye da kayan N.Y.S.C Pretty ɗin shi tana sanya takalmi ya shigo, sauran suka gaidashi suka basu guri itama ta ce an tashi lafiya? Ya ce yanda ki ka ƙwana nima haka kuma kin tashi da shirin zuwa aiki nima daga nan sai ofis." Ya ɗan ƙara bata baki duk da bata tanka ba yaji daɗin yanda tayi mishi addu'ar sauka lafiya. Bai koma gida ba kai tsaye ya wuce ofis, biyar saura ya shigo gida .
Zainab bata nan har ya yi wanka, Sunday ya gabatar mishi da abinci ga kuma Hollandia ya gama ya koma falo yana neman layin Pretty ya saba dan kullum sai ta tsinke sau biyu wata ran ma sau uku sannan ta É—auka.
Ya ce Pretty ko ki kira kiji yanda na sauka ko?" A ranta ta ce da kasan yanda na damu in san yanda ka je gida da baka ɓata bakin ka ba. Amma a wayar sai ta ce lafiya ai ita kesa aji shiru. Ya ce to ke yakike? Ta ɗan ja aji sannan ta ce lafiya lau, yanda take amsa mishi waya sai ya rasa me zai ce mata.
Suka yi shiru na É—an lokaci ya ce "ina labari?" Ta ce Æ´ar jarida ce ni zaka tambaye ni labari,ya ce to bani na kotu, ta ce ai ba can naje ba. Pretty me Momy ta ce miki jiya? Sai kaji,ka je ka tambaye ta."
Zainab ta shigo sanye da riga da siket sun ɗameta, ƙaramin gyale a kafaɗa hannunta riƙe da jaka da key ɗin mota ta zauna tana faɗin ka dawo ne ashe?" Bai tanka ta ba ya cigaba da wayarshi.
To Pretty tsakanina da ke ai akwai sirri, ta ce to ba san jin kake yi ba, ya ce to ki ɗanyi kissing ɗina I miss You,ta ce "bata nan? Tai maka mana." Zainab taja tsaki duk da bata jin me Ruƙayya ke faɗi tasan maganganun soyayya ne. Ya yi kissing ɗin wayar Ruƙayya ya kashe. Dariya ya saka ganin ya soma ciyo kanta.
Ya tamke fuska sannan ya dubi Zainab
"Ina kika je?" Ta ce a'a gida mana Hajiyata keson gani na." Ya ce shine bazaki nemi izni ba" ta ce tun jiya kaki ɗaga wayata don kana tsoron ƴar gold kada tayi fushi, ya ce shine kika fita ko? To bazan ɗauka ba, ta ce "duk inda zan je sai na gaya maka sai kace auren gargajiya?" Ya taso da faɗa kamar zai bugeta, ya ce ke jahilar ina ce? Wato har ma aƙwai auren gargajiya, to ban san shi ba,in Hajiyar ta koya miki to bazan ɗauka ba,be carefull zanyi maganin ki." Ya fita ta ce borin kunya dan yaga yaje ya ƙwana da waccan ƴar iskar,kai ma sai nayi maganin ka."
*** *** ***
Ƙwanci tashi su Ruƙayya sun gama sabis farin ciki ba wanda ya kai Dady tun ranar da ta dawo baya ma ƙasar yana Italy. Amma ya soma maganar biki,yana dirowa ya yi wanka sai Kabala.
Affa ya samu dan yasan in takan ƴar rigimar tashi ya bi sai ta dinga kawo mai uzuri,sun yanke sati biyu sannan ya sameta da maganar, ta ce ita wata biyu sai ta huta in kuma ya matsa mata sai ta fasa tarewar gaba ɗaya,ai dama dole akai mata, ya bata haƙuri tare da cewa ya yarda sai nan da wata biyun.
Ashe anyi rashin sa'a Umma ta ji,yana fitowa tsakar gida ta fito daga ɗaki tace kaje ka cigaba da shiri Yusuf sati biyun da kuka tsaida ba ƙari.
Bayan tafiyarshi ta yi ma Ruƙayya ta tas tare da cewa sai ta haɗa ta da Affanta nan ta shiga bata haƙuri tare da cewa ta yarda.
*** *** ***
Shiri ba kama hannun yaro duk ɓangare biyun, Ruƙayya ta taka har Katsina, Zaria ta gayyato ƙawayenta na secondary su Amira,su Munira da Armaya'u ba zama ita sati biyu ne tsakanin ta da Ruƙayya za'ayi nata su Yaya Murja da Fati ana ta shirin yanda bikin zai kasance ya yin da su Yaya Sadiya manyan yayye ana ta shirya Auta. Kowa faɗi yake tana da kishiya Mom ɗin su M Bash tazo ta ɗauki amarya dan kimtsi na musamman.
Ƙwananta biyu tai ƙyau ta gyaru har ita kanta tana jin sha'awar mijinta,tana ba su M Bash labari suka yi ta mata dariya ta ce ni tsoro nake kar yaje ya rakwaɓani a banza gara shi yana da wata.
Gefen Dady daga Kaduna har Abuja ya hana jama'a sukuni, gidajenshi ma sun san Pretty zata shigo an gyara ko ina sashenta ya zuba komai.
Zainab ma ya canza mata amma tana ta mita wai amaryar daya gama da ita tun a waje shine yake rawar jiki, ya ce mata ai Pretty ba irin ki bace ke dai dana taya tun a wajen da kin bani, sannan koda ban taya ba ai kin bama wasu. Ranar tayi kuka kuma tayi data sanin yi mishi wannan maganar.
An kawo aƙwatuna har goma sha biyar Affa ya kirashi yana faɗa ya ce kamar hauka? Gashi shine ya yi musu Anko. Bayan su launching, dinner, walima da sauransu.
*** *** ***
Amarya ta tare ɗakinta dake nan Kaduna gidan da Dady ya ƙera cikin gidan su. Bayan an kaita wajen su Momy aka basu amanar ta, aka maida ta ɗakinta kowa ya watse sai ƙawaye,Angwaye sun shigo har da Nuraddeen wanda shima ya rikiɗe ya koma abokin ango maimakon na amarya.
Anyi ɗan wasa da dariya anguna sun bada kuɗin da su Armaya'u suka buƙata na siyen baki, Al-Mustapha yaja Munirar shi suka nufi masaukinshi,ya yin da Ruƙayya ta riƙe Armaya'u wai sai ta ƙwana.
Da ƙyar ta ɓanɓareta ta gudu, Dady yazo yana lallashin ta dama tun da aka soma bikin kuka take yi musamman ranar da iyaye sukai mata huɗubar zaman aure idonta sai da ya kumbura saboda kuka.
Zahiri Ruƙayya tana da tsoro don haka koda Dady ya ce Pretty yo alwala mu gabatar da sallar ma'aurata sai ta ce mishi tana fashin sallah sannan ta ƙi yarda su ƙwanta tare, dole ya bar mata ɗakin,ba dan yaso ba,sai don kada ya ɓallo rikicinta.
Da safe bayan ta sheƙa ƙwalliya da super mai jajayen fulawa ta wuce Dady a falo ta nufi gefen su Momy, shima ya biyo ta yana cewa shine kika wuce ni? Sai ta nuna bata ganshi ba a zahiri kuma ta ganshi waya taji yanayi da Zainab, Momy ta ji daɗin ganinsu haka Dad a can suka yi break sannan suka dawo.
Kusan sati ɗaya kullum Pretty ta ce tana al'ada daya fita sai tayi sallanta, ranar da suka cika ƙwana goma tana ƙwance a falo hannunta riƙe da littafi tana dubawa, Yaya Fati ta bata shi ta ce zai taimaka mata zaman aure.
Dady ya fito sanye da jeans baƙi haka riga, ta kalleshi tana matuƙar son shi sai dai kishi, ya yi mata ƙyau.
Ya zauna kusa da ita ya ce "Pretty har yanzu baki fara sallah ba?" Ta ce lafiya ta qalau haka nake kayana. Ta cigaba da karatun ta, ya ce ko dan baki sona ne shine kike guduna?" Ta ce "zan ƙi yin sallah dan kai ne?" Ya ce ai Allah yana kallon ki fa,bata tanka ba.
Da dare ta fito wanka ta kulle ƙofa sannan ta tada sallah tana tahiyar ƙarshe taji shigowar shi ya yi amfani da wani key ya shigo, gabanta ya yi muguwar faɗuwa ya wuce ya gadonta ƙwanta ya ɗauki littafin da take karantawa mai suna 'TAWA TA SAME NI' yana dubawa tayi sallama kana ta sake tada kabbara. Yana kallon tayi ta sallah tun yana ƙirgawa a ranshi har ya daina. Ya tashi ya shiga toilet shima ya ɗauro alwala daidai tayi sallama ya ce Pretty biyoni jam'i gara in taya ki ko zakiyi saurin gamawa.
Raka'a biyu suka yi har tayi mamakin yanda Dady ya dinga jero musu addu'a ya ce Pretty ta so,taƙi tashi ya kamata ya cire hijabin daga ita sai ɗaurin ƙirji ta ce meye haka Dady bana so fa, ya ce haba Pretty kiji tausayi na ki tuna baya ki tuna dadynki nasha wuya kanki, ta ce "Ni nace ban son ji baka wani sona."
Ya dubeta"ina sonki ina ƙaunarki, nafi son ki da kaina,ki tuna baya." Ta ce kai dai kana son jikinane kawai, ya ce kinyi kuskure,na fara sonki tun baki girma ba,na so ki lokacin da baki mallaki komai na ƴa mace ba, baki da komai na soki badan ƙyaunki ba badan dukiya ba,badan cikar halitta ba, ya ƙara sassauta murya "Nasan da kin soni yanzun ban san me nayi miki ba." Ya ɗaga yatsun shi guda biyu "kalli zoben alƙawarinki yana cin jikina ban cire ba,ban ci amanar ki ba,ki bari mu fahimci juna. Tana shirin magana bakinshi yasa cikin nata ya shiga nuna mata wasu kalolin soyayya masu zafi da gaggawa tana son shi don haka bin shi tayi suka lula. Sai da tafiya ta soma nisa sai ta kasa tsoro ya shige ta ta soma faɗin "yi haƙuri Dady, don Allah ka barni,ba zai iya ba tunda ya jima yana jiran wannan rana, da zafi zafi yake nuna mata soyayyarshi don haka tayi mata nauyi gashi tasha gyara, wannan dalilin yasa tasha wahala ga Ruƙayya da son jiki ko allura bata so amma ganin babu sarki sai Allah nan da nan ta haƙura Dady ya kusan fanshe wuyarshi a kanta. Ta wahalu ƙwarai saboda...........
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
[8/21, 06:53] Ummi Tandama😇: *FIN ƘARFI BOOK 3*
*LITTAFIN*
*HALIMA ABDULLAHI K MASHI*